[10/16, 11:15 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* *No. 1⃣* "Bissmillahi Rahmani Rahim" Da sunan Allah mai rahama maijin kai... Mikewa tai azabure tare da kallan agoggon bango na dakin dasauri tamike ganin takusa makara, mamaki take yanda bacci yadauketa akan sallayar datai sallar asuba, kaya ta cire tai saurin fitowa tsakargida taja ruwa a rijiya tafada toilet, wankan minti 5 tai tafito tafada daki tazura doguwar riga baka tasa hijab fari tare da daukar nikaf dinta da jakar makarantarta, dama ita sam kwalliya bata dameta ba. Dakin ummanta tashiga azaune taganta tana ninke kaya tashiga da sallama tare da gaidata ta amsa cikin daure fuska Salmah kam tasaba da wannan hali na ummanta dan yanzu abin baya damunta, mikewa tai tare da cewa umma banga Abba ba koya fita ne? Kara hade rai umma tai tace ki wuce kigaida Goggo dan shikam ya fita tadan tabe karamin bakinta tare da karasawa dakin goggon ranta duk ba dadi, sam batasan matar. Sallama tai Goggo dake kwance ta amsa mata cikin gadara salmah tashiga tare da gaida ta goggo ta amsa tare da cewa yawan banzan za'a tafi? Salma tadaure tace goggo nidai makaranta zani😞. Goggo tai tsaki tace oho dai tunda ke da kamal kunfi karfin iyayenku ai sai kuyi tayi tace goggo yaza'aikifadi haka? cikin zafin rai goggo ta mike zaune tace karya aka muku? Wayasani ma ko kamal din yamanta dake yayi auransa acan kasar dayake ke ya barki nan kina yawon nuna jiki😏? Idanun salma suka ciciko da kwalla tadaure ta mike tace natafi makaranta goggo tace ke kika sani munafuka mudai kika kuskura kika dauko mana abun kunya sai kinsha mamaki, Salmah tai saurin yin waje tana share kwalla umma tagani a tsakar gida alamar duk zancen dasukai taji dasauri ta wuce dan tasan umma baxata taba sa baki a wannan maganar ba, nikaf ta daura takarasa waje. Titi ta fita tasamu bus din dazatai Buk tahau, acikin mota kanta kawai ta jingina a kujera tana tunanin wannan al'amari wai ace tsakanin ta da mahaifiyarta bawata shakuwa? Wai 'yar fari😟? Ita atunaninta tin yaushe aka dena wannan abun? Intayi magana sai Abba yace mata uwarta ai bafullatanace tai wata ajiyar zuciya tare da dauko hoton kamal cikin jakarta takuramai ido aranta tace yaya yaushe zaka dawo? I really miss you, lissafin kwanan wata tashigayi yaci ace yaya kamal yadawo dan ayanda yafada mata randa sukai waya saura 3wks su taho to yanzu gashi taga harda durin kwana 5 😞 lalai yaya kamar bai matsu yaganta ba? Rabonsu da juna tun shekara 3 dasuka wuce, maida hoton tai ganin sun iso tafito daga motar ta shiga makaranta. Lalai yau tayi late cikin hanzari tafara tafiya sam bataji motsin mota a bayanta ba sai da motar tazo daf da ita dasauri ta juyo cikin razana tare dayin gefe amma ina motar gudu takeyi gashi kamar dan koyo ne ke tuka motar sam ba'a seti take tafiya ba motar sai data gogi jikinta hakan yasa tafadi kasa tim🙆🏻 Tabi motar dakallo idanta taf da kwalla dan mutane sun taru suna kallanta abin haushi bawanda yataimaka mata, ahankali motar tafara yowa baya sai alokacin takalli number motar Prince 1 ne rubuce a jiki. Sai da motar tazo daf da ita dan harta runtse ido tadauka murkusheta za'ayi jin shiru yasa ta bude idanta ahankali kafar mutane uku tagani ahankali tafara dago idanta har ta dure su akan nagaban wanda tasani shine Prince Salman dan tanaganin rashin mutincin dayake yi a school din wani wahalalen yawo ta hadiya. Salman yakashe mata ido sannan yace limamiya bakya gani ne? Aranta tace limamiya? Yacigaba kosai muntaimaka miki da glass ne? Salmah tamakamai harara sannan tadaure tace ku bugeni maimakon kubani hakuri sai kuce me? Amir dake baya yai wata dariya yace hakuri? Oh prince kagane metake nufi ai😆? Salman yace ohh ai kaji halin talakawa sannan yaciro bandir din dari biyar yacilla mata yace sune matsalarki I know😏 Najib dayai shiru abaya dan shi yake koyon tukin motar azahiri shikam baijin dadin abinda ke faruwa amma yazaiyi? Salma tai wani murmushi tare da daukan kudin sannan takaraso kusa da Salman ta mikamai ganin yaki amsa ta daura akan motar sannan ta matso kusa da salman tace maza irinku masu daukan mutane banza sannan suke tunanin kudi na maganin komai suna matukar bani tausayi😏 tana gama fad'ar haka ta juya tafara tafiya, mutanen dake gun suka shiga gulma, ran salman yagama baci yamaimaita afili Tausayi? Sannan yakalli kayan jikinta yaga gaba daya kayan datasa basu wuce kayan 2000 ba amma takalleshi tace yanabata tausayi? Dasauri yakara kusa da ita ta baya ya fizgo hijab dinta, jikintane yafara rawa ganin bata taba shigowa makarantar ba nikaf bama bare hijab ahankali hawaye yafara gudu a idanta salma yadawo ta gabanta dasauri ta tsugunna tare da kankame jikinta, ya firgita ganin yanda Allah yamata kyau amma rashin mutuncin dake idananunsa sun rinjayeshi yatsugunno kusa da ita sannan yace tausayi? Nidake yanzu waye mai kalar tausayi? Hawaye kawai takeyi yai wata dariyar mugunta sannan yace banza 'yar tallakawa ya mike yafara tafiya tace kai da kake d'an masu kud'i fin wasu kai? Tsayawa yai chak sannan ya juyo yace ke kinsan niko waye ma? Tace why should I know? Yace be careful dan zan iya ruguza miki rayuwarki mark my word ya juya ya tafi. Amir yashiga tafamai yace woo Man kana burgeni, salman yai tsaki yafada mota yace najib zokaja cikin sanyin jiki najib ya shiga. Salma kam suna tafiya tadau hijab dinta tasa da nikaf dinta tamike tare da kallan agogon hannunta shikenan tayi missing lectures dan kusan 40mins kenan dashiga class ahanakali take tafiya tana jin wata muguwar tsanar salman jitake daza'a bata wuka ace anmata uzuri takashe mutun daya data tsana a duniyarnan to lalai ba shakka salman zata lumawa wannan wukar😡. Salma kam yaci alwashin sai ya nunamata shi basa'an yinta bane dan tunda aka haifeshi bawanda yataba fadamai maganar banza irin wannan banzar yariyar dabai masan ta ba, Amir yakalla yace adubomin ko ita wacece, Amir yace wannan yarinyar? Salman yace yes I can't live her like this. Amir yace angama prince.... Nace hmmm abin babba ne😕 By Ayusher mohd📚 [10/16, 11:15 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣ Salmah kam karkashin wata bishiya tasamu tazauna dan tarasa dalili tunda ta taho ake binta da kallo, cikinta taji ya murda tasani yunwace ke damunta hakan yasa tadauko jakarta tabude tashiga irga kudin ciki ~N~350 ne aciki ta ciro dari ta mike tai hanyar shop, har alokacin mutane na binta da kallo cikin rashin damuwa takarasa tare da mikama mai shop din kudi tace abani buns sai dai me? Kafin mai shagon ya amsa taji an wafce kudin ahankali ta juyo dan ganin wannan rainin hankalin wani saurayi tagani cikin mamaki ta dauriya tace malam mekenan? saurayin yace indai kinasan siyan abu anan to lalai ne ki kwabe wannan munafikin abinda kikasa muga mai kika nunama prince har ya tsugunna kusa dake tace me kake nufi da kalamanka? Yace oh kindauka bamusan manufarki ba? Salmah ta runtse ido tadaure ta juya batare da ta amshi kudin ba, jitai an mazan gun sun kwashe mata da dariya, ahankali take naga kafarta dan jin kafar take tamata nauyi. Sai datai tafiya mai nisa sannan tasamu guri tazauna kwalla ya cika mata ido, tunda tafara zuwa makarantarnan bata tunanin wani yasanta banda mutanen datake gaisawa dasu yau gashi anjayo mata duk inda ta wuce ana binta da kallo😰hoton kamal tadauko tafada afili yaya kamal kadawo plz😔 jitai ance lalai salmah soyaya har a skul? Tadago danta gane mai muryar tace zee ashe kin shigo, zee tazauna tare da cewa salmah meya hadaku da prince? Tace au kema harkinji? Zee tace hmm ni fa muna zaune munajiran Professor mannir kawai wani ya shigo class da gudu yace yan class kunsan salmah ai kawar zee? Sukace eh mai nikaf yace to tanacan ana show itada prince ya cire mata hijab da nikaf😂 nan yan class sukashiga dariya tundaga nan nafito nemanki banganki ba, Salma tai murmushin yake tace zee kodai inhakura da makarantarnan? Injira kamal yadawo inmunyi aure sai inkarasa. Zee tace haba salma akan wani can zaki durkushe rayuwarki? Kinsan prince yakai 2yrs a skul din nan kuwa? Tace haba? Zee tace hmm amma kinsan me? Haryanzu fa a level 200 yake salma cikin mamaki tace haba dai? Baya jaa ne? Zee ta kwashe da dariya tace inafa? Ance blanksheet fa yake submitting😝. Salma tace blank? To ya akai ya wuce level 100 zee tace ance wai da shugabar makarantar taso tadinga bashi mark sai dai shi dakanshi yace mata bayaso karta karamai haka, salma tace meyasa😳? Zee tace oho ba wanda yasan dalili, tadan tabe baki tace shiyasani zee tace waje iskanci cikin fanko😜nan sukasa dariya. Salman kam bai dade a skul ba ya wuce yawansa dan dama ba lectures yake shiga ba sai wajen magrib ya shiga gida ya ajiye mota yai bangarensa bayi nata gaisuwa yana isa daki yai wanka yazura doguwar riga yafito tareda bayinsa dake kuladashi yai bangaren fulani zuciyarshi taf take da bakin ciki suna isa harabar gun yacema bayin su jirashi yashiga, ahankali yakarasa kofar dankin bayin dake kula dagun suka budemai yashiga sai dai bakowa a kilisar da fulanin ke zama yai shiru zuciyarshi na bugawa da karfi. Wata baiwa ce tazo tace tana daki bari insanar mata, yace a'a bari in karasa tace to ranka ya dade, ahankali yakarasa dakin yakai hannu zai kwankwasa yaji maganar Ishaq (yayansa ne agun mahaifinsu) yanacewa yau ma dai kamar kullum salman yawansa yaje, fulanice ta saki dariya tace ka tabbatar dai kana kula da takunsa dukda kaini dan sarki nafarko bai zama lalai ka gaji sarki ba ehe. Ishaq yace haba ummi yaxakina fadar haka ke kina tunanin wannan shashashan Abba zaiba mulki? Yaranda banda yawo ba abinda yake? Haryanzu yakasa gama karatu? Tai dariya tace kasan sarki na tausayinsa ganin bashida uwa, ishaq yace tab aikin banza kenan to sau nawa yana zuwa gaida sarkin amma baya amsawa? Ahankali salman yafara yin baya idanshi yakada yayi jaa dakinsa ya koma yai saurin dafa kansa da kirjinsa jiyake kamar zai mutu dasauri ya bude drawer yad'auko magani ya hadiya yashiga karanta *INNALLILAHI WA INA ILAIHI RAJI'UN* ahankali yafara jin nutsuwa tana zuwa mai. Salmah zaune a tsakar ta zuba tagumi ga kwanukan wanke wanke a gabanta da alama shi takeyi tashiga tunani, abinda salman ya mata take tunani tai ajiyar zuciya aranta tace da yaya kamal nanan munyi auranmu da duk haka bata samen ba jitai an daka mata dundu a baya tadago cikin mamaki goggo tace kinci gidanku, wanke_wanke zakimana ko tunanin wancan dan iskan? Salmah tace goggo wai meyasa kika tsani yaya kamal? Ba dan uwan Abba bane? Tace oho ko dan uwa nane mai yadameni? Kedai kinji asara kannenki duk sunyi aure ke kinfi karfin iyayenki, salma tace nima da yaya kamal nanan ai...jitai an kwabe mata baki goggo tace mara kunyar banza kawai ke baki da aiki sai zancen kamal duk mutanen dasukazo neman auranki kim koresu shima Alhaji ai duk laifinshine aikin banza, tana zuwa nan tai gaba salma tabita da ido itakam bakomai zatajira kamal dinta 😗. By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:15 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* *NO. 3⃣* Motsin bude kofa taji salma ta mike da sauri dan tasan Abba ne takaraso inda yake ta rusunna tare damai sannu da zuwa ta amshi ledar hannun sa, cikin murmushi ya amsa yace andawo? Tace eh Abba, nan yakarasa daki itama tana biye dashi. Falo yashiga itakuma tai dakim goggo ta mika mata ledar sannan tai falo gun Abba, azaune taganshi umma nakusa dashi, Abba yakalleta yace salma ya akai? Tace Hmm Abba dama......tafad'a tana kallan fuskar umma, Abba yakalleta sannan ya kalli umma yace ko in fito? Tad'anyi kasa dakai, Abba yamike umma tad'aure tace hb Alhaji? Yace ke kinjiki ai yarinya nasan magana da mahaifinta, menene a ciki? Abba ya fito salma ta biyoshi tana kallan umma na harararta suna fita tace Abba kunyi waya da yaya kamal? Yai murmushi yace jiya daddadare dai ya kirani😊. Salma tasaki murmushi tace Abba yaushe yace zai dawo? Yace hmm lalai salma tadamu yayanta yadawo tunda harta fara tambaya, salma ta rufe ido tace Abba karatu yafara tsauri inaso insamu mai koyamin ne🙈..... Abba yai murmushi yace hmm banyarda da wannan wayan ba nida nakeso yana dawowa musha biki😀 dasauri tad'ago sai kuma ta ruga daki da gudu, yabita da kallo tareda murmushi yana san yarinyar duk cikin 'ya'yanshi yafi shakuwa da ita kasancewar uwarta bata shiga harkarta hakan yasa shine ke zama abokin hirarta tun tana karama. Salma kam gado tafad'a tashiga ajiyar zuciya na farin ciki itakanta takosa tai auren nan ko dangin mahaifiyarta zasu daina mata fad'a. Shekararta 22 amma tarasa dalilin dayasa idan kowa yake akanta kodayake kannanta 2 sunyi aure suna gama secondary, kaninta namiji kuma na makarantar kwana ta Gezawa. Wahsegari ta shirya yanda tasaba tafito ta tafi makaranta, 12 suka fito daga lectures itada zee wajen wata kujera suka zauna, zee tafara tambayar salma akan karatun dasukai yanzu, salma sosai tashiga yima zee bayani wani guy ne yazo yace wai ana magana da limamiya, cikin mamaki zee tace limamiya? Antaba kiran macce limamiya dama? Yace haka akacemin nidai taje inji prince, yana kaiwa nan yai waje. Zee takalli salma tace don't tell me ke ake nufi? Salma tai tsaki tace dalla share d'an iska, zee tace salma karfa asamu matsala dan prince inya tsani mutum har korarsa yanasawa ayi, Salmah tai tsaki tace keni duk wannan abun bai damenba menamai wai? Shine yaci mutuncina? Zee tace tashi mubar gun nan daga gani yaganmu ne. Mikewa sukai suka fara tafiya, salmah jitai an ja mata hijab dasauri ta juya tare dacewa wani irin iskanci ne.....kalamanta sun katsene ganin mazan jiya su uku Amir na rike da hijab d'inta, cikin zafin nama ta fizge sannan tace meye hakan kakeyi? Amir yace tambaya kike? Tace eh laifi ne? Mena muku wai? A tunanina kune kuka min abu amma na nuna ya wuce to why are u bothering me? 😠 tafad'a tana hararra salman duk da cikin zuciyarta taf yake da tsoro amma ta riga tasa aranta bazata juri wulakanci ba. Zee kam tagama tsorata ahankali tafara ja da baya, prince ne yakaraso inda take daf da ita hakan yasa tad'an matsa dan tanajin sautin numfashinshi, kara matsowa yai kusa da ita , zuciyarta sai bigawa take sai datakai jikin bango ya kara matsowa tadaure tace me kakeyin hakan? Yace dazu kin tambaya me kikayi shiyasa nake kokarin baki amsa, tadaure tace to d'an matsa yace in naki fa? Tai shiru. Salman yace abinda kika fad'a jiya shine dalilin dayasa nadawo yau kikace maza irinmu nabaki tausayi? Mamaki ya kama salma itakam sam ta manta ta fad'I haka to meye inta fad'a karya tayi? Jin salman tai yace meye abin tausayi agareni? Bayan ubanki ba d'an kowa bane? Ta dago ido cikin b'acin rai tace arziki shine komai kake tunani? Yace ke yar gidan Amadu mai gini kishiga hankalinki sannan kiyi gaggawar janye kalmarki ta tausayi agareni wannan shine last warning dina...... Salma mamaki yakamata wato bincike yasa ayi akanta? Tadaure tace kalmace bazan janyeba tunda ba karya nai ba😏gini kuma da mahaifina ke ye ai baiwace wani sana'ar yi ma bashi da ita🙄 tuni zuciyar salman tagama dugunzuma ba abinda yatsana a duniya irin ace ana tausayin sa jiyai kansa yafara sarawa, hannu yad'aga alamar zai mare ta dasauri ta runtse ido ko meya tuna sai yafasa tare da juyawa dasauri. Salma tabishi da harara Amir ya nunata da hannu sannan ya nuna idansa da hannu tasan meyake nufi wai they are watching me tace oho aikine bai isheku ba. Salman kam toilet yashiga dasauri ya dafe kirjinsa ya d'auko maganinsa ya had'iya ahankali yafara jin numfashinshi na fita dai_dai........ By Ayusher mohd📚 [10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.4⃣ Salmah kam suna tafiya gun ta tsugunna ta shiga maida numfashi ta dade ahaka kafin ta mike ganin mutane tai agun suna kallanta ta dauke idanta tare da kallan agoggon hannunta, gani saura 15 mins su shiga next lectures gashi ko sallah batai ba yasa tai saurin wucewa, tana dubawa ko zataga zee. Salman yauma sai magrib yashigo gun mai martaba ya wuce, ya dade kafin sarki yabashi izinin shiga, cikin nutsuwa ya shiga mai martaba yakalli fadawan gun yace kubamu guri suka amsa tare da mikewa. Sarki ya kalli salman yace matso nan, cikin sanyin jiki salman ya matso kusa da sarki tare da sake gaidashi ya amsa fuska a d'aure, sannan ya cigaba haryanzu baka da aiki sai tsokanar mutane a makarantar ko? Salman yai kasa dakai Yace Ranka ya dade ba........ Cikin b'acin rai sarki ya katseshi yace anfad'ama duk abinda kake a makarantar bana sani? Ka kasa maida hankali kai karatu sai bin kawayen banza da wulakanta mutanena, sannan kana kallo kaninka Nazir yai aure amma kai banda shegantaka bakada aikin yi😠. Salman kam idansa ya kad'a yai jaa batare da sarki yajira amsarsa ba yace wato yanzu rashin mutuncin ka ya kai wani mataki daka fara wulakanta mata ko? Salman yad'ago cikin mamaki sarki yace ina nan ishaq yazo yasanar dani ka cirewa wata hijab a makaranta ko karya aka ma? Gaban salman ne ya fad'I amma yadaure yace a'a, sarkj yace nagode salman kacigba da bakanta min rai. Salman yai shiru zuciyarshi na rayamai kabada hakuri, can wata zuciyar tace ka manta me suka ma? Jin bashi da niyar bada hakuri yasa sarki yace dama kai bakasaba yin laifi kabada hakuri, tashi Kaban guri, ga mamakin sarki gani yai salman na kokarin mekewa ranshi yakara b'aci yace kakuma tabbatar ka fito da matar aure nan da wata 1 dan bazan d'auki iskancin da kakeji dashi ba, salman yace Abba wata 1 ai......dasauri sarki ya katseshi yace wlh ka fita daga idona ka sani bana magana 2 dan haka ka kiyaye. Salman yai tsaye yakasa magana kuma ya kasa wucewa, wani bawa ne ya shigo yace ranka ya dade *Ishaq* na neman iso, sarki ya d'agamai kai alamar yashigo, dasuri ya juya, bai dade da fita ba ishaq ya shigo ganin salman yasa yasaki wani murmushi😏 tare da tsugunnawa ya gaida sarki, cikin sanyin murya ya amsa ishaq yace salman yanaganka a tsaye? Salman ya kalleshi sannan ya d'auke kai tare dacewa sarki nabarka lafiya, sarki bai amsaba salman kam da sauri yai waje. Ishaq yace Abba Allah yasa dai d'an kanin nan nawa ba laifi yama ba? Inkuwa laifi yai ina bada hakuri a maimakon shi, sarki yace kyale sokon yaro zanyi maganinsa, sannan kafad'ama fulani ta fara nemo yarinyar dazai aura dan in bai kawo wace zai auraba nan da wata 1 to ba shakka aure zan mai. Ishaq yace to ranka ya dade, sannan shima ya fita zuciyarshi fal farinciki lalai yau sunada karamin party. Salmah kam tagama aikin gida takoma d'aki ta d'auko littafinta kenan taji yaro na sallama sai dai kafin tafita goggo ta fita tace yaro ya akai? Yaron yace wai ana sallama da salmah inji Muftahu tace muftahu? Wanne kenan? Yace muftahu mai babban shagon can tace au toh nagane, je kace gatannan yanzu zata iso, yace to tare da yin waje. Goggo ta taho dasauri tana washe baki takaraso dakin salmah dake zaune duk taji abinda sukai da yaron, goggo tace tashi 'yar nan alkairi yasamemu😁 salmah tace name fa? Goggo tace gidan ku kina nufi bakiji me mukai da yaron can ba😠? Salmah tace au nad'auka sa'a yake nema( kanwarta da akai aure wata 4 dasuka wuce). Goggo tace kaji min 'yar rainin hankali sa'ar datai aure za'azo nema? Tace kin manta ne goggo kwanaki.....ta katseta rufemin baki yar iskar banza to ke ake nema kuma muftahu ne mai katan shagon can salma tad'an tabe baki tace goggo kinsan fa ni yaya kamal nakeso, goggo tace lalai dalla rufemin baki kamalo ba kamalu ba kinsan Allah salma😠 tashi kafin na fasa miki baki. Kasa tai dakanta tare da jan hijab dinta tai waje tana turo baki. Muftahu kam ansha shadda da hula ga motarsa Civic ya ajiyeta yana tsaye ya juya baya, yanajin motsin kofa ya juyo yana murmushi takalleshi tare da d'auke kai tace ina wuni? Yacw lafiya lau *Salmat*😊 tace salmat? Yace eh mana ni haka zan dinga kiranki ta juya kai tare da yin shiru, yace salmat plz nazo da magana mai girma hope zaki fahimceni? Ta juyo tare da kakaro murmushi tace am sorry muftahu nasan kasan inada Wanda zan aura. Muftahu yace salmat, kamal ba baida niyar auranki, inba haka ba shekararsa nawa acan? Kaf 'yan layin nan gulmar abin suke mahaifinki yabarki kina jiran d'an uwansa bayan kila shi yamanta daku. Salma kam ranta yagama b'aci batare datace komai ba tai hanyar gida ta bude kofar tai dakin ta da sauri tafad'a kan gado ahankali hawaye yafara zubo mata. ... By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.5⃣ Tanajin motsin umma a waje amma abin haushi ko tazo ta tambayeta meya faru, Abbanta nadawo wa tamike da sauri taje tagaidashi umma da goggo nazaune bayan ya amsa, goggo tace dazun korar muftahun kikai shima? Salma tai kasa dakai, Abba yace wai ke Basira meyasa bakyaji? Na dade da fad'a miki bana san kina takurama salmah, ko kin manta matar da kamal ce? Tace yahkuri Alhaji ganinai tanata zama a gida ba kamal ba labarinsa. Abba yace kada ki manta yanda muke da mahaifin kamal mu 2 ne a d'akin mu shine yayana kuma baki isa kisa zumuncin mu yai rauni ba, Goggo tace Allah yabaku hakuri, Alhaji nad'auka salma kamar 'ya take a gurina tunda nina raineta, Allah bai bani 'da ba..... Da sauri umma ta katseta tace Goggo kidaina wannan maganar, sannan takalli salma tace ke kuma tashi ki bamu guri, salma ta mike duk jikinta yai sanyi tai d'akinta. Umma takalli goggo tace kiyi hakuri hajiya, Alhaji bai kamata ka mata fad'a agaban wannan 'yar ba, Alhaji yace ai basira ce na dade ina mata magana bata ji, amma yanzu abar maganar nan zan kira kamal inji menene ya tsayar dashi dan ni kaina nasan gaskiya basira take fad'a, yana kai nan yai waje, umma tashiga ba goggo hakuri. Yau salma na zaune a class suna d'aukan lectures hankalinta nakan karatun da akeyi har malamin yagama koyarwa ya fita zama tai a theater room din tana duba littafinta. Ganin mutum tai ya zauna a saman desk din datake ta d'ago cikin mamaki tare da matsawa, mamaki ne ya kamata ta zaro ido sannan gabanta ya fad'I ta mike zata wuce hannu yasa ya fizgota tare da maidata inda take yace 'yar gidan Amadu ina zaki batare da uzinina ba? Tace izini? Yace eh ko kinfi karfi? Tai shiru tare da ture hannunshi tace wai menene dalilinka nasan shiga harkata? Yace I won't leave you har sai kin janye maganarki na tausayi daga kaina, in kuwa ba haka ba I promise you sai kinyi dana sani mai karfi. Salma tai wani murmurshi😏 duk daba ganinta yake ba tace in naki fa?yace then mark my word😠, tace prince I am not afraid of u, yace u are not? Ta daga kai alamar yes yai murmushi yace then I will have to make you, yana kai nan yai waje. Wata doguwar ajiyar zuciya ta rike hannunta dake rawa murya taji cikin sanyin ance salmah kiyi hakuri ki kuma ba salman hakuri, tad'ago cikin mamaki Najib tagani tace mena mai? Yace bakiyi komai ba amma salman ba abinda yatsana irin yaji ance yana ba mutum tausayi, ya juya ya fita, ta bishi da kallo tare da runtse ido tace yazanyi yaya kamal? 