Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Group Hausa novels and fashion Group Cool novel, makeup and kitchen1 Group And WOMEN24 TV Group WHATSAPP NO:+2349030159301 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 1* *Barka da sallah da fatan kowa yayi sallah lafiya*??? ****** Manyan motocine bak'ake guda biyar a jere da juna, suna tafiya a kan lafiyayyen titi wanda yaji kwalta sai jiyaniya kakeji Tana tashi " Wanda motar jami'an tsaroce Suka rako yarima sauban domin Kula da lafiyarsa." A katafaren wani babban gida Mai girman gaske mai d'auke da kwalliyar sarauta a jikin gidan duk wanda yaga gidan yasan gidan sarauta ne dibo da yanayin gidan da kuma fadawan dake, gadin get din kofar gidan, Idan ka diba KO wanne yana sanye da uniform dinsa blue tare da Dan sirkin ja a, jikinsu, gidan adalin SARKI ne maiji da mulki da k'asaita." Fadawa dake gadin get d'in k'ofar gidan zasu Kai kusan su ashirin ko wanne da abinda yake Kula dashi a wurin, Suna jiyo jiniya da sauri ko wannensu ya mik'e tsaye jiki na rawa Suka bud'e get sai murmushin farin ciki sukeyi tare da d'agawa motocin hannu cike da farin ciki, sai da motocin Suka gama Shiga cikin gidan gaba, d'aya snn suka rufe get d'in, Suka runtuma su dukansu sukabi bayan motocin suna zubawa yarima Sauban kirari." jiniya tare da kid'e kid'e da bushe bushe ya karad'e gidan sarautar ga baki d'aya Wanda duk, wani halitta dake rayuwa a cikin gidan yasan yarima sauban ya iso mahaifarsa." Da gudu sarkin gida ya Isa fada ya durk'usa a gaban maimarba sarki Abdullah ya Kai gaisuwa gareshi cike da, girmamawa tare da yimasa Albishir na isowar yarima cikin k'oshin lafiya." Murmushi sarki yakeyi Yana girgiza kai, Wanda duk Wanda ya kalli fuskar sarki kasan, yana cikin farin, ciki d'ansa Wanda yafi soyuwa a ransa ya, dawo, cikin k'oshin lafiya, , fadawa suka shiga cewa sarkin gida, "sarki yaji dad'in wnn Albishir naka, sarkin yayi murna, sosai, tukuicin ka na musamman ne a wurin sarki Mai Adalci." "Runsunawa sarkin gida ya Kuma Yi Yana "fad'in godiya nakeyi Allah ya k'ara Nisan kwana, da lafiya, Snn ya tashi ya fita cikin sauri yanufi sashen fulanin sarki domin y Kai mata Albishir d'in dawowar sauban." Cikin saurin masu Kula dashi suka fito daga motar da suke, suka zagaye motar da yake ciki sai da aka d'auki kusan minti biyar suna zagaye da motarsa snn suka bud'e Masa ya fito, duk da dama hakan Al'adarsa take baya saurin fitowa a mota da zarar anyi parking sai ya d'auki kusan minti biyar a ciki snn yake fitowa." Saboda tsaro😎 Kyakkyawar K'afarsa yafara zurowa a waje Mai d'auke da rufafin talkaminsa masu tsananin kyau, duk Wanda yaga yanda ya fito da k'afar sa a waje yasan mamanlakin k'afar ya Kai k'arshe wurin had'uwa da gayu, cikin k'asaita ya Kuma ziro k'afarsa d'aya sai da a kuma d'aukar minti biyu snn, Cikin isa da mulki yafito da gangar jikinsa daga motar, subahanallah tsarki ya tabbata ga mamanlakin wnn halitta, Dogone Mai matsakaicin tsawo fari ne fes, kakkaura Mai cikar halitta, fuskarsa Tana zagaye da saje Mai had'i da gashin Baki Wanda ya kwanta luf a fuskarsa ya k'ara yiwa fuskar k'awanya da adon kyau, hancinsa dogone har baka yana da manyan idanu, tare da d'an k'aramun bakinsa, fuskarsa Tana d'auke da murmushi Domin Yana cikin farin cikin ganinsa a cikin k'asarsa ta haihuwa wato Nigeria." *SAUBAN KENAN D'AN SARKI ABDULLAH* Busa Kakeji tak'ara tashi tare da kid'e kid'e Ana zuba Masa kirari tare da yimasa sannu da zuwa a Nan take harabar gidan sarautar ta cika da kuyangi da bayi tare da fadawa ko wanne sai kawo gaisuwa yakeyi cike da girmamawa Murmushi kawai yake sakar masu tare d'aga masu hannu Alamar ya Amsa, Kasancewar Sauban mutum ne Wanda baya wulak'anta nak'asa dashi, snn yana daraja d'an Adam musamman bayinsa da kuyanginsa da duk Wani Wanda yasan yana k'asa dashi, Dan hakan suma suke matuk'ar son sa suke gurmamasa tamkar sarki dake mulki, snn suka bi bayansa sukayi masa rakiya har zuwa sashensa." Hakince take akan kujerarta ta sarauta wacce tazo da ita tin daga gidan mahaifinta, da gudu d'aya daga cikin bayinta tashigo ta Kai durk'ushe a gabanta tana fad'in "ranki ya dad'e Allah ya taimakeki ya k'ara maki lafiya da Nisan kwana ya uwar gijiyata nazo maki da Albishir Mai dad'i, jarumin mijinki d'a d'aya tamkar da dubu kyakkyawan mijinki Mai cikar Kamala da haiba mai kyawawan halayya irin naki, a yanzun nan ya dawo daga k'asar England ranki ya dad'e na ganesa da idona yanzun nan ya nufi b'angarensa duk wannan k'id'e kid'e da bushe bushen da kikeji duk shi akeyiwa Ana tayashi murnar dawowarsa." Tsawa matashiyar budurwar Wanda bazata wuce shekara 25 ba, ta daka mata cikin d'aga murya tace "yimun shuru rufemun bak'in bakinki mummuna kawai marar kyawon gani tabbas yau sai kin fuskanci hukunci Mai tsanani a gareni tinda har kike iya durk'usawa a gaban idona ki dinga zanyanomun suffar mijina tare da yabonsa, Hakan ya nuna a duk lokacin da Kika gansa sai kinbishi da ido kina k'are masa kallo kina masa kallon k'urullah, kina kallemun shi tes tin daga k'asansa har samansa." shin ko kin Manta ban had'a yarima da kowa ba? Shin ko kin manta da Nasha fad'a maku da zarar kunga fitowarsa ko wacce daga cikinku ta rufe idonta kada ta kuskura ko sawon k'afarsa ta kalla bare a Kai ga kayan dake sanye a jikinsa." Ta nuna mata wani fili dake can bayan sashenta nesa da ita sosai filine Wanda ba komai a cikinsa sai itacen mangwaro da gwaiba tare da iccen bedi Wanda ya rufe wurin ruf ko wacce irin halittar k'waro mai cutarwa zaka iya samunta a wurin kasan cewar ba kowa yake zuwa wurin ba, Ta nuna mata wurin tace "a can Zaki dinga kwana har tsawon sati d'aya batare da anbaki abinci ko ruwan Sha ba, snn kada ki kuskura nazo wurin na tarar da kwarar ganye d'aya ya fad'o k'asa batare da kin d'aukeshiba." Runsunawa tayi tana fad'in tuba nakeyi ranki ya dad'e godiya nakeyi Allah ya k'ara girma da d'aukaka, snn ta tashi tanufi wurin da aka umurceta tana tafiya tana sharar hawaye domin tasan dolene ta aikata abinda uwargijiyarta tasakata Wanda tasan da zarar tashiga wurin mutuwa kawai zatayi domin batasan iya abinda zata tarar a wurin ba " Yana shiga harabar b'angarensa ya d'agawa fadawa hannu alamar su dakata cak suka tsaya tare da runsunawa cike da girmamawa snn yayi masu nuni akan suyi tafiyarsu, Cikin sauri suka juya suna fad'in kahuta lafiya yarima mai jiran gado, suna zuba masa kirari suka bar wurin, Wanda ya dad'e da shigewarsa sashensa. " K'ofar bithdrom d'insa ya tura yashiga komai yana nan a gyaransa tsaf tamkar yana rayuwa a cikin d'akin Wanda yasan aikin Amintattun bayinsa ne masu kula da b'angarensa tare da abincin sa. " Ajiyar zuciya ya sauke ya kai kwance akan lafiyayyan gadonsa Wanda yaji zanen gado na Alfarma, yashiga furta Alhmdulillah tare da kai hannunsa a fuskarsa yashafi sajen dake kwance a kan kyakkyawar fuskarsa har, zuwa gemonsa ya lashe leb'onsa na k'asa tare da lumshe idonsa yashiga tunanin rayuwarsa ta, baya tare da, rayuwar da akeyi a cikin masarautar nan tare da dalilin tafiyarsa, England. " Doguwar ajiyar zuciya ya sauke Tare da mik'ewa tsaye ya soma cire kayan jikinsa domin ya d'an watsa ruwa ya shirya ya tafi fada domin gaida maimartaba mahaifinsa Bayan ya kammala yin wankan ne yafito d'aure da towel hannunsa yana d'auke da d'an k'aramun towel yana tsane ruwan jikinsa zuwa kansa, Turo k'ofa akayi cikin isa da k'asaita ba tare da anyi sallama ba aka shigo, K'amshin turarenta ya tabbatar masa da wacce tashigo, masa d'aki a dai dai wnn lokacin, Ransa yab'aci matuk'a da rashin yin sallamarta, wato har yanzun saudat tana nan da halinta bata sauyawa ba, shi har ga Allah ya manta da yana da wata mata a rayuwarsa." Saboda Sam ya tsani halin saudat da duk wani mai hali irin nata, Ci gaba yayi da abinda yakeyi yayi kamar bai san tashigo d'akinba. " Tsaye tayi wuri d'aya ta hard'e hannayenta a k'irji tana k'are masa kallo sama da k'asa cike da burgewa tare da sha'awa mai cike da so da k'aunar gwarzon mijin nata, amma isa da mulki tare da girman kai da takeji yana mata yawo ya hanata zuwa ta tunkareshi domin tayi masa sannu da zuwa tanajiran sai ya farayimata magana snn." Jallabiyarsa ya d'auka ruwan madara yasaka tare da fesawa jikinsa turarensa mai dad'in k'amshi ya d'auki wata kyakkyawar leda wacce ya ajiye wuri d'aya da alama wani muhimmin abune ke cikinta ya zura talkaminsa ya rab'a ta gefenta zai fita. " Gabansa ta sha tana kallonsa tana murmushi cikin k'asaita take fad'in haba sadaukina sai kace baka ganniba, bayan kasan wurinka nazo, kaddai ace har yanxun halinka yana nan baka canzaba, Ko ka manta da cewa ni matarkace ta sunnah wacce katafi kabarni shekara d'aya KO waya baka mun bayan kasan Ina sonka Ina cike da kewarka." Kallo d'aya ya mata ya kuma tanke fuska ba alamar wasa a tare dashi ya sanya kai yayi ficewarsa ya nufi fada wurin maimartaba. " Sarkin gida a gaban fulani a durk'ushe yana kwasar gaisuwa, "Ranki ya dade Allah ya k'ara maki lafiya da nisan kwana, sarauniya a wurin sarki gimbiya a wurin sarki kece mai mulkin masarauta daga sarki saike wani Albishir naxo maki dashi "d'anki yarima Sauban ya sauka lafiya yanzun hakan yana cikin masarauta yana hutawa. " Gaban fulani ya fad'i tayi saurin mik'ewa daga kishin kid'en da take zuwa zaune, a nan take ta had'e fuska, Ta juya ta kalli sarki gida cikin k'asaita tace "bani labarin yanda ka gansa " Sarkin gida ya saki murmushi ya kuma gyara zama yace "ranki ya dade yarima ya k'ara fari ya k'ara k'iba da cikar kamala dakin gansa kinsan yana cikin kwanciyar hankali da walwala. " Tsawa ta daka masa tace "yimun shuru bashi na tambayeka ba, Tanuna masa hanyar waje tace tashi kafita. " Jiki na rawa sarkin gida yafita yana mamakin fulani KO dai akwai wani abin da yake faruwa ne da ita? . " Cikin fushi da bak'in cikin abinda yarima ya Mata tashiga b'angarenta, ta zauna akan kujerarta ta mulki, A nan take bayinta suka zagayeta KO wacce tashiga yimata hidima, a can mai kula da kayan marmarinta tashigo d'auke da tire na kankana tare da Apple ta durk'usa k'asa ta ajiye a gabanta ta yanko kankana tare da sunkuyawa tabata tace "ranki ya dade gata kisha idan kina da buk'ata. " Wani irin wawan kallo ta wurga mata ai bata bari ta sauke hannunta ba ta d'auke mata fuska da Mari tare da kifa Mata tiren kankanar a jikinta, tana fad'in tashi kifita Dan ubanki na fad'amki Ina bukata ne?" Mik'ewa tayi jiki ba kwari tashiga tsince duk kankanar da ta zube, tafita tana sharar hawaye tare da tsinewa hali irin na gimbiya saudat matar d'an sarki Sauban 'ya ga sarki Abdul'rahaman sarkin Bauchi Amini ga sarki Abdullah mahaifin sauban sarkin da ke mulkin Adamawa. " *labarina k'irkirana nayi mallakina ne idan kikaji yayi dai dai danaki to akasi aka samu* *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ *Page 3* *Wai meyasa kukeyimun hakan ne, wasu da yawa suna Bina prv akan sunaso suyi rigester wnn littafin, bayan nariga da tun farko nafad'a maku cewa wnn book din bana sayarwa bane kyauta ne barka da sallah ne ga duk wasu masoyana masu bibiyar labaraina, pls Dan Allah ku daina Bina prv kunacemun kunaso kuyi rigester, ku kwantar da hankalinku tunda na lura da kud'in hannunku k'aik'ayi suke maku zanyi maku littafi na kud'i Amma ba wnn ba, wnn kyauta ne fatana kubani had'in Kai wurin yimun comment domin na fahimci sak'ona Yana zuwa yanda nakeso ngd*👏🏻👏🏻👏🏻 ***** Runsunawa yayi cike da girmamawa da biyayya yace "nagode Ranka ya dad'e insha Allah zan kiyaye duk abinda ka umurceni dashi." Murmushi sarki yasaki Yana kallon d'an nasa Wanda yafi soyuwa a cikin ransa, ya girgiza kai, tare da furta Allah yayiwa rayuwarka Albarka Sauban." "Ameen Sauban yace snn yafita daga fadar ya nufi b'angaren Fulani." A kishingid'e ya tarar da ita akan kilishinta tayi matashin Kai da titimi Mai adon gaske, tana ganin shigowar Sauban tasaki wani irin murmushi sai da ta d'auki minti biyar snn ta tashi zaune cike da yanga da k'asaita ta dubi sauban tana jiran ya Kai durk'ushe a gabanta ya kwashi gaisuwa kamar yanda ake mata, sai ganinsa tayi yaja wuri d'aya ya zauna tare da tsureta da Ido kamar Wanda yake karantar wani abin a tare da ita. Bak'in ciki da takaici suka rufeta, wato Yana nufin ita zata Fara yimasa magana kenan a matsayinta na sarauniya, to Yake ta gaidashi ko meye Yake nufi, ta lura da yanda Yake wani ji da kansa da nuna Isa da mulki kamar shine sarki gaba d'aya, ta K'ara kallonsa a karo na biyu wnn karon Ido cikin Ido sukayi dashi suna kallon juna ko wannensu da irin kallon da Yake jifar d'an uwansa, a Nan take taga y Kara yimata wani kwarjini, Cikin ranta tace tsinanne kawai Mai halin uwarsa, saurin kawar da bintu nayi Amma bintu Bata mutuba domin tabarmun dafinta Wanda yafita fitina, Ta Kuma kallonsa na karo na uku tace a ranta ai nasan idan zamu kwana a Nan bazaiyi mun maganaba idan bani nayi Masa ba, Cikin dakiya da k'arfin Hali tace "barka da zuwa yarima, da fatan ka sauka lfy." "Lafiya k'alau yace a tak'aice, snn yace "Banga sadeeg da Sageer ba. Yi tayi kamar bataji abinda yace ba, a ranta tana fad'in d'an rainin wayo ko kagansu me zakayi masu bayan ka k'ara Tula masu haushi a ransu, Yasan taji abinda yace yasa bai Kuma yin maganaba illah yaciro wayarsa domin ya diba Miss call din da akayi Masa a lokacin da Yake fada a gaban mahaifinsa, Ganin sunan babban Amininsa Kuma abokinsa Wanda suyi fad'a suyi dad'i wato SAFWAN, murmushi yasaki domin yasan bai fad'a Masa cewar ya dawo Nigeria ba, Kuma tinda ya kwada Kiran numbersa ta Nigeria yaga yasamu yau zai Sha mita da surutu kenan Wata k'ila har kansa sai yasaka yayi Masa ciwo." Wayarsa ya mayar a Aljihu Yana k'ok'arin tashi tsaye sai gani yayi an zagaye shi da kayan abinci iri iri, kallo yabi abincin dashi, bai fasa yunkurin mikewa tsayenba, Ya kalli fulani yace "gimbiya ki huta lafiya yanufi hanyar waje." Cikin d'aga murya Mai sauti Wanda batasan tana da itaba, takira sunansa tace "Sauban baka ganin an ajiye maka abinci ne? ai yakamata ko lemu ne ka tsaya kasha idan baka buk'atar komai." Shuru yyi na d'an minti biyu yana nazarinta snn ya bud'a Baki yace "bana buk'atar cin komai a halin yanzun domin lokacin cin abincina baiyi ba, Snn Koda lokaci yayi nasan Saudat ta tanadar mun duk wani abinda nake buk'ata ki huta lafiya tare da ficewarsa ya nufi b'angaren sa Yana murmushinsa na gefen baki" Cije Baki tayi ta mik'e tsaye cike da takaicin asarar da ya janyo mata cikin d'aga murya tashiga Kiran jakadiya cikin sauri jakadiya tafito daga cikin wani d'akin takai durk'ushe a gabanta tana fad'in "gani ya uwargijyata, Fulani tace "jakadiya ya b'arar Mana da komai ya ruguzamana duk wani shiri namu, baici abincin ba yanzun meye mafita?" "Jakadiya tace "ranki ya dad'e ki kwantar da hankalinki, idan yasan wata ai baisan wata ba, na rantse maki da Allah ba wani Wanda zai hau kujerar sarki sai Sageer ko Sadeeq." Fulani tasaki murmushi ta kalli jakadiya tace "Dan hakan nake sonki domin ko shaid'an Yana tsoron sharrinki tare da muguntarki, yanzun meye mafita kinsan na kashe kud'i da yawa wurin karb'o maganin nan Amma shegen yaron Nan Mai Kama da Aljanu yasaka nayi asara." Jakadiya tace "ranki ya dad'e kibani Nan da zuwa gobe komai zai Kai k'arshe, Fulani ta Kuma sakin murmushi tace "tashi kitafi Nima akwai abinda nake sak'awa Nan da zuwa goben." ******************* Wani irin mulki takeji Yana mata yawo a cikin jinin jikinta sai juya bayi da kuyangi takeyi yanda ranta yakeso, duka k'afafunta biyu suna kan d'aya baiwarta wacce tafi tsana duk a cikin bayinta saboda bak'in da take dashi gata gajeruwa gata da k'aton Baki, A rayuwar Saudat ta tsani tayi Ido biyu da bak'in mutum ko marar kyan mutum tafison duk abinda zatayi Ido biyu dashi ya zamana Mai kyaune, Dan hakan ta tsani wnn baiwar tata." Baiwar sai zufa take had'awa tagaji iya gajiya sabida gaba d'aya ta sakar mata nauyin jikinta, Sauran bayin Kuma sai hidima suke mata cike da taka tsantsan gudun kada suyi laifi." Cike take da Jin haushin Sauban, hak'urinta ya kusa ya k'are a kan me Dan yaga tana sonshi, shine yake mata duk abinda yaga dama, itama fa jinin sarautace 'yar sarkice 'ya d'aya tilo a wurin mahaifinta, Yanda mahaifinsa yakeji dashi itama hakan mahaifinta yake ji da ita, duk wani abinda yakeji game da sarauta tamafishi jinsa domin sarautar masarautarsu tafi sarautar masarautarsu nuna mulki da Isa, yau kam ta shirya Masa duk abinda za'ayi sai dai ayi Amma tagaji da neman mata 'yan uwanta namiji takeso Kuma mijinta." Kuyangarta tashigo da gudu ta durk'usa a gabanta tace "ranki ya dad'e ankawo sabbin bayi 'yan mata ne wad'anda komai yaji a tare dasu nasan zakiji dad'in ma'a mala dasu sosai." Mari ta kwad'a mata a fuska har sau biyu tare da sanya k'afa tayi shuri da ita, sai da kanta ya daki wani tebur Wanda kayan fruit suke a jiye a kansa, cikin d'aga murya Mai cike da Jin haushi tace "bana buk'ata tashi kifita, Ta sauke k'afarta daga kan jikin baiwar tata, ta mik'e tsaye a fusace tanufi b'angaren Sauban." Zaune yake akan lafiyayyen gadonsa da waya a kunnensa Yana magana da Safwan yana fad'in "inajinka kasan fa banason surutu kafa kiyaye, Safwan yace "eh zakace hakan tinda kana kusa da gimbiya Saudat ni wlh Sauban kabani mamaki ace kadawo ko waya bazaka iya yimun ba ka shaidamun kadawo da Ban kirakaba da shikenan, Allah wnn halin naka ya kamata ka canza shi, Murmushi Sauban yayi tare da dafe Kai domin kansa ya Fara Sara Masa akan surutun Safwan yace "kaga yanzun dare ne inada buk'atar hutu gobe kazo zamuyi magana." Safwan yace "kace hakan jarababbe asha soyayya lafiya, Mere Baki Sauban yayi yace "Kai kasan abinda ake nufi da hakan, ni bansan hakan ba, Safwan yasaki dariya yace zaka sani ne ai, Da sauri Sauban ya kashe wayarsa domin kada ya Kuma damunsa a surutu." Wnn karon da sallama ta shigo d'akin, Wanda Sauban da yake zaune a kan gado sauke wayarsa kenan akan kunnensa ya d'aga Kai ya dubeta tare da amsa mata sallamarta." Ido ya zuba mata Yana kallonta, itama shi d'in take kallo anan take taji duk wata tsewa da rashin mutumci da tazo dashi ta nemesa ta rasa, domin ba k'aramun gwarjini ya mata ba." Kusa dashi ta nufa ta zauna a gefen gado a inda yake zaune k'afafunsu suna gogar na juna tace "Sadaukina lokacin cin abincinka fa yayi, Ya kamata a gabatar maka da komai." Shuru yayi bai amsa mata ba, Yin Shurunsa hakan Yana nufin Yana buk'ata kenan, ta mik'e cikin tafiyarta Mai cike da k'asaita da yanga tafita, da kanta ta had'o Masa duk wani abinda tasan yana buk'ata domin Bata barin bayi ko kuyangi su tab'a abincin mijinta domin tana tsananin kishin mijinta Bata son kowa ya rab'eshi sai ita kad'ai Gabansa ta dire Masa komai tare da zuba Masa farfesun kifi da fresh milk Mai sanyin gaske, sai da ya d'auki minti uku snn ya mik'a hannunsa da niyar zai d'auki kofin ya Kai bakinsa, tayi saurin sanya hannunta ta d'auka ta mik'a masa kallo Ido cikin Ido sukayiwa juna Sauban yayi saurin kauda idonsa daga kallonta snn ya amshi kofin ya Kai bakinsa Yana kurb'ar milk d'in, Sai da ta tabbatar da yaci komai ya k'oshi snn ta had'a kayan da kanta, tafita dasu waje, Ido yabita dashi Yana kallonta har zuwa lokacin da tafita daga d'akin , Yashiga tunani a ransa, indai kyaune Saudat kyakkyawace ajin farko domin babu inda Allah ya rageta, sai wuri d'aya zuwa biyu." Na farko shine Sam Bata da hallaya na gari akwaita da wulak'anta d'an Adam, d'ayan Kuma sirrinsa ne shi kad'ai yasan komeye, shi dai har yanzun yakasa jin wani abin Dan gane da ita yasan tana sonshi tana kishinsa Amma shi Sam bayajin hakan akanta, asalima wani lokacin jiyakeyi ya tsaneta musamman idan yaga yanda take wulak'anta bayinta da kuyanginta, tana son kasancewa tare dashi shi Kuma bayajin hakan a tare dashi, Hasalima idan ya tilastawa kansa dole sai ya kasance da ita Domin sauke nauyin da ya rataya a wuyansa jinsa yakeyi baya samun wani gamsuwa bare biyan buk'ata a tare dashi illah ma ya Kuma janyowa kansa wani sabon ciwon Mara Wanda yake fama dashi a koda yaushe Dan hakan. Yake yawaita yin azumi tare da Shan lemun tsami a cikin ruwan Lipton d'insa" Dogon tsaki yaja ya mik'e tsaye tare da cire kayan jikinsa ya d'aura towel yashiga toilet Domin ya watsa ruwa yayi Shirin kwanciya bacci." wasu fitananun kayan bacci tasaka a jikinta wad'anda suka fitar mata da sigar jikinta tasan komai jarumtar Sauban sai ya firgita yafita hayyacinsa idan ya ganta a cikin kayan baccin Nan, Ko wanne lungu da sak'o na jikinta sai da tabishi da turare domin Saudat akwai son k'amshi ga tsafta, Doguwar Alkibba tasaka ta rufe jikinta snn ta juya wurin 'yan matan dake kwance a d'akinta su biyar, d'aya daga cikinsu har ta Fara yimata kallon K'ululla tana had'iyar miyau dukansu kyawawane Yan mata ne masu cikar halitta bayine take zab'owa take sanyawa a gyara mata su Tana ajiyesu a d'akinta domin biyan buk'atarta. Wnn d'alibi'ar ta dad'e tana aikatata tin a England a inda tayi karatu, Ta dubesu da kyau tare da nuna masu wani d'akin tace "kutashi kushiga d'akin can domin yau bana da buk'atarku." Jiki na rawa suka bi umurninta sukayi shigewarsu d'akin snn taja dogon tsaki tafita tanufi d'akin yarima Sauban." *Mrs Ana's Bawa*😘 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 4* ****** Tsaye yake akan madubi cikin shirinsa na kwaciya bacci Yana feshe jikinsa da tsadadden turarensa Mai k'amshin dad'i." turo k'ofa tayi tashigo tare da sallama d'auke a bakinta, Idan zata shigo d'akin Sauban kawai take sallama, ko shi Dan tasan idan batayi sallama ba idan zata shekara goma a wurin bazai d'aga Kai ya dubeta ba, bare ya tanka mata." sab'anin duk inda zata sanya k'afarta a cikin gidan Bata sallama saboda nuna Isa da mulkinta gani takeyi idan tayi sallama kamar ta zubar da ajinta ne gani take ta kaskantar da kanta ne idan tayi sallama." K'amshin turarenta ya daki hancinsa Wanda yasa yayi saurin lumshe idonsa tsikar jikinsa tashiga tashi, Bai San lokacin da ya juyo ya kalletaba tare da amsa mata sallamar da tayi, Ido biyu sukayi a lokacin da ta cire Alkibbar da tarufe jikinta da ita, gaba d'aya duk ilahirin suffar jikinta ta bayya a cikin rigar baccin Wanda yasa Sauban yayi saurin cije leb'onsa na k'asa tare da kawar da kansa daga kallonta ya sauke ajiyar zuciya snn yanufi gadonsa ya kwanta tare da janyo pillow ya rungume a k'irjinsa." Murmushin mugunta tasaki Domin tasan tarkonta ya kama, Cikin tafiyarta Mai cike da d'aukar hankali tanufi gadon ta haye kai tare da matsawa daf dashi tasanya hannu ta janye pillow dake rungume a k'irjinsa ta maye gurben pillon." Runtse idonsa yayi Yana karb'ar sak'onnin da take aika Masa dasu, Wanda sai yayi yunkuren hanata yaji yakasa sakamakon yanda take sarrafa jikinsu a tare." Hakan Sauban yafita hayyacinsa Saudat sai wasanni take Masa ko wanne lungu da sak'o na a jikinsa." Ai Kuwa a Nan take Sauban ya bada kai, ya mirginata ya haye kanta yashiga sarrafa cike da kwarewa, nishin dad'i Saudat take saukewa domin mijinta gwarzone a wurin gamsar da macce sannan ya San sirrin ko wanne lungu da sak'o Wanda zai saka macce taji dad'i sosai." Shima ba laifi ya d'anji dad'in wasanni da Yake mata, Yana shigarta yaji dama yasani da bai kulataba, anan take yab'ata fuska ya had'e rai Domin ba abinda yakeji a tare da ita, Jinsa yakeyi kamar ya fad'a kwata, Ga wasu ruwa da suke fita a gabanta farare Wanda yasan ba ruwan ni'ima bane, Ita Kuwa sai ihun dad'i takeyi domin Sauban ya Kai mata inda macce 'yar uwarta Bata Isa ta Kai mata wurin majiya dad'in ba." Saman kanta yake sai tsuki yakeyi tare da yimata kallon tsana, aiki kawai yakeyi ba Dan ransa ya soba sai dan gudun kada ya sauka ya shiga hakkinta, ga wani irin ihu Mai had'e da Kuwa da takeyi Masa a kunne duk ta cika Masa kunne Jin kasansa yakeyi har ya Fara Sara Masa, Hannu yasaka ya make mata Baki tare da Jan dogon tsaki snn yaci gaba ba Dan yasoba." Sai da ya fahimci tasamu gamsuwa snn ya sauka a kanta tare da Jan dogon tsaki yanufi toilet domin tsaftace jikinsa." Nishi take saukewa Mai cike da jikin dad'i tare da farin ciki domin yau Sauban ya gamsar da ita ya wanke laifinsa na tsawon shekara d'aya da yatafi ya barta duk da dai itace tace bazata bishiba." Bayan yayi wanka tare da d'auro Alwala yafito fuskar Nan tashi a had'e ba wani alamar dariya a tare dashi, Tana ganin fitowarsa tasakar Masa murmushi ta tashi tashiga toilet din itama, Sai da ta gyara jikinta snn tafito, Tasameshi zaune a bakin gado ya rik'e kansa da hannu biyu da alamar akwai abinda yake tunani." Gabansa tazo ta durk'usa abinda Bata tab'ayiwa kowa ba a rayuwarta, ta rik'o hannunsa tare da Kiran sunansa, Tace "Sauban meyasa har yanzun baka Sona?" Meyasa ka kasa sanyawa rayuwarka soyayyata bayan kasan ni Ina sonka, Idonta ya cika da hawaye bansan dalilin da yasa Allah ya jarabeni da tsananin sonka da kishinka ba, Wanda a gaban kowa zan iya nuna hakan." Kayi hakuri da halayena domin nasan har dasu yasa ka tsaneni Amma kasani bazan iya canzawa ba domin tin tashina a gidanmu hakan Naga anayi, Amma nayi maka Alk'awarin zan canza wasu daga ciki in har hakan zai sakaka cikin farin ciki kafara Sona." Ta Kuma rik'e hannunsa tare da murzawa tace "bazan gaji da furta maka Ina sonka ba, Ina kishinka mijina domin Kai na daban ne a cikin Maza, Fatana na kasance da Kai ni kad'ai har k'arshe rayuwata." Sai yanzun ya d'aga Kai ya kalleta duk magagganun da takeyi, cikin ransa Yake furta kalmar so, So so fa take cewa a Koda yaushe tana yawan furta Masa tana sonshi to meye shi son?" Shi Sam bai sanshi ba, Kuma baya fatan yasan shi, Meye amfanin soyayya babu gamsuwa a cikinta bare biyan buk'ata." Mararsa yaji ta murd'a Masa yayi saurin cije bakinsa tare da dafe wurin, Ya kalleta cikin kasalalliyar murya yace "had'omun Lipton tare da lemun tsami." Cikin sauri ta mik'e tafita minti biyar sai gata da cup a hannunta ta mik'a masa, Amsa yayi ya soma Sha sannu a hankali sai da ya shanye duka snn ya ajiye cup d'in ya dubeta tare da had'e fuska yace zoki fita kitafi d'akinki." Yana gama maganar ya Kai kwance rufda ciki." Tasan halinshi Sarai idan yayi magana d'aya baya maimaita ta biyu idan Kuma ya fad'i magana baya canzata, Dan hakan ta d'auki Alkibbarta tasaka tafita tare da rufo Masa k'ofa." Yana ganin fitarta ya juya kwanciyarsa zuwa kallon sili mararsa saici gaba da murd'a Masa takeyi saboda rashin samun gamsuwar da baiyiba Wanda yasan sperm ne ya tarar Masa Wanda bai samu fitowa ba, sakamakon sha'awarsa da ta shi babu biyan buk'ata, Ciwon ya Kuma k'aruwa a tare dashi anan take ya dinga murkususu Akan gado Yana sauke Nishi sama sama, Can yaja doguwar ajiyar zuciya alamar yasamu sassauci kenan sakamakon lemun tsamin da yasha yayi nasarar tsinke Masa shi ya fito." Toilet ya Kuma shiga ya k'arayin wani wankan snn yafito wnn karon kasa Zama yayi sai safa da Marwa yakeyi a cikin d'akin hannunsa goye a bayansa, Tunani yakeyi dama hakan ma'aura suke rayuwar aurensu?" Dama hakan macce take?" domin shi tinda Allah ya halliceshi bai tab'a kusantar wata macce ba sai Saudat." To meye abin jin dad'i a jikin macce Wanda yakejin wasu mazan suna magana a wani lokacin sukance macce ni'ima ce, macce abar hutuwace, shin Suma hakan sukeji garesu?" Kuma har suke fad'in hakan?" Maganar Safwan ya tina da ita wani lokaci da yakira wayarsa tsakar dare Safwan bai d'aukaba, sai da aka d'auki a waya d'aya snn Yabiyo Kiran nashi, Shine Safwan yake ce Masa "meye hakan ne Yana tsaka da hutawarsa da iyalinsa Yana cikin Jin dad'i ya tsunduma cikin wata duniyar Mai dad'i Mai cike da ni'ima Amma Kiran wayarsa ya kusan katse Masa komai, Meye hakan sauban kake kirana tsakar dare?" Pls kayi sauri ka fad'i damuwarka zan koma second round tinda ka katse ni." Mere Baki Sauban yayi yace "Kai kasan wnn duniyar d'an iska kawai bakan Abu Mai dad'e da darajabane shi yasa kake fad'in hakan, snn ya fad'a Masa abinda zai fad'a Masa sukayi sallama safwan yayi saurin tsinke wayar sakamakon wani dogon nishi dayaji yasaki a cikin wayar." Mere Baki Sauban yayi Yana fad'in "a hakan shima yakeji tare da matarsa har Yake zuba mata kirari hakan?" Meye abin dad'i a ciki,da har wani lokacin safwan yake cemasa aci dad'i lafiya, musamman idan ya gane yana tare da Saudat a wuri d'aya." Yaje kan gadonsa ya kwanta tare da rufe jikinsa, Yaci gaba da tunanin iri iri a rayuwarsa, yauma komai yafi jagulewa wurin Saudat domin Ada tana d'an kamashi idan yashiga yanzun Kam a sake take ta k'ara bud'ewa, gaba d'aya ransa a jagule Yake, Saudat ta sanya komai ya kwance Masa ga wahalar da kansa tare da k'arfinsa wurin yi mata aikin da ba biyan buk'ata, *Hmmmmm ni dai nace malam Sauban macce ko ita ke mantar da sarki zuwa fada snn ita ke Kai namiji wata duniyar Mai wuyar misaltuwa wata k'ila Dan dai kawai baka dace bane, Amma irinku idan kuka samu macce Mai cikkiyar ni'ima sai kunfi Mai kura shafawa lol🤪* SHIN WAI WAYE SAUBAN WAYE SAUDAT MUJE ZUWA WANI PAGE DOMIN KUJI KO SUWAYE KAFIN MUCI GABA DA LABARIN YANZUN AKE BA'AYI KOMAI BA *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *DIDECTED TO Fateemah M Uthman* *Page 5* ****** Abdullah Abdulsalam, sarkin dake mulkin masarautar Adamawa, Wanda shima ya gaji sarautar ne a wurin mahaifinsa sarki na Tara wato sarki Abdul'aziz." Sarki Abdulsalam 'ya'ya biyu ya haifa a duniya, Abdullah shine na farko wato mahaifin Sauban kenan, snn k'anwarsa mai suna bahijja a wurin haihuwarta ta farko Allah ya mata rasuwa tamutu Bata haifi abinda ke cikintaba, ya rage sai shi kad'ai a wurin mahaifinsa sarki Abdulsalam, bayan sarki Abdulsalam ya mutu, Masarautar Adamawa ta dawo hannun Sarki Abdullah wato mahaifin Sauban kenan." masarautar Adamawa masautace Mai Adalci wacce take tafiyar da mulki dai dai yanda Addini ya tsara tare da tsantsan Adalci,da sanin ya kamata." Sarki Abdullah Yana da mata hud'u Jamila itace matarsa ta farko wato Fulani wacce 'yace a wurin wani hamshak'en Mai kud'i dake Nan cikin garin Adamawa, auren soyayya sukayi da Fulani, Wanda had'uwarsu ta kasance tin a makaranta a lokacin Yana mataki na k'arshe ita Kuma tana mataki na farko, Lokacin da yazo da zancen aurenta sam Mahaifinsa Abdulsalam bai so auren ba, domin yafison d'ansa Abdullah ya auri 'yar sarki,a Aurensa nafarko Amma Abdullah ya kafe akan cewa shi sam Jamila Yake so bayajin zai iya auren wata macce a duniya bayan Jamila." Hakan sarki Abdulsalam ya hakura ya shige Masa gaba a wurin neman auren nasa." Mahaifin Jamila yayi murna da farin ciki sosai najin cewa d'an sarki Abdulsalam zai auren 'yarsa ko ba komai za'a dama dashi a gidan sarauta wanda ya dad'e yana kutsa kansa bai samu shigaba, Snn yasan 'yarsa zata huta itama a dama da ita." Anyi bikin aurensa da Jamila lafiya aka dauko Amarya daga gidan mahaifinta aka shigo da ita cikin gidan sarauta a b'angaren da sarki Abdulsalam ya ginawa Abdullah domin ya zauna tare da iyalinsa." Tin zuwan Jamila gidan ta kyallara idonta taga yanda ake tafiyar da mulki da sarauta a Nan take abin ya burgeta domin tun farko ita macce ce Mai son nuna Isa da gadara Akan abu, to bare gata cikin gidan sarauta, Anan take ta farajin kanta tamkar itace a matsayin matar sarki, Cikin k'ank'anin lokaci ta Fara shinfid'a sarauta da mulki a gidan tamkar itace sarauniya." Ganin hakan da Mahaifiyar Abdullah tayi wato Sarauniya hajara wacce ake Kira da Hajja macce Mai dantako da sanin ya kamata duk Wanda ke cikin gidan Yana matuk'ar sonta bayi da kuyangi musamman mijinta wato sarki Abdulsalam Yana matuk'ar sonta wann dalilin yasa bai tab'a tunanin yi Mata kishiyaba domin duk wani farin ciki na rayuwa tana bashi a zamansu, Duk a cikin tarihin masarautar babu sarkin da yayi mulki Yana da Mata d'aya sai sarki Abdulsalam." Sarauniya Hajja macce ce marar son hayaniya ko Kuma damuwa, wnn dalilin yasa dataga take taken Jamila matar Abdullah Akan son mulki yasa ta Ta had'a bikin nad'a Jamila a matsayin gimbiya." Hakan kuwa akayi anyi bikin nad'in sarautar gimbiya Jamila, bayan kwana biyu duk wasu daga cikin ragamar gidan Sarauniya Hajja ta sakarwa jamila tashiga juya komai a yanda takeso, bayi da kuyangi kuwa sai yanda tayi dasu a gidan, domin gani takeyi tamkar itake mulkin sarautar, bak'in cikinta d'aya ne shine har yanzun Bata samu haihuwaba domin tasan da zarar Allah ya Bata haihuwa babu abinda zai Hana d'anta ya hau kujerar mulki." Ganin yanda take juya mutanen gidan da yanda take tafiyar da mulkin cikin gidan cike da Isa da gadara yasa Hajja tafara taka mata burki akan wasu abubuwa daga ciki Wnn dalilin yasa ta d'auko tsanar duniya ta d'orata a kan Hajja, inda takeji Ina wuta ta jefa Hajjah a ciki, koda zata huta." Akwai wani lokacin tafito daga b'angaren Hajjah tashigo d'akinta a fusace sakamakon kiranta da Hajja tayi tana fad'a Mata adaina Banzartar da abinci hakan, abincin da Yake wata d'aya a gidan sarautar yanzun sati biyu yakeyi drink's d'in da Yake sati biyu yanzun sati d'aya yakeyi ta tsawatar Mata tare da k'arb'e key d'in store d'in a hannunta gaba d'aya." Karb'e key d'in da Hajja tayi a hannunta ya Kuma sanyawa Jamila tsanarta sosai a ranta, Anan take tashiga safa da Marwan a cikin d'akinta ta Hana kowa shigo Mata d'aki, Sai tunanin abinda zata aikata domin kawar da Hajja a doron k'asa domin ganin ita kad'aice a gidan ta ke son hanata taci karanta babu babbaka a yanda take so a cikin gidan." Tana hakan Jadiyarta ta turo k'ofa tashigo cikin hanzari, Ta xube gabanta tace "ranki ya dad'e naji wani labari marar dad'in ji da sauraro Yana yawo a cikin gidan Nan cewa wai sarauniya Hajjah ta karb'e key d'in store a hannnki." Kallon jakadiya jamila tayi ta furzar da iska Mai zafi snn tace "hakan ne Sarauniya ta karb'e key a hannuna, ta nunamun ban isa akan komai na gidan Nan ba, ta nunawa jama'ar gidan ni ba abakin komai nake ba Wlh tallahi jakadiya na tsani matar nan, na rantse da Allah Da ba itace Mahaifiyar mijina Abdullah ba da tuni an Manta da tarihinta a cikin masarautar Nan." Jakadiya tace "wnn hakan Yake Amma duk da hakan ba a hakan za'a bartaba domin idan kika zuba Ido ko Mai sai dai kiga ana gudanar dashi a gidan nan, ke Kuma kina gefe kina kallo a matsayinki na gimbiya matar d'an sarki Mai jiran gado." Kallon jadiya tayi tace "meye mafita?" Dariya jadiya tasaki tace "mafita d'ayace akwai wata bokanya a can wani k'auye Wanda ake kira da k'auyen bokanya k'araba, ita wnn bokanyar babu abinda Bata iya aikatawa idan kaje Mata da buk'atarka anan take zata share maka hawayenka, Shawarar da zan Baki ya uwargijiyata itace kikawo kud'i masu yawa natafi wurin bokanyar nan nasaka tayi maki aikin da Zaki mallake komai na gidan Nan , ya zamana komai ya dawo a hannunki sai yanda kikayi dashi" Snn na Nemo mki maganin haihuwa da zarar kin haihu kin haifi d'a namiji, Kinga daga Nan sai musan yanda zamuyi mu kawar da sarki Akan kujerarsa sai mijinki Abdullah ya hau karagar mulki, Kinga sarautar duka ta dawo hannunki sai yanda kikayi da kowa dake cikin gidan nan domin kin Zama matar sarki kuma sarauniya ga Kuma d'anki yarima Mai jiran gado a hannunki." Wata irin dariyar farin ciki jamila tasaki Domin har tafara hango mijinta a kan kujerar mulki ita Kuma tazama Sarauniya, Tace "wnn shawara taki tayi jakadiya. Dan hakan nake sonki duk a cikin ma'aikatan gidan Nan, Tashiga bedroom dinta taciro kud'i masu yawa tafito ta mik'awa jakadiya tace tashi kitafi yanzun Nan kisani na mallaka komai a hannunki, idan kika zalinceni Zaki had'u da fushina domin kinsan ba kyau ne daniba, ban sassauci." Jiki na rawa jakadiya ta k'arb'i kud'in tana fad'in "Har Abada bazan tab'a zalintarkiba ya uwargijiyata ki daina ko kwanta a kaina, ta mik'e tsaye tace natafi sai nadawo." Hakan jadiya ta tafi k'auyen bokanya k'araba ta k'arb'o magani Wanda za'a sanyawa Hajjah a cikin abinci ko lemun Sha da zarar Tasha to duk abinda Jamila tace shi za'a aikata a gidan." Abinci suka shiryawa Hajja na musamman wanda yasha magani har ya gaji, Hakan Jamila ta sanya bayi suka d'auko abincin tana gaba suna bayanta a biye suka nufi b'angaren Hajjah dashi, Wanda suka sameta kishin gid'e tana cin Ayaba fuskarta cike da murmushi da Annuri kamar ko da yaushe, Tana ganinsu murmushin fuskarta ya kuma k'aruwa ta tashi zaune tana murmushi takai dibanta a wurin kuyanginta tace "kutafi ku huta saina nemeku." Cike da ladabin munafurci Jamila ta Kai zaune a gefen Hajjah tana Kai gaisuwa gareta snn ta gabatar Mata da abincin da tadaho Mata." Murmushi Mai cike da murna da Jin dad'i Hajja tayi, Tana kallon Jamila tana fad'in godiya nakeyi gimbiya Allah ya biyaki yabaku zuri'a Mai Albarka." "Ameen Jamila tace tare da janyo abincin ta Fara xubawa Hajjah a cikin plate tuwo ne miyar taushe Wanda tasan Hajja tana tsananin so." Murmushi kawai Hajjah take saukewa a fuskarta snn ta sanya hannu ta k'arb'i abincin tafaraci, Sai da tacinye tuwon dake cikin plate d'in tas snn Jamila ta zuba Mata ruwa ta wanke hannunta Tana murmushin farin ciki, Hajjah Kuwa sai Sanya Mata Albarka takeyi tare da yimasu Addu'ar samun zuri'a Domin a kullum Addu'arta d'aya ce Allah yabawa Abdullah haihuwa Mai Albarka ita dai taga 'yan jikokinta tun tana raye." Tin lokacin da Hajja taci abincin Nan Wasa Wasa yau ciwo gobe lafiya ya zamana komai na gidan sarautar ya Fara ja baya, anan take ta aika aka Kira Mata Jamila ta dank'a Mata key d'in store tare da duk wata ragamar gidan Domin taci gaba da kula da komai saboda a yanzun ba wata isanshiyar lafiya ne da itaba." Murna a wurin Jamila a lokacin abin ba'a magana, ai Kuwa a ranar sai da tayiwa jadiya kyauta ta ban mamaki, tin daga lokacin ragamar komai ta cikin gidan sarautar ya koma A hannun Jamila, tamkar itace matar sarkin." Shekarar Abdullah biyar da Jamila ko b'atan wata Bata tab'a yiba, Inda sarki yashiga damuwa sosai, shi Kuma Abdullah ko a jikinsa domin yasan Allah shike bada haihuwa ga Wanda yaso, Kuma shike hanawa ga Wanda ya ga dama, snn Allah baya tambayarka ya akayi baka haihuba, Amma idan ya baka haihuwa zai tambayeka yanda ka rik'e Amanar da ya baka, Sai dai ita haihuwa tana d'aya daga cikin kaso biyar cikin goma najin dad'in duniya, musamman a gidan sarauta." Wasa Wasa sai da Jamila ta shekara bakwai ba haihuwa ba alamarta, hankalin sarki Abdulsalam mahaifin Abdullah ya Kuma tashi yashiga nema Masa auren 'yar sarkin zamfara wato bintu, Abdullah bai san abinda akeyiba." Sai da suka kammala shirya komai na dangane da auren Abdullah da Bintu tare dashi da mahaifin bintu, har ranar d'aurin aure sai da suka tsayar snn sarki Abdulsalam ya Kira Abdullah yake shaida Masa tare da bashi umurnin ya tafi garin zamfara domin ganin matar da zai aura su fahimci juna domin aure ne ba fashi sai an d'aura, Nan da wata biyu masu