06/08/2019 à 00:06 - Les messages envoyés dans cette discussion et les appels sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations. 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _My Happiness *Amnoor*, barka da fara sabon novel mai sunan *matar farko* (dandab'asa), wannan novel kam namu ne domin damu ake, matan farko ba ba kamar su o'o ba, ina nufin momyn D....tasan sauran, su kam d'ogalawa ne.😁 Allah yasa ki gama lafiya kamar yanda kika fara lafiya._ 💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘 _My BK, nasan babu godiya tsakaninmu, to amma ya zama dole yaba kyauta, ina godiya BK ta Allah ya bar zumunci._ 💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘 🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾 _My Heenat, na rasa me zance ma, sai dai kawai nace Allah ya barmu tare, qauna ta gaskiya kam kina nunawa Sameera ita._🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾 _💘Mamien mu *(Maman Labyb)*, gaskiya ke uwace ta gari wacce ko wace d'iya ko d'a zaiyi alfaharin samunki a matsayin uwa, yanzu haka har na d'an fara kishi da BK ina ji inama nice 'yarki , to amma ba damuwa zan zauna a matsayin 'kawa kuma rabin ran d'iyarki._💘 _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣ Da alama ranta a b'ace yake ga k'aguwa a zahirinta ya bayyana, sake kallon agogo tayi na karo ba adadi sannan ta kalli k'ofar douche d'in taja dogon tsaki tana magana k'asa k'asa "wannan wulak'anci dame yayi kama, sama da awa d'aya kina wanka, ki bani wani banzan serviette (towel) na rik'e kamar ke wata musaka ce." Sake kallon agogon tayi sai dai kafin ta maido kallonta taji an bud'e k'ofar douche ana fitowa, da sauri ta kalleta amma saboda ganin santaleliyar budurwar ta fito daga ita sai d'an k'aramin silip (pant) d'inta ko soutien ( bras) babu yasa tayi k"asa da kanta, ita kam ko a jikinta takowa tayi ta zo gabanta ta karb'i serviette d'in ta d'aura a k'irji sannan ta karb'i dayan ta d'aura a kanta, gaban coiffeuse taja kujera ta zauna tana kallon madubi ita kuma mai aikin ta matso ta d'auki mai ta fara shafa mata, bayan ta gama ta shafa mata powder da pink d'in jan baki, ta fito mata da wani silp d'in da soutien ta bata ta saka sannan ta fito mata da riga da siket na atamfa, d'inki ne na yan zamani yayi kyau sosai gashi ya zauna a jikinta daram , mai aikince ta zuge mata zip d'in dake bayan siket d'in wanda ya kamata sosai komai nata ya fito masha Allah, d'an kwali ta kashe d'aurinshi sannan ta fito mata da sarka da yan kunnai da gani kasan sunji kud'i, sannan ta fito mata da jaka da takalmin da suka dace ta aje mata gabanta, sakawa tayi sannan ta d'auki turare ta fesheta dashi ita kam tana tsaye kamar gunki, tana kamalawa ko jiranta bata tsaya ba kawai tayi k'ofar fita abinta. Binta tayi da harara tana fad'in "wannan zanso naga gidan aurenki , mijinki ne zai miki wannan hidimar ko kuma mai aiki zai samar maki." Gyara d'akin tayi kamar yanda maishi zata buk'aci ganinshi sannan ta fito ta rufe mata d'akin. Ba tare data kalli kowa dake kan table a manger (dinning) d'in ba taja kujera ta zauna, wata mai aikince dake tsaye kusansu ta matso ta fara zuba mata abincin, ta zuba mata fritte zata bud'a wani kwanon kawai ta d'aga mata hannu tare da kallonta cike da wulak'anci tace, "Ya isa haka, ni ba jaka bace kamarku da zan zauna ina had'iyar abinci haka." Ja baya tayi kanta k'asa bata kalleta ba ita kuma ta fara cin fritte d'in, mahaifiyarta ce tace "mu kike so mu fara gaidaki kenan?" Cike da nuna an takura mata tace "ina kwana." Mamar ce tace "nice kad'ai a wajen?" Kallon saurayin da suke fuskantar juna tayi, amma ganin wani kallo da yake mata tare da murmushi yasa ta zabga masa harara, maida kallonta tayi ga mahaifinta, d'auke kai tayi ta kalli mahaifiyar tata tace "ki tabbatar min jiya bai shigo cikin maye ba, ni kuma saina gaisheshi." A tsawace uwar tace "ke, ashe baki da mutunci, wannan ba mahaifinki bane da zaki fad'a masa haka?" A wulak'ance ta kalli uwar tace "shi kenan mutunci ne yake sashi shigowa cikin gida a buge? kinga nifa karki b'ata min rai da safiyar nan." Duk da k'ok'arin rik'e hawayen da tayi saida suka zubo, cikin muryar kuka tace "ba laifinki bane, kiyi yanda kike so." Tana fad'a ta juya ta nufi d'akinta tana zubar da hawayen takaici, ita kuma ko kulata ba tayi ba bare taji ba dad'i, saima mahaifinta data kalla tace "zaifi maki kyau ki daina saka damuwa a ranki akan wannan da baisan kina yi ba." Tashi tayi ta bar abincin zata fita ,mahaifinta ne kalleta a marairaice yace "kiyi hak'uri mana gimbiyata, nayi alk'awari ba zan sake ba." Kallonshi tayi ta kalli saurayin dake zaune kusanshi tace "ka fad'awa wannan wawan watak'ila shi zai yarda da abinda ka fad'a, amma bani ba *Khairat*." Fita tayi ta nufi wajen motarta, d'aya daga cikin jami'an dake kula da mahaifinta ne ya taho shima a gadarance ya karb'i jakar hannunta da makullin mota ya nufi motarta dasu, dan in baiyi ba to masifa zaisha amma ba k'aramin d"aci ba abin ke mishi, har zata shiga mota taji saurayin nan yace "nine wawan?" A wulak'ance ta juyo ta kalleshi tace "to da wa in ba kai ba? da wani ne wanda ya fika zama wawa a duniyar nan? ai kai kad'ai ne namijin dake zuwa gidan wacce yake ikirarin yana so kuma ya zauna zaman dirshan har da mik'e qafafu." Nunashi tayi da yatsa tace "wallahi harka gama wa'adin daka dibarwa kanka ba zan tab'a kallonka a matsayin mutum ma bare harna fara tunanin soyayya da kai, désolé." Tana fad'a ta shiga motarta ta bar gidan cikin matsanancin gudu, shi kuma taushe b'acin ranshi yayi da har yanzu yana ji a jikinshi zata iya zama tashi, a ranar da kuma hakan ta faru zata gane wanene shi. ******************** Kafin ta fara gudanar da komai saida tasa masinger ya siyo mata fritte mai had'e da soyayyen nik'akk'en nama da jus d'in albasa da moutarde, tasa *Habiba* ta had'a mata kakkauran tea da zuma sannan ta fara wani sabon petis de jeûner d'in, tana fara ci Habiba ta sake shigowa cikin ladabi tace "madame, manager ne ke son ganinki." Kallonta tayi a wahalce tace "uhum, kice ya shigo." Juyawa tayi dan cika umarninta, takai wata lomar bakinta taji shigowarsu, amma jiji da kai yasa ta kasa koda kallonsu da ido, tsaye sukayi a kanta hakan yasa ta musu nuni da hannu akan su zauna, saida suka zauna sannan ta kallesu gaba d'aya ta kuma kalli manager tace "kai kad'ai aka ce kana son ganina, yana ganku ku biyu?" "Eh madame, wannan shine wanda za muyi magana akan ci gaban daya kawo mana." Sake kallon saurayin tayi wanda idonshi ke kan kallon yatsun hannayenta da take cin abinci dasu, jan lallen da suka sha da dogayen akaihu na kanti wanda suma ta lullub'esu da pink couleur d'in vernie, sosai suka birgeshi duk da dai ya tsani mai su d'in, maida kallonta tayi ga plate d'in abincinta taci gaba da ci har saida ta gama sannan ta d'auki bidon (gora) d'in ruwa ta zura hannunta ta tagar dake bayanta ta wanke hannu ta juyo da nufin aje bidon d'in ta d'auki lotus dan goge hannu, karaf idonta suka sauka akan gayen nan daya kasa d'auke idonshi akan kyakyawar hallitarta, da sauri ya d'auke idonshi tare da had'e fuska tamkar hadarin gabas, dan tunda ta fara aiki anan take tak'ama wajen mahaifinta ne ya lura tana da raini shi kuma ba zai d'auka ba, saida ta goge hannun ta tsaya ba yare data zauna ba ta kallesu tace "ina jinku." Hannu manager yasa a jaka ya fito da takalma ya mik'a mata yana fad'in "wannan shine sabon sanfarin da wannan ma'aikacin namu ya fito mana dashi, shine nace kafin muci gaba da bugawa sai mun samu izininki." Karb'a tayi bayan ya gama mata bayanin ta kallesu da kyau, tabbas sanfurin ya birgeta dan kuwa basu da maraba dana maza harda gidan babban yatsa, ga kuma tudunsu shima kamar dai na maza, ajesu tayi qasa ta cire na qafarta tasa wad'annan, su kam kallo suka bi qafar da ita yayin da saurayin ke ma qafar kallon qurilla wacce tasha jan lalle sai dogayen akaihu itama data saka masu kamar dai na hannuwa, ganin yanda suka zauna a qafarta suka mata kyau yasa ta cire ta zauna a kujerarta tace" kuje kawai ku ci gaba da bugawa, ku bar min wannan zanyi publié a Internet nasan zamu samu masu so." Cikin farin ciki bayan sunyi godiya suka tashi zasu fita, muryarta ta tsayar dasu tace "fasahar waye?" Juyowa sukayi manager kuma yace "wannan ne madame." ya fad'a tare da nuna na kusa dashi. Saida ta fito da wayarta a jakarta sannan tace "meye sunanka?" " *Umar Faruk*." ya fad'a a daqile. "Zo nan." ta fad'a kamar ta kira yaronta. Kamar ba zai zo ba saida manager ya sake cewa "madame na kiranka." Takowa yayi tare da k'ara d'aure fuskarshi, saida ya tsaya gaban tebur d'inta yana kallon idonta, jujjuya kujerar ta fara yi tana juyawa da ita ta fara magana "karka bari mu sake had'a ido da kai da sunan had'arin kallo, karka sake bari na maka magana so d'aya har sai an maimaita maka, karka bari na sake jin raina ya b'ace a kanka, sannan karka sake kallon min bayana idan na juya." Tsaye ta mik'e tare da d'aukar lotus d'in data goge hannu ta saka masa shi a aljihun gaban riga tace "ka aje min shi, gobe zan tambayeka." Zaune tayi tace "zaka iya tafiya." Saida ya gama mata kallon raini kafin ya gyara tsyuwarsa yace "idan baki son ana kallonki, to ki zama kamilar mace ta yanda ba zaki rinjayi shed'anun dake cikin zuk'atanmu ba bare har mu kalleki , ni kaina nasan nayi zunubi kuma dole na nemi gafarar ubangijina akan hakan, sannan ki sani ni ba d'anki bane da zaki takani yanda kike so, haka kuma talaucina bai k'ask'antar dani izuwa matakin dake kike k'ok'arin d'orani a kai ba, ina fata kin fahimta." Yana fad'a ya juya bar bureaux d'in, ita kuma ta bishi da kallo tare da tunanin koya masa hankali. Kasancewar bata jima da fara aiki a wajen ba yasa har yanzu akwai rashin sabo, yanzu haka tattara kayanta tayi Habiba ta biyota dasu ta nufi gida saboda bacci kawai take so tayi. ******************** Tunda ta shiga gidan taga guardcord (bodyguard) d'in mahaifinta kuma taji shiru dan haka ta shiga babban falon da zai sadata da nata d'akin, duk da ba bak'on abu bane a wajenta amma dai ta tsorata, tunda taji sautin tasan mahaifinta ne ke dukan mahaifiyarta, da gudu ta nufi d'akinshi ta jefar da jakarta, bata tsaya komai ba ta kutsa kai cikin d'akin ai kuwa bata tsaya ba wajen kaiwa mahaifiyarta d'oki , saman gadon ta fad'a ta rumgumo mahaifiyarta tana k'ok'arin kare jikinta, tunda ya ganta ya jefar da wayar hannunshi ya fara zare ido, yana kakkare jikinshi saboda daga shi sai gajeran wando, kama mamanta tayi suka sauko daga gadon ta d'auki rigarta a k'asa daya ketata da qarfi ta rufe mata jiki, tana rik'e da mahaifiyarta ta kalleshi sai k'yabta ido yake tace "wallahi idan ka sake dakar min uwa, to ka sani justice (kotu) ce zata rabani da kai, dan ba zai yiyuba ka dinga shak'o giyarka kana zuwa kana narkar min uwa ba." Tana fad'a suka fita daga d'akin saida ta kaita har d'akinta ta d'auko mata riga doguwa ta sauya ta d'auko mata maganinta ta bata tasha sannan ta kwantar da ita tana rufeta tana fad'in "banga abinda kike tsinta a gidan nan ba da ba zaki barshi ba, amma da nayi magana sai kice saboda ni kike zaune, ni zan kula da kaina ki koma wajensu Mammie ki zauna." Tana fad'a ta juya itama ta koma nata d'akin ta cire kayan jikinta ta watsa ruwa sannan ta d'auki kayan data fi jin dad'in zama dasu a cikin gida ta saka, wando ne na jeans fari tas sai dai iya cinyoyinta ya tsaya sai kuma riga ta dan sauko har cibiya amma k'ananan hannuwa gareta, kwance tayi ba jimawa bacci ya d'auketa. ******************* Tana tashi bayan la'asar brush tayi kawai ta fito bata damu dayin sallolin dake kanta ba, a falo ta zauna saman lunstumemiyar kujerar dake kai tana kallon tv, mai aiki ce ta kawo mata abinci tana ci mamarta ta fito rik'eda carbi , zaune tayi tace "kinyi sallah?" "Nayi." ta fad'a dan karta sake damunta. _Wannan yarinya ba dai k'arya ba_ Haka suka kasance wunin ranar ba wani dad'i, sai dai takalmin data d'ora a internet sun samu masoya, anan wasu manyan 'yan kasuwa suka ce suna son dayawa akan sari, anan suka tsayar akan gobe zasu zo ma'aikatar tasu sai suyi magana, kasancewar manyan mutane ne yasa tace wa mahaifiyarta ta tasheta k'arfe takwas na safe danta shirya da wuri, cikin dare sosai tana kwance tana chat taji motsi a falo, lek'owa tayi abin mamaki *Mujahhid* ne yake shiga d'akinshi cikin tsananin maye tare da wata budurwa, tsaki taja tace "dubunka ta cika, wallahi saika bar gidan nan tunda bana ubanka bane." Komawa tayi d'aki ta ci gaba da abinda take har bacci ya d'auketa da ecouteur a kunne tana sauraren wak'ok'i iri iri. ********************* *Da safe* zaune take a tsakiyar wani faffad'an gado na alfarma cike da magagin bacci da har yanzu bai saketa tace "nifa wallahi kun takura min, wai dole saina tashi ne?" Sake komawa tayi ta kwanta taja wata kakkabrar zanin rufa ta rufe, matar dake tsaye gefenta ta sake yaye zanin tana fad'in "dole ki tashi, ke da kanki kika ce na tasheki takwas daidai saboda bak'in da zasu zo." Tana jin haka ta tashi firgigit tana zare ido tare da kallon mahaifiyar tata tace "k'arfe nawa yanzun?" Tab'e baki tayi tace "08:20." Ai kuwa kamar zata bige uwar haka ta diro daga kan gadon ta nufi k'ofar fita, ta bud'e k'ofar matar tace "ina kuma zaki je da wannan kayan?" Ko saurarenta ba tayi ba kawai ta fice abinta, da gudu ta sauko daga matakalar benen, tsinkayar mahaifinta tayi a farfajiyar gidan d'aya daga cikin masu tsaron lafiyarsa ya bud'e masa mota yana daf da shiga, da gudu ta k'arasa tana kiran "papa, papa." Tsayawa yayi ya juyo yana kallonta, sai dai bashi kad'ai ba harda masu tsaron lafiyarsa dake cikin tenue d'insu na sojoji su hud'u, kayan baccine wando iya cinyoyinta sai kuma k'arama kuma siririyar riga mai kamar puscier, abinka ga fara kuma doguwa kyakyawa, ba tare data kulasu ba kawai tace wa mahaifinta "papa, ku jirani na shirya saiku ajeni a service d'in." "Motarki fa?" cewar papan Juyawa kawai tayi ta nufi cikin gidan tana fad'in "bana jin tuk'i yau." Ajiyar zuciya ya sauke dan babu yanda zaiyi dole ya jirata, yayin da jami'an suka bita da kallo iri iri suna kallon mazaunanta dake juyawa gwanin ban sha'awa. Kasancewar tana sauri yau shi yasa bata jima douche ba ta fito cikin k'ank'anin lokaci ta shirya, doguwar rigar tattausan tissue (matériel), wacce ta kama jikinta sosai k'asa kuma ta bud'e, kallabin rigar kawai ta d'aura ta d'auki jakarta tasa takalmi ta fito bayan fessa tsadaddun turarukanta masu d'aukar hankali dayawa, duk da jan jan-baki ne ta shafa kad'ai amma hakan bai hana kyawunta fitowa ba sai k'ananun kitsonta da suka kwanta a gadon bayanta. Tana fitowa matar na zaune a d'aya daga cikin kujerun falon ta kalleta, cike da nuna rashin jin dad'i tace "me yasa kullum kike burin mu dinga nanata kalma d'aya, yanzu ko nauyi ba kiji ki fita haka babu gyale bare hijabi." Wata babbar fridge ta bud'a tana fad'in "kece kike sha'awar bawa kanki wahala da kike maimaita abu guda kullum." Tana fad'a ta d'auki wani gateau da holandia yagourt ta fice abinta, tana zuwa jami'in ya bud'e mata gidan baya kusa da mahaifinta, shagalta da yayi da kallonta yasa bai bud'e k'ofar da kyau ba, cikin jin haushi ta daka masa tsawar da saida kowa ya zabura dake wajen tana fad'in, "Imbecile, q'est ce que tu regarde?" Da sauri ya bud'e mata ta shiga tana jan tsaki tana fad'in "sakarkarin banza kawai, ni banga abinda suke tsinana maka ba da har yanzu kake tare dasu, in banda k'yauyenci da shirme babu abinda suka sani." Haka suka ja motocin, mota d'aya ce a gabansu sai kuma wata d'ayar a baya tasu a tsakiya, saboda tsaro. Gâteau ta fara ci tana korawa da tana ci gaba da mita, shi dai mahaifinta saurarenta kawai yake,amma hankalinshi baya wajenta, har saida suka isa suna tsayawa a babban masana'antar ta sake kallensu tace "kenan babarku ce