😞 Batafi 1 hr ba zee tashigo dasauri tace salma me kikayi? Salma tace name fa? Tace an kafe sunan ki a notice board an baki suspension na 2 weeks na dasauri ta mike cikin kidema tace suspension? Ni *SALMAH AHMAD MOHD* ? Zee tace wlh sunan ki akasa tace menayi? Tafad'a hawaye na zubo wa daga idanta tace akan me? Zee tace kema kinsani ai, salma tace I have to go an ask dan salman yace a bani suspension dan ni ba 'yar kowa bace sai abani? Zee tace ki rufa mana asiri kar kisa a koreki daga skul din gaba daga, hannu tasa akai tafara kuka zee ta dafata tana rarrashinta. Dakyar ta tsayar da hawayenta tare da d'aukar jakarta tace zee na wuce gida kuma plz karki fad'a a gida abinda yafaru tace to salmah. A hankali take sauka daga steps din gun zuciyarta nakan tunanin abinda ke faruwa har ta iso titi tana jiran mota. Motace tazo kusa da ita tai parking tad'ago jajjayen idanunta, ahankali aka zuge glass d'in bayan motar, tana kallan wanda ke ciki haushi da wata muguwar tsanarsa suka mata yawa tadan matsa daga gun ahankali motar takara matsowa gun salman yace sorry limamiya I really pity you☹yanzu what can we do🤔? Jitai kamar tasa ihu d'an bakin ciki kalamansa amma me? Daurewa tai tace u don't have to pity me bawani abin bane dan anban suspension just take it as nasamu rest daga ganin mutanen dana tsani gani tana kainan ta matsa tafara tafiya da kafa. Salman yai kwafa haushin kalamanta suka kamashi yakalli driver dinsa yace dalla wuce mutafi yace to ranka ya dade. Salman na isa gida yana fitowa daga mota wanI bawa yazo yace sarki na nemanka, yace to tare dayin hanyar fadar sarki. Zaune suke su 2 sarki ya kalleshi yace ka kyauta da wulakantani dakai salman yace Abba bangane ba? Yace ai ni ka wulakanta tunda bakaji kunyar sawa abawa d'aliba suspension ba wlh salman sai kasan kayi kuskuren b'atamin suna dasauri ya d'ago yace Abba yarinyarce fa.......yace just keep silent ka kuma bani guri sanda ishaq ya fad'amin zancen nan I thought karya yakema amma yanzu na tabbatar dan haka mike kaban guri😠. Cikin sanyin jiki salman ya mike yana fita yai hanyar dakin ishaq sai dai yana tsaye daga waje yanajin shewar su ishaq da kannansa maza 4 suna murna kowa nacewa kai yarima ka birgeni, ishaq yace ai na dade da fad'a muku salman d'an karamin kwarone a gurina, ragowar sai jin jina mai suke ahankali ya juya yai bangarensa kansa na sarawa yana shiga d'aki ya zube ya shiga murkususu rike da kirji da kai dakyar yasha magani yashiga karanta *INA LILAHI WA INA ILAIHI RAJI'UN* ahankali yafara jin relief. By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.6⃣ Kuka sosai takeyi yi abinda ya kara tunzurata umma na zaune a waje tana goge kubewa amma ko ta tambayeta, ta dade tana kuka ganin ba mai lalasarta yasa ta mike tare da fitowa tad'au kwandam wanka tai toilet umma ta bita da kallo. Qur'ani ta d'auko tashiga karantawa ahankali tafara jin sanyi na ziyarta zuciyarta, jin motsin Abba yasa ta fito da sauri takarasa tare da mai sannu da zuwa yai murmushi tare da cewa 'yar Abba meya sami idanunki? Tai kasa dakai yakamo hannunta yace muje inji matsalar 'yata tunda duk gidan ba mutanen da zasu tambayeki. A falo suka zauna yace menene salma? Tace Abba aran wayarka nakira yaya kamal yace to naji amma fad'amin menene? Tace bakomai Abba banajin dadi ne, yace ayya sannu ko muje asibiti? Tace A'a Abba naji sauki yace to sannu sannan yamika mata wayarsa ta amsa tare da mikewa tabar falon. D'aki tashiga tareda yima kamal flashing sau 6 tamai amma abin haushi bai biyoba, daga baya tai deciding ta kirashi sai dai shima no answer tadanyi tsaki tace kila yana wanI sabgar ne☹.....nace hmmm. Ishaq ne zaune gaban sarki, sarki ya kalleshi yace nasani ishaq kaimesan d'an uwankane, ishaq yai kasa dakai cikin sanyin murya yace Abba yazamuyi da matsalar yarinyar daya kora daga makaranta? Abin na damuna😞, gashi mutane an fara gulmar abin ina tsoron kar hakan yajama salman tsana daga mutane😕. Sarki yace ni kaina abin na damuna amma bari insa akira waziri inji yazamuyi, ishaq yai murmushi😏 ba b'ata lokaci sarki yasa akira waziri nan ishaq yafad'amai abinda ke faruwa. Waziri yai shiru can yace yarinyar ya take? Ishaq ya shiga yin bayani akan binciken dayasa ayi akan salma da kyawawan halin yarinyar, waziri ya nisa yace mezai hana muyi haka? Sarki yace me? Mu nunama mutane bawai korarta yasa akai ba dalili ba matar dazai aurace yakesan abata lokacin shirye shirye tahakan ne kowa zaisan salman ba mutum ne mara mutunci ba mai wulakanta mace, sarki yai shiru yana tunani. Ishaq kam baiso ba amma saboda san ya wulakanta salman jin yarinyar 'yar talakace ba jinin sarauta ba ko 'yar masu kudi yasa yace waziri ka kawo shawara Abba ya kagani? Sarki yace kasa a kara bincike akanta waziri banaso salman ya auri matar da bazata rufamai asiri ba waziri yace to ranka ya dade angama, ya mike yai waje. Salman kam yau weekend bacci yake sosai sai azahar yai wanka ya fito, al'adar gidan ne aje gaida duk matan gidan da ranar asabar hakan yasa salman ya fito bangaren hajiya karama(Amarya)yafara zuwa, bawani shiri sukeba gaisawa kawai sukai ya mike ya fita ta bishi da harara itakam gadarar yaron na bata haushi gashi ita d'anta namiji shekararashi 7😠. Bangaren Hajiya babba yaje(ta tsakiya) sun gaisa cikin sakin fuska sannan ya fito saidai yasani itama ba sanshi takeba. Yakarasa bangaren fulani itakam yasan halinta sarai amma ita gani take baisan komai ba cikin farinciki tasa aka damomai fura tace salman sha fura dan musamman saboda kai nasa aka dama yai murmushi yace nagode fulani tace sai kace wani bare? Kaifa d'ana ne yace haka ne😏. Bayan ya fito yakoma d'akinshi ya kwanta tare da runtse ido kaf 'yan gidan yasani 'yan uwansa mata 2 ne kesansa kuma sunyi aure sai yara dabasusan rayuwar gidan ba. Shima kuma kallan kowa yake tunda haryau bai manta abinda sukai mai ba yana yaro har sarkin kuwa☹. By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.7⃣ Salma kwance akan gado sam ta kasa barci sai juyi take rashin mutuncin da prince ya mata ne ke dawowa kwakwalwarta dasauri ta mike zaune tare dayin kwafa tace a fili yaron nan da ace nasanshi dasai na rama rashin mutuncin dayamin😠wata zuciyar tace kinsan shi mana sai dai in tsoro kike😀, dasauri ta tashi tsaye tace tsoro? Nidin? Inji tsoron wannan banzan? Alla ya sauwake🤔, haka tai ta shirme a d'aki sai 12 tasamu tai bacci. Waziri ne zaune agaban sarki yace ranka ya dade daga gun malam nake anyi istihara akan al'amarin nan ba shakka wannan auran alheri zai jawoma salman mai yawa, sannan maganar yarinyar kawai dai 'yar talakace amma halinta kaf 'yan unguwar sun shaida kyan halinta. Sarki yai shiru can yai murmushi yace Alhamdulila, waziri yace ga kyau dan 'yan unguwar sunce kyanta dayanda maza ke binta yasa take saka nikaf, sarki yace naji dadin binciken nan zancen talauci kuma ai ba wanI abu bane da talaka da mai kud'I duk daya suke agun Allah. Waziri ya kara tsugunawa yace Allah yajada ran mai martaba, yanzu insanar dashi?sarki yace a'a kasan halin salman taurin kai, kafiya in har yaji to da matsala, waziri yace ai halinku d'aya ranka ya dade yafad'a yana murmushi, sarki yai gyaran murya hakan yasa waziri yace tuba nake ranka ya dade. Sarki yace yanzu kuje kai da yayana kusamu mahaufinta kuji ko an mata miji, waziri yace bamu zamu kirashi ba? Sarki yace a'a ai mu muke nema, waziri yace angama rnka ya dade yafad'a tare da mikewa. Sarki yai murmushi shi kanshi yakosa yaga salman ya nutsu, haka kawai yakejin farin cikin zancen auran nan. Waziri yasa asanar da Amadu zasu shigo da yamma, duk da Abba baisan meke faruwa ba jin ance wai wani mutumi kesan ganinsa akan wata muhimmiyar magana, haka kawai Abba yasamu kanshi da fad'awa d'an aikin in ba damuwa su hadu a sharad'a inda yayansa yake cike da mamaki d'an aiken yace ba damuwa. Nan Abba ya koma gida yaI wanka yasa manyan kaya, umma takalleshi tace meke faruwa? Yace nikaina bansani ba amma kibari inje indawo nikainan bansan menene ba kawai dai naji dan aiken yace mutumin kamar yanada hadi da gidan sarauta, tai shiru tace to Allah yasa alkairi ne yace Ameen Basira bata dawoba? Tace eh yace salma fa? Najita shiru, umma takauda kai tace inazan sani? Yai tsaki yace sai kiyi tayi ai hakan jiya 'yarnan fuskarta duk ta canza amma wai bakisan menene ba? Yai waje cikin fishi. Dakin salma ya shiga tana zaune rike da hoton yaya kamal tanajin salamar Abba tai saurin boye hoton yakalleta cike da tausayi yace zan fita tace to Abba d'aurin aure? Yacs a'a tace adawo lafiya yacs amin tare dayin waje, yana tausayinta sosai dan jiya ya duba yaga adadin kiran datama kamal amma bai kira ba shikam dan dai bayanda zaiyi ne amma shikanshi yanaso 'yarsa tai aure. Yayan Amadu wato Mustapha jin sakon kaninsa yasa aka gyara falon baki tare da siyo lemuka, bayan Amadu ya isone bada dade wa ba kira ta shigo wayar Amadu ya amsa jiyai ance bakin dazasu zone muna sharada gidan wa zamuce? Nan Amadu yashiga kwatanta musu har suka gane. Su Amadu na zaune da yayansa suna hira suka dingajin hayaniya a waje cikin mamaki mustapha ya mike ya fito Amadu na bayanshi. Mamakine yakamasu ganin motoci guda 6 sun jeru a kofar gidansa ga fadawa a tsatsaye Mustapha yace hala wani taro nasarauta za'ayi Amadu yace ko kuma hawa ba? Naga in gidan sarauta zasuyi aure suna hawa, nan sukai murmushi tare da juyawa ji sukai ance banan ne gidan Mustafa ba yayan Amadu? Atare suka juyo suka kalli bafaden dayai maganar, Amadu yadaure yace nan amma meke faruwa? Ahankali aka bude motoci biyun tsakiya kowace waziri da yayan sarki Modibo suka fito. Mustafa da Amadu sukai kuri suna kallo ga kutane sun cika gun, jisukai wani bafade yace a waje zaku barsu? Dasauri Mustafa yace ahhhh ku ku shigo. Waziri da Modibo suka nufi gidan shikam Amadu jiyai kamar yayi mutuwar tsaye tunaninsa d'aya laifi yayi kawai. Sun zauna su kuma su Abba sun tsugunna suna kwasar gaisuwa,modibo yaI murmushi yace haka ake neman aure a tsugunne? Cikin sauri mustafa da Amadu suka d'ago ido? Tare da kallan juna sukace aure?Waziri yace kuzauna mana, nan suka zame suka zauna, modibo yace muna namawa Salman d'an gidan sarki auren 'yarku salma, cikin kidima Abba yace eye? Waziri yace eh muna neman alfarma, sai dai in kun mata miji to fa wannan ba yanda zamuyi, Abba yai shiru zufa tashiga keto mai, yakali mustafa shima zufar yake, Abba yadaure yace salma? Waziri yace ita fa, Abba yace ku gafarceni ranku ya dade amma....dasauri mustafa ya katseshi yace mun baku indai Salma ce😬 waziri yace amma kuwa muna godiya, yace a'a ai mune da godiya, Modibo yace to *Alhamdulila* munji dadi sosai sai dai munada magana, Nan su Abba suka d'ago, Modibo yacee bamasan auran ya wuce wata d'aya Abba yace wata 1? Waziri yace eh sannan munaso ku taimakemu karku mata komai nakayan d'aki mustafa yace amma ina ake haka? Modibo yace wannan gudumawar sarkine na amsawa dakukai zaku bamu 'yarku, mustafa yace toh😳. Nan modibo ya ciro bandir din dubo d'aya guda 3 ya ajiye yace wannan kudin mun gani muna so ne kenan kudin gaisuwa cike da tsoro Abba yakalli kudin zaiyi magana mustafa yarigashi yace mun gode amma kudin nan yayi yawa, guda d'aya zamu d'auka sannan inkun tsaida ranar auran sai a turo afad'amin nan sukaita godiya suka mike. Abba ya zube a gun yace yaya yazamuyi da kamal? Mustafa yace kamal basan auran salma yake ba tunda haryakai wannan lokacin batare daya dawo ba bayan nasan yagama karatu, Abba yace salma fa? Datake tsananin sansa? Yace intai aure zataso mijinta kasan zuciyar mace ai. Hmmmmmm babar magana🤔 By Aysuher Mohd📚 [10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.8⃣ Abba tare suka taho da mustafa dakuma matarsa, salma na kwance a kasa inda tai sallah batasan sanda bacci ya dauketa ba. Mafarki take mai dadi, wai gata rike da hannun wani sai dai bataga fuskarshi ba sun je bakin ruwa sun zauna, yasa hannunsa a kafad'arta tare da kwantar da kanta a jikin kafad'arsa murmushi take sosai, tareda jin wani sanyin shaukin kauna na ratsata, a cikin bacci taji anacewa ke! Ke firgigit ta mike tare da kallan umma dake tsaye akanta, umma tace tashi ku gaisa da baffanki tace to tare da mikewa. A falo tagansu ta gaishesu suka amsa cikin farin ciki mustafa yakaleta yace salma inaso kisan duk abinda yafaru dake to ba shakka mukaddarine sannan mahaifinki dani masu sanki ne bazamu yanke hukunci akan abinda mukasan bazai taimakeki ba tace hakane baffa, Abba yace ungo nan ya mika mata d'ari 500 yace kije kisiyoma baffanki lemon fata da ayaba tace to tare da fita, taxo fita taga goggo tadawo nan tagaisheta ta wuce. Haka ta tafi tana murmushi haka kawai tunda tai mafarki takejin farinciki. Can bakin titi taje tana tafe cikin nikaf tana murmushi. Mustafa shi dakanshi yazaunar da umma da goggo da matarshi dake ciki time din batasan meke faruwa ba ya musu bayanin halin da'ake ciki, Goggo kam tayi murna ta kuma yi bakinciki. Tana murna salma zatai aure sai dai tana kishin auran d'an sarkin dazatai sai dai yaxatayi? Tunda batada 'da. Hafsa matar mustafa tace amma kamal.....dasauri mustafa ya katseta yace inhar kamal yadamu da salma da tuni ya dawo sannan daya dinga nemanta ta hanyoyi daban daban amma ina sane baya nemanta, umma kam batace komai ba. Abba yace kada kowa yafad'ama salma halin da ake ciki yanzu harsai bikin yazo kusa gudun kar sanda takema kamal yaja mata matsala sukace to. Salma tadawo gida tawuce d'aki tare da d'aukan hoton kamal tace yaya inaji ajikina munkusa fara rayuwa tare ganin irin mafarkin danai. Nace toh fa🤔 anya kuwa?. Fulani dakanta ta kira Zainab da Zeena 'ya'yanta manya masu aure kuma sune kesan salman nagaskiya, nan ta sanar dazu umarnin sarki na lefem salman da zasu hado, murna sosak sukai, fulank tace sai dai yarinyar yar talakawa ce dan haka kusan irin kayan dazaku hado? Cike da mamaki zeena tace bangane ba? Dan zai auri talaka sai akace ita ba mutum bace? Zainab tace mudai zamuyi abinda muka saba, fulani tace kukuka sani😠 sannan ance kar wanda yama salman zancen auran. Zainab tace bangane ba?baya santa ne ko me? Tace nidai nafad'a muku umarnin mahaifinku ne. Suka kalli juna cikin mamaki. Shirye shiryen biki ake sosai agidan sarki an tsaida lokaci nan da 3weeks, salman kam yafahimci akwai shirin biki da ake a gidan sai dai ganin ba wanda yamai maganar yasa shima ya basar ya nuna baisan me sukeyi ba. Haka gidansu salma ita ba makaranta take zuwa ba sai dai itakanta batasan shiga da fitar da ake a gidan ba gashi kullum goggo sai ta kawo mata abu a kofi tace tasha intai magana sai tace bayam inakallan yanda kikeyi da jiki gabadaya shawara da basir sun kamaki, shiyasa ko makaranta bakya iya zuwa tace hmmm. Yau saura sati 1 biki haka kuma yau ne sarki ya kira salman da daddare suka zauna a turakarsa, sunyi shiru na wasu lokutan sannan sarki ya nisa yace salman menene matsayina agunka? Salman ya d'ago da mamaki yace Abba yazaka tambayi 'da matsayin uba a gareshi? yacigaba Abba bani da kamarka aduniya, sarki yai shiru can yace nasani salman sai dai inasan intunatar dakaine yanda kakejin matsayin na agunka nima haka nakejin matsayinka aguna. Salman yai kasa dakai idansa ya kad'a yai jaa, Sarki yacigaba salman na maka mata ina fatan kuma zakamin biyaya a matsayina na wanda bakada kamarsa, cikin kid'ima salman yad'ago ya kalli sarki yace Abba mekake nufi da mata? Sarki yace eh salman wannan shine my first and last request to u a matsayina na mahaifinka, salman bakinsa yashiha rawa kanshi yafara zafi samun kanshi yai dacewa bakomai Abba, sarki ya saki murmushi yace nasank sarai bazaka bani kunya ba. Salman yai kasa dakai, sarki yace gobe ka shirya Mannir ya rakaka yace a'a nikadai zani, sarki yace a'a ko ishaq to kad'auka yacd zanduba, harya mike sarki yace nan da kwana 6 za'a d'aura auren ragowar sha'anin biki sai ta tare za'ayi tunda ba hali garesu ba, haushi yakamashi talakace ma kenan? yace da wuri haka? Abba yace mezamu jira salman? Kannanka fa sunyi aure yai murmushin yake tare da mikewa. Salma kam tanata sharar dakuna dan yau tun safe 'yan gidan suka tafi gidan baffanta, tagama da d'akuna tashiga falon Abba ta share sannan tad'auko tsinma ta fara goge_goge tazo goge gun tv taga invitation Cike da mamaki tad'aga dan ganin auran wa za'ayi? Mamaki ya kamata ganin sunanta daro_daro wai ana gayyatar walimar bikinta ranar juma'a da misalin karfe 4, takalla dakyau basunan namiji, tace mekenan? Badai yaya kamal bane zai dawo akaki fad'amin😬. Jitai ana kwamkwasa kofa tafi to dasauri makocinsu ne tagaidashi yace babankine yakirani wai inkawo miki waya zai kira tace to. Basu dadeba Abba yakira tad'aga yace salmah kiyi hakuri naso in nadawo nafad'amiki wata muhimmiyar magana sai dai I am too late, tace na me fa? Abba yace ki shirya zakiyi bako sannan dan Allah inhar kinsan darajata karki wulakantamin bako, da mamaki tace to amma bakon guna zaizo? Yace eh ki tambatar kin shirya sannan karki manta karki wulakantashi indai......ta katseshi da sauri to Abba naji😊. Yace kin yarda dani aiko? Tace in banyarda da Abba na ba dawa zan yarda yace good dan haka kitaimakeni karnaji kunya nida yayana tace Abba karka damu, nan sukai sallama..... Hmmmmm😱 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.9⃣ Wanka salma ta shiga bayan tagama komai ta shirya cikin less d'inta na sallah haka kawai ta kosa taga bakon da Abbanta yake magana. Salman ma ya shirya cikin kayansu na sarauta shida bawanshi suka fito dakuma driver, su biyu suna gaba shikuma yana baya rike da waya yana dane_dane, sam bai kula da inda suke shigaba dan driver dashi akazo ganin gidan tun farkon zancen auran, salman jin ana jugub_jugub a mota yasa ya dago kai, cikim tsananin mamaki yake kallan dan lokon da suke shiga, cike da mamaki ya kalli driver nasa yasa mamman ina kake kaini? Yace yalab'ai kayi hakuri mun kusa zuwa, cikin b'acin rai yace Mun kusa zuwa ina😡? Mamman yace gidan matar taka, salman da sauri ya juya baya tacikin glass yana kara kallan unguwar yace anan unguwar take? Yace eh tare dayin parking awani karamin gida salman yace me kenan? Yace an iso ga gidan nan, ya nuna wani karamin gida mai kofa karama salman yashiga yin wata dariya mai karfi, wanda hakan yasa suka razana bawan yace Ranka ya dade menene?salman yace bakuda hankali ne kuka kawoni nan? Mamman yace yallabai ai.....da karfi salman ya katsesu yace kuyi gaggawar fitar dani daga unguwarnan kafin kwalara takamani, mamman yace yallabai bakaga matar taka ba ai, yace wace mata kuma? Nace ku fita dani ko? Bawan yace to yallabai amma bari in ajiye mata sakon da sarki yabada yace aikin banza, ka fita ka kaimata inyaso ka taho daga baya yace yahkri yallabai ajiyewa kawai zanyi intaho yace komadai meye to kayi saurin dawowa inka wuce minti 5 tafiya zamuyi dasauri yace to yallabai. Boot din motar ya bude ya dauko manyan jakukuna guda 3 ya nufi gidan ya kwankwasa ciki sauri salma ta bude, sanye take da hijab amma batasa nikaf ba, kallanta tare da sakin baki, tadaure ganin kayan fadawa ajikinsa tace sannu? cikin in_in na yacs yauwa dan Allah hajiya salma nanan? Tadan kalleshi da mamaki tace nice salma tafad'a tare da nuna kanta, yace hmm gashi ance inkawo miki tace ni kuma? Yace eh kiyi hakuri ya shirya zuwa kuma sai wani uzuri yataso mai, tace wafa🤔?Zaiyi magana yaji anmai horn dasauri yajuya yace eh, tabishi da kallo tare da cewa shine bakon Abban? Sai kuma ta d'an daga kafada tare da kallan waje can taga motar ta kulle tad'au jakukunan ta shiga ciki tare da ajiyewa a falon Abba takoma d'aki ta kwanta, tunani take me katin bikin nan yake nufi? Bafaden kam na shiga mota yai ajiyar zuciya tare da cewa kai yallabai kayi sa'a wannan ita kad'ai ma kyanta ai ya isa ka wuni kana kallanta, salman ko kallanshi bai ba asari ma ranshi ne yakara b'aci. Sanda yana yaro mahaifiyarsa ta rasu, matan babansa basanshi sukeba haka 'yan uwansa, sannan yanzu matar dazai aurama maimakon abarshi yasamu wacce zataso shi shima yasota amma sai abashi auran kara buta? Lalai zai d'au mataki bayan auran nan. Salma kam duk abin duniya ya dameta tanajin motsin Abba ta mike da sauri taje ta gaidashi ya amsa tare da cewa kinga bakon? Tace eh wani bafadene yace wanda zaizo din wani uzuri ya hanashi zuwa, Abba yace toh😳? Yaza'ai haka? Tace gashi wanda yazo ya ajiye, Abba yace toh da alama uzurin mai karfine tunda ansanar dani ya fito daga gida, salma tace Abba katin can kamar na biki, Abba yace salma matso nan ta matso kusa dashi tana murmushi yace ki nutsu zan fad'a miki wata magana mai tace to Abba. Yace dani da yayana mun yanke hukunci yi miki aure tad'ago da mamaki tace aure kuma? Yace nasanki salma yarinyace mai biyayya kadaki bani kunya, idanta ya ciko da kwalla tace Abba yaya kamal fa? Yace salma kibar zancen kamal dan mahaifinshine yafara ansar maganar auran, tai shiru zuciyarta sai bigawa take, yace wannan juma'ar za'ayi yini da d'aurin aure da daddare akaiki saidai bansan koda wani abu dazakuyi keda kawayenki ba, tace Abba juma'a?yace eh salma kada ki manta ni mahaifin kene bazan tabayin abinda zai cutar dake ba sannan inaji ajikina auran nan alheri ne. Hawaye take sosai yace salma Allah yamiki albarka ta runtse idanta da karfi meke shirin faruwa da ita? Mafarkin datai dama na rabuwa da kamal ne?😭😭. Abba yace bazaki tambayi sunan mijin ba? Tace basai naji ba Abba tunda kun amince dashi ai shikenan yai murmushi tausayinta yakeji sosai. Mikewa tai tashiga d'aki ta hau kuka, umma najinta amma batako shigo dakin ba ga batare suka dawo da goggo ba ta dawo ba. Yau laraba gida ya fara cika salma kam na kwance ba lafiya sai dai hakan baisa an daina hidima ba, tun safe aka kwashi 'yan uwan umma da Abba suka tafi gidan mustafa acan za'a anshi lefe. By Ayusher Mohd📚 By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣0⃣ Salman zaune a gaban sarki, mai martaba yace za'a kwashe kayan bangarenka a sake wasu ko kana bukatar wani abun? Salman yace a'a duk yanda kuka gani, sarki yace inafatan kaje gun yarinyar kaji ko tana bukatar wani abun na biki? Salman yaji gabansa ya fad'I amma yad'aure yace tace bata bukatar komaI, sarki yace zancen banza kenan kai bakasan kawaici ba? Ko kataba ganin inda amarya tace bata bukatar kudi? Salman yai kasa dakai yace zan aika mata wani abun, sarki yace dakanka zaka koma, salman yadaure yace to Abba. Lefen da aka kai sai daya tsorata duk yan uwan dasukaje, mamakin irin kayan da aka zuba suke, kamar ba'a talauci a duniya? Kanwar maman salma kam kasa jurewa tai tace kai JAMA'A kayan nan ai sunyi yawa, zainab tace haba hajiya bakomai ai nan kowa yashiga jinjina wa salma lalai kam tagama warkewa, dan gidan sarki? Hmmm. Zeena kam zaune kawai take amma sam ranta badadi yama za'ayi ace salman guda a aura masa yarinyar da iyayenta basufi bayin gidansu ba😡 nan suka ajiye kudin dinkin amarya dana kwalliya, dubu dari biyu mamaki yakama mutane nan aka shiga gulma daga gani Abba saida 'yarsa yai inba haka ba wannan kudi da kaya haka? Shiyasa ma bikin ba'a wani ja shi ba, sudai 'yan kawo lefe nan suka tafi suma suna gulma. A gidan akabar kayan dan kamwar maman salma tace in aka kai kayan can gulma yawa zatai, nan suka debi d'inkakun kaya a karamar jaka suka fita. Salma na kwance zazzabin jikinta yafara raguwar dan bacci ya d'auketa taji guda a saitin kunnenta da sauri ta mike a zabure, dangin mamanta ne suke guda, wata daga cikinsu tace kai yarinya tayi goshi irin wannan al'amura haka? Salma kam kallansu kawai takeyi Asabe kanwar mamansu tace tashi kiyi wanka dalla kinwani zauna kamar wacce za'a kaita gidan marii, salma tace nifa.....Asabe tace so kike kibamu kunya?kin tashi ko sai na miki wanka dakaina? Salma ta mike tare da turo baki tai waje, nan aka shiga guda. Suna zaune ita da kawayenta 'yan uwa, sun sata agaba suna tsokana idanta duk ya cika da kwalla, Asabe tazo tace wai ma taci abinci? Sukace anya kuwa? Nan ta kama hannun salma tai dakin umma da ita tasa aka siyo maltina da madarar ruwa ta juye a kofi tace kafa kai? Salma tace nifa banajin yunwa☹ tace kin kafa kai kosai na mareki? Nan salma ta amsa tana sha tana kuka inta tuno kamal sai taji kamar ta kwalla ihu. Ran Alhamis da safe gida ya cika taf salma na kwance zazzabi yadawo sabo, jin gobe za'a d'aura aure kuma akaita, wank yaro ne yai sallama yace wai ana sallama da salma, Asabe ta shigo d'akin tace tashi kiji inaji angon ne salma ta hade rai takuma ki tashi, asabe tace kin tashi ko kuwa? Salma ta mike ta yayimi hijabin sallarta ta zura tai waje Asabe na kiranta amma ina hartakai kofa, zuciyarta taf take da masifa, sai dai me? Tana zuwa taga wannan bafaden na rannan, yana ganinta ya zube a kasa yashiga jera gaisuwa ita abin ma mamaki ya bata dakyar tace menene hakan? Yana tsugunne ya miko mata envelope takalleshi tace namiye? Yace aikoni akai inkawo miki, tace inji wa fa? Yace mai gidana, tace ina nasanshi?yace wanda zaki aurafa? Sai yanzu ta gane, haushi ya isheta tai tsaki tace kamaidamai kudinsa kace bana bukatar wannan, in yanaso ya birgeni to ya......tunowa tai dakalmar mahaifinta dayace nasani bazaki bani kunya ba, idanta ya ciko da kwalla tace ka maidamai kudinsa bana bukata tana fad'a tai ciki da sauri. Tana shiga kowa ya shiga kallanta ana tsokana, wato dan rashin hakuri shida za'a kaimasa ke gobe shine sai daya aiko aga lafiyarki?haushi ya kamata ko kulasu batai ba tai d'aki ta shiga bargo tasaki kuka. Salma kam hidimarsa yake kamar ba aurensa za'ayi ba su Amir ma abakin mannir sukaji zancen auren. Yau juma'a tun safe gida ya cika makil, salma kam tana d'akin goggo a kwance, Abba ne ya shigo tana kwance idanta duk ya kumbura, ahankali yakalleta tare da zama kusa da ita. Idanunta ta bude ganin Abba yasa ta kakaro murmushi tace Abba, tafad'a ta a kokarin mikewa hannu yasa a kafad'arta yace yi kwanciyarki salma, ta kwanta tare da yin shiru, yace salma ni najamiki ciwon nan ko? Tace a'a Abba, yace nasani salma kiyi hakuri laifinane dana bari yaya ya amsa tun farkon maganar, dasauri tace haba Abba ai nasan dan kun isa danine yasa kuka amsa, yace to meya saki zazzabi? Aranta tace ko mijin fa bansani ba? Nadaisan yana da hadi da gidan saraura tunda taji 'yan uwa nazancen, sai kuma bafaden nan data gani, amma afili tace cutace kawai, Abba yace salma Allah yamiki Albarka, da izinin Allab bazakiyi danasanin wannan auran ba, tai murmushi tare da cewa yaya kamal ya sani? Abba yace ai kamal sam ko babansa yakirashi baya d'agawa bamusan me yake tunani ba, tai shiru..... Abba yace da daddare za'a kaiki nasani ke yarinyace tagari amma gidan dazaki sai kinyi hakuri, tace wani iri ne? Yacr gidan sarauta tad'an juya kai kodai d'an gidan waziri zata aura? Abba dakanshi yasa aka kawo mata koko da kosai taci. Auren in anyi sallar juma'a ne hakan yasa Massallacin gidan sarki ya cika taf da mutane, manyan mutane na sarauta da kuma na milki. Salman na kwance a d'aki yana sharar baccinsa, sai nemanshi akeyi, najib ne ya shigo dakin kamar wasa dan baiyi tunanin zai ganshi anan ba,mamaki ya kamashi ganin salman daI_dai akan gado yana bacci karasawa yai kusa dashi tare da tabashi, cikin abin bacci salman ya bude ido, Najib yace prince me kakeyi hakan? Salman yace don't u see? Najib yace anacan ana nemanka amma kana nan kana bacci😳? Salman yace oh!!! Lokacin auran nasu yayi ne? Yafad'a tare da duba agoggon bango na d'akin, najib yace auransu ko auranka? Salman yai tsaki yace ni wannan shirman auran badamuna yai ba yarinyarce koma wacece kawai ina tausayinta, sannan ina tausayin kaina dan za'asani sharing din daki da wata kucaka😡 ko dayake servant zansamu, Najib yace salman kasan me kake fad'a kuwa? Yace malam kyaleni, najib yace naji amma tashi ka shirya kafin ran mai martaba ya baci, salman ya mike yasaki kwafa irin ta muguntarnan. By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:17 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣1⃣ Haka salman yashirya cikin dakakun kayan sarauta da Mai martaba ya aikomai dashi, shi kanshi yasan yayi kyau najib sai kodashi yake, yai dan karamin tsaki yace I wish wannan auran da budurwar danakeso akeyi,amma meye amfanin kwalliyar? Najib yace zaka fara ko? Dan Allah kazo mu wuce, turarensa ya fesa sannan yasa hula da takalmi ya fito cikin kasaitarsa. Tunda ya fito bayi da 'yan uwa kemai sannu da Allah yasanya alkairi amma kasaita da jin kai irin na salman ba wanda ya amsawa sai najib ne yashiga amsawa. Yana zuwa hanyar fada wasu bayi sukazo suka kewayeshi yace kun fara ko? Najib yace wad'annan fa? Salman yace ai aiki yaganka dan hakannan zasuyi tabinmu har agama, najib yace lalai kace alamace ta ango ya taho, salman ya juya kai ba tare dayai magana ba. Guri yacika sosai su Abba kam suna wani guri da aka ware musu, tsoro ya fara kama Abba shikanshi yafara tunanin kodai saida 'yarsa yai?. Salman haka yai ta ratsawa cikin manyan mutane suna gaisawa, basu dade ba aka shiga huduba ta sallar juma'a, bayan anyi sallah ne aka d'aura auran *SALMAN DA SALMA* akan sadaki dubu hamsin, dan Abba yace sadaki kad'an yafi daraja a aure duk yanda sukaso ko dari abada amma yaki yace hamsin ya isa hakan yasa aka hakura aka bada hamsin. Salman kam baimasan an d'aura auran ba yana waje suna hira da Amir da Najib sai dayaji masu busa da kirari sun matso kusa dashi sunayi nan fa mutane suka zagayeshi, haushi duk ya isheshi jin wai sunan matar salma, wato salman da salma kenan😡? Inama ace wacce yakeso ne take da wannan sunan kuma sukai aure? Da baisan irin kyautar dazaiyi ba yau. Najib ne yaja hannun salman yakaishi gunsu Abba, har kasa salman ya tsugunna yagaidasu, Mustafa yace ikon Allah sai yau mukaga sirikin namu, salman yai kasa dakai, Abba yadaure yace salman ko? Nan prince yace eh, Abba yace kada kamanta amana muka baka😊 salman aranshi yace amana🤔? Amma afili sai ya d'aga kai Abba yakaraji yaran ya birgeshi yace Allah yabaku aman lafiya, Najib cikin murna yace Amin. Salma na tsugunne tana alwala dan baccine ya d'auketa sai da aka tasheta, jin busa a waje da kid'an kalangu yasa mutanen gidan suka shiga sa mayafi suna fita kallo, salma kam abin dake faruwa a gidan sam haushi yake bata, da gudu taga mutane sun shigo suna guda