zuwa." Baiyiwa mahaifin nasa musuba ko jayayya domin Abdullah yaro ne Mai biyayya da kawaici musamman a wurin mahaifansa, Yana komawa yashiga shiri washe gari yashiga jirgi yanufi zamfara, A ransa Yake sak'awa tare da Bawa zuciyarsa hakurin duk yanda yaga yarinyar a hakan zai aureta tinda mahaifinsa hakan ya ke so, baya fatan ya watsa Masa k'asa a Ido." Saukarsa a masarautar zamfara yaga tarbo da kulawa na samman anan take akayi Masa masauki a cikin wani k'ayatattacen d'aki Mai adon gaske, aka cika Masa gabansa da kayan marmari, Minti goma da zamansa a d'akin, Bintu tashigo cikin shigarta ta Alfarma sanye take da Alk'yabbarta ruwan Madara wacce tak'ara yiwa fuskarta kyau da kwarjini, bayinta suna biye da ita a bayanta tare da yimata kirari 'yar sarki jikanyar sarki matar d'an sarki Wanda zai gaji sarauta , d'anki ma sarki hak'ik'a kinyi gadon sarauta gaba da baya Allah ya taimakeki ya k'ara mki lfy Fara Mai farar aniya." Hannu ta d'aga masu, tare da juyawa ta kallesu, cikin d'aure fuska tace "Ashe banyi maku gargad'i akan kudaina yimun kirariba?" Ashe bance ku daina k'ask'antar da kanku gareniba, Nasha fad'a maku cewa ni mutumci kamar ku, Dani daku duk d'ayane ba wani banbanci a tsakaninmu a wurin mahaliccinmu to kusani wnn shine gargad'i na k'arshe da zan mku a kan hakan, kutafi sai na shigo." Snn ta nemi wuri ta zauna tare da sunkuyar da Kai a gaban Abdullah tashiga gaidashi cike da girmamawa." Kallonta yakeyi Yana murmushi Yana Hamdala wurin ubangijinsa domin Bintu ta dace da rayuwarsa kyawawan halayanta sunyi matuk'ar burgeshi, uwa uba bintu kyakkyawa ce ajin farko domin tafi Jamila komai ta kereta ta ko Ina, yashiga godewa Mahaifinsa domin ya zab'a Masa abinda ya dad'e Yana nema a rayuwarsa." Ai kuwa cikin a waya uku da sukayi a tare suka fahimci junansu soyayya Mai k'arfe tashiga zukatansu kowa ya fahimci d'an uwansa tare da yiwa junansu fatan Alheri snn Abdullah yayi Mata kyauta Mai girman yayi Mata sallama ya dawo gida cike da farin ciki." Yana sauka Kai tsaye fada yanufa wurin maimartaba cike da farinciki gabansa ya Kai durk'ushe Yana zuba Masa godiya tare da fatan Alheri, Murmushi sarki yayi irin nasu na manya snn ya dubeshi yace "Magaji da alama zab'ina yayi maka naji dad'i da ganin hakan sai kafara Shirin auren ku Nan da wata biyu, godiya Abdullah ya shiga yiwa sarki snn ya Masa sallah yatashi yafita cike da farin ciki." Rasa yanda zai fad'awa Jamila yayi, Wanda yaga yanzun kwata kwata Bata da lokacinsa Bata bashi kulawa kamar da, mulki kawai ta sanyawa gaba, Dan hakan shima ya kyaleta ya zura mata Ido, Wasa Wasa duk safiyar Allah ta waye Abdullah da Bintu sai sunyi waya tafi a k'irga a tsakaninsu wata irin shakuwa da soyayya ta Kuma shiga Wanda sukeji idan d'aya bai auri d'aya ba bazai iya rayuwa ba." Biki sai k'aratowa yakeyi Wanda ya rage saura sati d'aya d'aurin aure, duk masarauta ta d'auka yarima Abdullah aure zaiyi kowa sai murna yakeyi sunajin dad'i wata k'ila canji zai shigo a cikin gidan sarautar, duk abin Nan da akeyi gimbiya Jamila Bata da labarin komai harkokinta kawai takeyi, Snn kowa tsoron tunkararta yakeyi ya fad'a Mata. A nan take aka shiga gyaran d'aya b'angaren dake kallon sashin Jamila, Inda Jamila tacika da mamakin ganin ana gyaran wurin to kyaran me akeyi a d'aya b'angare irin nata Wanda babu abinda ya banbantashi da b'angarenta Bata kammala tunaniba jakadiya tashigo Mata a firgice ta zube gabanta tana fad'in ranki ya dad'e najiyo wani labari a majiyar da Bata k'arya cewa yarima Abdullah mijinki aure zaiyi Nan da sati d'aya za'a d'aura auren." Wata irin zabura tayi ta mik'e tsaye daga kujerarta ta mulki tana fad'in k'aryane wlh babu wata Wanda da Isa ta jadani a gidan Nan ta zauna lafiya." Kirawomun bokanya k'araba yanzun Nan a waya tayi mun bugun k'asa taganemun tabbas da gaske Yarima Abdullah auren zaiyi ko maganar mahassadane da 'yan bak'in ciki." Cikin minti biyu jakadiya tashiga Kiran bokanya, ai Kuwa Kira biyu bokanya ta d'auki waya tana dariya Mai cike da Ban tsoro tace "anayimun waya daga masarautar Abdulsalam Akan maganar d'an sarki yarima Abdullah tabbas yarima Abdullah aure zaiyi Nan da sati d'aya Kuma aurensa dole ne za'ayi shi ba fashi babu ja da baya domin tauraruwar yarinyar da zai aura tana da haske sosai, snn akwai wani haske a tare da yarinya bugu da k'ari zatakawo farin ciki a cikin gidan sarautar, Saboda 'yar sarki ce, ubanta tsaye Yake akanta, idan kika matsa dole sai anfasa auren Zaki iya rasa rayuwarki koki haukace." Bokanya tana gama fad'in hakan ta yanke wayar." Wani irin gumine yashiga tsattsafowa Jamila a jiki tashin hankali Wanda ba'a Sanya Masa Rana, Ba babban tashin hankalinta jin cewa zatazo da farin ciki a cikin masarauta meye wnn farin cikin?" Jakadiya tayi karaf tace haihuwa ya uwar gijiyata, Hannu ta d'aga ta wanke fuskar jakadiya da Mari tana "fad'in k'aryane wlh babu wata wacce ta Isa ta haihu da Yarima a gidan Nan bayan ni." *Hmmmmm fitinar mulki kenan*🤔🤔 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *DIDECTED TO Fateemah M Uthman* *Page 6* Sunkuyar da Kai jakadiya tayi hannunta dafe da kuncinta tana fad'in "Allah ya huci zuciyarki ya uwargijiyata, abinda kike nufi bashine manufata ba, Tare da mik'ewa tsaye ta d'an runsuna tace "ki huta lafiya gimbiya snn tafita." Bak'in ciki duk ya gama lullub'e gimbiya Jamila sai zufa take fitarwa gaba d'aya a jikinta kamar wacce tafito daga wanka, tarasa mafita, anan take tashiga tunanin, ita Abdullah zai yaudara,ita Abdullah zai zalinta ace saura sati d'aya d'aurin aurensa Amma bai fad'a mataba meta mashi a rayuwa?" Takai zaune dafe da Kanta hawayen bakin ciki suka Fara wanke Mata fuska." Shuru tayi tashiga tunanin yaushe rabonta da Abdullah, Yaushe rabon da su tsaya suyi magana Kota minti talatin ne, Baza Manta Yana yawan aiko kuyangi kiranta mantawa takeyi Bata zuwa har ya gama jiranta yayi tafiyarsa, hakan ko a wurin kwanciya, Tana d'akinta Yana d'akinsa Bata zuwa wurinsa Domin jitakeyi tayi aiki ta gaji hutu take buk'ata, Shi Kuma Abdullah namijine Wanda baya bin macce d'akinta duk yanda yakejin buk'ata idan Bata kawo kantaba sai dai ya hakura." Wani kuka yazo Mata Mai k'arfi tayi saurin rufe bakinta dan kada kuyanginta sujita Su fahimci halin da take ciki, ta shiga fad'in nashiga uku " Ko saboda hakan zai k'ara Aure?" Wlh na daina Abdullah kazo kace mun kafasa Auren Nan zan gyara duka kuskurena." Mik'ewa tayi ta shiga toilet ta wanke idonta tafito ta Fara shirya tarbon mijinta, Domin yau ta shirya bashi hakuri idan wani laifi tayi Masa ko wani kuskure Wanda zai Sanya ya k'ara Aure yayi hakuri ta daina zata tarairayeshi fiye ma da da, Abinda Bata saniba Abdullah ya tsufa a zamfara bazai dawoba sai da matarsa." Shuru ba Abdullah ba labarinsa har zuwa k'arfe goma na dare Wanda a iya saninta dashi baya kai k'arfe goma batare da yadawo gida ba." Wasa Wasa har safiya ta waye ba Abdullah, hakan yasa ta yanke hukuncin zuwa sashen Sarauniya Hajjah Domin ta tambayeta ina Abdullah ya tafi duk da dai har da sa hannunta Abdullah zaiyi Mata kishiya." Zuwanta wurin Hajjah anan Hajjah take fad'a Mata ai Abdullah Yana zamfara bazai dawoba sai angama d'aurin aure sa." Wani bak'in cikin da takaici Mai had'e da zazzafan kishi ya rufe idon jamila Anan take tashiga fad'awa Hajjah maganar da duk tafito a bakinta taciwa hajjah mutumci Daga k'arshe tace ita meyasa sarki baiyi mata kishiyar bane." Ido kawai Hajjah tabi Jamila dashi cike da mamaki da Al'ajabi Domin a duniya babu Wanda ya tab'a ci Mata mutumci ido cikin Ido kamar Jamila surukarta matar d'anta." Sai da Jamila ta gama cin mutumcinta snn tafito daga b'angaren Hajjah a fusace tanufi sashenta zuciyarta na k'una da rad'ad'i." Bayan d'aurin auren Bintu da Abdullah, aka d'auko Amarya daga masarautar zamfara zuwa masarautar Adamawa, wani sabon bikin ne aka had'a a gidan Ango tare da wasanni irin na gidan sarauta, Wanda hakan ya K'ara kunawa Jamila rai ganin ita a lokacin da aka auro ta ba ayi hakan ba, ta Kuma d'aukar wani Alwashi a ranta, tare da Jin tsanar Bintu Mai tsanani ta d'arsu a zuciyarta." Shigowar Bintu a cikin gidan sarautar canji ya Fara samuwa a cikin gidan, Domin duk wani k'unci da ake Sanyawa fadawa da bayi tare da kuyangu duk ya kau, Domin Bintu macce ce wacce ta tashi a gidan sarauta tasan yanda ake gudanar da mulki cikin Adalci snn gata da tausayi Bata kaskantar da talaka da bayinta ta d'auka da ita dasu duk d'aya na wurin ubangiji bawani babbanci snn Bata d'aukar kanta ita wata ce, kamar Jamila." Hakan yayiwa Hajjah dad'i ganin. Halayya Bintu Mai kyauce sai yanzun take farin ciki da dariya ganin tilon d'ansu ya dace da macce ta gari wacce take dai dai da rayuwarsa." Hajjah taja Bintu a jikinta tashiga fad'a Mata duk wani sirrin masarautar Wanda Bata tab'a yarda Jamila ta sandasuba domin tin farko ta fahimci rayuwarta maccece Mai son kanta ga kuma mugunta." Kowa a gidan idan kaji ya bud'e Baki ba Wanda zai ambata sai Bintu Alherinta ake fad'i tare da Adalcinta, snn Bintu kaifi d'ayace ba tsoro ko shakka a tare da ita Dan hakan suke fito na fito da Jamila, Dan Bata tsoronta ko kad'an musamman da ta fahimci halayanta ba masu kyau bane, hakan yasa Sam basa Zama a inuwa d'aya Jamila tanaso ta Fara tin karar Bintu Amma kwarjininta yake hanata aikata Mata komai, Snn a duk lokacin da take yunkurin ai watar da wani zalinci a gidan, Bintu takan dakatar da ita ba tsoro ko shakka, zata shiga karanto Mata k'undun tarihin mulki.ba hakan yace ayiba." Dole Jamila takeja baya Domin tasan kowa Yana bayan Bintu a gidan daga ciki kuwa har da maimartaba sarki, Tabbas maganar bokanya tafito cewa Bintu zatazo da wani haske a gidan, to gashi ta Fara gani tanaji tana gani komai ya tsaya Mata cak." Abdullah Yana tsananin son Bintu Wanda son da Yake Mata yasa yakasa b'uyeshi a duk inda yake a duk yanayin da ya tsinci kansa, Hakan Jamila ta Kuma Jin haushi da takaici tashiga tunanin Ina wuta tajefa Bintu, Ana hakan Bintu ta Fara laulayin ciki, irin laulayin Nan Mai sakarwa mutum kasala da yawan amai anan take komai yayi sanyi a tare da ita." Kwajin farko aka tabbatar da cewa tana d'auke da ciki d'an wata d'aya. Murna a cikin masarautar abin ba'a magana har da d'an kwarya kwaryar biki aka shirya, Anan take sarki yayi Mata kyauta taban mamaki, hakan Hajjah wacce lafiya ta Kiya mata yau ciwo gobe lafiya, itama tayi murna sosai dama babban burinta kenan taga jikokinta." Jin labarin bintu tana da ciki ya k'ara d'aga hankalin Jamila ganin daga zuwanta daga baya har tasamu ciki dama tasan za'ayi hakan Kuma tasan ba Dan komai akayi Auren ba sai Dan ta shigo gidan ta haihu domin ta gaji sarautar masarautar tinda sun saba da mulki sunsan da d'insa, Ynzun ana nufin idan ta haihu d'anta kenan zai hau kujerar mulki, Ina bazai yuwoba, Anan take tabawa jakadiya kud'i masu yawa tace "taje wurin bokanya duk yanda za'ayi ayi a zubar da cikin dake tare da Bintu kada asake a barta ta haifeshi Kai idan da Halima har itama Bintu tabi cikin nata zuwa lahira." "Angama ya uwargiyata wnn shi dai dai kinyi tunani Mai kyau Allah ya k'ara maki kaifin basira snn jakadiya ta tashi tafita tanufi k'auyen bokanya k'araba." Karon farko bokanya da tayi diba tace "Ina ciki bazai zubeba sabida yarinyar da abinda ke cikinta haske ne dasu, tin farko nariga da ta fad'a Maku cewa tauraruwar yarinyar haske gareta, Jakadiya tace "Allah ya k'ara maki lafiya ya bokanya k'araba ba wani abu da za'ayi akan sai cikin da ita kanta idan da Hali akasheta tamutu ta tafi da cikin can lahira." Bokanya k'araba ta d'aga murya cikin wani sauti Mai firgitarwa tace bai yuwoba,zai yiwo a kashetaba domin idan akayi yunkurin kasheta komai zai iya faruwa dagani har ku, Sai dai ayi asirin da zata haifin abinda ke cikinta yafito duniya ba rai." Jakadiya tace "wnn ma yayi." Aka Bata wani turaren Wanda zasu dinga turarawa a lokacin da sukasan Bintu zata shak'i warin turaren a ko wacce Rana har tsawon wata bakwai, Wanda da zarar tana shak'ar warin turaren ako da yaushe to abinda ke cikinta bazai tab'a fitowa da raiba sai a macce." Hakan akayi kullum safiyar Allah sai sunyi turaren wnn maganin a k'ofar b'angaren Bintu a inda aka San Bata gani." Bintu baiwar Allah tana ciki a kwance tana fama da laulayin cikinta kuyangi sai hidima sukeyi da ita, dazarar sunyi turaren tashak'i warinsa, zata dingaji tamkar an k'ara mata wani wutar azabar ciwo a tare da ita." Wasa Wasa Bintu duk ta rame ta fita a hayyacinta ga azabar laulayi ga a azabar turaren da Jamila take turara Mata, Abdullah ya Kuma tud'ewa Yana tausayinta sai kula yakeyi da ita fiye da tunanin Mai karatu, wani lokacin yakanji warin turaren Amma baya kawo komai a ransa." Ana hakan cikin Bintu ya tsufa ya Kai wata Tara ya girma sosai a lokacin lafiya ta Fara samuwa da ita duk wani laulayi ya Kau haihuwa ake jira, da zarar jamila tayi Ido biyu da cikin ji takeyi kamar ta kurma ihu ko tasanya bindiga ta harbeta daga ita har cikin su mutu kowa ya huta." Wani Lokacin takan Kira jakadiya ta dinga ce Mata Anya kuwa abin dake cikin Bintu ya mutuwa kowa?" Jakadiya zatace ki daina ko kwanto a Kai yamutu ranki ya dad'e domin bokanya Bata k'arya da zarar tafad"i magana to sai ya faru." Snn hankalin Jamila ya kwanta ta d'an saki murmushi, tace na tsani Bintu kamar yanda na tsani mutuwa ta." Wani dare da k'arfe uku Bintu ta tashi da nak'uda a lokacin tana tare da Abdullah ganin yanayin da take ciki yasa yafita yaje yakira jakadiyar Hajjah Domin yasan Hajjah kawaici ne da ita ko ya fad'a Mata bazuwa zatayiba Jakadiyar Hajjah danjijuwace wacce zata iya Kai shekara 45 Amintacciyace a wurin Hajjah Domin Yardar da Hajjah tamata itace ta raini Abdullah tin Yana k'araminsa tsakaninsa da mahaifiyarsa hajjah sai dai yasha nono ya tafi wurin jakadiyar Mai suna ANNA." Suna zuwa tare da Anna cikin sauri sai dai sukaji kukan jariri Wanda kukansa ya k'arad'e b'angaren Yarima Abdullah duk wani mutum Wanda yake rayuwa a cikin sashen gaba d'aya yaji kukan jaririn, zubbur Jamila tayi tafito daga d'akinta Jin kukan jariri da tayi, Dama wani bacci kirki takeyiba domin tinda taga cikin Bintu ya tsufa ya Isa haihuwa ta daina kwana da Ido biyu sai da da Ido d'aya Domin tana sauraron taji bintu ta haihu, babban burinta shine taji ance Bintu ta haihu abin da ta haifa ya mutu, idan da Hali tafison tabi d'anta su mutu a tare." Jin kukan jaririn da tayi yasa tafito da sauri ba ko mayafi a kanta, tana zarar Ido tanufi b'angaren Bintu tana fad'in a Ina nakejin kukan jariri." kitibis tayi da santalelen d'a namiji sak mahaifinsa wani b'angare ya d'ebo mahaifiyarsa Yana hannun Anna ta gyarashi cikin kayan sanyinsa ruwan Madara masu tsananin kyau." Ido biyu sukayi da Anna suka kalli juna, Jamila tayi saurin sakin murmushi tare da mik'a hannu zata k'arb'e jaririn tana fad'in "ya akayi hakan, taga yaro Yana motsi cikin k'oshin lafiya, gabanta ya fad'i ta mere Baki tace Amma dai macce ce aka haifa ba namijiba, Anna tace namiji ne magajin sarki insha Allah had'ida mik'awa yarima Abdullah jaririn, Wanda hankalinsa Yana kan Bintu wacce take kwance a kan gado tana kallon kowa d'aya bayan d'aya tana murmushi." Jamila na ganin Anna ta hana Mata jaririn yasa taja da baya ta juya tafita daga d'akin Bata Kuma furta komai ba zuciyarta tana tafarfasa, tsakanin Anna da Jamila Kar Tasan Karne domin Anna tasha Kama Jamila a bayan gida tana bine wani abin ko tasamesu suna magana tare da jakadiyarta, Wnn dalilin yasa Jamila take shakka Anna domin rufuwar asirinta domin tasan Anna jardadiyar sarki ce sosai komai tafad'a Masa baya musu zai yarda" A Ranar kasa Zama Jamila tayi sai hawayen bak'in ciki yake Mata Ambaliya a fuska ganin tanaji tana gani wata tazo daga baya ta haihu kuma d'a namiji ita Kuma ko b'atan wata bata tab'ayiba tabbas dole ne ta Hana wnn yaron Zaman duniya dole ne ta salwantar da rayuwarsa Kai har ma da rayuwar mahaifiyarsa." Washe gari gaba d'aya gidan sarautar ya karad'e da murna bintu matar Yarima Abdullah ta haifi d'a namiji, Maimartaba sai da yayi sujjada ga mahaliccinsa domin Jin dad'i Wanda Kuma yazo Masa da Albishir ya Masa kyauta ta ban girma, hakan Hajjah sai da ta zubar da hawaye Dan murna, A ranar gidan kowa cike yake da murna da farin ciki sai hada hada akeyi fuskokin kowa cike suke da murna Amma Banda Jamila da jakadiyarta." A ranar suna yaro yaci sunan SAUBAN, Wanda maimartaba sarki yasaka Masa sunan da kansa sabida Yana tsananin son sunan domin ya Sha Alwashi da zarar anyi haihuwa a gidan indai namiji aka haifa to baya da wani suna da za'a saka Masa bayan SAUBAN." Bikin sunan Sauban bikin sunane Wanda ba'a tab'ayin irinsa ba a gidan sarautar domin bikine na masarauta biyu masarautar zamfara da masarautar Adamawa ko wanne yanaji da kud'i da mulki kuma ko wanne Yana nuna farin cikinsa da tashi bajinta domin Sauban shine jika na farko a masarautar biyu." Farin ciki a wurin Abdullah Abin ba'a magana domin duk inda yake Yana tare da matarsa da d'ansa Wanda hakan ya Kuma k'onawa Jamila rai k'ara d'auki Alwashin sai ta salwantar da rayuwar Bintu da d'anta Sauban." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *DIDECTED TO Fateemah M Uthman* *Page 7* Bayan bikin sunan SAUBAN Anna ta dawo da Zama gaba d'aya a b'angaren Bintu domin kula da ita da jaririnta, bisaga umurnin Hajjah domin tasan Jamila zata iya aikata masu komai idan taga ba kowa a kusa dasu tinda ba mutumci da imani ne da itaba." Sauban da mahaifiyarsa sun Sami kulawa ta musamman.a wurin Anna domin gasasu takeyi da ruwan zafi yanda ya kamata." Wanda hakan yayi matuk'ar k'ona ran Jamila, domin bataso Anna ta dawo b'angaren Bintu da zamaba, burinta shine ta fakaici idon mutane tashiga d'akin ta Sanya hannu ta shak'e wuyan Sauban ta kasheshi da hannunta kowa ya huta, Amma Ina ba Hali Anna ta saka Mata Ido sosai." Hakan suka kammala jegonsu cike da kulawa tare da tarairaya a wurin Anna da Abdullah." Sauban ya girma yayi wayo ya taso cikin farin jinin Al'umma gashi kyakkyawa ya d'ebo kyawon mamansa da babanshi duk Wanda yaga Sauban sai yaji yaron yashiga ransa, Wanda Jamila da zarar tayi Ido biyu dashi takejin tsananin tsanarsa a ranta Bata k'aunar ta gansa Dan hakan duk wata hanya da zaisaka ta tayi Ido biyu da Sauban Bata bi, A kullum safiyar Allah tunaninta d'aya ta wacce hanya zatabi ta kawar da sauban da mahaifiyarsa a doron k'asa." Ana hakan Sauban sai Kuma girma yakeyi Yana wayo Wanda a yanzun shekararsa biyu baya da wurin Zama sai fada kusa da sarki, wani lokacin tare da sarki suke kwana a d'aki d'aya saboda k'aunar da sarki yake Masa, Sauban jarumine tin Yana k'aramunsa ba k'aramun Abu ne yake sakashi kukaba, ko fad'uwa yayi hakan zai tashi da kansa batare da an tayar dashiba, Kuma ba alamar kuka ko Jin ciwo a tare dashi, snn baya da yawan magana tin Yana k'aramunsa domin ko magana ake Masa idan ba yaga damar amsawa ba baya amsawa shuru yakeyi tamkar bayaji, wani lokacin Kuma sai dai ya d'aga hannu alamar ya amsa. Wnn halin nasa yasaka sarki yake matuk'ar son shi domin jinin sarauta ne Yake yawo a jikinsa, hakan Yana nuni da cewa jarumin maza ne, za'ayi fafatawa dashi a fagen fama, Dan hakan sarki ya d'auki harmar bashi wani magani Mai saka jarumta da kaifin basira tare da kuzari." Shekarar Sauban biyu da rabi mahaifin Bintu ya rasu wato sarkin zamfara," Mutuwar da tarazana Bintu tare da sarki da Abdullah da Kuma Hajjah." Bintu tayi bak'in cikin mutuwar mahaifinta sosai, Wanda kuka da kewarsa ya kasa tsaya Mata a fuska, Abdullah sai aikin lallashinta kawai yakeyi." Bayan wata d'aya aka nad'a babban d'an sarkin zamfara wato yayan Bintu a kan kujerar mulkin." Bayan an nad'a sabon sarkin zamfara, akazo wurin rabon gado anan ake fad'a Mata tin kafin mahaifinsu ya rasu ya bar wasiyar cewa gidan gonarsa dake Adamawa a can cikin wani k'auye Mai suna lissa, ya bawa Bintu gidan gonar kada a sakashi a cikin rabon gado saboda tin Bintu tana k'arama take matuk'ar son gidan gonar Dan haka natane ya Bata, a fad'a Mata hakan a Kuma dank'a Mata ta kardunsa a hannunta." Bintu taji dad'in kyautar gidan gonar da mahaifinta ya Mata tashiga yi Masa Addu'ar samun rahamar ubangiji, Domin itama tana tinanin gidan gonar a ranta tana Addu'ar Allah yasa idan za'ayi rabon gado ya fad'a a cikin gadonta Domin tana tsananin son wurin tin tana k'ara hakan wani lokacin sarki zai d'auketa sushiga jirgi ya kaita gidan gonar domin kawai farin cikinta, Har zuwa girmanta Wanda ta mayar da zuwa gidan gonar duk k'arshen wata take zuwa tana kwana biyu a cikinsa tare da kuyangi tana nishad'i da farin ciki domin duk lokacin da tsinci kanta a cikinsa tana jinta cikin wani farin ciki marar misaltuwa hakan zata dinga murmushi da annashawa a cikinsa tanaji a jikinta akwai wani farin ciki babba Wanda ya danganci rayuwarta a cikin gidan gonar, Wanda Yake Cikin k'auyen Lissa a k'ark'ashin k'aramar hukumar mulkin Adamawa State." Bayan an kammala rabon gado, Bintu ta dawo gida tare da Abdullah da Sauban, Hakan Abdullah yaci gaba da kular mata da gidan gonar tamkar mahaifinta Yana Raye." duk k'arshen wata suke zuwa ziyara gidan gonar kamar yanda takeyi a can baya, tare da shi da ita da Sauban a lokacin Yana da shekara uku a duniya, Hakan Yana matuk'ar sanyata farin ciki, Yana cire Mata damuwar rashin mahaifinta da tayi." Ana hakan Bintu ta Fara laulayin samun wani cikin, Wanda Abdullah ya fahimci cikine da ita ya shiga farin ciki, Anan take gidan sarautar kowa ya d'auka Bintu ciki ke gareta duk kowa yashiga murna da farin ciki duk Wanda ka kalli fuskarsa a lokacin Yana cikin murna da farin cikin samun cikin bintu." Amma Banda Jamila domin k'ura takai Banga tsakaninta da Bintu duk abinda za'ayi sai dai ayi saboda bazai yuwo ta Kuma haihuwa a gidan Nan ba." Ana hakan cikin Bintu ya Kai wata hud'u, Tafiya ta Kama Abdullah zuwa Bauchi wurin nad'in sarautar babban Abokinsa Kuma Amininsa wato Yarima Hayat Wanda mahaifinsa sarkin Bauchi ya mutu, za'ayi bikin d'ora d'ansa Hayat akan kujerar sarauta." Yaso yatafi da Bintu sai dai yanayin jikin nata ne batajin dad'in sa, Kuma yasan zainab bazata bishiba saboda Bata k'aunar d'agawa daga gidan tayi ko tafiyar wuni d'ayace saboda kada tabar kujerar mulkinta." Hakan ya shirya yayi tafiyarsa shi kad'ai cike da kewar matansa musamman Bintu wacce take cikin lalurar laulayi." Tafiyarsa tayi matuk'ar yiwa Jamila dad'i, Dama ta shirya ai watar da komai na mutuwar Bintu tare da d'anta Sauban tako wacce hanya tinda maganin boka baya tasiri a kanta, idan tasan wata ai Bata San wataba." Hakan yasa tayo hayar manyan 'yan ta'adda domin su kashe Bintu da d'anta Sauban, Anan tabasu Kayan bayin gidan suka saka a jikinsu Dan gudun kada a ganesu, Kasan cewar gidan cike Yake da bayi da kunyangi suna shawagi Rana da dare." Wani dare Bintu tana kwance ita kad'ai, a lokacin Sauban Yana tare da sarki, Domin tinda ta Fara ciwo Yake kwana a wurin maimartaba, Acan cikin baccinta taji sautin muryar gardawa a kanta cikin sauri ta bud'e idonta, Ai Kuwa tayi arba da gardawa sanye da kayan bayi, Wanda da zarar ka gansu kasan ba bayi bane, Addu'a tashigayi d'aya daga ciki ya Sanya hannu ya make Mata Baki a anan take jini ya cika Mata bakin gaba d'aya." Yunkurin tashi takeyi d'aya cikinsu yabita ya haye kanta ya sanya filo ya danne kanta, Sai da yaga Bata motsi alamar ta mutu snn ya dagata suka gyara Mata kwanciya kamar wacce take bacci snn suka fita suka bar d'akin." Basuyi tinanin Ina d'anta Yake ba, Sukayi ficewarsu. Suna fita sukaci karo da Jamila, sukayi Mata nuni da aiki yayi kyau, ta mik'a masu jakar kud'insu suka fita ta hanyar baya." Safiya tana wayewa a gidan sarautar hankalin kowa a tashe cewar ankwanta da Bintu ba'a tashi da itaba, Mutuwar da tafirgita kowa a gidan duk Wanda kagani cike Yake da bak'in ciki fuskar kowa sai zubar da hawaye takeyi."😭 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *DIDECTED TO Fateemah M Uthman* *Page 8* Abdullah Yana cikin jama'a ana hidimar bikin nad'in sarautar Abokinsa Hayat gabansa sai fad'uwa ykeyi yarasa dalili, anan take jikinsa ya soma rawa yaji a duniya ba Wacce yakeso yagani sai Bintu, anan take ya Tina halin da ya barta na tsananin laulayi, Hakan ya fito daga cikin taron mutanen batare da anlura dashiba ya shiga motarsa tare da fadawansa suka d'auki hanyar komawa gida baiyi sallama da kowa ba." Saukarsu kenan bai wani jira aka bud'e Masa murfin motarba ya bud'e da kansa gabansa Yana fad'uwa, Kai tsaye b'angaren Bintu yanufa jikinsa sai rawa yakeyi ji Yake akwai abinda ya Sami Bintu Tafiya yakeyi kamar zai tashi sama burinsa ya gansa a b'angaren Bintu Wanda duk inda ya gifta fadawa da bayi sai kallonsa sukeyi cike da tausayi wasu suna sharar hawaye.' Bai lura da kowa ba domin idonsa a rufe yake hakan yasa bai fahimci kallon da ake masaba bai Kuma fahimci kukan da bayi da kuyangi sukeyi ba, hakan yasanya gaba cikin sauri ya Isa b'angaren Bintu, Wanda tin a k'ofar b'angaren nata ya ganshi cike da mutune sai a lokacin ya lura da yanayin fuskokin mutanen dake wurin zaune ko wanne ya rafka tagumi, ko wanne cike yake da damuwa wasu suna matsar hawaye." Gabansa ya fad'i cikin Azama ya tinkari d'akin Bintu Wacce aka kammala shiryata cikin sitirarta tana sanye da linkafani fari fes Wanda yayi Mata kyau fuskarta sai wani Annuri take fitarwa ga murmushinta Mai sanyi a kan fuskarta, Kai tsaye ido rufe yazo wurinta ya durk'usa Yana fad'in Bintu tashi nadawo Yaya jikin naki, ko mutafi asibity ne,? Bintu kitashi Mana Yana girgizata?" Ji yayi andafashi ta bayansa yayi saurin juyawa yaga Hajjah ce tana matsar hawaye abinda tin tashinsa bai tab'a gani a idon Hajjah mahaifiyarsa ba, ya Kuma rud'ewa, Hajjah ta d'agoshi ya mik'e tsaye ta rungume shi tana fad'in Abdullah sai dai kayi hakuri domin Bintu ta rigamu gidan gaskiya ankwanta da ita ba'a tashi da itaba." Wani irin razana yayi yasaki jikin Hajjah yanufi wurin gawar Bintu yashiga girgiza Yana fad'in kitashi Bintu Baki mutuba kitashi." Ina shuru ba motsi Bintu ta mutu, Wani irin kuka yasaki Mai tsoma zuciya Yana rungume da gawarta." Tausayi ya Bawa duk mutanen dake wurin suma sukashiga zubar da hawaye Mai k'arfi." Ana hakan sarki ya shigo tare da sarkin zamfara dama su ake jira ayi Mata sallah akaita gidanta na gaskiya, Ganin kukan da Abdullah yakeyi yabawa sarki tausayi ya d'agoshi ya rungumeshi Yana fadin daina kuka Yarima Addu'a ya kamata kayiwa Bintu adai adai wnn lokacin Addu'arka take buk'ata, in har kacika masoyinta, Kasani ko wanne Mai Rai zai mutu muyiwa kanmu fatan cikawa da imani Bintu lokacinta ne yayi." Hakan sarki yayi ta kwantarwa Abdullah da hankali har yayi shuru ya daina kuka ya koma Kukan zuci wanda yafi komai zafi, Hakan aka d'auki Bintu akayi Mata sallah snn aka kaita gidanta na gaskiya." Sai da aka Kai Bintu aka dawo snn Jamila tafito daga b'angarenta tana kukan munafurci tana fad'in bintu da Sauban Allah ya jik'anku hak'ik'a munyi Rashi babba a gidan nan" Kyara kalamanki Sauban Yana raye bai mutuba, Sautin muryar Hajjah taji ya dura a kan dodon kunnenta, Wanda yasa tayi saurin d'aga Kai a zabure ta kalli Hajjah da Anna sai Kuma Sauban dake kusa da Anna Yayi shuru Yana kallon kowa d'aya bayan d'aya bini bini sai ajiyar zuciya Yake saukewa jama'a duk sun zagayesu ana amsar gaisuwa." Kallon da Jamila tabi Sauban dashi cikin firgita yasa Hajjah ta d'ora a alamar tambya a kanta, hakan Anna wacce ta anyana a ranta tabbas mutuwar Bintu lokaci d'aya akwai wata sarka'nkiya a cikinta Amma insha Allah komai zai bayyana gaskiya zatayi halinta." Saitin muryar Hajjah ta kumaji tana fad'in " Sauban ba zai mutu a yanzun ba sai ya hau kujerar mulkin mahaifinsa bayan yayi murabus, kalaman Hajjah kenan karo na biyu." Zaro Ido Jamila tayi cikin sarkewar murya tace "tuba nakeyi ranki ya dad'e nayi kuskure abinda akacemun kenan." Ta Kuma kallon Sauban tace "zo Nan yarona hak''ika nayi farin ciki da ganinka Cikin k'oshin lafiya Allah ya jik'an mahaifiyarka." Ko kallon inda take Sauban baiyiba domin ko can dama baya yarda da ita, basa Zama inuwa d'aya da ita, Sabida duk suka had'a wuri d'aya daga ita sai shi sai tayi Masa mugunta Musamman idan Abdullah ya d'aukoshi ya shigo dashi sashenta bazai fitaba sai ta fakaici idon Abdullah tayi Masa muguntar da zata sakashi kuka har ya daukeshi ya mayar dashi wurin mahaifiyarsa." Ganin ko kallon inda take Abdullah baiyiba, taji haushi ta mik'e tsaye tana fad'in Allah ya bamu hakurin rashin bintu." Bayi suka amsa da Amin gimbiya Allah ya biya ya k'are Mana lafiyarki." Muryar Hajjah taji tana fad'in Allah yasa da gaske akeyi komai zai fito fili asiri zai tonu za'ayi hukunci marar dad'in ji da sauraro idan gaskiya tayi halinta, daga Abdullah sai Sauban a fagen sarauta domin sune suka cancanta, ko bayan ran kowa a wurin nan." Murmushin da yafi kuka ciwo Jamila tayi Bata tankawa Hajjah ba illah ma tayi kamar bada ita takeba ta wuce ta fita." Tana shiga sashenta tashiga cire Alk'yabbar jikinta tayi jifa da ita tashiga Kiran jakadiya, cikin hanzari jakadiya ta zube gabanta, Jamila ta dubi jakadiya tace "asirinmu Yana shirin tonuwa domin Hajjah ta sakarmun magagganu masu Kama da gugar zana, Babban tashin hankalinmu d'aya ne Ashe Sauban bai mutuba." "Bai mutuba ranki ya dad'e to ya akayi hakan ta faru?" "Abinda nakeso nasani kenan, lallai ansare macijine ba'ayar da kansa ba, Dole ne mubi ta wata hanya wacce zamu salwantar da rayuwar yaron can, Domin tin yanzun anfara yimun gorin sarauta cewa daga Abdullah sai.Sauban, Dafe k'irji jakadiya tayi tace waye yace maki hakan, Cikin d'aga murya Mai cike da tashin hankali da damuwa tace "waye ya Isa ya furtamun hakan bayan hajjah." Ta Kuma sakin wata irin dariya tace "ki kwantar da hankalinki Hajjah dake da Sauban duk a lokaci d'aya zan aikaku lahira domin kune damuwata a gidan Nan." "Kinyi tunani Mai kyau ya uwargijiyata Amma shawarata a Nan a d'an jira har mutuwar Bintu ta lafa sai a aiwatar da wnn aikin, Wnn karon aikin bokanya ne domin Bintu kad'ai ta gagari bokanya, tinda ankawar da ita komai zai zo cikin sauki, ta Kuma sunkuyar da Kai tace ya uwargijiyata ki natsu ki dinga saita kanki kada a gane wani abin dangane dake, Ina ganin ko Hajjah wani abin ta hango a idonki shiyasa tayi maki wnn kalamin." Shuru Jamila tayi tana nazari, Ganin tayi shuru yasa jakadiya tashi tayi Mata sallama tafita." Bayan mutuwar Bintu Sauban ya koma hannun Hajjah da Anna Wanda suke bashi kulawa suke taka tsantsan dashi a duk inda zai tafi da Kuma duk abinda zai Sha ko Kuya ci." Bayan wata bakwai da mutuwar Bintu a lokacin Sauban Yana da shekara hud'u har ya Fara zuwa makaranta Wanda Yardajen direban sarki Yake kaishi ya Kuma tsaya har a tashi ya d'aukoshi ya dawo dashi gida cike da kulawa, Wanda Sauban yarone Mai kaifin basira malamansa suke tsananin sonshi da Alfahari dashi a makarantar." Babban burin Jamila a Koda yaushe tayaya zata salwantar da rayuwar Sauban takeyi, Bokanya ta Bata maganin da zata zuba Masa a abinci da zarar yaci to sai dai wani ba shi ba, Abinda yafi d'aga Mata hankali shine, Taga Sauban a idonta wuya Yake Mata sai dai daga nesa baya zuwa wurinta Sam, snn ga wasu bayi da kuyangi manya manya majiya k'arfi da aka zuba a b'angaren Hajjah Wad'anda duk Wanda yazo shiga basa barinsa, Daga ciki Kuwa har da ita, duk da dai Bata tab'a yunkurin zuwa wurinba labari ne yazo mata a kunnenta cewa har ita idan taje bazasu barta tashigaba wnn umurnin Hajjah ne" Ana hakan wani dare ta tashi da amai da zawo sai shekashi takeyi ba sauki, Hankalin Abdullah ya tashi yashiga kula da ita Yana tausayinta domin duk a tinaninsa itama mutuwa zatayi ta barsa kamar yanda bintunsa ta mutu ta barshi." Cikin sauri ya d'auki wayarsa yakira family doctor dinsu, Minti ashirin saiga doctor yazo d'auke da Kayan aiki, yashiga Bata kulawar gaggawa awon farko ya tabbatar masu da tana d'auke da ciki na tsawon wata hud'u Bata saniba." A zabure Jamila ta mik'e zaune tana zarar Ido tana fad'in "ciki likita nice keda ciki har na tsawon wata hud'u?" "Kwarai Kuwa ranki ya dad'e cikine dake d'an wata hud'u, "Alhamdulillah Tashiga furtawa tare da Abdullah Wanda sai murmushi yakeyi Yana dariya tare da yiwa likita babbar kyauta." Washe gari gidan ya d'auka Jamila ciki ne da ita d'an wata hud'u, Masu murna sunayi wad'anda ko ajinsu sunfi masu murnar yawa, bayinta da kuyanginta basuji dad'in samun cikin nataba domin sunsan da zarar ta haihu wata sabuwar azabace zata kuma lunkuwa a kan wacce take basu a yanzun, Domin sun san Akan abinda ta haifa komai zata iya aikata masu, don wani sabon mulkine zata shinfid'a tare da abinda ta haifa d'in." Labari yakai har cikin fada cewar Jamila tana d'auke da ciki, Sarki yayi murna sosai sai da yabawa Dan Aiken kyauta Mai tsoka, Hakan da labari ya Sami Hajjah mere Baki kawai tayi domin ita da haihuwar Jamila da rashinta duk d'aya ne a wurinta." Samun cikin Jamila shine ya janye Mata hankali wurin salwantar da rayuwar Sauban domin tana ganin da zarar ta haihu idan namiji ta haifa Dole ne ya gaji sarauta." Anan hakan cikinta ya girma ya shiga watannin haihuwarsa, Wani dare ta tashi da nak'uda ta haifi d'anta namiji, Sak ita komai nata da d'an iri d'aya ne." Murna a wurinta da danginta abin ba'a magana, Ranar suna yaro yaci suna SADEEQ." Anyi bikin suna na kece raini, Amma Sam ko k'adan bai Kama k'afar bikin sunan Sauban da akayiba, Hakan akayi aka watse lafiya, taci gaba da renon d'anta Wanda ta d'auki burin duniya ta d'ora a kansa, Bata Bari kowa ya d'aukar Mata yaro, hatta jakadiyarta Bata Bata Sadeeq a cewarta za'a iya Bawa jakadiya kud'i masu yawa Dan ta salwantar da SADEEQ Dan ta lura da jakadiya bak'in kwad'ayine da ita da Kuma son abin duniya, duk a tunaninta abinda takeyi shi kowa keyi." Hatta da sarki idan ya aiko a d'aukar Masa shi, Bata bayarwa sai dai tace acewa sarki bacci yakeyi idan ya tashi zata aiko dashi, Har sarki ya daina aikowa a d'aukar Masa sadeeq Wanda Hajjah ko da Wasa Bata tab'a aikowa a d'aukar Mata Shiba indai Abdullah ya d'aukoshi yashiga dashi wurinta zata amshesa tayi Masa Wasa har tabawa Sauban shima yayi Masa Wasa idan zai fita ya daukeshi ya fita dashi." Ana hakan Sadeeq Yana cika shekara biyu a duniya a lokacin Sauban Yana da shekara shidda, Jamila ta Kuma samun wani cikin ta Kuma haihuwar d'a namiji aka sanya Masa SAGEER, Kuma haihuwar d'a namiji da tayi ta dingajin kanta tafi kowa a gidan daga ciki kuwa har da hajjah jitakeyi tafita Sai wani sabon salon iyayi ya tashi a gidan ganin d'iyanta biyu duk mazane gado nata ne." Dan hakan. In har tana raye ba Wanda ya Isa yayi mulkin masarautar nan bayan Abdullah sai yaranta domin ko a lissafi Bata Sanya Sauban domin ta San wurin da ta ajiyeshi kallon matance take Masa." *Hmmmmm d'an hakin da karaina......ku iyar Mata friends* *Mrs Ana's Bawa*✍ *Hmmmmm muje zuwa friends da fatan kuna biye Dani Kuma Kuna fahimtata* *Mrs Ana's Bawa* *Mrs Ana's Bawa gusau*😘😘 Yawan comment yawan typing idan naga ba'a comment to zai koma na kud'i KO a jikina🤷🏻‍♀ One luve my friends Mrs Anas bawa ce, Muje zuwa wnn karon naxo mku da wani sabon salon labari a kyauta👌🏻 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *DIDECTED TO Fateemah M Uthman* *Page 9* Hakan Jamila taci gaba da kula da yaranta Bata yarda kowa ya rab'e inda suke, bare a Kai ga d'aukarsu, A kullum tunaninta za'a iya zuba masu wani mugun Abu a cikin abinci suci su mutu." Kuyanginta ma tare da bayi, kullum cikin sabuwar wahala suke tare da Azabtarwa musamman idan taji kukan d'aya daga cikin 'ya'yanta to tabbas duk Wanda Yake kusa da d'akin da suke sai ya gane kurensa Dan yinin ranar a tsakar Rana zai k'are yininsa baci basha." A kwana a tashi ba wuya Wanda a yanzun Sauban Yana da shekara 12 a duniya Sadeeq Yana da shekara 6 Sageer Yana da shekara hud'u, makaranta d'aya suke karatu tare da Sauban Wanda a yanzun Sauban yake mataki na k'arshe a primary school d'insa jarabawar fita sukeyi." Sauban Yana tsananin son Yan uwansa Sadeeq da Sageer domin duk abinda yasamu a makaranta bashida wani buri illah ya Bawa Yan uwansa, Snn duk Wanda ya Dakar Masa Yan uwa a lokacin za'aga b'acin ran sa, don komai girmansa sai ya Rama masu, Hakan yasa soyayya tashiga tsakaninsa da Sageer a duk inda kaga sauban a makaranta Yana tare da Sageer, a tare suke cin abinci Wanda Sauban yake zuwa dashi, Domin shi bayacin abincinsu, wnn umurni ne daga Hajjah tin Yana k'aramunsa take lurar dashi, wnn dalili yasa ba komai yakeci ba, kwata kwata bayacin wani abin idan ba a hannun Hajjah yafito ba, ko a makaranta baya sayen komai sai dai ya sayawa 'yan uwansa musamman Sageer da jininsu yafi had'uwa, Wanda shine k'arami a cikinsu, Sadeeq Kuma sak halin mahaifiyarsa ya d'auko, baya k'aunar Sauban ko kad'an, Ko a makaranta Yana yawan had'a Masa tarko cikin ikon Allah Sauban Yake k'etarewa kasan cewar yaro ne shi mai tsananin wayo, Yana kallon kowa tsaf yasan Wanda Yake sonshi yasan Wanda baya sonshi." A na hakan Sauban suka kammala jarabawarsu ta primary aka had'a masu biki na musamman, Wanda harda sarki da Abdullah tare da Hajjah suka halarci bikin yayewarsu makarantar primary." Hakan Jamila itama tazo domin tana da labarin cewa harda Sauran classic za'a Bawa d'alibai kyauta wad'anda sukayi na d'aya Dan tana da yak'i nin har da yaranta a ciki saboda tana kiran malaman a bayan fage tana basu kud'i Dan su rik'a Bawa yaranta na d'aya ako WANNE k'arshen zango kamar yanda taga Sauban Yana d'aukar na d'aya, Domin ta fahimci Sageer da SADEEQ ba wani k'ok'ari ne dasuba musamman Sadeeq, Dan har k'ara Sageer Wani lokacin Sauban yakan zaunar dashi ya koya Masa karatu idan suna makaranta." Sab'anin Sadeeq da ba abinda yasani sai mungunta dason nuna mulki da Isa tin Yana k'aramunsa sak halin uwarsa👌🏻" Biki akeyi kowa sai murna yakeyi musamman Maimartaba da Abdullah da sukaga Ankira Sauban ya bud'e taro da Addu'a cikin harshen larabci, cikin natsuwarsa da kamalarsa tare da k'asaitarsa Mai fitar da kwarjininsa na jinin sarauta, Bayan ya gama Addu'ar bud'e taro cikin harshen larabci snn ya koma magana cikin harshen turanci irin turancin Nan Mai kyau irin na mutanan England, tamkar ba'a bakinsa harafin turanci yake fitowaba, Dad'i tamkar ya kashe duk wani masoynki sauban dake wurin , Amma Banda Jamila da takeji Ina wuta ta jefashi Dan bak'in ciki sai fad'i take a ranta tsinanne Mai halin uwarsa kaima ka kusan zuwa Ina tsinanniyar uwarka tatafi" Bayan ankammala komai aka Fara bada kyaututtuka, inda Sauban ya samu kyauta ta musamman. Domin duk wani Mai fad'a aji Wanda ya halarci taron sai da yabawa Sauban kyautar ban girma tare da burgewa." A nan aka zo Sauran classic duk