zata bud'e min k'ofar ko me?" Wanda baya tuk'in ne ya fito ya bud'e mata, tana fita ta kalli mahaifin nata tace "idan kaje mashayar ka shawu son ranka, kaga saika shigo mana gida a buge." Kallonta kawai yayi baice da ita k'ala ba, ita kuma ta wuce ta tunkari ma'aikatar, tana shiga ma'aikatan suka fara shan jinin jikinsu yayin da kowa ke gaisheta, sai dai babu mai sa'ar da zata amsa mashi gaisuwar , secretaire d'inta mai sunan *Habiba* ce ta karb'i jakar hannunta ta fara take mata baya tare da fad'a mata programme d'insu na yau bayan sun sallami bak'in, juyowa tayi a hassale ta kalleta tace, "Ki soke duk wani programme na yau dan babu abinda zan iya, bak'in nan kawai zan gani na koma gida." Shiru tayi suka haura sama a cikin acessaire in da zai sadasu da d'akin da bakin suke, tana shiga kallon mutanen ya dawo kanta in da kowa ke yaba kyawun fuskarta dana hallita da Allah yayi mata, bakin turawa ne duka ta mikawa hannu cikin sakin fuska suka gaisa kafin ta zaune kujerar dake tsakiyar sauran kuberun , saida kowa ya zauna mazauninshi harda secretaire d'inta ta zaune daga bayanta danta d'auki rahoton abinda zasu tattauna, sai lokacin kuma kallonta ya kai ga wata kujera da babu mazauninta, kallon habiba tayi tace, "Wane sakarai ne anan da bai shigo ba?" Cikin ladabi Habiba tace " *Umar Faruk* ne." Za tayo magana suka ji an bud'e k'ofar wajen, ganin saurayin cikin hanzari yake yasa ta tashi tsaye cike da raini tace "sannu da zuwa yallab'ai." Kallonta yayo ya kalli mutanen dake wajen, take ya fahimci abinda take nufi dan haka yace "je demande vos esxuze, je..." Tsawar data masa yasa yayi shiru "yi mana shiru, kenan muna zaune nan dan ka zo ka bamu hak'uri, kai mahaukacin ina ne da baka san mahimmancin lokaci ba? kawai mutane jahilai daku babu abinda kuka iya sai tumasanci da banlag...." "Ke, ya isheki haka." Wannan maganar ita tasa tayi shiru bata shirya ba..... Cikin b'acin rai ya ci gaba da cewa "me kika d'auki kanki? su waye jahilan? fad'a min matakin karatunki da har kike fad'a min haka, to bari kiji wallahi kika sake kirana jahilai saina fasa miki baki a wurin nan, ke in ba jahilce ke damunki ba me yasa zaki kira wasu da jahilai, kuma bari kiji aikine da nake a service d'inku zaisa kimin kallon banza ko? to na daina daga yau, saiki zauna ki cinye wurin idan zaki iya." Yana fad'a ya juya ya barta nan tsaye sake da baki, a fusace ya bar wurin kayanshi ya had'a dake kan teburd'inshi yana shirin fita, ta baya yaji an dafa kafad'arshi, juyowa yayi ya sauke idonshi akan babban abokinshi.... *Luv you guy's*😍 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ _Manzo (S.A.W) yace "Imanin d'ayanku ba zai cika ba har saiya soma dan uwansa abinda yake so ma kansa."_ *Imamul Bukhari da muslim suka ruwaitoshi* 2⃣ "Faruk lafiya na ganka rai a b'ace?" Cikin masifa yace "ina fa lafiya, wannan 'yar rainin hankalin tana nema ta b'ata min rai kawai dan tana ganin nan mallakin mahaifinta ne, ni dama tunda naga yarinyar nan nasan ba za ayi abun k'warai a wurin nan ba." Wani murmushi yayi yace "Faruk, to yanzu meya faru kenan?" "Me kuwa ya faru, na baro mata wurin,kuma daga nan gidanmu nayi dan ba zan iya aiki a k'arkashin yarinyar nan ba." Da sauri ya rik'e hannunshi daga shirin rataya jakar da yake shirin yi yana fad'in "me kace? Faruk kana da hankali kuwa? kasan me kake shirin aikatawa?" "To bari kaji in fad'a maka kuskuren da kake shirin aikatawa, wannan aiki shekara hud'u mukayi muna neman abinyi amma bamu samu ba, ka sani kafin mu sameshi munsha wahala sosai, bama wannan ba Faruk me yasa ba kayi tunanin mutanen da suka ci suke sha ta dalilinka ba, ko ka manta da irin nauyin dake kanka ne, sannan ka sani wannan aikin da kake neman watsarwa a yanzun, to ka sani akwai dubbun nan mutanen dake qaunarshi kuma d'aruruwan mutane ne zasu so da burin samun kujerar daka tashi, dan haka kayi tunani kafin ka yanke hukunci." Barinshi yayi tsaye yana tunanin abinda ya fad'a, ganin baida wata mafita data wuce ya zauna yasa ya ajiye jakar cikin sanyin jiki ya koma sale d'in bak'in, a hankali ya bud'e kofar yayi daidai da har sun gama tattauna abinda ya tarasu, kallonshi take sosai da mamakin abinda ya maidoshi, saida ta bawa bakin nata hannu sukayi musabaha sannan suka wuce, saida ta gama kallonshi shi kuma ya kasa cewa komai, wayarta ta dauka Habiba ta biyota da jakarta suka fita daga wajen, acessaire (lift) suka shiga Habiba na shirin rufewa ya kutsa kai ciki, tana ganin haka ta fito cikin zafin rai ta nufi matattakalar bene da sauri ta fara sauka, da sauri shima ya fito harda gudu gudu ya tari gabanta ya soma sauka ta baya yana kallonta yana fad'in "magana zamuyi dan Allah ki saurareni." Bata saurareshi harta sauka suna kaiwa tsakiyar ma'aikatar ya sake tare gabanta yana fad'in "dan Allah ki saurareni, hak'uri zan baki...." Marin daya sauka a kunci ne yasa yayi d'uf, dafe yake da kunci yana kallonta, itama shi d'in take kallo haka kuma duk mutanen wajen ita su suke kallo, kafin wani abu ya sake faruwa sai kuwa Faruk ya zabgeta da marin da yafi wanda ta mishi. Dafe kuncinta tayi baki bud'e tana kallonshi saboda mamaki, kasa motsawa tayi daga wajen yayin da shi kuma ya d'ora mata da wani sabon bayani "wallahi ke baki isa ba kisa hannu ki mareni, akan me? saboda kawai muna k'asanki." D'aukar kayanshi yayi ya bar ma'aikatar gaba d'aya, cikin fushi da ba zata iya misaltashi ba ta bar wajen, gudu take sosai a mota ba tare da tunanin wani abu ya sameta ba. Tana shiga ko rufe motar ba tayi ba ta wuce cikin gidan da gudu, daf da k'ofar shiga ta fad'a saman mutum, kallon kallon suka tsaya yi tana gama gane waye ya rik'eta ta fizge jikinta tana tureshi baya, shi kuma murmushi kawai yake mata, cikin masifa da son sauke bala'inta a kanshi ta fara magana, "Meye haka, kai mahaukacin ina ne? baka ganine da zaka bigeni harda wani tab'a jikina? to bari kaji wallahi yau duk uban daya tsaya maka a garin nan saika bar gidan nan, tunda bana ubanka bane." Duk da maganganunta sun masa zafi amma daurewa yayi yace "bake kika kawoni ba, ba kuma zaki fitar dani ba idan banyi niyya ba." Cike da gatsali tace "saboda uban kane ya gida gidan?" Cike da hassala ya fizgo hannunta kamar zai had'ata da jikinshi yace "wai ke me yasa baki da wayo ne, me yasa duk abinda ya zo bakinki fad'inshi kike? ke dai kinsan ubana ba matsiyaci bane bare kice zaki min gorin da kike wa wasu." Sake fizge hannunta tayi ta tureshi iya k'arfinta tace "banza kawai, wani arzik'i mahaifin naka yake da da har zaka fad'a min, to bari kaji yau dole ka bar gidan nan, dan ba zai yiyuba ka zauna kana kawo mana mata a gida ba bayan kasha giyarka." Muryar Mamie ce suka ji tace "Khairat dama rashin mutuncin naki har ya kai haka? waike wace irin yarinya ce marar ganin girman na gaba da ita? me yasa kika zab'arwa kanki wannan kakkaussar rayuwar da ba zata kaiki ko ina ba a matsayinki na mace?" K'arasa shigowa tayi cikin falo tana kallon uwar tace "nice ai ya kamata na miki wannan tambayar, me yasa kika auri mutumin da kinsan baya da hallaye masu kyau? sannan karki sake cemin bana da mutunci, dan inma hakane to gadone nayi" Kafin tayi wata magana ta d'ora da "kinga, wallahi yaron nan ya bar gidan nan yau, idan kuma ba haka ba zansa Papa yayi rashin mutunci a gidan nan, idan kuma shiya kasa saboda yana tsoronki, toni da kaina zanyi kuma zaku sha mamaki." A fusace ta rab'a uwar tayi d'akinta ta barsu nan, hawayen da suka fara taho mata ne tayi saurin saka hannu ta share tana kallon Mujahhid, murmushin yak'e ta masa tace "kana ji ko yarona, kayi hak'uri dan Allah k....." Katseta yayi ya matso kusanta da sauri yana fad'in "karki damu Mamie, ba komai wallahi, zan tafi, amma ni ke nake tunani yanda zaki ci gaba da rayuwa a gidan nan cikin kad'aici." Kallonshi tayi tace "a'a, karka damu dani, aini na saba, zan ci gaba da zama a haka, har lokacin da Khairat zata fitar da mijin aure, dan aurenta ne ya tsayar dani gidan nan." "Shikenan Mamie, zan tafi, bara naje na had'a kayana." Tana shiga d'aki ta jefar da jakarta ta k'arasa gaban coiffeuse tasa hannu tayi watsi da kayan dake wajen, matuk'a ranta a b'ace yake kuma tana so tayi abinda yafi wanda aka mata ciwo, a hankali ta fara zamewa a jikin bango tana sulalewa har takai qasa, fashewa tayi da kuka sosai, ta jima a gurin tana kuka har saida mai aiki ta bud'a d'akin zata shigo, cikin daka tsawa tace "ki fita ki bani wuri, bana son ganin kowa." Abinda ba'a so ne ya faru, saboda tsananin damuwa da kuka yasa qirjinta ya fara matsanancin ciwo haka kuma kanta ya fara mata bala'en'en ciwon da tafi fatan mutuwarta a kanshi, jin haka yasa ta rarrafa ta bud'a coffre ta d'auki maganinta, duk da dishidishi take gani hakan ta duba amma bata ga ruwa ba ba a d'akin , k'arfin hali tayi ta tashi ta nufi k'ofa danta samu ruwan, tana kusa ga kaiwa kawai ta fad'i a guri numfashinta kad'an yake fita, hannayenta ne duk bisa kanta saboda yanda yake fizgarta, daga haka kuma bata sake sanin meya k'ara faruwa ba a gaba. *Da misalin* 16:30 Papa ya shigo gidan, Mamie na zaune akan kujera cikin damuwa da tunanin halin da Khairat take ciki, ba tare da sallama ba kawai ya zauna kusa da ita yana fad'in "sannu da gida." Cikin sanyin jiki da tabe baki tace "yawwa, sannu da shigowa?" "Ba dai Khairat bata dawo ba?" ya fad'a yana cire hular kanshi. Saida ta sauke ajiyar zuciya tace "bata wuce awa d'aya ba da fita ta dawo, tana d'akinta." "Bacci take?" A sanyaye tace "gaskiya ban sani ba, ta shigo kamar ranta a bace yake, harma suka samu matsala da Mujahhid wanda yayi sanadiyar komawarsa gida, amma tunda ta shiga d'aki bata fito ba, kuma mai aiki taje ta dubo halin da take ciki ta korota." Jin tayi shiru yasa ya kalleta yace "ina jinki, sai akayi yaya?" "Ba komai, har yanzu tana ciki." Tsaye ya mik'e yana girgiza kai yace "ban san me yasa kike nuna mata rashin kulawarki ba kamar ba 'yar da kika haifa ba, da bake kika haifeta ba sai nace ba kya sonta, kinfi kowa sanin duk baccin da Khairat za tayi ba zata kai wannan lokacin tana bacci ba, amma ki kasa duba halin da take ciki." Yana bud'e k'ofar ya k'arasa a guje yana fad'in "oh mon Dieu, Khairat, Khairat!!!." Maida kallonshi yayi ga Mamie wacce ta shigo yanzu, cikin b'acin rai yace "kin gani ko, kin gani abinda kika jawo mana, wai me yasa kike nunawa yarinyar nan rashin kulawa ne? ki dubi sakacinki abinda yake nema yaja mana." Mamie da bata san meya faru ba itama cikin fad'a tace "to miye anfanin kulawar da zan dinga nuna mata, naga kaima da kake nuna mata kulawar ba wani girmanka take gani ba, bare kuma ni à banza...." Duk da ta kai k'arshen aya amma saida ta dire kalmar ba daidai ba saboda tsawar daya mata, cikin d'aga murya yace "dallah ki min shiru, zaki kama min ita ne ko kuma burinki ta mutu?" Qafafunta ta kama shi kuma ya d'auki duka rabin jikinta suka nufo da ita waje, ma'aikatan gidan na ganin haka suka fara tambayar lafiya meya sameta, biyarsu suke a baya har chauffeur ya bud'e musu k'ofar mota suka kwantar da ita a baya sannan suka shiga suka bar gidan, ma'aikatan kowa jini kan akaifa , ba zasu ce suna jin dad'i ba saboda rashin lafiyarta , amma dai sun san sun d'an samu hutu na wani d'an lokaci. ******************** *Faruk* ne zaune akan taburma shi da abokinshi *Ishaq*, yayin da wata dattijuwar mata mai kamala ke gefensu akan kujera yar tsugunno, sai kuma babban malamin dake tsaye ya tisasu a gaba yana fad'a akan aikinshi daya baro, cikin fad'a ya sake cewa, "Kai yanzu badan baka da hankali ba, daga k'aramin abu sai kawai kayi hushi, kai gaka uban zuciya ko? to bari kaji wallahi wannan aikin idan har ka bari ya kubuce maka, to wallahi za kayi nadama da daka sani, kai kafi kowa sanin kaine kusan rabin k'arfin gidan nan, to idan kace ka daina aikin kenan duk yayanka ne zai had'a ya d'auki har nauyinka.?" D'ago kanshi yayi yace "Baba bafa k'aramin abu bane, marina fa tayi a fuska, wallahi ko k....." Tsawar da Baba ya masa yana fad'in "ta mareka d'in, nace ta mareka saime? idan baka rama ba mutuwa za kayi, kuma tun farko ai kai kaja komai." "Dan haka ka jini da kyau, ka tashi yanzun nan ga Ishaq nan ya rankaka kuje ka sameta ka bata hak'uri, karka yarda ka rasa wannan aikin, in kuma kayi sake to ka sani, wallahi abincin gidan nan ma ka daina ci tunda kai sarkin zuciya ne, waika gaka *Umar Faruk* ko?" Sake d'ago kai yayi yace "Baba, cewa fa kake naje na...." "K'warai haka nake nufi, dole sai kaje ka bata hak'uri, in kuma ba haka ba to duk matakin dana d'auka kanka, kai ka siyo da kud'inka." Sai lokacin mahaifiyarshi tace "in banda abin Umar faruk ma, kaida maganar aure ka keyi amma kake k'ok'arin aje aikin da shine gatanka." "To, fad'a masa dai, tunda naga shi baya da hankali zuciya ce kawai yasa a gaba." Ishaq ne yace "kaga, ba wani abin damuwa bane, yanzu ya tashi mu tafi mu koma service d'in mu samu manager, nasan insha Allah zai taimaka mana kamar yanda ya taimaka mana muka samu aikin nan da farko." Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi kafin ya kalli Baba yace " kuyi hak'uri Baba, insha Allah zanje na bata hak'uri kamar yanda kuka ce." Addu'a Mama ta bishi da ita da fatan samun dacewa, Baba kuma na sake jaddada masa ya tabbatar ya bata hak'uri sosai harta hak'ura, haka suka fito da niyyar tafiya ma'aikatar wajen manager. Sun samu manager kuma Ishaq ya fad'a masa komai daya faru, yayi mamaki sosai dan baisan wainar da aka toya ba, yayi jimami sosai tare da k'ara tsorata Faruk akan karma ya fara tunkararta ya jira hukuncin da mahaifinta zai d'auka a kanshi ko kuma ita da kanta, baiji shakka ko d'ard'ar ba akan matakin da zasu d'auka, matsalarshi d'aya shine yanda mahaifinshi ya d'auka da zafi sosai, ganin baice komai ba yasa manager cewa, "A gaskiya *Umar Faruk* ba zan yarda a dalilinka na rasa nawa aikin ba, kayi hak'uri, amma taimakon da zan iya maka na riga da nayi maka shi, shawara d'aya da zan baka kawai shine, idan har ta dawo d'aukar fansa to ka qasqantar da kanka, ka nuna mata kayi nadama kuma a bisa kuskuren rashin sanin ko wacece ita ka mareta, idan kayi sa'a ta iya yafe maka, amma gaskiya bana tunanin zata hak'ura, dan wallahi yarinyar nan rashin mutuncinta ya kai mak'ura, bata kallon kowa da idon daraja babu tausayi ko imani a zuciyarta, kuma tun ranar da mahaifinta ya mallaka mata masana'antar nan na fad'a muku dukanmu sai munyi hak'uri da ita, saboda kaushinta yayi yawa." A sanyaye Umar faruk yace "zan jaraba na gani, bara naje bureau d'in nata." Murmushi manager yayi yace "ta yaya kake tunanin zata zauna a wajen nan, ina jin a lokacin da naga tafiyarta to a lokacin ne abun ya faru." "Kenan yanzu tana gida?" cewar Faruk d'in. "Ina tunanin haka." "Shikenan, zamu je har gidan, watak'ila ma tafi saurarenmu." cewar Ishaq Faruk ne yace "a'a fa Ishaq, gaskiya bana so naje gidansu, idan taga haka zata san nadamu sosai, zata d'auka gaba d'aya na bada rayuwata wa aikin nan, hakan kuma zaisa ta qara wani rashin mutuncin." "Muji ta d'auka a hakan in har ba zata koreka ba, meye a ciki?" Kai Faruk ya girgiza yace "waiku me yasa ne kuke shakkarta har haka? mutum ce fa kamarku kuma mace mai rauni a kanku, me yasa zaku dinga tsoronta har haka, nifa wallahi bana son irin haka gaskiya, dan wannan ai bayar da maza kuke, yarinyar da da zaku bud'e mata ido sau d'aya dole zata fara shakkarku itama, amma duk kubi kuna wani tsoronta kamar ita ta halliceku." Fuskar manager d'auke da murmushi yace "bawai muna jin tsoronta bane, sai dai ka sani kowane d'an adam a rayuwa yana buqatar ci da sha kafin ya rayu, to tamu k'addarar ta damka cin mu da shanmu ta sanadiyarta ne, ita kuma bata da kirki duk da bata jima a garin nan ba, amma na samu labarinta sosai kamar wanda yayi rayuwa a gidansu, dan ba tun yau muke tare da mahaifinta ba, kaga dole mubi a sannu." Faruk ne ya tashi tsaye yace "zamu je gidan, ina fatan ta amince kodan saboda Baba." Cikin tsokana Ishaq daya mik'e shima yace "da kana so amma kake wani nuna baka damu ba." "Amma ai kaji me nace, ina fata ta amince saboda Baba." ya fad'a ba tare daya kalleshi ba. Suna fita akan mashin d'in Faruk suka kama hanyar zuwa gidansu Khairat...... _Shin kuna ganin za suyi nasara kuwa? to wai zama su samu ganin Khairat d'in ko kuwa dai...???