sun tsaya akanta, takarasa d'auraye kafa ta d'ago jitai sunce Alhamdulila an d'aura auran *SALMAH DA SALMAN* jitai gabanta ya yenke ya fad'I cikin rawar murya tace ma naau gud'ar kud'an matsa in wuce, jitai an rungumeta idanta ta rufe kwalla ta zubo mata Asabe tace Alhamdulila salma naji dadi, Allah yakareki daga sharrin makiya. Ahankali hawaye suka shiga zubo mata ta d'aure tace Aunty sallah zanyi, Asabe tace muje in kaiki nan gida ya kara kaurewa da murna zee ma ta iso, sai dai ganin kawarta a wannan hali yasa jikinta yai sanyi. Wajen karfe 6 na yamma Asabe da goggo sun zauna sai gyara amarya sukeyi, dakyar suka lalabata tai shiru har zee tasamu damar yi mata kwalliya, motocin d'aukar amarya suna waje, dan wasu yan zumudin harsun shige. Lifaya ce aka nad'a mata wacce Matar mustafa dakanta ta siyo mata mai tsadar gaske tayi kyau sosai acikin orange din lifayar, ga zee ta mata kwalliya, tasha sarka da d'ankunne silver hakama takalmin kafarta. Sai kamshin humra da turaren wuta takeyi. Bayan sun gamane suka kaita d'akin Abba Tana zaune kusa dashi, Abba yace salma? Tace naam yace kiyi hakuri kinji? Tace Abba kadaina bani hakuri, yace naga salman a gaskiya ya kwantamin tai murmushin yake yace kuje mutane na jira gashi naji ance jarfe 8 akwaI abinda za'ayi acan tace umm... Nan suka mike ta kalli umma datai kasa dakai, kusa da ita taje tare da cewa Umma natafi d'agowa umma tai idanta yai jaa tace Allah yabada zaman lafiya salma bata amsa ba tai waje da sauri jin kuka zai kubce mata. Zee ce a gefenta sai Asabe dake kusa da ita sunzo fita kofa salma tasa kai shima yasa kai aikam suka gwari juna, zee tace sannu sannan ta d'ago tace malam la.......cikin wata irin murya salma taji ance mekuke nufi da nad'e mata kai? Dasauri ta yaye mayafin da aka rufeta tad'ago jikinta ne yashiga rawa ahankali tafara ja da baya tana girgiza kai wasu hawayen bakin ciki na zubo mata. Asabe ta d'aure tace meye hakan kuma? Tafad'a tana kallan mai maganar? Yace Aunty ni... Asabe ta katseshi bamu hanya nace? Yace Aunty.. Takara katseshi tace ka bamu hanya ko? Ahankali ya matsa idanshi taf kwalla Asabe ta fizgo hannun salma da karfi tafara janta sun zo fita kawai ya kama d'ayan hannun salma yace salma haka alkawari yace? Dama akwai ranar dazaki wuce gidan wani namiji bani ba? Takalleshi a zabure hawaye yakeyi shima runtse idanta tai dakarfe batasan sanda kuka ya kufce mata ba, yace isowata kenan ko gidan banjeba nace dan taxi yakawoni infara ganinki amma me? Sai infara ganin motoci, sannan in ganki kinfito da sufar amarya wacce za'a kai gidan wani? Salma mekeke shirin aikatawa rayuwar mu? Girgiza kai kawai take cikin matsanancin kuka tace Yaya *KAMAL* na shiga uku........yaxanyi? Hmmmmmmm babar magana inji kawata koxali🤔 By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:17 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣2⃣ Asabe kam da sauri ta juya tai d'akin Abba dan sanar me. Kamal yakaraso da sauri ya rungumeta kuka take sosai yace salma bazai yiwu ba, u are mine, muje gunsu Abban susan yanda......jin muryar mustafa sukai cikin zafin rai yace wani irin sabon iskanci ne wannan kamal😡? Dasauri salma ta janye jikinta, ya cigaba baka da hankaline? Matar wani kake rungumewa? Kamal yace Dady wai me kake fad'a haka? Yaza'ayi salma tazama matar wani bayan ni?dai_dai nan su Abba da goggo da Asabe suka karaso gun, mustafa yace bayan kai? Kai wa? Cike da mamaki kamal yakalli dadynsa zaiyi magana mustafa ya katse shi dacewa, kad'auka mudun shashashu ne? Tun yaushe ka gama karatu? Kamal yakalli salma sannan ya kalli Abban salma ya maida idanshi kan dady yace dady amma...... Mustafa yace banasan iskancin banza, dan kaga yarinya nasanka shine kadinga raina mata hankali daga kace saura 3wks ku gama sai ka kara cemata 2wks itakuma saboda shirme da yarda dakai yasa take d'auka, to bari kaji nasani sarai kafi 8month dagama makaranta dan wa'inda kwankwaso ya biya muku tare tuni suka dawo, ko sai kai kad'ane karage? Kamal yakalli salma zaiyi magana, tsugunawa tai da sauri tace wayyo ni😭 Mustafa yakalleta sannan yakalli Abba yace Amadu dagata dakanka ka kaita mota dan 'yan daukarta sun gaji da jira yakalli kamal sannan yace to yaya, tare da karasowa ya d'agata. Idanta ya rufe da kuka kawai sa kafa takeyi, dasauri kamal ya karaso kusa da ita yai kneel down yace salma please😥 mustafa yace Amadu ku wuce nace, cikin sanyin jiki da tausayin kamal Abba ya wuce da salma mota. Motocine guda 20 tata tana tsakiya nan akasata mutane harda makota ganin motar bilis yasa suka shiga😜. Salma kam zaune take a cikin mota tai kasa dakai banda kuka ba abinda takeyi zee ma kukan take dan tasan yanda salma kesan kamal, Asabe kam rungume salma tai tafara lallashi sai dai kamar zigata take. Sun isa gidan sarki salma batamasan ina sukeyi ba tadai ji sun yi parking. 'Yan uwa na gidan sarki sun fito taryarsu, nan aka yan Rakiyar bangaren salma, ita kuma su zainab suka riketa sukai bangaren fulani da ita, zee da Asabe na biye dasu. Sai da suka kaita duka bangaren matan sannan suka maidata bangarenta, yan rakiya sun rikice da kallo ganin irin dukiyar da aka zuba a bangaren, falone kato da kofofi uku, d'aya daki ne a cikinsa da bandaki a d'akin nan ne master bedroom, sai kuma dayar kofar da kuma daki ne da toilet aciki, sai d'ayan kitchen ne kato duk da bawani girki sukeyi ba amma anyishi ko akwai abinda zaisa ai girki aciki. Baban dakin aka kaita tanaji mutane nata wasa kayan gidan amma ita ko kallan dakin ma batai ba bare, hawaye sai gudu suke a fuskarta, wata baiwa ce ta shigo tace wai ance duk ku fito za'a wuce, sukace amarya bata shirya ba ai, baiwar tace eh ita yanzu za'a shirya ta zasu taho dashi. Nan suka fara fita, akabar salma ita kad'ai, kifa kanta tai tana kuka yanzu shikenan an rabata da yaya kamal? Wacce irin rayuwa zatai?jin sallama tai dasauri ta zauna tare da gyara mayafinta zeena ce da wasu mutane guda 2, zeena ta yaye mata mayafi aranta tace masha Allah sannan tace salma yanaga idanki a haka? Wani irin kuka kikai haka? Salma ta kakaro murmushi tare dayin kasa dakai. wata daga cikin matan tace hb Amarya yanzu ai an daina irin wannan kukan, zeena ta kalli d'ayar tace Meema Yaza'ayi? Tace gata so cute I wish bata b'ata fuskarta haka ba amma ba matsala zeena tace tnx. Nan meema ta matso ta yaye ma salma mayafin gaba daya ta zare d'ankwalin kanta, itakanta zeena sai datai mamakin gashin kanta, ahankali meema tashiga yima salma kwalliya sun d'au lokaci kafin su gama sai dai me? Duk wanda yaga salma to ba karya sai ya kara kallanta tayi kyau na garari.... Zeena ta shiga fasama meema kai, nan suka d'auko wani ratsatsen kaya wanda kyansa ya wuce tunanin mutum, dark blue ne sai kwalliyar jikinta da akai da golden rigar doguwa ce, ta baya jan kasa takeyi, nan aka d'aura mata gwagwaronta dark blue sannan aka yafa mata wani shara_sharan net golden, aka miko mata takalmi mai d'an tsini golden. Salma tayi kyau na karshe sai dai bata farin ciki sam. Zeena tace kai Amaryarmu karfa kisa kanina ya fad'I garin kallanki nan sukai murmushi salma kam ta juya kai. Nan suka ce mu mun wuce yanzu salman Zai zo ku tafi, nan suka fita suna murmushi. Salma na zaune tana tunanin rayuwa ita dake tunanin auranta da kamal sai gata a gidan wani can da bata sani ba, sannan tace a fili wai ahaka suke nufi zanje? Da wannan net din? Tasaki tsaki daidai nan salman yashigo ko salama baiba dan duk ranshi a b'ace yake da akace wai shi zaizo ya d'auketa. A bakin kofa yatsaya yace ke! Salma taki d'agowa yakaracewa ke! Takara kim d'agowa haushi ya isheshi yakaraso kusa da ita tana kallan kafarsa na tahowa duk da a tsorace take amma bazata yarda yace mata ke ba jitai ansa sanda a tabo mata kafad'a da mamaki tad'ago dan ganin wannan rainin hankalin. *tofah*🙄 Nan idanun ma'auratan ya hadu cikin tsananin mamaki mara misaltuwa salma ta mike tace *YOU?* salman yakalleta ba laifi kyanta ya wuce misali sai dai kamar yasanta, jikin salma ya shiga bari? Tad'aure tace me kake anan Prince? Yace oh kinsani dama? Tace ohhh baka ganeni ba? Wace ka cima mutunci a Buk? Me kazoyi nan? Ko nan din ma biyoni kai? Salman yai wata dariya mai karfi wacce tasa zuciyar salma tagama tsinkewa, sai daya gama sannan yace *SALMA*? Da mamaki ta kalleshi tace eh meye? Yakara dariya sannan kuma ya hade rai kamar zaki yace kina nufin kece matar? Ta kalleshi batare data amsa ba yace yar gidan Amadu u are really something, wato sai da kikasan yanda kikai kika aureni ko? Sai dai kuma I really pity you dan tun daga yau zaki fara regretting yar gidan masu gini. Salma tunda taji yace wai auranshi jikinta yafara rawa, zama tai a gadon dabas tace kai ne mijin😳? Yace ke banasan pretending din banza, zatai magana ringing din wayarshi ya katseta yad'aga. Najib ne yace to ango wato anga mata shine aka ahanyani a mota ko? Salman yakalli salma yace u will be really surprise inka ganta, najib yace to please kazo mutafI yaya zainab sai waya take, salman yace ok gamunan. Salma yakalla yace ke taso muje tace amma....ya katseta banasan wani munafirci taso muje, tace munafirci kuma? Yashareta tace wai da wannan mayafin zani? Yai tsaki yace ke bansan iskanci inkinga dama ki fito, yanakai nan yafara tafiya, itama tsakin tai tare da binshi, ya kalleta kawai yai kwafa yaga alama sai ya mata service😜😜😜😜 By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:17 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣3⃣ Tafe suke yana gaba tana baya, har suka isa kusa da motar najib ya fito da sauri yanacewa Amarya ansha kanshi, salma ta hade rai dan tagane shi, najib yace hmm salman Amaryarmu bata magana ne? Salman yai tsaki yace kaifa banza ne kamar bakasan munafircin wasu matan ba, najib yai saurin kauda maganar tare da cewa bismillah Ango ya budema Amarya kofa dan gimbiya ce😊 Salman yace wa? Nizan bude mata? Salma tace nima ban nema ba😏 ta zagaya ta d'aya bangaren ta bude ta shiga tare da rufo kofar da karfi. Salman ya kalli najib yace zakasha mamaki inkasan wacece najib yace naga itama ba sauki🤔 daga haduwa harkun fara fad'a? Da alama dai kunsan juna. Salman yace abar maganar shiga mutafi yafara kokarin bude gidan gaba najib yace yada haka? Ai a kusa da ita zaka zauna salman yace dalili? Najib yace naga an d'aura auran? Salman ganin baisan doguwar magana yasa kawai ya bude baya ya shiga, salma ta juyo ta makamai harara, yace ke wa kike harara? Tace wanda ya tsargu tafada tare da juyawa tana kallan window. Salman yad'auko waya yana dannawa, najib kam sai lekensu yake ta glass yana mamaki koda ace salman baisan yarinyar amma kyanta ai ya isa yasa yasota, shi jiyake inama za'amai auran dolen indai zai sami irin salma😜. Ba wanda yasake magana acikinsu sai najib dakebin wakar Aashiqui dake tashi a cikin motar, salma kam tunanin duniya ya d'auru akanta jitake kamar duk duniya ba wanda aka tsana kamar ita. A hankali najib yai parking, salman yace nifa natsani irin wannan gun na hayaniya😏najib yace haba salman ka hana ayi komai yanzu d'an dinner din ma bazaka bari ayi lafiya ba?salman Ya kalli salma dake cikin duniyar tunani yace ke tamai shiru yakara cewa ke limamiya! Ta juyo cikin bacin rai ta bugamai wani kallo kuma taki d'auke idanta, mamaki yakama salma yace ke who are u staring at? Tace in baxaka kirani da sunan da aka rad'amin ba kabarshi ya matso daf da ita har tanajin saukar numfashinsa akan fuskarta ya kai bakinsa saitin kunnenta dasauri najib yafita, salma kam numfashinta ne ya tsaya cak!! Salman yai wani murmushi yace how dare u talk to me like that? Dakyar numfashin salma yad'awo tad'aure tad'an turashi tace meye hakan? Yai murmushi yace u have to be careful bakomai nake d'auke ba. Yana fad'ar haka yai waje ta sauke wani numfashi tace wannan wani irin mutum ne? Najib ne ya kwankwasa mata glass a hankali ta zuru kafa ta fito, najib yace salman ku tafi atare plz? Yace kace ta matso, najib yace kid'an matsa ta matsa kusa dashi, najib yace dan Allah ku tafi a tare, salma ta kalli najib tace kacemai karyai sauri, salman yai wani murmushi wato tafi karfin tamai magana, itama aranta tace kaji ko da dadi. Ahankali suka fara tafiya sunje shiga aka ce su tsaya nan 'yan yara da akama anko suka zo suka tsaya a gabansu kuyangi kuma suka fara zuba flower ahankali suke tafiya har suka isa masaukinsu. Abin ya kayatar da mutane ganin shima salman light blue din shadda, mutane sun yaba kyan salma sosai,ga salman ma ba bayaba abun nasu chakwas😜 Sukansu 'yan uwanta dabadan sunsan itace Amarya ba da bazasu yadda salma bace ganin kyan datai. Anfara gudanar da shirye_shiryen da aka tanadar anyi gada, anyi kid'an gwarya sannan yan busa da kalangu, sai kuma DJ. DJ ya kira Amarya da Ango tsakiyar fili, sai dai duk maganar dayakeyi daga salma har salman ba wanda yake kokarin tashi, ganin haka yasa najib yazo kusa da salman yace hb salman so kake ka bamu kunya? Yai tsaki yace toshi Dj din cemai akai yakirani? Najib yace kayi hakuri plz, salman yace to kace ta taso, najib yakalli salma dake daf dashi yai murmushi shikanshi yasan ma'auratan kowa ba sauki amma yazaiyI? Haka ya juya yace Amarya kitashi kuje, salma tace kacemai yafara mikewa ai shine namiji😗 Salman yakalleta tad'auke kanta ganin mutane na kallansu ga dj ya saki murya sai kiransu yake yasa ya mike, ahankali itama ta mike suka nufi tsakiyar fili. Suna tsaye mutane sai barnar kudi suke suna musu liki, salma kam mamaki take sai kace takarda? Suna tsaye har dj yace su koma gunsu, ahankali suka fara tafiya zasu koma, tsautsayi yasa takalmin salma ya turgude tai baya luu zata fadi, da sauri salman yasa hannu ya tarota, nan suka kalli juna salman yace Will u stop pretending?dasauri ta mike tare da matsawa kad'an, ranta duk a b'ace. Nan mutane auka shiga tafi abin ya burgesu...... Nace hmmm By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:17 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣4⃣ Takarasa ta zauna a kujera fuskarnan a hade, najib ya kalleta ya kalli salman yaga shima fuskarnan a hade, yace oh god yad'an matso yace hb prince kad'an saki ranka mana 'yan jarida na kallo fa? Salman ya kakaro murmushin yake, sannan najib yakalli salma itama tad'an kakaro murmushi. Angama shagali nan aka fara d'aukan hutuna kana ganin salma da salman sai kasan murmushin yake suke a hutunan, bayan an gama 'yan uwanta suka mata sallama suka shiga mota, idanta ne ya ciciko ganin Asabe ta sata a motar da aka kawota sannan takalleta, tace salma kiyi hakuri, ki manta da kamal a ranki, yanzu ke matar wani ce dan haka ki kula da hakkinsa. Salma ta kalleta hawaye ya fara zubo mata tace Aunty meyasa kuka had'ani da salman? Cike da mamaki Asabe tace me salman din yai? Tace shikenan Aunty a bar maganar, Asabe tace koma dai menene ki rike mijinki, karki kuskura ki wulakantashi. Salma kam hawaye take ta rike hannun Asabe tace Aunty kicema yaya kamal......dasauri ta katseta tace salma me kike shirin yi? An fa d'aura miki aure, salma tai kasa dakai Asabe tace mun tafi sai munzo, Allah yabaku zaman lafiya. Salma ta bita da kallo hawaye na tsiyaya a idannunta,salman kam yanacan suna sallama da mutane sai can ya shigo shida kamal, lokacin salma kam ta hade kai da gwiwa tana zuba kuka, jin motsin bude kofa yasa tad'an sai_saita kukan salman yashigo ya zauna. Nan suka fara tafiya salma kam sai kuka take. Salman ne ya Kalli salma ta gefen ido dataketa shesheka tsaki yai yace malama dalla kimana shiru kin cikamana kunne, salma tad'ago ta makamai harara, ya juyo yakalleta tare dayin kwafa, najib ya ce salman hakuri zaka bata ba fad'aba. Salman ya kalleshi ta glass sannan yace ni? Yafad'a tare da nuna kansa, yacigaba ni wai kake nufi? Najib yace eh mana, salman yace over my dead body. Salma ta d'ago jajjayen idanunta tace kwantar da hankalinka nima I won't let that happen. Daga nan kowa ya d'auke kai ita ta jingina kanta da window, shikuma yad'au waya. Najib yace oh god....... Sun isa gida sai dai a bakin gun sukaga su zeena a tsaye nan suka kama salma sukai ciki da ita, dakinta suka kaita su ka sata a gaba wai sai taci abinci, nan ta daure tad'anci kadan sannan suka mata sallama suka tafi. Mikewa tai tacire gwagwaron tai alwala tazo tai sallar ish'ai tana zaune agun ta zuba uban tagumi , salman ne ya shigo dakin tare da sallama ta amsa kamar bataso ya shigo ko kallan inda take baiyi ba ya bude drawer yad'au kayan baccinsa yashiga toilet din dakin. Ruwa ya watsa sannan yasa kayan yana fitowa ya fad'a gadonsa, salma ta kalleshi da mamaki tace malam meye hakan? Ya d'ago yace mefa? Tace anan zaka kwana? Yace da dakinki ne? Tace ba haka nake nufi ba amma tunda nazo nan aka kawoni, yace wannan matsalarkice sai kinemi inda zaki kwana ko ki kwana a kasa, tace what? Yace oho kardai ki kuskura kibar dakin nan dan bayi suna falo in baki kwana anan ba zasu fad'ama fulani dan haka dolene ki dinga kwana a kasa, tace dole? Yace yes kinada jaa ne? Tace mikomin bargo inshimfida a kasan? Yace bargo? Nikuma fa? Tace sai ka yaye bedsheet din ka rufa dashi. Salman yace kin ma rainan hankali ana sanyin zakice inkwanta na bargo? Ko in ja bedsheet? Ce miki akai zan iya bacci akan katifa zalla? Ran salma ya b'aci tace to ya kakeso inyi? Yace oho miki amma bazanyi abinda kikeso ba salma ta cika tai taf sannan tad'aure tace miko pillow, yace I can't do that dan ni haka nake bacci in kwanta a d'aya in kuma rungume d'aya salma tai tsaki tace u are so selfish tana gama fad'ar haka ta mike tai hanyar kofa, dasauri salman yai dungure ya damko hannunta yace are u crazy? Tace mayb yace naga alama to ina zaki? Tace falo inje in kwana yace baki fahimci abinda nake nufiba kenan😡 tace ina zan fahimta? Yace go back yafad'a yana nuna mata cikin d'akin tace I can't🤔 da karfi yasa hannu ya fincikota yai ciki da ita yasa makulli ya cire makullim yasa a aljihu. Salma ta fizge hannunta tace karka kara tab'ani😠yace ina kika ga jikin daza'a tab'a? Haushi ya isheta kawai tashige toilet, salman yai tsaki yace kawai za'azo a takuramin nida dakina😏 wannan aure ne ko takura🙄? Nace ba ka tambayeni ba salman katambayi kanka😏. By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:17 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣5⃣ Salma kam tsaye tai a band'aki kara karema bandaki kallo tai, aranta tace band'aki shine akama wannan kwalliyar oh, sai kuma tai tsaki tace wlh nikam an cuceni mezanyi da salman?fuskarta ta shiga wankewa a sink dan bazata iya wanka a gidan da batasan kanshi ba, tad'an dade kafin ta fito, salman tagani kwance ya rungume pillow yana narkar bacci... Haushi ya isheta ganin ko bargon baiyi karar ajiyewa ba takai hannu kamar zata dakeshi, tad'an daki iska sannan tace d'an rainin wayau ni da wannan ai gwara abarni ko shekara 10 zanyi a barni na jira kamal ko a had'ani da d'an garuwa😏. Ta koma kan sallaya ta tada sallah, ta dade tana nafila sannan ta d'aga hannu tashiga jero adduo'I tanayi tana hawaye, sai wajen 2 sannan ta mike dan kashe wutar dakin, ta kashe ta juya zata zauna taji ance I can't sleep while light is off, dariya ma abin yabata a hankali tace dayake nepar a gidanku take😏 salman yace I can hear u, kuma ki kunnan wuta,tace gaskiya ni ban iya bacci da haske ba, yace wannan kuma matsalarki ne. Salman yace ki kunna min wuta ko? Dasauri ta matsa daga gun takaraso inda yake ta kunna yar karamar fitila ta dum light dakd side bed dinshi, zaiyi magana tai saurin juyawa zata koma kan sallayarta hijab dinta ya kamo ta baya yace ke! Ta juyo tace waye ke? Yace ke wannan hasken yamin kad'an,nida d'akina fa baki isa ki takuran ba😠 ta fizge hijab dinta tace sai kai hakuri da wannan inba hakaba ka bani makulli na fita🤔 tana kainan ta karasa kan sallaya ya kalleta taredayin kwafa. Itakam salma nan ta kwanta tare da takure jikinta, kan kaceme? Bacci yayi awon gaba da ita. Kamal kam tunda ya tsugunna a wajen nan bai tashi ba mahaifinsa yace kar wanda ya kulashi nan kowa ya watse aka barshi, sai wajen karfe 10 Abba yakasa jurewa yazo dakanshi ya d'agashi suka shiga ciki, sai dai kamal sam yakasa ko magana kawai idansa zaka kalla kasan yana cikin matsanancin bakin ciki. Da Asuba karfe 4:30am salman ya tashi,ya sauko yaga yanda salma ta takure dariya tabashi yace kad'an kika gani tunda ke kika ce ni kikeso, harzai samata bargonshi sai kuma yafasa yai toilet. Alwala yayi sannan ya fita, salma kam gajuya da rashin baccin wuri ga jikinta ba karfi saboda zazzaben datai agida yasa bacci mai karfi yai gaba da ita, sam bata farka ba lokacin sallah. Salman na dawowa ya kalleta tananan ayarda ya barta yai tsaki yace a waje kamar ustaziyar gaske amma ace mutum ko sallar asuba bai farkawa? Daga gani ba yau tasaba makara ba🤔 karasa wa yai inda take ya d'au sandar dake ajiye a d'akin yad'an zungureta dashi, cikin bacci tace Abba kafito? Salman ya tabe baki sannan ya kara zungura mata da karfi, cikin razana ta mike, sai dai me? Saman tagani ya harde hannunsa biyu. Haushi ya isheta tace wani sabon cin mutunci ne wannan? Bai mata magana ba ya juya ya hau kan gado takara cewa haka ake tashin mutum daga bacci?yace ke ni da sanyin safiyarnan bansan magana meye dan an zungureki?tace what? Kwanciya yai tare da juya mata baya, tai toilet batare data mai magana ba. Alwala tai sannan ta fito ta tada sallah, bayan ta idar ne ta kwanta wani baccin ne yasake d'auketa. Wajen karfe 9 sukaji anan knocking, salma ta mike da sauri ta bude kofar, wata baiwa ce tace ranki ya dade dafatan kin tashi lafiya? Salma tace lafiya, baiwar tace sunana Hanne baiwarki, salma tace baiwa? Tace eh zuwa nai nasanar dake karfe 10 zakuje gaida sarki, sannan karfe 12 baki zasu fara yimuku sallama. Salma tace toh😳 hanne takara kasa dakai tace karfe 9:30 zan kawo abinci, salma tace hmm to, nan hanne ta juya salma takoma ciki sannan tace nizan iya zuwa gun sarki kuwa? Tai maganar a fili, salman yace I can hear u, salma tad'an murguda baki tace mutum sai kunne kamar maciji? Yace inajinki fa? Tace oh ni😱 ta shiga duba drawer ko zataga kayanta sai dai kayan salman ne a jere tace oh wai nI ina akasamin nawa? Salman najinta amma ya shareta ya mike ya shiga wanka tabishi da harara. Tana zaune ya fito sanye da kayan daya shiga dasu yazo yad'au kaya a drawer yakoma toilet, tace ba laifi he has manner🙄 ta mike takara duba kayanta, sai dai bata gansu ba, salman ne ya fito sanye da wata dakakiyar shadda ya kalleta sannan cikin magana kamar bayaso yace ki duba akwatina, yanakai nan yaI waje ta bishi da harara wato yasan inda suke shine ya shareta, ta mike ta hau kujera ta janyo akwatin dake kusa aranta tace wad'annan akwatin masu kyau sune na lefen kenan? Cikin hanzari ta duba tarr da d'auko wani swiss less mai masifar kyau tace amma kayan sunyi kyau nan tashiga neman hijab dazata sa, sai dai babu da alama wanda tai sallah dashi shi kad'aine gashI na sallar irin burum din nan ne, kawai ta wuce tai wanka, tasa kaya sannan tazo ta shafa mai ta murza huda, nan taji an murda kofa ta juyo salman yace malama ki fito ga abincin anan, ta kalleshi shima kallan ta yai she is natural beauty haka yaji zuciyarshi tafad'a ya kauda zancen yace mekike shirin yi hakan? Ganin ta d'auko hijab din ta zura, tace me nake kuwa? Yace ki tambattar kin cire hijab din nan kinsa mayafi kalar kayan, yarinya sai kace a rigar fulani😏 Ta kalleshi tace waya sani? Ya juya batare daya amsa mata ba tai raurau da ido tace da ace mutumincan karami ne da sai na mai dukan tsiya💪🏼👊🏻 Nace hmm 😜 By Ayusher Mohd📚 [10/16, 11:17 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣6⃣ Mayafin kalar kayan tad'auko sannan tasa takalmi flat ta fito falon, salman na zaune a dinning kuyangi na tsaye a bayansa, ta karasa gun cikin nutsuwa. Kuyangin ne suka gaisheta a tare ta amsa tare da zama a falon, salman yai gyaran murya da alama magana yakesan yi salma ta mannamai, yasake yi hakan yasa tad'an dago yamata alama da fuska akan tazo taci abinci, ta juya kai tace nakoshi in ka gama mu wuce, ya d'aga kafad'a alamar ruwanta sannan ya kammala tare da mikewa yai hanyar waje, salma ta mike tare dayin tsaki tace mutum sai girman kai ai yacemin in taso😠, ta mike hanne da wata baiwar nabinta a baya salman tagani tsaye a waje takarasa nan bayi maza suka rufo musu baya, salman yad'aga kai sama mutane na gaisheshi amma ga mamaki salma ko amsawa bayayi. Sai da suka kusa isa fadar sarki, salman ya matso daf da ita yace u have to be careful dan karki kuskura ki bari wani a cikin gidan nan yasan irin zaman da muke, mark my word. Salma ta d'ago ta kalleshi gabanta ne ke fad'uwa tadaure tace sai ka fad'amin😗? Bai bata amsa ba ya cigaba da tafiya, sun isa fadar nan aka musu iso, bayan sun shiga salman ya tsuguna itama ta tsugunna nan suka gaida sarki ya amsa cikin farin ciki, nan 'yan fada suka fita suka barsu, sarki yakalli salma yai murmushi lalai yama d'anshi zabi mai kyau dan yarinyar ta kwantamai, yamaida idansa kan salman yace salman ina tsananin farin cikin wannan auran dan Allah ka rike yarinyarnan amana, kaji? Salman yai kasa dakai yace insha Allahu Abba, salma ta kalleshi ta gefen ido tace sai kace gaske ji yanda yakoma innocent😏. Sarki yace jeka waje salman inasan magana da sirikata salman ya d'ago tare da kallan salma sannan ya mike yai waje, sarki ya kalli salma yace 'yata matso, cikin kunya salma ta matsa kad'an sarki yace salma agaskiya ba yaba da yanda kike Allah yasa abinda nagani hakan yake, tai kasa dakai batare datace komai ba, yace salma dan Allah ki rike yaron can da mutunci ki kula dashi, yaro ne maraya he is so lonely, salma tad'an dago idanta maraya? Ta maimaita aranta yace eh salma maraya ne mamaki ya kamata ya akai yasan abinda ke ranta? Sarki yakatse tunaninta dacewa Allah yabaku zaman lafiya tai kasa da kai batace komai ba, yace jeki salma ta mike tare damai sallama. Tana fita ta saki ajiyar zuciya tare da dubawa ko zataga salman, sai dai ba alamarsa, hannece ta karaso tace ranki ya dade muje inkin gama, salma har zatai magana sai kuma ta fasa tace muje. Part dinta suka koma hanne tace sai gobe zaku gaidasu fulani tace to tare da shiga ciki, daki ta koma ga mamakinta salman taganI zaune yasa earphone a kunnensa haushi yakamata ko kallansa batai ba ta karasa kan karamar kujerar d'akin ta zauna tare da kifa kanta ajikin kujerar, tunanin rayuwarsu da kamal tafara, yanda yasota yakuma kula da ita, dashi ta aura tasan da sunanan suna diga luv💖 amma gata yau ta auri wanda kallansa batasan yi shima haka. Tunaninta yayi zurfi batasan sanda hawaye yafara zubo mata ba, muryar salman taji da alama waya yake, jitai yace kai fa dan iska ne najib ni kakema zancen wata amarya? Bataji mai akaceba sai jiganI tai yad'an kalleta sannan yace kai har kana tunanin akwai wata 'ya mace daxanyi lokacin ta? Ni ai a tarihin rayuwata ba mace kaima kasani, ganin yanda salman yai shiru daga ji magana ake sai jitai yace banda lokacinka sannan zancen lokaci kuma mu zuba mugani, yana kainan ya katse wayar sannan yakalli salma yace ke kuma meye na kallona ina magana? Tace mezan kalla? Yace banasan kallo gwara ki sani, haushi ya isheta dama a wuya take tace malam nifa nagaji da bakaken maganganunka salman nifa nasan nafika san rashin auren nan dan ni inada wanda nake so kaifa? Bana tunanin kasan me kalmar so take nufi, sannan.....dasauri ya katseta yace kinada magana ne? Tace ai maganar nakeyi yanzu😡 yace banjiba ko zaki maimaita😏? Bakin ciki ne yazoma salma wuya tarasa mema zatace kawai ta harareshi tare da cewa haka maraya yake?I thought mara uwa ba haka suke ba? Cikin hanzari taga salman ya sauko idanunsa ya kad'a yai jaa yakaraso inda take ya fizgota daga kan kujera sannan ya matseta a jikin bango, idanta ta runtse da karfi, ko miyau takasa yad'iya salman cikin zafin rai da wata irin murya yace *WHAT DO U KNOW*? Jikin salma yafara rawa, salman ya kara matse mata hannu har saidatai karamin kara yace *HOW DARE U TALK TO ME LIKE THAT?