d'alibin da yayi na d'aya, a ka shiga Kiran sunansa d'aya bayan d'aya ana basu kyauta, Jamila sai murmushi takeyi tana gyara hannu tana jiran Akira yaranta taje da kanta ta k'arb'ar masu Dan Bata buk'atar wani yaje ya amso masu." _halinki ba kyau jamila_ 🤔 Sai da aka kammala Bawa ko wanne class taga ba'a Kira yarantaba haushi da takaici ya k'umeta, Wayyo Allah kuxo kuga fuskar Jamila ganin ba'a Kira yarantaba bak'in ciki kamar ya kasheta ganin ko wanne yaro sai d'aga kyautarsa Yakeyi Yana Bawa mahaifiyarsa Amma Banda yaranta, Lura da hakan da Sauban yayi yasa yasaki murmushi ya tako yazo wurin k'annensa ya janyo hannunsu zuwa jikinsa ya rungumesu Yana lallashinsu tare da cewa kuyi hakurin kunji k'annena, Wani time d'in kuyi k'ok'ari, ku daina Wasa a karatu , Kuma za'a baku kamar hakan kunji." Sadeeq ya fisge jikinsa daga jikin Sauban ya nufi wurin mahaifiyarsa Yana sharar hawaye, Sunan Sauban akaji ana Kira cikin abar magana Wanda tasaka kowa natsuwa, Cikin takunsa yanufi wurin da ake kiransa a gaban governor yaje ya tsugunna Wanda shine yasaka akirashi, Governor yana murmushi Yana kallon Sauban ya d'auki wata kyauta Mai girman gaske Wacce aka lullub'eta a cikin wata Leda Mai haske da kyalli,ya mik'awa Sauban." Hannu biyu Sauban yasaka ya amsa cike da girmamawa Yana godiya, ai Kuwa aka shiga yi masu hotona, _wayyo mutuwa kozo kuga idon jamila_😂 Idon kowa Akan Sauban ya mik'e a gaban governor Yana tafiyarsa cikin natsuwa yana d'auke da kyautarsa a hannu kowa sai kallonsa yakeyi Kai tsaye wurin Jamila yanufa ya durk'usa gabanta ya mik'a Mata kyautar don ta Sanya Masa Albarka, Ido kansu kowa sai kallonsu yakeyi cike da burgewa Wad'anda suka San komai sun zuba Ido domin ganin yanda zata karb'eshi, Ganin Ido kanta snn ga Abdullah da sarki Suma kallonta sukeyi suna murmushi, yasa tasaki dariya ta k'arb'i kyautar tana murmushin Yak'e Wanda yafi kuka ciwo ta dafa kansa tana fad'in, d'ana kayi k'ok'ari sosai Allah ya taimaka." ai Kuwa aka shiga d'aukarsu hotona sai murmushin takeyi tana k'ara rungumo Sauban zuwa jikinta, a can cikin zuciyarta kuma jitakeyi kamar ta kurma ihu akan bak'in ciki, Ganin idanu sun janye kansu Sauban ya koma wurin maimartaba ana hotona yasa tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye tabar wurin tare da Jan yaranta suka shiga mota tanufi gida." Murmushi manyan Hajjah tasaki domin Sauban ya matuk'ar burgeta da yayiwa Jamila hakan, Don ko yanzun zata gane idan Rana tafito tafin hannu baya rufeta." Ana hakan taro ya watse sarki ya dawo gida cike da farin ciki da annashawa, hakan Abdullah sai dai Jin zafinsa d'aya Banda Sadeeq da Sageer Wurin bada kyauta kamar yanda yaga ana Bawa Sauran d'aliban da sukazo na d'aya, yashiga tinanin Kodai basa karatun ne?" Hakan yasa suna sauka a mota ya nufi b'angaren Jamila, Sageer da SADEEQ kwance a kan jikinta tana lallashinsu Sadeeq Yana fad'in Muguntace Sauban ya masu shine ya Hana a basu kyauta a makaranta Wanda Sageer yake cewa ba laifin Yaya Sauban bane laifin uncle ne, Jamila ta dakawa sageer tsawa tare da zare masa Ido tana fad'in wnn yaron da a asibity na haifeka da nace anyi mun canjenka domin na lura gaba d'aya baka biyo halina ba, Da zarar anfad'i laifin Sauban yi kakeyi kamar kafashe da kuka, ko ka dakemu, To bara kaji ka bud'e kunnenka da kyau kaji Sauban ba masoyinku bane Dan ba d'ana bane banice na nahaifeshe ba, kaga ku biyun Nan ku kad'ai na haifa, Sauban d'an ubane abokin gabarku ne, ko kashesa kukayi ba abinda zai faru, domin idan Baku kashesa ba kunaji Kuna gani zai hau kujerar sarauta, ku Kuna gefe kuna kallo sai yanda yayi daku kun Zama 'yan kallon kenan." Sallamar Abdullah yasa taja bakinta tayi shuru illah ta had'e fuska domin Bata ga alamar Wasa a tare dashi ba." Wuri ya samu ya zauna cikin d'aure fuska tace "barka da shigowa, "Yawwa yace snn kuyangi suka zagayeshi da kayan motsa baki." Kallonsa Sadeeq da Sageer sukeyi domin ba'a koya masu gaisuwa ba, shima bai damuba domin yasan irin tasu tarbiyar kenan, Wanda yayi fad'a har ya gaji ba wani sauyi a tare dasu, Kallonsu yayi snn ya d'aga masu hannu alamar su zo wurinsa, cikin sauri Sageer ya riga Sadeeq zuwa suka zauna a gefensa." Kallonsa Jamila tayi ta d'anyi murmushin tace yarona Sauban yayi k'ok'ari sosai." Shima murmushi yayi ya Kuma had'e fuska ya kalli sadig da sagir yace "meyasa bakuzo na d'aya aka Baku kyauta ba Kuma makaranta kamar yanda aka Bawa kowa?" Ashe dama ba karatu kukeyi ba?" Baza kuyi koyi da yayanku Sauban ba?" Sageer yace munaso Abba, Sadeeq yace "Ni nafison nafishi ta ko Ina." Murmushin Abdullah yasaki domin ya dad'e da fahimtar duk halin mahaifiyarsa sadeeq ya d'auko, Yace "tayaya zakafishi bayan baka mayar da hankali a karatu ba, Gargad'i na k'arshe da zan Kuma yimaku shine duk kuka kuskura hakan ta Kuma kasancewa sai na d'aukar maku mataki." Jamila tayi karaf tace "tayaya?" A'a nifa bana son hakan, duk abinda ya faru da akwai wata a k'asa, Kai kutashi kushiga daga ciki Allah ya rayamunku domin Ni ka d'ai ke sonku a cikin gidan Nan." Suka tashi cikin sauri suka nufi d'akinsu, Ido kawai Abdullah ya zuba Mata baice da ita komai ba ya tashi ya fita Yana tir da Hali irin nata." Fitarsa b'angaren Hajjah yanufa ya d'auki Sauban ya fita dashi yanufi Gidan gonar mahaifiyarsa, Wanda ya lura da Sauban Yana matuk'ar son zuwa wurin Yana Jin dad'in KASANCEWARsa a cikin gidan gonar Koda yaushe tamkar mahaifiyarsa bintu Sai kusan k'arfe bakwai suka dawo gida, BaYan ya Kai Sauban b'angaren Hajjah snn yawuce masallaci sukayi sallar magariba tare da maimartaba suna cikin masallacin akayi Isha'i kamar yanda suka Saba a kullum, bayan sun kammala yin sallar ne suka fito a tare suna tafiya dogarai na biye dasu a baya Sarki yake cewa "Abdullah ya kamata kayi aure ka maye gurbin Bintu Wacce ta mutu, Murmushi kawai Abdullah yayi bai tankawa mahaifin nasaba, Sarki yaci gaba da cewa idan ka shirya ko a gobe zan d'aura maka aure, sai dai wnn karon mata biyu zaka aura a lokaci d'aya domin inason lokacin da zan sauka a kan kujerar mulki idan za'a d'oraka akai ya zamana kana da Mata hud'u kamar yanda aka San ko wanne sarki, idan ka cireni daga ciki koni akwai dalilina nayin Mata d'aya." Murmushi Abdullah yasaki baiyi magana ba domin koshi Yana da buk'atar k'arin auren koba komai ya dinga samun kulawa ya Kuma dinga samun natsuwa idan buk'atarsa ta motsa domin Jamila yanzun Bata da lokacin komai sai mulki dasaka a gaba da hidimar yaranta." Sarki yace Kai nake saurare meye ra'ayinka ko baka buk'ata ne?" Girgiza Kai Abdullah yayi cike da girmamawa yace "duk abinda kace shine dai dai, Bana da zab'i sai naka a kullum burina nayi maka biyayya na faranta maka nasaka ka farin ciki, ko yanzun ka shirya Nima a shirye nake za'a iya d'auramun auren da ko wacce macce kake so zan karb'eta hannu biyu." Sarki yaji dad'in furucin Abdullah Wanda sai murmushi yakeyi Yana girgiza kai, Ba Wanda ya sake yin magana a cikinsu har Abdullah ya Kai maimartaba d'akinsa kamar yanda yasaba idan suka dawo sallar, sai ya kaisa har d'akinsa snn yayi Masa sallama yafito yanufi d'akin Hajjah itama yayi Mata sallama snn yanufi nashi d'akin domin ya kwanta, Wnn karon bayan ya Kai maimartaba d'akin nasa wuri yasamu a gefensa ya zauna tare da sunkuyar da Kai Yana jiran ya Sanya Masa Albarka kamar yanda yasaba snn yatashi yafita." Sarki ya juyo ya dafa kansa kamar yanda yasaba yashiga "fad'in Abdullah Allah yayi maka Albarka Allah ya sanyawa rayuwarka hak''ika wnn biyayya da kakeyimun Allah yabaka d'anda zai lunka maka fiye da hakan , snn kazama cikin shiri gobe za'a d'aura maka aure da wasu tsala tsalan bayi wad'an da Aka 'yanta Naga sun dace da Kai Allah yabaku zuri'a Mai Albarka." 'Ameen Abdullah yace Yana murmushi Mai cike da jin dad'i." Wayarsa tayi ringing yayi kamar bazai d'aukaba sarki yayi murmushi yace ka d'auki wayar Mana." Cikin sauri ya Sanya hannu a Aljihu ya d'auko wayar, Ganin sunan Abokinsa ne Wanda suka tashi a tare wato sarkin Bauchi Wanda mahaifinsa ya rasu aka d'orashi a kan kujerar mulkin, Yana murmushin ya d'aga wayar tare da karawa a kunnensa da sallama a bakinsa, cike da tsokana Yake fad'in ranka ya dad'e sarki Allah ya k'ara maka lafiya ya kake?" Murmushi Abdulrahaman yayi yace "yau Kuma 'yar zolayace "to kiranka nayi domin nayi maka Albishir Sarauniya ta haihu ansami 'ya macce." Masha Allah Abdullah yashiga fad'i tare da cewa Ina kusa da Abba gashi ku gaisa sai ka fad'a Masa." Jin hakan sarki yasan Abdulrahaman ne sarkin Bauchi yakira Abdullah domin shi kad'ai ne Yake kiransa Abdullah idan suna tare wani lokacin ya kan k'arb'i wayar su gaisa tare da lurar dashi akan abinda ya shege Masa duhu akan lamarin sarauta, kasan cewar mahaifin Abdulrahaman Amine ne a wurin sarki mahaifin Abdullah." Sarki ya amshi wayar ya kara a kunnensa Yana murmushi bayan sun gaisa, Abdulrahaman Yake fad'awa sarki anyi Masa haihuwa ansami 'ya macce, Kasancewar matansa hud'u ba Wacce ta tab'a haihuwa sai yanzun." Masha Allah sarki yace tare da fad'ad'a fara'arsa yashiga fad'in "Allah ya raya SAUDAT yasanya Mata Albarka." Murmushi sarki Abdulrahaman yasaki domin yaji dad'in sunan da sarki yasaka ma 'yarsa, yashiga fad'in Masha Allah sunan yayi dad'i Abba Allah yak'ara girma da d'aukaka, tabbas ada nayi rashin mahaifi Amma a yanzun samunka duk ya kawar mun da Kashi hamsin a cikin d'ari na Rashin mahaifi da nayi, nagode Abba, yashiga godiya sarki Yana amsawa Yana murmushi snn ya mik'awa Abdullah wayar." Abdullah ya k'arb'a Yana fad'in sunan 'yarmu Saudat lallai Abba ya it's zab'en suna Mai dad'i, Allah ya raya Mana ita sai munshigo bikin suna gaba d'ayanmu." Hakan sukayi sallama ya kashe wayar, Snn yayiwa maimartaba sallama ya tashi ya fita cike da farin cikin gobe ne d'aurin Aurensa snn Babban Amininsa ya samu k'aruwar 'ya macce wacce sarki ya SAKAWA suna "SAUDAT." Washe gari ya Kama ranar juma'a kenan a babban masallacin k'ofar gidan sarki bayan an kammala sallar juma'a aka d'aurawa Abdullah Aure da bayinsa Khadija da Aishat, d'aurin auren da kowa ya shaida." Wanda Jamila sai dai ta tsinci maganar daga sama bayan anyi komai angama, Anan take sarki yasaka aka gyarawa kowa part d'inta kasancewar part 4 a b'angaren Abdullah, Wnn aure ya ba k'anwata Jamila rai musamman da taji duk bayine aka 'yanta Kuma aka aurawa mijinta." Jikinta baiyi sanyiba sai da safiya ta waye suka shigo gaida ita, anan taga zallar kyau da kwarji, batasan lokacin da idonta ya rufeba tashiga surfa masu ashar tare da korarsu daga b'angarenta." Kasan cewar sun san halinta Sarai yasa ko wacce daga cikinsu hankalinta bai tashiba illah ma suka sakar mata murmushi suna fad'in Allah ya hushi zuciyarki, dama Yarima ne yace muzo mugasheki ba Wai yin kanmu bane, suna fad'in hakan suka tashi suka bar Mata sashen nata." Tabd'i jam Ashe tsugunne Bata k'are kenan tinda Abdullah ya auro wad'an Nan tsala tsalan Yan Mata tabbas tasan ko kallon banza a yanzun Bata ishesaba yo Mai zaiyi da ita Yana ganin wad'an Nan Yan Mata wad'anda bata inda Allah ya ragesu, Ga wani sabon rainin wayo da suka zo Mata dashi cewar Wai Abdullah ne yace suzo su gaida ita, wato da baice suzoba bazasu zoba kenan, tabd'ijam lallai akwai aiki a gabana, To ko Bintu da take jinin sarauta gaba da baya ta buga tabarni bareku bayin banza da aka 'yanta, Ko Bintu da takeji da mulki tayi mun biyayya tabini da dason a zauna lafiya hakan bai sa naraga mataba bareku fitsararri bayin banza." Ta d'aga murya tana kiran jakadiya! jakadiya!! jakadiya!!!" *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *DIDECTED TO Fateemah M Uthman* *Page 10* Cikin sauri jakadiya taxo ta tsuguna a gabanta tana fad'in "gani uwar d'akina Allah y taimakeki ya k'ara maki lafiya." Jamila ta dubi jakadiya cikin b'acin Rai tace "kinada labarin abinda yake faruwa a cikin gidan Nan kuwa?" Jakadiya ta Kuma rinsinawa tare da sunkuyar dakai tace "ranki ya dad'e uward'akina ban San komai ba, me Yake faruwa a cikin gidan nan?" Jamila ta kalli jakadiya cikin jin haushi tace " Ni wad'an Nan bayin banzan wad'anda aka 'yanta zasu ciwa mutumci a gaban idona." Ni zasu kalli tsabar idona su cemun Yarima Abdullah ne yaturosu wurina domin su gaida Ni, wato suna nufin bayin kansu bane kenan tirsasu yayi, a matsayina na gimbiya, Ta d'aga murya cike da b'acin Rai "k'arya ne wlh duk abinda suke tak'ama dashi nafisu jinsa" dubunsu sun buga sun barni baresu bayin banza da wufi." Jakadiya tashi kitafi wurin bokanya ki fad'a Mata duk abinda ya ke faruwa, kada a kuskura a barsu su haihu a gidan Nan snn kifad'a Mata tasakasu a b'angaren masu Zaman banza a wurin mijina, Sauran bayani idan Kika tafi kibani ita a waya zan iyar Mata dashi." Jiki na rawa jakadiya tamik'e tare da k'arb'ar kud'i tafita tanufi k'auyen bokanya k'araba." ****************** Kwana biyu Kwanciyar hankali tare da natsuwa suka shiga Abdullah inda Yake samun kulawa daga wurin matansa Khadija da Aishat, Wad'anda kwatakwata basa bin takan Jamila kula da mijinsu kawai sukeyi tare da hidimarsa, hakan itama Hajjah tayi farin cikin ganin yanda hankalin Abdullah ya kwanta sosai." Ana hakan suka shiga shirye Shiryen tafiya Bauchi wurin bikin sunan 'yar da aka haifawa sarkin Bauchi." inda Jamila ta shirya tsaf tare da yaranta da Abdullah suka nufi Bauchi biki akabar Khadija da Aishat a gida, Wad'anda duk a tunaninsu tare dasu za'ayi tafiyar, kamar yanda Abdullah ya fad'a masu akan su shirya dasu za'a tafi, abin mamaki sai dai yakirasu a waya yace suyi hkr ya tafi da Jamila." Kasancewar Jamila Abokiyar maijego ce sosai" Basu nuna damuwarsu akan hakan ba illah sukayi Masa fatan Alheri tare da Addu'a'ar a dawo lafiya." A b'angaren Hajjah bataso akayi tafiyar Nan tare da Jamila ba, saboda sanin halinta da tayi komai zai iya faruwa kafin su dawo." A garin Bauchi anyi bikin sunan Saudat bikin suna nane na kece raini domin duk Wanda kagani Yana yawo a gidan bikin to jinin sarauta ne ko wanne Yanaji da mulki da Isa,, Kasan cewar sarautar Bauchi sarauta ce wacce ake nuna tsantsar mulki da Isa tare a cikinta." sosai Jamila ta yaba da kyawon Saudat inda anan take ta furtawa Mahaifiyar Saudat cewa, A gaskiya Saudat yarinyar ta shiga raina sosai domin kyakkyawa ce, Inama Zaki Bawa d'anki Sadeeq ita, domin nayi Masa sha'awar aurenta idan suka girma, Murmushi Mahaifiyar Saudat ta sauke ta kalli Jamila tayi Mata kallon bakida hankali, Tace " ai mijin Saudat ba'a K'ASAR Nan Yake ba, domin duk Wanda Saudat zata aura sai ya zamana yayi fice a duniya kowa ya sanshi a b'angaren kud'i da mulki to wnn shine mijin Saudat." Dariya Jamila kawai tasaki domin idan wani mulki takeji Mahaifiyar Saudat ta shafeta domin ita matar sarki ce ita Kuma matar d'an sarki ce, Snn idan kyau take ji dashi Mahaifiyar Saudat ta shafeta, Hakan idan boka take tak'ama dashi Mahaifiyar Saudat tsafi takeyi, tsakaninsu Kar Tasan Karne, Dan hakan komai rashin mutumcin Jamila tana shafawa Mahaifiyar Saudat lafiya." Hakan dai suka kammala hidimar bikin suka dawo gida, inda tun a can ta dinga zubawa Abdullah surkullenta a cikin abinci da ruwan Sha Yana shanyewa batare da yasani ba." Tin kafin su dawo jakadiya ta karb'o sauran ragowar maganin a wurin bokanya tashiga ai watar dashi a cikin gidan sak'o da lungu har part din su Khadija da Aishat." Sun sauka lafiya Shigowar su cikin gidan sarautar a Nan take Abdullah komai nasa ya canza, Baya son ganin kowa a duniya sai Jamila, a maimakon ya nufi d'akinsa domin ya huta Kai tsaye d'akin Jamila yanufa suka shiga a tare tana ganin hakan tasan aikinta ya faraci tashiga murmushi murna da farin ciki domin aikinta ya Fara tafiya a yanda takeso saura wad'an can bayin banzan tare da Sauban." Tin shigar Abdullah d'akin Jamila kwana biyu kenan bai fitoba, hakan yasa sarki yashiga nemansa idan ya aiko kiransa sai Jamila tace "bacci yakeyi idan ya tashi za'a fad'a Masa, hakan Hajjah itama kwana biyu ta daina ganin Abdullah tashiga tambayar ko lafiya?", Tana zaune labari ya risketa cewa ai Abdullah Yana Nan lafiyarsa k'alau Yana b'angaren Jamila kwanansa biyu bai fitoba ko lek'e, anan Yake Zaune Yana aiwatar da komai nasa" Murmushi Hajjah tayi tace Akira Mata matan Abdullah Khadija da Aishat, Bayan minti talatin suka shigo suka durk'usa a gabanta tare da gaida ita cike da biyayya da girmamawa." BaYan ta amsa gaisuwarsu ne take tambayarsu Ina mijinsu yashiga kwana biyu?" Shuru sukayi domin basa da amsar da zasu Bata, Hakan ya tabbatar wa da Hajjah labarin da aka fad'a Mata gaskiya ne kenan, Murmushi tayi tace kutashi kutafi kuci gaba da hakuri tare da Addu'a komai zaizo cikin sauki." Cikin ladabi suka mik'e suka fita, Hajjah na ganin fitarsu itama tamik'e tsaye tare da gyara Alk'yabbarta kuyanginta suka Mara Mata baya tanufi b'angaren Jamila, karo na biyu kenan da hajjah ta tab'a sanya k'afarta ta shiga b'angaren Jamila saboda Hajjah macce ce Mai k'awaici da Alkunya ga duk abinda ya shafi Abdullah." Kai tsaye part d'in Jamila tanufa tare da sallama d'auke a bakinta, Jamila tana kishin gid'e a kan kilishinta kuyanginta duk suna zagaye da ita ko wacce tana Mata hidima." Mamaki Hajjah tacika dashi ganin yanda Jamila take shinfid'a mulki tamkar itace Sarauniya matar sarki, Ko ita Bata abinda takeyi." Ganin Hajjah yasaka Jamila mik'ewa zaune tana fad'in "sannu da zuwa umma." Yawwa Hajjah tace cikin had'e fuska tare da nuna mulki da Isa, Ta kalli Jamila tace "kirawomun Abdullah " Jikin Jamila duk ya mutu saitaga Hajjah tayi mata wani irin kwarjini Wanda yasa takasa yimata musu ko jayayya illah ta mik'e tanufi d'akin da Abdullah yake cikinsa , A kwance ta tarar dashi Wanda aikin nasa kenan kwanciya yanaso yafita yarasa dalilin nasa na Rashin fitar , Yana kewar mahaifansa da matansa Amma ya rasa dalilin da yasa baya da k'arfin gwarwar yunkurin fita, Kallonsa tayi takashe Masa Ido d'aya cike da kissa tace "umma tana falo tanason ganinka tashi mutafi." Jikinsa na rawa ya mik'e tare da sanya talkaminsa yafito falon, Kallon juna sukayi da Hajjah yayi saurin zubewa k'asa kamar yanda yasaba ya gaida ita Yana murmushi." Kallonsa takeyi cike da tausayi taga har ya d'an rame, tabbas Abdullah ya gad'u da shu'umar macce Azzaluma, snn tasaki murmushi tana amsa gaisuwarsa ta dubeshi tace tashi mutafi inason magana da Kai, Bata Kuma bin takan jamila ba ta juya ta fita." Jiki a sanyaye yabi bayanta suka nufi b'angarenta." A gaban Hajjah yake zaune tana Masa fad'a bai tankaba illah ya sunkuyar da Kai k'asa, " Abdullah meyake damunka ne?" Ina kashiga kwana biyu mahaifinka yayi ta neman ka?" Ka kuwa San halin da kajefa mahaifinka kwana biyun na Rashin ganinka bayan kasan baya iya yini d'aya batare da ya sanyaka ido ba, kasancewar Kai kad'ai yake dashi, Ina hankalinka da tunaninka suka tafi ne?" Kana aikin me k'aidin macce da makircinta sukayi tasiri a kanka?" Shin ko ka Manta cewa wata Rana Kai sarki ne Kai ne zaka gaji sarautar mahaifinka idan kace hakan zakayi wani kallo kake tinanin Al'umma zasu dinga yima ka?" Meyasa kayi sakaci da Addu'o'e da mahaifinka Yake baka a ko wacce safiya domin kariya daga jikinka da lafiyarka?" nasan kwana biyun Nan ka daina gaba d'aya domin da kanayi da abinda ya Isa yayi tasiri akanka" Dafe kansa yayi komai yashiga dawo Masa baya, yashiga karanto Addu'oe a cikin ransa tare da runtse idonsa." Shuru Hajjah tayi tana kallonsa cike da tausayin sa Sai da taga ya Fara samun natsuwa snn ta dubeshi tanuna Masa d'akinsa dake cikin babban falonta Wanda tin kafin yayi aure wani lokacin anan Yake kwana , tace tashi kashiga ciki kayi wanka ka canza Kaya, sann kayi Arwala kayi nafila raka'a biyu tare da karatun Alk'ur'ani,.idan ka gama ka karanta Addu'ar da mahaifinka Ya baka snn kafito katafi fada Yana nemanka." Jiki ba kwari ya mik'e yanufi d'akin nasa domin ya ai watar da umurnin Mahaifiyar sa" Ai Kuwa Yana kammala yin sallar had'eda karatun Qur'ani yaji duk wata natsuwa tashigesa anan take komai nasa ya dawo Wanda ya gushe Masa, Karon farko matansa yashiga tunani ko lafiya sukeyi, Meyasa meshi hakan Wanda kamar an mantar dashi komai, a kansa, Bai gama samun natsuwa ba sai da yashiga karanta Addu'oen da mahaifinsa ya bashi na neman tsari daga sihiri, Tare da warware sihiri a jikin mutum Koda anyi masa, Sosai yasamu natsuwa BaYan ya kammala yinsu a Nan take ya dawo cikin hayyacinsa, snn yafito Yana murmushi ya durk'usa gaban Hajjah yace "umma nagode hak''ika kin kubutar Dani daga duhu, insha Allah hakan bazata Kuma faruwa ba." Murmushi tasaki tace "sakacinka ne Abdullah, ka daina sakaci da Addu'a domin kasan kana zagaye da makiya da ma hassada tashi katafi fada Idan kafito katafi wurin matanka domin kaji buk'atarsu ka lallashesu ka Kuma kwantar masu da hankali domin Suma sunshiga damuwa Allah yayi maka Albarka ya tsareka da sharrin masu sharri." Ameen yace "had'ida sunkuyar da Kai ya tashi ya fita yanufi fada, A fada ma hakan ta kasance nasiha sosai sarki yayita Masa, tare da bashi wani rubutu dake cikin gora ya shanye snn yak'ara Masa wasu Addu'oe a Nan ya Kuma jinsa ya k'ara samun natsuwa snn yayi Masa sallama yafito, Da kwarin gwaiwarsa had'ida natsuwa ya nufi sashen matansa wad'an kansu Yake a had'e suna zaune a wuri d'aya a cikin falonsa kasancewar anan suke Zama suna tattauna matsalarsu da yanda zasu b'ullowa Jamila." Jin sallamarsa yasa suka saki murmushi suka mik'e gaba d'ayansu suka tarbeshi tare da yimasa sannu da zuwa" Rungumesu yayi ya sunbaci ko waccen su a goshi snn ya Rik'a hannunsu suka zauna a tare a wurin d'aya suka sakashi a tsakiya, Karon farko hakuri ya Fara basu, Tin kafin ya iyar suka tareshi cikin kissa suna lallashinsa tare da kwantar Masa da hankali." Snn daga k'arshe suka gabatar Masa da abincin tare da kayan ciye ciye." Murmushi yakeyi Yana godewa Allah Akan ni'imar da yamasa na iyaye na gari da Mata na gari, BaYan yaci abincin ne ya janyo su zuwa jikinsa yashiga kwantar masu da hankali cikin hikima Yashiga basu hakuri." Kwana biyu komai Yana tafiya dai dai inda Abdullah baya Wasa da ibadarsa tare da Addu'o'e hakan yasa komai ya kwancewa Jamila sai kisan kud'i takeyi ba biyan buk'ata, Anan ta yanke shawarar janyo kowa a jikinta cikin siyasance har ta cin ma biyan buk'atarta, Babu abinda yafi d'aga Mata hankali irin yanda taga Abdullah yadawo kamar Abdullah sa na da Wanda tasani, baya shakkarta snn duk abinda zaiyi Mata Kai tsaye Yake Mata , batare da wani dibanya ba ko shakka Snn ta lura da yanda Yake matuk'ar ji da matansa fiye da ita, domin idan Yana tare dasu baya buk'atar kowa ya rabesa, ba kamar ita da yake Allah Allah safiya ta waye yabar d'akinta snn ko a wurin kwanciya sai dai idan itace ta nemesa." Snn ga SAUBAN yaron shima komai nasa sai dad'a ci gaba yakeyi, a yanzun Yana aji d'aya a secondry school komai nasa sai dad'a ci gaba yakeyi, Ita Kuma nata yaran suna Nan a yanda suke komai nasu sai dad'a yin baya yakeyi Wanda har taji haushin hakan ta ciresu a makarantar gaba d'aya tafi buk'atar a Kira malamai a gida a karantar Mata dasu tana kallo." Dan hakan kowa ya zira Mata Ido akan yaranta daga ciki kowa har da Abdullah Wanda take nuna Masa tamkar bashi ne mahaifinsu ba." To bare Hajjah wacce da yaran da rashinsu duk d'aya ne a wurinta, Shi Kuma sarki Yana fada ba komai yake sani Yana faruwa a cikin gidaba saboda a kwai Sarauniya ita ke gudanar da harkokin gida." Sauban yarone Wanda Yake matuk'ar son zumunci da Yan uwansa, hakan yasa da zarar ya dawo daga makaranta Yake fita Hajjah Bata saniba Yake zuwa part din Jamila wurin Yan uwansa, Hakan zaije ya zauna Sadeeq yazo wurinsa ya zauna sauban yayi ta koya Masa karatu, Tin Jamila tana kyamatarsa har ya Kai ta farajansa a jiki domin cikar burinta." Wata Rana yazo wurin Yan uwansa bayan sun kammala karatu, Jamila ta zubamasa abinci tace gashi yarona zauna kaci yau kahuta da cin abincin hajjah, Girgiza kai yayi yace "nagode mommy." Sai a lokacin Sadeeq ya Masa magana duk da ba wata magana yake masaba ko zuwa yayi Sageer kawai Yake kulashi, Yace haba Yaya Sauba kaci abincin mana, na lura bakacin abincin mommy idan ta baka." Sauban yayi murmushi yace "ba hakan bane Sageer na koshi ne shiyasa Amma zanci ko kad'an ne." Ya k'arb'i abincin ya faraci cokali biyu yayi ya ajiye yace "Alhamdulillah had'ida mik'ewa tsaye yace "natafi Y'an'uwa na sai da safenku." Tafiya yakeyi ya farajin cikinsa Yana hautsinawa Yana daf dashiga b'angaren Hajjah ya yanke jiki ya fad'i, sai kunfa yake fita a bakinsa." Da gudu bayi suka nufi wurin Hajjah suka fad'a Mata cikin Azama tafito ta tarar da Sauban gaba d'aya ba rai a jikinsa, cikin sauri takira sarkin mota aka nufi asibity dashi " Da Gaggawa likitoci suka amshesa suka shiga bashi taimako cikin gaggawa, Sai da aka d'auki lokaci Mai tsayi snn aka samu nasarar ceto rayuwarsa, Inda duk aune aunen da likitoci sukayi sun rasa gane abinda yaci, Kuma ga duk kan alamu bincike ya nuna akwai abinda yaci Wanda ya haifar Masa da wnn matsalar wacce da ba'ayi saurin kawo shi asibity ba da sai dai ya rasa rayuwarsa ." Hankalin kowa ya tashi da Jin hakan inda Hajjah ta tabbatar da Sauban bayacin abincin kowa a gidan sai nata Ko natan sai Wanda ta dafa da hannunta, To a Ina yasami abinci yacin da yaci?" Hakan sarki shima hankalinsa ya tashi matuk'a tare da Abdullah, Wanda sai bincike sukeyi a inda Sauban yaci abinci snn menene aka zuba Masa a cikin abincin." Jamila taji dad'i sosai dajin Sauban Yana kan gadon asibity inda tashiga d'aki tarufe dinga rawa da murna tana Addu'ar Allah yasa daga can sai kabari, A lokacin Da Abdullah ya dawo gida domin bincike sai ta marairaice ta zama kalar tausayi kamar zatayi kuka tashiga tambayarsa Yaya jikin d'anta Sauban?" Kwantar Mata da hankali yashigayi ganin tana Shirin zubar da hawaye domin ya fahimci yanzun Jamila tana matuk'ar son Sauban, Yashiga fad'in "kiyi hakuri insha Allah Sauban bazai mutuba zai Sami lafiya da Yardar Allah domin a halin yanzun anyi nasarar ceto numfashinsa ya dawo, Wanda likitoci sunyi iya bincinsu sungano wani abi yaci a cikin abinci Wanda ansara gane ko meye." A zubure tace numfashinsa ya dawo kana nufin kace mun Yana motsi kenan?" Murmushi Abdullah yasaki yace yafara motsi, yanzun binciken da mukeyi waye ya bashi abincin?" Ta Ina aka zuba Masa abincin?" Snn menene aka bashi yaci." Sarki yayi Alk'awarin muddun aka samo Wanda yayi wnn aikin zai fuskanci hukunci Mai tsanani Hakan Nima ko waye idan asirin sa ya tonu sai yasha mamaki na, Snn ki kula da SADEEQ da Sageer domin Suma komai zai iya faruwa dasu tinda akayiwa d'an uwansu hakan." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *DIDECTED TO Fateemah M Uthman* *Page 11* Shuru tayi domin kwatakwata Bataso aka zo Mata da labarin cewar Sauban ya farkaba, Ta d'auka ganin Abdullah da tayi a dai dai wannan lokacin mutuwar Sauban ce yazo ya fad'a Mata, Amma sai taji sab'anin hakan." Bata ankaraba tana cikin tinani ta Kuma jin muryar Abdullah Yana fad'in "ki daina tinani insha Allah Sauban zai tashi zai rayu zai Sami lafiya da Yardar Allah, Ya mik'e tsaye tare da sanya talkaminsa yace "Ni natafi zamuje muci gaba da bincike Allah ya tona marar gaskiya" Girgiza kai kawai tayi da kyar ta bud'e Baki tace "Allah ya bashi lafiya." "Ameen yace "yayi ficewarsa." Tana ganin fitarsa ta mik'e tsaye tashiga safa da Marwan tana tinanin idan bincike yayi bincike asirinta ya tonu, wani irin hali zata shiga idan asirinta ya tuno aka gano cewar itace tabashi magani yaci domin ya mutu, Wanda itama kanta batasan ko wanne irin magani bane, ita dai , a wurin bokanya jakadiya ta karb'o Mata shi." Shin wanne irin hukunci ne sarki ya tanadarwa Wanda ya aikatawa jikansa hakan." Zufa tashiga wanke Mata fuska, Tana cikin wnn Halin kuyangarta ta shigo ta zube a gabanta tana fad'in "ranki ya dad'e sarkin gida Yana son magana dake." Gabanta ya yanke ya fad'i ta kalli kuyangar tace "meyafaru me Yake so yacemun?" "Ranki ya dad'e Nima bansaniba Amma yace "afad'a maki magana zakuyi Mai mahimmamci ." "Kije kiyi Masa iso ki ajiyeshi a falon saukar Baki kifad'a Masa Ina zuwa." "To ranki ya dad'e Allah ya k'ara maki lafiya, kuyangar ta mik'e tafita domin ai watar da umurnin uwar d'akin nata." Sai da aka d'auki kusan minti 15 Bata fitoba sai da ta dai dai ta natsuwarta akan rud'anin da tashiga sannan tafito cikin k'asaita da nuna Isa tanufi inda sarkin gida Yake a zaune a d'akin Baki." Tana zuwa cikin Isa da nuna mulki ta nemi kujera ta zauna, Wanda dama sarkin gida Yana zaune a kan cafet, Sai da ta zauna ta d'auki k'afa d'aya ta d'ora akan d'aya snn ta juyo ta kalli sarkin gida dake durk'ushe a gabanta Yana fad'in "barka da fitowa gimbiya barka da fitowa sarauniyar gobe Kuma fulanin sarki in Allah ya yarda, Allah ya k'ara maki lafiya, Tsawa ta daka Masa domin tin farko sarkin gida baya cikin tsarinta asalima haushi yake Bata saboda suffar munafukai garesa, don Yana tsananin shiri da Hajjah sannan ta lura Yana matuk'ar son Sauban da kulawa dashi akan yaranta dako kallon banza basu ishesaba." "Me Yake tafe dakai ta fad'a a tsawace." Murmushi yasaki domin yasan Bata son ganinsa, yace "ranki ya dad'e zuwa nayi domin na jinjina maki akan namijin k'ok'arin da kikayi hak'ik'a kinyi matuk'ar k'ok'ari wurin samun nasarar Sauban yaci abincin dakika dafa a jiya, saboda Sauban yarone Mai tsananin wayau Kuma bayacin abincin kowa sai na Hajjah." Zaro Ido tayi cike da firgici, Ko me tatina a Nan take ta Kuma saita kanta tare da daka Masa tsawa "rufemun Baki mekakeso kace ne?" Kana nufin nice nazubawa Sauban wani abin a cikin abinci domin yaci ya mutu?" Ko kana nufin nice nayi yunkurin kashesa?" Lallai kanaso kayi Wasa da rayuwarka, Binciken da aka turoka kayi mun kenan?" to bara kaji kada ka manta Kai sarkin gida ne, Ni Kuma gimbiya ce ko yanzun idan naso zan iya cireka daga matsayin da kake nabawa wani snn daga k'arshe idan naso zanyi sanadin barinka gidan gaba d'aya, Dan hakan. Ka tsaya iya matsayinka kada kayi yunkurin shiga hurumin da banaka ba." Sarkin gida yace "hakan ne gimbiya matar yarima, gskya kina namijin k'ok'ari a cikin gidan Nan." to Amma Ni abinda bansaniba shine komeye ribarki ta son kikashe Sauban?" Kina tinanin idan binciken da sarki yakeyi idan ya gano kece sila komeye makomarki?" Waifa Ina ganin Dubara ta b'ace maki idon ki a rufe Yake shiyasa Kika aikata abinda Kika aikatawa Sauban, diba kigani." Ya Ciro wayarsa a Aljihunsa ya kunna video tin lokacin da Sauban yashiga b'angarenta har zuwa lokacin da yafito har fad'uwar da yayi da lokacin da ya fad'i ta lek'a ta gansa yashe a k'asa tasaki dariya ta koma ta rufe k'ofarta." Murmushin mugunta sarkin gida yasaki yace "mezakice Dan ganne da wnn video snn bashi kad'ai bane na ajiye wani a wuri Mai mahimmaci, Ya mik'e tsaye yace idan kinshirya magana Dani Zaki iya nemana tin kafin lokaci ya k'ure maki." Jikin Jamila duk yayi sanyi hankalinta ya tashi zufa sai tsiyaya take Mata a jiki kamar wacce tafito daga wanka takasa bud'e Baki tayi magana Har sarkin gida ya Kai bak'in k'ofar fita, sannan tamik'e tsaye tace "dakata sarkin gida." Cak ya tsaya batare da yajuyo ya kalletaba, Tafiya ta farayi sai da tazo daf dashi ta tsaya tace " nawa kake buk'ata domin ka rufe wnn maganar?" zan baka duk abinda kake so in har zaka rufe wnn maganar a cikin gidan Nan." Murmushi sarkin gida yasaki domin anzo wujen dama abinda Yake buk'ata yaji daga bakinta kenan saboda yasan watan arzikinsa ya kama." Juyowa yayi ya kalleta yasaki murmushi yace "miliyan biyu kawai nakeso daga gareki ba yawa." "Bani account no naka tace a tak'aice, Cikin sauri yashiga karanto mata, Yana Nan a tsaye cikin minti talatin yaji alert din miliyan uku." Ta dubeshi tace harda k'ari naiyimaka domin bana buk'atar naji makamanciyar wannan maganar Kafi kowa sani komai zan iya aikatawa Wanda ya zalinceni, Kasani muddun maganar Nan tafita bayan nabaka kud'ina kasani da Kai da zuri'arka Kuna cikin tsaka Mai wuya mutuwa ko rayuwa." "Bakida matsala indai wnn ne ai tinda kin biya shikenan, Ya Kuma zuwa gabanta ya durk'usa yace "kina burgeni ranki ya dad'e kud'i ba matsalarki bane shin me zai Hana kisaki kud'i domin a aika da Sauban lahira." Murmushi tasaki ta taka zuwa kan kujerarta ta zauna, shima sarkin gida ya dawo ya zauna a gabanta domin yaga maganarsa tasamu karb'uwa a wurinta." "Mekake gani za'ayi domin biyan buk'ata ta na ganin sauban ya bar duniya?" "Ranki ya dad'e ai wnn aikin Mai sauk'i ne abinda za'ayi shine, kisaye likitan dake kula dashi a asibity da kud'i, ya masa allurar guba a Nan take zai mutu wnn shine mafita." Dariya Jamila tasaki Mai sauti tace "Ashe dama kana da wnn tinanin da hikima tin tini ka gujeni ka nuna k'iyayyata a fili?" Kiyi hakuri ranki ya dad'e kece tin farko Kika nuna tsana ga gareni, wnn dalilin yasa bana wata alak'a dake sai dasu Hajjah wad'anda babu abinda suka tsinanamun tin iya zamana dasu sai dai nayita masu bauta Ashe ke Alheri ce." "Ya Isa tace." "Ta Yaya zanga likitan domin muyi maganar?" Ranki ya dad'e indai Zaki saki kud'i ganin likita baya da wani wahala Ni da kaina zan d'auko maki shi na kawo makishi har cikin falonki. Sabida kinsan Hajjah da sarki sun yarda Dani d'ari bisa d'ari." Murmushin farin ciki Jamila tasaki tace "ka burgeni ban tab'ajin farin ciki irin na yau ba, Kaje ka d'auko mun likita ko nawane zan bashi in har burina zai cika ganin Sauban ya daina motsi a doron k'asa, kaima zakayi murmushi domin idan burina ya cika za kayi mamakin abinda zanyi maka." "Godiya nake ranki ya dad'e bara natafi kada a ga mundade a wuri d'aya a zargi wani abin, ki Sanya idon ganinmu xuwa anjima tare da likitan." ************** Bincike akeyi sosai a cikin gidan sarautar domin ganin an kamo masu hannu a cikin wad'anda sukayi yunkurin kashe Sauban, Ba wani abu da aka gano ko wata alama, Wanda har da Jamila ake binciken wnn yasa ta b'atarwa mutane da hankali akan ayi bincike a kanta." Saboda tana matuk'ar nuna bakin cikinta Akan abinda ya faru, Inda Abdullah yake Mata kallon tafi kowa shiga cikin damuwa na faruwan lamarin wani lokacin har lallashinta yakeyi." *************** Sarkin gida sai zirga zirga yakeyi tsakanin gida da asibity domin Hajjah tayi matuk'ar yarda dashi duk abinda za'a sawo Dan gane da magani ko wani abun to shi ake Bawa kud'i Ya sawo, Wnn dalilin yasa yasamu damar keb'ewa wuri d'aya dashi da likita ya fad'a Masa cewar gimbiya tana buk'atar ganinsa yau da misalin k'arfe 8 na dare." Likita bai kawo komai a ransa ba, domin yaga yanda sarkin gida yake zirga zirga a asibityn sannan ya lura da yanda aka yarda dashi Ganin anyarda dashi d'ari bisa d'ari yasa baiyi tinanin komaiba ya amsa Masa da to idan yatashi daga asibity idan zai koma gida Yana Nan tafe, Yashiga tinanin wata k'ila akan maganar ciwon Sauban ne take nemansa." Misalin k'arfe 8 sarkin gida ya tsaya a can bayan asibity inda ba Wanda zai iya ganinsa yakira likita a waya, cikin minti 5 likita yafito daga asibity dama lokacin tashinsa yayi, ya tarar da sarkin gida ya d'aukeshi a mota ya nufi wurin gimbiya Jamila dashi." Hak'ik'a Jamila tayi farin cikin ganin likita a gabanta zaune sai murmushi take saki a fuskarta, Ta kalli likita da kyau tace "barka da zuwa doctor." "Yawwa hajiya barka da gida Yaya iyali?" inji likita." Bata amsa Masa ba tace "Yaya jikin Sauban d'in ?" ta kuma jeho Masa wata tambyar." "Alhamdulillah sauki yanata shigosa sai dai har yanzun lakkan jikinsa Bata Fara aiki ba domin. Abinda akayi amfani dashi, Yana da k'arfi sosai domin yafi guba masifa a jikin d'an adam Wanda har yanzun mun rasa Gane ko meye." Murmushi ta saki ta girgiza Kai, tace "likita katab'a rik'a miliyan 20 a matsayin naka na kanka?" Wata irin zabura tare da Zaro ido sarkin gida yayi Jin Ankira miliyan 20 to Ashe shi da yace abashi miliyan 2 kad'an ya d'iba kenan tab da yasani da yace sai anbashi miliyan goma." Girgiza Kai likita yayi yace "ranki ya dad'e a Ina zanga miliyan 20 bare har na rik'eta, kinsan aikin namu a k'ark'ashin wani mukeci, sai dai idan wata ya k'are muke k'arb'ar Albashi Wanda bazai wuce dubu 80 ba dashi muke rufawa iyalinmu asiri tare da 'yan uwanmu." Wani shu'umin murmushi Jamila tasaki tace "kana son ka mallaki miliyan 20 naka nakanka?" "Kwarai Kuwa likita yace tare da Kuma gyara Zama." Jamila tace "so nakeyi a matsayinka na likita Wanda kasan sirrin jikin d'an Adam so nake kasan yanda zakayi cikin hikima da dabara irin taku ta likitoci ka kawar mun da Sauban yaron gidan Nan Wanda kake kula dashi, ya bar duniya." Idan ka kawar dashi to kasani zaka mallaki miliyan 20 Kai har da ma k'ari domin zan K'ara yi maka wata kyautar ta ban mamaki." Zaro Ido likita yayi gumi ya shiga wanke Masa jiki, ga k'oshi ga kwanan yunwa, Yana son kud'i sosai Yana son ya mallaki miliyan 20 din Nan, to Amma idan asirinsa ya tonu Yaya zaiyi da sarki maimartaba Yaya zaiyi da aikinsa Wanda ya dad'e Yana nema da kyar yasameshi." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 12* Taimakon Gaggawa aka shiga Bawa Sauban inda aka sakashi a cikin wata na'ura domin ceto rayuwarsa." tayi yunkurin shiga inda yake likitoci suka dakatar da ita tare da Bata hakuri da lallashin akan bazata Sami ganinsa ba, Sai Nan da wata d'aya domin Yana cikin wani yanayi Wanda Addu'arsu kawai ake buk'ata" Shuru Hajjah tayi taja da baya, hankalinta a tashe Dan ganin takeyi Sauban bazai tashiba mutuwa kawai zaiyi, dibo da yanda taga wani irin kunfa Yana zuba a bakinsa, Wuri ta nema ta zauna fadawa suka zagayeta babu abinda takeyi sai Addu'ar Allah yabawa Sauban lafiya tare da rayuwa Mai d'orewa." Gimbiya bilkisu ta matso kusa da Hajjah tace "umma kiyi hakuri da izinin Allah Sauban zai tashi, zai Sami lafiya, har Abada makiya baxasu tab'a samun galaba akansa ba, Kizo mutafi masaukina ki ki huta har zuwa gobe idan Abdullah yaxo sai a San mafita." Hakan Hajjah ta amince tabi Gimbiya bilkisu tare da fadawan, Ko can d'in hakan bilkisu da Anna sukayi ta kwantarwa Hajjah da hankali snn ta Fara sakin jikinta a gidan, sai dai duk wani motsi nata da t Sauban a bakinta tana jera Masa Addu'o,e." ************ Duk iya bincike anyi ba wata alama da tanuni akwai sa hannun wani daga cikin gidan sarautar wurin yunkurin kisan Sauban, domin duk abinda za'ayi Jamila tana tare da Abdullah ana binciken da ita ba abinda takeyi sai aikin kuka a cewarta tana tsananin tausayin Sauban Halin da makiya suka sakashi me ya tare masu a duniya." Ba abinda Abdullah yakeyi sai Bata hakuri, hakan yasa ba Wanda yataba kawo bincike a kanta , hakan shima sarkin gida, Wanda duk abinda za'ayi a gidan shine a gaba Yana bada tashi gudun mawar, sabida Yar jajen sarki ne da Anna sunyi imani bazai tab'a cutar dasu ba, Dan hakan Koda Wasa ba'a tab'a kawo komai a kansuba." Hakan aka kammala bincike ba wani haske da aka samu, hankalin kowa ya koma England wurin Sauban washe gari Abdullah ya shiga jirgi ya sauka k'asar England domin dibo jikin sauban." BaYan tafiyarsa da sati biyu komai yayita faruwa daga ciki har da samun nasarar samun lafiyar sauban, domin numfashinsa ya dawo har ya Fara motsi, anyi nasarar gubar Bata iyar da gauraye jikinsaba batayi tasiri a jikinsaba " Satin Abdullah biyu a can ya dawo gida Nigeria tare da sauran bayi hud'u aka barwa Hajjah d'aya da kuyanga d'aya tare da Anna, domin ganin lafiya ta fara samuwa ga sauban duk da dai har yanzun ba Bari akeyi ana ganinsaba Yana cikin na'ura." Gimbiya bilkisu itake hidima dasu Hajjah wacce ba yanda Abdullah baiyiba Akan zai kamawa su Hajjah wurin zama Amma saita nuna b'acin ranta, tana fad'in wato zai nuna cewa Hajjah shi kad'ai ta haifa, Banda su kenan, Har sarki Abdulrahaman ta bugawa waya ta fad'a Masa Wanda shima yanuna b'acin ransa sosai dajin abinda Abdullah yace, hakan dai Abdullah ya basu hakuri yabar Hajjah a Nan snn yadawo gida Nigeria a cewarsa idan Sauban ya cika wata daya kamar yanda likitoci sukace zai Kuma dawowa tare da maimartaba domin su dubashi." A d'an Zaman da Hajjah tayi tare da gimbiya bilkisu ta Gane bilkisu macce ce Mai tsananin nuna mulki da Isa tare da izzah, sannan tana tsananin nuna soyayyarta ga tilon 'yarta wato Saudat, Tana son Saudat sosai Wanda sabida son da take Mata Bata bawa kowa rainonta kamar yanda aka San matar sarki Bata rainon d'a da kanta, tsakanin ta da yaro sai dai idan ankawo shi yasha nono, Amma bnda gimbiya bilkisu wacce a kullum tana tare da 'yarta hakan shima sarki Abdulrahaman da zarar ya bugo waya baya da wata magana sai ta Saudat, Hajjah ta jinjinawa wnn soyayya da sukayiwa Yar su kwaya d'aya tilo" BaYan wata d'aya Alhamdulillah jikin Sauban yayi kyau yasamu lafiya Wanda har magana yakeyi Kuma Yana cin abinci sosai." A ranar sarki da Abdullah tare da sarki Abdulrahaman sukazo k'asar, tabbas sunji Dadi sosai ganin Sauban yasami lafiya Wanda yake zaune Akan kujera ana fira dashi." Anan sarki Abdulrahaman Ya kalli maimartaba tare da Abdullah da Hajjah ya Fara da cewa "ku ga farce ranka ya dad'e Ina neman wata Alfarma a wurinka Allah yasa zaka Amince da hakan, ranka ya dad'e Ina neman Alfarmar a bar Sauban k'asar Nan wurin gimbiya bilkisu domin taci gaba da kula dashi har lokacin da zai kuma samin lafiya, Snn idan ya warke Ina neman Alfarma akan a barshi a hannunta yayi karatunsa anan har zuwa lokacin da ya mallaki hankalin kansa yasan abinda Yake Masa ciwo lokacin da zai fahimci makiyi da masoyi snn sai yakoma gida Nigeria, diba da yanda ake farautar rayuwarsa makiyansa k'ok'ari sukeyi ta ko wacce hanya so sukeyi sai sunga bayansa." Shuru kowa yayi yarasa amsar da zaibawa sarki Abdulrahaman domin shawarar da yanke tayiwa kowa dad'i a wurin sai murmushi ko wannesu yake saukewa." Snn Sarkin yayi gyaran murya Fara magana kamar hakan "hak'ik'a Abdulrahaman kayi matuk'ar tunani tare da hangen nesa muna godiya da wnn karamci naka Allah yabar tare ya raya maka zuri'a." Hakan Hajjah itama tayi Masa Addu'oe godiya tare da sanya Albarka, Murmushin kawai Abdullah yakeyi cike da farin ciki domin yarasa abinda zaiwa Aminin nasa, iya k'auna sarkin Abdulrahaman ya nuna Masa ita da karamci, mik'ewa yayi tsaye fuskarsa tana saukar da murmushi yanufi inda Abdulrahaman yake zaune Abdullah ya rungume shi Yana Masa godiya, Yana fad'in " nagode Aminina yanda kayi mun Allah yabani abinda zanyi maka fiye da hakan hak'ik'a Kai abokine Kuma Aminine na kwarai." Yinin ranar kowa cike yake da farin ciki, Sai da sukayi sati d'aya a lokacin sauban ya Kuma Samun lafiya sosai har an sallamoshi daga asibity sundawo gida, snn suka tattara kayansu har da hajjah suka dawo gida Nigeria suka bar Sauban a England wnn shine dalilin Zaman Sauban a k'asar England karatu." _muje zuwa my friend's_⛹🏻‍♀ Bakaramin bak'in ciki da damuwa Jamila tashiga cikinsaba jin Sauban yasamu lafiya sosai k'arin Jin dad'i har da barinsa akayi a can domin yayi karatu, Wato ana nufin bama a kasar Nan zaiyi karatuba kenan, So akeyi yafi kowa karatu a gidan kenan?" Tacije Baki taji wani irin tsanar Sauban tare da Hajjah ya dirar mata a zuciya domin tasan wnn duk shirrin Hajjah ne, Domin ba Wanda Hajjah takeso takeso ganin ci gabansa kamar Sauban, ta rasa dalilin da yasa ta tsani nata yaran Sadeeq da Sageer, wadan da ta fahimci ba Hajjah kawai ta tsanesu duk mutanen gidan basa sonsu ganin ido NE kawai da Kuma tana tsaye a kan yaranta." ta d'auki d'amarar indai tana da Rai da lafiya ko a can Sauban bazai tab'a samun abinda yakeso ba, Indai kud'i suna aiki sauban bazai tab'a fitowa da sakamako Mai kyauba Sauban bazai tab'a Jin dad'in rayuwarsa ko bai mutuba sai Nigeria tayi Masa wahalar Shigowa sai ta Sanya anyi tir da alawaddan karatunsa." BaYan kwana biyu matan Abdullah suka haihuwa dukansu suka Sami 'Ya'ya Mata, Khadija ta haihu ranar Monday Aisha ta haihu ranar Friday." Murna a cikin masarautar abin ba'a magana, Wanda Ina wuta Jamila tafad'a domin kwatakwata batasan ma suna d'auke da cikiba sai dai kwatsam taji haihuwarsu daga sama abinda yafi Kona Mata Rai Kenan." Jakadiya ta shiga dokawa Kira cikin sauri jakadiya tazo ta zube a gabanta, Cikin d'aga murya tace "ya akayi wad'an can bayin banzan suka haihu a cikin gidan Nan?" Dama suna dauke da ciki Baki fadamun ba?" Ta d'aga murya cikin b'acin Rai ta Zaro Ido alamar komai tana iya aikatawa jakadiya tace fad'amun nawa suka Baki domin kib'oyemun cewa suna dauke da cikin Abdullah a cikin gidan Nan ban saniba." Sunkuyar da Kai jakadiya tayi cike da tsoro jikinta Yana rawa cikin girmamawa tace "ranki ya dad'e har Abada kud'i bazasu tab'a tasiri a gareniba har na Kai ga cin amanarki, Yanda Kika San Baki San komai Dan gane da cikin jikinsuba sai dai kikaji haihuwa daga sama, Nima hakan ne a gareni ban San komai ba akai kiyi hakuri ranki ya dad'e Allah ya huci zuciyarki, Amma Kuma ranki ya dad'e meye abin daga hankali da haihuwarsu Bayan dukansu Mata suka haifa ba maxa ba, Koda maza ne suka haifa Sadeeq da Sageer sune a gaban 'ya'yansu nesa ba kusaba nayi imani d'aya daga cikinsu shi zaiyi mulkin masarautar Adamawa." Wani murmushi Jamila tasaki najin dad'in ance d'anta zaiyi mulki, Ta dubi jakadiya tace "tashi kitafi naji kin wanke mun DUK wata damuwata, Kece da shegen kwadayin tsiya nasan za'a iya sayenki da kud'i Wanda idan na fahimci hakan sanyawa zanyi a saremun kanki kinsan ba tausayi ne daniba komai zan iya aikatawa, don hakan Dole ne na zargekeki kibi a sannu domin na tsane cin Amana" Tuba nakeyi ranki ya dad'e nafi kowa sanin halinki insha Allah hakan bazai tab'a faruwa ba, ki huta lafiya jakadiya tamik'e ta fita a ranta tana tsinewa Jamila akan tuhumar da tayi Mata bada laifintaba" Anyi shagalin suna a gidan sarautar Wanda Jamila ta bada tata gudunmawa sosai komai da ita akayi sosai take nuna k'auna ga matan Abdullah tare da jaririansu, Sai dai ta ciki na ciki bak'in ciki ne fal a ranta musamman yanda taga Hajjah tana farin ciki da haihuwar Wanda Sam bataga irin wnn farin cikin a fuskarka taba a lokacin da ta haifi su Sadeeq, Hakan shima Abdullah sai murmushi yakeyi Yana farin ciki daga ganinsa kasan Yana tare farin ciki, hakan dai akayi taron suna aka watse yara suka ci sunan fateema Bintu wato sunan mahaifiyar Sauban kenan wacce Abdullah bazai tab'a mantawa da ita ba, d'ayan Kuma taci sunan Hajaru wato sunan Hajjah Kenan, sarki yace Kuma Sam bai yarda da a canza basu suna ba a hakan za'adin kiran sunansu." Hakan yayiwa duk wani mutum dake cikin masarautar Dadi Amma Banda Jamila da mak'arabanta." ************** Sauban ya Fara zuwa makaranta secondry school inda ya Fara daga jss1 kasancewar karatun can ba d'aya bane da karatun Nigeria, Sosai Yake hazaka da k'ok'ari har malaman makarantar sun Fara Alfahari dashi Akan karatunsa, Hakan gimbiya bilkisu tana kula da karatunsa tare da addininsa sosai da Kuma tarbiyansa." BaYan wata uku da bikin 'ya'yan Abdullah, Sarki ya kwanta ciwo Wanda har asibity ya kwanta yasamu lafiya ya dawo gida, Tin daga lokacin lafiya ta Kiya Masa yau ciwo gobe lafiya, Wata safiyar juma'a aka waye gari sarki yace ga garinku Nan." Mutuwar sarki ta girgiza Al'ummar garinsa dama wajen garin Baki d'aya domin duk Wanda yasan sarki Abdulsalam sarkin dake mulkin masarautar Adamawa yasan sarki ne Mai Adalci da sanin ya kamata sai dai duk da hakan mutuwa Bata barin wani Dan wani." Abdullah yashiga cikin tashin hankalin mutuwar mahaifinsa hakan Hajjah wacce takasayin magana sai girgiza Kai kawai takeyi, hakan akayi Masa wanka akayi Masa sitira aka kaishi gidansa na gaskiya." Mutune k'asa k'asa jahohi sarakuna da shuwa gabannin k'asa duk sun zo wurin ta aziyar mutuwar sarki Abdulsalam, BaYan wata biyu da mutuwar sarki aka yanke hukuncin nad'a magajin sarki wato Abdullah." Murna a wurin Jamila abun ba'a magana domin idan kowa Yana bakin cikin mutuwar sarki ita farin ciki takeyi sabida mijinta zai maye gurbinsa ya Zama sarki Dole a kirata da Sarauniya Kuma fulanin sarki, Dole Hajjah taja baya tayi kallo don Dole sarautar gida ta dawo a hannunta don itace matar sarki a yanzun." D'aya ga watan match aka nad'aga sarki Abdullah a kan kujerar mulkin Adamawa hakan itama Jamila aka d'agata a matsayin Sarauniya Kuma fulanin sarki domin ta Hana a Bawa kowa sarautar fulani, tin daga lokacin sunanta ya tashi daga gimbiya Jamila ya koma Fulani ko Kuma kuce Sarauniya. Duk wani ragamar cikin gidan sarautar itace take gudanar da komai, batare da tayi shawara da kowa ba, Hakan sauran matan sarki Abdullah basa da abin cewa saboda dukansu ta kaisu wurin boka an d'aure Mata bakinsu sai yanda tayi dasu a cikin gidan." Duk abinda takeyi Hajjah tana sane da ita sai dai takawo nagani ta zuba Mata domin tasan komai lokaci ne garesa wata Rana sai labari, Hakan zata Kira sauran matan Abdullah ta dinga yimasu nasiha tare da basu hakurin akan abinda suke gani Jamila tana aiwatarwa a gidan komai Yana da lokacin sa." Basa nuna damuwarsu Akan ta saboda mijinsu bai wulakantasu bai bai nuna kyamata a garesu ba hasalima yafi samun natsuwa a tare dasu to meye abin daga hankali a ciki?" Sunsani Sarai harda shima Abdullah Bata barshi a banza ba Dan hkn yke biye Mata ga duk abinda takeso amma ai komai Yana da lokacin sa Mai hakuri bazai tab'a tab'ewaba." ***************** A kwana a tashi ba wuya har Sauban ya kammala karatun sa na secondary ya Fara zuwa jami'a mataki na farko a lokacin yana da shekara goma Sha tara Ya girma duk wani kyau nasa ya bayyana, dama Sauban kyakkyawa ne, snn mutum ne ba mai yawan son magana ba tin Yana k'aramunsa bare yanzun, snn baya son a damesa da yawan magana, Dan hakan baya da wani aboki sai safwan Wanda d'an abokin Abbansa ne da aka turosa karatu a Nan England Sosai tasu tazo d'aya da Safwan saboda safwan Yana da son karatu sosai kusan duk ra'ayinsu yaxo d'aya, sai dai shi safwan da zarar anyi hutu yake komawa gida Nigeria sab'anin Sauban da yake Zaune a k'asar gaba d'aya, Waje d'aya ra'ayinsu ya banbanta da sauban, Shine safwan akwai shi da son hirar 'yan Mata abinda Sauban ya tsana kenan , snn safwan Yana da yawan surutu da barkwanci da son ya shiga abinda da bai shafesaba abinda Sauban ya tsafi tsana kenan a rayuwarsa, dan hakan wani lokacin yakeji haushin safwan idan suka hadu a makaranta." A lokacin da Sauban Yake da shekara goma Sha Tara a lokacin Saudat take da shekara Tara a duniya, Saudat yarinya ce Yar gata sangartaccciya wacce uwarta da ubanta suke sonta, tare da sakanta ta, Basa son ganin kukanta bare b'acin ranta, A duniya duk abinda Saudat take buk'ata batare da b'ata lokaci ba ake Mata shi. Wnn dalilin yasa Bata ganin girman kowa musamman bayinta masu kula da ita maza da mata duk Wanda ya Mata ba dai dai zata d'aga hannu ta wanke sa da mari ko a gaban mahaifiyarta Bata ce Mata komai sai majinjina da zata kumayi Mata na burgewa " Wnn halayan nata na sangarta da rashin ganin darajar mutum tin tana karamarta, yasaka gaba d'aya yarinyar Bata burge Sauban, Kwata kwata Bata bashi sha'awa, Ita kuma Saudat tana tsananin son Sauban domin ko abinci aka kammala Bata ci sai har lokacin da Sauban yadawo a duk inda ya tafi snn zataje ta d'auko takawo Masa a d'akinsa su zauna suci a tare, ba Dan ransa Yana soba sai Dan gudun kada iyayenta suga kamar Yana tsanar yarsu", Bayan sunyi Masa halacci a rayuwa Amma shi a zuciyarsa har ga Allah ya tsane yarinyar ba Kuma yarinyar ya tsanaba sangartar ta da halayenta ya tsana, Bayaso kwata kwata tana shigo Masa d'aki tana fad'awa a kan jikinsa, Wanda ya lura ko a gaban idon mahaifiyarta ta fad'a a kan jikinsa Bata yimata magana illah ta dinga murmushi tana d'aukar hakan ba komai bane." Saudat tana aji hud'u a primary, Abinda Sauban ya lura dashi shine ko a makarantar tasu Wasa da maza ba komai bane a gareta, gaba d'aya Bata mu'amala da Mata 'Yan uwanta Abokananta sune maza." Akwai wani lokaci da yaje d'auko ta a makaranta kasancewar shi yake Kai ta idan zaitafi makaranta Yake ajiyeta idan Kuma ya dawo yakan tsaya ya daukota su dawo a tare, lokacin da yaje daukota ya tarar da ita zaune Akan k'afar wani malaminsu bature jar fata sai shafata yakeyi tana dariya." Cikin b'acin Rai ya fincikota daga jikinsa ya kifa Mata Mari sosai yayiwa baturen rashin mutumci snn yasakata a mota suka nufo gida." Duk a tunaninsa zata fadawa mahaifiyarta Domin ya shirya abinda zai fadawa gimbiya bilkisu Wanda sanadin hakan yafison ya bar gidan gaba d'aya dama Zaman gida yafice Masa a Rai sam." Amma Sam Saudat Bata fad'a mataba, Illah tin daga lokacin tashiga Jin tsoron Sauban duk wani abin idan tanayinsa Bata barin sauban yagani, saboda a duniya ba Wanda ya tab'a dukanta sai Sauban Dan hakan take tsananin jin tsoronsa." Wasa Wasa Saudat sai girma take k'arawa Wanda har ta kammala primary school tashiga jss1, A lokacin tafara sanin ko ita wacece ko ita 'yar wacece, Tafarajin kanta Yana Mata girma, dan ta Kira bayinta ta wulakantasu ba wani abin bane gareta, domin mahaifiyarta tana nuna Mata k'askantune a wurinta ta wulakantasu yanda ranta yakeso snn tayi mulkinta yanda takeso ita kad'ai CE wurin mahaifinta Kuma sabida da ita suke zaune a k'asar England." Wnn dalilin yasa Saudat ta tashi da girman Kai da nuna Isa da mulki Wanda a duniya ba Wanda take tsoro sai Sauban." Lura da tana D'an Jin tsoron Sauban yasa wata Rana Mahaifiyarta takirata tashiga fad'a Mata cewa ta dainajin tsoron Sauban idan ta ganshi ta daina firgita tana fasa abinda tayi niya, tasani ba wani dangata dake tsananinsu asalima taimakonsa sukayi suka tsiratar da rayuwarsa daga mutuwa." Shuru Saudat tayi batayiwa Mahaifiyar tata maganaba sai da d'auki Yan mintina snn ta dubi mahaifiyar tata tace "mommy Ina son Sauban shine mijina Zaki aura mun shi?" Ina sonshi a duk yanda Yake Tas taji Mari a kuncinta gimbiya bilkisu tana Mata wani kallo, cikin daga murya tace "nawa kike mekikasani a duniya dangane da aure shekararki nawa 13 kike zan cen aure, To bara kiji Koda kin Isa aure bazan tab'a aura maki Sauban ba saboda Baku daceba gaba d'aya baya cikin tsarin maxan da nakeso ki aura, Kisani ke kad'ai muka haifa a duniya mahaifinki sarki ne, Dan hakan Ina da burin ki auri namiji Wanda yayi fice a duniya Wanda sunan sa yayi fice kowa yasanshi a duniya ba kamar Sauban ba, kada na Kuma jin wnn maganar a bakinki, ta janyota tana lallashinta sakamakon Marin da tayi Mata." Duk abinda gimbiya bilkisu take fad'a a kunnen Sauban a lokacin ya tinkaro d'akin nata domin ya gaida ita, karaf a kunnensa yaji tana fad'in hakan ya girgiza Kai yafita shima a zuciyarsa Yana fad'in mezaiyi da ita Koda Mata sun Kare a duniya bazai tab'a auren Saudat ba." Wani abin d'aure Kai dake faruwa a makarantarsu Sauban shine yanzun shekara biyu kenan duk akayi jarabawa bayaci faduwa yakeyi duk su safwan sun wucesa, Bayan yasan duk a ciki d'aliban makarantar ba wani Wanda zai d'aga hannu ya ce yafishi k'ok'ari, indai a wurin karatune Sauban shine sahun farko, Amma abin mamaki da zarar an like suna ba wani ci gaba da Yake gani a tare dashi shekara biyu kenan Yana maimaita shekara duk wani mate nashi ya wuce shi a karatu." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 13* Abin Yana damun sarki Abdullah a kan rashin ci gaban karatun sauban, kullum Yana Nan a yanda yake." Hakan yayi tattaki yaje da kansa k'asar batare da kowa yasaniba domin yayi bincike Akan abinda Yake faruwa, Kai tsaye makarantar ya sauka a ofishin shugaban makaranta." Bayan sun gaisa tin kafin sarki Abdullah yayi magana ya fad'i abinda ya kawoshi shugaban makaranta ya Fara da cewa "ranka ya dad'e dama ko da bakazoba mun yanke shawarar zamu aika maka da sak'o ta hanyar wayarka domin musanar dakai abinda Yake faruwa koda Kai zaka d'auki wani mataki a kan yaronka,sauban Sabida munfad'awa mahaifiyarsa wacce suke tare a Nan duk abinda Yake faruwa akan karatun nasa ba wani mataki da ta d'auka har yanzun, domin mun yanke hukuncin da zarar mun fad'a maka baka kaima baka d'auki wani matakiba to tabbas kararsa zamuyi a makarantar nan" Wato yaronka Sauban nasara dalilin da yasa yafi ko wanne d'alibi fad'uwa a makarantar Nan Na Tara duka malamai nayi bincike akansa domin naji dalilin fad'uwar nasa, Amsa d'aya ce baya karatu." Dan hakan muka yanke hukuncin zamu kiraka mufada maka, idan wata makaranta zaka canxa Masa hanya a bud'e take mu munfi son hakan." Shuru sarki Abdullah yayi snn yabude Baki yace "abinda yakawoni k'asar Nan kenan don nayi bincike saboda nima abin Yana damuna matuk'a, Amma maganar Nan da kayimun na yanke shawarar fitar dashi daga wnn makarantar zan canza Masa wata, ya mik'e tsaye tare da mik'awa shugaban makarantar hannu yace "godiya nakeyi sai anjima yafita." Kai tsaye gidan Aminin nasa yanufa inda Sauban Yake da Zama, Bazata Sarauniya bilkisu taga zuwan sarki Abdullah, inda ta nuna mamakinta a fili." Bayan sun gaisa cike da girmamawa snn tasaka bayinta aka kawo Masa abinci tare da kayan motsa baki, sai da ya kammala cin komai snn ta Kuma dawowa cike da izzah da Isa suka Kuma gaisawa." Daga Nan Yake fadamata abinda ya kawoshi k'asar Akan karatun Sauban." Sosai Sarauniya bilkisu taji kunya domin ansanar da ita hakan a makarantar shap mantawa tayi Bata d'auki wani mataki akai ba." Lura da hakan da maimartaba yayi yasa ya kawar da zancen akan cewa 'ina shi Sauban din Yake Yana son ganin sa, yanaso suyi magana idan da akwai makarantar da yakeso ya fad'a, ayi komai daga you zuwa gobe, Domin gobe yakeso ya koma." Mik'ewa tayi jiki a sanyaye tanufi b'angaren Sauban domin ta kirashi, anan ta gamu da wani bafade Yana shawagi Wanda shi aikinsa kenan a cikin gidan, Takirashi tace yatafi d'akin Sauban yace yazo mahaifinsa sarkin Adamawa Yazo yana kiransa" Sauban Yana Yana kwance rigingine akan gadonsa Yana tunanin abubuwan da sukayita faruwa dashi tin Yana yaronsa har zuwa yanzun, Yanaso yaje k'asarsa ta haihuwa Amma saboda ana farautar rayuwarsa yasa baya sha'awar zuwa, Snn anan ma ba'a barsaba an hanashi yin karatunsa cikin kwanciya hankali sai shige da fice ake Masa Akan karantunsa Wanda yasan duk abinda Yake faruwa daga masarautar gidansu Yake fitowa Dan kuwa shekaranjiya Yana makaranta a zaune yaga waziri, yafito daga ofishin shugaban makaranta yayo Masa rakiya suna dariya fuskokinsu cike da farin ciki." Meya tare masune dabasa son ganin farin cikinsa, shifa haihuwarsu akayi bashine ya haifi kansaba laifin me ya masu, tabbas lokaci Yana zuwa da zai dakatar da duk wani mugun abunda suke nufi akansa." K'arar kwankwasar k'ofar d'akinsa ya ankarar dashi daga duniyar tunanin da Yafad'a Jikin ba kwari ya mik'e yaje ya bud'e k'ofar Yana kallon waye?"" Bafade yagani yayi saurin durkushewa gabansa Yana fad'in ranka ya dad'e maimartaba sarkin Adamawa yanason magana dakai." Murmushi yasaki na farin cikin jin mahaifinsa yazo, ya d'agawa bafaden hannu had'ida d'aga Kai alamar gashi Nan zuwa." Komawa yayi yasaka manyan kayansa harda hula sab'anin k'ananun Kaya dake jikinsa gudun kada sarki yayi Masa fad'a akan saka k'ananun Kaya kamar yanda yake Masa a duk lokacin da ya gansa da su." A gaban mahaifinsa yake Durkushe Bayan ya gaidashi cike da girmamawa, Murmushi kawai sarki yakeyi Yana kallon d'ansa mafi soyuwa a ransa tare da tausayinsa." Anan sarki yashiga fad'a masa abinda ya kawo shi, tare da yi Masa fad'a Akan ya dinga tsayawa Yana karatu ya daina Sanya Wasa a karatunsa ya d'iba yagani duk wad'anda suke karatu a tare duk sun wuce sa suna gabansa." Sunkuyar da Kai Sauban yayi sai da Abban nasa ya gama yimasa fad'a yayi shuru." snn sauban ya d'aga Kai ya kallesa cike da girmamawa ya d'an sunkuya yace Abba kayi hakuri insha Allah bazan sake ba." Washe gari sarki Abdullah bebar k'asarba sai da ya kammala yiwa sauban komai na dangane da karatunsa ya canza Masa wata makarantar da duk wani abin da yasan Yana buk'ata snn ya yaje yayiwa sarauniya bilkisu sallama tare da godiya yashiga jirgi yanufi k'asar sa NIGERIA" Sosai safwan yayi bakin cikin canjin makaranta da akayiwa Aminin nasa wani b'angare , idan ya Tina da dalilin yin hakan yakanji Dadi a ransa, domin yawan fad'uwar Sauban a makaranta shima abin Yana damunsa Wanda iya bincike sunyi bincike sun rasa sanin dalili, Sai dai duk da hakan amintansu tana Nan domin da zarar antashi daga makaranta safwan Yana wurin sauban duk dai da dai shi ke biyarsa Sauban ko ajikinsa domin wani irin miskiline Wanda baka Gane gabansa bare bayansa snn mutum ne ba Mai son yawan magana ba, snn duk abinda Yake damunsa bazaka tab'a ganewaba bare ganin b'acin rai a fuskarsa. sai dai ya bar komai a ransa." Hirar safwan da Sauban itace a kullum safwan baya da wata Hira idan suka hadu sai ta Aure a rayuwar safwan shi dai ya Matsu lokaci yazo yayi aure, domin shi kad'ai yasan yanayin da Yake shiga a duk lokacin da yayi Ido biyu da Jajayen fata masu yawo tsirara." Harara kawai Sauban Yake watsa Masa tare da jamasa dogon tsaki batare da ya tanka Masaba." safwan zai waiga ya kallesa ya mere Baki yaci gaba da maganarsa domin ba zai fasa gayamasa abinda ke ransa ba akan aure." Wani lokacin Kuma idan yanason tsokanar Sauban Dan yayi magana ya biye Masa, sai dinga cemasa dama irinku marasa maganar Nan idan Kika Sami macce sai kunyi kamar bazaku barta da Raina Akan jaraba, har gwara mu muna fitar da abinda ke cikin ranmu." To a lokaci Sauban sai Kuma Jan dogon tsaki tare da wurga Masa da kallon baka da hankali." Hakan rayuwa taci gaba da tafiya, Wanda canjin makarantar da akayiwa sauban ya Fara ganin haske a karatun nasa, Shima safwan ya kammala karatun NCE nasa Ya dawo a makarantar su Sauban ya jona dgree d'insa, suka Kuma had'ewa wuri d'aya." Akwana a tashi ba wuya Saudat ta kusan kammala secondary school yanzun tana aji shidda a secondry duk wata cika da halittar jikinta na matsayinta na cikakakkiyar macce duk ta bayyana, Ba laifi Saudat kyakkyawa ce Dan duk inda 'ya macce zata d'aga hannun ta nuna ita kyakkyawace Saudat zata d'aga nata, Sai dai rayuwar turai da ta ratsata zuciyarta, Gaba d'aya ta zubar da Al'adarta ta jinin saurata ta d'auko rayuwar turawa ta d'orawa kanta, Wanda da zarar kikaga Saudat idan bakin santaba bakya tab'a cewa ta had'a wata alak'a da musulmi, musamman yanayin shigarta da yanda take ma'amala da maza, Hakan bai saka Sarauniya bilkisu taga kuskurentaba bare ta tsawata Mata, Bare Sauban Wanda da abinda ya damesa yanuna zai dinga tsawata Mata bilkisu ta dakatar dashi tana fad'in ya barta tayi abinda ranta yakeso kada ya takurata tinda shi ba Wanda ya saka Masa Ido bare ya takurashi a kan duk abinda zaiyi." Tin a lokacin sauban ya kawo nagani ya zubawa Saudat akan shigar da takeyi baya Mata magana, sai dai Abu d'aya ne yaji baya iya kyaleta shine rungumar maza tare da Hawa Kan kafafunsu, ko kwantawa akan jikinsu wnn yakan Dan tsawata Mata idan yagani, Wanda wnn komai bane a wurin saudat." Takan d'anji tsoron Sauban idan ta ganshi tana daina wani abun a gaban idonsa." Saudat macce ce Mai yawan sha'awa, da zarar ta had'a jiki da namiji takejin wani Dadi ya ratsata har sai ta jik'a pant nata Wannan dalilin yasa take yawan fad'awa jikin maza suna cud'anya domin taji Dadi domin hakan yakan Dan rage Mata wani radadi." K'arfe biyu na dare Sarauniya bilkisu ta tashiga d'akin Saudat domin tadibo tagani kotayi bacci, wata k'ila tabar komai a kunne, daga Nan ta gyara Mata kwanciya tare da lullub'eta kamar yanda take Mata a kullum." Don d'aukar Saudat takeyi tamkar wata jaririyar goye gashi ta d'ora burin duniya a kanta.' Tura k'ofar d'akin nata da tayi taji saukar numfashi Yana tashi tare da k'arar TV alamar BF take kallo, Takai idonta akan gado a can ta hango Saudat ta ware k'afa tana Wasa da a gabanta da hannunta tanajin Dadi tare da sauke numfashi had'ida 'Yar kuwa kamar yanda taga sunayi a TV" Gaban bilkisu ya fad'i cikin zafin nama taje ta kashe tv tare da fincike jonin gaba d'aya har sai da cire Daga jikin bango, jin shurun da saudat tayai a lokacin ta lura da Ashe mommy ta shigo d'akin, tayi saurin zare hannunta Daga gabanta ta matse k'afafunta tare da runtse idonta gabanta sai fad'uwa yakeyi. Da sauri bilkisu tanufi wurin gadon Saudat ta Rungume tare da sakin kuka tana fad'in "Saudat waye ya koya maki wannan mummunan d'alibi'ar nasan ba yin kanki bane koya maki hakan akayi waye ya koya maki?" A Ina kikasamo wnn caset din?" Kuka itama Saudat ta fashe dashi tace "mommy kiyi hakuri nice nasaya da kudina, A lokacin da nake fadawa k'awayena abinda nakeji a duk lokacin da jikina ya had'u da d'a namiji, shine suka dinga yimun dariya suna fad'in sha'awa ce take damuna , ya kamata na fad'a maki Halin da nake ciki dan kuyi mun aure Ni kuma mommy Naga ko zancen aure bakyaso nayi maki kin d'auki burin karatu a kaina shiyasa na fad'a masu cewa Koda Wasa gida baza'ayimun aure yanzun ba, ana suka bani shawarar na dinga kallon wad'an Nan films din da hakan zan dinga cirewa kaina sha'awa." Mommy kiyi hkr bazan sakeba." Rungumeta mommy tayi sosai tak'ara fashewa da kuka tana fad'in "daga yau kada ki Kuma kallon irin wad'an Nan fina finan duk lokacin da kikaji hakan ta taso maki ki yawaita Shan lemon tsami snn ki waita yin azumi, kinji 'yata hak'ik'a gaskiya Kika fada Saudat har yanzun Baki Isa aure ba da sauranki duka duka nawa kike yanzun kike shekara 17, ajinki shidda a secondary school yaushe Daren yayi bare gari ya waye, Ki yawaita azumi 'yata insha Allah bazaki Karajin wnn sha'awar ta taso makiba ba." Girgiza Kai saudat tayi tare da share hawayenta tana fad'in to mommy ki yafemun bazan sake ba, gyara Mata kwanciya tayi kamar yanda ta saba tare da rage Mata sanyin Ac snn tayi Mata sai da safe taja Mata k'ofa, Snn tanufi d'akinta da tunani fal a ranta tabbas Saudat tana buk'atar aure domin tana da matsananciyar sha'awa Mai k'arfi, to Amma nawa take waye zata aura, har yanzun Banga mijin auren Saudat ya bayyana ba, Har yanzun da sauran lokaci, kafin bayyanarsa ta kammala dgree d'inta sai mu koma gida Nigeria gaba Daya ayi shagalin aurenta a can." Washe gari bilkisu ta aika aka Kira mata Sauban, Tabashi umurnin duk wani namiji da yaga Saudat tana mu'alama dashi a matsayin aboki tabada umurnin Akan Sauban yaja Masa kunne akan kada ya sake kulata ta Raba abotar har abada." Sauban ya amsa ta to, Yana Mai mamakin bilkisu yau ta kirashi da kanta domin ya tsawata Mata 'yarta mafi soyuwa a ranta, Hakan akayi duk wani Wanda Saudat take mu'alama dashi a makaranta Sauban ya dakatar dashi tare da yimasa gargad'i, daga ciki har da wani malaminsu Wanda yaga sun shaku da Saudat sosai." Duk abin Nan da akeyi Saudat Bata da labari, sai dai taga kowa ya canza Mata fuska a makarantar musamman friends DINTA maza wad'anda take Dan rage zafi a wurinsu ta hanyar tattab'ata da sukeyi, har yakai da zarar taje kusa dasu ta zauna kowa zai watse yayi tafiyarsa ya barta a wurin." Tashiga damuwa sosai gashi daf suke da Fara jarabawar fita makarantar wato ssce, tashiga damuwar sosai ga sha'awar da take fama da ita, idan Tasha lemun tsami a banza takeji baya Mata wani aikin komai, hakan idan ta d'auki azumin da zarar tasha ruwa takejin mararta ta kulle sha'awa ta taso Mata." Wata Rana bayan ta dawo daga makaranta gaba d'ayansu suka HALLARA a kan dining harda Sauban domin suci abinci abinda ya dad'e baiyi ba kenan cin abinci a tare dasu, Cin abincin sukeyi hankalinta Na Kan Sauban tana Kare Masa kallon sama da k'asa taga ya murjewa ya k'ara Mata kyau faffad'an k'irjinsa ya bayyana Wanda k'aramar rigace a jikinsa ya bud'e boter biyu Wanda Yake a saman k'irjinsa domin ya Sha iska gashin k'irjinsa duk ya bayyana, tare da zararan 'Yan tsunsa hannunsa wad'anda Yake sakawa a plate Yana d'ebo abinci Yana kaiwa a bakinsa, Had'iyar biyau tashigayi tana kallon wandonsa anan take idonta yayi ja taji wani irin sha'awarsa tare da matsananciyar kaunarsa sun durar Mata a lokaci Daya, sai had'iyar miyau takeyi kamar wata mayya Saurin mik'ewa tsaye tayi sai a lokacin mommy ta kalleta tana fad'in ya dai Saudat ba dai har kin koshiba." Daga Kai tayi alamar eh domin ko magana Bata iyayi, Cikin muryarta Mai cike da kasala tace mommy zantafi gidansu calfana na karb'o littafina Wanda na Manta dashi a hannunta gashi gobe zamu Fara jarabawa karatu nakeso nayi." Girgiza Kai tayi tace sai kindawo Amma kisaka direba ya kaiki kitafi da fadawa guda biyu saboda tsaro gashi Kuma dare ne." To tace snn tafita Wanda Sauban yanajinsu baiyi magana ba, sabida baya da abin cewa, Yana gama cin abincinsa ya mik'e tsaye yanufi d'akinsa domin yayi karatu sabida suna da test a gobe, a ransa kuma Yana jinjinawa rashin tarbiya irin wacce Saudat take samu daga mahaifiyarta, duk a ganinta gatane take Mata da nuna so." A daddafe suka Isa gidansu calfana, wato azahiri ba littafi tazo ta karb'aba zuwa tayi ta amshi kaset Wanda zata kalla ya rage Mata sha'awar da take damunta." Kai tsaye tashiga gidan Bata tare da tayi sallama ba kasancewa mahaifan calfana ba musulmai bane, hakan take shiga gidan batare da sallama ba sai dai idan taci karo dasu a falo ta DUKA ta gaidasu cike da girmamawa snn ta wuce d'akin calfana, Wnn zuwan Kuma ba kowa a falon da alama kowa yana d'akinsa, Dan hakan Kai tsaye ta nufi d'akin calfana ta tura k'ofa tashiga." Turus tayi taja ta tsaya ganin calfana kwance tsirara tare da k'awayenta su biyu kowannensu ba Kaya ajikinsa suna tab'awa junana jiki suna sauke kuwar Jin dad'i." Anan take idonta ya rufe dama a bukace take, batare da tayi masu magana ba itama tashiga cire Dan guntun seket dinta tare da rigarta tayi jifa dasu gefe D'aya ta fad'a Kan gadon, ai Kuwa gaba Daya suka dawo kanta sabida komai nata a tsaitsaye Yake tacika fam domin Saudat akwai cikar halitta, gata sabon hannun domin Bata tab'a aikata lesbian ba sai a yau" A Nan suka shiga aika Mata da sakon ninsu ko wacce da inda take tabawa a jikinta Saudat Kuma sai nishin dad'i takeyi Domin tashiga duniyar da Bata tab'a tinanin da akwaitaba." Sai da ta gamsu sosai ta zubar da duk abinda ya tarar Mata a Mara snn ta tashi tana murmushin Jin dad'i tare da Sanya kayanta tana kallon calfana tana fad'in "Amma ke muguwace wlh dama kinsan akwai wata hanya ta rage zafi Amma Baki taba fadamun ba Kika barni ina kallace kallace Ina wahalar da kaina a banza, dariya kawai calfana take mata snn Saudat ta d'auki wani littafi cikin littafan calfana tafita dashi domin tanunawa mommy shi ta karb'o" Tin daga lokacin Saudat ta Fara mu'amala da Mata gaba Daya namiji ya daina Bata sha'awa idan aka cire Sauban, domin shi na daban ne a rayuwarta, Macce d'aya Bata biyawa Saudat bukatar ta sai ta had'a macce hud'u ko uku ko wacce da inda take tabawa a jikinta, Hakan zata shigo da mata cikin gida suyi shige dakin tare da rufo k'ofa suyita aikata masha'a hankalin mommy bai taba hankaltar da abinda Saudat take aikatawa ba, sai ma murna takeyi tana Jin dad'i ganin gaba Daya yanzun Saudat Bata da aboki namiji sai macce ko yaushe da akwai kalar matan da take Shigowa dasu a gidan." Akwana a tashi ba wuya inda Sauban ya kammala karatunsa na cikin nasara har ya juna dgree d'insa shima safwan ya kammala nashi shirye shiryen komawa gida yakeyi." Saudat Kuma tafara zuwa jami'a makarantar su Sauban a mataki na farko, Zuwanta jami'a idonta ya Kuma bud'ewa da mata har ya Kai idan ta kalli macce tasan Mai dad'i tasan wacce baxayi Dadi ba, Dan hakan sai ta zaba, saboda tana amfani.da kud'in hannun ta wurin saye zuciyar turawa mata." Wani b'angare Kuma tana yawan sanyawa Sauban Ido Akan matan da suke bibiyarsa, Dan da zarar taga macce tana biyarsa da sunan tana sonsa har gidansu yarinyar zata saka fadawa su kaita taja Mata kunne a kan Sauban, idan ba hakan duk abinda ya faru aka. Yarinya tayi kuka da kanta, domin tanayiwa Sauban wani irin so Wanda Bata tab'a hada kowa dashi ba zata iya aikata komai Akan Sauban Wanda bai masan tanayiba." Wata yarinya d'aya ce wacce takeso tayi Mata taurin Kai akan kula Sauban da takeyi, Wanda taga alamar shima Sauban din yakan sakar Mata fuska Yana Mata murmushin Nan nashi Mai tsada wanda ba kowa yake yiwa irinsa ba, Sunan yarinyar Fatima Bintu ba hausa ce Yar NIGERIA Yar asalin garin Kano, Sauban Yana kula Bintu ne saboda tana da sunan mahaifiyarsa a duk inda yaji sunan fateema ko Bintu Yana tsananin daraja sunan da Mai sunan yakanji kewar mahaifiyarsa ta dirar Masa." Shigowar Saudat kenan a makarantar taci karo da Sauban tare da Bintu a k'ofar motar Sauban Yana k'ok'arin shiga Bintu ta tsayar dashi suna gaisawa Yana amsa Mata tare da sakin murmushi a fuskarsa, Ai Kuwa Saudat tayo Kan bintu ta kwad'a Mata Mari a fuska Hakan shima Sauban baiyi wata wata ya kwad'awa Saudat Mari a fuska, Yana nunata da hannu Yana fad'in bakya da hankali ne? Me tamaki kinsa ko ita wacce kinsan darajarta a wurina?." Ai Kuwa Saudat najin furucin Sauban Akan bintu ta kuma haukacewa idonta ya rufe da matsanancin kishi tayi cikin Bintu tashiga kokawa da ita tana dukanta har sai da tayi nasarar yaga Mata Riga, Sosai ran Sauban ya baci ya hau dukan Saudat tare da rik'o hannunta ya jefata a mota ya rufe, ya cire rigar sa ta sama ya jefawa Bintu alamar ta rufe jikinta yashiga mota yanufi gida da Saudat wacce sai kuka takeyi tana magagganu tana "fad'in na rantse da Allah duk wancce tace zata rab'eka sainaga bayanta, ba Wacce ita, Babu wata macce wacce ta Isa tayi soyayya da Kai, hakan babu wata macce wacce ka Isa kaso a k'asar Nan. Juyawa yayi cike da Jin haushin furucinta ya Kuma sanya hannu ya kwad'a Mata wani Marin tare da muge Mata Baki, Ai Kuwa ta Kuma fashewa da Kuka tashiga irin haukar Nan ta turawa idan suna cikin b'acin Rai hankalinsu fita yakeyi daga jikinsu." Tuk'insa kawai yakeyi Yana kallonta Yana jijjina magagganun ta to me take nufi da fad'in hakan?" Kaddai ace son shi takeyi?" Yayi saurin barin maganar Yana fad'in Kai Allah ya tsare ko Mata sun Kare a duniya ba abinda zanyi da wnn marar tarbiyar." Suna hakan har suka Isa gida, a kofar gida suka tarar da motoci birjek da alamar daddyn Bauchi NE yazo wato mahaifin Saudat, Saudat naganin hakan tayi saurin bud'e mota tafito da gudu ta shiga gida tana Kuka." [8/1, 7:05 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 14* Sauban na ganin hakan yasan kwanan zan can domin duk abinda Saudat zata fad'a shine gaskiya, Wanda zai fad'a k'arya ne, musamman yanzun da daddy yazo komai zai iya furta Masa a kan hukuncin da ya Mata saboda shima bak'aramun so yake mata ba." Fasa shiga gidan yayi ya juya da motarsa yanufi masaukina safwan ransa a b'ace zuciyarsa tana Kuna, Safwan Yana ganinsa cikin wann yanayin ya rikasa ya zaunar dashi akan gado ya d'auko ruwa masu sanyi ya tsiyaya Masa a cup ya Mika masa, a take Sauban ya shanye tare da ajiye cup d'in sannu a hankali ya zame jikinsa ya kwanta Akan gado cikin minti biyar bacci yayi awon gaba dashi." Ido kawai safwan yabishi dashi Yana kallonsa cike da tausayi domin rayuwar Sauban tana matuk'ar bashi tausayi, yasan ko yanzun akwai abinda Yake faruwa Wanda ko ya tambayeshi bazai fad'a Masa ba." Da gudu tashiga cikin gidan Kai tsaye a kan jikin mahaifinta ta fad'a ta fashe da wani sabon kuka Mai sauti Wanda ya rikita duka mahaifan nata suka shiga tambyarta a lokaci Daya "Saudat lafiya me Yake damunki? Dago Kai tayi ta kalli mahaifin nata tace "Daddy Sauban ne, Daddy inason Sauban ka auramun shi." Duk wata damuwata itace Sauban daddy idan kunason ganin farin ciki na ka aura mun Sauban, ko baya Sona Ni Ina sonshi idan mukayi aure zan Sanya dole ya Soni." Wani murmushin farin ciki daddy yayi domin ya dad'e Yana shirya wnn auren had'in lokaci kawai yake jira, sai gashi saudat tazo Masa da wnn zan can Kuma abin dubawa da bakinta take furta ayi Mata aure, tabbas yimata auren shine mafita, domin da zarar yarka macce ta nuna tans son aure to mafita d'ayace ka hanzarta yi Mata shi tin kafin ta lalace maka sabida bakasan yanayi k'arfin halittar da Allah ya Mata ba, _hmmn Ni kuwa nace daddy ai tini Saudat ta lalace ta Zama kufai_🙊 Daddy yasanya hannu yashiga share Mata hawaye yana fad'in daina kuka indai Akan Sauban dama shine mijinki bakida wani miji bayansa tinda kinason aure ya Zama Dole muyi maki shi, illaso daga baya saikici gaba da karatunki a gidan mijinki." "Bazai yuwoba inji Sarauniya Bilkisu Saudat nawa take da za'ayi Mata aure yanzun snn a rasa Wanda za'a aura Mata sai Sauban Wanda rayuwarsa take cikin hatsari mutuwa ko rayuwa Wato itama laifinsa ya shafeta idan aka kaita masarautarsu a had'a har ita kashe kenan." Harara sarki Abdulrahaman ya wurgawa bilkisu wacce take nuni da Baki Isa ki canza maganar da nafad'a ba, Ya Mike tsaye cike da mulki yace "idan kin Isa idan akazo daurin auren Saudat da Sauban ki dakatar damu kada mu daura ya Riga hannun Saudat suka nufi d'akinsa inda yake sauka Ida yazo." Anan suka shiga shirye shirye yanda bikin zai kasance dashi da Sauban wacce sai dariya takeyi tana murna." Anan daddy ya d'aga waya yakira Aminin nasa sarki Abdullah ya fad'a nasa kudurinsa Akan Saudat da Sauban, Sosai sarki Abdullah yayi farin ciki da murna, domin shima Yana da kudirin wnn had'in domin zumuntarsu ta k'ara k'arfi." Satin daddy Daya a England bai Sanya sauban a idonsa ba, Wanda Sauban ya d'auki Alkawarin yabar gidansu Saudat kenan har Abada bazai Kuma Zama a cikinsaba, Hotel ya kama sannu a hankali duk ya kwashe kayansa a gidan ya mayar hotel a kusa da d'akin safwan yaci gaba da karatunsa" Da zarar daddy yakira wayarsa a kullum cemasa yakeyi Yana makaranta jarabawa sukeyi shiyasa har yanzun basu samu ganin junaba." Hakan sarki Abdulrahaman da