_ ********************* Suna zuwa k'ofar gidan suka tsaya suka sauka akan mashin d'in suka nufi k'ofar gidan, mai gadin gidan ne mai sanye da kaki irin na sojawa ya taresu yana fad'in "yadai malamai, daga ina, wa kuke nema?" Ishaq ne yace "sannun ko, dan Allah munzo ganin Hajia Khairat ne." Kallon tuhuma ya musu yace " Hajia Khairat? to tasan da zuwanku ne?" Kallon juna sukayi tare da yin shiru na 'yan dak'ik'u kafin Ishaq ya sake cewa "gaskiya bata san da zuwanmu, mu daga service d'inta muke, manager ne ya turo mu saboda wani aiki daya d'an taso." Kallonshi Faruk yayi saboda jin abinda ya fad'a , mai gadin ne yace "kuyi hak'uri mazaje, duk wanda ku kaga ya shiga gidan nan to an san da zuwanshi koda kuwa d'an uwane, kunsan gidan manyan mutane." "Yanzu kenan babu wata dama da zata saka mu ganinta?" cewar Faruk. "Gaskiya babu, dan Hajia Khairat ko tasan da zuwan mutun ma zata iya tsayar dashi a k'ofar gidan nan na tsawon awa uku, idan na barku kuka shiga zan iya rasa aikina." Faruk ne yace "yanzu dan Allah to ya zamuyi muganta?" Mai gadin ne yace "in dai abu mai mahimmaci ne, to zan iya fad'a muku wurin da zaku sameta, yanzu dai kunga ta shiga gida, kuma da alama ranta a b'ace ta shigo." "To kenan ina zamu sameta?" "Duk kwana uku takan je wajen casu, amma takamaimai wajen da take zuwa kuma wannan kuma ban sani ba, dan tana zuwa club da dama daga manya har qanana, yau kuma nasan zata fita saiku had'u acan." Da mamaki Faruk ya kalleshi yace "malam, mufa a ma'aikatarta muke aiki, ba wani abu bane a tsakaninmu da ita ba, amma ta yaya zamu sameta a wannan wajen kuma fa sai cikin dare." D'aure fuska mutumin yayi yace "kunga dan Allah kubar nan, taimako kuka ce kuma shi nayi muku." Yana fad'a ya koma mazauninshi ya barsu tsaye, mashin d'insu suka hau akan hanya suna tunanin wata shawarar, amma Faruk yace shi bai tab'a zuwa gidan rawa ba ba kuma zai fara zuwa yau ba. Suna zuwa gida suka fad'awa Baba yanda ake ciki, fafur Baba ya rufe ido yace bai yarda su tashi su koma, ganin basu son tafiya yasa Baba ya tisa k'eyar Umar faruk gaba yace su tafi, haka kuwa akayi akan mashin d'inshi suka tafi, amma wannan karan suna zuwa mai gadin yace musu an tafi da ita likita babu lafiya, da alama ma kamar babu rai a tare da ita, tabbas Umar faruk yaji ba dad'i kuma yana tsoron ace abinda ya faru tsakaninsu ne ya janyo faruwar hakan, likitar aka fad'a musu suka nufi can shi da Baba. _Faruk ni dai a ganina da kun hak'ura da son ganinta kawai._😉 Cikin sa'a kuwa suna zuwa sukaga masu tsaron mahaifinta a kusa da d'akin da aka shigar da ita cikin gaggawa, kusa da d'akin suka tsaya amma ba suyi magana ba saboda ganin mahaifin nata nata kai komo a wajen ya gagara nutsuwa, duk da baisan mahaifiyarta ba amma da gani yasan ita ta haifeta saboda tsananin kamar da suke, kuma dama tun daga fatar jiki zaka san uwace tayi ba mahaifinta ba dake tillik'ik'e kuma bak'i wulik dashi,🤣 had'in gambiza ba, duk da akwai damuwa sosai a fuskarta amma dai babu alamun hawaye a tare da ita. D'auke kai sukayi kamar ba wajensu suka zo ba, amma abin mamaki shine muryar Baba da sukaji yace "kina zaune hankali kwance, da alama so kike ta mutu ki huta ko? to ta Allah ba taki ba wallahi." Tsaye ta mik'e cikin jin zafi tace "eh, so nake ta mutu na huta, kai a ganinka idan ta mutu ba zan samu salama ba? idan da abinda ya janyo mata wannan halin bai wuce kai ba, wallahi duk kai kaja mana halin da muke ciki saboda bak'in halinka, yarinyar nan tun tana k'arama ta fara fahimtar halayenka, amma hakan baisa ka daina ba, me kake so ta zama? wallahi ka sani alhakin lalacewar rayuwarta yana wuyanka ne, addu'a d'aya nake mata yanzu shine, kar Allah yasa ta fara shaye shaye da bin maza kamar yanda kake lalata 'ya'yan wasu." Fizgota yayi daf dashi cikin hassala yace "ke ya isa haka, ke me yasa baki da kunya ne? a cikin mutane zaki nime tozarta ni, kuma ni ai nasan 'yata, wallahi ba zata tab'a bin maza ba." Fizge hannunta tayi tasa gyalenta ta share hawayen idonta tayi murmushin takaici tace "kenan baka so ta fara bin maza ko, ka manta da fad'ar Manzo (S.A.W) ne, _cewar duk abinda kayi sai an maka_? kayi gaggawar aurar da ita, idan kuma ba haka ba to wallahi ni zan barka na koma wajen iyayena, dan ba zan iya supporter naji kona ga wani abu ya sameta ba." "Ke marar mutunci, wallahi zai karyaki a warin nan, shashashar banza kawai." Duk maganar nan yayita ne da d'aga hannu kamar zai mareta, zaburowa tayi tace "ka dakeni mana, ina jin tsorone ? dukanka wane irine ban gani ba ai sai dai kuma na gaba." Hannu ya d'aga kam da nufin kai mata mari sai kawai ya tsaya cak saboda ganin Khairat d'in da aka shiga da ita ranga ranga amma ta fito da k'afafunta, kamar dai yanda suka taho da ita haka ta fito babu takalmi ba kallabi, kallon iyayen nata kawai take sai huci take saukewa, takowa ta farayi gabansu docteur kuma ya biyo bayanta yana neman ta tsaya dan farfad'owarta kenan taji hayaniyar iyayenta, saida ta tsaya gabansu ta kallesu da kyau sannan ta kalli drivensu tace "muje ka mayar dani gida." Wucewa tayi mahaifin nata ya rik'e hannunta yana fad'in "gimbiyata, ina kuma zaki je ya jikin naki?" Da iya k'arfinta ta fizgo hannunta tana mashi jan kallo tace "lache moi ma main." ta k'arashe da d'aga murya. Wucewa tayi suka bi bayanta Papa na kiran sunanta harta shiga mota ta rufe, haka suka shiga motar ba tare da kowa yayi magana ba har suka kai gidan. Faruk kam da Babanshi mutuwar tsaye sukayi, mamaki ya gama kashesu a wurin, tabbas akwai wasu abubuwa a cikin rayuwar gidan, da alama arzik'i ne Allah ya musu amma babu kwanciyar hankali. _Wallahi da auren wani mai kud'in gwara auren talaka in dai da kwanciyar hankali, Allah ka k'ara mana kwanciyar hankali da ni'ima a qasarmu dama sauren qasashe baki d'aya._ ********************* Gida suka koma dan sunga babu alamun nasara, amma duk da haka Baba bai hak'ura ba yace koma da safe ya shirya ya tafi gurin aikinshi kamar yanda ya saba, watak'ila idan da rabo ma ba zata masa magana. *Luv you guy's*😍 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _My BK, kiyi sauri ki dawo fa._ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ *Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a garesa yace* " _Kaji tsoron Allah a duk inda kake_" *Rawahu muslim* 3⃣ Tunda ta shiga d'aki wanka tayi ta saka kayan data saba sakawa wato k'aramin wando iya cinya da k'aramar riga, zaune tayi akan gado tana tunanin abinyi, har akayi sallah magrib da isha amma bata tashi daga in da take ba, wani tunani da tayi yasa ta tashi ta fito daga d'akin, duk da duka iyayen nata na zaune a falon amma babu wanda ta kula bare ta masa magana, farfajiyar gidan ta fita, masu tsaron mahaifinta ne zaune a kusa da mai gadi suna hira, tsaye tayi nesa dasu cike da raini tace "kuzo nan." Kallon juna sukayi cike da raini suka tashi a kasalance suka nufi wajenta, tsaye sukayi kowa ya d'auke kai babu mai kallonta, cikin jin haushi ta daka musu tsawa "kai, ni kuke wa wannan kallon? to ku saurareni da kyau kuji aiki zan saku." Shirun da sukayi yasa ranta ya sake b'aci , a harrzuk'e ta shak'o uwan rigar d'aya daga cikinsu tana fad'in "kai matsiyacin banza, ku har kun isa ina magana daku kuna wani d'auke kai, ko kun manta k'ark'ashin mahaifina kuke, kufa ba komai bane face maqasqanta wanda suke wuni dare da rana a bayan iyayenmu domin tsare lafiyarsu, yaushe kuka fara tunanin kuna da matsayi da har zaku rainani?" Mai sauk'in cikin sune yace "kiyi hak'uri Hajia, ki fad'i aikin da zamu miki." Tureshi tayi yayi baya baya kamar zai fad'i sannan ta kalli wanda yayi maganar tace "ku nutsu ku jini da kyau, akwai wani saurayi da nake so ku d'auko min shi gobe, ina so ku kaishi d'aya daga cikin gidajen Papa, idan kun d'aukoshi saiku kirani zan sameku acan, amma kafin nazo ku tabbatar kun canzamin kammaninshi ta yanda ba zai iya gane kanshi ba bare kuma wani." Da hannu ta nunasu tace "kun fahimta?" D'aya daga cikine yace "amma ta yaya zamu iya ganeshi kenan?" Sai lokacin ta tuna da hakan, a wulak'ance ta kallesu tace "ku jirani anan, yanzun nan zan samo photonshi." Binsu tayi da harara tare da fad'in "banzaye kawai marasa anfani." Tana wucewa wanda ta shak'e ma wuyan riga yayi wani huci tare da rik'e gudu yana kallonta, a hassale yace "wallahi saina ma yarinyar nan rashin mutunci ta yanda gobe ba zata sake sha'awar wulak'anta wani ba, dan muna aiki qasan mahaifinta bashi ke nuna maqasqanta bane kamar yanda take d'auka, wallahi na gaji dan abinda take mana ko wannan banzan mashayin uban nata bai isa ya mana ba bare kuma ita banza." D'aya daga cikine yayi dariya yace "toya zamuyi tunda Allah ya d'orasu akanmu, kuma da kake cewa zaka mata rashin mutunci, ita fa 'yar akuya kai kasan haka, kenan me kake tunanin yi mata?" Da sauri ya bashi amsa da "dukan tsiya zan mata wallahi har saina sab'a mata kammaninta." Shak'iyin cikin ne ya lashe baki tare da d'an cije leb'e yace "ku naku duk wasa ne, irin yaran nan ai duka baya gyarasu, karfa ku manta gatane ta gani shi yasa take abinda take so, ni wallahi ban tab'a jin wai na daketa ba, dan duka ba shine mafita ba." "Miye mafita to? danni dai na gaji da rainin hankalin yarinyar nan." Saida ya kalleshu yana murmushi kafin yace "kona fad'a ma ba zaku iya ba, dan haka ku barni kawai ni zanji da komai." "Kamar ya ba zamu iya ba? ka fad'a in dai har za muyi maganinta wallahi za muyi." Sake kafesu yayi da ido yace "kun tabbata?" "Eh, ka fad'a kawai." Ajiyar zuciya yayi yace "kullum tana cikin qananan kaya, hakan kuma na tayar min da sha'awata, abinda za muyi kawai mu takurata ta hanyar samun biyan buk'atarmu, ta hakane kad'ai zamu iya huce abinda ta mana." Tuni d'aya daga ciki har shaid'an ya k'awata masa abin, cewa yayi "kuma fa hakane wallahi, dan shi fyad'e idan kayiwa mace ba zata tab'a mantawa ba har abada, kaga zamu tashi 1-1 mu da ita ,ita ba zata manta ba muma ba zamu manta irin wannan cin kashin data mana ba." Hannu ya bashi suka bige suna dariya yace "da kyau mutumina ka fahimceni daidai, kuma ma wannan yarinyar ai da gani kasan ba mune zamu fara ba, da alama wasu sun rigamu kai da gani kasan ba budurwa bace, a idone kawai muke ganin haka." "Gaskiya ne kuma." "To amma ni gaskiya ina d'an jin tsoro, gaskiya ban tab'a yi ba tunda nake, kuma kaga za ayi binciki akan lamarin nan idan aka ganemu, kunga fa shikenan munyi asarar rayuwarmu mun b'ata k'uruciyarmu a banza." "Bama za'a ganemu ba, ai za muyi anfani ne da kasancewarmu sojiji miyi aiki da ilimi, insha Allah komai zai wuce babu abinda zai faru, kuma muma ai bamu tab'a yi ba." "To ya zamuyi kenan?" "Abu mai sauk'i, kawai za muyi anfani da gidan rawar da take zuwa duk kwana uku sai muyi komai acan, kunga ta haka zamu fita daga zargi kuma babu wani bincike, domin kuwa cikin biyu dole suyi tunanin d'aya." "Kamar me dame kenan?" "Na farko za suyi tunanin kodai ita da samarinta ne da suka saba shek'e ayarsu, ko kuma dai tunda wajen rawa na b'ata garine , kaga za'a ce ta had'u da marasa jine kawai suka mata fyad'e wannan shine." Cikin dariya d'aya ya bashi hannu yana fad'in "gaskiya Musa kanka naja sosai, wannan tsarin fa yayi." Cikin dariyar mugunta yace "ko baiyi ba dole zan fito da wani, dan burina kawai buk'atata ta biya a kanta." Musa ne yace " ku zama cikin shiri , dan ko yau bata fita saboda abinda ya faru, watak'ila kwana uku mai zuwa ta fita." Da wannan shawara suka tsaya akai. _Allah ya kiyaye_👏 Tana shiga d'aki wayarta ta d'auka a saman gado k'irar IPhone XMax, kira ta aikawa manager yana d'auka cike da salon bada umarni tace "ina so cikin 5 minute ka aiko min da adreshin gidansu yaron nan tare da photonshi." Tana gama fad'a ta kashe wayar, zaune tayi tsakiyar gadon tana jiran shigowar sak'on manager, 2 minute saiga sak'on ya shigo adreshi da kuma photonshi, a hankali ta furta sunan unguwar tasu " *Bassora*" Take ta tuna marin daya mata, bata san lokacin data goge photon ba daga wayar saboda b'acin rai, ajiye wayar tayi a gefenta ta fara sauke nunfarfashi ita kad'ai, jin qirjinta ya fara nauyi yasa ta tashi ta bud'a coffre ta d'auki maganinta tasha sannan ta koma gado ta kwanta, bacci harya fara d'aukarta wayarta ta fara k'ara, tana dubawa taga sunan *Macho* ya fito, d'auka tayi ta d'ora a kunne tare da jan zanin rufarta ta rufe tace "hello macho." Daga d'aya b'angaren tace "yane macho? naganki shiru, yau kin fito ne?" "A'a macho ba zan fito ba, kawai ki tafi kuji dad'inku." "Haba macho, me yasa to ba zaki je ba? kin ganni fa harna shirya." "Ba zanje ba macho, kije kawai, sai gobe naje." "To in dai hakane, nima saina bari har goben sai muje kawai." A daqile tace "wannan kuma matsalarki ce." Tana gam fad'a ta kashe wayarta gaba d'aya ta koma baccinta, a cikin bacci taji kamar ana tab'ata, bud'a ido tayi taga mahaifiyarta ce ke shafar kanta sai kuma mahifinta daga gefenta a tsaye, cike da masifa ta tashi zaune tace.... "Meya kawoku nan kuma a wannan dar....." Da sauri Mama ta rufe mata baki tace "kiyi hak'uri Khairat, na yarda nayi kuskure, amma ki sani mufa iyayenki ne dole mu damu da halin da kike ciki, mun kasa bacci saboda tunanin damuwar dake damunki." A raunane ta kalleta tana shirin fashewa da kuka tace "Mamie, ya kike so nayi? kince na daina shiga harkarki kuma na daina, yanzu me kike so nayi to?" Shiru sukayi kafin ta sake cewa "Mamie, ki fad'a min tunda muke dake kin tab'a nuna min soyayyarki, kullum hantara kike da yimin fad'a tare da kokarin aibatani, ban tab'a yin daidai ba a wajenki idan nayi ma bakya yabawa, babu abinda kuka koya min babu abinda kuke koya min wanda zai anfane ni, da fadanku na bud'e idona kune kullum cikin fad'a da aibata junanku, duk da kunsan matsalar da hakan ya janyo min amma baku daina ba, shin so kuke sai ranar da kuka bud'e ido baku ganni a duniya sannan zaku daina?" Kuka Mamie ta fashe dashi tace "a'a Khairat, wallahi ina sonki, kinsan babu yanda uwa za tak'i yar data haifa, ni ina so ki zama yarinyar kirki amma mahaifinki bai damu da rayuwarki ba, ina damuwa da halin da kike ciki, kawai dai akwai dalilin da suka sakani nuna miki rashin kulawa, amma ki yafe min kinji yata ba zan sake nesantarki ba." Ta fad'a tana rumgumeta, itama rumgumeta tayi cikin kuka tace "Mamie na riga dana b'ata rayuwata." "A'a Khairat, kar kice haka, wallahi......" Kafin ta k'arasa uban dake tsaye yace "wato kullum laifina ne ko, kullum burinki shine ki d'ora min laifi ni kad'ai ko? to wallahi baki isa ki rabani da yata ba muguwa kawai." Kallonshi Mamie tayi tace "eh naji, in ni muguwa ce kai kuma fa? ai kaine babban mugu tunda duk kaine ka jefamu halin da muke ciki, kuma wallahi in har baka tuba zuwa ga Allah ba sai kayi *nadama*." Matsowa yayi kusanta a hassale yace "wallahi kika sake magana a wajen nan saina tattakaki, saboda kin rainani ina fad'a kina fad'a ko?" "Allah yana gani bai rainaka ba kaine dai ka raina kanka, kuma nasan Allah ma ba zai kamani da laifi ba." "Ke..." wata k'ara da Khairat tayi yasa suka maida hankalinsu kanta, saukowa tayi daga kan gadon ta kama hannayen iyayen nata ta tisa k'eyarsu suka fita daga d'akin, saida ta kallesu kafin ta rufe k'ofar tace "ba zaku tab'a gyaruwa ba, wannan shine babbar damuwata, baku damu daku tozartani ba ko a dinga yayatani ba, a duk in da kuka samu kanku fad'a ku keyi da junanku." Tana fad'a ta rufe k'ofarta ta koma gado ta dinga kuka da takaicin rayuwar iyayenta. _Novel hausa akace, dan haka kuyi hak'uri 'yan uwa, ba zan sake saka muku wani harshe ba insha Allah domin kowa ya fahimta._ *Shin su musa za suyi nasara akan Khairat kuw*? *Wai me yasa iyayen Khairat suke haka*? *Meye matsalar da Khairat ke ciki?