* I can tolerate anything but don't u dare to say something like that😡.. Salma kam jikinta rawa kawai yake yana gama fad'ar haka ya saketa tare da d'aukan makullin mota yabar dakin, idanta na rufe sai dataji ya bugo kofa da karfi sannan ta bude ido a hankali jikinta har a lokacin bai daina rawa ba ta kalli hannunta dake mata zafi, ganin guntai yayi jaa dakyar ta furzar da wata iska sannan ta tsugunna tare da rike kanta, tace me nace da ranshi ya b'aci haka? Ahankali hawaye yafara zubo mata tace yaya kamal yazanyi? Nima kaina jikina rawa yake ganin salma acikin wannan yanayin📚 [10/16, 11:20 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣7⃣ Salman yana fita mota ya fad'a yai hanyar Buk, tafiya yake amma ransa duk a b'ace, inda najib yake ya nufa, a kusa da makarantar Buk yake da zama, najib bad'an kano bane daga bauchi yake, karatune yakawoshi nan. Salman yai parking din mota ya fito ya nufi d'akin najib, knocking yai najib dake zaune yana kallo yataso ya budemai, cike da mamaki yake kallan salman sai dai kafin ya firta wata kalma salman ya ture hannunsa dake jikin kofa ya wuce cikin d'akin, najib yakalleshi yace Ango? Ya haka? Salman ya fad'a gado tare da d'aukar remote yace waye angon? Najib ya rufe kofar tare da karasowa yace salman bai kamatafa aganka a wajeba yau🤔salman yace tunda kaine ubana ba? Najib yace Allah yabaka hakuri dagaji ranka a b'ace yake, salman yai tsaki tare da canza tasha yace nifa banajin zan iya sati 1 da waccen 'yar rainin hankalin a d'aki d'aya😏 najib yace haba salman meyasa kake hakane? Kasani sarai su ishaq dasaninsu suka tinguno zancen auren nan, plz ka jure mubasu kunya. Salman yace yarinyarce kanta na rawa tagama rainani, sai kace ni din sa'an tane😠. Najib yace salman yarinyar nan fa batada laifi ina ganin yanda kake mata, ni naji dad.....salman yakatseshi yace kasan wacece ma wai? Najib yace naji dai Amir yace 'yar skul din mu ce, salman yace kyale banza shi baisan me ake ciki ba sai yaje yana yad'a maganarsu mannir, wannan 'yar rainin hankalin nan cefa mai *Ninja*😏najib yace ninja? Salman yace kaifa banza ne ninja mana basune suke rufe fuskarsu da wani bakin kyalleba? Najib ya kwashe da dariya yace amma prince sai a hankali nikaf din ne ninja? Yace to yarinyar cefa? Najib yace badai wacce nakusan bigewa ina koyon nan ba? Salman ya juya kai yakalli gefe sannan ya ceji baki yace ita fa, najib yace ita😳? To dama ka santa ne? Salman yace dalla malam inazansan wannan kucakar?nifa an cucenI wlh, najib yace amma ta hadu akwai kyau😁. Ran salman ya b'aci yad'au pillow ya makamai yace cemaka akai kyai shine komai?nan dai sukaita musunsu nikam naja jiki nabar gun😒. Salma kam ta dade kafin tadawo normal nan ta gyara d'akin dan taga falon har an gyara kafin su fito ankuma sa turaren wuta, bayan tagamane 'yan uwa sukaita zuwa yi mata sallama sai azahar tasamu nutsuwa tai alwala tai sallah, so take ta zaga taga gidan sai dai kunyar hakan takeyi, hakan yasa kawai tazauna a d'aki ganin qur'anI yasa tad'auka tafara karantawa, jitai cikinta na kara tasanI yunwace amma fitina irinta salma taki fita taci. sai karfe 2;30 hanne ta kwankwasa salma ta bude, tace ranki ya dade ankawo abincin rana tace to tare da mikewa nan tazauna a dinning ganin abinci kala_kala yasa tace hanne abincin ai yai yawa🤔 hanne tacs haka ake kawowa sai dai inkungama sai akwashe, salma ta girgiza kai tace oh nan tafara cin abinci, taci sosai sannan tasha lemo ta koma d'aki. Hartai isha'I salman bai dawoba hakan yasa ta kwanta a gado ta shige bargo, dan sanyi akeyi, jiya data kwanta a kasa sanyi ya ratsata ga ba bargo, da ciwon jiki ta tash. Jinta mike akan had'aden gadon d'akin yasa tasaki ajiyar zuciya, takwanta tashiha tunanin masoyinta, da ace tanada waya dako Abba takira taji lafiyar kamal😞 tana tunani bacci mai karfi yai gaba da ita. Salman sai 11 ya dawo ya shigo, ganin d'akin dulim ba wuta yasa ya kunna, mamaki ne yakamashi ganin salma tai dai_dai akan gadonshi, yakarasa cikin bacin rai yad'au sandarshi ya zunguro ta ta farka cikin razana tare da rike gun, ganin salman yasa ta hade rai tace malam banasan haka, nafad'ama kadaina zungurata salman yai murmurshI 😏yace kinfisan in tab'aki? Dasauri tace karka kuskura ehe😗 yace to mike mai guri yazo ai kin mori gadon, salma kam taji dadin bacci akan gado tace ina zani? Yace inazaki? Inda kike kwana mana🤔tace tab aikam yau bazan yarda ba sai dai kanani pillow da bargo😕salman yace bakya ganewa ko? Yafad'a yana nuna kansa, tace oho ko mezakace baxan yadda insake kwana a kasa ba😠. Salma yace matsalarkice wannan sannan yad'au rigar dayake bacci da ita ya wuce toilet ta murguda baki tace ai naga alama sai nima nadinga zakewa😠. Ai naga yanada d'an manner nasan yanda zanyi yaban bargo, Hijab din sallarta tad'auko tasa a tsakiyar gadon, yana fitowa ya kalleta yace baki sauka ba? Tace oho gashinan na raba mana ni nan bangaren kai nan, salman yai wata dariya yace what? Gadon nawa kika raba harda wani ni nan ke nan? Tace eh sannan kar wanda ya kuskura ya gangaro bangaren d'an uwansa😏 salman yace lalai kin girma dayawa tace da nid'in yarinya ce? Yace kin cire hijab dinnan kin sauko ko kuwa? Tace kazabi d'ayan uku, ko in koma falo na kwanta, ko kaban bargo ko kuma mu kwana a haka😏 salman yakalleta yace in zaba? Tace eh u have to choose a'a bama haka ba u most choose😎.... 😳🙊nace lalai salma an zake😜 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣8⃣ Salman yai ajiyar zuciya yace ke karki kuskura kib'atamin rai a daren nan dan zakisha mamaki, salma tad'an juyakai batare datayi magana ba, salman yace kwanta!in so kike mu kwana tare😏 dasauri ta juyo tace na'am? Yace eh ba haka kike son jiba? Ta mike daga kan gadon tace yaza'ayi mukwana tare😳? Salman ya matso inda take yasa hannunshi a kugunta ya janyota jikinshi, da sauri ta runtse ido, yai wani murmushin mugunta yace ba haka kike so ba? Ta d'aure tazare jikinta tace a'a ka kwanta😞. Salman yace a'a mukwana taren ko? Dasauri ta girgiza kai tace a'a nabarma bargon da pillow d'in yaI kwafa aranshi yace kin d'aukan bansan burga zakimin ba? . Kwanciya yai tare da jefo maya pillow din, ta amsa tarr da kallanshi☹, sunyi shiru dukansu kowa da abinda yake sakawa,can tad'aure tace sorry cikin sanyin murya, shima cikin magana mai sanyi yace 4 what? Tace maganar dana fad'a dazu I think bai kamata nafad'a ba, salman yad'anyi juyi yace at least kinsani, tace eh amma kaima u overreacted yace so kike nima in baki hakuri? Tace in mutum yai abinda bai daceba hakuri yake badawa ai, yace in hakane I can't zatai magana yace karki damen bacci nakeji🤔 aranta tace kamar nadamu muyi maganar😒. Karfe 4 ta tashi tai alwala ta fara nafila batai minti goma da tashi ba salman ya mike ganin tana sallah kwarai yaji dadi aransa, mikewa yai yashiga toilet shima yad'auro alwala ya fita, harya dawo tana zaune tana karatun qur'ani sai dai a zuciyarta takeyi. Wucewa yai ya hau gado sai dai ba bacci yai ba waya ya d'auko yana dannawa. Wajen 7 ta kwanta yana kallanta sannan shima ya kwanta, basu tashiba sai da hanne tai musu knocking, salma ta mike tare da bude kofar, hanne tace ranki ya dade ku shirya zaku gaisuwa gun matan gidan, tace to nagode, hanne tace aikin nane ai. Salma takoma ciki tare da kallan salman tace zamu gaisuwa, yai tsaki tare da juya mata baya ta makamai harara aranta tace so rude. Kaya ta d'auka ta wuce toilet tai wanka ta goge jikinta tasa kayan, tana fitowa ya shiga ta kalleshi tace mutum sai isa🤔? Yace I can hear u dasauri ta rufe bakinta, ta shafa mai tare da murza hoda, ta zura kwalli tayi kyau dan dama mai kyan ce. Mayafi tad'auka tare da cewa dole insa akawomin Abba yad'inkon hijabai ko biyu ne ta yafa mayafin tai falo, shayi ta had'a ko kulolin bata budeba, ta kurba ruwan tea din jin daxafi yasa ta ajiye tashiga tunani, ko ina yaya kamal? Wai ahaka zata kare rayuwarta a gidan nan? Kwakwalwarta ta cunkushe da wannan tunanin da basu da amsa, batasan salman harya fito ya zauna a kujerar gefenta ta d'ayan bangaren, jin motsin bude kula ne yasata ta d'ago wata baiwa ce ke bude kwanukan tana tambayarshi abinda yakeso? Salma takalleshi ta tabe baki, a ranta tace abincin ma sai an budema? Ko kallanta baiyiba itama tad'auke kai tashanye shayinta ta mike da sauri hanne ta karaso tace ranki ya dade bakici abinciba ai😞? Salma tace banajin ci ne hanne karki damu, hanne tace jiyamafa bakice na safe ba, salma tace nakoshi ne, hanne zatai magana salman yace kin min shiru ko kuwa? Batace ta koshi ba? Hanne tai kasa tace yahkri ranka ya dade, salma ta kalleshi ranta in yayi dubu ya b'aci ta koma falo ta zauna a kujera batare datace komai ba. Salman harya gama sannan, ya mike tare da kallanta dasauri hanne takarasa gunta tace ki taso, salma ta d'ago ganin salman na kalleta ta harareshi tare da d'auke kai, ya ce taso mana? Ta mike fuskarnan a hade suka fito a jere ya matso yace kin manta abinda nace miki ko? Karki bari wasu susan halin da muke ciki ta kalleshi tace kaikuma fa? Yace ni me? Tace shikenan. Ya juya kai nan suka wuce bayi nata gaisuwa, salma na amsawa ya matso yace kidaina amsawa ki wuce kawai tace amm...yace bansan musu tad'an turo baki batarr datayI magana ba haka suka karasa bangaren hajiya karama tana zaune a kilisarta sun shiga sun gaisheta ta amsa tare da tambayar salma yazaman bakunta, daganan bata sake magana ba shima salman haka, nan suka taso sukai hanyar bangaren hajiya babba itama sun gaisa tad'an tambayi salma koda abinda takeso? Tace a'a nan ma taga sunyi shiru har suka taso, mamaki ya isheta haka ake rayuwa a gidan bad'an hirar rayuwa da shakuwa? Sun isa bangaren fulani zasu shiha ishaq ya taho shida mannir tundaga nesa ishaq kebin salma da kallo har karkata kai yake, suna isowa kofa ya kura mata ido sam yamanta da salman, sai da mannir ya kula yadan tabashi sannan, itakam salma duk ta tsargu ganin irin kallan dayake mata, ishaq ya had'eyi yawo tare da cewa Ango kasha kanshi😁 salman yaI murmushi tare da cewa muje ciki ishaq ya kalli salma yace Amarya muje😁, takalleshi tareda yin murmushi ai jiyai kamar ya fad'I har salma ta shige ciki itada salman ishaq bai kula ba sai da mannir ya matso yace yaya me kake kitsimawa? Ishaq yace mannir waccen yarinyarce matar salman? Mannir yace eh mana dan ma baka ganta agun dinner ba🤔 ishaq yai ajiyar zuciya yace amma na cuci kaina ai dani ta dace gaskiya da sake😠. Mannir yace sai hakuri dan tazama matar kanninka, haushi ya ishi ishaq yace bazan yarda ba kasan irin wannan matar nake dreaming arayuwata? Najib yace yaya mai kake shirin yi? Yace I have to think amma bazan bari ta kubcemin ba😕 ishaq😳 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.1⃣9⃣ Salma da salman zaune a gaban fulani, sun gaisheta ta amsa fuska a sake tare da cewa salman da ai jiya kasa hakuri nai nafara tunanin inje inga salma da kaina dan randa aka kawota banganta sosai ba saboda mutane dake bangarena😀. Salman ya kalleta yasani sarai munafurci ne amma sai yai murmushi shima yace gashi ai tazo gaisheki, fulani ta kalli salma tace salman kayi dace yarinyar tamin sosai😊, ya kalleta sannan ya kalli salma yace nima tamin fulani😊, salma ta kalleshi tasan sarai karya yake amma batasan meyasa ta jin wani abu aranta? Salman ne ya kalli fulani zai yi magana yaji an turo kofa, baijuya ba dan yasan su ishaq ne, dasauri ishaq ya karaso ya zauna kusa da fulani, ishaq ya kalli salma yace Amaryarmu ya kike? Salma tad'ago ta kalleshi ganin yanda yake kallanta yasa tai kasa dakai tace lafiya, yace kanina dai baya wahalar dake ko? Takalli salman, tai murmushi tare da cewa a'a, ishaq yad'an hade rai yace salman akula da ita fa? Salman yace basai ka fad'aba, maganar taba ishaq haushi amma ya daure harsu salman suka fita yai tsaki yace ni wlh an cucen. Fulani datasan halin d'anta sarai inyaga kyakyawa tace kul! Wlh ishaq ka fita daga idona, yace menai kuma? Tace nafad'amaka dai dan nasanka. Salma kam suna isa d'aki ta kalli salman tace kai nafijin dadin fulani kamar kunfi shakuwa😀 gaskiya tanada mutunci, amma.....wani mugun kallo yawatsa mata yace will u keep ur mouth shut?tace me kuma nai? Dan nace fulani nada..karasowa yai ya jawota jikinsa yace what did u know? Idanta a runtse, ahankali ta bude idanunta ya kalleta jiyai wani abu na tsirgamai dasauri ya saketa, ya juya baya yace in bakisan komai ba kiyi shiru banasan magana😏 itama ta juya tace to. Falo salman ya fita, ya kunna tv, ta fito ta tsaya a jikin labile tace aran waya please? Ya juyo yakalleta yace bangane ba? Tace uhm Abbana nakesan ma waya, yace sai kije kimai ai🤔tace to ai banda waya☹. Kallenta yai tare da murmushi ya taso ya shigo d'akin tare da d'auko wayarsa dake kan side bed, ya kalleta yace baki da waya?tace eh mana baka kula ba? Yai dariya yace in these era? Tace to dole ne? Yace a'a ba dole bane amma in har kinaso inbaki aran wayata kidinga waya tofa dole kidinga bin umarnina😉 , tace da bana bi🙄? Yace inafa kike bI? Tai shiru can tace ai kai din ne, yace ni me? Tace kaima kasani ai yace bansani ba, tace to yanzu dai kaban nai waya sai musa rule din daga baya, yace a'a banyarda ba, ta turo baki tace to naji zan d'inga bi bani nai wayar, ya mika mata tare da zama akan gadon, takalleshi tace bazaka fita ba? Yace infita kimin bincike a waya? Tace ni😳? Yamata alama da ido yes, ta koma can jikin kujera ta danna number Abba, ringing biyu ya d'aga. Tai sallama ya amsa tace Abba salma ce, yace salma nagane ya gida? Tace lafiya Abba yasu umma? Yace duk lafiya, tace Abba yaya kamal fa? Salman dake zaune ya d'ago ya kalleta dama tanada yaya? Sai dai yanda yaga ta kalleshi ta kuma sa hannunta ta toshe wayar yasa jikinshi yabashi da wani abun, Abba yace salma meke damunki? Wani kamal kuma? Tai kasa da murya tace nasani Abba so nake naji ko yana gari ko ya koma? Abba yace bansanI ba kuma indai akanshi zaki dinga kira to karki sake kirana tace Abba.....jitai an kashe tace Abba☹. Salman ne ya taso tare da fizge wayarsa yace daga wayar farko harkim b'atamai rai? Tace bafa haka bane😕yakoma jikin gado ya tsaya yace bari inkira inji dakaina me kikai?tunda ke dama haka kike dasan b'atama mutum rai😏. Dasauri ta taso tace dan Allah karka kira, takaraso gunsa tace karka kira plz, ran Abba baci zaiyi inyaji kanannan nai waya, salman yace ohhhh kinsan bakida gaskiya kenan, kamal ko? Tace a'a mikon wayar ingoge number Abba, yace naki yafad'a tare da d'aga wayar sama, tafara dage tana kokarin kamowa, kafarta tad'anyi rawa tafada jikin salman wanda shikanshi d'agen yai dama kafarsa ba a daidai takeba nan sukai baya dukansu suka fad'a akan gado, salma tafad'a saman sa. Ahankali suka bud'e ido, zuciyoyin biyu suka shiga bugawa salma kallanshi take shima haka, dasauri tafara neman tashi salman yai saurin sa hannunshi a kugunta ya rikota ta kalleshi, yaI murmushi yace haka kikeso dama ina kuma zaki gudu? Tace yaushe nace haka nakeso? Tafad'a cikin shagwaba, ya kwaikwayi maganar ta, ta turo baki tace sakeni plz? Ahankali salman yasaketa ta mike dasauri tai toilet, shikanshi jikinshi tsima yakeyi key yad'auka yai waje.... Hmmmmm By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣0⃣ Salma ta dade a toilet ba abinda takeyi tana tsaye, jin motsin bude kofarsa yasa ta fito daga toilet din, akan gado ta zauna tare dayin ajiyar zuciya. hanne ce ta kwankwasa mata, ta bude tare da cewa hanne ya akai? Hanne tace ranki ya dade bakiga gidan ba kuma naga ko falo bakya fitowa, Salma tai murmushi aranta tace wani gida tunda basan juna muke ba, afili tace muje kirakani, tare suka dinga shiga salma tayi mamaki ashe akwai wani d'akin bayan tagama dubawa tad'an zauna a falo, hanne ce ta kawo mata madara nan salma ta amsa tasha, salma tace wai haka zanta zama ba abinda nake? Hanne tace eh mana aikinki shine ki huta, salma ta mike tare dacewa nama tuno, littafinta na makaranta tad'auko tafara dubawa, itakanta tausayin kanta takeyi tanasan karatunta amma batasan kozata cigaba ba. Yauma sai 9 salman ya dawo lokacin salma na d'aki rike da littafinta salman yashigo tare da sallama, salma ta amsa batare data kalleshi ba ya shigo yare da cewa yau kuma karatu ne ya motsa? Tace eh thanks to someone, I can't even finish what I start🤔 salman ya karasa kusa da ita yace is that someone Me? Yafad'a tareda nuna kansa👉🏻. Ta d'ago tace eh mana, ya juya tare da cewa ko kika ja ma kanki ba? Tace hmm wai kai yaushe zaka koma skul? Yace ke share sai sanda nai ra'ayi tace ra'ayi? Yace eh ko kinada ja? Ta tabe baki a hankali tace dama mutumin da bai zuwa makaranta ina zaici jarabawa?. Salman yace I can hear you, dasauri ta rufe baki tace wannan wani irin mutum ne? Can tace hmm nikam zan koma d'akincan da kwana😞yace ban bada permission ba, tace ehye? Yace kin manta menace miki ko? Tace banmantaba amma....kallon daya mata yasa tai shiru, ta kike ta fita ganin ya shiga toilet, pillow da bargo tad'auko a d'akin ta dawo, yana fitowa ya kalleta baice komai ba ya kwanta. Tanaso ta tambayeshi yaci abinci? Amma takasa. Salman kam yana kwanciya yai bacci, salma tayi shimfid'a ta kwanta, sai dai ta dade kafin bacci ya d'auketa. Yau kwanansu 8 da aure sai dai rayuwarsu tananan ayanda take. Salma kwance Cikin bacci takejin kamar ana nishi, idanunta ta bude tare da kalan gadon da salman yake, da yake da haske yasa taganshi a durkushe, da sauri ta mike ta matsa kusa dashi, ganin yanda yake zufa gashi ya rike kirjinsa sai nishi yake da kyar yasa dafashi cikin kid'ima tad'an birketoshi kankameta yai yana *inalilahi wa ina ilaihi Raji'un* salma ta kankameshi itama tace prince menene? So yake yai magana amma ya kasa ta kara rikecewa, tunda take bata taba ganin wani a irin wannan yanayin ba cikin rudewa tace bari insa akira likita tafad'a tana mai zare hannunsa daga jikinta, kara rikota yai ya girgiza mata kai. Hawaye ne yafara zubo mata tace banganeba, kaganka fa😰? Ya d'aure azabar dayakeji ya nuna mata drawer din jikin gadon, ta kalleshi tare da budewa, ganin magani a 'yar farar roba yasa ta mikamai tare da janye jikinta ta miko mai ruwa, ya amsa ya had'iya ahankali yafara jin relief, can ya saki ajiyar zuciya,salma kam hawaye kawai take gani takw kamar mutuwa zaiyi, tariga tasa a ranta indai yasha magani bai warkeba ba ruwanta nemowa zatai akaishi asibiti ko a kira likita. Salman ya d'ago ya kallI hannunshi data kankame tana hawaye,ganin ya d'ago yasa itama ta kalleshi, yace is ok I am alright, cikin hawaye tace wani irin ciwo ne wannan? Kana zuwa asibiti kuwa? Salman ya kakaro murmushi yace Is not a big deal fa, ta janye hannunta tare da mikewa zata wuce, hannu yasa dasauri ya kamo hannunta ta tsaya batare data juyo ba har a lokacin hawaye take, salman yace please karki fad'awa kowa, kinji? Ta juyo a fusace tace abinda zakace kenan? Wace irin rayuwa kakeyi? Bakada lafiya baza'a sani ba? Ya runtse ido batare da yai magana ba yasaki hannunta, dasauri takara matsowa tace jikin ne😰? Ya bude ido ahankali yace bacci tai ajiyar zuciya. Salman bacci ne yai gaba dashi saidai salma takasa bacci kusa dashi tazo ta zauna tai shiru, batasan sanda bacci yad'auketa ba, cikin baccinta mafarkin rannan tasakeyi gata da wani hannunsu a rike suna kallan ruwa, sosaI dadin mafarkin takeji, dan murmushi harkan fuskarta. Salman daya farka ya kura mata ido tana kwance tana bacci sai dai da alama mafarki me dadi take, abinda yaban mamaki shine ganin shima salman ya saki wani murmushin. A hankali ta bude idanta salman ta gani kusa da ita tad'an turo baki tace ya jikin😞? Yace I am ok👌🏻zatai magana yace a haka kika kwana? Ta kalleta akan kujerar jikkn madubi data jawo take a zaune ta kwanta a jikin gadon, tace hmmm, yai murmushi tare da mikewa, haryaje jikin toilet ya juyo yace tnx 4 ur concern😉 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣1⃣ Kallanshi tai tad'anyi murmushi, salman ya wuce toilet itama ta mike ta maida kujerar inda take, bayan salman ya fito ya wuce massalaci itama ta shiga ta d'auro alwala, bayan ta idar da sallah haka kawai tasamu kanta da d'aga hannu sama tana rokarma salman saukin wannan ciwo nashi😰. Ga mamakinta daya dawo daga massallaci bai koma bacci ba itama hakan yasa ta zauna tare da d'aukan qur'ani, wajen 7 salman ya mike yakalleta yace zan shiga makaranta, salma ta rufe qur'anin tare da kallanshi, tad'an kakaro murmushi tace to, yace do u resent me? Ta kalleshi tace sosai ma☹, yai murmushi tare da wucewa toilet. Tabi bayanshi da kallo, salman bayan ya fito yad'au kaya ya koma toilet yasa, kananan kaya yasa yayi kyau sosai, salma ta kalleshi tace ka fad'amusu a kawoma abinci ne? Yace nop bana cin abinci da sassafe, tad'an tabe baki tace hmm. Salman ya dau waya ya fita, takalleshi tace jakar makarantar fa? Yace mezan da ita? Tace au haka ake zuwa? Yai tsaki yace nidai na wuce najib na jirana, takalleshi aranta tace tab. Mikewa tai tafara kad'e gado, maganin jiya tagani, ta kurama maganin ido, tace ko maganin meye? Ta bud'e drawer ta side_bed ta ajiye zata rufe taga wani karamin album hannu tasa ta jawoshi, ahankali ta bude, hoton wata tagani, suna tsananin kama da salma ga hoton na da ne hakan yasa tai tunanin mahifiyarsa ce, takara budewa hotunan salman ne wanda baifi d'an 20yrs ba alokacin shida wata yarinya, kana ganinsu kasan suna cikin farin ciki, ice cream sukesha, wani gurin kuma suna kan keke, wani kuma suna zaune a kan grass carpet, murmushin dake kan fuskar salman ne ya bata mamaki, bata tab'a ganinshi a cikin farin ciki haka ba, zata bude wani gun taji an fizge album din. Dasauri ta d'ago, salman ne tsaye ranshi a b'ace yace bincike kikemin in na fita? Dasauri ta mike tace wannan ne bincike? Maganinka naje maidawa nagani, amma wac.....katseta yai tare dacewa bansan tambaya, ya d'au makullin mota daya manta ya fita da album d'in. Ta bishi da kallo a fili tace wacece ☹? Tadade a zaune haka kawai take tunanin yarinyar, da alama hotunan bama na kasar nan bane, a ina ne? Ganin batada wanda zai bata amsar tambayoyinta yasa ta mike ta cigaba da gyaran d'akin, bayan ta gama tai wanka, ta fito tai breakfast. Salman kam ya dade a mota rike da album din, idanshi ya kad'a yai ja a hankali ya bude album din ya kalli mahaifiyarsa, sannan ya bude ya kurama budurwar ido, yasa hannunshi akan fuskarta yana shafa, ya dade a haka kafin ya rufe, yaja motarsa. A falo salma ta zauna tasa kallo, hanne da wata na zaune a kasanta, salma tace hanne ko mu fita nan tsakar gida? Wajen garden d'incan? Hanne tace to ranki ya dade abinda kikeso shizamuyi, ta mike tare da yafa mayafinta suka fito, zamatai a garden tare da littafinta tana karatu. Ishaq ne yazo wucewa, dama kullum yazo wucewa sai ya leka bangarenta sai dai kullum ba kowa sai bayi, yau kam yayi sa'a yana lekawa yaga salma zaune akan kujera hankalinta gaba d'aya ya tattara akan littafin datake karantawa, kura mata ido yai jiyake kamar yaje ya rungumeta, fadawan dake bayansa ya kalla yace ku tsaya anan, shikuma ya shiga. Hanne ce ta d'ago jin motsin mutum, ishaq ya kalleta yamata alama da hannu su fita, cikin hanzari suka fita, ishaq ya karaso daf da ita yad'an sukunyo yace Amaryarmu karatu take? Cikin tsananin mamaki ta d'ago tare da saurin mikewa ta matsa baya, salma ta gaidashi, ya amsa tare da cewa Amarya kina lafiya? Yafad'a tare da matsawa, takara matsawa tare da cewa lafiya, amma yarima me kake anan? Ishaq ya tsaya tare da cewa laifine in nazo ganin matar kanina? Yafad'a cikin shagwaba, haushi ya kama salma amma tad'aure tace ayya nagode, zan shiga ciki naga kamar lokacin sallah ya kusa, bata jira mai zaiceba tai saurin wucewa ciki. Ishaq ya bita da kallo tare da cewa wow yarinyar nan tana kasheni gaskiya👌🏻... Salma na shiga ciki d'aki ta wuce ta hau kujera tace wannan kuma wani sabon salon fa? Meye namin shagwaba? Tsaki tai tare da cewa ni zaman d'akin ma yafimin😕. Haka taita zama har tai sallar isha'I, aranta tace wannan rayuwa haka zan d'ingayi? Da yaya kamal na aura nasan bazan kare a haka ba😞 bayan tayi isha'I tana zaune har bacci yafara d'aukanta. salman ya shigo ganinta a zaune akan kujera tana barci yasa ya karasa inda take ya kalleta, gaskiya tanada kyau, wata zuciyar tafad'amai haka, tuno yanda ta kuladashi jiya yai, tunda yake a duniya jiya shine rana ta farko da wani d'an adam yasan da cutarsa harya kula dashi, hannu yasa ganin kanta yad'an lankwashe garin bacci, salma kam jin kwanciyar ta mata dadi yasa ta cigaba da baccinta. murmushi yai ganin yanda take baccinta sannan ya kalli hannunsa da fuskarta take kai, wata zuciyar tace ahaka zaka zauna? A tsaye? Harsai ta tashi? Motsin daya d'anyi da hannunsa ne yasa salma ta bude ido da sauri ya zare hannunsa tare dayin gyaran murya, ta mike da sauri tace ka dawo? Ya juya baya yace ke kuma meye hakan?tace mekuma nai daga dawowa? Ya juya yai waje batare dayai magana ba, tace neman a d'auramin laifi dai🤔. ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣2⃣ Salman na fita a kujera ya zauna tare da furzar da wata iska, yace menai? Meyasa nazo nan? Ya mike tsaye tare da bude fridge yad'auko ruwan faro ya bude, ya kafa kai sai daya ahanye ruwan tas sannan ya saki numfashi. Daki ya koma, salma ya kalla dake shimfid'a ya d'auke kai tare da hawa gado ya d'aure fuska yasa earphone a kunnansa, salma takalleshi aranta tace oh ni salma, jitai yace dani kike? Dasauri tace ba abu kakeji ba? Yace au in nasa earphone gulma ta kike kenan, ta juya baya tace nidai badakai nake ba, yace shine kika kira sunana🤔? Ta matsa kusa dashi kad'an tace ni? Yaushe? Yace kice baki kira sunana ba? Tace ni wlh sunana nakira, yai tsaki tare da kwanciya, ta harareshi tace oh 🤔 juyawa tai zata wuce, yasa hannu ya rikota, ta tsaya tare da juyowa😳, yace oh me?tace nifa badakai nake ba☹tafad'a cikin shagwaba, jawota yai ta fado kan gadon kusa dashi, ahankali tad'ago ta kalleshi. Yace oh me? Tace wai dakai nake? Yacs dakanki kike? Tai shiru, yace dazu natambayeki do u resent me kikace eh ko? Ta dan harareshi tace ba gaskiya kakeso nafad'a ba? Kaima kasan dole ne tunda kasa akaban suspension, sannan yanzu bana tunanin zan iya karasa karatuna😕. Salman yasa hannu ya jawota jikinshi, yazo saitin kunnenta cikin rad'a yace bake kikace ni kike so ba😏? Haushi ya isheta ta zare jikinta tare da mikewa tace Allah yatsaren😠, mikewa yai tare da riko hannunta ta baya da karfi ta juyo dan taji zafin rikon, fuskokinsu ne sukai daf da juna yanda kowa najin numfashin d'an uwansa, salman ya d'aure yace Allah ya sauwake? Ni ya kamata infad'I haka ko ke? Kasa tai da kanta tace hannuna😞 tafad'a cikin sanyin murya, salman ya kalli hannunsa ganin yanda yakama mata hannu yasa ya zare a hankali, ta rike hannunta tare da kallanshi🙄yace Allah ya isa ko? Tace yaushe nafad'a kuma☹? Ya juya ya koma gado. Ta dade tana kallanshi kafin itama ta kwanta sunyi shiru sai dai dukansu ba bacci suke ba, salma tace bacci? Cikin sanyin murya yace no, tace inada tambaya, yace tame? Tace yarinyar daxu wacece?salman yai shiru, takara cewa wacce? Jin bai amsaba yasa tace sry ina b'atama ra......jitai ya katseta dacewa *FARHA* tamaimata sunan tace wacce farha? Yace u don't have to know, tai shiru duk da bataji dadin amsar ba amma bata kara magana ba, salman yasan bataji dadi ba amma shi kanshi baisan tunowa, dan yanzu maganar dasukai akan farha shikad'ai yasan me yake ji. wajen 9 yagama shiri tana zaune tana kallansh, tace yau zanje gaisuwa gunsu fulani, yace to, tace aran waya in kira Abba plz kafin kafita, ya mika mata, ta amsa ta kira Abba sai dai an dade ba'a d'agaba harta katse, takara kira, jin muryar mutumin datake kewa yasa ta mike tsaye tare da cewa yaya kamal? Tafad'a tana kallan salman, ganin ya juya baya kamar hankalinshi ba'a kansu yakeba yasa tace yaya kamal ina kwana? Kamal kam duk ya rude jin muryar salma, yace salma Kinga Abba ba lafiya munanan ma asibitin aminu kano, dasauri cikin kid'ema tace what? Yace eh salma jiya da daddare muka kawoshi, dasauri ta kashe wayar,hawaye yafara zubo mata,kusa da salman ta karaso ta rike mai riga, salman ya juyo yana kallanta, ganin hawaye yasa ya rikece yace salma menene?tunda take yaune rana tafarko daya taba kiranta da sunanta, sai dai bata kula ba dan hankalinta nakan Abbanta. Salman yakara cewa menene? Jikinshi tashige tasa kuka, shikanshi baisan sanda yasa hannu ya rungumota ba yace menene wai? Tace Abba na ba lafiya yana asibiti, prince yazanyi😰? D'agota yai yace meya sameshi? Tace bansani ba nima😪. Yace wuce kiyi wanka sai in kaiki, tace to nagode, dasauri tai toilet ya bita da kallo, cikin tausayi, salma kam wanka tai tad'auro towel sam ta manta salman na d'akin dan a kid'ime take, ta fito da d'aurin kirji, salman dake tsaye ya juyo ya kalleta, 😳 itama tana ganinshi tai saurin yin kara tare da komawa toilet din, yai murmushi tare da yin falo, sam ta manta yanannan kayan data cire ta maida ta fito, sai dai bakowa a d'akin tai saurin zura duguwar rigar atamfa tashafa mai da huda ta yafa mayafi, ta fito. Salman dake zaune a falo ya kalleta, tace dan Allah ba inda zan sami hijab? Yace ki zo mu tafi dan nima ina sauri ne, tace to tare da binshi. Sun isa asibitin Aminu kano, ta kira number Abba a wayar salman, kamal ya d'auka tare da musu kwatance, nan suka isa gun, suna sauka a mota kamal ya taho da sauri ganin salma, ya kalleta wani abu na tasomai, itama kallanshi takeyi duk ya rame, salman dake tsaye yana kallansu. Salma ta daure tace yaya yanaga ka rame? Yace salma kema kinsan dole ne banajin zan iya rayuwa bake😞, idanta ya ciciko tace yaya ina Abba? Yace kuje ciki, ta juyo ta kalli salman dake tsaye ta inda ya fito daga cikin mota yana kallansu, tace muje cikin? Ya zagayo tare da cewa muje mana, kamal ya kalla wanda ya kuramaI ido, kana kallan kamal kasan kallan kiyaya yakema salman, salman ya d'auke ido tare da zagayowa ya kalli kamal yae d'an rakiya muje ko🤔? Kamal ya hade rai yace d'an rakiya? Salman yace wuce mana kana b'ata min tym😏. Kamal kam ji yake kamar ya shake salman sai daI kafin yai magana salma tace yaya muje mana makaranta zai wuce, tafiya yafara kamar mara lafiya salman ya kalleshi ya tabe baki. By Ayusher Mohd📚 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣3⃣ Sun isa gadon da akaba Abba, salman ya kalli d'akin kusan su bakwai ne a ciki, umma da goggo na zaune kusa dashi, salma da sauri ta karasa kusa da Abba, ta kuramai ido ganin yanda ya rame yasa hawaye kawai ya fara zubo mata. Salman kallanta kawai yakeyi jiyake hawayen da take har zuciyarshi yake tab'awa, juyawa yai ya kalli su umma da goggo ya tsugunna ya gaidasu da mai jiki, sannan ya mike, idanshi ne ya diri akan kamal dake kallan salma shima hawayen yake, wani mugun kallo yama kamal haka kawai yaji bayasan yaron. Daurewa yai yakalli goggo yace meke damunshi wai? Tace hawan jininshi ne ya tasha yace ayya nan yace bari inga likita tace to, ya juya ya fita. Salma kam kuka takeyi, kamal ji yake kamar ya rungumeta ya lallasheta, juyowa tai tace umma meyasa ba'a fad'amin ba? Umma ta juya fuska, goggo tace Alhaji ne ya hana, salma tace su sa'a fa? Goggo tace yace kar afad'awa kowa kema kamal ne yafad'amiki dan baisan ya hana ba. Tai shiru tare da waigawa, ganin bataga salman ba yasa ta cigaba da lekawa, goggo kam ta fahimceta tace to mara kunya, yaje gun likita, dasauri tace kiji goggo ce miki akai shi nake nema? Kafin goggo tai magana sai ga salman da wani babban likita, ya gaidasu sannan yace zamu maidashi wani d'akin, goggo tace meyasa? Likitan ya kalli nurses din dake bayansa yace ku turo gadon, sukace to. Sannan salman yace goggo acan sai anfi kula dashi, tace to. Nan suka meke dukansu salma takalli salman tai murmushi Shima murmushin ya mata, kamal dake kallansu kishi duk ya isheshi. Wani babban d'aki aka kai Abba, kana ganin d'akin kasan d'akine na mai matsayi, salma ta kalli salman tace d'akin nan yamana girma, salman ya harareta sannan ya kalli goggo da umma dakesan su fad'I abinda salma ta fad'a yace goggo karku damu ba wani abun bane, goggo tace angode d'an nan. Salman yai murmushi sannan ya kalli salma ya mata alama da kaI ta biyoshi,sannan ya kalli su umma yace na wuce, dakyar umma cikin kunya tace angode, yai murmushi ya fita, salma ta kalli kamal wanda ya had'e rai sannan ta fita. Kusa dashi taje tace makarantar zaka? Yace eh kinsan mai martaba yasa mai kula dani, in har banjeba da matsala, tai murmushi tace nikam shekarunka nawa? Salman ya had'e rai yace bangane ba😠 tai dariya tace bakafi 26 to 27 bako? Ya hade girar sama data kasa yace zaki fara ko? Tace sry gani nai ace har yanzu sai ana kula dakai🤔 ya juya yace ki biyoni mota, kallansa tai tare da sakin murmushi. Kudi yad'auko mata mai kauri yace ki rike in case ko za'a bukaci wani abun,tace a'a nasan da kudi agun.....yace kinsan banasan musu ko? Hannu tasa ta amsa yace ko kefa? Natafi tace to zaka dawo ko in wuce? Yace da ke kad'ai kikazo dazakimin wannan tambayar? Tai kasa dakai, mota ya shiga yaja, har akasan ranta. Juyawa tai, idanunta suka had'u dana kamal, ta karaso inda yake tace yaya, kamal ya juya cikin b'acin rai da sauri tasha gabanshi tace yaya meya faru? Kamal yasa hannu yaja hannunta ya fara tafiya tace yaya😳? ina zaka kaini? Kamal kam tafiya yake sai da sukai tafiya mai nisa, mutane nata kallansu, har sukaje gunda ba mutane sannan ya saketa. Tace yaya me kakeyi hakan? Kamal yace tambaya ta ma kike? Salma dama akwai ranar dazaki zauna da wani namijin cikin farin ciki bayan ni? Ta kalleshi da mamaki tace yaya ya kakeso inyi da rayuwata😰? cikin d'aga murya da fad'a yace salma tambaya ta kike? Duk son da kika nunamin dama na karyane? Ni zaki yaudara? Nad'auka yanda nake sanki haka kema kike sona ashe ba haka bane? Me zaki cemin? Itama cikin fad'a da kuka tace yaya ya kakeso inyi? So kake in kashe kaina? Duk jiran danamaka ka manta dani, kabarni da tsananin begenka, ba nema? Kamal ya dafa kafad'arta hawaye ya zubo mai yace salma ban barku ason raina ba y don't u understand? Ta ture hannunshi tace fahimtar dani yanzu😠, kamal yai shiru tace bazaka iyaba? Dama nasan bakada abinda zakace, ta juya tafara tafiya. Hawaye take harta isa d'akin, goggo ta kalleta tace daga rakiya shine kila dade? Batai maganaba ta zauna kusa da Abba ta kama hannunsa ta rike tana hawaye. Salman kam dama inya shiga class wayarsa yake d'auka yai ta d'annawa ba ruwanshi da abinda akeyi, yau kam yayi shiru tunanin salma kawai yakeyi, ko mahafin nata ya farka daga allurar baccin da akamai? Ko jikin ya kara tashi? In ya tashi ya salma zatai? Wannan dalilin yasa yai shiru, har malamin ya fita baimasan me akeyi ba. Najib ne yatab'ashi yace Prince ya akai? Amir yace hala tunanin Amarya ake, salman ya mike yace tunanin Amarya? Allah ya sauwaka, ya fita waje najib ya bishi yace ina zaka? Salman yace hm wani guri, sai gobe. Dasauri ya fad'a mota yai hanyar asibiti. Salma na rike da hannun Abba taji yayi motsi, dasauri ta d'ago tace Abba😥? Yakalleta tare da lumshe ido tasa kuka tace Abba laganka kuwa? Murmushi ya kakkaro ta kalli umma tace umma me za'a bashi? Ta mike ta zubo mata faten tsaki wanda yasha manshanu da yakuwa, salma ta amsa tare da taimakawa Abba ya mike, nan ta shiga bashi,ahankali ya dinga amsa har ya shanye. Salman gudu yakeyi ya kai wajen titin gyad'I_ gyad'I mota tamai faci, haushi duk ya isheshi ga yamma tafarayi, waya yama driver dinsa yace ka kawomin prince 4 yanzu, yace to ganinan ranka ya dade. Salman nazaune a mota haushi duk ya isheshi ga salma bata da waya, sai wajen 5 ya iso. Dasauri ya amshi motar tare da barin driver din anan gun d'ayar motar. Salma ganin Abba ya koma bacci, ga goggo ta tafi gida, umma ce a ciki yasa ta fito waje ta zauna a dakalin gun, kamal ne yazo yazauna kusa da ita, ta d'ago ranta a had'e ganin kamal yasa ta mike, dasauri yasa hannu ya kamota yamaida ita inda take, tace yaya. Kamal yace salman jarabawa na fad'I sai dana zauna wata semester din tazagayo na sakeyI😞 kiyi hakuri dana barki ke kad'ai. Kallansa take tana hawaye tace yaya meyasa baka fad'aba ko ta waya? Yace banso kisan saurayinki rago ne gun karatu, ta runtse ido kwalla sai zubo mata take, yace muje ki rakani na siyoma umma lemo, nima inasan kati. Ta mike suka jero suna tafiya, salman da tun da ya iso yana kallan sanda kamal ya rikota duk yagansu duk da baisan me suka ce ba amma ranshi yagama dugunzuma. Ganin sun taho tare yasa ya kunna mota, cikin tsananin bakin ciki da bacin rai ya kunno motar da karfi, da gudu ya taho, saura kiris ya kadesu, dan sukam sun gama tsorata kamal ya kamo hannun salma yasata a bayansa da sauri, salman sai dayazo daf da kamal ya taka burki jikake kiiiiiiiiiiiiii... Kallan kallo suka fara, sai a lokacin kamal yaga ashe salman ne, salman kam hannun kamal daya rike salma ya kalla, daure wa yaI tare da fitowa daga motar, ya saki murmushi kamar ba komai ya matso kusa da kamal ya zare hannun salma sai alokacin tasan salman nema, ta kalleshi cikin tsoro, saidai ga mamakinta murmushi ya saki tare da kallan kamal yace ayya kamar baka gani? Ka dinga kula in kana tafiya karkaja a ragema farashi😉. Kamal kam mamaki ya hanashi magana, salman ya kalli salma yasa hannu yajawota yace kema kamar bakya gani? Tace hm hm bankula bane🙁 yaceina zaki? Without my permission? Ta kalleshi sannan ta kalli kamal tace dama....ya katseta yace muje muduba Abba mu wuce gidanmu, yafad'a tare da kallan kamal. Salman yafara tafiya itama ta bishi a baya, kamal kam ya kame yama kasa tafiya yana kallo har suka shiga ciki haushi ya isheshi yakaima motar naushi da kafa, sai dai maimakon yaji sauki sai zafin dayaji akafarsa😕 Hmm to fa🤔 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣4⃣ Sun isa d'akin, Abba na jingine sai dai ya rame sosai, salman ya karasa tare da gaidashi, ahankali Abba ya amsa tare dama salman godiya. Salman ya kalli umma ya gaida ita, tai kasa dakai ta amsa, sun d'an yi shiru kafin Abba yace kuje gida dare yayi, salman ya kalli salma sannan ya musu sallama, itama salma ta musu sallama ta fita. A waje ya tsaya, yanakallan kamal ma tahowa gunsu yai murmushi tare da kallan salma yace muje ko? Ta kalleshi tace eh, ahankali ta matso suka jera suna tafiya, sai da sukazo daf da kamal sannan salma ta kalli kamal idanta taf da kwalla, salman ya kalleta ganin yanda take kallan kamal yasa ransa ya b'aci amma iya basarwa ta salman sai ya kalli kamal yace mr d'an rakiya dan zo ka shiga da ledojin nan tunda ciki zaka😉, kamal ya kalleshi sannan yace kai meyasa dazaka shiga baka wuce dashi ba? Salman yace karaso ka amsa, yafad'a tare da karasawa motar. Kamal ya kalli salma ranshi duk a b'ace tace yahkuri yaya ba....wani kallo da kamal ya mata yasa tai shiru, kamal ya tsaya kikam salma tafara tafiya ta juya tace yaya? Kamal ya d'aure ya karaso, salman yai murmushi tare da mikomai manyan ledoji guda biyu yace tnx d'an rakiya😊, kamal yace karka kara kirana da sunan nan😠. Salman ya shiga mota tare da rufowa sannan salma ta shiga, ya zuge glass d'in mota ya kalli kamal yace ban san sunanka ba me kake so ince? Salma zatai magana ya juyo ya kalleta tai shiru tare da turo baki, ya kalli kamal yace nyt😏, yaja mota da gudu ya bud'ama kamal kura. Kamal ya kalli motar yace wlh mutumincen sai na👊🏻. Salma kam a mota suna hawa titi salma ta kalleshi tace plz ka dainacemai haka☹. Cikin zafin rai salman yai gefe ya taka burki da karfi, salma kam ta tsorata da sauri ta jiyo ta kalleshi, sai dai yanda taga idansa yasata tai shiru, ya kalleta tare da nunata da yatsa yace karki kuskura! *karki kuskura ki kara tarema wani a gaba* don't u dare do that again😡. Salma kam jikinta rawa yake amma ta daure tace menai kuma? Ni meyasa kakemin haka? Tafad'a tare da zubo da hawaye, sai dai ganin tana hawaye yasa jikinsa yai sanyi ya juya tare da fara tafiya batare dayace komai ba. Salma ta juya kai tana kallan window, wajen mai saida waya ya tsaya baice mata komai ba yafita, takalleshi tare dacewa kada Allah yasa kacemin kana zuwa😗. Yad'an dade kad'an kafin ya fito, ya bude mota ya shiga, baice komai ba itama haka, har suka isa gida sun fito zasu nufi bangarensu wanI bafade yazo gun salman yace Ranka ya dade mai martaba na kiranka, ya kalli salma tare da mikamata karamar ledar yace wuce dashi ina zuwa tace to. Amsa tai ta wuce shima yai banaren mai martaba, salma na shiga bangarenta hanne ta taho da sauri tace ranki ya dade kun iso lafiya? Salma tace lafiya, hanne tace ina kukaje ranki ya dade🤕? Bakiga fad'an da fulani tai ba mai martaba ma sai da yai fad'a. Salma tace bangane ba😳? Hanne tace a ka'idar gidan ba'a fita sai mace tayi wata biyu amma ke kun fita ku biyu ba driver kuma ba wanda yasani😞. Salma tace bansani ba ai dana sanar😰, yanzu mai zai faru? Hanne tace kawai dai fad'a za'amai tunda ansan ke bakisani ba. Salma ta mike tai d'aki tare da zama dabas a kasa ta jingina kanta a gado, tasan salman bazai yi bayani ba saboda pride dinsa yanzu tasan anacan anamai fad'a. A hankali hawaye ya fara zubo mata tace because of me😪 kanta ta had'a da gwiwa, tayi wajen minti 30 a haka sannan salman ya turo kofa kallanta kawai yatsaya yanayi, meyasata kuka? Jin sheshekarta yasa ya kasa jurewa kofar ya rufe tare da karasowa inda take, ya tsugunna yasa hannu ya jawota jikinsa, ahankali tad'ago tace me akacema😰? Ran sarki ya b'aci ko? Sai a lokacin yasan dalilin kuka, hannu yasa ya fara shafo bayanta, ta kankameshi tace am sorry because of me...katseta yai yace ba saboda ke bane, meyasa kike da saurin kuka ne? Salma kam tai luf a jikin salman sai d'an shesheka datakeyi. Salman shiru yai yana tunanin fad'an da sarki yamai, shifa shiyasa bayasan zaman gidan nan, ace komai sai ka sanar?. Sun dade a haka kafin hankali salma ta zare jikinta, ta mike salman yasa hannu ya jawota ta zauna a inda take yace wa........sai kuma yai shiru, azahiri so yake ya tambayeta meye tsakaninta da kamal? Amma jiyai bazai iya ba, kamar zata rainashi tai tunanin ya damu da itane, kallansa tai tace wa me? Hannunta yasaka tare da kikewa yai gyaran murya yace hm waya nake nufi wace kika shigo da ita, kiyi amfani dashi in kinaso, yana gama fad'ar haka yai toilet. Salma ta kalleshi tare da rangwad'ar dakai tana kallon ya shiga toilet tace kace kawai kasai min waya☹ ta mike da sauri ta bude wayar, 😳 kalan wayar tace inazan kai wayar nan? Iphone 6 taga ga an rubuta a jikin kwallin tace ahh wasa yakemin hala🤔 inani ina wannan wayar? Tanajin ya fito ta mike takalleshi ta karaso inda yake tace amma dak ba wannance wayar bako? Ya kalleta dariya takusa zuwa mai ganin yanda takeyi da ido, ya d'aure fuska yace bata miki bane? Tace ni😳ina na isa? Ai wai naga.....ya katseta yace in ta miki to ya isa 😒 ya fad'a tare da matsar mata da hannunta yai ciki, ta karaso da sauri batasan sanda ta rungumoshi ta baya ba tace thanks a lot😊. Salman jinta a bayansa yasa yai murmushi, salma ta sakeshi tadawo tagabanshi tace nagode sosai prince ta saki wani sanssanyan murmushi tare da lumshe ido shima murmushin yai....... Nikaina murmushin nai😜 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣5⃣ Kado ya hau ga mamakinsa duk b'acin ran dake damunsa ya tafi, ahankali yake satan kallanta tana duba wayar. Salma ta taso tazo kusa dashi ta tsaya tace kamar ba sim a ciki ko? Ya d'an dago tare da jingina a jikin gadon yamata alama da hannu ta zauna a kusa dashi, ahankali ta zauna tare da mikamai wayar, ya amsa yace ina ledar? Ta mike ta d'auko nan ya d'auko sim pack din yasa sim din sannan ya mika mata, ta kalleshi tace bakasamin numberka ba, ya amsa ya samata tare da kallan wayar so yake yaga mezatayi saving din sunan, ganin yana turo kai yasa salma tai dariya tare da rungume wayar, cikin zolaya tace me kake lekawa? Dasauri ya koma inda yake yace me kuwa? Tace me kakeso insa akan sunanka? Yace dama mutum ake tambaya me yakeso? Ta mike tare da dariya tace nama tuna, shima ya mike zaune yace me kika tuno🤔? Tace hmmm yama? Yace what? Tace to ai namanta☹ tafad'a cikin shagwaba, ya koma ya kwanta tarr da cewa bawani nan, tai murmushi tare da zama a shimfidarta azuciyarta tace mezansa? Rude? S?ahh me zansa? Tafad'a tare da rike haba, salman na kallanta yai murmushi tare da juyawa. Wata idea ce tazo mata kawai tai dialling number salman din, ganin waya ta shigomai kuma new number yasa ya d'ag da mamaki amma baiyi magana ba, salma tai kasa da murya tace hiii🙋🏻, jin muryar mace yasa yace waye? Salma tace is me😉 jin maganar kamar a d'akin yasa ya juyo tai murmushi tare da daga wayar ta jijiga, yace ahh what is this? Tace my no.😀 ya katse tare da sakin murmushi, tace kai saving. Ta taso a hankali tazo kusa dashi, salman daya kurawa number ido yana tunanin mai zai sa, jin motsin salma yasa ya rubuta Stubborn, salma ta fizgo wayar tace stubborn? Ni din😠 ya mike yace ba haka bane? Tace eh mana yace to yaya ne? Tace bandai sani ba amma banda wannan🤔 tafad'a tare da juya baya, hannu yasa a kugunta yaje juyo da ita ta taho gaba daya, ta fad'a jikinsa, ahankali ta d'ago nan fa suka shiga kallon juna, salman ganin tasa wayar a bayanta yasa yajawota ya rungume sannan yasa d'ayan hannun ya zare wayarsa, ya nuna mata sannan yace me kikeso insa? Tace inza'a sama mutum suna shi ake tambaya? Yai murmushi jin ta kwaikwayeshi, ta mike zata tashi ya rikota yace in baki fad'aba zan bashi a sunan d'azu, tace in kasa sunan d'azu nima zansa duk abinda yazomin arai, ka yarda?ya d'aga gira. Nan ta mike tare da kwanciya a kasa sai dai takasa bacci, sai juyi take, abubuwan daya faru tsakaninta da salman take tunowa, lumshe ido taja bargo.....ita kanta batasan meke faruwa da ita ba. Yau saturday hakan yasa salman ba inda zashi da safe bayan sun tashi, kawai yau tasamu kanta dacemai ina kwana? Mamaki ya kamashi a hankali ya amsa tare da cewa duk farin cikin ganin wayar ne? Ta rufe ido tace bafa haka bane☹ yace to naji, ki tashi mu shirya muje asibiti ko? Tace kasanar da sarki dalilin fitarmu ta jiya ne? Yace sai na sanar? Mamaki ya kamata tace kasan fa abinda yafaru jiya, yace to sai me? Zaki fasa zuwa duba mahaifinkine saboda wasu suna kai gulma? Tace ba abinda nake nufi kenan ba amma jiya anma fad'a yau.....yace ke akama? Tace a'a amm...yace ki tashi ki shirya in zaki, in bazaki ba kuma ki zauna, yana kainan yad'au kaya ya shiga toilet,salma ta rike kai tace yazanyi? Number Abba tasa ta kira, kamal ne ya d'aga tace yaya ya jikin Abba? Yace da sauki dan gashima a zaune nan ya mikama Abba suka gaisa, Abba yace basai kinzo ba yau kinga bai kamata daga aure kidinga yawo haka ba tace Abba amma ai yakamata inzo, yace na yafe zuwan, tadaure tace wannan ce numberta Abba kayi saving yace lalai ina murna tace na gode, nan ta kashe wayar. Salman na fitowa ta kalleshi tanaso tamai magana sai dai ganin ya d'aure fuska yasata tai shiru, mai yashafa yasa turare ya fita falo, tai tsuru a zaune can ta mike tai wanka ta fito falon, yana ganinta yad'an saki rai takaraso dinning ta zauna har suka ci abinci ba wanda yai magana suna gamawa ya shigo d'aki da niyyar d'aukan makuli, salma ta biyoshi,ta tsaya a bayanshi tace dan Allah kabari na tambaya inzamu fita, ya juyo cikin b'acin rai, harzai yi magana ko me ya tuna kawai taga ya fita da sauri, tabi bayanshi da kallo idanta taf da kwalla tace yazanyi😥? Salman na fita mota ya fad'a yazauna yana tunanin zata fito, salma kam ganin tsayuwar bazata mata amfani ba yasa ta jawo mayafi ta fito da sauri sai dai ba salman a falon ganin haka yasa ta zura takalmi tai waje bayinta suka biyota, da sauri ta bude kofar tsakar gidan zata fito dai_dai nan ishaq ya taho ai kuwa su kai gware baya tai da sauri tare da kallan wa ta bige? Ishaq ne ya d'ago cikin fad'a shima sai dai ganin fuskar daya dade yana bege yasa ya saki ajiyar zuciya, salma tai kasa dakai tace yahkuri yarima ban kula bane, murmushi yai yace are u alright? Tace eh kayi hakuri plz, yace indai bakiji ciwo ba is okay😉, ta d'ago da mamaki ta kalleshi yace yes that's what I hope😊, kasa tai dakai tare da juyawa cikin gida ta turo kofar, hanne tace kinfasa fitar? Tace eh. Salman ganin ba alamar salma yasa yai waje da gudu ranshi a b'ace, dakin najib ya wuce, yana shiga ya fad'a gado, najib yace prince meya faru? Naga kamar kana kan fire😂. Salman yace banasan magana yau, najib zaiyi magana wayar salman tai kara ya kalli wayar stubborn ne yafito ajiki, ture wayar yai gefe, najib ya kalleshi yace waye stubborn? Salman yace ina ruwanka? Najib yace don't tell me salma😂? Lalai taci sunnan itama naga ba kanwar lasa bace amma salman stubborn a waya? Lol so childish😜. Salman yace ina ruwanka? Zan fita daga d'akin nan fa? Najib yace sorry amma kana kallo bazaka d'aga ba? Salman ya kalli wayar harta tsinke, salma takara kira, najib yace salman please, salman yace ba ruwanka malam bakasan metamin ba😠 najib yasa dariya yace har anfara love_ fight hahh lalai prince. Cikin zafin rai salman ya mike yace love fight? Lalai kaci mutincina nida wa? Najib yace haba salman, cool down meye da zafin ran ko dai haka ne? Kakesan ka waske? Salman ya kwanta tare da juya baya, yanaji salma tai kira na 3, sai dai yaki d'auka itama batasake kira ba. By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣6⃣ Salma kam haka ta zauna sukuku a gidan sam batajin dadi gashi tasan duk kiran dazatama salman ba d'agawa zaiyi ba. Salman kam da yamma yad'au najib sukaje suka dubo Abba yau kam kamal bayanan sai mahaifinsa, sun d'an dade kafin su taho, gidan najib ya koma, najib ya kalleshi yace prince wai meye hakan? Bazaka wuce gida ba? Salman yace malam ba ruwanka dani😠 najib yace amma salman ai hakan bai dace....ganin salman yayi ya mike tare da komawa gado ya kwanta, najib ya kalleshi sannan ya girgiza kai, salman sai juyi yake can kuma ya mike ya d'au makulli yai waje, najib ya bishi da kallo tare da murmushi yace tunda yazo yau hankalinshi baya nan amma yaje inda hankalinsa zai kwanta pride dinsa ya hana🤔 Salman ya isa gida, salma tunda tai sallar isha'I tana zaune akan sallayar ta d'aura kanta akan gwiwarta tayi shiru tanajiran salman, ahaka batasan sanda bacci yafara d'aukanta ba, ahankali salman ya turo kofa sai dai ganin salma tana bacci yakara tunzura shi wato ita ko ajikinta ko? Shigowa yai ya d'au kaya ya wuce toilet yai shirin bacci, yana fitowa ya tsaya a jikin gado ya kurama salma ido, yarasa mai yake tunani, haka kawai yasamu kanshi da rashin san d'auke idanunta, a fili yace tanasan bacci a takure. Salma dake bacci ahankali ta bude ido, idanun salman tai arba dasu, dasauri ya d'auke idanunsa, salma ta mike da sauri tazo kusa dashi tace yaushe ka dawo? Salman ya shareta, tace yanzu? Ya mata banza gado ya hau yasa earphones akunnensa ta zauna kusa dashi tace sannu da zuwa, salman yai kamar baya jinta, tace plz kace wani abun☹, tafad'a cikin shagwaba, salman kam wani gun ma yake kallo. Tarasa yazatai, hannu tasa tare da zare earphone na kunne daya ta Matso tasa a nata kunnen, wani sauti mai dadi ke tashi, dagaji piano ne,da mamaki salman ya kalleta, ta lumshe ido jin dadin sautin amma wannan kid'an bazai hana mutum jin magana ba wato yana jinta kenan, ido ta bude, sai dai salman tagani yana kallanta, tace sautin yamin dadi, sa hannu yai ya zare na kunnenta, ta hade rai tace dan Allah ni ka kulani, ko fad'ane kamin, amma ni bansan shirun nan. Ganin bashida niyyar mata magana yama juya kansa d'aya gefen, itama komawa d'aya part din tai tasa hannu ta zare duk earphone din ta mike da sauri, salman ya kalleta yace bani abuna? Tace um um naki, tafad'a tare da noke kafad'a ta katasa wajen madubi, ya mike yafara tahowa inda take yacd bazaki bani ba? Tace naki sai ka tsaya munyi magana. Ya karaso inda take, dasauri ta boye a bayanta, ganin yana tahowa yasa sai sauri ta koma wajen gado, yakara tahowa yace bazaki bani ba? Tace naki, inkanaso kacemin ka hakura😉salman ya bita nan fa suka salma tasa gudu shima ya fara binta, ta gado ta haura ta zagayo shima ya bita ta ka ra zagayowa ta hau gado kenan yasa hannu ya kamo hannunta, itama ta fara ja a tare suka fad'a kan gadon, suka yi rigingine kowa na ajiyar numfashi. Can salman ya d'ago ya matso daf da ita yace bani🤔? Yafad'a tare da mike hannu, itama ta d'ago tace ungu? Ya matso da hannun tace naki sai ka hakura, tafad'a tana kokarin tashi, jawota yai ya kwantar da ita ya matso daf da ita yanda kowa najin numfashin d'an uwanshi, yace kinsan me kika min? Yafad'a cikin wata murya mai rikitarwa ga sanyi, a hankali ta kalleshi zuciyarta sai bugawa take itama cikin sanyin murna tace sry I didn't mean to hurt you, yace then? Tace narasa yanda zanyi ne😞 yace akan me? Tai shiru yace ba amsa? Ya fad'a tare da kokarin tashi da sauri tace banasan asake ma fad'a ne, tafad'a tare da runtse ido. Juyowa yai da sauri, baiyi tunanin amsar dazata bashiba kenan, yaji dadi har cikin ransa at least ta damu dashi, ganin yanda ta runtse ido yasa ya turo fuskarsa, zuciyarshi na haskomai bakinta, girgiza kai yai tare dasa hannu ya lakuce mata kumatu yace meyasa baki fad'amin ba? Ta bude ido sai dai ganinshi daf da ita yasa tai saurin murginawa d'aya bangaren tare da zama, tace um um to ba inasan ma maganaba ka fita tafad'a tare da turo baki, murmushi yai yace basai ki min text ba? Tace ince me? Yace abinda kikace yanzu, tai murmushi tare da rufe fuska. Yamike yace kin b'atamin gun kwanciya ki tabbatar kin gyara kafin nasha ruwa😏 yanakai nan yai waje tace ahhhh wai wannan wani irin mutum ne?