sarki Abdullah suka yanke ranar auren Sauban da Saudat wata shidda masu zuwa, Murna da farin ciki kamar ya kashe Saudat inda bilkisu takejin wani bakin ciki a cikin ranta Akan auren." Duk abin Nan da akeyi Sauban bai San abinda yake faruwa ba, Hankalin sa a kwance, domin barin gidan yayi yafi samun Kwanciyar hankali Akan Yana cikinsa, A d'akin Safwan Yake akwance safwan Yana shirya kayansa a kwati domin gobe zai koma gida Nigeria gaba Daya sakamakon ya kammala karatunsa, Inda Sauban yake kwance rufe da Ido domin yasan sai yayi kewar abokin nasa, Yana hakan wayarsa ta d'auki ringing dibawar da zaiyi yaga Abbansa NE." Dagawa yayi cike da biyayya,.ya gaida Abba ya amsa Masa, Anan yake bashi umurni akan ya had'o kayansa Yabiyo safwan yadawo gida tinda sun Sami hutu idan hutu ya K'are sai ya koma makaranta akwai maganar da yakeso yayi dashi wacce batayi a waya sai gashi gashi, snn ko banza k'asarsa Nigeria tana kewarsa tare da a halinsa." Sosai sauban yaji dadin umurnin da Abba ya bashi Wanda dama irin wnn lokacin yake jira Wanda za'a bashi umurnin yadawo k'asarsa ta haihu." Tare da Safwan suka shiga had'a kayansa, washe gari sukabi jirgin karfe goma suka nufi Nigeria." Dan Zaman da daddy yayi na sati daya a England abinda bai tab'a yiba iyakacinsa yayi kwana Daya zuwa biyu ya kwana, A Nan yaga yanda Saudat take gudanarwa da rayuwarta wurin yanayin shigarta da yanda gaba Daya rayuwarta ta turai ce take gudanar wa, Anan take hankalinsa ya tashi yayi tir da irin wnn rayuwar,. Kamarsa sarki, Mai mulkin kasar hausa k'asar Addinin musulci k'asar da musulmai sunfi kafirai yawa ace yarsa ta cikinsa wacce yafiso Akan komai take wnn shigar wacce da ita da tsirara batada wani maraba, Wacce ya kamata a ce tana sanye da sitirarta da Alk'yabbarta ta lullub'e jikinta tana zuba mulki Amma ace itace take bayyanar da suffarta a gaban kafurai makiya ma'aiki ransa ya baci matuk'a, Anan take yabada umurni su shirya gobe gobe zasu sabar k'asar Nan gaba dayansu Kuma su sani daga har Abada bazasu Kara zuwa turai su zauna ba sai dai su shigota su fita." Murna Saudat tayita domin itama tana son taje NIGERIA Wanda Sarauniya Bilkisu ta k'ara cika tare da Jin haushi" Washe gari suka had a kayansu gaba daya tare da fadawa sukabar k'asar zuwa Nigeria." *************** Biki aka shirya na musamman Dan tarbar Sauban, Wanda ya shekararsa goma Sha biyar kenan rabonsa da k'asarsa, Sosai Hajjah take murna da jin dadi, hakan fulani Jamila itama ba laifi tanuna farin cikinta tare da matan sarki." Shigowar Sauban a cikin gidan komai dawo Masa sabo tin daga lokacin da yafito sashen Jamila a lokacin da tabashi abin Wanda sanadin cin abinci bai Kuma sanin inda kansa yakeba sai dai ya farka ya gansa a turai har zuwa gwagwarmayar rayuwar da yasha a cikin gidan, Yar kwallah ta ziraro Masa Ido yayi saurin Sanya hannu ya dauketa a lokaci da yayi Ido da Hajjah tana sakar Masa murmushi farin cikin ganinsa, da sauri yaje ya rungumeta Yana Mai cike da farin ciki hakan ya itama Anna tana farin cikin ganinsa." Anan aka gabatar da komai, Masu farin cikin nayi masu bakin ciki Suma sunayi na ganin ci gaban da Sauban ya samu ya girma huta ya zauna a jikinsa kamaninsa da mahaifinsa da mahaifiyarsa sun bayyana a tare dashi, Ina Sadeeq yakejin want sabon bakin cikinsa Sageer Kuma sai murna yakeyi da dawowar Dan uwansa, Hakan hajaru da Bintu kannensa wad'anda bai tab'a ganiba sai a waya suma suna farin cikin ganinsa." BaYan komai ya lafa, sarki yakirashi ya zaunar dashi Yafad'a Masa dalilin Kiran nasa da yayi So yakeyi yayi aure snn ya zab'ar Masa matar auren wacce yasan zai farin ciki da sanin ko wacece wato saudat." Gaban Sauban ya fad'i cike da firgici ya kalli mahaifin nasa, Amma Dan gudun kada ya fahimci wani abin yayi saurin dakewa tare da sunkuyar da Kai baiyi maganaba, domin baya fatan Allah ya kawo lokacin da zaiyi musu da mahaifin nasa." Sosai ya amshi auren Saudat hannu biyu batare da yanuna alamar baya sontaba yasan hakan rayuwarsa zataci gaba da tafiya ba wani farin ciki a cikinta." Anan take maganar auren Sauban ta karad'e gidan sarautar cewar yarima Sauban zaiyi aure zai auri Saudat Yar sarkin Bauchi Amini ga sarki Abdullah." Ina wuta Jamila ta fad'a wato yarinya da ta kwallafawa Rai Akan Sadeeq ko Sageer dayansu ya aura sabida sarautar masarautarsu gata ita kad'aice a wurin mahaifinta shine aka Bawa Sauban ita, Ta dafe Kai Wai meyasa duk abinda ta Sanya a gaba sai Sauban yayi Mata katanga dashi, wato ta kashe Bintu Ashe Bintu Bata mutuba kenan tabar baya da k'ura." Gata Bata isa ta tunkari gimbiya bilkisu akan maganar afasa auren ba domin tsakaninsu Kar ta San Karne domin duk abinda take tak'ama dashi gimbiya bilkisu ta shafeta." Hajjah tayi farin cikin wnn had'in auren domin tasan sarki Abdulrahaman Aminin Abdullah sannan Yana da karamci a idonta kodan taimakon da yayi masu a lokacin da lular ciwo tasame Sauban, Zaman Saudat a cikin masarauta Tasha wahala sosai kafin tasaba da saka manyan Kaya tare da Alk'yabba, sai da tasaba snn aka shiga koya Mata yanda zata gudanar da mulkinta a matsayin da Gimbiya Yar sarki, Anan take Saudat Taji girman Kai ya shigeta tare da jinin mulki dake yawo a jikinta, cikin wata biyu ta Fara taka duk Wanda takeso ta Kuma wulak'anta duk Wanda taga dama dama hakan sarautar masatautarsu take, A b'angarenta har kujera gareta wacce take Zama ta sarauta wacce take zuba sarautarta Akai tare da mulkinta a yanda take so sai yanzun takejin kanta duk a can baya ba rayuwa takeyiba sai yanzun take rayuwa, b'angaren Mata Kuma ba Wai dainawa tayiba, sai ta kalli cikakkiyae kuyanga wacce taji komai da komai tasaka a gyara Mata su akai Mata d'akinta domin biyan buk'atarta." Komawar safwan gida ya shima ya tarar da mahaifinsa yasaka Ranar Aurensa wata uku masu zuwa, Inda ya had'ashi da Yar k'anwar mahaifin nasa Mai suna SAFINA, wacce dama itace zabin safwan, Wato Sai anyi bikin safwan kenan snn ayi na Sauban." Bayan bikin safwan inda an Sha shagalin biki na Dan gata komai anyi na k'awatar, Tare da Sauban aka raki safwan gidan sa wurin Amaryarsa Wanda Sauban baiso zuwa sai da yaga b'acin ran safwan snn ya yarda akatafi kaishi dashi." Washe gari tin da safe sauban yakira safwan a waya lokacin Yana tare da Amaryarsa rungume a jikinsa Yana shaye Mata Albarkatun kirjinta, Kiran Sauban ya shigo wayar sa da kyar ya Mika hannu ya d'auka, a kasalance yak'ara wayar a kunnensa." Mere baki sauban yayi daji yanda safwan yake amsa Masa maganarsa, Karon farko safwan yace "lafiya kuwa Sauban Kira hakan tin da safe ko kamanta ba'a England mukeba snn yanzun fa ni inada iyali ya Ina cikin wata duniya zaka dawo Dani cikin duniyarku fadamun me'akayi." Dogon tsaki yaja Sauban baiyi maganaba illah ya kashe wayar gaba d'aya Yana tinanin dama akwai duniyar da mutum zai shiga BaYan wacce yake cikinta." D'an iska kawai ai kasamu abinda kakeso saikafi Mai kura shafawa yacewa safwan sai kace Yana jikinsa😂 Safwan shine baizo wurin sauban ba sai misalin k'arfe hudu na yamma Wanda yasaba da zarar safiya ta waye suna tare bacci ne kawai yake rabasu Amma tinda jiya ya kwana da matarsa sai yanzun yasamu damar fitowa daga gida." Kallonsa kawai Sauban yakeyi cike da mamankinsa yanda yakejin safwan Yana Masa iskanci Yana fad'in "Haba malam Ni wlh na matso wata uku Nan yazo a Kai maka matarka Saudat a gidanka kaji yanda naji a dare jiya na rantse maka da Allah saura kad'an na shed'e Akan dad'i, Wai kasan duniyar da nashiga kuwa?" Hmmm Sauban yace yaci gaba da kallon safwan, zakasha mamaki idan naci gaba da fad'a maka yanda Daren jiya ya kasance mun Ni kam daga yau nagane hanya." Lumshe Ido Sauban yayi kamar Mai yin bacci Yana saurarensa, Dariya safwan yasaki yace zaka daina wnn Jin Kan naka idan kashiga hannun macce dan lokacin da zaka durkusa a gabanta bazaka saniba." Da sauri Sauban ya bud'e idonsa yana Masa kallon bakada hankali, cikin muryarsa tare da maganarsa D'aya Bayan D'aya yace "Ni zan durk'usa a gaban macce?" Ya mere Baki yace Allah ya kyauta, har yanzun ba'a hallici wnn maccen da zan durk'usa a gabantaba, har Abada bayan Hajjah babu wata macce a duniya wacce ta Isa na durk'usa a gabanta." Safwan zaiyi magana Sauban yayi saurin daga Masa hannu yana fad'in "ya Isa safwan maganar ta Isa hakan, Kai da kaji kana iyawa kaje kayi duk abinda zakayi jarabbe kawai meye a jikin macce wacce har kake zaucewa hakan dare Daya duk ka susuci kafita a tunaninka, bazanyi mamakiba domin ka dad'e kana da buk'atar hakan Dole kafi Mai kura shafawa jarabbe kawai." Dariya safwan yayi yace "naji Ni jarabben ne, amma kasani duk jarabata ban mayar da Shan lemun tsami da ruwan Lipton abincina ba asalima ban tab'a shansu ba." Kuma bana yin azumi a Kai akai kamar yanda kakeyi." Kallonsa Sauban yayi ya hararesa wato dashi Yake kenan shida yake yawan shansu idan yaji mararsa ta Fara yimasa ciwo, mere Baki yayi yace "wnn Kuma ra'ayinane ba Dan wata manufa nakeyi ba d'an iska kawai." Dariya safwan yasaki domin yau ya kular da Sauban har yakai dayin doguwar magana hakan." ********************* Shiryen Shiryen bikin Sauban akeyi inda gaba Daya ko wanne gida suka shiga cikin hidimar biki, Sarki yasaka aka ginawa Sauban gida Mai kyau da motsi a can bangare d'aya dake cikin gidan sarautar Ginin gidan yayi kyau domin ankashe kudi wurin tsara gidan, musamman. B'agaren sauban fadin tsaruwarsa Bata lokacine." Anzubawa Saudat Kaya nafitar hankali hakan duka b'angarenta anzagaye shi da kuyangi tare da bayi, Ranar juma'a aka d'aura aurenta saudat da Sauban aka kawota masarautar Adamawa a matsayin Matar " *DAN SARKI SAUBAN* Sosai safwan Yake tsokanar Sauban akan yau zai kashe Arna yau zai Zama mutum yau zai Manta kansa da komai nasa idan ya tsunduma a cikin wata duniyar." Kyalesa kawai sauban yakeyi Dan shi kad'ai yakai ya Masa hakan ya kyalesa sab'anin sauran k'awayensa wad'anda ko fuska basa gani bare su tsokanesa." Bayan kowa ya watse Sauban yashiga b'angaren da yanzun komai nasa yadawo wurin, Babu abinda kakeji yanatashi sai kamshi turare Wanda dama yasan Saudat kwanace wurin zuba turare, mere Baki yayi yayi shigewarsa b'angarensa." Saudat Kuma dama tace da zarar anga shigowarsa a fad'a Mata domin tasan bazai tab'a iskota a d'akinta ba, suna ganin shigarsa bayinta masu gadinta wad'anda aka zuba Mata suka nufi wurinta cike da girmamawa suka fad'a Mata cewar yarima yashigo." Kuma Sanyawa tayi aka gyarata aka Kuma feshe Mata jiki da turare snn sukayi Mata rakiya zuwa b'angaren Sauban." Sai da suka kaita bakin k'ofar d'akinsa tayi masu umurni da suyi tafiyar su snn ta burd'a k'ofar d'akin tashiga, Kwance Yake Akan gadonsa Bayan yafito wanka Yana sanye da kayan bacci, yanajin Shigowarta ta hanyar k'amshin turarenta wanda yadaki hancinsa, Had'e fuska yayi tamkar bai San da akwai wata halitta a wurinba a rayuwarsa ya tsani saudat." Kai tsaye wurinsa ta nufa saiti k'afarsa taje Wanda ya turo k'asa ta Kai gurfane tare da rok'o k'afar tasa ta fashe da kuka Mai cike da so da kaunarsa tana fad'in "Sadauki kayi hakuri da kaddarar aurena kasoni kamar yanda nake sonka zanyi maka biyya tamakar baiwarka kayi hakuri ka amshe Ni a matsayin Matar aurenka , ta Kuma rushewa da kuka." Tausayinta yashigesa ya tuna da nasihar mahaifinsa a kan zamantakewar aure ya tuna da yanda Abba yayi Masa nasiha Kan ya kyautatawa rayuwar Saudat ko Dan darajar mahaifinta kada ya wulakantata, ya Kare Mata hakkinta snn ya sauke Mata duk wani nauyi dake saman kansa kada ya Bari tayi kuka Akan wani Abun da take buk'ata daga garesa, Anan ya Sanya hannu biyu ya tallabota zuwa jikinsa yashiga share mata hawaye ba tare da ya Mata magana ba, sai da yaga tayi shuru tana murmushin farin ciki." Snn ya saketa ya mik'e yashiga toilet ya d'auro Alwala yafito yayi Mata nuni da hannu Akan itama tashiga tayi, Mik'ewa tayi tashi tanufi toilet domin ai watar da abinda yace Dan idan da sabo tasaba da halin sa na Rashin yin magana sai dai kawai ya bada umurni da hannu." Bayan tayo Arwala tafito yashiga gaba ya tayar da sallah, Raka'a biyu sukayi snn ya sallame, tare da yin Addu''oe ya mik'e ya haye Kan gado ya kwanta ya barta anan zaune." Tana ganin hakan itama ta mik'e ta soma cire Alk'yabbar jikinta anan take wasu fitinannun kayan bacci suka bayya a jikinta farare fes komai nata ana gani a cikin kayan baccin." Kan gadon ta nufa ta kwanta a bayansa, tare da Sanya hannu ta lakk'amosa ta manna Masa kirjinta bayansa suka tokaresa." Lumshe Ido yayi yanajinta babu abinda Yake Masa yawo a Kai sai nasihar mahaifinsa Akan ta, Jin ya gyaleta baiyi Mata maganaba yasa ta zura hannunta tashiga shafa gashin k'irjinsa cikin wani salo, Anan take yaji tsikar jikinsa tafara tashi mararsa ta murd'a masa sannu a hankali ya Kuma gyara kwanciyarsa kamar Mai yin bacci." Ganin tana tabasa baiyi maganaba yasa tasaki murmushin mugunta taci gaba da aika Masa da sak'onni, Wata irin mik'a yayi ya janyota ya had'e ta da k'irjinsa yashiga sarrafata cikin zafin nama domin idonsa a rufe suke duk ta gama birgitashi ta tayar Masa da sha'awar shekara da shekaru wacce ya dad'e Yana juriya a kanta." Sosai Saudat Taji Dadi yanda Sauban yanke sarrafata, Yau ya Kai Mata inda ba'a tab'a Kai mataba, taji dad'in da tun da tazo duniya Bata tab'a Jin irinsaba sai Nishi take saukewa tare da Yar kuwa irin yanda taji turawa sunayi a BF. Sauban Kuma ba abinda Yakeji Dan gane da ita aikin kawai yakeyi cikin wani shauk'i da Yake dibarsa da kyar yasamu yayi relexing snn ya sauka daga kanta Yana sauke dogon tsaki tare da ajiyar zuciya sai mere Baki yakeyi" A lokacin ba Wanda ya fad'o Masa a Rai sai safwan da yaketa zuzuta Daren farko, Dan kuwa shi baiji wani abinda har ake fadin mutum zai iya Manta kowa da komai na a jikin macce☹." Mararsa yaji ta Kuma murd'a Masa sai da yasha ruwan Lipton snn ya Dan samu sansauci snn ya tashi yashiga toilet ya tsaftace jikinsa yayi wanka yafi ya d'auki fillo yajefa a kan kujera yaje yayi kwanciyarsa Yana tinani iri iri a ransa." Hakan itama Saudat tashi tayi ta gyara jikinta tafito tayi hayewarta akan gado tayi kwanciyarta domin yau burinta ya cika ta d'and'ani zumar sauban, Wanda taji wani matsanancin sonshi da kaunarsa ya kuma dirar Mata jitakeyi idan wata macce tace taza rab'eshi tabbas zata iya rabata da numfashinta." Washe gari Saudat ta shirya tare da bayinta suka rakata domin ta gaida mutanen gidan daga Nan ta zagaya gida wurin Hajjah ta Fara zuwa, Hajjah tana ganinta tayi murmshi tare da yi Mata sannu da zuwa anan Hajjah tasamu damar k'arewa Saudat kallon sama da k'asa, anan taga tsantsan mulki a tare da ita tare da tsantsar soyayyyar mijinta a cikin idanunta, Anan Hajjah taji dad'in ganin hakan ko ba komai jamila tasamu wacce zasu Kara da ita a cikin gidan nan, Hajjah ta gyara Zama tashiga karantowa Saudat duk halinda mijinta Yake ciki Akan makiya domin zagaye Yake da makiya rayuwarsa tana cikin hatsari don ana amfani da abin Sha ko abinci ana cutar dashi Dan hakan in har tana buk'atar rayuwar mijinta sai ta tashi tsaye Akan mijinta. Anan Hajjah tayi ta karantar da ita yanda zatayi tattalin mijinta Wanda tuni Saudat tasan da hakan domin yanda takejin Sauban ko baiwa ta Kama tana kallonsa sai ta fille Mata Kai Ko tayi mata hukunci mafi tsanani to bare har tabasu abinci sudafa su bashi yaci, to ita meye amfaninta." Godiya tayiwa Hajjah snn ta tashi ta shiga b'angaren duka matan sarki suka gaisa, Har b'angare fulani jamila inda tabi Saudat da kallo cike da kyashi da hassada Dan ko kayan jikin Saudat abin kallo ne bare gwala gwalan dake sanye a jikinta, A ya tsine take kallon Saudat wacce itama Saudat take Mata kallon Mai bisa ruwa." Kalmar da tafito a bakin fulani Jamila itace "ba girin girin ba tayi Mai Allah yasa ankawo budurci a gidan mijin Domin Banga farin gyalle Yana yawo a cikin gida ba kamar yanda Al'ada take." Kallon shekeke Saudat tayi Mata tace "ai Koda farin gyalle zaiyi yawo bazai tab'a Shigowa wnn bangarenba domin an kusan walkiya komai zai bayya Dan Ina sa ran shigowata cikin gidan sai na bayyak'o asirin kowa daga ciki harda masu yunkurin kashe farin cikin rayuwata, Tana kaiwa Nan tayi ficewarta." Zufa tashiga karyewa Jamila me wnn yarinyar take nufi ne?" Tana nufin tasan komai a kanta ne?" Tana cikin tunanin hakan hankalinta a tashe taji wayarta ta d'auki ringing debawar da zatayi taga sunan Sarauniya Bilkisu wato Mahaifiyar Saudat kenan, Cikin ran Jamila tashiga fadin Kiran me bilkisu takeyimun BaYan ta hanawa d'ana auren marar kunyar yarta, kafin wayar ta tsinke tayi saurin d'auka tare da karawa a kunnenta." Sautin muryar Sarauniya Bilkisu taji tana fad'in "Sarauniya Jamila matar sarki Abdullah Kuma fulanin sarki Abdullah maccen da take mulkin cikin gidan masarautar Adamawa, Kira nayi domin na fad'a maki 'yata tashigo cikin masarautarku, Kada wani abun yasami 'yata, Tsakanina dake kin sanni na sanki Kar Tasan Kar ne, Na rantse da Allah inda nashiga a cikin duniyar Nan Koda mafarki bazakiyi tinanin Zaki shiga wurin ba, nasan bakya buk'atar k'arin bayani Dan gane da koni wacce ce, Dan hakan a kiyaye aso abinda 'yata takeso koda mafarki kada ayi yunkurin cutar mun da ita Dan bazan tab'a yafewa Wanda yayi yunkurin yin hakan ba." D'if taji ankashe wayar." Mik'ewa tsaye tayi tana safa da Marwan me Sarauniya Bilkisu take nufi ne?" Tabbas tasan bilkisu hatsa bibiyace, da duk wani abinda take tak'ama bilkisu ta shafeta, idan tana karama da mulkin miji bilkisu har gobe ita kadai ce a wurin mijinta. Bata da kishiya idan tana tak'ama da mulkin cikin gidan kujerar Saudat ta mulki ta cunawa kujerar ta, Idan tana tak'ama da bokaye bilkisu tsafi takeyi tabawa bunki jini ya Sha." Tayi saurin kaiwa zaune ta d'ora hannu a hab'a🤔 tana tunanin Allah yasa ba'ajalinta bace Saudat aka kawo a cikin gidan nan" Tin daga lokacin Jamila Koda Wasa Bata kallon Saudat da sunan jefa Mata habaici ko wata magana, inda Saudat take batabi ta wurin ta wuce snn mulki a cikin gida tanayi Saudat nayi ba Wanda ya Isa ya takura wani, Dan mulkin Saudat yafi karkata Akan mijinta saboda tana son mijinta tana Kare Masa lafiyar sa, duk abinda tasan Sauban Yana buk'ata da kanta take Masa hatta abincinsa da kanta take girka Masa kofin ruwansa ba wata kuyanga ko baiwar da ta Isa ta Sanya hannu ta tabashi idan Bata hukuntataba, Hakan da zarar Sauban yafito daga b'angarensa bayi da kuyangi suke sunkuyar da Kai k'asa suna Mai gaisuwa a garesa har sai lokacin da yawuce snn suke daga kansu, Domin duk wacce tasake ta kallesa bare ta kalle kayan da yasaka hukuncinta na daban ne." _Saudat kina wuta_🤙 Sosai hankalin hajjah ya kwanta tare da maimartaba domin Sauban Yana samun kulawa a wurin matarsa." Wanda sauban duk abinda takeyi baya gaban sa domin kallon marar tarbiya Yake Mata wacce take azabtar da bayinta hakan Yana tsananin K'ona Masa Rai Wanda shi mutum ne Wanda yasan darajar Dan Adam." Aurensu da wata uku ya shirya ya koma England domin ci gaba da karatunsa, Yabar Saudat a Nan wacce Bata damu da tafiyar tasa ba saboda akwai Mata a kusa da ita wad'an sai ta darje domin biyan buk'atar ta." Komawarsa makaranta asirin wasu daga cikin fadawan masatautarsu ya Toni inda sukaje makaratar su Sauban suka kaiwa shugaban makarantar kud'i har miliyan goma Akan duk Sauban yayi jarabawa ya dinga zubar dashi." Shugaban makarantar baiyi k'asa da gwaiba wurin Kiran jami'an tsaro aka catke Masa su, dama sunyi magana da sarki Abdullah da zarar irin hakan ta faru ya d'aga waya yakirashi zaizo yaga wad'anda sukeyiwa Sauban wnn zalincin, na mayar dashi baya a karantunsa." Washe gari sarki Abdullah ya duro k'asar inda aka kaishi wurin mutanen abin mamaki fadawansa yagani wad'anda yayi matuk'ar yarda dasu, Abin ya d'aure Masa Kai tare da Sanya shi cikin rud'ari, hakan ya bada umurni ayi ta dukansu har sai sunfadi Wanda yasakasu, Duka akayi masu sosai Amma basu fad'aba daga k'arshe da kansu suka Sha guba suka mutu domin dama aikin sai da rai suka fito mutuwa ko rayuwa." Sarki yayi bakin cikin mutuwar tasu hakan yasaka aka rufeso yabaro k'asar tare da yiwa shugaban makaranta godiya, Tin daga lokacin sauban yasamu dama da Kwanciyar hankalin yin karatunsa har yasamu nasarar kammalawa shekara D'aya da ta rage Masa yadawo gida Nigeria Cike da murna da farin ciki." kamar yanda kuka gani a cikin page 1 yanda ake murnar dawowar tasa." _Mu Koma Kan labarinmu na baya muka had'e a page 15_ _idan ba comment yasin sai kunyi sati daya ba posting_🤒 *Mrs Ana's Bawa*✍ [8/2, 7:31 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 15* _hmmmm mutum mutum sai Allah🤔 Ina kallonku masu Kan kwakwa aci gaba da zuwa Rafi wata Rana tulu zai fashe 'yan bu........._🙊 _Cigaban labari_ Da kyar ya samu asuba tayi sai sak'awa yakeyi Yana kwancewa Akan Saudat, Gaba D'aya zuciyarsa a dagule take, Wanda yarasa dalilin hakan, Hakan jiki ba kwari ya fad'a toilet yayi wanka tare da d'auro Alwala yafito yanufi masallaci domin gudanar da sallar asuba." Sahu D'aya suka jera da maimartaba mahaifinsa, Bayan sun kammala yin sallar ne suka fito a tare suka jera suna , Tafiya suna Hira cike da burgewa suka nufi b'angaren sarki, sarki Yana tsananin son d'ansa Sauban saboda hankalinsa da tunaninsa ga ibada Wanda duk iya Zaman da yayi a turai bai Sanya ya zubar da Addininsa da Al'adarsa ba, Yana jijjina tarbiyar Sauban tare da yaba Masa duk da baiyi rayuwa a cikin masarauta ba Amma yafi sauran yaransa Sadeeq da Sageer tarbiya da son Addini, wad'anda kafin ka gansu sunfito sallar asuba a masallaci ma wuyacin Abu ne, Wani lokacin har sai ya shiga da kansa b'angaren nasu ya tayar dasu Daga bacci suna kunkuni suna komai snn suke fitowa massalaci ayi sallar dasu, Sab'anin Sauban Wanda in har Yana garin Nan sahu. Daya suke Zama dashi ko wacce sallah wani lokacin har shi yake tayar dashi idan yarigashi fitowa, hakan ba k'aramun Burgesa yakeyi ba tare da sanyashi farin ciki, yasan ko yanzun ya fad'i ya mutu ya bar magajinsa Wanda zai rik'e Al'umma da gaskiya da Amana ga Kuma Addinin." Tafiya sukeyi a jere sai da Sauban ya Kai sarki har cikin d'akinsa ya zaunar dashi a kan kujera snn ya D'uk'a a gabansa cikin girmamawa yana fad'in "ABBA barka da asuba Ina kwana." Murmushi sarki yasaki Yana kallon d'an NASA mafi soyuwa a ransa, yace "barka Kade magajin sarki, katashi lafiya ya kwanan iyali?" Sunkuyar da Kai Sauban yayi cike da jin kunya yace "lafiya k'alau Abba." Cikin zolaya Abba Yake kallonsa yace "Alhamdulillah tinda ka kammala karatunka lafiya hankalina ya kwanta muna fatan result Dinka shima zaiyi kyau, kamar ynda muke hasashe Yanxun Abu D'aya nakeso a wurinka shine kabani jika, Inaso Naga zuri'arka a doron k'asa tin kafin mutuwa ta daukeni, Wanda nasan burin Hajjah Kenan itama taga d'an jikanta mafi soyuwa a ranta." Sunkuyar da Kai Sauban yayi cike da jin kunyar maganar Abba, Abba yasaki dariya ganin Sauban yanajin kunyar maganarsa yace "Ina ganin wata k'ila d'ana Sauban baya da wani kuzari a wurin iyali, tabbas sai na gana da jakadiya domin naji tabbas kuwa tana baka dauri kana Sha." 'yar dariya sauban yasaki ya sunkuyar da Kai cike da jin kunya, A zuciyarsa Yana fad'in dama ruwan zafin da Anna take kawo Masa masu kamar wani ganyen magani ta tsareshi a gaban idonta tace Dole sai ya shanyesu a she akwai wata manufa a cikinsu, Dan hakan yakeji da zarar ya shanye ciwon Mara Yake sanyoshi a gaba har sai ya Kai da Shan ruwan Lipton da lemon tsami snn yakejin saukin jikinsa." Sarki ya katseshi da fad'in "Allah yayi maka Albarka Sauban tashi katafi wurin iyalinka." Har zai Mike ya kuma komawa ya zauna ya d'an runsuna yace "Abba yau ne nakeso zan tafi gidan gonata tare da Safwan domin mukai ziyara daga can inaso zan wuce masarautar zamfara domin mukai gaisuwa. " Murmushi sarki yayi "yace Allah ya taimaka tabbas kayi tinani Mai kyau na zuwan naka zamfara ziyara idan katafi kace Ina gaida sarki Abdulmalik." Zan fad'a Masa insha Allah inji Sauban snn yayi Abba sallama yafita." Kallo sarki yabi bayansa dashi cike da k'aunar sa tare da sauke murmushin farin ciki Yana godiya ga Allah da yabashi d'a nagari Wanda yafito a tsatson tarbiya." ******************* A d'akinsa shiri yakeyi cikin wata dakakkiyar shadda milk colour Wacce tasha aiki a jikinta ya d'auko hula yasaka itama milk colour agogonsa na gwal wanda sai kyalli yakeyi ya d'auko daga Kan madubi ya d'aura Akan tsintsiyar hannunsa, ya tsun hannunsa guda uku suke sanye da zoben azurfa da zinari Mai shegen kyan gaske sai kyalli sukeyi, talkaminsa ya saka Suma milk colour ya Kuma feshe jikinsa ta turarensa Mai dad'in k'amshi, kansa ya kalla a madubi Yana gyara Zaman hular kansa, tabbas Sauban yayi kyau iya kyau domin kuwa dama kyakkyawa ne." K'arar bud'e k'ofa yaji anshigo tare da sallama ko ba'a fad'a ba yasan Saudat ce, Amsa sallamar yayi yaci gaba da shirinsa, d'auke take da tiren break fast nashi, Itama Tasha ado cikin wani leshi Wanda ya amshi jikinta sai kamshi take zubawa dama Saudat gwanace a wurin kamshi." A jiye tire tayi a kan d'an matsakaicin dining table dake cikin d'akin, Wanda Yake Zama akai yake cin abinci wani lokacin." Tana ajewa taJuyo ta tanufeshi tana kallonsa cike da sha'awa tare da matsananciyar k'aunarsa Mai cike da sonshi da yake fisgarta, A gabansa taje ta tsaya tare da rik'o hannunsa duka biyun ta d'an sunkuyar da kanta saiti fuskarsa tana kallon cikin idanunsa, k'amshin turarensa ya daki hancinta tayi saurin lumshe ido, ta furta kayi kyau mijina Ina Alfahari da Kai." had'e fuska yayi ba alamar dariya a tare dashi." Ganin hakan ta saki hannunsa ta d'an ja baya ta had'e hannuwanta wuri D'aya tana kallonsa👏🏻 tace "Sadaukina Ina kwana?" Murmushi ya D'an saki Akan lab'b'ansa domin taso tasakashi dariya yace "lafiya k'alau kintashi lafiya?" Murmushi tayi na farin ciki, tace lafiya k'alau break fast Yana jiranka komai ya kammala." Baiyi magana ba ya dubi agogon hannunsa yaga k'arfe 10am lokacin break d'insa yayi ga lokaci Yana tafiya har yanzun safwan baizoba bai Kuma kirashiba, Kai tsaye wurin dining table din yanufa, Cikin tafiyarsa ta k'asaita, hakan tabi bayansa kowa Yanaji da mulki Yana yawo a cikin jinin jikinsa, tana ganin ya zauna akan kujera itama taje ta zauna a kan kujerar dake kallonsa, tashiga zuba Masa duk abinda tasan Yana buk'ata ruwan te sune farko." D'auka yayi ya Sha Yana lumshe ido, zuba Masa Ido tayi sai kallonsa takeyi kamar ta cinyeshi Akan so, Dan kuwa kwalliyarsa tayi Mata kyau, don ta amshi jikinsa a ranta tace "Sadaukina kayi kyau manyan kayana suna maka kyau." Ashe maganar tafito fili yanajinta Sarai yayi kamar baiji abinda taceba, don fahimci Saudat irin matan Nan ne Masu yawan naci Akan abuda suke so, snn ya lura duk mulkinta duk k'asaitarsa duk wulak'anta mutanen da takeyi tana D'an Jin shakkarsa, snn macce ce jarabarbiya Mai yawan son a Koda yaushe a kusanceta tafison Koda yaushe namiji Yana kanta, Wanda shi a wurinsa wahalar da gab'ob'en jikinsa kawai yakeyi dan ba wani abunda Yake amfanuwa da yin hakan, Illah sai ita da yakejin tana sauke numfashi tare da kuwa kamar alamar tanajin Dadin hakan, mere Baki yayi ☹ Wanda d'ali'arsa ce,ya ya mai da idonsa Yana kallon agogon hannunsa yaga 10:30am ya ajiye cup d'in hannunsa ya mik'e tsaye tare da d'aukar wayarsa ya shiga Kiran number safwan." Ringing biyu safwan ya d'aga a dai dai lokacin da yafito wanka SAFINA tana rungume a jikinsa dukansu ba Kaya a jikinsu sai zuba Masa shagwaba takeyi zaiyi tafiya ya barta. Baisan lokacin da ya d'auki wayarba ya k'ara a kunnensa, a maimakon yayi magana hankalinsa ya tafi wurinta yaci gaba da lallashinta Yana fad'in "sorry baby bafa tafiyar kwana zamuyi ba, kekoda kwana ya riskemu bazamu wuce kwana biyu mudawoba sorry kinsan Ina tare da ke akoda yaushe zumata." saukar dogon tsaki yajiya da k'arfi a kunnensa Wanda Sauban ya sakar Masa cike da Jin haushin iskancin safwan, Safwan Kuma Gaba ya Manta da ya d'auki wayar sauban safina duk ta rikitashi." Murmushi safwan ya saki Yana fad'in yi hakuri abokina gani Nan zuwa yanzun nan, Na tsaya aikin lallashi Dan kada naje na dawo a juyamun baya nashiga uku na." Kuma Jan wani tsakin Sauban yayi baiyi magana ba ya kashe wayarsa." Kan gado yanufa ya zauna, a rayuwarsa ba abinda ya tsana kamar jira Kuma Safwan yafi kowa sanin hakan." Saudat ta matsa taje kusa dashi ta zauna har kafafunsu suna gogar na juna idonta a kansa, don idan zata shekara tana kallonsa bazata tab'a gajiyaba, Cikin muryarta ta Mai cike da k'asaita tace "Sadaukina tafiya zakayi ne?" Kallonta yayi yaga ta D'an bashi tausayi ya d'an janyota zuwa jikinsa, ai Kuwa ta lafe tana shak'ar k'amshin turarensa, cikin muryarsa Mai tsada yace "gidan gona zan tafi tare da Safwan." Iya abinda yace da ita kenan yaja bakinsa yyi shuru." Lumshe idonta tayi wata irin wutar kaunarsa takeji tana ruruwa a zuciyarta, Tashiga tinanin yanzun tafiya zaiyi da wnn kwalliyar Wacce tayi tsananin yimasa kyau jikinsa, Kafin ya Kai mota Allah kad'ai yasan bayi da kuyangi Mata wad'anda zasuyita kallonsa, Snn idan yatafi Allah kad'ai yasan adadin maccen da zata kallesa ta yaba kyansa." Wasu siraran hawayen kishin mijinta suka zubo Mata Akan fuska tayi saurin Sanya hannu ta daukesu, Tana kallonsa tana fad'in "Allah ya tsaremun Kai a duk inda ka Sanya k'afa, Allah ya makantar da 'yan Mata daga kallon kyakkyawar fuskarka, hak'ik'a Ina kishinka mijina." _hmmmm Saudat kenan_🤔 Wani murmushin gefen Baki yasaki Dan yasan kishin saudat Sarai tun a turai, mik'ewa tsaye yayi yafita sakamakon Kiran wayar safwan da yashigo wayarsa alamar ya iso." Bayansa tafi suka jera suna tafiya a tare , tin daga harabar b'angarensa bayi Mata da kuyangi suke zubewa k'asa tare da sunkuyar da Kai suna Kai gaisuwa ga yarima, daga masu hannu kawai yakeyi alamar ya amsa." Sai da ta kaishi bakin get din fita daga part dinsu snn ta d'aga Masa hannu ta juyo cike da k'aunar mijinta tare da kishinsa." A bakin motar da zasuyi tafiyar ya tarar da safwan Yana jiransa sai waya yakeyi yana dariya da alama da safina yakeyi domin ita kad'aice matsalar safwan inji sauban😄" Tsaki Sauban ya Kuma ja, yabawa fadawa umurni tare da jami'an tsaro wad'anda zasuyi tafiyar a tare umurnin da sushiga mota sutafi, a bar safwan wurin tinda bai tashi lafiyarba😄 Kasancewar duk inda zaitafi indai tafiya Mai nisace sarki yaba umunin yadinga tafiya tare da fadawa da matakan tsaro saboda tsaro da Kuma kula da lafiyarsa." Cikin sauri fadawa suka bud'e masa mota ya shiga safwan shima ya shiga aka rufe k'ofar, motoci suka Fara fita daga gidan D'aya Bayan D'aya Wacce mota zata Kai kusan guda goma a Nan take aka Fara sakin jiniya Wacce ta Karad'e gaba D'aya gidan sarautar alamar d'an sarki zai fita kenan." Safwan wayarsa kawai yakeyi da matarsa yana dariya harda su d'aga k'afa yanayi Yana kallon sauban cike da tsokana, Yana fad'in "haba Zumata nafad'a maki ki kwanatar da hankalinki, Ni dai tafiyar Nan idan bakyaso Allah yazun zan iya dawowa gida" Wani kallo Sauban ya wurga Masa Mai cike da harara Mai dauke da ma'anar baka da hankali." Can yaga safwan ya tintsire da dariya Yana fad'in ok to shikenan ki gyaramun komai naki, ki kula da kanki domin idan Kika Bari wani abin yasameki bazan tab'a yafe makiba, yasakar Mata kiss a waya tare da kashe wayar " "Mere baki sauban yayi yace" dama d'an iska a duk inda Yake zai iya nuna halinsa." Kallonsa safwan yayi Yana dariya yace "ranka ya dad'e ko gaisawa bamuyiba sai zagi ya biyo baya." Da matata fa nake waya zaka Kira da Dan iska, to idan hakan ne Kai wayasan iskancin da kayi kafin kafi cikin gidanka." Gyaleshi Sauban yayi ya janyo laptop d'insa yashiga dannawa." ***************** K'arar jiniyar da ta karad'e gaba D'aya gidan sarautar alamar " *D'AN SARKI SAUBAN* zai fita kenan Hankalin Sadeeq ya tashi matuk'a domin idan shi zai fita mota D'aya ake bashi ta fadawa wad'anda bazasu wuce guda biyar ba, wad'anda zasuyi Masa rakiya Amma Sauban harda wasu jami'an tsaro suke dafe Masa baya ana Masa jiniya" Kai tsaye wurin mahaifiyarsa yanufa fulani, Yana huci, Fulani dake kishingid'e ana Mata tausa, Tana ganin shigowar Sadeeq Ransa a b'ace tabawa baiwar umurnin tafita zata gana da yarima cikin saurin baiwar tafita." Ta kalli Sadeeq tace "yarima lafiya meya faru?" Cikin maganarsa ta rashin tarbiya yace "meyasa ake nuna Mana fifiko a cikin gidan Nan, Sauban yafimu ne ko yafi kowa ne a cikinmu idan zaifita tamkar sarki zaifita yanda akeyiwa sarki jiniya hakan ake Masa sab'anin mu da ake sakinmu a sake, ba matakan tsaro wato Ana nufin mu ba Yaya bane shine d'a." Na rantse da Allah sai Naga Bayan Sauban sai Naga Sauban baya motsi a doron k'asa, bana sonshi yanda na tsini mutuwata hakan na tsaneshi." Murmushin farin ciki fulani Jamila tayi, tajanyo hannun Sadeeq tace "zauna d'ana yanzun na tabbatar da kasha nono na, Kabar komai a hannuna Ni nasan abunda nake shiryawa, Abunda nakeso da Kai ka rage nuna tsanarsa a gaban mutane kabar abin a ranka Indai Ina motsi a doron k'asa Sauban bazai tab'a Kai labari ba." _kuyi hkr nasan kun Matsu labari Sauban ya Kare mukoma Kan labarinmu to Amma idan Kuna biye Dani sai kun fahimci tushen labari snn zaku fahimci duk abinda zaici gaba da faruwa a Nan gaba idan muka Koma Kan labarinmu,_ *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 16* Jiniya kakeji tana tashi sannu a hankali manyan motoci kirar jeb bak'ak'e suke ta gangarawa a cikin k'aramun k'auyen Lassa dake k'aramar hukumar mulkin Adamawa." gaba D'aya jiniyar ta k'arad'e dukan k'aramun k'auyen Wanda maza da Mata tare da dattijai da samari kowa sai Kama 'ya'yansa yakeyi yana shigarsu cikin gida wasu Kuma sai gudu sukeyi suma fad'in sarki ne yazo tare da 'yan sanda. _kusan fulani da tsoron Yan sanda lol_🤪 Babu abinda yafi daga masu hankali irin jami'an tsaro Yan sanda da sukaga gani tsaitsaye a Bayan mota ko wanne ya hak'a bindigarsa kamar wad'anda ke fagen yak'i fuskokinsu ba wani alamar sauki ko dariya a tare dasu." Kai tsaye babban gidan gonar suka nufa, Wanda Yake zagaye da fadawa da masu gadin wurin, cikin zafin nama aka hangame masu k'atun get din gidan gonar suka dinga shigar da motocinsu d'aya Bayan Daya." Murmushi kawai sauban yake saukewa domin tinda aka shigo k'auyen na Lassa ya tsinci kansa cikin wani farin ciki tare da Annashawa duk ya Manta wata damuwarsa domin Yana tsananin son k'auyen nan tare da gidan gonarsa" Parking motocin suka shigayi a cikin parking space, sai da suka tsaitsaya, Snn cikin sauri fadawa suka nufo motar da Sauban Yake a cikinta suka bud'e Masa, tare da zagaye motar har da jami'an tsaro suna jiran fitowarsa." Sai da ya d'auki minti biyar kafin yafito, Wanda Al'adarsa ce baya saurin fitowa a mota lokaci daya sai ya d'auki minti biyar zuwa goma saboda tsaro😎." Safwan ne yafara fitowa snn Sauban yabiyo bayansa, cike da mulki da k'asaita, Yana fito yashaki k'amshin garin yayi saurin lumshe idonsa tare da d'aga kansa sama cike da farin ciki Yaci gaba da shak'ar iskan garin Wanda Yake yawan sanyashi farin ciki da Annashawa." Gidan gonar yashiga k'arewa kallo Yana Mai murmushin Jin dad'i da farin ciki a fuskarsa." Sai da ya d'auki minti goma a hakan fadawa duka sun zagayeshi snn ya juya yafara tafiya suka rufa Masa baya zuwa cikin gidan gonar a wurin da suke sauka idan sukazo." Fad'in fad'i da girman wurin tare da tsaruwar wurin Bata lokaci ne Amma iya tsaruwa wurin ya tsaru babu abunda babu a cikinsa Dan gane da kayan fruit da duk wani Abinda ya danganci shuke shuke, A can d'aya b'angaren Kuma wani wurin hutawane Wanda aka zagayeshi da manyan kujerun k'arfe domin zama, Sai Kuma gefe D'aya da na hango wani babban dining table ne da alama shima an ajiyeshi ne domin zama asha fruit, sai Kuma wasu manyan d'akuna guda uku da na hango a jere da juna wad'anda anyisu ne domin hutawa musamman idan tafiyar kwana tasameka, babu abunda babu a cikin d'akunan na dangane da kayan buk'atar rayuwa, d'aya daga cikin d'akunan wanda Naga Anfi k'awatashi da komai a cikinsa Bintu take sauka wani lokacin suke kwana a duk lokacin da sukazo tare da maimartaba Suna hutawa." A can d'aya b'angaren dake kallon Bayan gari, wani Babban wurin wanka ne anzagayeshi da furanni Wad'anda suka k'awata wurin, cike wurin Yake da ruwa gwanin ban sha'awa." Idan Kika matsa gaba kad'an fanfuna ne tare da rijiyoyi wad'anda sarki yasaka aka Gina domin jama'ar k'auyen su dinga Shigowa ta k'ofar baya suna dibar ruwa kasancewar k'auyen suna fama da k'arancin ruwa amfani." K'auyen Lassa k'auyen ne na fulani, ko fulanin ma irin fulanin dajin Nan masu masifar kyawo wad'an suke rayuwa a cikin daji tare da shanunsu da 'yayansu da matansu." Domin duk inda ka wurga idanunka tungayen fulanine tare da bukkokinsu dake k'ank'afe a tsakiyar k'auyen sai tarin shanu da suke shawagi suna kiwo a cikin k'auyen." K'auyen Lassa basa Wasa da Al'adunsu na fulani wad'anda suka tarar anayi suka gada tin daga iyaye da kakan ni hakan Kuma suna girmama Wanda Yake d'aukar Al'adunsu da muhimmanci ." ***************** D'aya daga cikin kujeren dake jere a wurin Sauban yaje ya zauna ya d'ora k'afa d'aya Kan d'aya daga cikin kujerar Yana sauke murmushin farin ciki, domin idan bai Manta ba rabonsa da gidan gonar Nan ya shekara uku." Fadawansa tsaitsaye a kansa Suna gadinsa, inda safwan Yake can wurin Mai gadi Yana surutu saboda yasan koda yazo wurin Sauban ba wata Hira zasuyiba Kuma shi mutum ne Wanda bayason yaji anyi shuru da baki." Hannu ya d'agawa fadawa alamar kowa ya Kama gabansa suje su huta Tare da nuna masu d'aya daga cikin d'aku Nan dake jere a wurin ya furta idan Kuna buk'atar wani abin kushiga ciki zaku samu dukan abin bukata ya nunawa jami'an tsaron d'aya d'akin yace kuma idan kunada buk'atar wani abin kushiga nan akwai komai , snn yace "duk Wanda Yake buk'atar yaci duk abinda yakeso yashiga cikin gidan gona babu shamaki ya tsinka dukan abinda Yake buk'ata kowa yayi abinda ransa yakeso." Yana gama fad'in hakan ya Sanya Kai yanufi d'akin da yafi ko wanne ado da kyau yayi shigewarsa." Suna ganin ya shiga suka shiga yimasa godiya cike da farin ciki snn ko wanne ya nufi cikin gidan gonar domin tsinkar 'ya'yan itatuwa." Da shigarsa d'akin Kai tsaye wurin k'aton hoton mahaifiyarsa yanufa Wanda Yake lik'e a gaban bangon d'akin, Wanda tayishi tin tana budurwa kafin tayi aure tana sanye da Alk'yabbarta ruwan Madara tana murmushi a fuskarta tamkar kakirata ta amsa." Hannunsa yasaka yashiga shafa hoton tare da runtse idonsa Yana tsananin kewar mahaifiyarsa, sai da ya d'auki kusan minti biyar a hakan snn ya bud'e idonsa ya nufi wurin d'aya hoton Wanda sukayi a tare a lokacin Yana Dan shekara uku tare da mahaifinsa, inda Yake zaune a kan k'afarta ta Sanya hannu biyu ta rungume sa a jikinta tana kallonsa cike da k'auna, shi Kuma mahaifinsa yana kallonsu dukansu suna sakarwa juna murmushi cike da burgewa a hakan aka d'auki hoton." Rungume hoton yayi hawaye suka shiga zuba a idonsa yashiga fad'in "Allah ya jikanki umma Allah ya Kai haske a kabarinki." Hakan yabar wurin yanufi Kan lafiyayyen gadon dake d'akin ya kwanta rigingine yayi filo da hannuwansa ya dulmiya cikin duniyar tunani." Sautin hayaniya yaji a Bayan window wacce take kallon k'ofar baya da alama rikici akeyi domin yaji sautin muryar macce kamar tana magiya." Mik'ewa yayi yanufi jikin window domin ganin abinda Yake faruwa yad'an zuge labule ya rik'a k'arfen window da hannu biyu Yana hango abinda ke faruwa." Wata farar yarinya ya hango 'yar kimanin shekara goma Sha biyar, tana sanye da kayan fulani a jikinta kanta ba d'ankwali sai Yar sarkar da suke sanyawa a tsakiyar Kai anyi mata kitso Wanda ya zubo gaban fuskarta zuwa gadon bayanta, hannunta dauke da fanteka alamar ruwa takeso ta d'iba maigadi ya hanata shine take Masa magiya Akan ya barta. Sai fad'in yakeyi cikin hausarsa ta fulani marar dad'in Jin "Allah SAFNAH Bazan barki ki d'ebi ruwa a dai dai wnn lokacin da yarima D'an birni yake hutawa ba, Wato so kikeyi ki janyo mun kura daga aiki na kenan, Yanuna ta da sanda Yana fad'in "Safna kiyi tafiyar ki tin muna shaida juna" Durk'ushe takai a gabansa tana magiya idonta Yana zubar da hawaye domin tasan yau idan Bata d'ebo ruwan Nan ba kashinta ya bushi." Tashiga fad'in sale ka taimakeni kabar Ni na d'ibi ruwan Nan." " Ya kuma har zuka Yana fad'in wlh Allah bazan barki ba, Safna kiyi tafiyar kawai." Sautin muryar yarima yaji a bayansa Yana "fad'in zoki d'iba, Ya juya ya kalli sale yace "dama hakan kakeyiwa Al'umma idan suka zo dibar ruwa?" Da sauri sale ya zube gabansa Yana fad'in "ranka ya dad'e kayi hakuri ba halina bane ba hakan nake masuba, yau ne kawai ko yau din Dan naga kazo kana hutawa ne gudun kada su dameka." Shuru yayi bai tankawa sale ba, Idonsa Yana kan SAFNA wacce sai Jan ruwa takeyi a rijiya tanayi tana share hawayen fuskarta da alama tana cikin damuwa." Kyawon yarinyar da farinta yake kallo Domin Fara ce fes har Farinta ya fara sir kawa da yellow, kyakkyawa ce ajin farko sai dai k'azantar jikinta abin kyamata ce, don kuwa kayan da ke sanye a jikinta na fulani fararene da alama Amma akan daud'a har sun koma ruwan k'asa." Yana tsaye a wurin ta kammala cika fantekar ruwanta ta d'auka ta d'ora a saman Kai ta juya cikin sauri zata fita, Karaf sukayi Ido biyu da yarima Yana tsaye Yana kallonta, jikinta ya soma rawa domin duk a tunaninta yayi tafiyar sa, Hankalinta Yana kan dibar ruwa burinta tayi ta cika tanufi gida domin gudun azabar da da isko, A gabansa tazo dauke da fantekar ruwan a kanta ta durk'usa tana fad'in nagode D'an birni Allah yabaka abinda kake buk'ata." Kallonta Yake a can k'asan lab'b'ansa ya amsa da "Ameen." Wanda tuni Safna tanufi hanyar fita daga wurin cikin sauri domin ta Isa gida takai ruwan tin kafin lokacin da aka d'ibar Mata yacika. Sai da yaga tab'acewa ganinsa snn ya juya ya kalli Sale yace tashi a gabana daga yanzun duk Wanda yazo dinar ruwa kabarshi, musamman macce, Saboda macce darajar gareta ba'a wulak'anta macce." Kayi hakurin ranka ya dad'e bazan sakeba, Bai Kuma saurarensa ba ya juya yayi tafiyar sa." Juyawarsa yaci karo da Safwan ya nufo shi Yana murmushi Yana fad'in "yarima me kakeyi anan naje nemanka baka d'ak'i." Bai tankawa safwan ba sai da yayi gaba Yana tafiya snn yace naxo zagaya." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 18* "Rok'onsa taci gaba dayi, tana Kuka tana fad'in "dan Allah kayi tafiyarka, nagode da taimakonka, mutane da yawa sunyi k'ok'ari wurin su taimakeni Amma daga k'arshe basu Kai labari ba, Banason wani abin yasameka na rokeka kabar wurin nan tin kafin su kuma dawowa su tarar da Kai." Ganin duk ta firgice yasa hankalinsa ya k'ara tashin tausayinta ya yashigesa yaji Koda zai mutu bazai tab'a barinta cikin wannan Halin ba." Rik'eta yayi da hannu biyu, Domin ganin a firgice take, yashiga girgizata domin tadawo hayyacinta, cije lebonsa na k'asa yayi Yana kallon kyakkyawan fuskarta Mai cike da kwarjini, Sannu a hankali yakira sunanta cikin taushin murya "SAFNA ki natsu Mana babu abinda zai sameni, ko sunzo wurin Nan ba abinda zasuyimun." Girgiza Kai tashigayi domin tasan Halin Jarmai Sarai ga duk Wanda yagani Ya rab'eta ko Yana magana da ita." Ta kwance hannunta daga rikon da ya Mata tana kallonsa tare da ja da baya tana girgiza Kai tana fad'in kayi tafiyarka ce nagode da taimakonka, kabar ni a yanda ka ganni." Kafin ya Bata amsa a can ta hango ta wagarsu JARMAI sun nufota, hakan Yake da zarar tafito kiwo ko dibar ruwa zai dinga zagayenta, yanaso ya Kama Wanda zaigani yana Mata magana, mudun ya Kama Wanda tsotsayi ya hau kansa a ranar sai dai wuyarsa ta haifi wani domin sai ya mashi dukan mutuwa." Tana ganinsu ta Kuma firgicewa ta rud'e cikin tashin hankali, tashiga tura Sauban Bayan wani iccen bedi tana fad'in "boye a nan gasu nan zuwa, idan suka tarar da Kai dukanka zasuyi." Tura Sauban takeyi alamar ya boye, sai gani tayi yayi tsaye ko motsi ba yayi, Ganin hakan ta fashe da kuka domin tasan kwanan Sauban a yau ya K'are, Suna k'arasowa wurinta suka hango shi a gabanta, Ai Kuwa gaba d'ayansu suka daga sanduna suna fad'in wani Mai k'aranren kwana ne Yake magana dake." Suka nufi Sauban gadan gadan zasu doka Masa sanda, saurin zuwa gabansa tayi ta kareshi tana fad'in kada kucutar dashi ba magana yakemun ba Nima a Nan na tarar dashi bansan koshi wayeba." Tsaye Sauban Yake Yana kallonsu cike da mamaki da Al'ajabi, Kallonsa sukayi domin ganin ko waye, domin idonsu ya rufe basu tsaya kallon fuskar ko waye ba, Ido biyu sukayi da yarima, Cikin sauri suka zubar da sandunan hannunsu suka zube k'asa suna fad'in "ranka ya dad'e ayi hakuri tuba mukeyi bamusan kaibane." Murmushi yarima yasaki ya Sanya hannu a Aljihu ya Ciro kud'i ya basu yace "zaku iya tafiya." Cikin sauri hannuwansu yana rawa suka k'arb'i kud'in suna godiya suka wuce cike da murna da jin dadi domin yau sunsamu kud'in Shan sigari🤒 Ajiyar zuciya ta sauke had'ida goge hawayen fuskarta ta d'aga Kai ta kalli Sauban Wanda idonsa akanta Yana kallonta, Ido biyu sukayi tayi saurin janye idonta daga kallonshi, shi kuma idonsa kyar akanta Yana k'are Mata kallo." Waigawa yayi bayansa yaga wani k'aton dutsi cikin muryarsa Mai taushi yace mutafi can yanuna Mata inda Yake nufi." Bamusu tabi bayansa tafiya yakeyi cike da mulki da Isa, Ita Kuma sai Kare Masa kallo takeyi ta bayansa, tana fad'i a ranta " iya had'uwa D'an binni ya had'u gashi kyakkyawa zuciyarsa Mai tausayi." Saman dutsin ya zauna itama ta janyo wani k'aramun dutsin da ya nuna mata da hannu a alamar ta d'auko shi ta zauna, taje ta d'auko yayi Mata alamar ta zauna, A gefensa ta ajiye dutsin ta zauna tare da sunkuyar da kanta k'asa, Shanun da tafito kiwo Yake kallo yanda suke faman cin ciyawa, suna kiwonsu gwanin ban sha'awa." Juyawa yayi ya kalleta har a lokacin tana sunkuye da Kai tana Wasa da Zara zaran Yan tsun hannunta, Cikin taushin murya yakira sunanta yace "Safna tayi saurin d'ago Kai ta dubeshi domin jitayi sunan yayi matuk'ar Dadi a bakinsa." Yace "kin yarda Dani?" Kin yarda bazan cutar da keba?" Kinaso na taimakeki na fitar dake daga kuncin da yake damunki?" Daga Kai tayi "Alamar eh." Yace "ke wacece?" Waye mahaifinki?" wnn Jarmai din waye shi a wurinki?" Share hawayen da suka zubo Mata a fuska tayi tace "kamar yanda nafad'a maka sunana Safna, Ni 'yar garin Nan ce, mahaifina sunansa Jabiru ana kiransa da JAURO, tinda na tashi bansan dad'in rayuwaba, a kullum cikin kuka nake da k'unci tare da wahalar rayuwa Mai tsanani a wurin uwar rik'o na, Wacce a farko na d'auka itace mahaifiyarta sai daga baya da BABA yake fad'amun cewar ba itace mahaifiyata ba, Sabida yaga irin wahala da tsangwamar da nakesha a wurinta Yasa wata Rana ya zaunar Dani a lokacin Bata Nan tafita wurin biki, Yake fad'amun cewar nayi hakuri da duk abinda INNO zatayimun nasani cewar ba itace mahaifiyata ba, asalima Bata tab'a haihuwaba Dan hakan yasa Bata San zafi da darajar 'ya'ya ba, Yace "SAFNA Kiyi hakuri da kaddarar rayuwa da tasameni domin kuwa har ni Nan banine mahaifinki ba, Na tsinceki ne a k'ofar gari a lokacin nadawo daga kasuwa misalin k'arfe 8 na dare a lokacin nayo Daren dawowa gida, Anan Naga wani kwali a jiye bakin hanya jariri Yana ta faman kuka a cikinsa, Lek'a kaina nayi a cikin kwalin naganki kwance kina sanye sanye da kayan sanyi da hula da Safar hannu da k'afa masu shegen kyau An dunkuleki da towel Mai kyaun gaske kasancewar lokacin sanyi NE hannunki Yana sanye da zoben zinari Mai tsadar gaske, Tausayina ya kamashi ya duka ya daukeni ya rungumeni a jikinsa yanufi wurin maigari Dani, Anan yayiwa maigari bayanin a inda ya tsinceni." Sosai maigari ya girgiza da maganar, Hakan safiya ta waye a ka shiga cigiyata ko Allah yasa za'a Gane iyayena a tunaninsu Koda barayine suka shiga wani gida suka satoni idan iyayena sukaji sanarwa zasuzo su karbeni." .shuru ba Wanda yazo yace yasan ko Mai Kama Dani, Washe gari maigari ya yanke shawarar akaini birni a ajiyeni a gidan marayu." Baba ya nuna Yana sona zai rik'eni domin baitaba haihuwa ba, shekararsa 20 da matarsa, Hakan maigari ya Amince yabawa baba ni, Ya kaima matar sa INNO." INNO batayi farin cikin amsoni da baba yayi ba, Dan da farko cewa tayi bazata amsheni ba, sai da taga zata rasa igiyar aurenta snn ta amsheni." Tin Ina makaramata nasan wahalar rayuwa domin da zarar nayi Kashi ko fitsari Inno zata dinga dukana tana zubamun ruwan sanyi a jiki, Tin baba Yana fad'a Yana magana har ya Kai ya daina yashiga Jin shakkunta Wanda da alamar takaishi an d'aure Masa baki a wurin boka." Hakan na girma duk wani aiki na gida nice keyinsa Dan Gane da girki d'ibar ruwa kiwo faskaran iccen da za'ayi sawwa dashi duk nice keyinsa, lokaci take d'ibarmun da zarar lokaci yacika bandawoba zan Sha wahala a wurinta zata Sanya bulala ta dakeni daga k'arshe bazata bani abincin da zanciba a ranar da yunwa zan kwana" Allah yayi Mai farin jinin jama'a A yanda naji ana fad'a cewar ni kyakkyawa ce duk cikin k'auyen Nan ba Wanda ya kaini kyau, Dan hakan ake mantawa da rashin asalina saboda kyawona masoya suke turuwa a kaina." Duk Wanda yazo neman aurena INNO take korarsa musamman idan ta fahimci Dan gidan mutumci ne, Wanda tasan idan ya aure Ni zanje na huta." Duk abin Nan da akeyi baba bai San abinda akeyiba, Shi a ganinsa rashin samun mijin aure da banyiba, Wata k'ila Aljanu suka aure Ni, Dan kuwa duk sa'ata sunyi aure wasu har sun haihu, Ni har yanzun shuru ba miji gani kyakkyawa ajin farko." Mutum d'aya ne ya jure korar jummai da tsangwamarta ya nace akaina cewarsa tinda Yana Sona sai ya aureni babu Wanda ya Isa ya Hana, Sunan shi AUDU." Audu D'an sarkin kiwo ne dake cikin k'auyen mu, Sosai Yan matan garin suke ruguguwa a kansa domin yace Yana sonsu bai furta hakan ba sai a kaina." Bana son Audu sam a Raina domin ni duniyar ma gaba d'aya taficemun a Rai fatana Akoda yaushe Allah yayi mun mafita, ta Alheri ya bayyanarmun da iyayena domin naji dad'in da yasa suka jefar dani a lokacin da nake da buk'atarsu." Hakan Nan nake kula Audu nasanyawa rayuwata zan aure shi Koda bana sonshi, kodan na huta da azabar Inno." Ana hakan D'an maigari JARMAI JAN WUYA shima yafito neman aure na, Sosai Inno tayi farin cikin fitowar Jarmai domin tasan da zarar sun Kara da Audu wurin shad'i, ba makawa zai cinye Audu, dele a d'aura mun Aure da Jarmai, duk yarinyar da jarmai yace Yana so a garin Nan sai ya aureta Koda Bata sonshi Dan kuwa, za'ayi zab'en fidda gwani a filin shad'i kamar yanda Al'adarmu ta fulani take duk akayi shad'i Jarmai keda nasara, duk mutunen garin sun San da hakan, Yanzun shekara 7 kenan duk shad'in 'akayi shine ke cinyewa, Kuma a Nan take za'a aura Masa yarinya, dare D'aya Yake farketa batare da yaji tausayintaba sai ya gama biyan buk'atar gareta har na tsawon sati daya snn yake sakota wasu yaran mutuwa sukeyi wasu Kuma sukan kamu da ciwon yoyon fitsari, wasu Kuma Allah ya taimakesu su gyaru, yarinya bakwai Jarmai ya aura a cikin garin Nan duk hakan yake masu." Ta share hawayen fuskarta taci gaba da cewa, "yanzun saura wata biyu ayi shad'in mu, zasu Kara tsakaninsa da Audu duk Wanda yacinye shi zan aura, nasan jarmai ke da nasara domin duk mutanen gari sun shaida hakan." Tin daga ranar da aka saka ranar shad'inmu duk Wanda yagani, ya rabeni da sunan yana sona, ko yana mun magana indai namijine sai Jarmai yayi Masa bugun mutuwa." Mutum biyu Yana kashewa Akan sun furta suna Sona, Hakan ya Hana Audu yin magana Dani, Shi kad'ai Yake magana Dani duk a cikin garin Nan, Dan hakan idan nafito kowa baya son ya ganni bare yayimun magana Domin gudun wahalar Jarmai, Idan nafito kiwo zai dinga zagayena duk ranar da Mai rabon wahala yasa yayimun magana a ranar sai dai uwarsa ta haifi wani." Wnn dalilin yasa nadinga fad'a maka Kayi nisa da rayuwata gudun kada ya ganmu a tare yayi maka illah sai gashi kasayeshi da kud'i a lokaci d'aya." Ta fashe da kuka Mai sauti tace "tayaya zaka taimakeni?" Kabarni kawai har zuwa lokacin da mutuwata zatazo ta daukeni Dan kuwa bana da gata, iyayena sun zubar Dani a lokacin da nake da buk'atarsu." Sosai idon Sauban yacika da hawayen tausayinta, Ashe a duniya akwai Wanda yafishi shiga cikin matsalar rayuwa?" Saurin goge hawayen fuskarsa yayi Dan gudun kada tagansa, Yasanya handkichif yashiga share Mata hawayen dake zuba Akan fuskarta ji Yakeyi kamar ya janyota ya rungumeta, shima ya fad'a Mata damuwarsa, kukanta ya tsaya cak jin hannun D'an birni a kan fuskarta Yana share Mata hawaye, Sai da ya goge Mata hawayen tas snn ya juyo da ita suka fuskanci juna yace "daga yau kukanki ya k'are, bana son ganin zubar hawayenki." Safna Kin Amince Dani?" Ta d'aga kai alamar eh." Ya Dan saki murmushin gefen Baki, yace "yanzun a wane wuri Audu yake Zama?" Tace "Audu baya gari yatafi binni sai ana gobe shad'i zai dawo." Girgiza Kai yayi alamar gamsuwa zaiyi magana Kenan wayarsa ta dau ringing yacirota yayi a gaban Aljihunsa ya duba safwn yagani yaja dogon tsaki ya d'auki wayar tare da karawa a kunnensa yayi shuru batare da yayi maganaba , "Muryar safwan yaji Yana fad'in "aboki kana Ina ne nadubaka banganka ba." "Meyafaru?" Sauban yace." Tambayar me yafaru tabawa safwan haushi, yace ai Kaine zan cewa meyafaru sabida a yanda naji muryarka baka cikin natsuwarka Kana ganin la'asar ta gabato kazo muyi Shirin tafiya, kamanta ne har zamfara zamutafi, Wai kana Ina ne hakan?" "Bansaniba Domin baka aikeniba, Kajira gani Nan zuwa yanzun. idan kuma a matse kake kana iya komawa gida, Dan nasan abinda zaka cemun kenan." Dariya safwan yasaki, wacce yasa Sauban yayi saurin kashe wayar tare da Jan dogon tsaki, Mik'ewa tsaye yayi Yana kallon Safna yace "ki waita Addu'a kisanya Allah a gaba domin shine Mai yin komai, Ki daina ganin laifin mahaifanki domin bakisan dalilin da yasa suka jefar dakeba." Ki daina yawan kuka saboda kuka yakan haifar da matsaloli a lafiyar D'an Adam." Snn ki yawaita zagayowa wurin Nan saboda a Ko wanne lokaci zan iya zuwa nemanki a Nan." Ya juya yayi tafiyarsa har yayi nisa ya juyo ya kalleta yaga shi take kallo tana murmushi, D'an murmusawa yayi yace "kicire tsoro Jarmai a ranki domin babu wani abu da ya Isa yaimaki Kuma insha Allah bazaki aure Shiba, Ya juya yayi tafiyar sa." Tafiya yakeyi tunaninta yake tare da juya magagganun da ta fad'a Masa dangane da rayuwar ta, Tabbas tana buk'atar taimako." A hakan har ya Isa gidan gonar ba Wanda yaga dawowarsa Kai tsaye d'akinsa yanufa ya fad'a kan gado yayi filo da hannunsa yashiga duniyar tunani, Ba abinda yake tunani sai ta wacce hanya zaibi domin ya taimaketa, D'an karamun bakinta yashiga hangowa yanda take juyashi tana Masa magana, tare da manyan idanunta masu zubar da Hawaye, Tabbas Safna tana da kyau domin ko a turai baitaba wacce tayi kyantaba, wahalace da danti yasaka kyawon nata ya kusan disashewa." Dogon tsaki yaja ya Kuma mirginawa, tare da janyo filo, Sai mutum yaji a kan filon,. D'aga idonsa yayi domin ganin ko waye,.safwan ya gani kwance Yana kallonsa cike da mmki." Tsaki ya Kuma ja Yana fad'in "meye hakan safwan?" Safwan yace "meye hakan Sauban da ka kusan Hawa kaina." Me Yake damunka ne Naga duk ka birgice kashiga duniyar tunani kamar Wanda ya fad'a soyayya a lokaci Daya Ina kafito?." Jan tsaki Sauban yayi ya Kai Masa harara." Dariya safwan yasaki tare da sauka daga Kan gadon yace "ko tsaka da tayi tsaki Allah sai da ya tsine mata, Malam katashi tinda kadawo mu fara Shirin tafiya kasan inada iyali." Kallonsa Sauban yayi yace "sai gobe zamu bar nan, ba yau ba." Daga hakan ya mik'e ya bar Masa d'akin, domin Yana da buk'atar Zama yayi dogon tunani Wanda yasan indai safwan Yana a wuri surutunsa bazai barka kayi wani nazariba, _kai Safwan a rage surutu kayi hakuri Sauban Nima hakan nake fama da nawa safwan din har ciwon Kai Yake sakani_🤦🏻‍♀ Bin bayansa safwan yayi Yana fad'in "dakata malam Wai meyake damunka ne munzo lafiya k'alau lokaci d'aya duk ka wani birkice." Kyalesa sauban yayi yaci gaba da tafiyar sa yanufi wurin lambu domin shak'ata, daga yayi tinanin da ya damesa." _comment dinku Yanayin k'asa sosai idan Naga ba'a comment zan ajiye rubutun na Bari sai Bayan sallah wata k'ila naci gaba?_ *Mrs Ana's Bawa*✍ _Not edited_ *Mrs Ana's Bawa*✍ _comment dinku Yanayin k'asa sosai bakwa comment shiyasa banajin k'arfin gwaiwar yi maku typing kullum, gaskiya idan Baku gyaraba 'DAN SARKI SAUBAN zai koma na kud'i yasin ko a jikina🤷🏻‍♀_ *Mrs Ana's Bawa*✍ _kome ke faruwa Kuma Sauban_?🤔🧐 *Mrs Ana's Bawa*✍ *Mrs Ana's Bawa*✍ *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 19* Kwance yake akan doguwar kujerar dake zagaye da lambun yana kallon sama, ya d'ora hannunsa Akan goshinsa ya lumshe idonsa da alama, Tunani yakeyi, babu abinda Yake Masa gizo a idonsa sai kyakkyawar fuskarta tare da D'an k'aramun bakinta a lokacin da take bud'eshi tare da juyashi tana fad'a Masa damuwarta." Dogon tsaki yaja ya Kuma juya kwanciya daya tina da yanda idonta yake zubar da hawaye alamar tasaba da kukan, Kuma Jan wani tsakin yayi ya mik'e zaune tare da dafe Kai." Kallonsa safwan yayi dake gefensa a zaune akan d'aya kujerar dake kusa dashi Yana latsar laptop d'insa, Ya d'an dakata da dannar laptop din yana kallon sauban tabbas akwai abinda yake damunsa a rai, shi dai iya saninsa lafiya kalau sukaxo k'auyen nan, Murmushi yasaki yace "ya dai abokina?" Tsakin da kakeyi akai akai nameye Allah yasa ba gamo Kayiba?" Kuma Jan wani tsakin sauban yayi yamike tsaye tare da wurgawa Safwan harara Yace "idan kaga dama katashi mutafi muyi sallah magariba idan kuma sai ka tsaya yimun tambayoyin abinda yake damuna sai kayita zama, yayi gaba abinsa ya bar safwan yana kallonsa." Mere Baki safwan yayi ya rufe laptop d'insa ya mik'e yabi bayansa Yana fad'in idan tayi wari ai maji." Banza dashi Sauban yayi yaci gaba da tafiyarsa, Bayan sun kammala yin sallar magariba dukansu suka fito fadawa sai gaisuwa suke kaiwa a gaban Sauban, d'aga masu hannu kawai yakeyi alamar ya amsa, ya wuce yayi gaba." D'ak'i yashiga ya fad'a toilet ya yyi wanka yafito ya canza Kaya izuwa jallabiya ruwan k'asa mai d'an gajeren hannu ya Sanya silifas yafito, A tunaninsa zai ga safwan yabiyo bayansa cikin d'akin, sai yaga ashe bai biyoshiba, yaji dad'in hakan, sannu a hankali ya sulale ya fita ta k'ofar baya yanda ba wanda zai ganinsa, cikin gari ya nufa Kai tsaye batare da kowa ya gansa ba. Kasancewar duhu ya Fara mamaye garin gashi ba wutar nepa, hakan yasa yayi amfanin da fitilar wayarsa ya kunna yashiga haska gabanshi." Wurin da suka zauna dazun yanufa, baiyi dibon dare neba, gudun kada wani abin ya cutar dashi kasancewar wurin dajine ba mutane a wurin sai yawan itatuwa." Zagaye wurin yayitayi yakai yadawo Yana dube dube ko Allah zaisa zai yahangota, shuru ba Alamarta, sai da yaji anfara Kiran sallar Isha'i snn ya hakura ya Koma inda yafito zuciyarsa ba dad'i ya rasa dalilin b'acin ran nasa, Kai tsaye massalaci yanufa bai ko jira safwan ba, Sai dai safwan ya tarar dashi zaune a sahun gaba, mamaki ya cika safwan yashiga tambayar kansa meyake damun Sauban ne munzo lafiya Amma lokaci Daya duk ya birgice." Hakan sukayi sallah suka Koma cikin gidan gonar, har a lokacin Kan sauban sama yake Yana tunanin tare da Jan dogon tsaki, zuciyarsa tana tsananin tausayin Safna jiyakeyi tamkar ya dauketa suyi tafiyarsu ya kaita cikin masarautarsu domin tasamu yanci kamar ko wanne yaro Mai gata." Dogon tsaki yaja ya juya da karfi Cikin d'aga murya mai sauti Wanda bai San yana da itaba yake fadin natsani zubar hawayenki insha Allah Nine gatanki zanyi maki gata tamkar iyayenki." Maganar zuci yakeyi bai San tafito fili ba." Wata irin dariya Mai sauti safwan yasaki Yana kallon sauban Yana fad'in "haba sai yanzun na Gane wnn sauyin naka Ashe kogin soyayya kafad'a, ni ko wacce yarinyace wnn Mai sa'a a duniya,?" sunkuyawa safwan yayi gefen sauban cike da tsokana yace "ranka ya dad'e, kogin soyayyah ne kafada ba KO tantama sonta kakeyi." DA sauri sauban ya kallesa ya kuma Jan tsaki yana fad'in " ita wa?" Wacece kake magana a kanta?" ya dafe kansa yace "banga dalilin DA yasa nataho DA Kaiba wlh." Dariya safwan yasaki yana fadin "kafini Sanin KO wacece, Kada kadamu ko yanzun muna iya bin hanya mukoma gida idan baka iya kwana Kai kad'ai sai da macce, don kuwa nima kaina a takure Zan kwanta." Juyawa yayi ya wurgawa Safwan harara yace "kadauka kowa irin ka ne." Dariya safwan ya saki yace "har gwarani Ina a mayar da abinda ke raina bana barinshi a rai har yafara sanyani sabbatu maganar zuci tafito fili." Gyaleshi Sauban yayi ya rufe Idonsa tamkar Wanda Yake bacci shi kad'ai yasan yanda yakejin a ransa akan tausayin Safna." Hakan suka kwana Sauban bai samu wani baccin kirkiba da zarar ya motsa safna yake gani a idonsa tana kukan nan nata, tunani kawai yakeyi hanyoyin da zaibi domin ganin ya taimaketa." dakyar yasamu safiya tawaye masa,Bayan sunyi sallah suka shiga Shirin barin garin zuwa masarautar zamfara, Sosai yayiwa masu kula da gidan gonar Alheri, hakan suka tafi wurin Mai gari sukayi masa sallama shima Sauban yayi Masa Alheri Mai gari sai godiya yakeyi Yana Jin dad'i snn suka fito." Tunani yake a Ina zai ganta gashi bai San gidan su ba, Waigawa yayi ya Kalli safwan dake gefensa yana waya, ya wurga masa harara cike DA jin haushi tare da jan dogon tsaki, Wanda sai da safwan ya Dan juyo ya kallesa yayi masa alama DA hannu meya faru?" Kauda idonsa gefe sauban yayi yaci gaba da kallon gefensa da bayansa yana tinanin ta Ina zata fito." Karo sukaci DA wani d'an fillo yana kiwon shanu, sauban ya nufi wurinsa yana fadin "Assalamu Alaikum malam Dan. Allah tambaya nakeyi. K'asa d'an fillo ya zube yana kallon yarima yana fadin ranka ya Dad'e da kanka Allah yasa nasani." Hannu sauban ya mik'a masa alamar yatashi tsaye, AI kowa cikin sauri d'an fillo ya mik'e tsaye." Hannu yarima a cikin Aljihun wandonsa , yake kallon d'an fillo cikin maganarsa daki daki yace "kasan gidansu Safna?" Safna ranka ya dad'e?" D'an fillo ya jeho masa wnn tambayar." D'aga Kai sauban yayi alamar eh ita nake nufi." Kallo safwan yake binshi cike DA mamaki DA Al'ahabi tare da ayar tambaya a bakinsa." D'an fillo yace "duk garin nan safna d'ayace budurwa, wata fara marar jiki kyakkyawa, hannu sauban ya daga masa ya furta ita nake nufi Ina ne gidansu." Cike DA mamaki d'an fillo ya shiga kwatanta masa gidan, Girgiza Kai sauban yayi alamar ya gane, ya Ciro kudi a Cikin Aljihu ya mikawa d'an fillo, hannu na rawa ya amsa yana zuba godiya" Sauban bai tanka masaba yajuya yanufi inda yayi masa kwatancen, Safwan yana biye dashi cike DA mamaki ba damar yayi magana yasan halin sauban sarai DA zarar yayi magana bazai tafi dashiba, idan kuma ya dage akan sai yatafi dashi yafison yafasa ai watar da abinda yake da Niya, Wanda bazai so hakan ba yafiso yabishi a hakan har yaga yarinyar da tafara yasaka sauban sabbatu." Sauban a gaba safwan yana biye dashi a baya, sai shanye kwana sukeyi suna bullewa wata, suna karya wata kwana kenan wanda zata sadasu da da gidansu safna kamar yanda d'an fillo yayi masu kwatance, sai ganin mutum sukayi anjefo daga cikin gida Wanda sauban yake tunanin nan ne gidansu safna Safna ce kwance a k'asa tana rungume da fantekar d'ibar ruwa, matar DA tajehota waje sai kunfar baki takeyi tana d'aga murya daga cikin zauren gidan tana fad'in "munafuka mai bak'in jini duk sa'arki sunyi aure sunbarki, to kisani bazakici abinci a gidan nan ba, har sai kin d'ebo mun ruwa, tinda ba ubanki yake kawo abincin ba tsinanniya wacce aka tsinta a cikin bola." Wayasani ba ko cikin shege uwarki tayi ta zubar dake a bola, Aljana Kawai." Durkusawa sauban yayi ya rok'ota ya mikar DA ita tsaye cike da tausayi, safna tana ganin sauban ta kara fashewa da kuka, yayi saurin runtse idonsa zuciyarsa tana k'una a rayuwarsa ya tsani zubar hawayenta." Ya juya ya kalli inno dake tsaye a cikin zaure sai zarar ido takeyi ganin yarima, Murmushi ya Dan Saki ya tako zuwa k'ofar zauren gidan ya d'an sinkuya yace ' Ina kwana Inna." Zubewa k'asa inno tayi tana fadin ranka ya dade DA kanka a kofar gidan nan barka da zuwa bara nakira maka jauro, ta zuba cikin gida DA gudu." Yacika DA mamaki dama jauro yana cikin gidan akeyiwa safna wnn cin mutumcin to meye amfaninsa tinda matarsa tafi karfinsa, Dogon tsaki yaja ya juya ya kalli safna wacce take goge jikinta tana sharar hawayen fuskarta safwan yana,mik'a Mata fantekar d'ibar ruwanta." Dogon tsaki yaja ya kuma juyar da fuskarsa kofar gidan, Wanda yayi dai dai da fitowar jauro" *ABIN MAMAKI BAYA K'AREWA SAI DA NA TSAYAR DA RUBUTA WNN LITTAFIN AKAN RASHIN COMMENT DINKU, SNN NADINGA GANIN ANABI PRV ANA BANI HKRI WASUMA BANYI TINANIN SUNA KARANTAWA BA, TO KUBARI KUJI KO YANZUN IDAN BANGA RUWAN COMMENT BA AJIYE RUBATA SHI ZANYI SABODA INA DA ABINYI BAZAI YIWO NA B'ATA LOKACINA NAYI MAKU TYPING SABODA JIN DADINKU COMMENT YAYI MAKU WAHALAR YI, ALLAH BANDA NARIGA NAYI ALK'AWARIN BAZAN SAYAR DA WNN LABARIN BA DA TINI NA MAYAR DASHI NA KUDI KO A JIKINA*🤷🏻‍♀ [9/3, 6:26 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 24* *SHAD'I* Kamar yanda kowa yasan yanda Al'adar fulani take musamman fulanin daji masu rok'o da Al'ada, wad'anda suka d'auki Al'ada da mahimmaci tamkar Addini." *FAGEN SHAD'I* Jarmai ne tsaye a tsakiyar fili rik'e da zungureriyar bulalarsa sai zarar ido yakeyi yana d'aga kwanda💪🏼, yaransa sai zuba masa kirari sukeyi suna k'Ara masa kwarin gwaiwa suna fad'in "sai kai oga mijin Safna kaine mai nasara domin nasara takace, Gaban JARMAI a Audu ne a tsaye shima rik'e da bulalarsa fuskarsa alamun wasa a tare da shi, sai hura hanci yakeyi👃🏼 Dukansu ba riga a jikinsu jiran umurni kawai sukeyi sufara dukan junansu." Gaba d'aya jama'ar gari maza da Mata sun hallara a wurin, sun zagaye fagen wasar suna kallo suna jira a fara, A can gefe d'aya akan kujera maigari ne zaune tare da hadimansa suna kallon yanda shad'in zai kasance." Can d'aya gefen kuma Safna ce tsaye kusa da Baba sai kuka takeyi idanunta sunyi jajir sun kumbura Baba sai lallashinta yakeyi yana fad'in ta daina kuka Addu'a ya kamata tayiwa Audu Allah yabashi sanara ya cinye." D'aga kai tayi alamar "to ta daina kukan, illah taci gaba da sharar hawayen domin duk yanda takeso taga kukan ya tsaya ta kasa saboda kuka shi keyin kan sa ba ita keyin saba, waige Waige kawai takeyi ta inda Sauban zaifito mata domin taji a jikinta zaizo gareta." A can ta hangoshi tafe ya tunkaro wurin cike da k'asaita da isa mai cike da tsantsar mulki, fuskan nan tashi sai Annuri take fitarwa, safwan yana gefensa, fadawa guda biyu suna bayansa sun take masa baya, wani irin murmushi tasaki Wanda batasan tanayin irinsa ba, yunkurin zuwa wurinsa tayi cike da farin ciki Baba yayi saurin tareta yana mata gargad'in kada ta karya Al'ada." Ido yadawo kansa kowa cike da mamakin zuwan nasa yakeyi, Murmushi maigari yasaki yana kallonsa domin ganinsa a dai dai wnn lokacin ba k'aramun mamaki yabashi ba." Maigari yabada umurnin akawowa yarima abin zama, Cikin minti uku aka d'ora kujeru sauban da safwan suka zauna fadawa suka zagayesu a baya." Gaisuwa maigari ya kai wurin yarima, yarima yana fara'a suka gaisa." Tare da tambayarsa yaya maimartaba?" Lafiya k'alau sauban yace, maigari yana murmushi yacewa sauban "yau Allah ya kawoka a dai dai lokacin da muke gudanar da Al'adarmu ta shad'i Allah yasa zata k'ayatar dakai, duk da dai kaima bafulatanine amma na birni." Murmushi sauban yasaki tare da jinjina Kai." snn suka maida hankalinsu wurin shad'in a dai dai lokacin da ake neman maigari yayi magana a fagen wasa domin yayi gargad'i tare sanarwa tare da yin tini akan abinda ya gabata akan shad'i kodan ganin yarima ya halarci wurin ." A can ya hangota tsaye kusa da baba tana kallonsa tana murmushin farin ciki hawaye suna zuba a idonta." Shima murmushi ya Sakar mata, Yayi mata alamar ta share wayenta ta daina kuka." Ai kuwa cikin sauri ta share hawayenta tana sakar masa murmushi." Ido Safwan yake binsu yana kallo cike da mamaki k'iri k'iri ga gaskiya ta bayya sauban son Safna yakeyi Safna son sauban takeyi amma saboda taurin kai irin na Sauban baitab'a yarda da Sonta yakeba har b'acin rai yake nunawa idan akace sonta yake, sai yace shi tausayinta yakeyi a daina cewa yana sonta saboda shi baya da lokacin wata soyayya can ta shirme bai masan abinda an soba kuma baya fatan yasani saboda baya da lokacin shi son." Safwan ya Rik'e baki yana mamaki to yanzun kuma meya kawosu nan?" Maigari yasoma bayani kamar hakan "kamar yanda kuka sani a duk bayan shekara d'aya mukan gudanar da Al'adarmu ta fulani wato shad'in fidda gwani, Wanda Al'adace wacce muka taso muka tarar iyayemun da kakanninmu sunayi kuma suka d'oramu akai, Indai Kai bafulata nine Wanda kake rayuwa a cikin wnn k'auyen dama wajen nan in har zaka mallaki macce, komai kudinka KO Mai mulkinka saikayi shad'i tare da abokan kashewar ka, Anan zaka nuna bajintarka da k'arfinka snn k'arfinka ya baka macce." Dokokin shad'i sune bamason hayaniya tayi yawa, Snn duk Wanda aka daka har zafin duka yasakashi ya fad'i k'asa, kamar yanda kuka sani yafad'i a fagen shad'i, Wanda kuma bai fad'i ba shine mijin Safna banason fad'a ko wani tashin hankali a nan." Snn yaba da umurnin a Fara wasa." Anan take jarmai da Audu suka shiga dukan junansu da bulala ba girma ba arziki, Ko wanne k'ok'ari yakeyi yakai d'an uwansa k'asa." Sosai Audu ya daku ya jigata jikinsa da fuskarsa suka fara fitar da jini, amma yaki ya fad'i sai buga in buga sukeyi da jarmai Wanda jikinsa kawai ne yayi kwancen bulala, jini bai fitaba, Kuka safna ta fashe dashi a lokacin da taga jarmai yana neman cin galaba akan Audu domin jini har ya fara wankewa Audu fuska amma har yanzun bai fad'i k'asaba, Wanda da zarar ya fad'i shikenan jarmai ya ci galaba a kansa." hakan Audu yake dukan jarmai jarmai yake dukan Audu, a can jarmai yasami sa'ar Audu ya doka masa bulala a tsakiyar kai, anan take Audu yasaki wata irin k'ara ya fad'i k'asa a some." Da gudu Safna tanufi wurinsa tana kuka tana jijjagashi tana fad'in katashi Audu katashi meyasa kabari Azzalumi yaci galaba akanka?" kana gani za'a auramun azzalumi, ta d'aga murya cikin sauti sai da gaba d'aya wurin ya amsa tace Audu katashi ." Dariya Jarmai yasaki cike da jin dad'in samun nasara, Hakan masu goyon bayansa suna murna tare da ihu suka d'aukeshi suka d'agashi sama suna juyashi, Yashiga yiwa kansa kirari kamar hakan "saini jarmai angon Safna mainasara, sai ni Jarmai d'an maigari ba Wanda ya isa ya tab'ani ya zauna lafiya." Snn ya sauka daga d'aukar da aka suka masa, Yanufi wurin safna dake durk'ushe a gefen Audu tana jijjigashi tana kuka tana fad'in tashi Audu karka mutu, hannu jarmai yasaka ya ruk'o hannunta ya mik'ar da ita tsaye ya Janyeta a wurin, tana tirjewa tana dukan hannunsa a kan yasaketa yak'i yasaketa sai da yafito da ita tsakiyar fili ya d'aga hannunta sama yana fad'in saini jarmai na Safna, Safna ta wace idan akwai wani Wanda yakeji da kansa yafito mukara idan uwarsa bata haifi wani ba." Safna tana kuka idonta akan sauban, Wanda ya runtse ido jikinsa sai rawa yakeyi alamar ransa a b'ace yake." Cikin zafin nama sauban yamik'e tsaye tare da cire rigar jikinsa sai ciccira yana neman yashiga filin shad'in, Safwan ya rik'eshi hakan fadawa sukayo kansa suka rik'eshi suna fad'in ranka ya dad'e meye had'inka da shiga filin shad'i?" bazaka iyaba, ka rufamana asiri bamaso mujewa maimartaba da mummunan labari." Hannu biyu yasaka ya turesu gefe d'aya dukansu sai da suka fad'i k'asa har safwan, jikinsa sai rawa yakeyi yanufi wurin jarmai ya fisge hannun safna daga hannunshi ya turata gefe d'aya snn ya duk'a ya d'auki bulalar da Audu ya jifar k'asa Yanuna Jarmai yana fad'in, Kana fad'in sunanka Mai nasara amma yau kasanyawa ranka daga yanzun sunanka marar nasara, domin bakomai akeyin nasara akansaba, har yanzun Safna bataka bace Safna ta mai raboce tsakanin ni da kai." Da gudu safna ta nufo wurin yarima tana kuka takai durkushe a gabansa tana fad'in banaso na rasaka, domin bazaka iya da wnn Azzaluminba kayi tafiyarka kawai." janyeta yayi a gabansa domin ya tsani ganin kukan nan nata a idanunta, ransa ya kuma b'aci jijiyoyin kansa duk suka firfito jikinsa sai rawa yakeyi yana kallon jarmai." Dariya Jarmai yasaki yana kallon yarima yace "d'an birni zaka iya karawa dani?" Bai iyar da rufe bakinsaba cikin zafin rai Sauban ya sakar masa bulala a tsakiyar gadon bayansa, wacce anan take wurin ya tulb'e da jini, Ai kuwa shima jarmai yashiga kaiwa yarima duka kota Ina, Idon yarima a rufe suke saboda b'acin rai da zuciya bayajin dukan da jarmai yake masa shima cikin zaffin nama yake kaiwa jarmai duka anan take bakin jarmai ya fashe da jini abinda bai tab'a faruwa dashiba, Dukansa sosai sauban yakeyi dukanda bayaji baya gani domin idonsa a rufe suke, Dukan da ya kaimasa a tsakiyar kai yasaka jarmai zubewa k'asa a some." Ihu mutan gari suka d'auka suka tunkaro sauban suka d'ashi sama suka shiga juyashi kamar yanda Al'ada take." umurni ya bada akan a saukeshi sakamakon kansa da yakeji yana Sara masa, Ana saukeshi Safwan yanufo wurinsa ya mik'a masa riga yasaka, da gudu safna ta nufoshi ta fad'a kan jikinsa tasaki kukan farin ciki, Hannu yasaka ya rungumeta tare da runtse idonsa, sai da suka d'auki minti goma a hakan snn ya Janyeta a jikinsa aka bashi umurnin ya rik'a hannunta ya d'aga sama kowa yagani kamar yanda Al'ada ta tanadar kamar ynda jarmai yayi." D'aga Hannunta yayi idonsa a rufe sakamakon biyu biyu da yake ganin mutane, ya kasayin magana, Maigari yana ganin hakan yaturo dagaci yayi magana a maimakon yarima, Yagaci ya fara magana kamar hakan "yarima Safna takace ka mallaki safna idan akwai Wanda yakeda ja yafito su Kara da yarima, shuru kowa yayi, ba mai bakin magana, Sai da dagaci ya maimaita har sau uku ba Wanda yakeda ja, Snn wuri ya d'auki kuwa da sowa, Masu bakin ciki sunayi masu farin ciki sunayi." Ganin yarima yana Neman fad'uwa cikin sauri fadawa suka rik'ashi suka nufi gidan gona dashi." a nan take taro ya fara watsewa inda aka yayyafawa Jarmai ruwa, anan take ya farfad'o daga suman da yayi yana borin kunya yana fad'in ina yariman yake yafito mukara a karo na biyu waye yafad'a masa anaja da Jarmai." Sowa mutan gari suka shiga yimasa cike da murna don kuwa anan take Allah ya cire masu tsoronsa a ransu." Duk abin nan da akeyi fadawan da Saudat ta turo suna kaimata rahoton komai har Dukan da akayiwa yarima da cinye shad'in da yayi duk sunfad'a mata Suka k'ara da cewa ranki ya dad'e yarinyar ta cacci hakan kodan saboda kyawon da Allah ya Mata, Dan kuwa yarinyar kyakkyawa ce yanda kika san Al'ajana." Wani irin ihu Saudat tasaki tayi jifa da wayar hannunta ta cire d'ankwalin kanta tana fad'in k'aryane wlh, na rantse da Allah sainayi Ajalin duka zuri'arsu *Tofa* *Mrs Anas NASA*✍ [9/4, 7:56 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 25* "Tamkar mahaukaciya hakan saudat ta koma sai ihu takeyi tana jifa da duk abinda yatari gabanta, tana fad'in k'arya ne wlh ba wata shegiya data isa ta aure mun miji, in har inada rai ina motsi a doron k'asa." Cikin sauri tamik'e tsaye tanufi wurin wayar wacce tayi jifa da ita can gefe d'aya, Allah yasa bataci screen ba, Ido rufe Tashiga Neman number mahaifiyarta sarauniya Bilkisu." Bugu d'aya zuwa biyu sarauniya Bilkisu, Tabada umurni a d'auki wayar Cikin sauri Kuyangi suka d'auki wayar tare da Kara mata a kunneta, Muryar safna taji tana kuka sosai kamar wacce akayiwa mutuwa." Cikin tashin hanki da hanzari ta karb'i wayar daga hannun kuyanga ta juya ta kallesu tayi masu umurnin subar d'akin, Da hanzari suka fita daga d'akin, cike da tashin hankali take cewa my daughter meya faru kike kuka?" A duniya na tsani naji kukanki banason zubar hawayenki meyake damunki?" Meyake faruwa?" Me kikeso?" Kuka saudat takeyi sosai, tana fad'in mommy Sauban ne, Mommy sauban kishiya zaiyi mun, Sauban aure zaiyi mommy" "Aure sarauniya bilkisu tace cike da firgici, K'arya ne wlh bai isaba,waye shi da zai yi maki kishiya, nawa kike yaushe aka haifeki, da a turai muke ko a cikin lissafin aure ba'a d'orawa akanki bare azo akan maganar kishiya, Na rantse da Allah 'yata bazata zauna da kishiya ba kamar yanda nima bana zama da ita." 'yar Gidan Uban waye?" Wani matsayi keda ubanta?" 