* _Kafin sanin amsoshin bara mu koma baya mu fara sanin tushen labarin._ _Ku biyoni😍_ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣ *TUSHEN LABARIN* *Alhaji Mani Bukar* babban mutum kuma mai babban dangi, asalinshi haifaffan garin *Maradi* ne kasuwancine ya kaishi *niamey* daga nan kuma harya tsunduma siyasa, mahaifinsu mutum ne daya sha boko sosai ya k'oshi, hakan yasa yake da kula da takatsantsan da yaranshi, matan mahaifinshi biyu amma gaba d'aya yaranshi guda biyar saboda tazara da ake sawa, mahaifinsu irin tsofaffin masu kud'in nan ne, hakan yasa bayan rasuwarsa yaransa suka kwashi rabonsu bayan rabon gado. Bayan rasuwar mahaifin sai kowa ya fara abinda yaga dama, haka ma Alhaji Ousmane wanda sukafi kiranshi da *Mani*, bana ce muku mutumin kirki ne ba amma dai yana da wasu manyan halaye wanda muke da tabbacin duk mai aikatasu, to tabbas babu abinda zai iya gagararsa kuma zai iya yin komai, wannan halaye kuwa sune *zina* da shan *giya*, duk da wannan halayen amma ubangiji ya masa talala ta hanyar k'ara sakawa dukiyarsa albarka, yana cikin holewarsa tare da abokai kuma sai Allah ya had'ashi da *Na'ima*. *Na'ima Bilal Abdallah*, yarinya mai hankali nutsuwa da kuma tarbiya, ta samu duk wannan ne a wajen iyayenta saboda yanda suke tsaye a kanta, asalinsu mutanen *Arlit* ne amma aiki ya kai mahaifinta qasashe da dama tun kafin aurenshi da kuma lokacin da yayi auren harda cikinta ma, wanda daga qarshe dai a *India* aka haifeta, bayan wasu shekaru sai mahaifin nata ya rasu, kasancewar a ma'aikatar ana kula da ma'aikatan da kuma iyalensu yasa basu bari mahaifiyar da yarinyar sunsha wahala ba, sunci gaba da zama a gidan compagnie tare da d'aukar d'awainiyarsu, a lokacin tana da shekara ashirin suka zo Arlit ganin danginsu, wanda kuma suka tarar da auren cousine d'inta wacce za'a kawota Maradi, dole tasa suka zo anan kuma qaddararta ta fad'a dan anan suka had'u da Mani. Tunda ya d'ora ido a kanta sai Allah ya jarabceshi da sonta har cikin zuciyarshi kuma karo na farko da yaji yayi sha'awar aure, Na'ima kam tunda ta ganshi ita kuma sai taji bai mata ba, bugu da qari da taji k'awayen amarya na fad'in halinshi na son mata saiya dinga lasar baki yana maka kallon iskanci, gashi kuma Allah ya masa muni dan babu wani abun birgewa a tare dashi, bak'i k'irin yake ga kuma k'iba da yayi saboda hutu, haka ya fara nuna mata abinda ke ranshi amma bata bashi dama ba, bayan shagalin ya kammala haka ya nemi sanin komai a kanta, rana kwatsam saiga Mani Arlit kamar daga sama. In dai tak'aice muku, abinka ga mai kud'i wanda dama zamanin nan masu kud'i suke auren kyawawan mata, haka ya shiga ya fita tare da kutsawa duk cikin wani danginta mai ruwa da tsaki a kanta har saida ya samu Na'ima, babu irin kuka da bala'in da ba tayi ba ta kuma fad'a musu ba mutumin kirki bane, amma su basu ga haka ba dan yanda ya nuna musu, a qarshe dai amarya ta tare gidanta a Maradi, bayan qalubalen data fiskanta tun daga darenta na farko har zuwa sauran darare, bayan wani lokaci kuma sai suka koma niamey da zama to tun daga shi sai dai suzo gaishe da dangi Maradi da Arlit, bayan lokacin kad'an kuma sai mahaifiyarshi ta rasu itama. Komawarsu niamey yasa ya k'ara tandarewa babu uwa babu uba babu mafad'i sai abinda yaga dama yake yi, kuka a wajen Na'ima harya zama jiki dan a wannan lokacin baya neman mata idan ba cikin gidanshi ba bayan ya shigo a bige, abun na matuk'ar damunta sosai ga rashin sonshi ga kuma bak'in cikin da yake d'ura mata, wani abin takaici shine lokacin data gama gane halinsa saita fara masa qiyo a shinfid'a in har ya nemeta, abinka ga mashayi kuma haka zai zage qarfinshi ya daketa son ranshi idan ta jikkata sannan ya turmusheta da qarfinshi ya biya buqatarsa, yarinya mai kama da indien sai gashi ta fara fita hayyacinta ta fara lalacewa, wata uku ta d'auka a wannan rayuwa, a lokacin data rame sosai saiya fara zargin ko cikine da ita shi kuma bai shirya hakan ba yanzu, daya tambayeta sai tace bata da komai dan itama bata sani ba, domin d'aukar mataki saiya fara bata qwayoyin hana d'aukar ciki, kwana uku da fara shan maganin saita fara ciwon mara kafin kace me sai jini ya fara mata zuba, bayan zuwa asibiti aka tabbatar ta cikin jikinta ya zube sakamakon shan magani ba abisa qa'ida ba , duk da taji tayi asarar beby amma kuma taji dad'i ko ba komai bata fatan haihuwa dashi. Wata babbar dama ce ya bata dan tun daga lokacin saita fara shan maganin ba qaqqautawa, tun bai fara saka abin a kanshi ba harya fara damuwa saboda ganin an d'auki lokaci mai tsayi, wasa wasa sai gashi ta d'auki shekara biyar ba tare da nadama ko data sanin abinda take yi ba, a lokacin ne kuma Mani ya dakatar da ita tare da cewa ya shirya haihuwa, hakan baisa ta daina ba dan ranar ya shigo a bazata ya samu za tasha maganin, a ranar dukan tsiya ya mata bana wasa ba sannan ya karb'e duka maganin, cikin ikon Allah wata biyar saita samu ciki, amma kuma mai matuk'ar had'ari da wahala. Saboda shan maganin data dinga yi yasa mahaifarta a had'ari hakan yasa cikinta ke buk'atar kulawa dan komai zai iya faruwa da bebynta, a lokacin da cikin ya fara girma aka mata scanning aka tabbatar da macace a cikinta, take sai Mani yaji qaunar yarinyar tun ba'a haifeta ba, visa ya samar musu suka koma India tare wajen mahaifiyarta wacce tafi jin dad'in zamanta acan. A lokacin data haihu aka tabbatar da mahaifarta ta lalace ba zata sake samun wata haihuwar ba, babu yanda ta iya dole aka cire mata mahaifar domin rage mata nauyi, Allah kuma ya jarabcesu da son *Khairat*, da k'yar Na'ima ta dawo gida niger amma zamanta gaban mahaifiyarta ya mata dad'i sosai, dan tunda suka tai bai nemeta ba, sai dai daga yanda yake fita ya jima yasa take jin ya samu wasu masu d'ebe masa kewa. *Rayuwa bayan haihuwar Khairat* tafi mata k'unci akan kafin haihuwarta, dan a wannan lokacin ya fara harkar siyasa, baya zama gida harkoki sunsha gabanshi, harkar mata ta k'aru sai dai shan giya ya d'an ragu sai daddare kawai, duk wannan bai damunta kamar yanda idan yayi shigowar dare yake ritsata a gaban Khairat ya nemeta, duk k'ok'arin da zatayi na samun dama baya barinta, haka zai kwanta da ita a gaban Khairat duk da tana bacci, ta d'auka kodan tana qarama ne yake haka duk da ba a hayyacinshi yake ba, amma sai gashi Khairat tayi wayo da girmanta da komai zai fara k'ok'arin nemanta, yarinyar ce kawai ke barin wurin saboda tsoro. Duk da haka Khairat na ganin soyayya a wajen mahaifinta da k'auna , babu wanda ya isa ya harareta baiga wulak'anci ba gata take samu a wajenshi sosai, sai dai duk da haka takan ji tsoronshi kuma bata zuwan wajenshi sai inshi ya zo wajenta, ta fara karatu a ecole (school) d'in da tafi kowace a garin, sai dai duk k'ok'arin Na'ima na ya barta taci gaba da zuwa makaranta amma ya k'iya saboda ta fara zuwa ranar ta dawo tace malam ya daketa, bai bari ta sake zuwa ba kuma Na'ima data fara koya mata a gida, ranar ya samu tana kuka bayan ya tambayeta tace mama ta daketa dan bata iya karatun data koya mata ba, bayan fad'a da Na'ima tasha y kuma ce karta sake shiga harkar 'yarshi, saboda b'acin rai sai yasa Na'ima yin alk'awarinba zata sake kulashi da yarshi ba, idan Allah ya nufeta da shirya ta shiryu, idan kuma akasin hakane to matsalarsu ce. _Kash, wannan ba mafita bace, duk inda aka je aka dawo ke uwace kin fishi asara , dan ko gidan aure taje za'a ce laifin uwane._ *Ranar talata* rana ce da Khairat ta kasa mantawa da iya duk da k'arancin shekarunta, mahaifiyarta na saka mata kayan bacci ya shigo, kamar dai yanda aka saba daga yanayin bud'e k'ofar ta gane waye da kuma halin da yake ciki, ganin yana yowa kanta yasa ta fahimci komai, tsaye ta mik'e ta tura Khairat gefe tace "kije d'akinki ina zuwa." Kallonta Khairat tayi a matuk'ar tsoro ta kalli mahaifin nata, bayan mahaifiyarta ta koma ta b'oye, lokacin kuma ya kawowa uwar cabka ya fara k'ok'arin keta rigarta, sake turata tayi ta nufi k'ofa tace "kije nace ko." Duk da tsawar data mata baisa ta tafi ba, wani mari ya kifa mata a cikin muryar 'yan shaye shaye yace "d'iyar tawa zaki ma wannan tsawar, ita sa'arki ce, nace sa'arki ce ita, tsararki ce da zaki mata wannan tsawar?" Duk ya k'are tambayoyin ne da marinta, belt (ceinture) d'inshi ya fiddo zai fara dukanta Khairat ta fita a guje tana kuka, bakin k'ofar d'akin ta tsaya tana sauraren kukan mhaifiyarta da kuma sambatu da kukan mahaifinta keyi, kamar abu yayi sauk'i sai taji k'arar belt d'in nan da kuma kukan mamarta, ta tabbatar itace yake duka, kasa jura tayi kawai saita shigo d'akin a hankali, ganin mahaifinta babu komai a jikinsa haka ma mahaifiyarta kawai sai tayi k'ara mai tsanani ta fad'i qasa somammiya, shine ya fara kai mata d'auki kafin uwar tasa kayanta ta nufi wajenta itama, a daren ba suyi bacci ba ko kad'an bayan sun samu Khairat ta farfad'o, daga lokacin sai abubuwa suka fara canzawa amma fa na d'an wani lokaci. Khairat ta daina walwala a gidan mahaifinta, tafi so ta zauna shiru ko kuma tasa écouteur (hearpeas) a kunne tana sauraro, Na'ima kuma ta fita harkarta daidai da gaisuwa bata had'ata da ita, ko abinci bata ce mata fito kici ta dinga nuna mata rashin kulawa, mahaifin kad'ai ke kulata ke kuma bata farin ciki. Khairat nada *shekara sha shida* ta fahimci abinda iyayenta keyi a kowane dare wanda kesa mahaifiyarta kuka, kowane dare da abin sauraro take saboda kar taji abinda ke faruwa a wajen iyayen nata, a hankali sai damuwa da kad'aici da kuma tsoro yayi tasiri sosai a rayuwar Khairat, hakan kuma ya janyo mata matsanancin ciwon qirki da kuma ciwon kai dake damunta duk lokacin da ta shiga b'acin rai ko damuwa, bayan Mani ya fahimci hakan saiya kaita asibiti anan aka d'orata akan magunguna, amma matsalar ba daga ita bace daga garesu ne, ganin abin ba sauk'i yasa Mani ya mayar da ita india wajen mahaifiyar Na'ima, komawarta can kuma yafi mata kwanciyar hankali da jin dad'i, gata da lele ta sake samu acan saboda ita d'in ta zama 'yar gudaliya a wajen kakar tata, sannu sannu sai Khairat ta fara zama mai tsauri da rashin kunya kuma marar qaunar talakawa mai wulak'anci gana k'asa da ita, taci gaba da karatunta acan kuma ta shiga gidan koyan rawa wanda hakan baima Na'ima dad'i ba ,amma tunda tace ta daina shiga harkarta yasa bata mata magana ba, a kwana a tashi saiga Khairat har akan je da ita wajen concert ko wani competition na rawa kuma ta zama zak'ak'urar 'yar rawa da shugabansu ke ji da ita, soyayyar data fara da wani yaro abokin rawarta mai sunan *Rajveer* yasa hankalin Na'ima ya tashi lokacin da ta zo ganin mahaifiyarta, ganin basu da shamaki sukan tab'a juna ba tare da jin wani abu ba yasa bata tafi ba sai tare da ita, duk da ita bata so ba amma haka suka tafi, yayin da Raj yaji mahaifiyar bata gyara masa ba danshi yana sonta sosai. *Shekara d'aya* da dawowarta kuma Mani ya mallaka mata wannan compagnie nashi a matsayin kyautar anniversaire d'inta na cika shekara ashirin da biyar, a lokacin ne kuma ta fara aiki a ma'aikatar, duka duka sati uku kenan da fara aikinta, amma gashi *Umar Faruk ya b'ata mata rai.* *Luv you guy's*😍 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ *BILQEES* WANNAN PAGE TAKI CE, KE KIKA FARA COMMENT. 5⃣ *CI GABAN LABARI* A hankali ta farka daga baccinta, saida ta tashi zaune tayi hamma sannan ta d'auki wayarta ta duba agogo, 10:40 tashi tayi ta fito sai dai bata sauko ba daga sama ta dinga hangen falon harta hango d'aya daga cikin mai aikinsu, daga saman ta kwallo mata kira "Biba." "Na'am Hajia." ta fad'a cikin ladabi tare da zubewa qasa. Juyawa tayi kawai ta koma d'akinta ta zauna saman gado tana wasa da kitson kanta, Biba ce ta shigo ta durk'usa tace "gani Hajia." Kanta qasa tace "ki had'a min ruwan wanka." "To." tace ta nufi bayin. Saida ta gama had'a mata da duk wasu turaruka da take aiki dasu sannan ta fito ita kuma ta shiga, saida ta d'auki awa d'aya sannan ta fito daga bayin, d'aya mai aikin ta samu wacce take tayata shiryawa, kamar yanda suka saba yanzu ma hakane ya faru, da taimakonta ta shirya cikin riga da siket na shadda wanda suka kama jikinta sosai suka fito da k'irarta, d'an k'aramin gyale ta d'auka sai dai a d'aya kafad'a kawai ta d'orashi tare da rik'e jaka a hannu da wayarta sannan ta fita, a falo ta samu duka iyayen nata a tsaye da alama magana suke, wucewa tayi ba tare data kallesuba tace "da alama kun tashi lafiya." Bata jira amsarsu ba tayi gaba, Mamie ce tace "Khairat abincinki fa?" Bata ji ba bare ta amsa saboda ta rigayi da tayi nisa, motarta ta shiga k'irar RENGE ROVER ta nufi ma'aikatarsu da tunanin had'uwarta da Umar faruk. Ai kuwa kamar yanda ta saba da shan k'amshinta ta shigo wajen, a gadarance take kallon kowa har saida idonta ya sauka akan Faruk, murmushi ta farayi tana takowa wajenshi har saida ta tsaya gabanshi, jin tattausan k'amshin turare a bayanshi yasa ya juyo a hankali, da sauri ya mik'e tsaye gabanshi na fad'uwa dan baisan me zai biyo baya ba, dama ya zone saboda umarnin mahaifinshi, cikin rainin wayo tasa yatsarta ta shafi sajen fuskarshi tana fad'in "Umar Faruk ko?" "Sannu jarumi, sai dai kuma nayi mamakin ganinka anan, na d'auka ai ka daina aiki, amma kuma saina ganka nan, meya faru?" Bata bari yayi magana ta kama mab'ullin rigarshi ta fara b'alle masa tana fad'in "karka d'auka ka mareni ka ci bulus kenan, ka kula da kanka dan babu abinda zai hanani *d'aukar fansata* a kanka ba, kayi abinda ko iyayena ba suyi ba, da wannan nayi alk'awarin cin mutuncinka ko ta wace irin hanya, ina fata ka fahimta?" Wasa wasa ashe ta cire duka mab'allan rigarshi, saida ta wuce bureau d'inta sannan ya fahimci hakan, maida mab'allanshi ya farayi yana kallon mutanen dake kallonshi, saida kowa ya fara aikinshi ya sulale ya nufi bureau d'in nata, Habiba ce ta shigo tace yana son ganinta amma tace ta fad'a masa bata son ganin kowa, rok'on alfarma yayi akan ta barshi ya shiga, a gadarance tace ta barshi ya shigo, shigowa yayi yana kallon fuskarta har ya tsaya gabanta, saida ta kallesa rai b'ace tace "kayi kuskure, kafin ka bar nan wajen zan saka wani aiki." Kud'i ta fito dashi 'yan goma goma guda uku ta bashi tace "karb'i wannan, kaje ka samu masinger ka tambayeshi komai akan abinda yake siyo min, saika siyo min dan banyi kari ba." Wani kallo ya mata yana lumshe ido d'aya kamar zai sake bigeta amma saiya dake ya juya ya fita, haka yaje ya samu masinger ya tambayeshi, tsaf ya fad'a masa komai sannan ya hau mashin d'inshi ya tafi. Cikin awa d'aya ya dawo, har bureau ya kawo mata ya aje, kallonshi tayi cike da mugunta tace "kaga plateau ( plate)can d'auko ka saka min." Kallonta yayi amma babu yanda ya isa sai d'aukowa ya zo ya zuba mata, tura mata plate d'in tayi tasa hannu ta fara ci ya fito da kud'i ya aje gabanta tare da cewa "canjinki." Fuska a had'e tace "aini bana karb'ar canji, ka rik'e wanjenka nasan zasu maka anfani." Ganin kamar ba zai d'auka ba yasa ta kalleshi tace "ba kaji mena ce ba?" Dauka yayi ya rik'e a hannunshi sannan yace "dan Allah kiyi hak'uri akan abinda ya faru, wallahi kuskure ne insha Allah ba zan sake maimaita kamarsa ba." Saida ya gama ta kalleshi tace "ka d'auko min ruwa masu sanyi a fridge." Yanda yayi tsaye baida niyyar yin abinda tace yasa ta jingina da kujerarta ta lumshe ido, idonta ya kalla wanda sukasha mascara sai sukayi kamar fossile, fridge d'in ya nufa yana fad'i a ransa "kyawunta hallinta babu kyan hali, ina ma zaki gyara d'abi'unki da kin more kyawunki duniya da lahira." Daukowa yayi ya aje mata, cikin marairaicewa ya sake cewa "dan Allah kiyi hak'uri, wallahi