🤔 Mikewa tai tana gyara tana murmushi, shikanshi a falon zama yai yana murmushi. Nace ku kuka sani😏 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣7⃣ Salman zama yai afalon yai shiru tunaninsa shine meke sashi farin ciki bayan da ba haka yake ba? Idansa ya lumshe fuskar salma ya hango tana murmushi dasauri ya mike tsaya yafad'a a fili mai ke damuna🤔? Salma kam kwanciya tai ganin salman bai dawoba yasa ta mike tayi hanyar falo, lokacin salman ya kashe wutar falon yai hanyar d'aki, salma data fito ganin duhu yasa tafara laluba bango ko zataji makunnar wutar gware sukai, salma ta saki wata kara, dasauri salman ya jawota ya rufe mata baki, yakai bakinshi kunnenta yace is me🙂 ajiyar zuciya tai ya rike ta tare da kunna wutar ta kalleshi tasa hannu tad'an bigi kirjinsa kad'an tace ka tsoratani wlh😰, salman ya rike hannun da ta dakeshi yace dakin d'auka meye? Ta turo baki cikin shagwaba tace tokai meyasa zaka zauna a duhu? Yace d'akin zan shigo shiyasa nakashe, tai ajiyar zuciya tace bakaji zuciyata ba wlh☹ yace kedai kawai kinfiya raki, ta kwace hannunta tare da juyawa,,ya kalleta yace me kika fito yi? Tace hmm.... yace don't tell me fitowa nemana kikai?ta harareshi tace ni? Dalili? Ran salman ya soso yaso tace gunsa tazo, salma kuwa takarasa fridge tad'auko ruwa tace ruwa nazo sha, tawuce d'aki tabarshi agun. Dakin shima ya shigo batare dayai magana ba ya fad'a gado, salma tuni tai bacci, sai dai salman sam yakasa barcin sai juyi yake, kallan salma yake wacce da alama tai nisa a bacci. Ganinai salman ya mike yazo kusa da salma a hankali ya d'agata yakaita kan gado ya kwantar da ita tare da lilibeta, yazauna kusa da ita yana kallanta, mamaki yake yanda sam baisan yadaina kallonta, yadade a haka kafin ya mike ya d'au pillow ya sauka kasa. Ga mamakina gani nai ya kwanta a gunda salma ke kwanciya😳nace prince din?hmmmm... Salma kam bacci yayi dadi gashi sai mafarkin saurayin nan take, suna zaune a bakin ruwa taga ya mike ya far gudu itama ta bishi, ganin yanda yake gudu da alama wani gurin zaije, ita kuma sam batasan ya tafi, gudu take sosai tanaso ta kamoshi sai dai gudun da saurayin yake yafi nata, ganin ya mata nisa sosai yasa ta zauna a kasa tahau kuka, yau ma bataga fuskarshi ba, a zabure ta mike, dai_dai nan salman ya fito daga toilet yayi alwala. Yace lafiya? Ga mamakinta hawaye taji a idanunta, salman ya zauna kusa da ita ya dafata cikin kid'ima yace menene?rungumeshi tai tsam batace komak ba, yace menene? Mafarki kikai? Ta d'aga kai yace mafarkin me? Tai shiru, ahankali ya d'agoda ita yace kidinga addu'a in kikai mafarkin da bashi da kyau, ta d'aga kai tare da kakaro murmushi, yace bari nai sallah tace to, ya juya ya fita. Binshi tai da kallo sannan takalli inda take, mamakine ya kamata, ya akai taganta a gado? Meya faru? Sam takasa tunano komai, mikewa tai tare da wucewa toilet. Salman kam da ciwo jiki yatashi, tun dayake ranar ce rana tafarko daya kwana a kasa duk jikinshi ciwo yake. Sai 6:30am salman ya shigo tana zaune tana karatu, tana kaiwa aya ta rufe qur'anin tareda mikewa taje gunsa, tace ina kwana? Salman ya amsa tace ya akai naganni anan?salman yai gyaran murya tace badai kaika maidani ba😬 ya hade rai yace jiyane naji bayana naciwo shi yasa na kwanta akasa, tai murmushi tace yanzu fa? Yadaina ciwo? Ya kalleta yace a'a, hannu tasa tace in bubuga ma? Ya kalleta yace bansaki ba😏 ta hade rai itama tace dacema akai inaso inma? Ta juya, hannu yasa ya rikota yace serious jikina ciwo yake dannamin plz. Kwanciya yai akan gado tashiga danna mai, ahankali yake lumshe ido bacci mai dadi ne yai gaba dashi, salma ganin yai bacci ta matso da fuskarta inda yake ta kalleshi, jitai zuciyarta na bugawa, sai ta hau shakuwa, dasauri tai falo ta bude fridge ta d'auko ruwa tasha. A kujerar dinning ta zauna tace menene hakan? tadade anan kafin ta dawo d'aki ta kwanta. Karfe 9 ta tashi dan yau zasu gaisuwa, matsawa tai takalli salman tare da murmushi, ga mamakinta shima murmushin yai cikin bacci, jitai zuciyarta yashiga bugawa dasauri takoma ta zauna,wayarta ce tai kara tad'aga tace waye?zee tace banza nice mara mutunci, salma tace duk ni kadai? Zee tace dazu naje gun Abba shiyaban number ki, tace ayya nan suka shiga hira, salma ganin zata tashi kamal yasa tafi to tai d'ayan d'akin, zee tace badai laulayi kike ba? Daga shiga? Salma tai tsaki tace kefa bakida mutunci, zee tace ah to meza'a jira? Salma tai shiru, zee tace badai haryanzu baki bada kaiba? Salma tace dalla nikimin shiru, dan Allah ni akwai abinda nakesan tambayar ki, zee tacw name? Salma tace watace intaga wani sai zuciyarta tad'inga bugawa shine ta tambayeni menene dalili, nikuma bansani ba nace bari na tambayeki. Zee ta kwashe da dariya tace ai kinji matsalar ke bakisan kowa ba sai kamal inafa zakisan karfin soyayya? Salma tace duk sanda nakema kamal? Zee tace oho dai amma kifad'ama mai tambayar ba shakka ta kamo da soyayya mai karfi tunda har zuciyarta take amsawa, cikin tsoro salma tace what? Soyayya? Bakisan me kike cewa ba🤔, zee tace oho sai dai inkim gaskiya zatai amma wannan shine gaskiya, dasauri salma ta kashe wayar tace ah hb? Ni? Ta ina?how? Tana komawa d'aki ta tadda salman bayannan da alama yana toilet, bayan ya fito takalleshi sai kuma ta girgiza kai ta wuce toilet dasauri, ya kalleta yace wannan kuma lafiya? Salma kam haka tai wanka sukuku, tasa kaya. Abinci kuwa ruwan zafi kawai tasha salman yace shikenan abinda zakicI? Tace nakoshi😞yace wasa ne, tace in muka dawo zanci to, yace naji amma meyasa tun d'azu bakya kallona?tace hmm bakomai, yace bazaki kallanba? A hankali tamai alama da bayin dake gun, hakan yasa yai shiru suka mike sukai cikin gida. Sunje bangaren hajiya karama da babba kafin suje gun fulani, ishaq na kalisarta tunda suka shigo yake kallan salma, itakam kasa tai da idanta dan sam batasan wannan kallon,sun gaida fulani nan tace salman rannan ka fita akaita fad'a nikam duk banji dadi ba nasan dai fitar dakai aI da dalili haka kawai bazaka fita ba😞salma takalleta, a iya saninta hanne tace fulani ce taita masifa kodai hannen bata fahimta bane? Muryar salman taji ya ce nasani ai kin damu dani, ishaq ya kalli salma yace salman amma matarnan taka bata magana ne? Salman ya kalleshi yaji haushin tambayar amma ya saki murmushi yace kai ya ishaq ko tana magana yaza'ai ta saki tai ta magana kana gun😏? Haushi ya kama ishaq yace nid'in meye?salman ya kalli fulani yace umma kodan abunda yakeyi zata sake jiki dashi? Yafad'a yana wani mugun murmushi, fulani ta kalleshi ta kalli ishaq bakin ciki ya isheta tace eh mana gaskiya ya fad'a. Salma ta d'ago ta kalli salman mamaki take yanda yake fad'ar bakar magana yana murmushi, wannan wani irin mutum ne? Lol nikaina AYUSHER so nake inji😆 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣8⃣ Duk shiru sukai ad'akin ishaq ya mike a zuciye zai fita, salman ya kalleshi yace yaya ishaq sai ina? Ya juyo a zuciye yace duk inda zani sai na sanar dakai? Salman yai murmushi yace maida wukar yaya adawo lafiya, fulani ta cije lebe inama d'anta ne haka? Amma tana bakincikin yanda salman ya ninka d'anta komai. Salma ce tai kasa dakai tace fulani ayi hakuri abunda yafaru rannan munyi kuskure😞 tafad'a tare dayin kasa dakai, salman ya maka mata harara ta gefen ido amma a bayyane sai yace umma kinji hakuri take badawa bayan ninai laifin, fulanI aranta tace wato kana nufin kai kafi karfin bada hakuri kenan? Salman ya kalleta yasan metake tunani amma a fili yace umma bari mu wuce ina tunanin zamu d'an fita akwai inda zata rakani, yafad'a yana murmushi, sannan ya kalli salma yace muje dear😉 salma ta d'ago aranta tace dear😒? Mikewa tai salman yace umma yau nasanar dake ko? Fulani bakin ciki ne ke neman kasheta amma tad'aure kamar tai kuka ta saki yake tace eh mana, salman ya kalli salma yamata alama dakai muje, salma tafara tafiya jikinta yai sanyi, itakanta tasan bakaken maganganu salman ke fad'a amma ita ta d'auka bakar magana rai abace akeyinta?. Suna Shiga d'aki takalleshi tace dagaske gun Abba zamu😬? Ya hade rai yace saki nai? Tace mene? Yace hakurin da kika bada mana🙄, saki nai? Tace hm ganinai kamar.....yakatseta karki sake banaso, tace amma ai....yace zaki fara ko? Ke ba'a isa ace kaza kice to bako? Salma ta turo baki tace to, salman ya matso yaja leben ta da karfi, ai kuwa ta fara shure_shure, ya saketa tasa kara tace da zafi fa😢tafad'a cikin shagwaba, salman yai dariya yace in ba zafi mezaisa inja? Tace ni wlh ban yarda ba☹ya juya baya yace shikenan in baki yarda ba sai mufasa zuwa gun Abban, dasauri ta dawo gabanshi tace a'a na yarda sosai ma😬 murmushi yai tare dasa hannu ya dungure mata kai yace sai ki fito. Ya juya yai waje, tsayuwa tai a gun tare da daga gun da zuciyarta take, jitai tana harbawa tacw wayyo ni! Yaya ka....dasauri ta toshe bakinta tare da girgiza kai, fuskarta tad'an gyara ta yafa mayafi ta fito. A mota tasami salman tashiga tare da murmushi salman ya hade rai yace da ai nafara tunanin fasa zuwa, dasauri takalleshi tace na'am😱? Yatada mota tare da cewa ina nufin da baki fito ba nan da 5min😏, salma tace ahhh ya fara tafiya, tace hmm yauwa kaga kud'in rannan a jakata sam namanta ban baka ba, tafad'a tana mikowa, hannu yasa ya dunkule hannunta da kud'in yace keep it, salma kam tai sororo jinyanda ya rike hannunta. Shikanshi wani abune ke ratsashi da sauri ya saketa, sai dai salma tana rike da kud'in kuma bata d'auke hannunta ba, akasarima batasan yad'auke hannunsa ba, juyawa yai yakalleta a yanda ya barta, hanni yasa a kafadarta yace menene? Dasauri tai firgigit tadaure tace bakomai tunanin Abba nake. Salman yace karki damu zai warke, kallanshi tai tad'an karkatar dakai aranta tace yaxanyi? In nikad'ai nafara sansa? Tasani sarai ita bata iya so ba. A wani karamin mall ya tsaya ya fita, yana fita salma taji karar waya, wayarta ta duba taga ba ita bace ahankali ta kalli wayar salman, tace oh ankirashi gashi bayannan, tafad'a tare da kallan wayar, number ce, harta kai hannunta zata d'aga tai saurin girgiza kai tace ba ruwana😕. Salman na dawowa tace mai ankiraka yace wa? Tace number, yace ok, yace bazaka kiraba? Ya kalleta yace 4get, ta tabe baki tace nima haka zai dingamin in na kira baya kusa? Batasan afili tafad'a ba jitai yace in kin kira sau d'aya bazan kiraki ba amma in sau uku kika kira bana kusa I promise to call u back. Haushi ya kamata wato sai ma tayi sau uku?tace au in sau d'aya nakira bazaka kira ba? Yace yes saboda inkika kira sau d'aya ai abun ba important bane kenan, salma tadafa kanta aranta tace na shiga uku ni salma🤔. Asibiti suka sauka ahankali suka karasa d'akin Abba, kamal na ganinta yashiga washe baki, sai dai yau salma murmushi kawai tamai tad'auke idanunta, sun gaisa da Abba, nan Abba yasakema salman godiya yace kaganmu ashirye sallama za'a bamu yanzu, salman yace Abba baka gama warkewa ba wacce sallama? Abba yace kayya ai nikam yau gida zani, goggo tace ai fa yadage sai hakuri, salman yace shikenan bari in anso sallamar sai in kaiku gida. Sunzo shiga mota salman ya kalli kamal yace kai sai ka biyomin ko a mashin ne dan gun bazai ishemu ba ko? Kamal ya harareshi yace sai ka fad'a😠nan suka shiga mota sukai gida. Tunda suka iso unguwar salman ke kallan unguwar tausayi duk ya kamashi, yanzu anan salma take? Amma ya hanata karatu a skul? Dasuka iso gidan jikinsa duk yai sanyi ya daure ya ajiyesu ya kalli salma yace ana la'asar zanzo tai murmushi tace to zan kula da wayata😊 yanda inka taho sai ka kirani yace to, harta juya ta dawo tace sai na ganka😊 yace hmm sai kin ganni😊 wani murmushi sukama juna yad'ago zaiyi magana aka sake kiranshi, tace bye tare dayin ciki shikuma yabita da kallo tare da d'aga wayar yasa a kunne. Jiyai ance yayana is me? Cikin kid'ima da rudewa yace what? Aka kara cewa haba yayana ai sai in fishi in kace baka ganeni ba, Ur Farha ce, salman yace what? Farha? Tai murmushi tace naji kunya yayana dabaka d'au muryata ba☹anyway gani a airport kainake jira😊 tana gama fad'ar haka ta katse layin. By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.2⃣9⃣ Salman ciki kid'ima yai hanyar airport gudu kawai yakeyi, yana isa ya shiga kiran farha a gigice sai dayai kira 2 ana ukun tad'aga tace yayana har nayi fishi, salman yace farha? Dariya tai tace yayana kana ina? Nan ya mata kwatance. Sanye take da riga da wando na 'yan kanti, sai dai rigar takai gwiwa, tayane kanta da bakin mayafi karami, jakar dake jikinta irin doguwarnan ce itama black sai takalmi flat akafarta black,tana jan trolley d'Inta. Karasowa tai inda salman yamata kwatance, daga d'an nesa ta hangoshi tasaki murmushi tare da karasowa, sai datazo daf dashi ta ajiye trolley d'in tayi d'age tasa hannu ta rufemai ido, salman yai ajiyar zuciya tare da zare hannun ya juyo a sukwane, tofa kallon juna suka shiga yi, farha ta rufe idanta tace yaya wannan kallon fa? Salman yai gyaran murya yace farha? Kece? Dama zan ganki? Ta turo baki tace ba wani nan bayan kamanta dani?☹ tai maganar cikin shagwaba, salman yace wasa kike kema kinsan I can't, tace nasani yayana kaima kasani ai ko? Tafad'a tana kallansa, yai murmushi yace ina nasani ko mazan paris sun mantar dake ni🤔. Tace su sun isa? Yace waya sani, atare sukai dariya yace muje mota ko? Ta kalli akwatinta sannan ta kalleshi, yace hmm badai ni akeson ind'au jakar ba? Tace yayana nifa mace ce☹kallanta yai ya wucewarsa mota, takalleshi tare da jan jakarta tace har yanzu dai halin nanan. A baya tasa jakar sannan ta bude gaba ta shiga, farha ta kalleshi tace yayana how many years?yace hmm 4 ko? Tace ahh gaskiya mun dade ko? Yai murmushi yace sosai ma, hannu tasa takamo nashi tace yaya kasan meyasa nazo? Ya kalleta yace a'a, tace yaya jinai inban gankaba akwanakin nan kila mutuwa zanyi😪 salman yace haba farha meyasa kike fad'an haka? Tace yaya bakasan yanda nakeji ba, gashi narasa dalili dana ma mum maganar zuwa hanani tai, yace y? Yace cemin tai wai ko kayi aure😄ta d'auka zan yanda in hakura da zuwa, salman ya kalleta yace gaskiya tafad'a farha, cikin tsananin mamaki tace what?me kake nufi da hakan? Bai bata amsa ba yaja motar yace gida ko? Tace eh amma....ganin ya d'auke kai yasa kawai tasa kuka, daurewa kawai yake dan sam bayasan kuka, ganin yanda take shesheka yasa kawai yai parking ya kalleta yace farha?dasauri ta matso ta rungumeshi, janyeta yad'anyi sannan ya miko mata tissue yace bansan kukan nan kinsani sarai, bari in fita inkin gama sai inshigo, yafad'a tare da mikewa zai fita, dasauri tajawo hannunsa tace nadaina, karka fita plz. Yakalleta sannan ya shafa gefen fuskarta yace yauwa farha, kallanta tai tace yaya amma......yace farha please karkibatan rai bayan inajin farincikin ganinki, tace cewa fa zan kasai min icecream😰murmushi yai yasan waskewa tai amma sai yace bari muje a siya. Haka farha taita sashi yawo daga tace ka za sai tace ka za har suka kai 5 sannan sukai gida. Farha kanwar matar sarkice wato mahaifin salman, lokacin salman na 10yrs Abbansa yakaishi paris gun kanwarsa bayan mahaifiyar salman din ta rasu, anan suka kulla wata muguwar soyayya da shakuwa tsakaninsa da farha, sai dai Abba yabada umarnin gaggawa akan salman ya dawo gida, wannan dalilin yasa salman ya rabu da farha kuma bai karasa karatunshi daya fara acan ba. Salma kam na zaune sai kallan waya take amma sam bataga salman ya kira ba, kamal dake zaune yana mata magana sam batasan me yake cewa ba kawai dai tanacewa eh, ganin hankalinta ba'a kansa yake ba yasa yafit, Abbane ya kwalla mata kira dasauri ta mike ta karasa gunshi. Abba yakalleta yace salma dare yafarayi kinga ankusa kiran magriba, ki kira salman kiji, tace to Abba. D'akinta tashiga tare da kiran wayarsa, sai dai har kira uku tai bai d'aga ba kuma bai kira ba, zama tai taredayin shiru tace ina ya shiga? Salman kam shiya raka farha gun fulani, nan akasa aka gyara mata d'akin dazata zauna, tajashi tace yarakata d'akin nan suka shiga taitamai zance sam yamanta da d'auko salma ga wayarsa na kan madubin farha,a silent take, sarai ta kula da wayar na haske amma ita batasan salman ya tafi, hakan yasa ta juya wayar. Sai da salman ya mike zashi masallacin jin kiran sallar magrib yad'au wayarsa missed call din daya gani na salma ne yasa ya kalli farha yace farha am sry bari inje indawo, takalleshi da shagwaba tace yayana yaushe rabon mu hadu? Ina laifin kai sallah a nan? Ya kalleta kamar baisan metake nufi ba yace zanje mosque daganan zanje wani guri, ta mike tace yaya ina kuma? Nifa yau so nak........ga mamakinta bata karasa maganarta ba taga ya fita. Salman kam yana fita ya kira wayar salma,itakam hartagaji da mitar goggo na tazo ta tafi, ganin kiran salman yasa ta mike da sauri ta d'aga, salman yace kinjini shiru ko? Tace wani abun ne ya tsare ka? Yai murmushi yace ganinan zuwa, kafin tai magana ya katse, ta girgiza kai sannan tai murmushi, goggo tace shi ne? Salma tace eh gashinan, goggo tace ah to gwara dai, dan naga akwai wata yarinya a garinmu daga zuwa ganin gida mijin bai kara komawa ba sai takarda tagani, salma tace shi ai ba haka yake ba😒goggo tace iye? Lalai su bera, salma ta juya zatai d'aki ganin kamal tai a tsaye da alama yaji me suka ce ta, dasauri tai d'aki. Salman ya iso ya kira salma tafito, kamal na kallanta kamar yai kuka sai dai ba yanda zaiyi, salma ta shiga mota ta kalli salman tace irin wannan jirgawa?ya juya yace don't tell me harkin gaji da ganin gidan kinaso ki tafi naki🤔? Dasauri tace bafa haka nake nufi ba nufina ba kira🙄. Wata sansanyar dariya yai yace abinda na dade bangani ba yau nagani shiyasa na sha'afa, duk da gaban salma ya fad'I amma tadaure tace da alama wannan abun nada matsayi, salman yace ehm sosai,yafad'a yana kallanta, ta bata rai tace mutum ne?yace eh, cikin tsoro tace mace?kallanta yai yace lawyer kika koma? Tace bahaka bane yanda kai maganar ne ai☹yace hmm. By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣0⃣ Atare suka saho, har suka isa part d'insu, sai dai me? Suna shiga falo salma taga wata budurwa zaune tana kallo, mamaki yakamata, budurwar tana ganinsu ta mike da sauri tace yayana......sai dai maganar ta ta tsaya a wuya ganin salma, kallanta ta shiga yi, badai itace matar ba?wannan kyakyawar😳? Salma ma kallanta take, kamar tasan fuskar. Salman ne ya karasa shigowa tare da cewa yaushe kika zo? Sai alokacin ta d'aure ta kalleshi, cikin sanyin jiki tace d'azu, ganinai baka dawo ba😕. Salma ta kalleta sannan ta kalli salman tamai alama dakai wace? Murmushi yai sannan yamatsa gun farha yace kefa dadina dake kenan farha, ba hakuri. Gaban salma ne yafad'I farha? Farha? Farha? Abinda zucuyarta keta maimaitawa kenan, da sauri tai hanyar d'aki, farha ta kalleta tace in_law ku nake jira muyi dinner fa? Salma ta kalleta sannan ta d'auke kai riga da wando ne a jikinta 'yan kanti sai d'ankwalli data d'aura, salma bata amsa mata ba takara yin hanyar d'aki, salman yace magana take miki fa? Salma ta juyo kamar tai kuka tace ina zuwa, yace alright. Salma nashiga d'aki ta zauna a gado dabass...ta rike kanta tace nashiga uku, meke faruwa? Can wata zuciyar tace kika sani ko kanwarsa ce uwa_daya uba_daya? Sai a lokacin tai _Hamdala_ sannan ta d'an mari fuskarta kad'an da hannu biyu tace hakane, salma kidaina tunanin komai. Toilet ta shiga sannan ta fito, suna zaune a dinning farha na kusa da salman, ahankali salma ta karasa tazauna, farha kam ta tsorata dakyan salma sai dai bataso agane. Har salma takaraso ta zauna idan farha na kanta, daga d'an nesa dasu kad'an taxauna, farha tace in_law kin fito? Salma ta kakaro murmushi tace yp, salman ya kalleta sannan ya d'auke kai, farha ta fara jawo kwanuka tafara zubama salman abinci, salma naxaune na kallam ikon Allah, bayan farha ta gama sai ta bud'e kwanon karashe,tace kai kamar da tafarnuwa, tafad'a tare da d'an d'anawa, dasauri tasha ruwa ta kalli bayin dake gefe tace ke meyasa kuke sawa abincinsa tafarnuwa?salma tace bangane ba? Meye da ita? Bayan magani ce? Farha tace haba in_law yayana fa is allergy to tafarnuwa, jikin salma yai sanyi takalli salman sai dai takasa cewa komai. Salman ya kalli farha yasaki murmushi yace ya isa, basu sani bane, farha tace nidai akula kar a jama wani abun, in rasa ya zan, salma dake kallan salman tuni ta maida idanta kan farha, cikin tsananin mamaki tace me kika ce? Farha tace bakomai, salman ya kalli salma yace kici abinci, salma dakyar ta zuba sai dai ko loma d'aya takasa ci, farha ta kalli salman tace yayana kasan nima nadainacin tafarnuwa? Yace why? Tace yaxa'ayi inci abinda baka ci☹? Salma kam ranta yagama b'aci da karfi ta ajiye cukalin dake hannunta, dukansu suka juyo tamike tare da kallansu ko magana bata musu ba tanemi wucewa, tazo saitin salman, yasa hannu ya riko ta, ta tsaya cak,batare da ta juyo ba,idanunta taf kwalla, salman yace kI koma kici abinci,salma ta had'iyi wani abu, ta runtse ido tace na koshi banajin yunwa, salman zai magana farha da kishi ya zo mata wuya tai sarin tasowa ta raba hannunsu ta rike salma tace in_law kici abinci plz? Salma ta fizge hannunta tace nace miki na koshi, ko bakya fahimtar yaren? Tana kainan tai d'aki, farha ta kalli salman tace yayana matarka ta iya fad'a, sannan kamar kuka zatai, an ma.........kafin ta karasa taga salman ya mike, d'akin ya shige ya barta anan. Salman na shiga ya salma azaune tana kuka, ya kalleta yace ke kuma fa? Dasauri tafara goge hawayenta ta mike zatai toilet da sauri ya jawota jikinsa ya rungume yace menene? Baki da lafiya? Bakin ciki ya kamata wato baimasan meke damunta ba? Salma ta kwace jikinta tace kaina ke ciwo, yace eyya akwai magani a drawer inkin fito kisha, yafad'a tare da juyawa, salma tace ina zaka? Yace gun farha,jitai kamar tasa ihu, tad'aure tace nikam farha ya kuke? Yace oh banfa fad'a miki bako? Cousin d'ina ce,'yar kanwar Abba ce. Salma jitai kamar ta mutu sai dai gani tai salman ya bude kofa ya fita, komawa tai tazauna akasa, hutunansu ta tuno, tace shikenan nikam😰. Salman na fita yaga baiga farha ba,dakinta ya wuce, tana kwance tana kuka, girgiza kai yai tare da karasawa, ya d'au tissue yazauna kusa da ita, yace ga tissue, zan fita inkin gama kukan nadawo, yafad'a tare dayin kamar zai mike, dasauri ta rungumoshi ta baya tace karka fita plz yaya, yace to meyasa ki kuka? Tace kawai gani nai kamar now I am useless in ur lyf, salman yace ya zaki fad'I haka bayan kinsan matsayinki? Yafad'a yana zare hannunta, kara kankameshi tai tace yaya naga fa yanda ka mike dazu, yace naji to sakeni sai muyi magana ko? Tace uhm uhm nidai a haka, nafijin dadi☹ tafad'a cikin shagwaba, murmushi yai yace badai haka kike taba mazan paris bako? Dasauri tasakeshi tace haba yaya😕nifa ban taba rike hannun wani ba bayan kai, ya kalleta yace anya kuwa? Tace 'yar iska kamaidani? Yace haka kalmar take nufi? Farha tace ohh yaya bakar magana fa kake fad'amin☹ yai murmushi yace kedai kin fassara kawai. Ta sauko tazo gabansa ta tsugunna tace yaya plz karka yada ni, yace yaza'ayi in ya da 'yar uwata🤔?tace bafa irin wannan ba, nasani sarai kai bakasan auren ko mace biyu shiyasa nake farin ciki,bazakamin kishiya ba to yanzu gashi kayi aure yazamuyi?salman ya kalleta tare da mikewa yace umarni kike nema ki bani ko me? Tace ba haka bane yaya, amma ai kaga ni kakeso, sai ka rabu da waccen ka aureni ko? Salman yakalleta yace farha kanki d'aya kuwa? Itama ta mike tace menai kuma? Yace bakisan niba kenan indai kinsan banasan kara aure ba, ban kuma fi tsanar saki ba😏 . Yana kainan yai hanyar kofa binshi tai da sauri tasha gabanshi ta tare kofa da hannunta, yace me kike?tace to ya kake so inyi yaya? Yace bani gu farha akwai abinda zan? Hawaye ya zubo mata tace zakagun matarka?yace oh god farha meke damunki? Tace kishi tafada tare da tsugunnawa agun tasa kuka mai tsuma zuciya, tugunawa yai ya jawota jikinsa yana shafa bayanta, sai dai baice komai ba, farha kam kuka kawai takeyi. Salma bayan tayi sallar isha'I tai shirin bacci, sai dai har lokacin salman bai dawoba, ahankali ta bude kofar falon, ga mamakinta ba kowa a falon, gabanta ya fad'I badai suna tare ba? Nikam na shiga ukuna🙆🏻 kanta taji ya shiha sarawa ta kalli maganin kawai taga bazata ma iya sha ba, ta rufe drawer tare da mikewa da kyar tai shimfid'a, ta zauna tana jiran salman saI dai har 1q ba labarinsa, har bacci yafara d'aukanta. Salman kam nacan dakyar farha tai shiru nan tacemai ya tsaya ta nunamai wani abu, nantashiga kunnamai videos dinta a paris tana yawon inda suka saba zuwa da salman,dariya kawai suke sam abin yad'aukemai hankali. Bai ankaraba sai ganin 12:30 yai yace farha dare yayi so