'Yar gidan wanne hamshak'in ne a cikin garin Adamawa?" Saudat na kuka tace "ba 'yar gidan uban kowa bace, 'yar k'auye ce ko a k'auyen a can cikin k'auyen Fulani k'azamai marasa wanka masu warin nono da manshanu." tasaki kuka tana fad'in Yana tsananin sonta domin har da dukansa akayi akan son da yake Mata wai duk a cikin Al'adar k'auyen ne. Domin kawai yasameta, mommy ya zanyi da rayuwata nashiga ukuna." mommy ta fusata tace baki kishiga ukuba, domin "Bai isaba wlh sai dai ya mutu akan son da yake mata amma bazai tab'a aurenta ba, ba zai tab'a kawota cikin gidanki a matsayin kishiya ba." har Abada sauban bazai tab'a yimaki kishiyaba in dai inada rai da numfashi a duniya, Waye sauban waye ubansa ko uwarsa da tana a raye bata isa ta ja daniba bare shi din banza." Mataki na farko da zamuyi amfani dashi shine, duk wata zuri'ar da ita yarinyar suke Alfahari da ita sai mun hallakasu." Gobe zanturo dakaru tare da kayan aiki gaba d'aya su ruguza k'auyen da duk a halin dake cikin k'auyen ke harda ma mutanen dake rayuwa a cikin k'auyen, A cinnawa gidansu wuta duk su k'une, bana buk'atar koda ganin gawarsu ayi." A tashi k'auyen gaba d'aya kowa ya huta, kinga idan mukaYi hakan Ankare da matsalarta ki sanyawa rayuwarki bake ba kishiya har Abada indai inada rai da lafiya ynda ban zauna da kishiyaba hkn kema har abada bazaki zauna da itaba." Dariya Saudat tasaki cike da farinciki tana fad'in "nagode mommy na Dan hakan nake tsananin k'aunarki fiye da daddy domin kece Mai sharemun hawayena bakyason ganin kuka na, *Kuyi hkr d wnn yau banajin yin typing din* *mrs Anas Bawa*✍ [9/8, 12:57 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 26* "A kan gado fadawa suka ajiye Sauban inda yake rufe da ido shi kad'ai yasan zugin zafin da yakeji a bayansa, Safwan ya taimaka masa yacire masa rigar jikinsa yana masa fifita, ganin shatin bulala ya kwanta a bayansa yayi masa jajir akan lallausar fatar jikinsa Abu ga farin mutum gwanin ban tausayi." Cike da jin haushi safwan yace "meye hakan ka janyowa kan ka kaga kuwa yanda jikinka da bayan ka, da duk ilahirin jikinka yayi? Wani irin so kakeyiwa safna Wanda har kake neman hallaka kanka da rayuwarka, a kan macce, na rantse da Allah ko ni kaina da nafika damuwa da macce bazan iya wnn wahalar ba, nafison na barta ko wacce ce har Abada in dai har sai anyimun irin wnn dukan za'a bani ita, haba ga mata nan 'yan birni birjek sai ka darje saika zab'a." Ni yan zun ban san yanda zanyi da kaiba gashi wnn zuwan bamuzo da doctor ba kamar yanda muka saba zuwa dashi a duk lokacin da zamuyi tafiya mai nisa." Wani bafade yashigo da sallama ya tsuguna a gaban safwan yana fad'in ranka ya dad'e mahaifin yarinyar akayi shad'inta ne, tare da yarinyar suke neman iso." Mere baki Safwan yayi domin cike yake dajin haushin halin da sauban ya jefe kansa a kan macce, A bazata yaji muryar sauban yana fad'in "kace masa ya shigo." Sauri Safwan yayi ya juya ya Kalli sauban, yace "Ashe dama kana iya magana kabarni inata surutu ni kadai kamar mahaukaci." Harara sauban ya jefa masa tare da jan tsaki." Sallama Baba ta katse Safwan daga maganar da yakeyi, son ya mayarwa sauban." Baba ya shigo Safna tana biye dashi a baya wurin zama Safwan ya nuna masa akan kujera tare da gaidashi." Amsa gaisuwar yayi tare da girgiza Kai, ya zauna k'asa yana fad'in Barni na zauna anan ya isa, Tsaye safna tayi idonta a kan yarima tana kallonsa cike da tausayi ganin duk jikinsa yayi ja akan kwancin bulala, Shima idonsa a kanta yana kallon fuskarta anan take yaji wani irin farin ciki da kuzari sunzo masa a lokaci d'aya, ya dafa gado ya Tashi zaune tare da yanyo rigarsa ya rufe jikinsa ya Kalli baba yace "Baba ina wuni." Lafiya k'alau Baba yace yaya k'arfin jikinka?". "Alhmdulillah sauban yace idonsa nakan safna dake sharar hawayen tausayinsa." Baba ya Ciro wani magani a Aljihunsa ya tashi daga inda yake yanufi wurin yarima yana fad'in "ranka ya dade magani nakawo maka Wanda zai taimakeka wurin kariyar dafin bulala." domin muna amfani dashi a duk lokacin da hakan ta faru, musamman ga Wanda akayi shad'i dashi Saboda yana karye dafin bulala yanda bazata kwanta ajikinkaba bare tayi maka tabbo." Murmushi sauban yasaki yace "nagode Baba, Baba yace "bakomai zaka iya gyarawa na Shafa maka A duk inda bulalar ta kwanta maka." Gyara kwanciya sauban yayi ya ajiye rigar da ya rufe jikinsa gefe d'aya, Baba ya matso ya shiga shafa masa maganin a duk inda bulala ta kwanta masa." Sosai jikinsa ya d'auki zafi alamar akwai zazzab'i a tare dashi, idonsa a kan Safna wacce take tsaye a Bayan Baba tana kallon yanda kwancin bulala duk ya b'ata masa kyakkyawar fatar jikinsa, hawaye tausayinsa kawai ke zuba a idonta, Wanda duk wani d'igo na hawayenta jinsa yakeyi har cikin zuciyarsa tamkar ana yayyafa masa ruwan zafi yakeji, saurin runtse idonsa yayi cike da k'unar zuci domin baya son ganin zubar hawayenta ko kad'an a rayuwarsa." A hakan Baba ya kammala Shafa masa maganin ya gyara masa kwanciya ya nemi wuri a kusa dashi ya zauna, Baba yayi gyaran murya yace Allah yabaka lafiya insha Allah wnn maganin zai taimake ka sosai zakaji k'arfin jikinka da walwalarka duka zata dawo, Ranka ya dad'e idan ba damuwa inaso zanyi magana da Kai." Bud'e idonshi sauban yayi ya tashi zaune yana kallon Baba da Safna wacce ganin Baba ya zauna itama taje kusa dashi ta zauna a gefensa, har yanzun hawaye ke zuba a idonta tana gogewa da bayan hannunta, Kallonta sauban yakeyi yana jijjina wnn soyayyar dake tsakanin Baba da Safna domin ya lura yana tsananin sonta itama hakan." Baba ya fara da cewa "hakika kayi namijin k'okari wurin karawa da Jarmai a wurin shad'i, kuma daga k'arshe Allah yabaka nasara akansa Wanda duka Mutanen gari suke cike da mamakin hakan har yanzun, Kamar yanda kasani jarmai yakanyi shad'i akan yasami macce idan yasa meta yayi nasarar Aurenta daren farko yake keta mata mutumcinta yayi mata illah sosai Zara kasa moruwa, da yawa daga cikin wad'anda ya aikatawa hakan wasu sun mutu wasu sun nakkasa yanda bazasu tab'a moruwaba har Abada." Ranka ya dad'e nasan kasami wnn labarin ne shiyasa ka shiga shad'i domin ka taimaki rayuwar Safna ba wai dan kana sonta ba har cikin zuciyarka, Alfarmar da nake nema a wurinka itace, ka taimaka mun ka Auri Safna koda baka sonta saboda tafita daga cikin wnn k'auyen Wanda zamanta a cikinsa a halin yanzun yanada hatsari sosai a rayuwarta da tawa baki d'aya, musamman idan jarmai ya gyallara ido ya dinga ganinta, tana yawo a cikin garin nan." Ranka ya dade koda baka ra'ayin Aureta bata cikin tsarinka, Ina neman Alfarma a Karo na biyu shine a cikin bayinka KO kuyanginka ka nemo Wanda ka yarda dashi ka yarda da hankalinsa ka aura masa Safna, Babba burina a rayuwa shine Safna tabar garin nan, Tasami inda zata zauna cikin kwanciya hankali da natsuwa." Ka dubi maraicinta Safna bata da iyaye Allah shine gatanta." Sharad'in shad'i a garin nan shine, idan kayi shad'i kamar a yau, A gobe duk Wanda yacinye zai tura mahaifansa a wurin maigari domin asaka ranar Aurensa da yarinyar, Ranka ya dad'e miye mafita kai nake saurare." Murmushi sauban yasaki domin duk magagganun da Baba yakeyi yanajinsu suna durar masa har cikin zuciyarsa tsantsar tausayin Safna mai zafi yakeji yana dakar masa zuciya, Idan yabari yabawa wani aurenta bai san yanda zai amsheta ba, bai san yanda zai tausaya mata ba, shi ya kamata ya amshi Aurenta domin yafi kowa sanin ko wacece safna domin ya rik'eta tsakani da Allah yaji tausayin maraicinta ya share Mata hawayenta, Da duk wahalar da Tasha a baya tazama tarihi a rayuwarta." cikin muryarsa ta marasa lafiya yace "Baba ni Zan auri Safna, Ni Zan zauna da Safna domin tasami farin ciki mai d'orewa, yanda zata manta da batada iyaye ta manta da ko ita wacece a duniya." Yau komai dare Zan koma gida gobe zan turo maimartaba da fadawa domin a nemamun Auren Safna." Wani irin murmushin farin ciki Safna tasaki Wanda yasa Sauban shima murmusawa, Yaci gaba da fad'in Ka kwantar da hankalika Baba babu abinda jarmai zaiyiwa Safna tin daga yanzun har zuwa lokacin da zatabar garin nan, kafin na wuce zanga maigari zan zauna dashi zamuyi magana." Godiya sosai Baba yake masa har sai da sauban ya dakatar dashi, Snn Baba yayi masa sallama tare da fatan samun lafiya yanufi hanyar waje Safna tana biye da Baba a baya." Kallo sauban yabita dashi yana murmushi Wanda baisan yana yinsaba, har zasu fita daga d'akin sauban yakira Baba yace "Baba Ina neman Alfarma zanyi magana da safna." Cak Safna taja ta tsaya a inda take, Baba yana murmushi yace badamuwa ya kalli Safna dake tsaye ta sunkuyar da kai yace "kije wurin yarima ki kula da kanki, Snn Baba ya wuce yanufi gida." Tsaye tayi wuri d'aya a inda take takasa motsawa, kanta a sunkuye cike dajin kunya." Kallonta yakeyi cike da Burgewa domin yana son macce mai kunya, Juyawa yayi ya kalli safwan Wanda yake zaune a kan kujera latsar waya kawai yakeyi azahirance kamar baisan abinda akeyi ba, Amma Duk abinda da akeyi yanaji a kunnensa kuma yana gani da idanunsa, mamakin sauban yakeyi a yanda soyayya tayi masa mugun kamu wacce baisan yanayin taba, Bai san tayi masa mummunan kamu ba." Sauban yana kallon Safwan ya had'e fuska yace " malam saika fita magana zanyi da ita." Banza Safwan yayi dashi kamar badashi yakeyiba." A hasale Sauban yace Safwan kanajinafa nace kad'an bamu wuri magana zanyi da Safna." Sai a lokacin Safwan ya kallesa yasaki murmushi cike da tsokana yace "cewa zakayi nad'aga nabaka wuri soyayya zakayi da safna." Harara sauban ya kai masa yace "ka d'auka kowa irinka ne, mutu macce." Dariya mai sauti Safwan yasaki yanufi hanyar waje yana fad'i waye ni ai duk abinda nakeyi shafin maine dan ka zartani a fagen soyayya yarda ne kawai bakayiba." Mere baki sauban yayi yabishi da harara, sai da yaga fitarsa snn ya koma kan safna wacce take a tsaye a bakin k'ofa sunkuye da kai cike da jin kunya." Muryarsa taji yana kiran sunanta cikin wata irin murya Mai taushin gaske, "Safna kizo mana." Sannu a hankali take takawa kanta a sunkuye a k'asa ta nufi wurinsa." Murmushi yake saki a fuskarsa ganin batason had'a ido dashi, A gabansa tazo tayi tsaye kanta a sunkuye gefen gado yanuna mata a kusa dashi yace " zauna a nan." Da sauri ta d'aga kai ta kallesa ta kuma sunkuyar da kai tace "A nan Zan zauna tana nuna k'asa." Kallon d'an k'aramun bakinta yayi tare da kyakkyawar fuskarta yaji ta burgeshi, Yace "safna musu zakiyi dani tin yanzun?" Da sauri ta girgiza kai alamar "A'a." Yace "zo nan ki zauna, ya kuma nuna mata gefensa." A hankali ta tako tanufi inda yace ta zauna, tare da sunkuyar da Kai ta zauna" Idonsa akanta yana murmushi, Yace "safna wnn kunyar tayi yawa a d'an ragemun ita." Rufe fuskarta tayi da tafin hannunta tana murmushin jin kunya." Murmushin shima yakeyi yace "ko sannu ya jiki baki cemun ba, bayan akanki aka dokeni." Janye hannunta tayi a fuskarta ta kallesa cike da tausayi ta zame daga kan gadon zuwa k'asa tana kallonsa tace "kayi hakuri ya jiki?" Insha Allah zakasamu sauk'i." Kallonta yakeyi cike da burgewa ji yakeyi kamar ya janyota ya d'orata akan k'irjinsa, Cikin kasalalliyar murya yace "tashi kidawo inda kike ki zauna, Cikin shagwab'a wacce d'abi'ar tace, Take fad'in ni sai ka amsamun gaisuwata ko Zan tashi." "Wow Sauban yace domin tayi matukar burgeshi shagwab'ar tayi mata kyau, Ajiyar zuciya ya sauke snn yace "Alhmdulillah naji sauki Safna rigima sai a tashi azo a zauna." Tana murmushi tazo ta zauna a gefensa, Yana kallonta yace "Safna burina a koda yaushe naga wnn murmushin ya danwama a kan fuskarki banason ganin kukanki, dan hakan na yanke shawarar Zan amshi Aurenki domin d'orewar farin cikinki kinsan dama nayi maki Alk'awarin Zan taimakeki Zan samar maki farin ciki Mai d'orewa, Safna ki yarda dani? Zaki Aure ni?" Hawayen farin ciki suka shiga d'iga a idonta, domin tarasa bakinda zatayi masa magana, A gabansa takai durk'ushe hawaye suna zuba a idonta, Tace ni wacce ce da Zan furta bana sonka, Kai ka taimakeni kayimun dukan komai a rayuwata, yarima nasan kafi k'arfina ni ba ajin aurenka bace, amma saboda ganin nasamu farin ciki wanda iyayena basa tunanin nasameshi tinda suka iya jefar dani akan titi, batare da sunyi tinanin halin da zan shigaba, Kaine mutum na farko da ka sanyani farin ciki, kaina wanda kake tausayina kake sharemun hawayena Ni wacce da zan furta bana son ka?" Kaine wanda ya taimakeni daga fad'awa daga cikin wata rayuwa wacce har gara wacce nake cikinta a yanzun da wacce Zan fad'a a hannun jarmai, Babban burin yarima shine ya taimakeni ya bani gata ya 'yanta daga cikin k'angin bauta, bakinta yana rawa akan kukan da yakeson yaci k'arfin ta kuma matsowa daf dashi saiti k'afafunsa ta sunkuyar da kai tace Yarima inasonka zan Aureka Zanyi biyayya a gareka tamkar baiwa, Zan bi dukkan umurninka fatana kada kajuyamun baya idan katina da ni shegiya ce banada iyaye, ta fashe da kuka mai sauti tamik'e tafita da gudu tabar d'akin tanufi hanyar gida tana kuka." Runtse idonsa yayi zuciyarsa cike da tausayinta yakai kwance anan take zazzab'i Mai zafi ya rufeshi." Safwan ne yashigo ya tarar dashi cikin yanayin zazzab'i, Anan take yakira direba suka shiga shirin tafiya domin yaga likita." Sauban yana jin jiki, amma Hankalinsa yana kan zuwa wurin maigari domin ya gana dashi yayi maganar safna akan gobe zai turo iyayensa." Zazzab'in da yake damunsa yaci k'arfinsa sosai ko magana baya iyayi idonsa a rufe, cikin gaggawa Safwan ya Rik'ashi yasakashi a mota suka bar k'auyen suka nufi gida." ******************** Mota goma sarauniya Bilkisu tacika da dakaru masu shirin yak'i domin sutafi k'auyen su safna sutayar da garin" Kafin sutafin sai da takira Saudat tak'ara yi masu kwatancen k'auyen, kamar yanda fadawa suka fad'a mata." gudun kada asami matsala wurin aiwatar da aikin tacewa fadawan da tatura, Tabasu umurnin akan su dakata kada sudawo sujira zata turo dakaru domin su nuna masu gidansu safna, Tana buk'atar a tashi k'auyen gaba d'aya." Anan suke fad'a mata yarima Sauban yabaro k'auyen yana kan hanyar komawa gida." [9/9, 6:09 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 27* ***** " murna Saudat takeyi jin sauban yabaro k'auyen, yanda dakaru zasu sami damar cika aikinsu batare da wata matsala ba." Kiran sarauniya Bilkisu Saudat tayi, tace "mommy bani d'aya daga cikin shugaban dakarun zanyi magana dashi." Mommy tabata shugaban rundunar gaba d'aya Wanda yafi sauran rashin imani da kafirci." Saudat takira sunansa "tace "Barde kanajina, umurni nabaka kafin Ku cinnawa gidansu yarinyar wuta, Ka tabbatar da kayi mata kaca kaca kayi mata fyad'e Wanda har abada bazata k'ara moruwa ba, snn ku cin nawa gidan wuta duk su k'une da duk zuri'ar su." Dariya Bard'e yasaki yana fad'in "angama ranki ya dad'e duk abinda kikace hakan zamu aiwatar Allah ya k'ara girma da d'aukaka, Snn ta kashe wayar a jiye gefe d'aya tana sakin dariyar farin ciki da jin dad'i, burinta ya cika domin da zarar anruga kauyen anyi Mata fyale koda ta rayu a duniya bazata tab'a moruwaba, yarima zaiji ya tsaneta tinda ta riga da ta nakkasa." A guje dakaru suke shek'a gudu bana wasaba, duk wasu kayan aiki sun tanadesu cikin motocinsu Kai tsaye suka nufi k'auyen Lassa." **************** A gaggauce Safwan suka iso, kai tsaye asibity aka nufa da sauban domin jikin nasa yayi nauyi sosai numfashi kawai yake saukewa baya iya bud'e idonsa, Taimakon gaggawa likitoci suka shiga bashi, Snn safwan yakira maimartaba yake shaida masa a inda suke a yyanzun, suna asibity da sauban ankwantar dashi baya da lafiya." Hankali maimartaba ya tashe idonsa rufe yakira Hajjah ya fad'a mata halin da sauban yake ciki Anan take, Hajjah da Anna suka shiga shiri tare da fadawa suka nufi Asibityn." ai kuwa cikin minti goma gidan sarautar ya d'auki Labarin yarima Sauban baya da lafiya yana kwance a asibity." Inda Sarauniya jamila tayi murna tayi farin ciki tare da Addu'ar Allah yasa daga can sai k'abari A bakin wata baiwa Saudat taji labarin cewar mijinta baya da lafiya, Ai kuwa hankalinta ya tashi cikin zafin nama da k'unar zuci, tashirya ta nufi asibityn kasan cewar family hospital ce kowa yasanta." bak'aramun tashin hankali hajjah tashi cikin saba a lokacin da taga yanda sauban ya rame lokaci d'aya, Uwa uba taga duk jikinsa kwancin bulala ne, tayi masa jajir akan farar fatar jikinsa, Wurinsa tanufa cike da tashin hankali, yana kwance a kan gado ana masa k'arin ruwa idonsa a rufe yana bacci tare da sauke numfashi sannu a hankali, kansa tashiga shafawa tana fad'in Sauban meya sameka?" Meya faru da kai?, nashiga uku wnn yaro marayan Allah kana ganin rayuwa iri iri." Saudat ta bud'e k'ofa ta shigo ido rufe tanufi wurin sauban ta fad'a kan jikinsa ta saki kuka mai sauti." Kallonta hajjah takeyi cike da tausayi ta janyota zuwa jikinta ta rungumeta tana lallashinta, Ganin yanda jikin Sauban ya kwanta da bulala ya kuma sanya Saudat ta fashe da kukan bak'in ciki da tsananin kishi, domin tasan dukan da akayi masa ne akan tsinanniya yarinyar da yakeso 'yar k'auye, yanzun gashi nan yana neman ya hallaka kansa da rayuwarsa." Likita ya turo k'ofa yashigo tare da Safwan yana biye dashi a baya, kai tsaye wurin sauban likita yanufa, ya k'ara dubashi tare da yi masa Allura, Safwan yana bayan likita a tsaye yana kallon sauban cike da tausayi" Kallon Safwan Hajjah tayi tace "Safwan meyasami abokinka ne a lokacin da kuka tafi gidan gonar?" Turo k'ofar da akayi ita ta hana Safwan ya bawa hajjah amsar tambayar DA tamasa." Maimartaba sarki ne da kansa ba aike ba, Yashigo fadawa suna biye dashi a baya, Ganin yanda Sauban ya koma lokaci d'aya ba k'aramun firgita sarki yayi ba, musamman yanda yaga jikin nasa duk ya kwanta da shatin bulala." Safwan sarki ya kalla cike da ayar tambaya yace "Safwan meyasami magajin Sarki hakan?" Ya akayi naga jikinsa da kwancin bulala?" Meya faru a cikin gidan gonar?" Sunkuyar da kai Safwan yayi cike da ladabi yashiga bawa sarki labarin shad'in da akayi da yanda sauban ya kamu da son yarinyar bai san yanayi ba." Sautin kukan Saudat sukaji wacce tafita a d'akin da gudu saboda bakin cikin abinda Safwan yake fad'a." Sosai maimartaba ya tausayawa sauban domin yasan zafin dafin so tin a kan mahaifiyarsa Bintu, Yasan yanda so yake illahta zuciya da gaggar jiki gaba d'aya, so yakansa mutum ya makance ya daina ganin kowa sai abinda yakeso So ya kansa mutum ya haukace ya zama tamkar marar, hankali ya dinga sabbatu a duk inda ya tsinci kansa, masoyi zai iya sadaukar da rayuwarsa da,farin cikinsa da lafiyarsa a kan masoyinsa, Wanda shine sauban yayi ya sadaukar da gaggar jikinsa,da lafiyarsa domin ganin ya ceto masoyiyarsa daga halaka." girgiza kai maimartaba yayi yana murmushi domin shi sam baiga laifin sauban ba, idan akace bintu zata dawo duniya zaiyi abinda yafi hakan akanta." Ran Hajjah ya b'aci matuk'a musamman da ganin Saudat tafita tana kuka, Tace "wnn ai sakarci ne, ta yaya zai kara jikinsa a dinga zuga masa bulala har hakan a kan macce wace irin macce ce wnn wace tafi sauran matan duniya, Na rantse da Allah da Nasan wnn sakarcin zaitafi yayi da bazan barshi ya tafi gidan gonar ba." Murmushi maimartaba yayi yace kiyi hakuri Hajjah jarumin namiji shike nuna bajintarsa akan abinda yakeso, sauban yayi matukar k'ok'ari wurin karawa da fulanin daji a wurin shad'i, wnn ya nunamun cewa Sauban jarumine ko a fagen yak'i zai iya fafatawa da mak'iya ." Hajjah ta wurgawa sarki harara cike da jin haushi tace "ai dama duk abinda sauban yakeyi kai kake d'aure masa, Har yaje ya kashe kansa da kansa a kan macce." Cikin fushi hajjah tabar d'akin saboda takaici tanufi wurin Saudat domin ta lallasheta, Wayam tagani ba Saudat ba fadawanta ba alamarta, Alamar tayi zuciya kenan tabar asibityn." ******************** Sai wurin k'arfe goma na dare dakaru suka Dura k'auyen su safna, Rarraba k'afa sukayi gaba d'aya suka zagaye k'auyen, Fetur suka fito dashi da ashana karon farko suka shiga kunnawa runbun hatsin da duk sukaci karo dashi, Anan take garin ya d'auki hasken wuta, tanaci bal bal, Tin shigowarsu hankalin mutanen k'auyen ya tashi domin yanda sukaji shigowar motocin suka tabbatarwa da kansu ba lafiya, duk Wanda yake bacci aka tayar dashi yara k'anana iyayensu suka goyasu a bayansu sukayi tsaitsaye suna jiran mutuwa ko rayuwa." Hakan gidansu safna Wanda yake zagaye da dakaru, Idon safna biyu domin batayi bacci ba gabanta kawai takeji yana fad'uwa yarima take gani yana mata gizo a idonta, anan take ta tabbatarwa da kanta yana cikin mawuyacin hali." Sautin maganar mutane taji a bayan d'akinta suna fad'in mu cinawa gidan wuta kawai kowa ya k'one, Wani Mai kakkausar murya yace "gimbiya Saudat tace "na haye yarinyar na moreta son raina, snn daga k'arshe mukasheta." Idonta ya cika da hawayen tausayin kanta domin, ta tab'ajin sunan matar yarima Saudat a bakin Safwan, Wani lokacin suna tare da yarima safwan yakira wayar sa, Yake shaida masa da cewa ya ina ne, GIMBIYA SAUDAT takira wayarsa tace tajita a kashe, tace ya kirata tanason zatayi magana dashi, A lokacin dogon tsaki taga sauban yaja bai bawa Safwan amsaba illah ya kashe wayar gaba d'aya ya ajiye, anan ta fahimci matarsa ake nufi Cikin ranta tashiga fad'in Ashe sunanta Saudat, tin daga lokacin sunan Saudat ya tsaya mata a rai, Duk lokacin da taji an anbaci sunanta takanji gabanta ya fad'i ta rasa dalili hakan da takeji, hannu tasaka tashare wayen fuskarta ta mik'e tsaye, tanufi k'ofar fita, Tana fad'in wato itace ta turo a kasheni kenan burinta ayi mun illah a rayuwa mai natare mata?" Hasalima bata sanniba ban santaba." Tanajin muryar su a waje suna shawar yanda zasu shigo cikin gidan, Cikin sand'a tabud'e k'ofar d'akin tafita tanufi d'akin baba Wanda suke tare da inna idonsu biyu sunajin duk abinda ake fad'a a waje ko wanne sai zarar ido yakeyi cike da tsoro, Ganinta da sukayi Baba ya taso ya rungumeta yasaki kuka itama safna kuka takeyi domin sun rigada sun sadakar lokacin mutuwarsu ne yazo, Inna sai fad'I takeyi muna zaman zamanmu lafiya muka d'aukarwa kanmu bala'i da masifa Safna ke annoba ce a rayuwarmu." Jin anfara durowa cikin gidan, yasaka inna yin shuru, bakinta kawai ke rawa." Hannu Baba safna ta Rik'e cike da zafin rai tace "baba mugudu bana son rabuwa da Kai." Girgiza kai Baba yayi yace "Safna ta ina zamu gudu bayan gasu nan suna shigowa cikin gidan da Zarar munfita kashemu zasuyi." Safna tace "baba idan bamu fita a gidan nan ba cinnawa gidan wuta zasuyi duk muk'une a cikinsa, Baba zaiyi magana wani k'arfi yazowa Safna ta fisgo hannun Baba suka bud'e k'ofa suka fito inna tana biye dasu a baya, K'atti majiya k'arfi hud'u suka gani a cikin gidan sun juya baya sunajiran shigowar Sauran, Cikin sand'a safna take Rik'e da hannun Baba sukabi ta bayansu suka nufi k'ofar baya sukafita, Wani irin ihu inna tasaki a lokacin da ta taka k'usa a k'afa, Wanda ya hankaltar da dakarun inda suke." Suka nufo wurin inna tana kwance rik'e da k'afa, Safna tana rik'e da hannun Baba sai gudu suke shek'awa." Ai kuwa dakarun sukace gata can ta gudu, Suka dafawa safna, Gudu kawai sukeyi dakaru suna biye dasu a baya da makamai a hannu, Baba ya fisge hannunsa daga na Safna sakamakon gajiyar da yayi da gudu ji yakeyi kamar numfashinsa zai d'auke, Ya kalli safna hawaye suna zuba a idonsa yace "safna kiyi tafiyarki Allah zai taimakeki zai tsiratar dake a duk inda kika tsinci rayuwarki, kibarni su kasheni domin baxan iya kub'utar DA kaina daga garesuba, bazan iya aikata komai ba, Allah yayi maki Albarka, Ki mik'e kada ki karya kwana a kan hanya kike, zatayi magana kenan ta hango dakaru sun kusan zuwa wurinsu, a lokacin Baba ya zube ya d'auke numfashi, tanaji tana gani tabar Baba a wurin ta keci daji da gudu, Gudu takeyi suna biye da ita a baya jefa k'afa kawai takeyi a cikin daji batasan inda takeba ga duhun daji." *Wayyo safna*😭😤 *Mrs Ana's Bawa*✍ [9/9, 7:43 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 28* ****** " Gudu take shek'awa Idon rufe jefa k'afa kawai takeyi a duk inda tasamu hanya, Wanda takejin zugin zafi k'afarta kasancewar ba talkami a tare da ita, Wani irin k'aton macije tagani ya tashi tsaye a gabanta Wanda girmansa baya misaltuwa, Wani irin ihu tasaki ta zube wurin a some." Sautin ihunta yayi dai dai da farkawar Sauban a kan gadon Asibity, babu abinda yakeji a kunnensa sai sautin kukan safna tare da ihunta da ya farkar dashi." Waige waige yakeyi akan gadon asibityn domin yakasa barin jin sautin a kunnensa, Hajjah ta taso tanufoshi tana fad'in "Sauban ka farka me kakeso?" Girgiza Kai yayi alamar baya son komai, ya lumshe idonsa hawaye suna zuba a gefen idonsa." Kallonsa takeyi cike da mamakin ganin hawaye suna zuba a idonsa, yaushe rabon da taga hawayen sauban tin yana k'arami, KO a lokacin ba komai yake sakashi zubar da hawayeba, Sai gashi yanzun da girmansa yana zubar da hawaye." Matsawa ta kumayi a gefen gadonsa tana share masa hawaye tana fad'in "magaji meyake damunka?" Me kakeso?" Kukan me kakeyi?" Girgiza mata kai yayi alamar ba komai hawaye sukaci gaba da zuba a idonsa." Babu Neman da dakaru basuwa safna ba a cikin dajin amma basu ganta ba wata alamarta." ai kuwa Sai k'ara kutsa Kai sukeyi cikin dajin, da manyan fito masu hasken gaske a hannunsu, D'aya daga cikinsu yaji wani abin ya sareshi a k'afa, wani irin Ashar yasaki ya juya domin ganin Ko meye wani irin k'aton maciji yagani ya nad'e wuri d'aya, ya kuma kai masa Sara a cinya, Ihu yasaki ya d'aga murya yana fad'in ku gudu kada ku karaso maciji, ai kuwa anan take kumfa yashiga zuba a bakinsa ya fad'i wurin a macce, Sauran dakarun sunajin hakan suka juya a guje, macijin yabi bayansu shima suna gudu yana gudu yana biye dasu a baya yana masu rakiya sai da yayi nasarar kashe mutum biyu a cikinsu snn saura suka tsira." Koda suka shiga cikin k'auyen suka shiga cinawa gidaje wuta k'urumus suka k'one gidansu safna tare da makotansu snn suka shiga mota sukabar k'auyen cike da bakin cikin mutuwar yan uwansu." Mutan gari sunajin tafiyar tasu suka firfito suna kuka domin ba k'aramar b'arna akayi masu ba, Ank'ona masu rumbun abinci ankashe masu shanu wasu sun rasa rayukansu me sukayi masu? Suwaye suka aikata masu hakan?" Daren ranar gaba d'aya garin basuyi bacci ba, babban tashin hankalinsu gidajen da aka k'ona daga ciki har da gidansu Safna Wanda a yanzun ya zama fili, Kuka suka fashe dashi domin sunada ya k'inin har mutanen dake cikin gidan an k'onasu sun mutu." Yanda sukaga dare hakan sukaga safiya, Koda safiya ta waye duka garin ya cika da jama'a ana masu jaje tare da amsar gaisuwa, Acan bayan gari aka hango inna tafe tana jan k'afa fuskarta duk tab'aci da jini ba hijabi bare d'an gwali akanta, Ai kuwa da sauri aka nufota aka rik'ata aka zaunar da ita, Ruwa aka bata tasha jama'ar gari suna fad'in Alhmdulillahi Allah ya kub'utar DA lnno ta tsira, cikin muryar kuka tace "dukanmu mun tsira harda malam da Safna domin kuwa su guduwa sukayi, Ta kuma fashewa da Kuka tana fad'in Safna Annobace a garin nan ranka ya dad'e duk ita ta Janyo mana wnn bala'in." Maigari yace "subahanallahi Allah ya kyauta, ba Wanda ya janyo mana duk abinda yasamemu daga Allah ne bama d'orawa kowa laifi, Alhmdulillah tinda sun tsiratar da rayuwarsu Allah ya tsaresu a duk inda suke Mun san zasu dawo garemu komai daren dad'ewa." Anan sukaci gaba da amsar gaisuwar wad'anda suka mutu tare da jajen shanun da aka kashe." *************** Cikin wata bunka ta farka ta tsinci kanta a cikinta, gefenta akushine Wanda yake d'auke da waina da miya da manshanu, Wata mata tagani 'yar fillo irinta sanye da kayan fulani irin nata zaune a gefenta Tana kallonta tana murmushi, a k'allah matar zatayi shekara 40." Murmushi safna tasakarwa matar tare da k'ara waigawa domin ganin inda take, Matar tace "sannu Safna har kin farka." Zaro ido safna tayi tana mamakin a Ina take? Wacece wnn?" Ya akayi tasan sunanta?" Anan take komai yadawo mata sabo cikin razana ta motsa tana neman ta firgita, tare da kallon hannunta tana fad'in macijin ya sareni ko?" Murmushi matar tasaki tace "bai sarekiba ki kwantar da hankali, Ta mik'a mata Akushin dake d'auke da waina tace 'ga abinci kici." K'amshin abincin ya daki hancin safna a nan take cikinta ya k'ulle akan yunwa ta tina da rabon ta da abinci har ta manta, ta karbi abincin ta Faraci, citakeyi tana lumshe ido domin ba kad'an takejin dadin abincin ba, Sai da ta cinye wainar gaba d'aya snn tasha ruwan pure water dake ajiye a gabanta, Murmushin matar takeyi tana kallon safna cike da tausayi, Itama safna kallon matar takeyi, tana tinanin a ina tasan wnn fuskar tabbas ko a inane tab'a ganin wnn matar kuma tasanta sosai." A mafarki wata zuciyar ta fad'a Mata, Tabbas a mafarki kika santa anan kike ganinta, da zarar kinshiga damuwa ita ke zuwa tana lallashinki tare da kwantar maki da hankali." D'aga kai tayi ta kuma kallon matar wacce take sakar mata murmushi tace "Safna kin tinani?" Kin tina inda Kika sanni?" hawaye suka soma gangarowa safna ta taso tazo gabanta ta durkusa tace "Inna bazan tab'a mantakiba domin kina taimakona a duk lokacin da nafad'a cikin k'unci da damuwa, Ke wacece?" Murmushi matar tayi ta dafa kan Safna tace "zakisan KO ni wacece idan lokacin sanin yayi, kafin nan kitashi kitafi domin akwai sauran k'alubale a rayuwarki, Ta nuna Mata wata hanya tace "kibi nan kiyitafiyarki domin tsiratar da rayuwarki, Snn kiya wai ta Addu'a a a duk halin da kika tsinci kanki a cikinsa sai wata Rana." Share hawayen fuskarta safna tayi, tayi matar godiya, Matar ta bata silifas tasaka Wanda tanemi zugin zafin da takeji a k'afarta ta rasa, Snn ta nufi hanyar da aka nuna Mata tafara tafiya." Tafiya takeyi sosai tanayi tana hutawa saboda gajiya har yamma ta Mata a kan hanya, Hakan take tafiya cikin daji, batare da wani tsoro ko fargaba a tare da itaba, Kwatsam ta ganta a tsakiyar hanya akan wani babban titi wanda motoci suke wucewa da k'arfi ba batare da sun tsayaba, Wani Mai sayar da abinci ta hanga a can tsallaken titi taji cikinta yayi kuka alamar yunwa takeji ga kuma kishirwa, Hawaye ta share a idonta tana "fad'in Allah Sarki Baba Allah ya jik'anka ya gafarta maka. Ta mik'e tsaye tanufi wurin Mai sayar da abincin, Tanaso ta k'etara titi tsoro takeji saboda yanda taga motoci suna wucewa da gudu, sai tazo ketarawa sai kuma ta dawo baya tana sharar hawaye, A can tajiyo jiniya tajuya ta hango motocine tafe wad'an da basa da iyaka, cikin zafin nama ta nufi kan titin da gudu tana fad'in kafin ku k'araso na k'etara, Ai kuwa sai dai taji a d'auketa da mota ta fad'i a tsakiyar titi jini yana fita a hancinta da bakinta." Da sauri motocin suka taka burki suka tsaya, Wata kyakkyawar macce wacce hutu ya zauna a jikinta 'yar birni 'yar gayu tana sanye da glass a fuskarta sai k'amshi take zubawa wacce shekarunta bazasu wuce 37 ba, tabud'e mota tafito ranta a b'ace take kallon direbanta tana "fad'in yahuza baka ganine ko idonka a makance yake kadiba kagani aikin da akayi d'an Adam ba dabba bane." A nan take Tabawa escort d'inta masu take mata,baya umurni tace "ku dauketa kusakata a mota mutafi asibity da ita." Cikin sauri aka tallabi safna aka sakata a mota suka d'auki hanyar babbar asibity dake zaman kanta a cikin garin Adamawa." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 29* ******* A lokacin da aka nufi asibity da Safna ba rai bare numfashi a tare da ita, Kai tsaye Emergency aka nufa da ita cikin gaggawa likitoci suka k'arb'eta suka duk'ufa a kanta domin ceto rayuwarta da tsayar da jinin dake fita a hanci da bakinta." Sosai hajiya LAILA ta girgiza da ganin yanayin da yarinyar tashiga, danko fuskarta bata tsaya ganiba hankalinta a tashe yake matuk'a." Hajiya laila mace ce mai mai tausayi mai son 'ya'ya, haihuwarta d'aya a duniya 'yarta d'aya macce mai suna *SUHAILAT* wacce ta b'ata tin lokacin da ta haifeta bikin sunanta kawai akayi washe gari aka wayi gari babu ta ba alamarta tab'ata." B'acewar da har yanzun ba labarinta bare a san dalilin b'atan nata, wacce a kullum hajiya laila take kukan rashin 'yarta kwaya d'aya tilo wacce take tunanin itace kwanta a duniya, tun daga gareta KO b'atan wata bata kumayi ba, amma sai dai tanaji a jikinta Suhailat d'inta bata mutuba, tana raye domin tana yawan mafarkin 'yarta ta girma tana cikin mawuyacin hali." A kullum Addu'a takeyi Allah ya bayyanar mata da tilon yarta cikin k'oshin lafiya" Cire glass din idonta tayi ta share hawayen dake zuba a idonta, snn ta mayar da glass din a fuskarta, takoma cikin mota ta zauna tare da jinginawa akan kujera, Wayarta ta d'auka kira mijinta Alhaji *HABIB SANI NAIRA*, *RINGING* d'aya zuwa biyu Alhaji Habib ya d'auka, a lokacin yana office suna mitting tare da yaransa akan cigaban da aka samu a kanfaninsa, Yana ganin kiran nata Saida yasaki murmushi ya kalli wayar, Snn ya tsayar da maganar da yakeyi, Snn Ya d'auki wayar , Cikin so da k'aunar matarsa, kuma Amaryarsa yake fad'in "Amarya bakya laifi koda kin kashe d'an masu gida, da fatan kin isa lafiya." Murmushi tasaki tana fad'in "Alhajina akwaika da tsokana shekara goma shatakwas kake kirana da Amarya, Da ace Suhailat tana raye aida munfara shiga sahun iyaye dan kuwa kasan kamar yanzun mun sami suriki." Murmushi yasaki domin shi kansa ta tayar masa da dafin b'atan 'yarsa wacce tafi soyuwa a ransa, Itama yanzon yasan tashiga cikin damuwar domin yasan da zarar akayi zancen suhailat sai ta zubar da hawayenta, Gyaran murya yayi yace "Amarya kamar yanda yake kiranta meyafaru dake ne?" domin najiya a jikina kina tare da matsala." Share hawayen dake zuba a idonta tayi, cikin da sanshinyar murya tace "Alhajina muna kan hanyar tafiya, munzo gaf da fita cikin gari muka samu matsala, Yahuza direba ya bige wata yarinya 'yar fulani tana sanye da kayan fulanin a jikinta , a lokacin tana k'ok'arin k'e tara titin, yanzun hakan muna Asibity." "Subahanallahi Alhaji Habib Naira yace, Tare da mik'ewa tsaye a firgice, yayiwa yaransa Alama da hannu akan sutafi sai ya k'ara nemansu, Cikin Sauri yanufi hanyar fita , Da waya a kunnensa yana fad'in wacce asibityn kuke a halin yanzun?" Hajiya laila ta fad'a masa sunan asibityn." OK gani nan zuwa yace "yanufi wurin motarsa escort dinsa suka bud'e masa yashiga, Suma suka shinshiga cikin nasu motocin suka nufi Asibityn." *************** Kwance yake akan gadon Asibityn Sauk'i yasamu garesa Dan kuwa ba abinda yakeji yana masa ciwo a jikinsa, Likita kawai yake jira yashigo ya sallame shi, Gabansa yakeji yana fad'uwa akai akai, Da zarar yaji hakan ba wacce take fad'o masa a rai sai Safna, Tabbas yasan tana cikin mawuyacin hali, Musamman rashin ganinsa da batayi ba, bataga yatura wurin maigariba domin a tsayar da ranar aurensu, dolene tashiga cikin damuwa." Runtse idonsa yayi yanajin wani abin yana bugar masa zuciya wanda yarasa ko meye shi, Babu abinda yake gani sai Fuskar safna yake kallo a idonsa, a lokacin da take ce masa , "Yarima inasonka zanyi biyayya a gareka, zan zama tamkar baiwa a gareka, Kada kajuyamun baya idan katina DA ni shigeyace bana da iyaye." Hawaye suka shiga zuba a gefen idonsa,jikinsa yasoma rawa, ji yakeyi kamar ya tashi ya tafi k'auyen a d'aura masu aure da ita ya d'aukota ya taho da ita domin yabata gata tabbatar da cewa *MARAYU MA 'YA'YA* ne kamar kowa., Hajjah tana ganin zubar hawayensa wanda har tagaji da ganin suna fita a idonsa, tin Tana Tausayinsa tana tambayarsa damuwarsa har ya Kai ta zuba masa ido tana kallonsa, Dan tasan halin sauban sarai akwaishi da zurfin ciki, idan zai shekara dubu da abu a ransa yana damunsa baxai tab'a furtawa ba, hakan zai barshi a ransa yayita damunsa, yana ramewa sai dai idan kai ka fahimta da kanka snn ka magance masa matsalar cikin salama." Hakan yayi a lokacin Auren Saudat bai furta baya sonta ba, Sai da akayi bikin yashiga cikin damuwa yana ramewa, Tambayar duniya ba wacce ba'ayi masaba akan ramar da yakeyi kodai auren da akayi masa ne baya so, Hakan zai girgiza kai alamar yanaso shi ba abinda yake damunsa, Sai daga baya da hajjah ta saka masa ido anan ta fahimci baya son Saudat shine dalilin ramar tasa, Hakan tayita kwantar masa da hankali akan ya rik'e matarsa hannu biyu tinda anriga da and'aura auren har ankawota gidansa, Dole ne Ya koyawa zuciyarsa soyayyarta illaso daga baya idan yasami wacce yakeso sai ya aure ta." sai gashi shigowar Saudat gidan lokaci d'aya tashiga ran hajjah saboda tsananin son da takeyiwa sauban wanda bata iya b'oyeshi a duk inda take ko a gaban waye, Snn shigowar saudat cikin gidan lokacin sauban yasami kwanciyar hankali da zama a lafiya a cikin masarautar dan kuwa gimbiya jamila tsoron mahaifiyar saudat takeyi." Maimartaba ya turo k'ofa yashigo da sallama, Ganin hawaye suna zuba a idon yarima ya dakatar da fadawa akan kada sushigo su dakata waje ya mayar da k'ofa ya rufe." Cikin takon mulki yake takowa ya isa gaban gadon sauban ya sanya hannu ya dangwalo hawayen dake fita a gefen idonsa, ya dubesu da kyau cike da mamaki ya tabbatar da tabbas hawaye ne ke zuba a idon magajin sarki, Cikin gid'ima sarki yake kallonsa bakinsa yana rawa yace "magajin Sarki hawaye a idonka?" Ina raye a duniya?" Meyafaru?" Ina yake maka ciwo?" Sam ba girma bane hawaye su dinga fita a idon gwarzon namiji kuma magajin Sarki, tashi zaune muyi magana." Jiki a sanyaye sauban ya tashi zaune yana kallon mahaifin nasa, Hannu Sarki yasaka ya shafe masa hawayen fuskar tasa, Yana kallonsa yace "bani labarin abinda yake damunka Wanda inada raina da lafiyata magajina yake zubar da hawayena akansa." Kallon mahaifinsa sauban yayi ya sunkuyar da kai yace "Abba damuwata safna ce." Sarki yasaki wani murmushin irin nasu na manya, Hajjah taja dogon tsaki ta juyar da kai gefe, domin ita wlh ta d'auka wani abin can daban yake damunsa ko yake masa ciwo wanda yake sakashi yana zubar da hawaye. Ita tarasa ko yaushe sauban ya susuce yazama raggo hakan DA. har yake zubar da hawayensa Mai tsada a kan macce." Sarki ya juya ya kalli hajjah yasaki murmushi snn ya nemi wuri ya zauna a gefen gado a kusa da sauban ya kallesa yana murmushi yace "fad'amun meyasami safna d'in?" Kallonsa sauban yayi ya sunkuyar da Kai k'asa yace "inaji a jikina akwai wani mummunan abu da yasameta, Abba Safna abar tausayice bata da iyaye bata da kowa sai Allah saini dana d'auki Alk'awari Zan taimaketa, Abba bawai son safna nakeyiba kawai ina tausayin halin da take cikine, DA kuma Wanda zata shiga idan tarasani," Abba Ina neman Alfarma a Karo na farko a wurinka itace katura fadawa yanzun nan sutafi k'auyen domin a tsayar da ranar aure na da Safna, domin gudun kada asami Matsala a cikin Al'adarsu." Murmushi Sarki yasaki Wanda har sai da hakoransa suka fito, Yana kallon sauban cike da wauta wai ba sonta yakeyi ba, bayan ga soyayyarta nan ya gani k'arara a cikin idonsa, Murmushi Sarki ya kuma saki yana kallon sauban Yace "hakan kakeso a aiwatar yanzun magajin sarki?" D'aga kai sauban yayi alamar eh." Sarki yace to "idan maigari yace a lokacin yake so d'aura auren naku a tsaya a amso maka aurenta ko kuwa abarshi rana kawai kakeso asaka maka?" Shuru sauban yayi ba amsa. Sarki yasaki dariya wacce yasaka sauban shima ya d'an murmusa cike dajin kunya, Sarki yace kabani amsa kai nake saurare domin da kaina zantafi ba aikeba " Cikin jin kunya sauban ya sunkuyar da kai yace "duk yanda kace ranka ya dade a aiwatar da hakan." Sarki ya kuma sakin dariya yace "wnn amsar kai zaka bani ita, Saboda a lokacin da kake zubar da hawayen k'auna baka nemi shawara daniba." Cike da jin kunya sauban ya kuma sunkuyar da kai sarki yana ganin hkn ya had'e fuska cike da zulaya yace "to shikenan Zan fasa tafiyar zan tura fadawa Zan ce masu da zarar suntafi akace za'a d'aura aure a lokacin zance kabada umurnin "kada a d'aura kai baka ra'ayin hakan, rana kawai kakeso asaka maka, Idan sukace ba hakan sukeyiba, Zance kace kabarwa duk Wanda yake sonta a d'aura dashi." Da sauri sauban ya d'aga Kai ya kalli Sarki yaga da gaske yake ba wani alamar wasa a tare dashi yace "ranka ya dad'e ba hakan nake nufiba, a d'aura auren dani, sutaho tare da ita." Dariya ta sub'ucewa sarki wacce tasaka sauban jin kunya, Yayi saurin kwanciya tare da juya baya yana murmushi cike da jin kunya." Hajjah tana jin duk abinda sukeyi bata tanka masuba domin ta dade da sanin Sarkin Abdullah shi yake sakanta sauban yake yin duk abinda yaga dama." Sarki ya mik'e tsaye yana murmushi ya kalli hajjah yace "umma zamutafi karb'owa jikanki Aure a k'auyen gidan gonarsa, saiki shirya tarbon kishiya ta biyu." Mere baki hajjah tayi tace kafin a d'aura ayi binciken asalinta da abinda ya kashe iyayenta domin naji yana fad'in bata da iyaye, Snn a tabbatar da asalinsu mai kyau ne tafito a cikin gidan asali, da daraja basa da wani abin fad'a, kodan samun zuri'a mai tsafta, Snn kada ka manta a cikin gidan sarauta zata shigo shi kuma gidan sarauta duk Wanda kagansa yashigo cikinsa a matsin matar Sarki KO d'an Sarki KO jikan Sarki dolene ya zamana yana da asuli Mai kyau. Idan babu wnn to tabbas bata cancanta da zama matar saba dole ne ya barta duk son da yake mata." Gaban sauban ya fad'i dajin furuncin hajjah." Sarki yace "tabbas hakan ne umma, Sai dai inaji a jikina kamar farin cikin da mahaifiyarsa take fad'ar masa zai samu a cikin gidan gonar sa, Ina hasashen shine ya fara bayyana a garesa." Domin samun macce ta gari babban farin cikin d'a namiji, yasami rabin duniyarsa domin kullum cikin farin ciki zaiyi ta zama har k'arshen rayuwarsa Yanufi k'ofar fita yace "muntafi, Hajjah tace "adawo lafiya." Snn Sarki yafita ya bawa fadawa umurnin sushiga mota, ya fad'a masu inda za'a tafi, Suka d'auki hanyar k'auyen Lassa." Suna fita daga asibityn Anawa Sarki jiniya, Alhaji Habib Naira shima yashigo da tawagarsa sarki yabada umurni a tsaya, hakan shima Alhaji Habib yaba da umurni a tsaya, anan suka fito daga motar suna dariya suka shiga gaisawa da juma cike da farin ciki da kewar juna, Tare da tambayar yaushe rabo, Domin Alhaji Habib business dinsa baya barinsa zama yau yana wannan k'asa gobe yana wancan k'asa jibi yana wancan k'asa." Anan Alhaji Habib yake tambayar Yaya Sauban?" Ai yanzun Yasan yaron ya girma sosai." .dariya sarki yasaki yana fad'in sosai kuwa har yayi aure, Yanzun hakan k'arb'o masa auren mata ta biyu zamu tafi muyi." Kuma tab'awa sukayi suna dariya Alhaji Habib yace "yaro yayi gadon ajiye mata da yawa, kaine baya ko ni." Sarki yasaki dariya yana fad'in lafiyar kenan, ai duk Wanda ya ganmu yasan ba rangwanci a tare damu." Suna dariya tare da zolayar juna sukayi sallama ko wanne yashiga motarsa Alhaji Habib yana fad'in abokina kafin natafi zan shigo fada domin asakamun Albarka, Sarki yana dariya yace "badamuwa sai ka shigo, Sukaja mota suka tafi cike da farin cikin ganin juna domin abokanaine sosai kasuwanci ne yarabasu da junansu." Sarki yana fita daga asibityn likita yashigo ya k'ara duba jikin sauban yaga yasami lafiya, Anan take ya sallamesu direba tare da fadawa suka d'aukesu a mota suka nufi gida su." **************** Dawowar dakaru da labarin da sukaje dashi na tarwatsa k'auyen su safna ba k'aramun farin ciki yasaka Saudat da mahaifiyar taba, Musamman dasukaji cewar Safna ta mutu domin, Sunce dajin da tabi da gudu anan ne maciji ya kashe biyu daga cikin mutanensu, suma dakyar suka sha, Suna da yak'inin ko gaggar jikin safna baza'a gani bare gawarta shikenan ta mutu sai dai wata ba itaba" Wayyo dad'i a ranar Saudat kid'a tasaka a b'angarenta saboda farin ciki sai cashewa takeyi tana rawa, tana juyawa Yau duniya tamata dad'i, gaba d'aya ta manta da mijinta dake kwance akan gadon asibity." Har sauban yadawo gida batasaniba, Hakan ya nufi part d'insa ya shiga toilet yayi wanka yafito, yasaka k'ananun kayansa marasa nauyi farin wando riga bak'a, Yunwa yakeji amma babu abinci a b'angaren nasa, Hakan ya janyo 'ya'yan itatuwa ya soma ci, Ciyakeyi yana lumshe ido Babu abinda yake masa yawo a kai sai magagganun da hajjah tayi akan Safna, sune suke masa yawo sunaso su birgita masa, kwakwalwa, Wad'anda take cewa _dole ne a binciko asalinta atabbatar da suna da kyakkyawan asali basa da wani abi fad'i, domin duk wacce taza shigo gidan sarauta dolene sai in tana da cikakken asali mai kyau_ To yanzun idan sarki ya shiga bin ciken asalinta yasami cewar tsintar ta akayi a gefen hanya, ana nufin bata da asali shegiyace Shikenan." Rasa zaiyi bazai taimaki rayuwarta ba?" Runtse idonsa yayi yanajin zuciyarsa tana k'una, Jiyakeyi duk abinda zai faru sai dai yafaru amma bazai tab'a barin rayuwar safna ta sallawanta ba, akan wani dalili can nasu na masarauta." sautin kid'a yakeji yana tashi a part d'inta Wanda duk ya damesa ya hanashi sukuni bare yayi tunanin mafitar abinda yake damunsa, kwakwalwarsa da kansa duk sun har gitse, Cikin zafin rai yafita yanufi part dinta, Har ya tura k'ofa yashiga batasaniba abinda baitab'ayiba shiga d'akinta." Manyan mata yagani su hud'u kwance a kan gadonta KO wacce ba kayan kirki a jikinta, Tana tsaye a tsakiyar d'aki sai rawa takeyi tana juyawa, irin rawar da turawa sukeyi idan suna cikin farin ciki." Wani bak'in ciki ya kamasa ya kashe soket d'in, Jin shurun da tayi ba sauti t Yasa ta juya a fusace domin ganin Wanda ya kashe mata sauti." Ido biyu tayi dashi tsaye a bayanta, Anan take gabanta ya fad'i, Ta juya da sauri ta kalli matan da ta ajiye a kan gadonta." ajiyar zuciya ta sauke ganin ba abinda suke aikatawa a kwance kawai suke, Kallonta yakeyi cike da tsana da takaici da ace shi ma'abucin dukan macce ne da yau babu abinda zai gana ya daki saudat yayi mata duka irin na mutuwa." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 29* ******* A lokacin da aka nufi asibity da Safna ba rai bare numfashi a tare da ita, Kai tsaye Emergency aka nufa da ita cikin gaggawa likitoci suka k'arb'eta suka duk'ufa a kanta domin ceto rayuwarta da tsayar da jinin dake fita a hanci da bakinta." Sosai hajiya LAILA ta girgiza da ganin yanayin da yarinyar tashiga, danko fuskarta bata tsaya ganiba hankalinta a tashe yake matuk'a." Hajiya laila mace ce mai mai tausayi mai son 'ya'ya, haihuwarta d'aya a duniya 'yarta d'aya macce mai suna *SUHAILAT* wacce ta b'ata tin lokacin da ta haifeta bikin sunanta kawai akayi washe gari aka wayi gari babu ta ba alamarta tab'ata." B'acewar da har yanzun ba labarinta bare a san dalilin b'atan nata, wacce a kullum hajiya laila take kukan rashin 'yarta kwaya d'aya tilo wacce take tunanin itace kwanta a duniya, tun daga gareta KO b'atan wata bata kumayi ba, amma sai dai tanaji a jikinta Suhailat d'inta bata mutuba, tana raye domin tana yawan mafarkin 'yarta ta girma tana cikin mawuyacin hali." A kullum Addu'a takeyi Allah ya bayyanar mata da tilon yarta cikin k'oshin lafiya" Cire glass din idonta tayi ta share hawayen dake zuba a idonta, snn ta mayar da glass din a fuskarta, takoma cikin mota ta zauna tare da jinginawa akan kujera, Wayarta ta d'auka kira mijinta Alhaji *HABIB SANI NAIRA*, *RINGING* d'aya zuwa biyu Alhaji Habib ya d'auka, a lokacin yana office suna mitting tare da yaransa akan cigaban da aka samu a kanfaninsa, Yana ganin kiran nata Saida yasaki murmushi ya kalli wayar, Snn ya tsayar da maganar da yakeyi, Snn Ya d'auki wayar , Cikin so da k'aunar matarsa, kuma Amaryarsa yake fad'in "Amarya bakya laifi koda kin kashe d'an masu gida, da fatan kin isa lafiya." Murmushi tasaki tana fad'in "Alhajina akwaika da tsokana shekara goma shatakwas kake kirana da Amarya, Da ace Suhailat tana raye aida munfara shiga sahun iyaye dan kuwa kasan kamar yanzun mun sami suriki." Murmushi yasaki domin shi kansa ta tayar masa da dafin b'atan 'yarsa wacce tafi soyuwa a ransa, Itama yanzon yasan tashiga cikin damuwar domin yasan da zarar akayi zancen suhailat sai ta zubar da hawayenta, Gyaran murya yayi yace "Amarya kamar yanda yake kiranta meyafaru dake ne?" domin najiya a jikina kina tare da matsala." Share hawayen dake zuba a idonta tayi, cikin da sanshinyar murya tace "Alhajina muna kan hanyar tafiya, munzo gaf da fita cikin gari muka samu matsala, Yahuza direba ya bige wata yarinya 'yar fulani tana sanye da kayan fulanin a jikinta , a lokacin tana k'ok'arin k'e tara titin, yanzun hakan muna Asibity." "Subahanallahi Alhaji Habib Naira yace, Tare da mik'ewa tsaye a firgice, yayiwa yaransa Alama da hannu akan sutafi sai ya k'ara nemansu, Cikin Sauri yanufi hanyar fita , Da waya a kunnensa yana fad'in wacce asibityn kuke a halin yanzun?" Hajiya laila ta fad'a masa sunan asibityn." OK gani nan zuwa yace "yanufi wurin motarsa escort dinsa suka bud'e masa yashiga, Suma suka shinshiga cikin nasu motocin suka nufi Asibityn." *************** Kwance yake akan gadon Asibityn Sauk'i yasamu garesa Dan kuwa ba abinda yakeji yana masa ciwo a jikinsa, Likita kawai yake jira yashigo ya sallame shi, Gabansa yakeji yana fad'uwa akai akai, Da zarar yaji hakan ba wacce take fad'o masa a rai sai Safna, Tabbas yasan tana cikin mawuyacin hali, Musamman rashin ganinsa da batayi ba, bataga yatura wurin maigariba domin a tsayar da ranar aurensu, dolene tashiga cikin damuwa." Runtse idonsa yayi yanajin wani abin yana bugar masa zuciya wanda yarasa ko meye shi, Babu abinda yake gani sai Fuskar safna yake kallo a idonsa, a lokacin da take ce masa , "Yarima inasonka zanyi biyayya a gareka, zan zama tamkar baiwa a gareka, Kada kajuyamun baya idan katina DA ni shigeyace bana da iyaye." Hawaye suka shiga zuba a gefen idonsa,jikinsa yasoma rawa, ji yakeyi kamar ya tashi ya tafi k'auyen a d'aura masu aure da ita ya d'aukota ya taho da ita domin yabata gata tabbatar da cewa *MARAYU MA 'YA'YA* ne kamar kowa., Hajjah tana ganin zubar hawayensa wanda har tagaji da ganin suna fita a idonsa, tin Tana Tausayinsa tana tambayarsa damuwarsa har ya Kai ta zuba masa ido tana kallonsa, Dan tasan halin sauban sarai akwaishi da zurfin ciki, idan zai shekara dubu da abu a ransa yana damunsa baxai tab'a furtawa ba, hakan zai barshi a ransa yayita damunsa, yana ramewa sai dai idan kai ka fahimta da kanka snn ka magance masa matsalar cikin salama." Hakan yayi a lokacin Auren Saudat bai furta baya sonta ba, Sai da akayi bikin yashiga cikin damuwa yana ramewa, Tambayar duniya ba wacce ba'ayi masaba akan ramar da yakeyi kodai auren da akayi masa ne baya so, Hakan zai girgiza kai alamar yanaso shi ba abinda yake damunsa, Sai daga baya da hajjah ta saka masa ido anan ta fahimci baya son Saudat shine dalilin ramar tasa, Hakan tayita kwantar masa da hankali akan ya rik'e matarsa hannu biyu tinda anriga da and'aura auren har ankawota gidansa, Dole ne Ya koyawa zuciyarsa soyayyarta illaso daga baya idan yasami wacce yakeso sai ya aure ta." sai gashi shigowar Saudat gidan lokaci d'aya tashiga ran hajjah saboda tsananin son da takeyiwa sauban wanda bata iya b'oyeshi a duk inda take ko a gaban waye, Snn shigowar saudat cikin gidan lokacin sauban yasami kwanciyar hankali da zama a lafiya a cikin masarautar dan kuwa gimbiya jamila tsoron mahaifiyar saudat takeyi." Maimartaba ya turo k'ofa yashigo da sallama, Ganin hawaye suna zuba a idon yarima ya dakatar da fadawa akan kada sushigo su dakata waje ya mayar da k'ofa ya rufe." Cikin takon mulki yake takowa ya isa gaban gadon sauban ya sanya hannu ya dangwalo hawayen dake fita a gefen idonsa, ya dubesu da kyau cike da mamaki ya tabbatar da tabbas hawaye ne ke zuba a idon magajin sarki, Cikin gid'ima sarki yake kallonsa bakinsa yana rawa yace "magajin Sarki hawaye a idonka?" Ina raye a duniya?" Meyafaru?" Ina yake maka ciwo?" Sam ba girma bane hawaye su dinga fita a idon gwarzon namiji kuma magajin Sarki, tashi zaune muyi magana." Jiki a sanyaye sauban ya tashi zaune yana kallon mahaifin nasa, Hannu Sarki yasaka ya shafe masa hawayen fuskar tasa, Yana kallonsa yace "bani labarin abinda yake damunka Wanda inada raina da lafiyata magajina yake zubar da hawayena akansa." Kallon mahaifinsa sauban yayi ya sunkuyar da kai yace "Abba damuwata safna ce." Sarki yasaki wani murmushin irin nasu na manya, Hajjah taja dogon tsaki ta juyar da kai gefe, domin ita wlh ta d'auka wani abin can daban yake damunsa ko yake masa ciwo wanda yake sakashi yana zubar da hawaye. Ita tarasa ko yaushe sauban ya susuce yazama raggo hakan DA. har yake zubar da hawayensa Mai tsada a kan macce." Sarki ya juya ya kalli hajjah yasaki murmushi snn ya nemi wuri ya zauna a gefen gado a kusa da sauban ya kallesa yana murmushi yace "fad'amun meyasami safna d'in?" Kallonsa sauban yayi ya sunkuyar da Kai k'asa yace "inaji a jikina akwai wani mummunan abu da yasameta, Abba Safna abar tausayice bata da iyaye bata da kowa sai Allah saini dana d'auki Alk'awari Zan taimaketa, Abba bawai son safna nakeyiba kawai ina tausayin halin da take cikine, DA kuma Wanda zata shiga idan tarasani," Abba Ina neman Alfarma a Karo na farko a wurinka itace katura fadawa yanzun nan sutafi k'auyen domin a tsayar da ranar aure na da Safna, domin gudun kada asami Matsala a cikin Al'adarsu." Murmushi Sarki yasaki Wanda har sai da hakoransa suka fito, Yana kallon sauban cike da wauta wai ba sonta yakeyi ba, bayan ga soyayyarta nan ya gani k'arara a cikin idonsa, Murmushi Sarki ya kuma saki yana kallon sauban Yace "hakan kakeso a aiwatar yanzun magajin sarki?" D'aga kai sauban yayi alamar eh." Sarki yace to "idan maigari yace a lokacin yake so d'aura auren naku a tsaya a amso maka aurenta ko kuwa abarshi rana kawai kakeso asaka maka?" Shuru sauban yayi ba amsa. Sarki yasaki dariya wacce yasaka sauban shima ya d'an murmusa cike dajin kunya, Sarki yace kabani amsa kai nake saurare domin da kaina zantafi ba aikeba " Cikin jin kunya sauban ya sunkuyar da kai yace "duk yanda kace ranka ya dade a aiwatar da hakan." Sarki ya kuma sakin dariya yace "wnn amsar kai zaka bani ita, Saboda a lokacin da kake zubar da hawayen k'auna baka nemi shawara daniba." Cike da jin kunya sauban ya kuma sunkuyar da kai sarki yana ganin hkn ya had'e fuska cike da zulaya yace "to shikenan Zan fasa tafiyar zan tura fadawa Zan ce masu da zarar suntafi akace za'a d'aura aure a lokacin zance kabada umurnin "kada a d'aura kai baka ra'ayin hakan, rana kawai kakeso asaka maka, Idan sukace ba hakan sukeyiba, Zance kace kabarwa duk Wanda yake sonta a d'aura dashi." Da sauri sauban ya d'aga Kai ya kalli Sarki yaga da gaske yake ba wani alamar wasa a tare dashi yace "ranka ya dad'e ba hakan nake nufiba, a d'aura auren dani, sutaho tare da ita." Dariya ta sub'ucewa sarki wacce tasaka sauban jin kunya, Yayi saurin kwanciya tare da juya baya yana murmushi cike da jin kunya." Hajjah tana jin duk abinda sukeyi bata tanka masuba domin ta dade da sanin Sarkin Abdullah shi yake sakanta sauban yake yin duk abinda yaga dama." Sarki ya mik'e tsaye yana murmushi ya kalli hajjah yace "umma zamutafi karb'owa jikanki Aure a k'auyen gidan gonarsa, saiki shirya tarbon kishiya ta biyu." Mere baki hajjah tayi tace kafin a d'aura ayi binciken asalinta da abinda ya kashe iyayenta domin naji yana fad'in bata da iyaye, Snn a tabbatar da asalinsu mai kyau ne tafito a cikin gidan asali, da daraja basa da wani abin fad'a, kodan samun zuri'a mai tsafta, Snn kada ka manta a cikin gidan sarauta zata shigo shi kuma gidan sarauta duk Wanda kagansa yashigo cikinsa a matsin matar Sarki KO d'an Sarki KO jikan Sarki dolene ya zamana yana da asuli Mai kyau. Idan babu wnn to tabbas bata cancanta da zama matar saba dole ne ya barta duk son da yake mata." Gaban sauban ya fad'i dajin furuncin hajjah." Sarki yace "tabbas hakan ne umma, Sai dai inaji a jikina kamar farin cikin da mahaifiyarsa take fad'ar masa zai samu a cikin gidan gonar sa, Ina hasashen shine ya fara bayyana a garesa." Domin samun macce ta gari babban farin cikin d'a namiji, yasami rabin duniyarsa domin kullum cikin farin ciki zaiyi ta zama har k'arshen rayuwarsa Yanufi k'ofar fita yace "muntafi, Hajjah tace "adawo lafiya." Snn Sarki yafita ya bawa fadawa umurnin sushiga mota, ya fad'a masu inda za'a tafi, Suka d'auki hanyar k'auyen Lassa." Suna fita daga asibityn Anawa Sarki jiniya, Alhaji Habib Naira shima yashigo da tawagarsa sarki yabada umurni a tsaya, hakan shima Alhaji Habib yaba da umurni a tsaya, anan suka fito daga motar suna dariya suka shiga gaisawa da juma cike da farin ciki da kewar juna, Tare da tambayar yaushe rabo, Domin Alhaji Habib business dinsa baya barinsa zama yau yana wannan k'asa gobe yana wancan k'asa jibi yana wancan k'asa." Anan Alhaji Habib yake tambayar Yaya Sauban?" Ai yanzun Yasan yaron ya girma sosai." .dariya sarki yasaki yana fad'in sosai kuwa har yayi aure, Yanzun hakan k'arb'o masa auren mata ta biyu zamu tafi muyi." Kuma tab'awa sukayi suna dariya Alhaji Habib yace "yaro yayi gadon ajiye mata da yawa, kaine baya ko ni." Sarki yasaki dariya yana fad'in lafiyar kenan, ai duk Wanda ya ganmu yasan ba rangwanci a tare damu." Suna dariya tare da zolayar juna sukayi sallama ko wanne yashiga motarsa Alhaji Habib yana fad'in abokina kafin natafi zan shigo fada domin asakamun Albarka, Sarki yana dariya yace "badamuwa sai ka shigo, Sukaja mota suka tafi cike da farin cikin ganin juna domin abokanaine sosai kasuwanci ne yarabasu da junansu." Sarki yana fita daga asibityn likita yashigo ya k'ara duba jikin sauban yaga yasami lafiya, Anan take ya sallamesu direba tare da fadawa suka d'aukesu a mota suka nufi gida su." **************** Dawowar dakaru da labarin da sukaje dashi na tarwatsa k'auyen su safna ba k'aramun farin ciki yasaka Saudat da mahaifiyar taba, Musamman dasukaji cewar Safna ta mutu domin, Sunce dajin da tabi da gudu anan ne maciji ya kashe biyu daga cikin mutanensu, suma dakyar suka sha, Suna da yak'inin ko gaggar jikin safna baza'a gani bare gawarta shikenan ta mutu sai dai wata ba itaba" Wayyo dad'i a ranar Saudat kid'a tasaka a b'angarenta saboda farin ciki sai cashewa takeyi tana rawa, tana juyawa Yau duniya tamata dad'i, gaba d'aya ta manta da mijinta dake kwance akan gadon asibity." Har sauban yadawo gida batasaniba, Hakan ya nufi part d'insa ya shiga toilet yayi wanka yafito, yasaka k'ananun kayansa marasa nauyi farin wando riga bak'a, Yunwa yakeji amma babu abinci a b'angaren nasa, Hakan ya janyo 'ya'yan itatuwa ya soma ci, Ciyakeyi yana lumshe ido Babu abinda yake masa yawo a kai sai magagganun da hajjah tayi akan Safna, sune suke masa yawo sunaso su birgita masa, kwakwalwa, Wad'anda take cewa _dole ne a binciko asalinta atabbatar da suna da kyakkyawan asali basa da wani abi fad'i, domin duk wacce taza shigo gidan sarauta dolene sai in tana da cikakken asali mai kyau_ To yanzun idan sarki ya shiga bin ciken asalinta yasami cewar tsintar ta akayi a gefen hanya, ana nufin bata da asali shegiyace Shikenan." Rasa zaiyi bazai taimaki rayuwarta ba?" Runtse idonsa yayi yanajin zuciyarsa tana k'una, Jiyakeyi duk abinda zai faru sai dai yafaru amma bazai tab'a barin rayuwar safna ta sallawanta ba, akan wani dalili can nasu na masarauta." sautin kid'a yakeji yana tashi a part d'inta Wanda duk ya damesa ya hanashi sukuni bare yayi tunanin mafitar abinda yake damunsa, kwakwalwarsa da kansa duk sun har gitse, Cikin zafin rai yafita yanufi part dinta, Har ya tura k'ofa yashiga batasaniba abinda baitab'ayiba shiga d'akinta." Manyan mata yagani su hud'u kwance a kan gadonta KO wacce ba kayan kirki a jikinta, Tana tsaye a tsakiyar d'aki sai rawa takeyi tana juyawa, irin rawar da turawa sukeyi idan suna cikin farin ciki." Wani bak'in ciki ya kamasa ya kashe soket d'in, Jin shurun da tayi ba sauti t Yasa ta juya a fusace domin ganin Wanda ya kashe mata sauti." Ido biyu tayi dashi tsaye a bayanta, Anan take gabanta ya fad'i, Ta juya da sauri ta kalli matan da ta ajiye a kan gadonta." ajiyar zuciya ta sauke ganin ba abinda suke aikatawa a kwance kawai suke, Kallonta yakeyi cike da tsana da takaici da ace shi ma'abucin dukan macce ne da yau babu abinda zai gana ya daki saudat yayi mata duka irin na mutuwa." *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 30* *ALHAMDULILLAH ALLAH NAGODE MAKA DOMIN KAINE ABIN GODIYA,* *INA KUKE MASOYA DA ABOKANAN ARZIKI INA GODIYA A GAREKU DOMIN KUN NUNAMUN KULAWA BABU ABINDA ZANCE SAI DAI NAYI MAKU FATAN ALHERI A DUK INDA KUKE, DA MASU KIRAN WAYANA DA MASU TUROMUN MASSAGE DUKA NAGODE ALLAHU YA BAR K'AUNA NAJI SAUKI SOSAI ALLAH YABANI IKON FARANTA MAKU NAGODE NAGODE NAGODE*🤝🏻🤝🏻 ******* kallon tsana Sauban yaci gaba da wurgawa Saudat, cike da jin haushi da tak'aicinta, yaja dogon tsaki ya juya ya bar wurin yanufi d'akinsa, Kan gado ya kwanta rigingine ya rufe ido yana tunanin mugun hali irin na Saudat." Saudat kuma tana ganin ya yafita, A fusace ta juya ta kalli 'yan matan dake kwance a kan gadonta ta sakar masu harara cike da bak'in cikin ganin da mijinta yamasu a hakan, wani irin kishin mijinta taji ya taso mata, taja da baya ta jingina a bango tana sauke numfashi da sauri da sauri kamar wacce tayi gudu, hawayen bak'in ciki suka shiga kwarara a idonta, bakad'an taji zafin ganin da sauban ya masu cikin tsinanun kayan dake sanye a jikinsu ba, Bud'e idonta tayi wad'anda suka rine zuwa launin ja, ta d'orasu akansu, ta warga masu kallon tsana, A fusace ta daka masu tsawa tace "kutashi kufita na tsaneku, bana son nasake ganin fuskokinku, Kuma kusani sai kun d'and'ani azabata mai tsanani sakamakon ganin tsaraicin da mijina yayi maku Tin yanzun kuzab'awa kanku horo mafi tsanani kafin na zab'a maku da kaina." Gabanta suka kai durk'ushe tare da had'e hannayensu wuri d'aya alamar ban hak'uri, Suna fad'in ranki ya dad'e tuba mukeyi, Ki gafarcemu bazamu sake ba, bamusan yarima zai shigoba ayi hakuri ya uwargijiya mai Adalci, "Kufita nace tare da nuna masu k'ofa waje, Cikin sauri suka fita suka bar d'akin." Juyawa tayi tafita tanufi d'akin yarima, tura k'ofar d'akinsa tayi sannu a hankali da sallama a bakinta, Jin shuru ba'a amsa bata ba yasa taja ta tsaya tana kale kale a ina zata ganshi A can kan gado ta hangosa kwance yayi rigingine idonsa a rufe tamkar Wanda yakeyin bacci, Ajiyar zuciya ta sauke tashiga takawa sannu a hankali ta nufi wurinsa, A gefen gadon taja ta tsaya a dai dai saiti kansa ta d'an sunkuyar da kanta tana kallon kyakkyawan gashin kansa wanda yake kwance a kansa tamkar gashin kan jariri, Hakan ya kuma sanya fuskarsa tayi kyau da adon, sajensa Wanda yake zagaye da fuskarsa har zuwa bakinsa, tashiga kallo anan take tsikar jikinta ta tashi tafarajin wata irin matsananciyar sha'awarsa tana dirar Mata, Tana' tsananin son gashin bakinsa, tana son tayita kallon kyakyawar fuskarsa mai cike da Annuri, A hankali ta sanya hannu ta shiga shafa masa gashin bakinsa tana fad'in "Sadaukina kayi hakuri idan na b'ata maka rai." Idonsa ya bud'e ya d'orasu a kanta ya wurga mata wani irin kallon tsana snn ya mayar da idonsa ya rufe." Firgicewa tayi da kallon da ya Mata, Ta kuma narkewa tana basa hakuri, Shuru yayi bai tanka Mata ba, sai da tayi magiya ta gaji, ganin baya da niyar tanka mata yasa ta tashi nufi kicin domin shirya masa abinci wata k'ila yunwa yakeji, ko ganin hakan zai sanya zuciyarsa tayi sanyi." ****************** Alhaji Habib Naira yana shiga cikin Asibityn gaba d'aya idon mutane sukayo kansa, Anan take masu Neman taimako suka zagayeshi domin shi mutumin jama'a ne, mutum ne mai Alheri da tausayi Dan hakan da zarar jama'a sukayi ido biyu dashi to kukansu ya kare domin Alhaji Habib Naira zaiyi masu kyautar girma da ban mmki." Hakan aka zagayeshi sai kud'i yake bawa mabumuk'ata, da gajiyayyu, Da gyar escort nashi suka da katar da sauran jama'a snn yasami hanyar wucewa ya isa wurin matarsa Hajiya laila wacce take zaune a cikin mota tana kallonsa." Motar da take ciki escort nashi suka bud'e masa ya shiga, Idansa akanta yana sakar mata murmushin so da k'auna a duniya bayan iyayensa babu abinda yakeso da ganin farin cikinsa kamar hajiya laila, Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungumeta yashiga share mata hawayen dake zuba a idonta, cikin sigar lallashi yake kwantar mata da hankali akan ta d'auki kaddara akan duk abinda ya faru ta daina sanyawa ranta damuwar b'atan suhailat." Doguwar ajiyar zuciya Hajiya laila taja snn tasakarwa mijinta murmushi tare da rik'o hannunsa duka biyu ta saka a cikin nata hannun ta d'an matse kad'an cike da shauk'i tashiga fad'in na daina mijina ina Addu'a a koda yaushe Allah ya k'aramun dauriya da dangana a kan rashin tilon yata danayi." Dariya Alhaji yasaki yace "Ameen tare da kashe mata ido d'aya yana fad'in insha Allahu wnn dawowar danayi sainayi k'ok'ari nabaki wata Suhailat d'in kinga shikenan na kashe bakin magana." Dariya tasaki tana fad'in "kai Alhaji bakada dama mezan iya tsofai tsofai dani." Hararar wasa ya sakar mata yana fad'in "a Ina tsofan yake, a yanda nakejinki kinfi sabuwar budurwa dal a leda komai, Dan kuwa duk Wanda ya kalleki yasan nayi dace nayi sa'a a cikin maza samun kyakkyawar macce mai tsafta da iya ado uwa uba ga k'amshi, ni kuwa me zanyi da wata macce a duniya idan kina tare dani." Murmushin farin ciki take saki domin tana yawan jin wnn yabon a bakin gwarzon mijin nata, ."nagode mijina Allah yaci gaba da faranta maka kamar yanda kake farantamun." Ameen yace tare da cire hannunsa cikin nata yana fad'in "mutafi naga marar lafiyar Allah yasa ta farfad'o." Hakan suka bud'e k'ofa suka fita fuskokinsu cike da farin ciki escort suka take masu baya suka nufi d'akinda Safna take ciki a kwance cikin mawuyacin hali." Wurin gadonta suka nufa inda Alhaji Habib naira yana yin ido biyu da fuskarta sai da gabansa ya fad'i, yayi saurin k'arasawa wurin gadonta yana kallonta, Hajiya laila kuma ta juya tana bawa escort umurni akan su dakata a waje kafin sufito, Snn ta juya ta cewa Alhaji mutafi, ganin baya kusa da ita, yasa Cikin sauri d'aga kai ta hangosa a bakin gadon safna yana k'are mata kallo cike tausayi, Wurin ta nufa taja ta tsaya a kusa dashi tana fad'in Alhaji kaga yarinyar ko gwanin ban tausayi, Dam gabanta ya fad'i da tayi ido biyu da safna wacce a lokacin ta farfad'o daga allurar baccin da akayi mata." Cikin sauri hajiya Laila tanufi wurin safna tana kallonta ido ciki ido Wanda itama safna kallonta takeyi hawaye suna mata zuba a gefen idonta, Sannu yaya jikin naki Hajiya laila tace." D'aga Kai safna tayi alamar da sauk'i, Hawaye kawai kezuba a idonta ga wani irin fad'uwar gaba da takeji tarasa sanin kona meye." Suna tsaitsaye akan gadon safna ba Wanda ya kuma yin magana dukansu su uku gabansu sai fad'uwa yakeyi bakinsu ya rufe ba Wanda ya kuma furta kalma d'aya, Likita ya turo k'ofa yashigo tare da sallama." Gaida Alhaji yyi snn yanufi wurin safna, yacire mata ruwan da ya k'are ya kuma juna Mata masu, Ido kawai safna take bin koya dashi tana kallo hawaye suna Mata zuba, Gyaran murya likita yayi ya kalli hajiya yace "Alhmdulillah ba wata matsala a tare da ita, Duk iya gwaje gwajen da mukayi mungano buguwa ce kawai tayi a kanta Wanda insha Allah nan da kwana biyu zata sami lafiya." Alhaji yace Allah ya k'ara bata lafiya." Suka amsa da "Ameen." Muryar safna ta tsinke masu magana da take kallon Hajiya laila tace "umma zan sha ruwa, yunwa nakeji." Dam gaban Hajiya laila ya fad'i, dajin yarinyar takirata da suna umma sai taji sunan ya dace da ita, karon farko Taji wani girma ya darar mata taji k'aunar yarinyar ta shigeta a lokaci d'aya, idonta ya cika da hawaye tayi saurin sanya hannu ta share ta matsa a kusa da Safna ta d'ora Hannu a saman goshinta tana gyara Mata gashin kanta daya kusan lullub'e mata fuska tace "yata yunwa kikeji?" Safna ta d'aga Kai, alamar eh." Hajiya laila tasaki murmushi tace "kada kidamu yanzun za'a kawo mki abinci kinji." Safna ta d'aga kai alamar "to." Hajiya Laila ta janyo kujera ta zauna tana murmushi tana kallon fuskar safna, domin lokaci d'aya ta tsinci kanta cikin farin ciki da k'aunar wnn yarinyar sai takeji kamar 'yarta ce Suhailat ta dawo gareta." Alhaji Habib naira yana tsaye a kansu yana kallonsu cike da farin ciki Dan kuwa shima a lokaci d'aya soyayyar yarinyar tashiga ransa." Hajiya laila ta kamo hannun safna ta rik'e tace "meye sunanki 'yata." "d'an murmushi safna tasaki domin kalmar da hajiya laila takirata da ita ta 'yata tayi matukar yimata dad'i domin tinda tayi wayo ta girma idan aka cire Baba ba Wanda ya tab'a kiranta da wnn kalmar ta 'yata, azahiri wasu har kyamatarta sukeyi basa son tarab'esu, saboda tana shegiya bata da asali, Hawaye suka wanke mata fuska da ta tuno da Baba, Ta kalli hajiya cikin muryar kuka tace "sunana Safna." Hannu Hajiya laila tasaka tana share mata hawaye dake zuba a idonta tana fad'in daina kuka 'yata daga yau kukanki ya k'are, Wanne gari kike suwaye mahaifanki domin Zan tura a sanar dasu halin da kike ciki don gudun kada ayi ta nemanki." Bana da kowa ni kad'ai nake rayuwata, kowa kyamata yakeyi, mahaifina kuma ya rasu Ta fashe da kuka mai sauti gwanin ban tausayi." *MRS ANAS BAWA*✍ *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍ 🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴 Writing by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *Page 31* Runtse ido hajiya Laila tayi domin tanajin Sautin kukan Safna yana ratse KO wanne lungu da sak'o na jikinta, Hannunta tasaka tarik'o hannun safna cike da tausayi, ta tashi daga kan kujerar da take a zaune ta hau kan gadon da Safna take a kwance ta janyota zuwa jikinta ta tsura Mata ido sosai tana kallonta snn tayi k'arfin halin yin magana tace "daina kuka Safna, Allah ya jikan mahaifinki da rahama, Ki kwantar da hankalinki daga yau kukanki ya k'are bak'in cikinki ya k'are idan duk duniya kowa yana kyamarki mu bama kyamarki domin zamu taimakeki zamu taimaki rayuwarki." Girgiza kai likita yayi cike da tausayi, Wanda yake tsaye a wuri d'aya yana jin duk abinda yake faruwa, Hanyar fita yanufa yana mai tausayin rayuwar safna, yarinya k'arama mai k'ananun shekaru kyakkyawa amma bata da gata, tabbas rayuwarta abar tausayice ." Bayan fitar likita daga d'akin, direban Alhaji Habib ya turo k'ofa yashigo yana rik'e da ledodin abinci Wanda Alhaji yabashi umurnin ya sawo, A gaban Hajiya laila ya durkusa ya ajiye snn ya juya ya fita." Hajiya Laila ta tayar da Safna zaune cikin dabara da kwantar da hankali tashiga bata abinci da kanta tana kumajin k'aunarta da tausayinta suna ratsata, hakan shima Alhaji Habib shi yake tsiyaya mata ruwa a kofi yana bata tare da yimata nasiha akan ta d'auki kaddara a duk yanda tazo mata a matsayinta na musulma." ****************** A k'auyen lassa maigari da fadawansa tare da mutanen gari dake zaune suna zaman makoki akan yan uwansu da sukayi rashi, mutanen k'auyuka na kusa da garin sai ketarowa sukeyi suna masu jaje tare da gaisuwa, KO wanne yana zaune a fadar maigari maza da mata sai jimami akeyi, Suna hakan zazzaune jigum jigum sukajiyo jiniyi tare da manyan motoci suna shigowa cikin garin." hankalin kowa ya tafi zuwa wurin domin KO ba'a fad'a masuba tabbas sun tabbata wnn jiniyar da yawan motocin wnnan tafiyar Sarki ne da kansa ba yarima." A gaban fadar maigari sukayi parking din motocinsu a jere, inda maigari ya mik'e tsaye tare da mak'arabbansa suka nufi wurin motor Sarki domin tarbonsa, Manyan Fadawan sarki suna Rik'e da manyan buloli, suka zagaye motar Sarki KO wanne ya bud'e babban rigarsa suka kare bakin motar Sarki zaifito daga mota. Saida yafito aka kuma gyara masa rigarsa snn suka janye domin bawa Sarki hanya ya wuce." Taku yakeyi cike da k'asaita fadawa suna zuba masa kirari yanufi wurin maigari dake tsaye wuri d'aya tare da hakin mansa cike da farin ciki, Babbar kujera aka d'orawa sarki ya zauna, snn mutanen gari suka shiga kawo gaisuwa d'aya bayan d'aya, Sarki yana murmushi yana amsawa fadawa suma suna amsawa, yana k'arewa garin kallo da mutanen dake cikinsa ganin duk mutanen dake cikinsa a hargitse suke, Bayan an kammala gaisuwa, kowa ya nemi wuri ya zauna, ana zaman sauraren abinda sarki yazo dashi domin duk a tunaninsu jaje yataho yamasu." Gyaran murya sarki yayi yafara da cewa, "Alhmdulillah Ina matuk'ar godiya da wnn tarba da nasamu a gareku hakika na dade da sanin mutanen garin nan masu karamci ne da karrama bak'o, sai dai wannan zuwan da nayi na fahimci gaba d'aya a halin garin dama garin baki d'aya suna cikin damuwa da firgici meyake faruwa?" Kallon juna suka shigayi ganin a she Sarki baisan abinda yake faruwa ba, Cikin girmamawa maigari ya sunkuyar da Kai yashiga bawa Sarki labarin duk abinda ya faru ya rufe daga k'arshe ya rufe maganar da b'atan Safna wacce yarima yayi shad'i akanta, tare da mahaifinta har yanxun ba'a gansuba, ba'a sami labarinsu ba." wasu suna fad'in sun mutu, mafi inganci Labari Wanda mukaji a bakin matar mahaifinta gata can a zaune cewar guduwa sukayi basu mutuba." "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un sarki yake fad'i cike da jimami da tausayawa, Maigari ya kalli inno yace matso kiyi masa bayani yanda abin yafaru, tana rawar jiki ta matso ta Kai durk'ushe a gaban Sarki tare da sunkuyar da kai tana fad'in ranka ya dad'e ba mutuwa sukayiba guduwa sukayi, nima naso nabisu mugudu a tare, fad'uwa nayi sakamakon k'usa da nataka a k'afata, Ranka ya dad'e Allah kawai ya k'addari zan rayu da a kwai kwana na gaba, saboda a lokacin da nafad'i sai da wani k'aton garde yabi takaina ya wuce yana fad'in zamu dawo mu iyar da kaiki lahira, Inajin hakan na d'aga kaina naga sun dafawa su Malam da safna wad'anda suke rik'e da hannun juna suna gudu, Ina ganin g Hakan Nashiga jan ciki har nasamu nakawo kaina bayan gida a k'ark'ashin wani iccen mangwaro a nan na b'uya har suka dawo sunata nemana basu ganniba." Ta fashe da kuka tana fad'in ranka ya dad'e "Safna Annobace rayuwarmu tunda malam ya tsintota a kan hanya ya kawota cikin gidanmu muke had'uwa da bala'i iri iri, Allah kad'ai yasan irin zuri'ar su." Fadawa suka daka mata tsawa, ganin nan take fuskar Sarki ta canza alamar b'acin rai, suka shiga fad'in "gyara kalamanki sarki ya gaji da saurarenki kina iya tashi kitafi." Tana gogar hawaye hannunta d'aya rik'e da zanenta, tanufi wurin zamanta, Snn Sarki yayi gyaran murya ya kalli maigari yace "gaskiya ne abinda wnn matar tafad'a akan yarinyar da yarima yayi shad'i akanta?" "Gaskiya ne ranka ya dad'e bamusan asalinta ba a gefen gari malam Audu ya tsinto ta ya kawomun ita, daga k'arshe yanuna yanason ya taimaketa zai rik'eta domin bai tab'a haihuwa ba." Girgiza Kai Sarki yayi domin duk inda ransa yake ya b'aci, Wato Sauban yana nufin shegiya 'yar tsintowa zai aura ya shigo da ita cikin gidan sarauta mai cike da asali kyakkyawan tarihi, Murmushi Sarki yasaki ya danne b'acin ransa yace "hak'ik'a nayi bak'in ciki da tausayin abinda yasami ahalin garin nan Wanda har yayi sanadin mutuwar wasu rayunka daga cikinku, Kuyi hakuri Ku d'auki kaddara Zan taimakeku Zan tsaya tsayin daka domin ganin ko suwaye suka aikata maku hakan." Had'a baki sukayi suna godiya, Snn Sarki yabada 'umurni a bud'e but a d'auko kud'i abawa duk Wanda yake wurin dubu ashirin kafin yayo masu aike." Hakan aka shiga rabamasu kud'in suna godiya cike da farin ciki tare da yiwa Sarki fatan Alheri, Snn Sarki yamik'e yashiga mota fadawa suka maramasa baya yafita daga k'auyen KO gidan gona baiyi tunanin zaigashiba domin duk inda ransa yake a b'ace yake." ********************* Sauban kwance a cikin lambun dake part d'insa inda yake yawan zama yana shan iska, Safwan zaune a gefensa yana bashi labarin yanda ginin kamfaninsa ya wakana bayan kwanciyarsa a asibity, irin cigaban da aka samu, a kamfanin wurin ganin ginin ya fito yayi kyau, Kasan cewar Safwan yaci gaba da gudanar da komai har komai ya kammala a yanda yasan sauban yakeso." Fad'a masa yakeyi irin kud'in da aka zubawa wurin gaskiya maimartaba ya taka rawar gani domin ganin komai ya maka a yanda kakeso, Banza dashi sauban yayi sai dannar wayarsa yakeyi yana kuma kallon kan screen din wayar, Ba komai yake kalloba sai hotunan Safna wad'anda suka zamar masa madubin dubawarsa akoda yaushe." A zahirance Kuma duk abinda Safwan yake fad'i yana jinsa yana kuma saurarensa sosai yakejin dadin maganar da yake masa akan kamfaninsa Wanda shine cikar burinsa." Safwan baidamu da rashin kulawar da sauban baiyi masaba domin idan da sabo ya isa ace yasaba da wnn murd'and'en halin nasa, Wanda duk yanda kake dashi baka isa ka gane farin cikinsa ko Akasin hakan ba, Yaci gaba da cewa "a gaskiya Abba yana sonka duk a cikin 'yayansa ba wanda yake son yadinga ganin farin cikinsa kamarka, Shawarata anan abokina itace kaci gaba da yiwa Abba biyayya ka faran tamasa kamar yanda akoda yaushe yake k'ok'arin yaga ya faranta maka, Allah ya k'ara masa lafiya da nisan kwana." Sai a lokacin sauban ya d'aga Kai ya kalli Safwan yasakar masa murmushi yace "Ameen." Tare da d'aukar lemu dake cikin cup yakai bakinsa ya d'an kurb'a snn ya ajiye, Ya kalli Safwan yace "wani lokacin kana magana cikin natsuwa da hankali tare da fahimta, wani lokacin idan kayi wata maganar nakanji kamar na rufeka da duka." Dariya Safwan yasaki yana fad'in Allah yabaka hakuri Dan nasan ka kusan sanya fadawa su dakeni, Murmushi Kawai sauban yasaki, Safwan ya kallesa yace Abokina nafa manta ban fad'a makaba, Na kusan zama Daddy Dan kuwa Allah yayi najefa kwallo a cikin raga, Saura Kai, a gaskiya ya kamata kayi k'ok'ari daren yau kada kayi bacci har sai kasamu kajefa kwallonka a cikin raga." Had'e fuska sauban yayi ba alamar dariya a tare dashi yaci gaba da dannar wayar hannunsa, Jiniyar motocin sarki sukaji hakan ya tabbatarwa sauban Abba yadawo kenan." Shima Safwan yanajin hakan ya mik'e yace "Abokina nizan tafi domin kuwa kasan banason Ina Jan dogon shak'o bana kusa ga love d'ita bare Kasan yanzun laulayi mukeyi, Ya d'an sunkuya gefen kunnen sauban kamar zai fad'a masa wata magana Wacce bayason kowa yaji, cike da tsoKana yace "wai kasan wani abu kuwa gani nakeyi kamar 'yan uku ne na zuba Mata a mahaifa." Yana kaiwa nan yasaki dariya yayi tafiyarsa." Da kallo sauban ya bishi dashi har sai da ya daina ganinsa snn ya girgiza Kai ya mere baki, ya tashi yanufi part dinsa domin ya d'auro Arwalar sallar magariba yatafi masallaci, Domin yana son ganin maimartaba, yanason yaji halin da Safna take ciki, Murmushi yasaki wata zuciyar tace wata k'ila an d'auro Auren, Dam gabansa ya fad'i a lokacin da wnn tunanin ya fad'o masa rai." *pls kuk'ara hakuri dani wlh jikin ne nawa har yanzun sai a hankali pls kucigaba da tayani da Addu'a* Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Group Hausa novels and fashion Group Cool novel, makeup and kitchen1 Group And WOMEN24 TV Group WHATSAPP NO:+2349030159301