idan na rasa aikin nan mahaifina zai iya yin hushi dani, ki taimaka min dan Allah kar....." Katseshi tayi da fad'in "ka kira min manager." Kallonta yayi ya kalli telephone d'in dake kusanta wanda anfaninshi kenan kiran wanda take so, juyawa yayi rai b'ace ya fita ya kira mata manager, tare suka shigo sukayi tsaye suna kallonta, ji yake kamar ya gaggabjeta da wasu marikan yanzu haka, kallon manager tayi tace "ka turo min takardar sallamarsa zansa hannu a kai da kaina." Manager kallonta yayi ya kalli Faruk babu damar da zai bada hak'uri, cewa yayi "to Hajia." Zai juya Faruk ya rik'e rigarsa yana kallonta yace "dan Allah kiyi hak'uri wallahi ba zan sake ba, da aikin nan na dogara, dan Allah karki koreni wallahi zanyi duk abinda kike so." Wani murmushi ta saki ta kalleshi tace "ka tabbata za kayi komai?" "Wallahi zanyi in dai ba zaki koreni ba." Lotus ta d'auka ta goge hannunta ta jingina bayanta a kujera tana juyata tace "to ka durk'usa ka ban hak'uri, ni kuma saina yafe maka." Shiru yayi yana tunanin abinda zaiyi, amma tuna hukuncin da Baba ke shirin d'auka a kanshi yasa yayi kasa da kanshi, a hankali ya sulale gwiwoyinshi ya zube qasa kamar yanda take so, kasa had'a ido yayi da ita saboda tafasar da zuciyarshi keyi, abune da bai tab'a faruwa dashi ba sai yau, haka kawai yaji hawaye na fitowa a idonshi dan Baba ko Mama ce kad'ai idan suka masa fad'a bada hakk'inshi ba yake sashi zubar da hawaye, ganin ya kasa furta komai yasa ta mik'e tsaye da wayarta a hannu tace "tunda ka zama kurma ni zan fita waje." K'ofa ta nufa tana shirin bud'ewa yace "kiyi hak'uri." Tsayawa tayi ta dawo ta zauna tana kallonshi tana murmushi, cike da raini tace "tashi, kaje gida ka kwanta ka huta, ba zan hak'ura cikin sauk'i haka ba." Tsaye ya mik'e ba tare daya bari sun had'a ido ba ya juya ya fita,manager ma zai fita tace "zan turo maka da adreshin club d'in da zanje an jima, ka fad'a masa ya sameni acan." "To Hajia." Yana fita tayi dariya tace "zaka gane kuranka, zan had'aka da macho tamin maganinka." Misalin *14:00* tayi parking a wata restaurant mai sunan *Amandine* dan taci abinci kafin ta wuce gida, saida taci ta k'oshi kafin ta mik'e zata fita, juyowar da za tayi sukayi karo da juna ita da wani had'add'en matashi, ware manyan idonta tayi ta kalleshi kafin ta fara k'ok'arin wuceshi, saurayin kam da yayi mutuwar tsaye saboda ganinta saurin rik'e hannunta yayi, a fusace ta fizge hannunta ta kalleshi tace "akan me zaka tab'ani?" Saida ya kalli tsayayyan qirjinta ya lashe leb'e sannan yace "yi hak'uri, ban tambayi izini ba kafin na tab'a." "Mtsssss." taja dogon tsaki ta wuceshi, biyo bayanta yayi yana kallon k'ugunta ya kasa magana, bud'a motarta tayi ta aje jakarta da wayarta sannan ta shiga ta tayar, zata fara tafiya ya tari gabanta yace "ko zamu iya yin magana?" "Babu lokaci." ta fad'a tana sake taka motarta, rik'e k'ugu yayi yace "in baki bani dama ba, to sai dai mu kwana anan." Murmushin gefen labb'a ta masa tace "sai dai ka kwana asibiti." Tana fad'a ta tako motar ta nufo kanshi gadan gadan, ganin da gaske take yasa yayi saurin kaucewa sai dai ina saida motar ta bugi gwiwarshi, rik'e gwiwar yayi yace "kuttt, wannan fa yar akuya ce ta gaske." yaji zafi sosai dan da qyar ya taka qafar ya koma cikin restaurant d'in yana tunanin sanin ko wacece ita da kuma k'arasa abinda yayi niyyar yi a kanta. Yana zaunawa akan kujera abokinshi wanda shigowarshi kenan a wajen kamar yanda sukayi akan su had'u anan, ko zaune baiyi ba yace "kai wa naganka da ita yanzu?" Wata uwar harara ya wurga masa yace "wace tambayar iskanci ce kuma, daga zuwa ko zama ba kayi ba sai tambaya akan wata cika, wallahi tafi mu shed'anci wannan daka gani." Zaune yayi yana kallonshi da mamaki yace "ba saika fad'a ba nasan da haka, ina so nasan meya had'aka da Khairat?" Shima da mamaki ya kalleshi yace "ka santa ne, dan Allah fad'a min gidansu, wallahi saina tarfa yarinyar nan, kasan meta min kuwa?" Tab'e baki yayi yace "koma meta maka in dai Khairat ce ta wuce haka, danta wuce duk in da kake tunaninta, ka ganni nan ko gaisuwa bata tab'a had'ani da ita ba, kuma unguwarmu d'aya da ita." "Kai dan Allah, kenan itama a *Présidentielle* take? kenan kace babbar yarinya ce?" "Sosai ma kam, kaga muyi abinda ya kawo mu." "Kai, nifa wallahi yarinyar nan ta shiga raina kuma ni gaskiya." "Gaskiya me? kai hin wallahi fita idona in rufe, karka ja mana abinda yafi k'arfinmu , karka d'auka mu yayan manyan mutane ne, to ubanta wallahi ya take ubanninmu ya jikesu ya shanye, domin kuwa d'iyar *Mani Bukar* ce." Ido ya fiddo yace "ashe abun babba ne, ah dole tayi rashin mutunci saboda sune gwamnati." D'ora mashi yayi da "kuma ga kud'i an tara mata." Da haka suka rufe shafin maganar suka fad'a abinda ya kawosu , ita kuma tana kaiwa k'ofar gida ta tsaya saboda wani dattijo daya taho kanta da dugu gudu yana mata sannu da zuwa, kashe motar tayi ta fito a kasalance tana wani yak'una fuska, duk gaisuwar da tsohon keyi babu wacce ta amsa saida yayi shiru tace "lafiya ko?" Cikin muryar kuka ya fara magana "Hajia dama 'yata ce ke asibiti babu lafiya, mun kaita an rubuta mana magani, sai dai bamu da halin siyan maganin, shi yasa na zo ki taimaka mana kamar yanda Allah ya taimakeki." Takardar dake hannunshi tasa hannu ta amsa ta bud'a, saida ta d'auki kusan 2 minute sannan ta kalleshi tace "Baba, me yasa kuka yiwa yarinya aure da qananan shekaru? yanzu gashi kun jefa rayuwarta a matsala, ina mijinta yanzu?" Cikin kuka dattijon yace "ai tunda ta kamu da ciwon yoyon fitsari mijin ya saketa." Ajiyar zuciya ta sauke ta mika masa takardar ta bud'a motarta ta d'auko jakarta ta fito da kudi, mika masa tayi tace "na duba kudin maganin, jikka talatin da shida da rabi ne, nan kuma jikka hamsin ne, kaje ka siyi maganin sauran kuyi wani abun dasu, idan kuma wani abun ya taso kayi gaggawar zuwa ka sanar dani." Tana gama fad'a ta shige motar mai gadi ya bud'e mata ta shige ciki, godiya sosai dattijon keyi mata yana hawaye tare da saka mata albarka, wani abu daya k'ara birgeshi shine, wannan shine karo na biyu daya zo neman taimako kuma ta taimaka masa. _Duk da Khairat bata da halin qwarai, amma akwai wani babban arzik'i da Allah yayi mata, shine *taimako*, duk wanda Allah ya bawa zuciyar taimako to hak'ik'a yayi dace, dan ko baya da abun bayarwa zaiyi iya qoqarin da zaiyi yaga ya kyautatama wani, wani kuma idan Allah bai bashi zuciyar taimako, sai kaga Allah ya wadatashi da abin duniya amma sai yaji baya iya cire ko sile ya taimaki wanda baya da, Allah ka wadata zuciyarmu._ Babu kowa a falon sai masu aiki a farfajiyar gida suka mata sannu da zuwa, kai tsaye d'akinta ta nufa ta cire kayan jikinta ta watsa ruwa ta saka kayan da tafi so, wayarta ta d'auka da abin sauraro ta laka a kunne sannan ta fito da silipas a qafarta, Mamie ta samu zaune a kujera tana kallo, zaune tayi kusanta tare da fad'in "sannu Mamie." "Yawwa sannu, yaushe kika shigo?" cewar Mamie cikin sakin fuska. Ita kam mamakin ganin sakin fuskar yasa ba tace komai ba, sake cewa tayi "kinci abinci kuwa?" "Naci abinci kafin na shigo." Janyo kanta Mamie tayi ta d'ora saman cinyarta ta fara shafar kanta, mamaki duk ya ishi Khairat dan rabon da haka ta faru harta manta, sun jima a haka kafin Mamie tace "ni kam Khairat wai sai yaushe zaki kawo mana sirikina ne?" Gyara kwanciyarta tayi ta fuskanci Mamie tace "Mamie, nifa har yanzu ban shirya aure ba saboda ban samu wanda ya dace dani ba." Cikin zolaya Mamie tace "haba gimbiyar Papa, yanzu duk samarin nan naki ace babu wanda ya dace dake? amma ai naga duk kyawawane masu aji da ilimi, ki duba kiga d'an uwanki fa Mujahhid, ga kuma *Muzaffar* ga *Ahmadi*, ace duk cikinsu babu wanda ya miki." Tashi tayi zaune tace "Mamie, Mujahhid bai dace dani ba, eh shi kyakyawane ajin farko amma idan na auresa zanyi irin rayuwar da ki keyi ce yanzu, Muzaffar kuma yana da wani hali da ban sonshi, yana da son mata da kuma qyamar talakawa, Ahmadi kuma gaskiya shi yana da babban familly ne masu yawa, ni kuma ba zan iya d'aukar kwaramniyar danginshi ba." Komawa tayi ta kwanta qafarta tana fad'in "kawai kici gaba da min addu'a na samu wanda ya dace, ni ban damu sai mai kyawu ba, ina son samun namijin da kallo d'aya zaka samu tabbacin lalle cikakken namiji ne shi." Mamie dai bata sake magana ba tana saurarenta tana biyar wak'ok'in da take saurare har bacci ya d'auketa, ci gaba tayi da shafar kanta bata gushe a wajen ba har saida la'asar tayi ta tashi sannan tace taje tayi sallah itama ta nufi nata d'akin dan yin sallah. Misalin *22: 30* ta fito cikin shirin tafiya club, kallonta Mamie tayi sosai tace "Khairat dan Allah ki zauna gida karki fita wurin nan bai dace ba." Cikin sakin fuska tace "karki damu Mamie, akwai wanda zamu had'u dashi ne, ba jimawa zanyi ba." Tana fad'a ta fita ta shiga motarta, tana d'aukar hanya su Musa suka bi bayanta cikin bak'ak'en kaya da rufaffiyar fuska ta yanda ba zata iya shaidasu ba, a hanya kuma ta turawa manager adresse d'in in da Umar zai sameta, sannan ta kira macho amma sai tace tuni tana wajen. _Allah ya kareki Khairat._ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ *Alhamdulillahi lazi ahyana ba'ada ma amatana wa illaihi-noushour.* _Addu'a tashi daga bacci._ 6⃣ Umar Faruk na k'ofar gida saman dakali yana chat yaga sak'on manager, zaune yayi daga kishingid'ar da yayi yana kallon sak'on, bud'ar bakinshi yayi yace "kodai akwai abinda yarinyar nan ke nufi danine, me yasa ba zamu had'u a wani wajen ba? Ganin babu wata mafita yasa ya shiga gida yayi wanka ya shirya cikin kayan da yafi ta'ammali dasu qanana, turarenshi ya d'auka *Gold* ya fesa bayan yayi anfani da *nivea men* sannan ya d'auki makullin mashin d'inshi ya fita, yayi doguwar tafiya kafin ya isa club d'in, yana sauka daga mashin d'in ya hangi motarta, tsaki yayi sannan ya nufi k'ofar masu tsaron k'ofar ne suka tareshi, ganin kallon da suke masa yasa kafin suyi magana yace "Khairat na ciki?" D'aya ne yace "kaine Umar Faruk?" "Eh nine." ya fad'a yana hararensu. Bud'a mashi hanya sukayi ya wuce, yana shiga yaji ranshi ya sake b'acewa, hayak'i da wari ne kala kala na kayan shaye shaye, ga masifaffen kid'in dake tashi duk da a wurinsu mai tab'a zuciya ne, yanda mata da maza ke cakud'e ya sake harzuk'ashi wasu tsirarane kawai baka kirasu amma da kayan dake jikinsu basu da maraba da tsirara, ga hasken wurin mai jane sai sauran fitilun dake bayar da haske mai kala kala, haka yake kutsawa yana shiga har ya tsaya cak saboda hango Khairat da yayi, tsakiyar fili take tana tik'ar rawa abinta tare da wani dogo kuma had'add'en guy, tabbas ta iya rawa sosai dan daga yanda take sarrafa jikinta zaka gane haka, shima matashin da alama ya iya rawar sosai, abun haushi shine yanda suka rik'e da juna suna tab'a jikinsu duk yanda suka so har wani cirata yake sama, ran Faruk kam k'ara b'acewa yayi daya kalli kayan jikinta, rigace a jikinta bak'a mai kyau da walk'iya amma mai siraren hannaye iya cinyoyinta, duk wutsilniyar da take har pant d'inta na ciki ake gani fari shima bai wuce cinyarta ba, balerine ne a k'afarta sai dogayen kitsonta data sakeshi yake kad'awa yanda yake so shima, kid'in da suke takawa ne ya zo qarshe dan haka suka k'arar da kid'in tare da rungume juna suna sauke numfashi, tapi aka musu da shewa sannan suka raba jikinsu dana juna, sakinshi tayi zata koma mazauninta ya fizgota ta sake komawa qirjinshi, kallon juna suke kamar daga sama ya kalli kwayar idonta yace " *ina sonki* Khairat." Yana fad'a ya kai bakinshi a nata ya sumbata, da sauri ta raba bakinsu tana kallonshi, amma saita kasa cewa komai ta nufi mazauninta, babbar kujerace a wajen ita kad'ai zaune, haushine ya nemi kashe Faruk dan haka kawai yaji ranshi ya matuk'ar b'acewa, jiki a sanyaye ya fara d'aga qafarsa zai nufi wajenta, cak ya sake tsayawa saboda wani sabon saurayin daya zauna kusa da Khairat suka rumgume juna, da alama babban yaro ne dan harda masu tsaronsa a bayanshi. K'ura masu ido yayi yana kallo cikin takaici yana ji kamar zuciyarshi zata fashe, a hankali ta raba jikinta da nashi, kallonta yayi yace "Khairat, me yasa baki so ina kusantoki?" Saida ta harareshi tace "to me yasa kai kuma saika kusanceni, mu zauna a haka mana." Cikin wata irin murya yace "Khairat ba kowa bane zai iya, in dai namiji lafiyayyene ya ganki dole yaso kasancewa dake, wallahi Khairat kasa bacci nake, kece ke zuwa min a cikin tunani na." Hannu ta d'aga masa tace "kaga Muzaffar, nifa saboda kaine yasa har yanzu na kasa tsayawa waje d'aya, kullum da club d'in da nake zuwa amma na rasa ta yaya kake sanin in da nake, me yasa kake takurawa rayuwata ne, dan Allah ka rabu dani bana sonka." Kasancewarshi mutum ne mai saurin fushi kawai saiya mik'e tsaye yace "ke baki isa ki wulak'antani ba wallahi, ina sonki Khairat kuma ko zaki mutu wallahi saina mallakeki koda kuwa bayan darenmu na farko zamu rabu dake." Tsaye tayi itama tace "oho, kenan burinka kawai daren farko, kaga ka nuna min kai jikina ne kawai a gabanka, to kaji wallahi yafi k'arfinka har abada ba zaka sameni ba." Baiyi magana ba sai wucewa da yayi da k'arfi har saida ya bangaje Umar tsabar hushi, binshi da tayi da kallo yasa ta sauke idonta akan Umar Faruk dake kallonta, da d'an yatsa ta masa alamar ya taho, takowa ya farayi sai dai d'uffff, wutar wajen ta d'auke, wayoyi wasu suka fara k'ok'arin kunna fitila kafin haka ta faru kuma, Musa ya toshe bakin Khairat ya d'auketa daga wajen. Kasancewar sun shirya abun hakan yasa babu wanda ko yaji faruwar wani abu, bayan 'yan mintuna wutar ta dawo amma babu Khairat a in da take, rik'e kugu Faruk yayi yace "dama danta raina min hankaline yasa tace na zo nan." K'wafa yayi tare da juyawa ya fita daga wajen, k'awarta kam tana can tana soyewarta bata san wainar da ake toyawa ba, tafiya yake akan mashin d'inshi yana tsaki yana sake hangota a jikin mazan da ba maharramanta ba, k'ok'ari yake ya share kawai amma ya kasa sai dawo masa take a kwakwalwa. Kallon motar dake gabanshi yayi ganin yanda take gudu, yana kallo har motar ta shiga wata kwana ta ratsi wata hanyar kamar zata bar gari, wucewa yayi shima amma abun mamaki saida ya sake juyawa ya kalli motar sai yaji gabanshi ya fad'i, tsayawa yayi yana kallon da motar tabi kawai kuma saiya tayar da mashin d'inshi yayi gaba abinshi. Tunda yaje gida ya shiga d'akinshi kasa samun nutsuwa yayi, haka kawai yake jin gabanshi yata fad'uwa ba kuma shine abinda yafi damunshi ba, shine yanda Khairat ta kasa barin tunaninshi, ganinta kawai yake a idonshi , kasa samun nutsuwa yayi sai gashi ya raya darenshi da tunani da k'ara jin tsanar Khairat da haushinta, ba kamar yanda ya saba rayashi da anbaton ubangijinshi ba. Wani gida suka kaita suka jefata saman k'aramin gadon dake ciki, tun a cikin mota suka d'aure mata baki da qafafu lokacin da zasu d'aure mata hannuwa saita fara kokawa dasu, hakan yasa ba tare da tausayi ba suka bank'are mata hannu har saida taji k'arar hannu kuma ta tabbatar ya karye, tana ganin sun jefata ta fara kallonsu cikin tsoro sai dai ba zata iya fahimtar kosu waye ba, so take tayi magana amma ina babu baki sai gunguni kawai kake ji, baya baya ta fara ja daga kwance saboda ganin d'ayan yana nufota yana zare zip d'in wandonshi, kuka ta fashe dashi mai tsanani tana ci gaba da ja baya kamar tafiyar tsutsa, kusan fad'uwa tayi hakan yasa Auwal dake bayanta ya turota da k'arfi ta dawo tsakiyar gadon, Musa na ganin haka ya k'arasa janyota ya haye sannan ya kallesu yace "ku bamu wuri ko, zan kiraku." Wucewa sukayi Bello na fad'in "saura kuma ka kwashe komai ka barmu." Suna fita ya kwance mata d'aurin qafafun ya bud'e qafarta da k'arfi yana shirin zare pant d'inta, k'ok'arin tashi tayi saiko ya kama gashinta ya fizgota , fashewa tayi da k'ara sai dai bata fito ba ma bare aji, cikin jin zafi tasa qafafunta ta fara harbinshi, shima cikin b'acin rai ya wanketa da mari ya kuma janyo kanta ya had'ashi da kan gado, tuni kanta ya fashe sai jini duk da haka bata sasuda ba tayi nasarar yakushinshi ta bayan hannu, saboda dogayen akaihu da tasa yasa har saida jini ya fito masa, ai kuwa sai yasa hannu da iya karfi da tsabar mugunta ya fizgo akaihun, wani ihu ta saki saboda azabar da taji, akaihunta uku ne suka fita tare da asalin akaihunta, shak'e mata wuya yayi ya sunkuya cikin kunne ya rad'a mata "zaki mutu a banza kuma ba zamu fasa abinda mukayi niyya ba." Yana fad'a ya janye pant d'inta daga jikinta, ware qafafunta yayi ya fara k'ok'arin shigarta, bille bille take tana kuka amma ina ko saurarenta baya yi, hanya yake nema amma abun ya gagara, ya d'auki lokaci yana so ya shiga amma shiru, ganin abun bana lafiya bane yasa ya sake buda qafafunta sosai har saida magangamar cinyarta tayi qara, da gaba d'aya karfinshi ya tusa kanshi ciki, duk da bakinta d'aure yake amma data fasa ihu saida sauran dake waje suka ji, ganin ya samu hanya saiya fara aiki tuburan. Saida ya nutsu sannan ya barta, yana fita d'aya ma ya shigo a haka suka dinga shigowa d'aya bayan d'aya har suka kammala, kuma duk wanda ya shigo cikinsu saiya nemi k'ofarshi da kanshi saboda matsewar da take, wannan itace hallitar Khairat, tun tana motsi harta daina gaba d'aya bata san meke faruwa ba, tsaye sukayi akanta suna kallonta Bello yace "wallahi ban d'auka budurwa bace da ban fara ba." Musa ne yace "kai dallah fita harkarta, ba dai mun gama ba, to ku tsaya ku gani." A hankali ya cire belt d'in k'ugunshi kafin suyi magana harya fara labta mata shi, tambayarshi suke me yasa amma bai iya ce musu komai ba, saida yaga ya mata ligaliga harta sauya kammani sannan ya maida belt d'inshi ya kallesu yace "ubanta da yake lalata 'ya'yan wasu aishi baya musu haka, kuma duk lokacin da za'a rama mugunta to ka rama fiye da wacce aka maka." _Wannan ba gaskiya bane, ba kuma koyarwar shari'a kenan ba, Allah ka shiryemu shirin addininmusulunci_ K'aramar rigarta data yagalgale cire rigar sukayi suka kwasheta a haka suka fita da ita, a mota suka sata bayan sunyi tafiya mai nisa suka tsaye, Musa da Auwal ne suka fito suka kamota, a gefen hanya suka jefar da a ita suka tafiyarsu. 