sai😳sarai tasan time, amma sai tace inalilahi yaya yazamuyi?gashi 12 ake kulle ko ina ko? Salma yace eh, yanzu yazanyi? Tace yaya in akaga ka fito daga nan sai anyi gulmar abun, kawai kabari da safe tunda fulani ba fitowa takeba, in an sauko sai ka fita kamar irin daga gunta kake d'in nan, salman yai shiru, yace a'a idan na kira salma nace tazo mu tafi tare ba wanda zai zargi komai, yafad'a tare da laliban wayarsa, haushi yakama farha. Sai dai me? Wayarsa nakan dinning🤔yakalli farha yace nabar wayar a gida, dadi yakamata tace yaya ka kwana anan kawai, yace me zaisa inkwana anan?tace yay.....ya katseta there must be another way bayan wannan🤔. Nikam haushi duk ya ishen na d'auko sanda nace aikuwa ka kwana anan salman rad'a ma sandarnan zan😣😏. By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣1⃣ Farha tace yayana.....salman ya kalleta sannan yaja hannunta ya zaunar da ita akan gado, yace Farha ko za'ai maganata I can't sleep here, ko in cemiki I won't, kallansa tai idanta yai rau rau tace banaso ama magana ne, yace in banasan magana sai kuma inkwana d'aki d'aya da ke? Ba muharramata ba? Tace amma yaya ai ni.....yace farha please, yasaketa tare da juyawa takalleshi kwalla ta zubo mata, tana tsananin san salman kishin salma ne yashiga taso mata. Salman kam fitowa yai kai tsaye yai hanyar kofa, masu kula da gun suka kalleshi sukace ranka ya dade ya muka ganka anan? Yace in d'a ya zauna agun mahaifiyarsa laifine? Ko in ishaq ne yazauna zakumai magana? Dasauri sukace kayi hakuri ranka ya dade, nan suka bude kofa, salman ya fita. Salma kam tana zaune bacci take amma mai wuya, dan wani zazzafan zazzabine ya rufeta ga kanta ciwo yake tana zaune a takure kawai sai nishi takeyi. A hankali salman ya shigo, gaban salma ya fad'I tare da d'agowa da kyar ta kalli agogon d'akin d'aya saura, ahankali ta maida kanta wasu kwalla suka sake zubo mata, salman ya shigo tare kallan inda take,kallanta yai tare da saurin karasawa inda take ya tsugunno kusa da ita, ahankali yace menene? Yanaganki a haka? Haushin tambayoyin nan ya kamata, salman ya sa hannunsa a goshinta tare da cewa kan ne? Sai dai me? Yanda yaji kanta yad'au zafi yasa ya d'ago fuskarta, hawaye ne ya gangaro mata, cikin rikecewa yace salma menene? Ya naganki haka? Y are u burning? Idanta ta runtse datake jin yamata nauyi, sannan ta girgiza mai kai ahankali tace dare yayi kaje ka kwanta, kallanta yai cikin tsananin tausayi yace wake zancen bacci kina cikin wannan yanayin? Ta bude idanta ahankali batace komai ba, salman baisan sanda ya jawota jikinsa ba ya rungumeta, sai dai zafin jikinta har jikinshi yakeji, d'agata yai kamar 'yar tsana ya d'aurata akan gado sannan ya miko mata magani, kallansa kawai take dagaske san salman ne yaja mata ciwo? In haka ne ta shiga uku, zuciyarta bata mata adalci ba zata had'ata da san maso wanI. Hure mata ido salman yai yace me kike tunani? Kallansa tai tare da amsar maganin tasa abaki ya mika mata ruwa ta sha. Gyara mata pillow yai yace kwanta, kallansa tai inama wannan abun acikin soyayya ne?salman ganin tayi shiru yasa ya kwantar da ita da kansa, tace kaifa?yace don't worry. Shiru tai tana kallansa sai hawaye, ganin haka yasa ya matso ya zauna kusa da ita yace da ciwon dake damunki zakiji ko da kuka me aka miki? Dasauri ta goge tace ba kuka fa nake ba, in ima zazzabi haka nake, yace au, sannu, juya baya tai ta runtse idanta, wannan wani irin bala'I ne? Salman sai dayaga tayi bacci sannan ya kwanta a kasa, ranar kam makara sukai sallar asuba, sai 7:30 salma ta tashi dakyar tai alwala tai sallah sannan tazo kusa da salman ta tsuguna ta kura mai ido, hannu tasa akusa da kuncinsa, sannan takai hannun saitin bakinshi, gani tai salman ya bude ido ai kuwa idanunsu ya hadu, da sauri salma ta mike, jikinta duk ba karfi. Salman ma ya mike yace haka ake tashin mutum? Ta kalleshi batai magana ba dan gabanta fad'uwa yake, salman ya karaso kusa da ita yasa hannu akan goshin ta sannan yai ajiyar zuciya, yace Alhamdulila naga zazzabin ya ragu sosai, salma kam kallanshi kawai take. Kamo hannunta yai yazaunar akan gado sannan ya wuce toilet, ta bishi da kallo. Ishaq yazo shiga bangaren fulani yaji masu gadin gun na gulma ya kallesu yace kuzo nan, suka karaso da sauri ishaq yace menene? Sukai shiru, yace kun fad'a kosai na sallameku?d'ayan yace dama jiya ne yarima salman sai d'aya saura ya fito daga gun fulani shine muke tunanin ko laifi yai akamaI fad'a kayi hakuri yarima mai jiran gado. Ishaq ya shiga ciki da sauri, yazo shiga yaga farha na fitowa, yace farha? Jiya ance kinzo amma danazo ganinki bakya nan, tace muna tare da ya salman ya grn? Ishaq yace sai ina da safen nan? Tace zanje ganin yayana ne, ishaq yasa dariya yace da matar tasa zaki? Tace to meye? Tafad'a tarw da wucewa, ya bita da kallo yace tab amma wannan......sai kuma yace wait..to ai ni adadi na ko😬?nace a dadinka na me?. Ishaq ya shiga suka gaisa da fulani nan ya tambayeta jiya me salman yai?fulani tace name? Yace ance jiya sai d'aya saura ya fita badaga gunki yake ba? Fulani yace nI? Badai niba, ishaq yace badai yana........wata dariya yasaki itama fulani ta d'ago tasa dariya yace umma lokaci yayi inaji da Abba zai daina damuwa da salman😂. Farha ce ta shiga bangaren su salma, sai dai ba kowa a falon, ga breakfast nan da alama ba wanda yaci, Haushi ya kamata badai salma tasa yayanta a d'aki ba abincin safen ma taki bari yaci?wani mugun kishi ya kamata kawai ta saki wani kara, salman wanda ya fito daga wanka yanzu, da salma dake cikin bargo, suka fito da sauri, da bayin dake bangaren duk suka fito,farha suka gani kwance tana murkususu akasa, hanne ta kalleta da mamaki, yanzu fa taganta a tsaye?farha kam sai murkususu take da sauri salman ya karasa ya d'agota yace farha menene? Duk ya rikice, salma ta kalli farha dake rike da ciki mamaki take bata fara ciwon cikim ba sai anan?haushin yanda salman ya rikice shine duk ya isheta, jiri ta faraji, ahankali ta juya tai d'aki batare datace musu komai ba, salman ya kalli farha datad'an rage murkususun yace sannu? Ya lafa? Tad'aga kai, nan bayin sukai waje, yataimaka mata ta zauna akan kujera. Ishaq zaune agaban sarki yana hawaye, sarki yace menene? Kaki magana? Ishaq yace ranka ya dade bansan yaxanyi da kanina ba bayajin maganata sam, sarki yace salman ko?meyai kuma? Yace baya gudun magana yanzu jiya fa sai d'aya saura ya fito daga d'akin farha yanzu me mutane zasu ce😰? Ran sarki ya b'aci nan yasa akira salman. Salma kam a d'aki kwanciya tai sai taji waya ahankali ta d'aga zee tace Amarya ya ango? Salma tace ni kyaleni dan Allah banajin dadi zee tace kodai laulayi kike? Jitai kamar ana magana a falo, dasauri tace zee ina zuwa. Dasauri ta fito, fadawa tagani tace lafiya? Tafad'a tana kallan salman dake zaune ko ajikinsa wayama yake dannawa, ga farha a kusa dashi, bafaden yace umarni aka bamu mu taho da yarima salman, tace umarni? Laifi yai ko me? Bafaden yace bamu sani ba sakon sarki ne, farha ta harari salma sannan tace kaji yayana. Salman ya shareta,salma ta karaso kusa dashi ta fizge wayar yad'ago rai abace yace meye hakan? Tace mahaifinka ke kiranka, salman zai magana sai kuma ya fasa, yace nasani ban wayata? Jitai jiri na d'ibarta ya kalleta yace lafiya? Daurewa tai tace please kaje prince, ya kalleta ganin ta juya tayi hanyar d'aki tana d'an tangadi. Kallan fadawan yai ga mamakin farha jitai yace ina zuwa, ya wuce d'aki,a kwance ya ganta ya matso daf da ita yace lafiya? Jikin ne? Tace plz kaje gun mahaifinka, yace zanje kawai dai nasan gulmata aka kai, ta kalleshi tace wa? Mikewa yai yace wasu, sannan yace ki d'aure kici abinci, bansan how long zan kai acan ba, kafin tai magana ya fita, ko kallan farha baiyi ba yace muje, nan suka rufamai baya. Farha jitai kamar ta mutu By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣2⃣ Salma naji sanda salman ya fita, kanta dake sara mata tadafa,jin ana knocking yasa ta mike da kyar, hanne ce tace hanne ya akai? Hanne tace yarima ya bani umarni dazai tafi insa kici abinci, salma ta daure ta karaso falo tazauna ta kalli hanne tace hanne kinsan abinda yai aka kirashi? Hanne tai shiru, salma tace kifad'amin koma miye ba komai. Hanne tai shiru sannan tace naji ance wai jiya da daddare sai d'aya saura ko ya fito daga d'akin.....sai kuma tai shiru, salma tagane me ke faruwa, kwalla ya taru a idanunta, zatai magana taji hanne tace gimbiya nikam banasan matar nan, d'azu fa lafiya kalau tashigo naganta fa a tsaye amma wai ima fita naji kararta, nikam bata burgeni😞 salma tai shiru, can tace yanzu tana ina? Hanne tace ta bishi, salma najin haka ta mike tai d'aki tad'au waya takira zee, zee tace kingama? Salma tace zee ki bakin ciki zai kasheni, zee tace name? Nan salma tafad'a mata zee tai tsaki tacs kefa banza ce, zamq zakiyi ta kwace miki miji? Salma dake rike da kanta tace zee ba 'yar kasar nan bace☹salma tace ko 'yar inace nikin ban haushi ma, salma zatai magana taji zee ta katse layin. Runtse ido tai, nikaina bansan meta tunoba sai ganinai salma ta mike ta shiga toilet wanka tai shaf_shaf ta zura kaya tasa mayafi,duk da batajin dadi amma cikin sauri tai shirin, ta fito. A waje taga su hanne tace hanne muje, hanne tace ina? Salma tace muje gun mai martaba, hanne ta zaro ido, salma tace muje nace ko? Hanne jiki na rawa tace to, nan sukai hanyar bangaren sarki. Salman na zaune sai da mai martaba ya sallami kowa sannan yadawo kan salman sai dai dul fad'an dayai salman baice kala ba, hakan yakara tunzura sarki, ya kalli salman yace san farha kake? Insan ta kake to ka aureta banasan iskanci, salman dai bai magana ba, sarki zaiyi magana wani bafade yace mai martaba hajiya farha na neman iso, da mamaki sarki ya kalli salman, sannan yace ta shigo, farha na shiga tafara hawayen munafurci sai dai kafin tai magana bafaden yakara cewa mai martaba gimbiya salma na neman iso? Sarki yace salma? Salman ma da tunda yazo bai d'ago ba amma jin ance salma yasa ya d'ago, farha ma haka, sarki yace ta shigo. Salma ta shigo a nutse, ta tsugunna ta kwashi gaisuwa sannan takalli farha dake kukan munafirci sannan tai kasa dakai tace ranka ya dade duk laifinane😪,sarki yace laifinki? Kinsan me kike cewa salma? Mijinki ne fa ya munafurceki? Salma takara kasa dakai hawaye ya zubo mata tace jiya wajen 11:30 zazzabi ya rufeni muna tare da farha lokacin zata tafi, yanda taga ina zazzabi ga dare yayi, salman yace zai kira likita shine ita kuma tace tanada magani, shine ya bita ya amso, salman da farha a tare suka kalli salma cikin tsananin mamaki, sarki yace to 11:30 meyakaishi yin awa d'aya a d'akin? Salma tace mai martaba kasan jiya tazo, dole sai ta duba kayanta, sarki yai ajiyar zuciya wani dadi ya kamashi, ya kalli salman yace salman ai sai kamin bayani tun farko, yace kema haka farha, salman yai kasa dakai cike da mamakin furucin salma yace ayi hakuri, sarki yace na hakura ni abinda banaso inji ana gulmarka da zubar ma da k'ima, amma yanzu tunda na gane kowa ya fad'I abinda yaga dama bazan kula ba, salma tace mun gode mai martaba. Tunda salma ta shigo jikinta rawa yake, bata iya karya ba, gashi ba lafiya gareta ba, sai dai tanaji tana gani bazata bari a d'auki mijinta d'an iska ba, bayan tasan ba haka bane, munafircin farha ne tadaina bari yana tasiri akanta. Nan sarki ya kara musu nasiha sannan ya dinga shima salma albarka,farha kamar ta mutu, akarshe yace su koma bangaren su. Sukai godiya suka mike, suna fito wa salman yaga yanda salma ke tafiya ya matso daf da ita yace zaki iya karasawa? Kema baki da lafiya meyasa kika taso? Harara ta makamai tace da kai ka kawoni? Ko kai kasani zuwa? Mamaki ya kama salman kafin yai magana ta kalli hanne tace hanne rikeni, da sauri hanne ta matso ta riketa, farha dake tsaye salma ta kalla ta watsa mata Harara sannan suka wuce, salman ko kallam farha baiyi ba yabi bayansu salma. Farha da sauri tai d'aki tafad'a gado tasa kuka ta raina salma ganin kamar bata waye ba, yau gashi salma ta ruguje mata komai, bayan taso tafad'ama sarki a hadasu aure😠. Salma na shiga ta wuce d'aki, hanne tace abincin fa? Salma batai maganaba tai d'aki,tafad'a gado,har alokacin bata ware ba, salman ya shigo da sauri, ya zauna kusa da ita, dasauri ta juya, yakara zagayawa nan ma ta juya, kawai yana juyawa ya kwanta tare sa hannunshi a kafad'a ya riketa, kallan juna sukai? Yasa hannu akanta ahankali yace jikinki zafi, ture hannunsa tai tace meya dameka?salman yace meyasa kikai? Takalleshi tace me? Yace kareni..tace ni ban kareka ba kaina na kare, ya jawota jikinsa ya rungume yace nasani ni kika kare, naji dadi kin yarda dani, hawaye ya zubo mata, yace nagode, ahankali tace for? Yace baki tambayeni ba, sannan kin yarda dani, tureshi tad'anyi sai dai da sauri yakara jawota, ahankali tafara kuka mai d'an sauti nan ya shiga lalashin ta, sun dade a haka kafin ya mike, falo ya fito ya kalli hanne yace zubo min acinci a plate, tace to, nan ta zubo ta miko mai, ya shigo tare da ajiyewa yataimakama salma ta jingina yasa pillow ya d'aura mata abincin, ta kalleshi cikin shagwaba tace nifa banjin yunwa, cokali ya d'auka yace wasa kike bude bakin, yafad'a tare da mika mata, ahankali ta amsa nan ya dinga bata dakanshi, salma kallanshi kawai take, sonshi na dada ratsa mata jiki... By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣3⃣ Sai dayaga ta cinye tsaf sannan ya mike, ta kalleshi tace skul fa? Yace kiji da jikinki, ta turo baki tace to kamaci abincine kai? Ya juyo yace cikinki ne? Harararsa tai tace ni ai cikinkane kasani naci dole🤔? Yai wani murmushi yace saki nai? Dama can yunwa kikeji😏 ta kwanta akan gado tace shikenan tunda haka kace,bazan kara ci ba☹. Matsowa yai kusa da ita ya tava goshinta yace hmm gashi dai zazzabin ya ragu sosai bare ince surutan zazzabi kike🤔. salma ta ture hannunsa tace abinda yafi🙄 yai murmushi tare da kama leben bakinta tafara jijiga kai, yace wato baki da lafiya amma bazaki bar fitsara ba ko? Dakyar ta ture hannunshi tace bafa ni da lafiya😞tai maganar cikin shagwaba, salman yai dariya tare da bud'e drawer yace mike kisha magani, tace uhm uhm yace kin tashi ko kuwa? Ta juya baya tace ni ba ruwana dakai, yai murmushi yace naji amma tashi kisha magani, ganin taki tashi yasa ya d'agata tare da miko mata magani ta amsa sannan yabata ruwa tasha, yakalleta zai yi magana yaji ana knocking ya kalleta tafara kokarin tashi, yace let me check, yai hanyar kofa. Yana budewa yaga farha, da mamaki ya kalleta yace farha ya akai? Salma dake zaune tanajin sunan taji gabanta ya fad'I, farha ta kalli salman tace yaya so nake ka rakani gidan dangin dad d'ina, salman yace bazaki iya zuwa ke kad'ai ba? Tace yaya kaima kasani fa😰 tafad'a tare da share kwalla, salman yace shikenan amma yakamata ki saba dasu farha, salma dake kwance ta mike, fita zasuyi tare? Kafin ta nemo amsar tambayoyinta taji salman yace bari nad'auko key, salma dake kwance kamar tai ihu. Salman ya shigo d'akin ya kalli salma yace zan fita, salma ta sauko daga kan gadon tace nima zani🙄salman ya kalleta yace ina? Tace nagani da kwanciya so nake in fita☹salman yai wata dariya yace bafa ki da lafiya? Tace ai na ware, yace don't tell me kishi kike🤔 dasauri ta juya tace wa? Ni? Inji wa? Yace to meye na mikewa kice xaki fita? Tace bana fad'amaba😞 yace shikenan muje tai murmushi ta gyara fuskarta sannan ta yafa mayafinta. Farha na zaune tana auna yau intaja salman sai 11, motsin kofa taji, ta mike da sauri sai dai me? Salma tagani da salman😳cikin jin haushi da kishi tace yaya meye hakan? Salman yace me? Tace yanaga in_law? Tafad'a tana kallan salma, ya hade rai yace kin manta matatace? Tana da right?farha tace ba haka nake nufi ba amma....yace inzaki muje in bazaki ba to. Farha ta kalli salma dake murmushi jitai kamar tasa ihu, salman yace ke nake jira, tace zani mana yaya😕 yace muje to, nan sukai waje. Salman ya bude mota ya shiga ga mamakin salma gani tai farha tashige gaba, tsayawa tai tana kallan ikon Allah, jitai salman yace bazaki shigo ba? Salma ta makama farha harara tare da bud'e baya tunani take ko ta jawota?sai dai akwai fadawa a gun, hakan yasa ta daure ta shiga ba. Zama tai ta jingina da jikin kujera, ta hade rai, farha ta kalli salman tace yaya kasan me?yace a'a tace kullum sai naje shagon nan dakake siyomim ice_cream, salman yai murmushi yace amma yanzu kindaina shan ice_cream sosai ko? Tace eh mana tafiyarka tasa na rage dolena, tai maganar cikin wani salo. Salma kamar ta mutu, ta kalli salman taga yana murmushi jitake kakar ta fita daga motar, salman ya kalli salma ta mirror yace jikin ne? dakin kwanta, ta kalleshi tare da daurewa ta saki murmushi tace muna tare a mota ina kallon gari inafa zan kwanta? Salman ya kalleta cike da mamaki, amma sai ya danne yai murmushi, farha zatai magana salma tai saurin cewa nikam a bayan nan bana ganin komai sosai,salman yace meyasa to baki zauna a gaba ba? Ta harari farha tace kanwata ta rigani shiga yazanyi? Salman ya kalli farha wacce kalaman salma sunzo mata wuya, wai kanwa? Tama raina mata hankali, tasani sarai ta girmeta, salman yace farha fa ta girmeki duk da bansani ba, salma tai murmushi tace ai ni matar wanta ce ko? Tafad'a tare da dafa farha, murmushin yake tai tace haka ne, salman yai murmushi yace lalai, salma aranta tace nadaina yarda kima min iskanci, ke ba kishiyata ba bare ince..... Sun iso wani makeken gida, salman ya isa gun parking sannan suka fita, salma ta zauna a mota, salman dake waje ya leko yace me kike? Tace naga bataso inzo, kuje kawai, salman yace wasa take kamar baki santa ba? Tace bansanta ba😏 yace in barki anan kike nufi, tace eh, salman ya fito tare da kallan farha yace muje ko? Tace in_law fa? Yace muje kawai, harsun yi gaba salma tai tunani yanzu tana nan in farha ta fara ma salman kisisina fa? Dasauri ta mike ta fito. Sun kusa shiga bangaren farha ta hango salma da mamaki tace yayana ka ga? Salman ya tsaya har ta iso, ya kalleta baice komai ba, tace nafasa zaman motar, ganinai gwara muje nima nagaidasu, salman yai murmushi yace kin kyauta dan kuwa har biki sunzo, itama murmushi tai tace kanwata muje 😊 farha ta harareta tace to. Ishaq ne zaune kusa da fulani, ya kalleta yace umma dagaske kike salmata ita taje gun sarki ta kare salman? Fulani tace Wani zancen banza Ne wannan salmata?baka da tunani ko? In wani ya jika fa?yace wake zancen wannan kina ganin alama ne na tafara san salman bayan ni yakamata taso? Fulani taI tsaki tace shiyasa haryanzu Abbanka bai daina tunanin salman zai gaje shi ba dan sam kai baka san rayuwa ba, ishaq ya mike cikin b'acin rai yace nafad'amiki kidaina had'ani da wannan yaron tun ina karami, ke komai sai kice salman yafini😡ya juya azuciye yai waje, tsaki tai tace tunda nake bantaba ganin salman ya nuna bacin ransa a waje ba ko ran nasa ya baci amma wannan...?I wish ishaq ne salman😕... Nikam Ayusher dariya fulani ta bani, nace stop dreaming😂😂 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣4⃣ Suna isa farha ta dana kararawa, ba'afi 2min ba akazo aka bude, daga ganin wace ta bude mai aiki ce ta gaishesu tare da tambaya, salman yace hajiyar nanan? Tace a'a ta fita sai mami dasauri farha tace a'a yaya ma dawo wata ran, ya kalleta yace Baffan fa? Tace tare suka fita da hajiyar, ya kalli farha tace a'a yaya kasan halin mamin nan, muje kawai madawo daga baya. Juyawa yai batare dayace komai ba, salma ta kallesu aranta tace mekenan? Itama dai batai maganar ba har suka isa mota, farha ta bude gaba zata shiga salma ta rike kofar tace kanwata kin manta? Farha ta mata wani kallo salma itama ta harare ta, tunani take wanda da kishiyarta ce yazatai?itama farha tunani take lalai inta auri salman sai ta gyarama salma zama, salman ne ya kallesu yace ke farha ki koma baya mana dolene sai kinzauna anan? Tace yaya ni nafisan zama kusa dakai☹salma tasa dariya tace me? Salman yai tsaki yace bansan iskanci ki wuce baya itaba matata bace? Farha ta bude baya tana turo baki, salma ta shiga tare da hade rai, salman yaja mota, sun dade suna tafiya a haka kafin salman yace kinga gari? Salma ta daure fuska tace hm yace ke kuma wannan cin maganin fa?ta kara hade rai yace jikin ne? Yafada tare dayin gefen titi, salma batai magana ba,parking yai tarr dasa hannunsa a goshinta, ya kalleta tare da hararar wasa yace ai bama zazzabin yanzu, ta kalleshi batare data ce komai ba, farha jitai kamar ta shake salma ganin sai wani hade rai take shikuma yana wani lallabata bayan ita akama abu amma bai kula ba😠. Yafara tuki takalleshi tace tunani nake yace name? Tace mun fito bamu tambaya ba kar yazama wani abun, salman yai tsaki yace ki daina damun kanki da wad'an nan abubuwan,ace mata da miji basu isa su fita ba sai sun tambaya? Har kasan ran salma taji dadin mata da mijin dayace amma a fili tace amma ai dokace☹ yace I don't care about that, yafad'a tare da kallan titi, farha kamar tai kuka in ta kallesu. Sun isa gida suka fito dukansu, sai dai suna sauka ishaq ya karaso gun, cikin bacin rai ya kalli salman yace kaifa bakada mutunci, salman yai murmushi yace badai sai yanzu kasani ba😉 ishaq yace mu bar nan muje bangarenka dan yau bazan kyaleka ba, salman yai wani murmushi yace ahhh I hope bazaka canza kudirinka ba😏. Sun isa bangaren su Farha ta kalli ishaq tace ya.....wata harara ya maka mata yace dalla fita daga nan, a zuciye ta juya tana kunkuni, ishaq ya kalli salman yace kaji asara wlh dazakasa baiwar Allah karya akan wata lalata dakake, salman yace ahh badai baiwar Allah daka fada tana nufin matata ba?salma da sauri tai hanyar kitchen, ishaq yace ita mana to wlh bazan.....salman ya katseshi yace matata? Ba matar ishaq ba ko? Nad'auka haa zancen yake? Ishaq yai shiru yana huci, salman yai murmushi yace yaya ina tausayin ka dasan shiga zancen ma'aurata😞 yazanyi in kaje kai baban laifi🙊? Ishaq yagama kuluwa jiyake kamar ya mutu, salma dake kitchen tai murmushi tace amma salman😀. A hankali salma ta fito dauke da ruwa da lemo, sannan ta kalli ishaq tace kazauna😊 wani sanyi ya kamashi nan yazauna yana kallanta kamar ya had'iyeta, salman ya kalli ishaq ganin yanda yake kallanta yasa yace yaya kasan me? Yace me😡? Yace akwai wani kare da ya takuramin, bayan nasai wani abu mai kyau sai na kua karan yasamin ido, burinshi yaga ya d'au abin nan, ishaq yace a ina karen yake? Salman yai murmushi yace kanaji? Yace eh, salman yace kasan menama karen? yace a'a, yace zuwa nai nasashi a kejin daba mai budeshi har karshen rayuwa🙂 ishaq ya tabe baki yace ka kyauta, nifa karnuka basumin ba, salma dake tsaye tasan lalai magana salman yake dankarawa ishaq amma mamakimta shine badai ishaq ne karan ba ko? Salman ya saki murmushi ganin ishaq baisan mema yace ba, yace yaya inkaje ka tambayi fulani labarin karen ita tasani ai, ishaq yace to tare da kallan salma. Yana fita salman yai tsaki tare dayin d'aki dan yafarajin kansa na sarawa, dasauri ya had'iyi magani ya kwanta, salma ta shigo tare da zama kusa dashi tace labarin karen nan? Ya kalleta, tace badai dashi kake bako? Yai murmushi yace ashe kina gane maganar boye? Ta tabe baki tace me ka d'auken? Yace ummm bari muga....tasa hannu ta mintsineshi a ciki, hannun ya kama tare da jawota jikinsa yace umm ina tashi ramawa me kike tunani?ahankali tad'ago tace to ai kaid'in ne☹yace ni me? Tace wato bama kasan me ka d'aukeni ba🤔 habarta ya rike da hannu d'aya yafara juya fuskarta, yana cewa bari inga, ture hannun tai tare da mikewa, dasauri ya jawota, ta fad'a kanshi sunyi shiru na wani lokaci banda zuciyoyin biyu da suke bugawa, cikin wata irin murya salman yace haushi kikaji? A hankali itama tace um, wani sansanyan murmushi sukama juna yace bada wani abun na fad'aba, tace nasani yace then? Tace bantabaji kaba wani hakuri ba tunda nake, yace so?tace meyasa? Yace kawai, tace ummm nagane, yace bansan kid'inga zuwa inda kikasan ishaq na zuwa, in gurin fulanine kibari muje tare, tace y?yace kawai, ta tabe baki sannan tace to amma menene abu mekyau da kake magana d'azu? Yace u don't have to know tace shikenan😞naji. Zaune suke akan dinning suna lunch, salma ta kalli salman tace bayan tafarnuwa meye bakaso?yace bangane ba? Aranta Tace banason wata tazo ta dinga nunamin tafini sanin mijina, tabude baki zatai magana taga salman na dariya, tace meye kuma😞 yace kedai zuba abinci, wato da farha kike ko? Tace mene? Yace wace zata nunamiki ta fiki sanina😉 dasauri ta rufe fuska dama yaji? Ahh kunya ya kamata,murmushi yai tare da matsowa kujerar kusa da ita, ahankali ya zare hannunta tai kasa dakai yace uhmm bari in tashi nama daina jin yunwar, dasauri ta rikeshi tace a'a muci dan Allah, yai murmushi tare da kallanta itama shita kalla, yamata alama da kai ta zubamai taI murmushi tare da jawo plate......... Ummmmm nikam nace tunda abin ba tayi bari nai nan🏃🏼🏃🏼 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣5⃣ Ishaq zaune a kusa da fulani ya bata labarin kare, ranta ya baci ta mike a fusace tace kai amma kazama babban shashasha kana zaune salman ya gane kanama salma wani kallo, ishaq yace to sai me? Tsoranshi nake? Tace to kasan waye karen? Ishaq yace bayace kinsan karen ba? Haushi ya kamata a fusace tace to kaine karen dakai yake banza, tafad'a tare dayin d'aki, ishaq ya mike yace ni? Nine kare? 