😭😭😭😭😭😭😭 Kwance take kamar gawa babu alamun rai, a haka ta zauna bakin titin na tsawon lokaci, sallah asuba tasa mutanen dake wajen suka fita sukayi sallah, wani dattijo ne da gidanshi ke bakin kwalbati yazo tsallakawa da fitila a hannu yaga mutum kwance tsirara, tsorata yayi da farko amma saiya daure ya sake haskawa , gaba d'aya yaga mutum duk da kalarta harta fara sauyawa , nan ya fara kwaroroto yana d'aga murya har mutane cikin gida da waje suka hallara. Nan fa suka fara shawarar yanda za ayi, wani matashi ne mai zafin nama ya k'arasa wajenta, rigarshi ya cire ya rufe mata k'asanta zuwa k'irji, kallon mutanen yayi yace "dan Allah ku samo abin hawa mu kaita asibiti." Basu b'ata lokaci ba suka suka samu mota aka saita suka nufi asibiti da ita koda ta mutu ma sai a nemi danginta. 😭😭😭😭😭😭My Khairat. 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 7⃣ Ganin halin da take ciki yasa likotoci suka amsheta tare da umarta da sukai report a wajen police, matashin nan ne ya tafi dan cika umarnin, baisha wahala ba ya samo takardar izini a dubata, yana kawowa likitoci suka duk'ufa kanta, tun matashin nan na kai da kawowa harya fara zaune yana jiran fitowar likotocin, mutanen da suka taho tare ma jira suke tare da jimami, ana haka wata docteur ta fito tana tambayar wanda suka kawota, a sukwane suka rufeta suna fad'in sune, a nitse tace "kune 'yan uwanta?" Matashin ne yayi karaf yace "a'a, muma tsitarta mukayi, ina fatan dai lafiya ko?" Wani kallo ta masa tace "kai baka ga yanda kuka kawota bane har kake maganar lafiya, muna buk'atar dan ginta dan akwai aiki da za'a mata ana buk'atar saka hannunsu." A raunane yace "gaskiya bamu san kowa nata ba, amma in ba damuwa mu saimu saka hannun." A wulak'ance ta kalleshi tace "ok ina zuwa." Juyowa matashin yayi yace "dan Allah iyayena kuyi hak'uri, ina so ku bani had'in kai mu taimakawa baiwar Allah nan." Wani dattijo ne yace "ba komai yaro, muma fa iyayene, fatanmu dai Allah ya bata lafiya." Fitowar docteur d'in tasa suka maida hankalinsu a kanta, matashin ta kalla tace "ka biyoni tare da wani dattijo d'aya a cikinku sai kusa hannun." Binta sukayi ta kuma nuna musu suka saka hannu, saida suka tashi zasu fita matashin yace "dan Allah wane irin aikine za'a mata?" "Kai baka san aikin da za'a mata ba kasa hannu, saboda ba yar uwarka bace kenan?" Kai ya girgiza yace "ba haka bane, kawai dai muna so ne mu taimaketa." Tsaye ta mik'e ta wuce tana fad'in "d'inki za'a mata saboda tana zubar da jini dayawa." A haka suka kasance har rana ta take sosai amma ba wani labari, ganin haka yasa dattijawa biyu suka bar wajen ya rage sai su uku a wurin. *Tun daren jiya* Mamie ta kasa bacci saboda ganin k'arfe d'aya tayi, a al'adar Khairat kuma bata kai wannan lokacin, kai kawo ta dinga yi a tsakiyar falo ita kad'ai duk hankalinta a tashe, *03: 17* Papa ya bud'o k'ofar d'akin ya shigo a halin daya fi shigowa, tsaye tayi tana kallonshi harya k'araso ya zube saman kujera yana maganganun dashi kanshi baisan me yake fad'a ba, durk'ushe tayi gabanshi cikin kuka tace "Alhaji, Khairat fa bata dawo gidan nan ba har yanzu, dan Allah kayi wani abu kar komai ya samu 'yata, dan in haka ta faru wallahi ba zan yafe maka ba." Wani fizgo hannu ya fara a cikin muryarshi ta maye yana fad'in "to saime idan bata dawo ba, ita d'in yarinya ce? ki barta tayi sha'aninta taji dad'in rayuwarta, ke kad'ai ce a duniyar nan baki waye ba ai." Cike da damuwa ta sake cewa "dan Allah Alhaji ka taimaka ka dubo min ita ko kasa a dubota, wallahi nasan Khairat ba zata jima haka kawai ba a waje saida dalili, jikina yana bani kamar akwai wani abu dake shirin faruwa, wallahi hankalina ya kasa kwantawa gabana fad'uwa yake." Abin takaici ashe duk maganar da take yayi bacci, dole ta gyara zamanta a k'asa tana ci gaba da kiran wayar Khairat gashi tana kururuwa amma ba'a d'auka ba, haka ta kasa rintsawa har gari ya waye lokacin kuma Papa ya farka a cikin hayyacinshi, a lokacin data fad'a masa halin da ake ciki hankalinshi ya tashi sosai kuma harya fara mata fad'a wai bata fad'a masa ba, nan ta fad'a masa halin daya shigo da abinda suka tattauna kafin bacci ya d'aukeshi. Aifa hankaline ya tashi dama na Mamie tuni a tashe yake, a lokacin kuma su Musa sunzo wajen aikinsu cikin kaki, nanfa ya sasu nemo mashi Khairat duk in da take, saboda su sun san komai kawai sai suka fara tafiya gidan rawar suna binciken k'arya, anan kuma suka samu wayarta , haka a wajen da suka jefar da ita suka tsaya suna tambayan mutanen wajen ko basu ga wani bak'on al'amari ba, saboda ganinsu da kayan soja yasa aka fad'a musu abinda ya faru, nan fa suka dawo gida da qarfin gwiwa sun samu labarinta, Papa da Mamie basu zauna ba suka rankaya zuwa asibitin, kai tsaye asibitin *Clinic Poudrière* anan suka samu mutanen da suka kawo Khairat asibitin, matashin ne ya fad'a musu halin da suka kawota, cikin fitar hayyaci Papa ya shak'i wuyan matashin yana fad'in, "Wallahi baku isa ba sai kun fad'a min abinda kukawa 'yata, ka fad'a min me kuka mata?" Matashin kam zare ido ya fara yi baisan me zaice ba, suna haka likitoci biyu maza da d'aya mace suka fito daga d'akin da Khairat take, da sauri suka nufi wajensu banda Mamie data zube wajen kamar gawa sai hawaye kawai dake zuba a idonta, "likita meya faru da yarinyata?" A tsanake likitocin suka kalleshi kafin babban docteur d'in yace "kaine mahaifinta?" "Eh nine, dan Allah ka fad'a min meya faru da ita?" "Ok to, yallab'ai ka biyoni ciki saina maka bayani." Kamar zai tashi sama haka ya bishi har kamar zai shiga gabanshi, sun d'auki 'yan mintuna da shiga Mamie ta dawo hankalinta ta tashi tabi bayansu dan taji abinda za'a fad'a, da isarta yayi daidai da bayan kwantar da hankalin da likitan yayiwa Papa ya kalleshi yace "kayi hak'uri yallabai, fyad'e akawa 'yarka." Mamie na jin haka ta k'arasa fad'uwa a gurin somammiya, Papa kuma wani kuka ya saki kamar yaro yana kiran "a'a, a'a, ba dai akan 'yata, me yasa ba za'a rama a kaina ba, na shiga uku na lalace." Likitan ne yace "yallab'ai ka saurareni kaji." Kallonshi yayi yana goge hawaye da babbar rigarshi yace "ina jinka." A hankali kuma a nutse likitan ya fara magana "'yarka tana cikin wani hali da take buk'atar kulawa, bawai fyad'en ne ba abun tashin hankali, yawan mutanen da suka mata fyad'en sune abun dubawa, duk da mun rasa wasu hujjoji saboda ba'a kawata da wuri ba a asibiti, amma dai munyi k'ok'arin gano wasu abubuwan, mun bata duk wata kulawar da take buk'ata a yanzu tare da taimakon wanda suka kawota, mun mata gwaje gwaje na cutuka da akan iya d'auka ta hanyar saduwa, kuma alhamdulillah a yanzu dai babu wani abu mai yiyuwa ko nan gaba, sai kuma akwai raunika da dama da aka ji mata mai yiwuwa tayi fad'a da mutanen sosai, dan mun samu karaya a hannunta da tsakanin cinyarta da k'ugunta, sai kuma gocewa a yatsunta biyu da kuma wasu raunika da suke nuna dukanta akayi, akwai ciwo a kanta daya ja mata matsala sai dai munyi k'ok'arin shawo kanta, badan ciwon a cikin gashinta yake ba da iska ya shiga akwai yiyuwar ta kamu da ciwon mantau. "Ciwon daya bamu wahala, shine ciwon da suka ji mata a gabanta, 'yarka tana d'aya daga cikin irin matan nan masu tsukakken gaba, wasu daga ciki zaka ga ko haihuwa basa iya yi da kansu sai an masu aiki, wasu kuma ba zasu haihu da farko ba amma sai kaga cikin ikon Allah sun haihu a gaba da kansu, gaskiya 'yarka bana jin tana daga cikin masu samun damar haihuwa da kansu ko a gaba in ba wani iko na ubangiji ba, ko mijinta ne na aure zai shigeta dole saiya had'a da dabaru, amma kasancewar sun mata ta k'arfi hakan yasa sun b'arkata sosai, idan kaga gabanta kafin a mata aiki zaka d'auka *anus* d'inta da *vessie* (gabanta da duburarta) a had'e suke, amma cikin ikon Allah mun di'nketa sosai d'inki kuma ba adadi, sai kuma jini da muka d'auka a lab muka saka mata dan tana buk'atarshi." "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un." abinda Papa ya dinga maimaitawa kenan, hawaye taf da ido ya dag'o yace "kana ganin zata rayu ma? danni na cire rai da ita." "Haba yallab'ai, ya zaka cire rai da rahamar ubangiji? ai insha Allah babu abinda zai sameta, zata tashi in Allah ya yarda ma." Sake kallonshi yayi yace "to ya take yanzu?" Cikin i'ina yace "eh...to, yanzu dai..tana kwance...insha Allahu,zata farka , amma dai har yanzu a some take bata san in da kanta yake ba, kawai muna gane tana raye da ta hanyar na'urar dake nuna mana numfashinta." "Yanzu miye abunyi?" "Eh yanzu kam babu wani abu, akwai magungunan da za'a d'orata ne kawai idan aka siyo, sai kuma kud'in duka aikin da aka mata, gashi nan a rubuce." ya fad'a tare da mik'a masa takardar. A sanyaye ya amshi takardar ya mik'e ya fara takawa, yana bud'e k'ofar yaci karo da Mamie kwance a wajen, da sauri ya zube yana jijjigata yana kiran "Na'ima, Na'ima, dan Allah ki tashi, meya faru dake?" Likitane ya k'araso ya kiran likita mace suka kamata aka shiga da ita emergency dan bata taimakon gaggawa, Papa ji yake shima kamar zai fad'i amma da taimakon su Musa ya samu ya zauna numfashinshi na fita d'aya d'aya, saida suka d'auki kusan awa d'aya sannan likitan ya tsaya gaban Papa, ganin halin da yake ciki yasa yace masa "ka kwantar da hankalinka yallab'ai, Hajia na samun sauki, zata farfad'o nan da zuwa yamma." Cikin kuka yace "dan Allah zan iya ganinsu?" "Eh to, sai dai Hajiar amma banda 'yarka." Sake sunkuyar da kai yayi yana ci gaba da zubar hawaye, wucewa likitan yayi shi kuma ya bawa su Musa takardar maganin yace su duba mota akwai kud'i su siyo, saida suka tafi ya nufi wajen mutanen da suka kawo Khairat asibiti ya basu hannu yana musu godiya, wani dattijo ne yace, "Ba komai yallab'ai, ai yiwa kaine, Allah dai ya bata lafiya." Idon nan jawur ya kalleshi yace "ameen na gode, amma dan Allah kun shaidani?" Murmushi sukayi d'aya yace "yallab'ai waye bai sanka ba, ai mun shaidaka tun shigowarka." Duk da baiji dad'i ba amma haka yace "to dan Allah wata alfarma nake nema a wajenku? ina so dan Allah abin nan daya faru akan yata ya zama sirri tsakanina daku, idan maganar nan ta fita wallahi zamu shiga uku, ko yarfen siyasa saiya addabemu bare kuma jama'ar gari." Had'e hannaye yayi alamar rok'o ya sake cewa "dan Allah, ku rufa mana asiri, kar maganar nan ta fita waje, wallahi za'a mana dariya ne ana fad'in munanan kalmomi a kanmu." Matashin saurayin nan ne yace "yallab'ai karka damu, wallahi babu wanda zaiji maganar nan, insha Allah zamu rik'e wannan sirrin tunda ba wani abun fad'a bane, duba da zamanin da muke ciki, idan bai faru akan k'anwarka ko yayarka ba, to zai iya faruwa da wata shak'ik'iyarka." "Na gode sosai, Allah ya saka muku da alkairinsa, Allah ya taimakeku kamar yanda kuka taimakeni." Haka suka bar wajen suna mata fatan samun lafiya, shi kuma ya zauna zuciyarshi na tafasa, sai dai a yau yana ji har abada ya daina neman mata da kuma shan giya, kanshi qasa a hankali ya furta "in dai anyi duniya dan Manzon Allah S.A.W, to nabar giya da matan banza har abada, domin abinda nayi da yaran wasu yau gashi an ninka wannan abun akan yata, ban tab'a ma 'yar kowa fyad'e ba tunda nake, kowace mace na kusanta to da son ranta ne na kuma biyata, amma yau sai gashi namiji fiye da d'aya ya kusanci 'yata da k'arfi, wannan cin zarafi yayi yawa, Allah ina rok'onka gafara abisa zunubaina, wannan tuba tubane na gaskiya, wallahi ba zan sake ba har duniya ta nad'e." Bayan su Musa sun kawo maganin da wasu allurai an kaiwa likitan, Papa kuma ya tara su Musa yayi tsaye gabansu yace "ku jini da kyau, ina so ku koma gidan rawar nan ku bincika min komai daya faru a wajen, ina so ku zage damtse ku samo min wad'annan 'yan iskan da suka lalata min rayuwar ya, dan wallahi ba zasu ci banza ba dole na d'auki mataki a kansu, dan haka kuyi da jiki ku gaggauta kawo min su cikin kwana uku, ina so kafin Khairat ta dawo hayyacinta su fuskanci hukunci." D'orawa yayi da "kun fahimta?" Da k'arfi suka amsa da "Eh yallab'ai." "To ku motsa, ni ku barni da driver, yanzu wannan shine aikinku kuma yafi tsarona mahimanci." Anan ya basu umarni shi kuma ya shiga d'akin da Mamie take, k'ura mata ido yayi yana tunano rayuwar da sukayi, hakika yana k'aunar Na'ima fiye da yanda yake k'aunar kanshi, abubuwan da yake kawai sabone yasa kasa dainawa duk da bata so, amma yau kam yayi tuba na gaskiya, likitace ta shigo tana fad'in "sannan yallab'ai, ya mai jiki?" Kai ya girgiza yace "ku zaku fad'a min, dan har yanzu banga ta farka ba." Murmushi tayi tace "zata farka yallab'ai, saboda hawan jininta yasa aka mata allurar bacci, kuma gashi jininta ya hau, amma yanzu zan sake dubawa na gani." Sake awo ta mata sannan tace masa "mu gode Allah yallab'ai, jininta ya koma daidai, amma dole a guji abinda zai tayar mata da hankali idan ta farka." Shiru yayi dan yasan ba lallai taso ganinshi ba idan ta farka, dan kullum maganarta kar abinda yake ya shafi yarsa, kuma yanzu yasan da bai tab'a kusantar 'yar kowa ba ba abisa sadaki ba, to da duk rashin kunyar Khairat babu wanda ya isa ya mata irin wannan cin zarafin , dan haka ya tashi ya fita daga d'akin, a lokacin 'yan uwa na kusa dana nesa har sun fara samun labarin Khairat ba lafiya da Hajia Na'ima, zuwa bayan magrib yan uwa sun fara zuwa ganinsu, Mamie kad'ai suke gani su koma hakan yasa Papa ya shawarci likitan suka k'ara tsaurara tsaro akan Khairat. *Tun daga wannan rana*.... 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *Bismillahi walajna, wa bismillahi kharajna, wa 'allah lahi rabbina tawalkalna* _addu'ar shiga gida._ _Bismmilahir-rahman-rahim_ 8⃣ *India* tun jiya Mammie ke kiran shalelenta Khairat amma bata dagawa, bayan gari ya waye ta sake doka mata kira amma shiru, abinne ya dameta dan haka ta fara kiran Mamie, amma itama ba'a dauka saboda wayar na gida, ganin itama an kasa dauka yasa ta fara kiran Papa cikin b'acin rai, shi kuma tun daren jiya yasa wayar vibration saboda kar a takura masa, nan ma ba amsa dan haka Mammie take jin in har aka sake riskar gobe a haka to tabbas zata shigo gida niger. Wani jami'i ne aka tsayar dashi a kofar d'akin da Khairat take ba'a bari kowa ya ganta, kannan Papa da Mamie ne kad'ai suka ganta shima sau d'aya, tunda Mamie ta farka take kuka tana wa Papa Allah ya isa cikin fitar hayyaci, hakan yasa itama ta zama cikin tsaro tunda ya zama kamar suna fallasa sirrin gidansu ne, har yanzu Papa baije gida ba haka ma Mamie gaba d'aya basa cikin nutsuwarsu, hakan yasa kuma sai maganganu suka fara fita musamman daga wajen yan uwa wanda suka ga jikin Khairat d'in Nan suka fara fad'in kila wa kala ama dai suna gani kamar fyade aka mata, dama duk abinda aka ce ya fara da jitajita to dole a samu banbancin kalamai, a cikin *kwana uku* sai gashi manganu suna yaduwa akan amma Khairat fyade, duk da tsaro da kuma boye abinda ake amma bai hana maganar fita ba. Wasu kuma suna cewa ba wani fyade kawai dai dubunta ce ta cika watakila sun samu matsala da abokanan shekewarta ne kawai, to haka dai aka dinga yada wannan magana, kuma abu ga manyan mutane dan danan sai labari ya game gari, mutane nata tururuwar zuwa dan ganin kwam amma babu mai ganinta koda kuwa cousine d'inta ne, haka labari ya samu masana'antarta kuma suma sun zo ganinta sai Papa kawai suka ma jaje, amma manager Papa yace a barshi ya ganta saboda sun jima tare ya aminta dashi. *Duk badakalar nan* da ake Khairat bata san me ake ba, tana kwance da na'urori a jikinta kamar wacce ta shiga halin doguwar suma, ruwa da sassaukan abinci duk ta tiyo ake bata su, duniya kenan. *Umar Faruk* ma tun ranar bai sake zuwa masana'antar ba, sai dai ya shirya ya fita kamar ya tafi aikin saboda Babanshi amma kuma fafutukar samun wani aikin yake zuwa, dan ya riga daya cire rai da aiki a karkashin Khairat. Yau ta kama *lahadi* Faruk na kwance d'akinshi akan kafarshi Baba ya shigo, yana ganinshi ya mike zaune yana fad'in "sannu da zuwa Baba." Bai amsa mashi ba sai kallonshi da yake, tsarguwa yayi da kallon dan haka yace "Baba, da wata matsala ne?" "Eh, da matsala." Kallonshi yayi yace "subhanallah, meya faru Baba?" Gyara tsayuwarsa yayi yace "Faruk, yanzu har kiyayyar da kake ma yarinyar nan ta kai haka, da har zata kwanta rashin lafiya amma ka kasa fad'a mana ko dai mu mata addu'ar samun sauki?" Duk da bai fahimci Baban ba amma haka yace "kayi hak'uri Baba, wace yarinya kenan?" Dakuwa Baba ya masa yace "ban sani ba, har ni zaka tambaya wace yarinya? aiku ku kafi kowa labarin abinda ke faruwa tunda ku ke aiki a ma'aikatarta." Cikin mamaki yace "Baba wai, Khairat kake nufi? meya sameta to? ni bana da labari." Shima da mamaki ya kalleshi yace "Umar Faruk kamar ya baka da labari, kai yanzu kace baka san meke faruwa ba? bayan kullum kana fita." Ganin karya ballowa kansa wani liki kawai sai yace "a'a Baba, kasan da yake ina da aiki sosai shi yasa bana da lokacin wani shirme , amma wallahi bansan meya faru da ita ba." Juyawa Baba yayi zai fita yace "amma Baba me yake damunta?" "Humm, idan kaje bureau d'in gobe kaji meke faruwa." Yana fad'a ya bar d'akin shi kuma ya fad'a duniyar tunanin abinda ya samu Khairat, gashi dama har yanzu yana ganinta a idonshi a cikin wannan shigar, tsaki yayi kawai ya kwanta amma ya kasa komai sai tunanin wannan daren yake. *Safiya* nayi ya shirya kamar yanda ya saba ya fita sai dai yau ma'aikatar ya tafi dan jin meke faruwa, da sameshi ko sai yayi sa'ar ganin manager a farfajiyar wajen zai shiga mota da alama fita zaiyi, da sauri ya karasa suka gaisa kafin manager yace "Faruk ashe kana nan ka daina zuwa aiki?" Kai ya shafa yace "eh yallabai ina nan, nasan ko nazo ba zata barni ba shi yasa ma bana zuwa." "To yanzu meya kawoka?" Nan ma kai ya shafa yace "yallabai nazo ne naji meke faruwa anan? dan jiya Baba ya sameni yana fad'an wasu maganganu da ban gane ba." "Kamar me kenan?" Shiru ya d'anyi sai kuma ya kalli saman ginin yace "Hajiar tana ciki?" Da mamaki yace "Umar Faruk, kar dai kace min baka san meke faruwa ba? Hajia Khairat ai yau kwananta hud'u bata fitowa." Dammm , yaji gabanshi ya tsinke ya fad'i, saida ya had'e yawu yace "to meya sameta?" Ajiyar zuciya manager ya sauke yace "yanzu dai kaga ganinta ne zanje, idan zaka iya mutafi tare mana?" "Ganinta kuma, a ina?" "Asibiti." Ji yayi duk ba dad'i sai kawai yace "ba damuwa muje." Zagayawa yayi ya shiga motarshi suka d'auki hanya tare, amma ya rasa dalili sai yaji zuciyarshi na bugawa d k'arfi ga gabanshi dake ta fad'uwa babu gaira babu dalili, a haka suka isa asibitin jami'in dake tsaron k'ofar d'akin yana ganin manager ya kauce masa ya wuce amma saiya hana Faruk, manager ne yace "dan Allah abokina ka barshi ya wuce, dani dashi duk d'aya ne." Cewar jami'in "gaskiya ba zai wuce ba wannan doka ce, kayi hak'uri ka koma." Papa ne yaji maganarsu daga cikin d'akin dan haka ya lek'o duk da baiga ko suwaye ba amma kawai sai yace "barsu su shigo kawai." Da sallama suka shiga amma sallamar Faruk saita tsaya cak saboda ganin Khairat a wani hali na daban, cikin sanyin jiki da rauni ya k'arasa gaban gadonta ya tsaya yana kallon fuskarta dake d'aure da bandeji , Papa kuma d'akin kusa dana Khairat ya shiga in da Mamie take kwance, a hankali ya kalli manager yace "meya sameta haka, hatsari tayi?" Kai kawai ya girgiza masa, sake maida kallonshi yayi gareta yana k'ara jin tsoron ubangiji na shigarshi, wai wannan matashiyar mai tsiwa da girman kai da raina mutane yau gata kwance, ta sauya kamanni kamar ba ita ba duk kusan rabin jikinta bandeji ne sai jini, bin qafarta yayi da kallo wacce tayi sumtum da ita ta kunbura , kallon yatsun qafar yayi wanda suka sha akaihu da kalar pink, kallon fuskarta yayi idonta rufe gashin idonta duk ya kwanka luf kamar na kanti, wata har sharasharar rigace fara aka lak'aba mata. Suna haka wayar manager tayi k'ara dan haka ya fito da ita ganin mai kira yasa ya fita daga d'akin dan amsa wayar, kujerar dage gaban gadon Faruk ya zauna yana kallon k'afarta dake rataye da gado tasha k'arafa saboda dorin da aka mata haka ma hannu, sosai zuciyarshi ta karye saboda ganin halin da take ciki, sama sama ya fara jiyo murya daga d'aya d'akin ko ba'a fad'a masa ba yasan muryar iyayenta ne, tsaye ya tashi saboda ji da yayi muryoyin na sake sama kuma kamar zasu fito daga d'akin. Juyawa yayi da nufin barin d'akin kawai yaji har sun fito, muryar Mamie ce ta fara magana cikin tsananin kuka da fitar hayyaci ta nuna Khairat dake kwance tace "ka dubi yarinyar nan dake kwance waya ja mata shiga wannan halin? kaine duk kaine sila." "Ka sani wallahi jira kawai nake 'yata ta samu sauk'i mu raba kanmu da kai , dan in har zamu ci gaba da zama da kai , to ya zama dole sai mun shirya karb'ar bala'en da suka fi wannan, bansan me yasa nayi wannan kuskuren ba duk da na karanta cewa bai hallata ba zama da fasik'i ba, yau gashi abinda ka shuka yarka ta fara girbarshi, gashi gyaran kuskurenka zai zama alhakin 'yarka, to sam ba zan yarda ba wallahi, dole ka sakeni nayi nesa da kai da yata dan mu tsira da rayuwarmu da lafiyarmu." "Ka dubi k'ask'ancin da aka mata, nasan ko kai baka tab'a shigar da 'yar wani a wannan halin ba, amma yau gashi yarka mutum d'aya d'aya har guda hud'u ne suka keta mata haddi , yanzu haka ya maka daidai kenan? kaji dad'i?" Duk da kuka yake amma cikin dakakkiyar zuciya yace "Na'ima, wai me yasa kike da taurin kaine? me yasa baki da yafiya a rayuwarki? tunda abin nan ya faru nake baki hak'uri amma kinki hak'ura, na rantse miki da Allah Na'ima nayi nadama kuma na tuba ga Allah, wallahi ba zan sake aikata sab'o irin wanda nayi a baya ba, dan Allah Na'ima ki sake bani dama mu sake sabuwar rayuwa, muyi fatan ganin Khairat ta samu lafiya, ni kuma na miki alk'awarin saku farin ciki sannan zan samar ma Khairat miji na gari na had'ata dashi, kuma wallahi daga yanzu duk abinda ki kace nayi zanyi Na'ima amma banda rabuwa dani." Murmushi tayi tace "oho , kenan sai yanzu zaka fara maganar yi mata aure, kenan yanzu ne kake ganin Khairat ta isa aure? to kai a ganinka waye zai yarda ya aureta a yanzu bayan ta rasa kimarta , ai kowane namiji yana alfahari ace shiya fara sanin matar daya aura, wallahi Mani duk wanda kaga ya auri Khairat a yanzu to abu d'aya ne, shine dukiyarka, amma duk wanda ya auri Khairat dan Allah to ka sani wallahi taimakonta yayi kuma *JIHADI* yayi." Juyawa tayi ta zauna kusa da Khairat ta fara shafar kanta tana zubar da hawaye, shima Papa hawayen yake yi yana kallonsu, Umar Faruk kuma ya kasa motsawa saboda tunanin kamar basu lura dashi ba ma a wajen, baya baya ya fara ja yana so ya sulale daga wajen kawai yaji an bud'o k'ofar an shigo, ya dauka manager ne ashe Kakar Khairat ce ta zo daga India, maida kallonsu sukayi gareta da sauri duk suka tashi kowa na fad'i "Mammie, yaushe kika zo?" Hannu ta d'aga musu tana kallon Khairat dake kwance a tsananin mamaki, bata d'auke idonta akan Khairat ba tace "meya samu gimbiyata? me kuka mata?" Mamie ce ta fara kame kame tace "Mammie babu komai fa, ta samu wani d'an hatsari ne." Cikin d'aga murya tace "wane irin hatsari ne wannan? zaku fad'a min gaskiya ko saina tsine muku albarka." Da sauri Papa yace "a'a Mama, dan Allah kiyi hak'uri, wallahi..." Kuma sai yayi shiru, ganin Mammie ta kafe Mamie da ido yasa ta fara i'ina tana fad'in "Ma...ma wa...sune..suka , wasu ne....suka, suka mata fyad'e." ta k'arasa da fashewa da kuka. A nitse Mammie ta k'arasa gaban gadonta ta durk'usa tana shafa kanta tana zubar da hawaye, kuka suke sosai babu wanda yake bawa wani hak'uri a cikin wannan hali Umar Faruk ya sulale ya fita, a farfajiyar wajen ya samu manager yana waya , saida ya jira ya gama suka shiga mota suka wuce in banda tunanin halin daya ga Khairat da abinda yaji mahaifiyarta ta fad'a babu abinda yake, a haka har suka kai ma'aikatar manager yace kawai ya shigo yaci gaba da aikinshi kafin Allah ya bata lafiya. Nan ya shiga ya kuma zauna mazauninshi, abokinshi Ishaq da wasu ma'aikatan mata da maza ne suka taru suna tattauna abinda ya faru da Khairat d'in, d'aya daga ciki ne yace, "Koda dai har yanzu babu tabbas, amma duk mai hankali ai zaiyi zaton wani abu." "Gaskiya ne, wallahi abar tausayi, nasan tana cikin wani hali ne shi yasa ma ba'a bari a ganta." Wata matashiya ce tace "wacece abar tausayin? Khairat d'in, ni kuma wallahi ko kad'an banji tausayinta ba, dan nasan ba wani mummunan abu bane a wajenta." Faruk ne ya kalli matashiyar ya taso ya tsaya gabanta, duk da yana k'ok'arin tausar kanshi, amma haka kawai yaji zuciyarsa na masa zafi akan abinda suke fad'a, basu san da zuwanshi ba sai muryarshi suka ji yace "wannan maganar bata dace ace ta fito daga bakinki ba a matsayinki na mace, tausayi da jimami ya kamata a gani a tare dake, kamata yayi ace kinji cewar an tab'a kimarki kema saboda 'yar uwarki mace aka tab'a, ki tuna fa kema macece kuma bana miki fata, amma kema kina cikin wannan k'alubalen dan haka zata iya faruwa dake, dan Allah ku dinga kyautatawa juna zato." Tab'e baki tayi ta kau da kai tana fad'in " ni dai nasan ina zaune da kowa lafiya, kuma kamar yanda na fad'a a baya bana jin Khairat wani sabon abune ya sameta bare kuma taji zafinshi." Sake gyara tsayuwa yayi cikin b'acin rai da d'aga murya ya fara magana "bata jin zafi kike cewa? kinsan me fyad'e yake nufi? shin kin tona zuciyarta kinga me take ji? shin kin tab'a kwatanta me zaki ji a zuciyarki ace namijin da baki had'a komai dashi ba ya tursasaki ya kusanceki? kefa macece, ki misalta kona second goma kiji me zaki ji a zuciyarki." "Shin kinsan halin da take ciki? kin ganta da idonki bare kisan me take ji? kije, kije kiga halin da take ciki, kina gani nasan dole ki yarda tana cikin wani hali, kinsan zafin karaya a hannu bare kuma a qafa? shin kin tab'a yin hatsarin da yasa kika ji raunika? to ita a sanadiyar abinda ya faru tana can kamar wacce babbar motar ta bige, dan Allah ki sawa zuciyarki tausayi kodan kasantuwarki mace." Yana fad'a ya bar wajen ya fita farfajiya zuciyarshi in banda tafasa ba abinda take, ji yake kamar zai fashe da kuka amma kuma ya kasa, a hankali ya tambayi kanshi "wai me yasa ka damune? Khairat ce fa." Saida yasa hannu ya goge idonshi da yaji sun cika da k'walla sannan yace "rashin imanina bai kai na kasa tausaya mata ba." *Haka* Faruk ya kasance cikin wannan damuwa da tunani har yaje gida, haka ya dinga tunanin abinda idonshi suka gane mishi a ranar, kai da kawo yake a tsakiyar d'akinshi yana fad'in "rigarta, wannan saurayin, matashin da yazo daga baya, d'aukewar wuta, dawowar wuta bayan qanqanin lokaci, b'atan Khairat, sai kuma....sai...sai kuma me?" Ci gaba yake da kai da kawowa har saida ya tsaya cak baki bud'e ido waje, a hankali ya furta "wannan motar, wannan *CRV Honda* d'in, tabbas akwai alamun tambaya akan wannan motar, me yasa take gudu a cikin wannan daren, sannan ina suka nufa da suka ratsi wannan jejin?" "Dole nasan wani abu a game da motar nan, dole na koma wajen nan." Wata zuciyar ce kuma tace "to wai akan me? ka barsu da matsalarsu mana." "A'a, ka tuna fa kana k'annai mata dayawa, ya zaka ji idan d'aya daga cikinsu ce? koda namiji d'aya ne ba zaka ji dad'i b bare har hud'u saboda rashin imani, zanyi wannan taimakon a matsayin *jihadi* fisabilillah." _To Umar Faruk Allah ya bada sa'a._ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 💃💃💃💃💃💃💃 _Farin ciki auntynmu ta dawo, *ASMA'U GALADIMA* (ummu Maryam), marubuciyar *Dijah Qaya* ina miki barka da dawowa._ _Bismmilahir-rahman-rahim_ _Allahumma antas- salam, waminkas-salam, tabarakta ya zuljalali wal- ikram._ 9⃣ Har gaggawa yake gari ya waye, alwala yayi ya fara tsayuwar dare kamar yanda ya saba, ya jima yana sallah har aka kira asuba sannan ya nufi masallaci tare da sauran 'yan uwanshi, saida gari yayi haske suka dawo yana zuwa shiryawa yayi ya fita ko kari baiyi ba, kai tsaye asibiti ya nufa dan yana so ya d'an samu wata makama da zai iya dafawa a matsayin k'warin gwiwarshi. Sammakon da yayi yasa ya tarar da Papa a k'ofar d'akin da Khairat da Mamie suke tare dasu Musa bayan sun fad'a masa har yanzu basu samu wani abu ba, cikin b'acin rai da sassauta murya yace, "Wannan ai maganar banza ce, ba zai yiwu ba, ku dubi Khairat nan fa kwance har yanzu bata farka ba, me kuke so nace mata idan ta kalleni? to kuji wallahi ku shiga duk in da zaku shiga ku nemo min 'yan iskan nan, idan ba haka ba ranku ne zai b'ace, kunji na fad'a muku." Yana fad'a ya koma cikin d'akin su kuma suka jiyo Musa na fad'in "kaji d'an wahala, to ya zaiyi in bamu samosu ba? dole dai a qarshe ya hak'ura tunda ba mik'a k'anmu zamuyi ba muce mune muka mata fyad'en." Da sauri Faruk ya juya yana binsu da kallo matuk'ar tsoro ya bayyana a fuskarshi sosai, yana kallo har suka shiga motarsu CRV Honda, hannu yasa ya rufe bakinshi yana fad'in "inna lillahi wa'inna ilaihir-raju'un." Juyawa yayi ya koma ya hau mashin d'inshi dan baya da hujjar da zaice sune kai tsaye dole ya samu wata makama da zai nuna eh sune, saida ya koma har club d'in nan sannan ya fito ya d'auko hanyar, a hankali yake tafiya yana dube dube har saida ya kawo wajen da motarnan ta shiga kwana, nan yabi yana waige waige yana dubawa ko zaiga gida da makamantansu, wasa wasa dai bai samu komai ba har saida hanya ta b'illo dashi kusa da unguwar airport, ganin idan ya koma baya zai maida kansa baya ne kawai saiya shiga kwanar da zata sadashi da titi, zai hau titi kenan motar su Musa ta shigo kwanar suka nufi