😖😡 amma salman yagama cimin mutunci kuma wlh sai na hukuntashi sai yasan nidin kare mai cizo ne😡. Salman kwance a d'akin najib yayi rigingine tare da dora hannunsa a a goshi, najib ya kalleshi tare da girgiza kai yace prince dagaske bazamu fitan ba? Salman yai shiru, najib yace prince wai menene? Tun d'azu kazo kawai ka kwanta, salman ya mike da sauri yazauna akan gado yace najib, zo ka tab'ani kaji ko dai ina zazzabine? Najib ya matso tare da sa hannu a wuyansa, yace lafiyarka kalau🤔salman yace to meke nan? Najib yace wai me? Salman yace kai inaji gun likita na zani ina bukatar amsa, najib yace jikin ne? Salman yai tsaki yace haka kawai tunda nafito nake tunanin salma sannan daga na rufe ido sai indinga hangota, gashi in muna tare in tai wani abun sai inga kamar ita kad'ai nake gani a duniya, abinda yafi damuna in ta matso kusa dani ko na matsa sai injo zuciyata na bugawa, najib baka tunanin yakamata inga likita? Najib ya kwashe da dariya harda rike ciki, salman ya hade rai tare da mikewa yace wani sabon iskanci ne wannan kuma? Najib ya tsagaita yace salma dana d'auka kana masifar san farha me kenan? Salman yace insanta mana kamanta tare muka taso? Najib yace kundai shaku amma ba soyaya ba, salman yace bangane ba? najib yace prince yanzu kafara soyayya bada ba ai😂salman yace bansan iskanci meye hakan? Najib yace ayya prince salma ta gama da zuciyarka indai har ka kai wannan stage din😀gaskiya ina tayata murna da alama ya kamata in kirata muyi party😬 yafad'a yana d'aukan wayarsa, salman daya tsaya kamar sanda yana nanata kalaman najin, ganin najib yad'au waya yasa ya fizge wayar yace wani iskanci kake hakan? Najib yace abin murnane ai, salman yace ba wani soyaya so kake inka fad'amata tarainamin hankali😠najib yace kaifa matsalata dakai kenan, salman yace tashi mu fita, najib ya mike tare dacewa abokina ina tayaka murna😉, salman ya makamai harara yace kamanta, wannam d'in abun murnane kaifa bakada aikinyi😏. Salma na zaune a falo rike da littafinta,ganin mutum tai agabanta tasauke littafin tare da kallan wacce ke gurin, farha ce sanye da riga da wando, salma ta mata wani kallo tace na sallama? Farha tace ina yayana? salma tai wani murmushi tace menene? Farha tace meya dameki? Salma ta mike tare da d'aukan littafinta tace inkin fita ki rufe kofar ni nayi nan, farha tace kina nufin anan zaki barni😠? Salma tace naga ba guna kika zo ba kuma Wanda kike nema bayannan kinga sai kijira a falo inkin gaji sai ki tafi ko? Farha tafara muzurai salma takalleta tare da tura kofar d'akin. Tana shiga ta zauna akan gado ranta duk a bace tace what? Yayana😏? Tanaji farha ta fita tai tsaki tace yarinyar nan tama gama rainamin hankali. Falo ta fito dan ta bar wayarta acan, sai dai me? Muryar farha taji a waje da mamaki ta leka, salman taganj da farha akan kujerar gun suna hira, jitai kamar zata fashe dan kishi dakyar ta saisaita kanta ta fito wajen,salman tunda yaji motsi ya juya yaga salma ya zuba mata ido, yakasa d'aukewa, farha ta kalleshi tasa hannu ta taba hannunsa ya juyo tace yaya ina baka labarin skul, yace oh inaji, yafad'a tare da kallan gun da salma take, salma takaraso gun tace ashe kana nan? Salman yace eh yanzu na dawo, wani abun ne? Haushi yakama salma wai wani abun ne? Tahade rai tace ba wani abun🙄 tafad'a tare da juya,baisan sanda ya kama hannunta ba tad'an yi murmushin farin ciki sannan ta juyo, tace menene☹? salman daya rasa mai zaice yace umm dama ce miki zan kid'aukan earphone d'ina, salma ta kalleshi sannan ta kalli farha datasaki murmushi ganin kallan da salma tamai yasan taji haushin maganar, fizge hannunta tai wtare da juyawa, salman ya kalleta sannan ya kalli farha yace nashiga ciki tace yayana ba.....kasa karasawa tai ganin yayi gaba, haushi ya isheta ta mike tai d'aki a fusace. Salman na shiga d'aki yaga salma azaune akasa tad'aura kanta a gado, jikinsa yai sanyi, yakarasa gunta shima ya zauna a gefenta yasa kansa a jikin gadon yana facing d'inta, kallansa tai idanunta taf kwalla,yace haushi kikaji? Tace haushin me? Yace shikenan amma miye na tahowa? Tace mezan muku agun? Yai shiru tace kagani ko? Nasani ai, yace me kika sani? Tasa hannu tashare kwallar data zubo mata tace shikenan, salman yasa hannunshi a kuncinta tare a shafa kanta yace bakisan komai ba, dan haka kiyi shiru, ta kalleshi sai dai yanda yake kallanta yasa takasa magana,shima kallanta yakeyi ahankali ya matso yakai bakinshi kan goshinta yai kissing, salma ta lumshe ido jitake zuciyarta kamar zata fashe, jawota yai ya rungumeta tsam ajikinsa tare da sakin wani nannauyan ajiyan zuciya, salma tai luf akirjin salman wata kwallar dadice ta zubo mata....... Nikaina jinake kamar inyi kwallar amma ni ta bakin ciki dan can na hango farha a zuciye tayi d'aki tare da rufo kofa dakarfi da alama kuka zatai🤕😥 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣6⃣ Fulani zaune a kilisarta bakar maganar da salman ya fad'a wa d'anta ta dameta dayawa wata baiwa tasa ta kira mata ishaq ganin yau sam bai shigoba da alama shima haushin abinda fulani ta fad'a yake. Salma ta shirya tsaf, dan salman ya fita makaranta kuma tafad'amai zataje gaida fulani, sun fito itada hanne, azahirin gaskiya gani take kamar bai kamata ace sai lokaci_lokaci take gaida fulani ba, ganin matan gidan kusan kullum sai sun gaidata, tana tsoron kar hakan yaja ma salman wani abun. Sun isa bangaren, wata baiwa tace kishiga tana kilisarta,tace duk bayin su fita amma ke ai ba matsala, salma tace tom tare dayin hanyar. Fulani zaune itada ishaq takalleshi tace wai haushi kaji? Yace umma ni narasa me kikeso inyi ki yabeni? Tace ina yabonka ishaq kawai banaso ne kadinga zama na karshe in aka had'aka da salman,ishaq yace nifa umma na tsani ganin yaron nan dan yana takuramin, daidai nan salma tazo shiga sai dai tasa hannu zatai knocking kofar taji fulani tace kodai musa amaidashi kasar waje? Ishaq yace ko? Tace eh mana ni kaina na tsani ganin salman gashi yai tamin kwarjini, inaji dai kawai musan yanda zamuyi yakoma can, dama acan yataso, salma da jikinta yashiga bari sai jitai ance in_law me kike anan? Salma ta juyo ad'an tsorace ta kalli farha, dakyar ta saisaita kanta ta kalli farha tace yanzu nazo tafad'a tare da kwankwasa kofar, fulani ta kalli kofar tace shigo? Salma ta d'aure murd'a kofar, farha ta kalleta tai tsaki tace da alama yau ranar ba sa'a tunda nafara karo da waccen. Salma jiki a sanyaye ta shiga tazauna tare da gaida fulani,ta amsa itama a sanyaye dan tana tsoron ko taji, ishaq kam ya zuba mata ido kawai yana kallo,fulani ta kalli salma tace ina d'an nawa? Salma tad'aure tasaki murmushi tace yana makaranta, fulani tace salma ki kulamin da d'ana kinji? Kinga maraya ne😊 salma aranta tace lalai akwai 2face dayawa a duniya amma afili tace insha Allahu, ishaq ya kalleta yace ni naza'amin magana ba🤔 tad'an dago ganin kallan dayake mata yasa tamaida idanta kasa tace ban kula kana nan ba tuba nake, sai a lokacin hankalin fulani ya kwanta, indai tajisu to aikuwa tasan ishaq nanan, ishaq yace au hakane? Wato jikinki bai......dasauri fulani ta katse maganar da cewa salma kingadai sarki natsananin san salman dan Allah ki taimakamai karya dinga abinda ransa zai b'aci tace to, tare da kallan ishaq, tana mamakin me yakesan cewa d'azu. Mikewa tai taredayi musu sallama, tana fitowa ta kalli kofar d'akin tace a waje kamar.......ta juya tai waje duk jikinta a sanyaye, tana shiga d'aki ta zauna abakin gado, lalai yau ta yarda in mutum ya rasa uwa to fa yayi babban rashi, idanta ya ciko da kwalla tausayin salman ne ke ratsata, tace ko ya sani? Can tace da alama ganin yanda Yake musu. Bayan isha'I salman ya dawo tana zaune tana game a waya, tanajin motsin kofa ta mike da sauri tad'au turare ta kara fesawa ta gyara zama, salman ya shigo da sallama salma ta amsa tare da murza iso, yashigo yace wai bacci? Tad'an kalli agogo tace kadad'e harna fara bacci☹ yakaraso yace uhmm anya kuwa baccin ake? Tace eh mana🙄, yai murmushi tare da sa hancinsa a wuyanta yace amma kamar yanzu akasa turaren na? Sannan ya sa hannunshi a bayanta yace kamar kuma wayarnan amfani ake da ita? Ta mike da sauri tare da ware ido ta turo baki tace ahhh wai kai ba'a fooling d'inka☹? Yajawota jikinsa yace inafa bayan baki iya pretending d'in ba? Kawai dai kice so kike ind'inga dawowa da wuri ko ba haka akeso acemin ba? Yafad'a yana kallanta, dasauri tashige jikinshi jin wani shock yai daga kansa har zuwa 'yan yatsun kafarsa, jiyai salma tace ni kad'ai d'in ne ba dadi☹ yai gyaran murya sanna yace insamomiki 'yan tayin zama? Tace suwa? Yace inada kanne mata ai ga farh.....tureshi tai tare da zama akan gado, ya kalleta ba shakka wannan kishi salma takeyi, kenan itama tana sanshi? Zama yai kusa da ita yace in mutum baisan abu yafad'a kawai bawai yad'inga had'e rai ba🤔 salma tad'an matsa tare da harde hannayenta tace eh banaso, happy? Yai murmushi batai auni ba taga kan salman a cinyarta, ta runtse ido inama salman na santa? Da gani zatai tafi kowa farin ciki a duniya, a hankali ta bude idanta, salman na kwance idanunsa ta kalla, shima kallanta yake, dasauri tad'auke idanta jin gabanta na fad'uwa, salman ya kalleta tare dasa hannu yadawo da fuskarya kansa yace yau nagaji shiyasa zan d'an kwanta anan, an bani pass? Ta kalleshi tai murmushi tace kunsha yawo kenan da najib ya kankance ido yace ummm da alama matar nan tasa ana bina🤔 salma tai dariya fararrn hakoranta suka fito, tace sai an dubamin? Bayan nasan me kuke a skul d'in? Yace ahh ashe fa hakane. Tace yaushe zaka fara karatu? Ya kalleta da mamaki yace da wasa nake? Tace nasani da saninka kake mika farar takarda, yace what? Mezai sani hakan inba rashin sanin amsa ba? Tace uhmm anya kuwa? No matter how much I think zuciyata ta kasa yarda da hakan,u are a smart person babu yanda za'ai kace ba ka fahimtar komai, salman ya juya kansa zuws cikinta yace mubar maganar, salma tasa hannu akansa tace why? Yace later, tai ajiyar zuciya tace to. Salman yayi shiru a jikin salma, zuciyarsa na kwadaitamai kusantarta, sai dai yayi alkawarin a rayuwarsa bazai tab'a kusantar macen dabata sanshi ba, yazama dole yatantance meke ran salma. Salma kam ta d'auka bacci yake tai shiru tana kallansa, maganar su fulani ce take dawo mata, shafa kan salman tai tausayinsa na ratsata. Salman ganin bazai iya bacci a haka ba yasa yai kamar yana bacci, yad'an mirgina, salma ta matso daf da fuskarsa tana kallansa a fili tace *Sweet one time, cold one time, rude one time, mean one time and romantic one time* Tai ajiyar zuciya tare da rufe ido, can ta mike tai shimfid'a ta kwanta. Salman ya bud'e ido ahankali ya maimaita kalaman data fad'a yai murmushi tare da kwanciya wani farinciki yakamashi da alama salma nasansa. By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣7⃣ Yau juma'a salman na kwance har wajen 10, salma tad'an tabashi ya motsa tare da bud'e ido cikin kalar bacci, yace ya? Tace skul fa? Yace bazani ba, yafad'a tare da juyawa tai ajiyar zuciya tare da mikewa,jawota yai takoma ta zauna tare da kallanshi, ya d'ago a hankali yace kishirya zamuyi tafiya bayan an sauko, takalleshi tace zuwa ina? Ya saketa tare da juya baya ta kalleshi aranta tace ko ina zamu? Mikewa tai ta fita falo, tana zaune tana kallo, salman ya fito, ta kalleshi har yayi wanka tace ka tashi? Yace umm tare da zama, farha ce ta shigo salma ta harareta aranta tace yau kuma? Salman ya kalli farha yace kin iso? Salma ta kalli farha kin iso? Farha ta kalleshi tace na iso yayana😊, takalli salma tace hi in law salma tace sannu, farha ta kalli salman tace yaya rakani zakai fa☹? Salman yace ina? Tace kai yaya kafa sani, salman yace yanzu? Yafad'a tare da kallan salma dataci magani ta kafeshi da ido, salman yad'auke kai yace muje, farha ta kalli salma ta saki wani murmurshi, tai gaba. Salma ta makama salman harara tai d'aki, d'aki da sauri ya kalleta yai murmushi tare dayin waje. Salma tai d'aki tare da kwanciya tad'au pillow ta d'aura akanta. Salman na fita suka karasa gun mota da farha, yad'au waya yakira wani, suna zuwa bakin mota farha taga driver takalli salman, salman yakalli driver yace habu kiranka nai zaka kai farha unguwa, dasauri farha takalleshi tace yayana😳? Salman yace inzaki fita kid'inga neman habu zai dinga kaiki, yana kainan yai gaba. Farha tabi bayanshi da kallo tana kiranshi ko kulata baiyi ba, habu yace muje hajiya? Farha cikin masifa tace bazani ba😡 tai cikin gida da sauri tana shiga tad'auko akwati ta shiga zuba kaya tana hawaye. Salman na shiga yai d'aki, a kwance yaga salman ta rufe kanta murmushi yai tare da zama kusa da ita, ya zare pillow din, ta d'ago a hankali ta kalli salman, cike da mamaki tace har ka dawo? Ya kalleta yace ina zani da? Tace ba fita zakuyi ba? Yace ahh yazanyi? Matata sai kishi? Tace bafa kishi bane☹ yace ummm to menene? Tace kawai dai.....yace hmm kinshirya mana kayan? Tace bakace sai an sako ba? Yace nafasa mutafi yanzu. Tace wai ka fad'a? Yace na sanarwa mahaifina ko akwai wanda yazama dole infad'amai bayan nan? Takalleshi sannan tai murmushi tace nibance ba, ahankali ta mike ta jawo karamar jaka, tafara zuba kaya tana gamawa yace muje, tace wai saurin nameye?yace so nake insami sallah acan, tace to. Sunfito tasanar da hanne, nan sukai waje suka shiga mota, suka fara tafiya, sunyi tafiya mai nisa harta daina ganin gari, wudil taga ansa ta kalleshi tace wudil? Yai murmushi tare da gangararawa, sai da suka je karshen garin wani d'an karamin had'adden flat suka isa, ahankali mai gadi ya bud'e gate d'in salman ya karasa yai parking, salma ta shiga kallan gida sosai gidan ya burgeta gashi ba girma gareshi ba, sai kyau da tsari, mai gadin ya iso da sauri ya kalli salman yace yarima barka da isowa, shekaru dayawa? Salman yace ashe zaka gane? Yace ina na isa namanta dakai? Bayan nasan bamai zuwa sai kai? Salman yai murmushi ya fito,mai gadin yai saurin budewa salma kofa tare da gaisheta yace kai uban gidana masha Allah, salman ya kalli baba tsoho yace kai baba? Nan yad'au jakarsu yai ciki, salman ya kalli salma yace kishiga bari nai sallah tace to. Salma tashiga ciki tare da kallan gidan,da alama ana kula da gidan, a hankali ta karasa cikin falon mai cike da tsari, ta karasa gun wani hoto dake kusa da tv, ta d'aga,tare da gogewa da hannunta salman ne da mahaifiyarsa, tagane mahaifiyarsa ta kurama salman ido, tace suna kama,ajiye pic din tai ta d'auko tsintsiya tafara kad'e falon tagama share falon tai d'aki, sai data gama ta shiga wanka, tana wanka taji motsi, takalli kanta daga ita sai towel, tanaji salman ya murd'a kofa da alama ya fita, tai saurin fitowa, tana fitowa shikuma ya tuna yabar wayarsa a d'akin ya murda kofar, salma ta juyo a rude, salman ya kalleta daga sama har kasa, d'an karamin towel d'in dake jikinta, duk cinyoyinta a waje, ya kura mata ido,itama kallansa take da sauri ta juya baya, salman ahankali ya tako inda take, yasa hannunsa a kugunta, idanta ta runtse, salman ya kwanto ta bayanta tare da sakin ajiyar zuciya, salma tai shiru tsoro duk ya kamata, ahankali ya juyo da ita,idanunta a runtse suke kam.....kawai jin bakinsa tai anata, wani salo salman kewa salma, jitai kafarta bazata d'auketa ba ahankali yakaita gado, ganinai ya zame towel din jikinta, umm nikam ganin yanda salman ya rud'e yashiga aikama salma wasu sakonni dasu kad'ai sukasan ma'anarsa sam sun fita daga hayyacinsu as wannan shine na farko ga kowannensu, nikam ganin hankalinsu yabar jikinsu ahankali naga salman ya d'ago ya hararen yamin alama da kofa, dasauri nafita tare da ja musu kofa........masu karatu kuyi hakuri bazan samu damar d'auko rahoto ba dan salman ya koroni😭😭 Salma taji jiki salman sai daya tausaya mata, waya ya d'auka yai searching nan ya tashi ya cika baho da ruwan zafi ya d'auketa kamar yar tsana yasa ta aciki, tad'anyi kara sai dai daga baya taji dadin ruwan, salman dakanshi yataimaka mata tai wanka, sannan ya d'aukota ya maida ita d'aki,sannan shima yai. Kusa da ita yazo tana kwance, zama yai, ya nuna mata cinyarsa yace kwanta my wife😊 salma ta kalleshi tare da rufe ido, yace ki kwanta, a hankali ta gyara ta kwanta, ya shafa kanta tare da cewa nagode *salmah* a hankali ta kalleshi, sannan tai murmushi yace salma kinsan ina ne nan?,ta girgiza kai yace inda nafara zama da mahaifiyata ko ince inda aka haifeni, salma ta kalleshi jikinta yai sanyi, salman yai murmushi yace munzama d'aya yanzu dan haka I can't keep any secret 4rm u kema I hope u won't ta kalleshi wani dadi na ratsata yace salmah? Ta d'ago ido ta kalleshi, yace can I say it? A hankali tace me? Bakinsa yakai goshinta ya sumbata yace *I LOVE YOU* Salma ta zaro ido zuciyarta ta shiga bugawa ahankali kuma hawayen dadi yashiga zubo mata.. Nace uhm su salman da salma😏 By Ayusher Mohd📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣8⃣ Salman ya jingina pillow shima ya kwanta, sunyi shiru na d'an wani lokaci, salma dai banda murmushi ba abinda takeyi, can taji salman yace kinsan me? Tace a'a. Salman yace mahaifina da sarkin daya sauka wa da kani ne, mahaifina Alhaji Sadiq yataso cikin gidan sarauta sai dai tunda bashi zai zama sarki ba yasa zaman yafara gundurarshi, suna tsananin shiri da yayansa sai dai mutane kullum cikin gaima sarki gulmar Abba suke hakan yasa yanemi alfarma yadawo nan wudil garin mahaifiyarsa da zama, a lokacin Abba ya auri fulani dan alokacin 'ya'yanta biyu mata, itadai bataji dadin barin gidan ba, gashi tana fama da laulayi. Dakyar ta lalabashi yabarta a kano akan inta haihu sai ta dawo wudil, bayan tahowar Abba anan garin ya had'u da mahaifiyata suka fara soyayya mai karfi harta kaisu ga aure. Fulani taji haushin wannan aure sosai gashi sanda ake bikin ita kuma ta haihu, taji d'adin haihuwar namiji datai, d'an data haifa akasamai ishaq, nan gidan aka kawo mahaifiyata, tana tsananin san Abba, fulani kishi yasa tace sai dai tacigaba da zama a kano Abba yad'ingazuwa can, wannan dalilin yasa basu zauna tare ba. Umma shekararta 1 da aure ta samu ciki, farin ciki agun Abba ba'a magana, mun shaku da Abba sosai harnakai shekara 9 sai dai umma batasake haihuwa ba sai bari, alokacin ne sarki ya aikoma mahaifina da takarda akan yanasan ganinshi. Abba yashirya yaje sai dai yana zuwa ya taradda sarki ba lafiya sosai, cikin hawaye ya karasa yace meyasameka yaya? Ba wanda yasanar dani? Yace nasan bamai fad'ama shiyasa natura kazo, Abba yace meke damunka haka? Sarkin yace Abubakar inaji ajikina bazan wuce yau ba, cikin rudewa Abba yatambayeshi dalili? Sarkin ya mikamai takarda tare da kiran manyan mutane masu matsayin a masarautar yasanar dasu Abba yabawa mukaminsa da milki, ba Abba ba kowa yasha mamaki ganin yanada 'ya'ya maza, sarki yace asanda mahaifinmu yabani mulkinnan saidaya sa nad'au alkawarin zan baka kafin yabani, Abba jikinsa yai sanyi yaso yaki amma ganin yayansa na rokonsa yasa ya amsa. Nida umma muna gida yau tunda umma ta tashi take kwance ba lafiya, in nace a kira Abba sai taki yarda, bayan magriba da Abba yakira sai ta d'aga ta nunamai lafiyarta kalau, nan yasanar da ita halin da ake ciki, ta tayashi murna kafin suyi sallama. Jikin umma ya tsananta ga Abba kwanansa uku kenan dan washegari daya shirya tafiya sarki yace ga garinku nan, hakan yasa aka rikeshi yazauna. Ganin umma bata ko iya mikewa yasa na d'au wayarta na fito falo na kira Abba,sai dai harta katse bai d'aga ba, nakirashi yafi sau nawa bai d'agaba, na ajiye wayar naje gun mai gadi na fad'amai, nan danan yakira driver muka wuce asibiti. Abba kam alokacin suna zaman makoki, muna isa asibiti akai emergency da umma, duk ta rame, anan muka kwana,duk yanda nake kiran Abba bai d'agaba, waahe gari uku, a ranar da yamma aka shirya nad'a mahaifina, alokacin jikin umma yai tsanani, kuka nake sosai. Wajen karfe d'aya mahaifina ya kira da sauri na d'aga yanacikin mutane, hakan yasa yace ku shirya za'azo a d'aukeku yanzu,dan da yamma za'ai nad'I,nace nad'I?cike da mamaki yace salman? Kaine? Nace Abba umma fa bata da lafiya inata kiranka, yace kuna ina? Nace asibiti yace ok bari azo yanzu a taho daku nace to. Ba'afi hour daya da rabi ba aka turo mota babba ta d'aukemu, umma kam batasan meke faruwa ba dan bata hayacinta nikuma sai kuka nake, muna isa gidan dan Abba ya ganta kafin mu wuce asibiti, ina zaune rike da hannunta, tace salman? Ahankali na kalleta nace umma kin warke? Tace salman ka kula da mahaifinka, nace naam? Sai dai kafin takara magana naga tana wani abu😰. salman na zuwa nan yai shiru, salma kam banda hawaye ba abinda take. Can salman yace na fita da sauri akan in kira wani, ganin Abba na tahowa yasa nai gunsa da gudu na fad'amai, dasauri ya karaso sai dai muna zuwa mukaga umma tace ga garinku nan. Hawaye ya zubowa salman yace kinsan me? Salma cikin tsananin tausayi da hawaye ta girgiza kai yace su fulani, da ragowar manyan mutane a gabana sukacema Abba wai abirne maganar mutuwar nan tunda sarakuna da manyan mutane suna gidan, a je kawai a mata wanka in ba haka ba mutane zasuce mahaifina da gawa ya fara a mulkinsa, salman ya rike kansa, salma ta mike da kyar ta matso inda salman ya kwanta hawaye na gudu a idonta, salman ya kalleta yace kinsan kuma me? Ta girgiza kai yace Abban ma ya yarda da maganarsu, shine daga baya ganin ina zaune sam bana magana yasa aka kaini paris gidansu farha. Yana kainan yaji kirjinsa ya fara amsawa, jawoshi jikinta tai ta rungume tana kuka tama rasa me zatace, wace irin rayuwa salman d'inta yai? Tun yana karami an gama b'ata rayuwarshi da bakin ciki? Ganin yafara numfashi sama_sama yasa ta bude jaka tad'aukomai magani ta mike dakyar ta d'auko ruwa yana sha ta koma kusa dashi itama ta kwanta tarr da rungume salman, addu'a kawai takeyi, ahankali salman yaji numfashinsa ya daidaita, baccine ya fara d'aukarsa, salma ta kalleshi tace *I LUV U TOO MY PRINCE* kuma insha Allah I will take care of u😭. Hmm soyayya oh ni indo nima tausayin salman ne yakamani sai kwalla naji a idona😭 By AYUSHER MOHD📚 ☄☄☄☄☄☄☄ 💥 *NI DA PRINCE*💥 ☄☄☄☄☄☄☄ *NA AYUSHER MOHD* NO.3⃣9⃣ Farha ce tagama had'a kaya cikin hawaye ta jawo akwatinta, fulani dake zaune tace farha ke kuma meye hakan? Farha takarasa gunta tasa kuka, fulani tace ke da salman ne? Farha ta d'ago da sauri fulani ta kalleta tace nasan komai farha amma fad'a kuka?,farha cikin kuka tace sam bai damu dani ba matarsa kawai ya sani nikuma bazan juri ganinsu tare ba, fulani tad'anyi wani dariya tace haba farha mata da mijinta? Ai dole ki gansu tare kuwa, farha ta turo baki, fulani tai ajiyar zuciya aranta tace da alama nasamu wacce zata sa salman a koreshi, a fili tace kamar bakida wayau? Keda kika taso a kasar waje har matar data taso anan zata fiki sanin yanda ake jan ra'ayin maza? Farha tace duk nayi, kinsan halinshi ai😪fulani tace nasani to ba sai kibi ta hanyar dazaki shiga tsakaninsu ba? Inta fara zarginsa ko ya fara zarginta aikinga dole su rage damuwa a juna, farha tace wow nagane, fulani tace ko kefa?.... Nikam dariya ma sukaban da alama basu san basa gidan ba😂😂 Sunyi bacci sosai dan sai 4:30 suka tashi, salma ce tafara mikewa sai dai yanzu tafijin karfin jikinta, a hankali ta janye jikinta daga na salman ta mike da kyar tai hanyar toilet tai alwala, ta tada sallah salman ya mike, ya kura mata ido, a ranshi yace Allah nagode maka dakasa salma itace matata😊, Sannan ya mike yai alwala, salma ta dade tana rokon Allah yau kam duk addu'arta ta salman ce, bayan ta idar ta mike tai kitchen. Kitchen din ta shiga dubawa, taga ba kayan abinci sai wasu ledoji akan dinning nan takarasa ta bude, take away ne, da alama salman dazu dasu ya shigo ta bude d'ayar ledar, kaza ce da dankali, sai dayar kuma lemo. A hankali tadau ledojin takarasa kitchen ta dauko plates tafara wankewa, salman ya karaso inda take yasa hannu a kugunta tare da turo kansa ta wuyanta, yace beauty me kike? A ranta tace beauty? Ta juyo ta kalleshi da mamaki kafin tai magana ya manna mata kiss a kumatu, yace ba dream bane😉 murmushi tasaki sannan ta maida kanta gun wanke_wanken, tace andaina stubborn d'in? Kara kankameta yai yace sosai ma😊 ta turo baki ta juyo ta kalleshi tace ba wani bayan a wayarka haka aka sa? Yace oh ashe fa hakane, shan yace wait......kefa? Dasauri ta maida kanta tace umm nikam dama d'azu da abinci kataho? Baka fad'amin ba? Ya kwanta a bayanta yace inafa na tuna🤔? Ta gama wanke wanken ta goge dinning d'in sannan ta jera ta kalleshi tace abinci, yazauna tare da kallanta, itama tazo ta zauna a kujerar kusa dashi, ta zubamai abincin, nan suka fara ci,sai dai insuka had'a ido sai duk suyi murmushi, sun gama suka mike, salman ya kalli yanda take d'ingisa kafa, karasowa yai inda take kawai sai jitai ya d'agata da sauri takalleshi 😳 Ya juya kai tare da cewa tunda nina saki d'ingishi I have to take responsibility, tai murmushi tare da cewa ahh ni kunya nakeji🙈 ya fara tafiya tare da cewa toh yaza'ayi? Gashi nikima banasan mace mai kunya 🤔 dasauri ta bude ido, tace naa daina, dariya yasa tare da zama akan kujerar da ita, yakalleta yace wai daga fitata kikai duk wannan aikin? Tace yayi yawa ne? Ko tayani zakai? Ya kalleta yace ahh sai dai inmiki sannu dan inaji tunda nake ban tab'a rike tsintsiya ba bare shara, salma tace na sani ai basai an kara sanar dani ba☹ ya ja kuncinta kad'an yace umm haka nakeso, tace bafa kayan abinci? Yace toko muje a siyo? Nikaina ina kwad'ayin cin abincinki, tace in kuma ba dadi fa? Yace anya kuwa? Bayan inaji ajikina ta iya? Salma ta mike daga cinyarsa tace yallabai muje? Tafad'a tare da kallansa, salman ya kalleta tare da had'e rai, tace menene kuma? Yace waye yallaban? Tace bafa suna bane☹kawai fad'a nai yanzu, yace au sannan ya mike yai gaba tabi bayanshi da kallo tace oh ni. Sun shiga mota sun zauna salman ya d'au waya tare da yin dialling sai dai salma dake zaune taji wayarta na ringing awajen radio ta ajiye wayar a tare suka kalli wayar da salman sai dai me? *My Prince* yaga ya fito a jikin wayar, kallansa tai tare da saurin d'auke wayarta, yai murmushi tare da kunna motar. Sunyi siyayya sannan suka koma gida, a falo suka zauna salman yakalli salma yace jikin fa? Tace da sauki, salman ya sauko kasa sannan yakalli salma dake kan kujera ya miko mata hannunshi, kallansa tai sannan ta mika mai nata,tare da sauka in da yake, sunzauna daf da juna dan rabin jikinta ma a jikinsa yake, hannu yasa ya kwanto da kanta jikinsa, ta gyara kwanciyar tare da lumshe ido, salman cikin magana mai rad'a yace baza'a fad'amin sunan nawa ba? Ta kara shigewa jikinshi, yai gyaran murya yace ahh nikam bansan mace mai kunya, salma tai shiru, ahankali yaji tace my prince🙈 yai murmushi tace ahh nikam banjiba🤔 tad'ago tace Allah kaji☹kiss ya manna mata abaki yace beauty daga yanzu kid'inga kirana haka, tace naam😳? Yace me? Bakyaso? Dasauri tace a'a bafa haka nake nufi ba, yace to me kike nufi? Tace sai dai in muna mu biyu, yace banyarda ba to in muna cikin mutane sai kice salman? Tace ahh ni? Yace to me zakice? Tace to ai in a cikin mutane ne bana fad'ar suna, yace ohh sai kice kai? Tace 🙊 ni? Ban isa ba, salman ya kwantar da kansa akan kujera yace shikenan. Murmushi tai tare da sako fuskarta inda kansa yake tace zan d'inga fad'a kaifa? Yace wa? Ni? Ke kina tunanin ni zan kasa yin abinda naso? Tace ina fa? Rungumeta yai, salma tai ajiyar zuciya tace prince? Yace umm tace ban iya san abu ba, ina tsoron kar sanka yamin yawa in rasa ya zanyi? Kara kankameta yai dadi yakeji har ransa yace nabada dama kisoni harsai zuciyarki takai yanda bazaki iya rabuwa dani ba, tace I am afraid😞 ahankali ya d'agota yace of? Tace you, yace me? Tace eh, kara rungumeta yai baice komai ba, hawayen dasuka taru a idanta ne suka zubo. By _```AYUSHER MOHD```_📚