hanyar daya fito, da sauri ya taka birki ya juya yana kallonsu, bai b'ata lokaci ba yabi bayansu har suka tsaya k'ofar gidan da Papa ya basu duk lokacin da suke bakin aiki. Nesa da gidan ya tsaya da tunanin ko zasu fito, amma shiru shiru su Musa basu fito ba har suka kwashe awanni uku, tun yana gyara zama akan mashin d'in har ya kai gayin kwance a sama nan ma ya gaji ya sauka ya aza takalminshi ya zauna qasa. Su kuma suna ciki dama duk lokacin da Papa ya matsa musu lamba nan suke dawowa suyi kwancinsu su huta sannan su koma suce masa babu labari, _(rainin wayo)_, sai lokacin suka fito suka shiga motarsu sukayi gaba abinsu, anan ya bar mashin d'in ya nufi gidan, ganin k'ofar rufe take amma katangar gajera ce yasa ya tuna yarinta d'araf ya haye katangar ya haura gidan. 🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣 Ganin k'ofar falon itama a rufe take kawai yasa ya dinga bangazar k'ofar har saida ta bud'e da k'arfi, nan ya shiga d'akuna hud'u ne a ciki, kowane d'aki b'alle k'ofar yayi ya dinga bincikawa ko zaiga wani abu amma shiru, d'aki na qarshe daya shiga ganin bai samu komai ba yasa ranshi ya b'ace ya daki armoire (wradrob) d'in da k'arfi, abinka ga d'akin maza ba'a kimtsa komai, kayane suka zubo daga ciki. Durk'usawa yayi zai kwashe kawai yaga wata bak'ar mask ta fuska, d'auka yayi ya kalleta da kyau yana tunanin ko meye anfaninta, zai mayar da kayan saiya sake ganin wata, dan haka ya sake dubawa saiga guda hud'u ras sun bayyana, kai ya girgiza ya mayar da kayan har da mask d'in sannan ya rufe wradrob d'in fito ya daga d'akin, maida k'ofar falon yayi ya rufe duk da bata rufu ba. Har zai wuce kuma ya tsaya yana kallon poubelle (abun zuba shara) d'in wajen, cike da mamaki yasa hannu ya ciro rigar da koba a fad'a masa ba yasan ta Khairat ce dan itace a jikinta a ranar, duk rigar ta yage sosai ga jini a jikinta har da pant dinta da kuma takalminta duk a cikin sharar, ji yayi idonshi sun kawo ruwa amma saiya aje rigar ya da kayan ya fita ya bar wajen, gudu yake sosai akan mashin d'in har saida ya kai asibiti. Ya samu 'yan uwa dayawa a wajen wanda ba'a bari shiga ba, mai tsaron k'ofar Umar ya cewa "dan Allah ko zan iya ganin yallab'ai?" "Lafiya ko? yallab'ai yace kar a takura masa fa." "Kaga wallahi magana ce zamuyi mai mahimmanci, dan Allah ka barni na ganshi." "Ka fad'a min ko miye saina fad'a masa." cewar jami'in yana d'auke kai. "Maganar nan sirri ce, dan Allah kace ina son ganinshi." A hassale jami'in yace "kai, wai kai wane irin mutum ne? nace maka yace kar a takura masa ko, kai baka ga yan uwa ba duk gasu nan amma ba'a bari sun shiga ba sai kai, dallah ka b'ace min da gani." Ganin fa ba zai barshi ba yasa dole ya yanke shawarar fad'a masa, d'an sassauta murya yayi yace "kaga abokina, wata masaniya na samo akan mutanen da yallab'ai yake nema, dan Allah ka barni na ganshi kar lokaci ya qure mana." Ido ya zaro yace "kenan kasan mutanan da ake nema? to su waye, kuma me sukayi?" Kallon rainin wayo ya masa yace "kana nan kace baka san akan me ake nemansu ba?" Cike da son jin gulma yace "wallahi ban sani ba, ba'a yarda kowa yasan meke faruwa ba." Cike da k'osawa yace "yanzu zaka iya yimin magana dashi d'in ko kuwa na tafi?" "A'a jira ina zuwa." Yana fad'a ya shiga d'akin dan fad'a ma yallab'ai Papa, zaune ya samesu shiru dasu abin tausayi suna kallon Khairat, sunkuyawa yayi kusan kunnen Papa yace "yallab'ai wani saurayine a waje kesan ganinka, kuma yace akan maganar mutanen da ake nema ne." Kallonshi yayi da sauri yace "ka tabbata?" "Eh to, haka dai yace min." Tsaki yayi yace "yanzu haka d'an jarida ne yayi basaja ko kuma masu son sanin meke faruwa, kawai kace masa ina wani uzuri ba zanga kowa ba." Duk abinda ya fad'a a kunne Mamie dan haka bata ce k'ala ba ba ta mik'e zunbur ta fita daga d'akin, tsaye ta samu Umar Faruk yana jira, saida ta kalleshi da kyau tace "sannu bawan Allah, kaine kake son ganin Alhaji?" "Eh nine Mama." Cikin muryar tausayi tace "ka fad'a min wani abu da zaisa naji dad'i dan Allah." Ajiyar zuciya ya sauke tare da gyara tsyuwa yace "kiyi hak'uri Mama, bansan taya zaki fahimci abun ba, amma dai tabbas anci amanarku, wanda suka ketawa yarku haddi suna nan tare daku, hasali ma sune kuke sawa nemo muku masu laifin." A jujjuye ta fahimceshi dan haka tace "ban fahimceka ba yaro? ko zaka iya yimin dalla dalla?" "Mama ba zan iya fad'a muku komai ba, amma ku aika wasu jami'an na daban ba wanda kuke tare dasu ba, suje unguwar airport daga farkon shiga unguwar a gida mai number 8, suyi bincike da kyau karsu bar komai, ina tabbatar muku zaku samu hojojjin da suke nuna masu laifin anan suke." Tuni hawaye suka wanke fuskar Mamie tana kallon Umar Faruk tace "jirani ina zuwa kaji yarona." Tana fad'a ta juya ta shiga ciki da gudu, Umar Faruk na ganin haka shima yayi murmushi kawai ya juya bar wajen, tare da Papa Mamie ta fito amma basu ga Faruk ba, nan Papa ya ciro waya jiki na rawa yasa aka turo mashi wasu jami'an, dan danan asibiti ta cika da jami'an kama daga police soldier da gendarme, nan fa suka basu jawabin abinda Umar ya fad'a musu, ina Papa ma ba'a barshi ba saida ya bisu. Suna gaf da fita daga k'ofar asibitin motar su Musa tazo shigowa, nan suka tsaya suka fito suka sarama manyansu suma wasu suka sara musu, nan Papa yace su shiga mota su tafi an samu labarin in da mutanen nan suke, ganin yanda ya masu magana bai nuna wani abu ba yasa ransu yayi fari suna tunanin wasu ne aka lak'ama sharrin, amma tunda suka ga ana nufa unguwarsu gabansu ya fara fad'uwa, babu wanda baiji gudawa ba lokacin da aka tsaya k'ofar gidansu. Duk da unguwa ce da babu mutane sosai amma saida jama'a suka fito kallo ganin yanda jami'an suka cika unguwar, Papa na fitowa ya duba yaga kwatancen daidai ne kawai ya juya ya kalli su Musa da sukayi sukayi sharkaf da zufa, hannu Papa ya nuna musu yace "ku kama min su." Tuni aka cika aikin yallab'ai akayi ram dasu Musa aka d'aure su , gidan suka shiga nan fa suka fara shiga kusfa kusfa ana bincike, saboda Umar Faruk ya rage musu wahala hakan yasa suka samu hujjojin da Faruk ya gani har dama wanda shi bai gani ba kamar bras d'inta da d'an kunnai, haba su Musa ai tun daga nan suka fara shan duka. _Kuyi hak'uri jami'an mu, akwai fa zafin rai._ Kasancewarsu jami'an yasa ba'a tausaya musu ba, cikin k'ank'anin lokaci har sun canza kama wai wannan somin tab'i ne kafin su gurfana a gaban kotu, tuni labari ya karad'e gari akan abinda ya faru da Khairat da kuma kama masu laifin, duk mai zuciyar imani ya tausaya mata sosai ace har mutum hud'u. *02: 40* na dare Khairat ta farka da ihu tana fad'in a taimaketa zasu kasheta, Mamie da Mammie ne suka rik'eta sosai suna tofa mata addu'a harta nutsu, kuka take sosai tana d'aga murya kamar ranta zai fita, haka har suka wayi gari bata daina kuka ba, tunda likitoci suka nufi wajenta ta dinga kuka tana fad'in karsu tab'a ta su saketa ta koma gida, babu abinda suke ji kamar d'orin qafarta dan yafi hatsari, ganin abin ba qarami bane yasa Papa ma yace su sallamesu kawai. Duk da ba haka aka so ba haka aka sallameta aka koma gida da ita, a d'akinta aka sake mata wani tanadin na ci gaba da jinyarta , amma duk da sunzo gida ma ba'a bari kowa ya ganta saboda kukan da take. *Bayan sati d'aya* jikinta yayi dama dama sai dai har yanzu bata fara taka qafar ba, qananan raunikanta ne suka warke har akaihunta guda biyu sun toho, in banda shiru da tunani da hawaye babu abinda Khairat keyi hakan kuma na damun iyayenta. Da farko an fara barin 'yan uwa na zuwa dubata, amma ranar da Mujahhid yazo da abokanshi su uku saita firgita sosai tana fad'in sune sune, tun ranar sai Mammie ta yanke shawarar tafiya da ita india danta samu ta dawo daidai. Umar Faruk ya ci gaba da zuwa wajen aikinshi sai dai i zuwa yanzu babu wata damuwa a tare dashi, gaba d'aya ma mantawa yake da wata Khairat bare ta dameshi , yayin da d'aya b'angaren kuma yake soyayyarshi hankali kwance da 'yar uwarshi *Zubaida* wacce suka fi kira da *Zuby*, kuma suna jiran hutun 'yan makaranta domin shi zai basu damar zama miji da mata. An shigar dasu Musa kotu kuma sun samu hukuncin shekarun da doka ta tanadar ga duk wanda ya keta haddin wata, tun akan akan hayarsu ta zuwa sabon gidansu suka fara tuhumar juna suna dorawa Musa laifin, shi kuma yace ba gaskiya bane tunda bai tilasta kowa ba. _Wallahi ni duk abokin da ba zai anfaneni duniyata da lahirata ba to banga anfaninshi ba, domin kuwa kamar abotar shedan da yan uwata zata kasance, bayan ya ganka cikin wuta zai kora maka jawabinsa, bayan ya muku dogon jawabi da bama fatan jinshi daga qarshe dai zai ce ._ *Karku zargeni ku zargi kawunanku.* _Allah ka karemu da yayenmu daga fuskantar qasqanci irin wanda Khairat ta fuskanta, Allah ka shirya mana zuri'armu shirin addinin musulunci._👏 Mamie da Mammie ce suka kama Khairat daga bisa kujerar guragunta suka cire mata kaya sannan suka sata cikin bahon wanka dake d'auke da magunguna na ice kala kala, suna zaunar da ita ta rintse ido saboda zafin dake da ruwan, duk da kullum ake mata tunda suka komo gida amma ta kasa sabawa , a hankali ta bud'a ido hawaye suka gangaro, Mamie ce ta fita daga ban d'akin sai Mammie ta dinga tausarta da kalaman har saida ruwan suka huce sannan ta kira Mamie suka kamata suka fito da ita. Mamie ce ta shiryata cikin doguwar rigar kantie iya gwiwa sannan suka zaunar da ita akan kujerarta, abinci Mamie ta d'auka ta fara bata a baki, da sun had'a ido Mamie take saurin dauke nata, ganin kuma ta kafeta da ido yasa duk ta tsargu , a raunane ta kalleta tace "akwai abinda kike so ki fad'a ko?" Lumshe ido kawai tayi ta kawar da kai, Papa ne ya shigo cikin shiri da alama fita zaiyi, saida ya sumbaci goshinta yace "shalele ya kike?" Da ido kawai ta kalleshi, sake fad'in "ya jikin naki? da sauk'i dai ko?" Ganin dai ba za tayi magana yasa yace "shaleleta kiyi hak'uri kinji da abinda ya faru, ina tabbatar miki hakan ba zata koma faruwa ba." Take idonta ya kawo ruwa cikin mamakin abinda ba suyi tsammani ba suka ji Khairat tace "wane mai hankalin ne zai sake sha'awata kuma? akwai wani abinda ya rage min ne da har zan birge wani?" Maida kallonta tayi ga Mammie tace "Mammie, ki kaini waje dan Allah ina so nasha iska." A hankali ta tuka kujerarta ta fitar da ita kamar yanda tace, lambun dake bayan gidan ta kaita ta barota kamar yanda ta buk'ata, shiru tayi tana kallon firanni na kad'awa ga iska mai dad'i. Papa da Mamie ne suka fito daga d'akin nata suna zuwa falo yayi daidai da shigowar manager, bayan sun gaisa ya fad'a musu tare da sauran ma'aikata yake suna so suga jikin Hajia, Papa ne yace su shigo sannan yace Biba mai aiki taje ta taho da Khairat, zaune sukayi suna jiran shigowarta, Mamie kuma ko kad'an bata lura da Faruk ba yaron da take nema danta gode masa, madafa ta nufa domin samo musu d'an abun tab'awa. Shigowar Khairat a keken guragu yasa kowa maida kallonshi gareta, mamaki al'ajabi duka a tare da ganin Khairat, ita kam ido ta kafesu dashi tana kallon kowa, a lokacin da kallonta ya sauka kan Umar Faruk kuma sai gabanta ya mugun fad'i, duk da haka kuma bata d'auke idonta ba, shima a nashi b'angaren gabanshi ne yayi mummunar tsinkewa ya fad'i, d'auke kanshi yayi ita kuma suka k'arasa shiga falon, sannu kowa ke mata da jiki amma babu wanda ya amsa, Papa ne ya shafi kanta yana kallonsu yace, "Sai hak'uri fa, har yanzu magana na mata wuya, muma haka muke zaune da ita." A bazata Umar Faruk ya sake satar kallonta amma sai idonsu ya sake had'ewa , suna haka har Mamie ta fito amma da qyar wasu suka sha ruwa dan ganin Khairat ya girgizasu sosai, tashi sukayi gaba d'aya suka fita, amma Umar Faruk dake daf da barin falon sai yaji kamar muryar Khairat a bayanshi, dan haka yayi saurin juyowa ya kalleta, dama itama shi d'in take kallo dan haka suka kalli juna, d'an sakin fuskarshi yayi daga had'ewar daya mata baisan sanda ya saki wani basaraken murmushi ba, ita kum sai taji haushi ya kamata dan tunaninta yayi farin ciki da abinda ya sameta. *'YAN TEAM UMAR FARUK.*😛😛😛 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾 *Raina Fansane gareta* 🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾 _My sweet Heenat, ina tayaki murnar kammala wannan littafi, tabbas ya qayatar tare da nishadantarwa, ga ilima da muka samu a ciki, wannan shine labari ina fatan ubangiji ya yafe miki kurakuranki sannan ya baki ladar dake cikin wannan fad'akarwa da ki kayi._ sai mun jiki a next novel. _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣0⃣ *Haka* kwanaki suka dinga tafiya sati ma ya fara shud'ewa har aka fara lissafa abinda ya faru da sati uku, a *sati uku* kuma duk wasu qananan raunika sunyi sauk'i sosai sai qafarta da har yanzu takata ya zama aiki, har yanzu Mammie na gasata a ruwan zafi tare da wasu saiwar magunguna da zai taimaka mata, haka ma an sake maidata asibiti an mata gwaje gwaje amma cikin ikon Allah babu wata matsala har yanzu. A lokacin data cika wata d'aya sai suka fara shirye shiryen tafiya india, a lokacin kuma Mamie ta matsawa Papa akan ya bata takardarta, shi kuma ya dage ba zai bayar ba, amma ita taci alhwashin tafiya ko babu takardar saki, Mammie bata fahimci komai ba dan basa nuna da wata matsala a gabanta, Papa kam yayi tuba na gaskiya ya daina duk abinda yake yanzu, sai dai akwai barazana da wasu matan ke kawo masa saboda suna samun arzik'i sosai a hannunshi, duk da Khairat bata cika magana ba a yanzu amma dai bata kula Papa sosai haka ma Mamie. Yau ta kama ranar *juma'a* Papa ya fito cikin shirin massallaci misalin k'arfe *10:00*, zaune suke a falo yayin da suka bishi da ido, durk'usawa yayi gaban Mammie ya gaisheta tare da fad'in "Mama zan tafi masallaci sai a mana addu'a." Murmushi tayi dan ita har ranta tana ganin d'iyarta tayi sa'ar miji na gari, cikin sakin fuska tace "Allah ya tsare ya kareka daga sharrin masharranta, insha Allah ba zaka tab'e ba, domin kai mutumin kirki ne, duk da ban haifeka ba amma ka d'aukeni tamkar mahaifiyar data haifeka, babu abinda zance sai dai nace Allah ya saka maka da alkairi." "Ameen ameen Mama, na gode da addu'ar nan Allah ya bar mana ke." "Ameen." itama ta fad'a sannan ya mik'e yana kallon Mamie yace "ni zan wuce." Cike da murmushi tace "to abban Khairat Allah ya tsare, saika dawo." Shima cikin murmushi yace "ameen na gode." Maida kallonshi yayi ga Khairat ya dafa kanta yace "shalele ni zan wuce, kiwa Papa addu'a kinji." Sanin ba za tayi magana sai kawai ya wuce, muryar Khairat yaji tace "Allah ya kiyaye, a dawo lafiya." Da sauri ya juyo ya taho a sukwane ua zube gwiwoyinshi gaban kujerarta, cikin farin ciki yace "Khairat, yau kece ki kawa Papanki addu'a? kai Allah na gode maka." Duk da hawaye sun fara taho mata haka tace "Papa, duk munin halinka kai mahaifina ne, Papa ku yafe min da duk abinda na muku wanda ya b'ata muku rai, nasan hada hakk'inku dana kasa saukewa da kyau shi yasa haka ta faru dani." Hannunta ya rik'e da sauri yace "a'a shaleleta, ba laifinki bane, laifina ne duk ni na ja miki, amma ki sani Papanki yayi nadama sosai kuma ya daina duk abinda yake yanzu." "Khairat yanzu mahaifinki ya rabu da duk wani shirme na maida al'amurana ga ubangijina, shaleleta ki yafe min domin na cutar dake, duk nine...." "Papa" cewar Khairat tana kau da kai gefe. Shiru sukayi babu mai magana dan haka Papa ya tashi yana goge hawaye ya fita, Mamie ce ta matso kusanta ta rik'e hannunta tana shafawa tace "Khairat, ki yafe mana a bisa kurakurenmu, nima na taka rawa wajen faruwar komai a matsayina na uwa, amma yanzu mun shirya gyara kuskurenmu." Da ido kawai ta kafe Mamie ba tace komai ba har Mamie ta gama surutunta ta koma mazauninta, haka suka zauna shiru dan yanayin da gidan yafi zama kenan tun faruwar abinda ya faru. Bayan Papa ya dawo daga masallaci sunci abinci Mamie taje d'akinsa ta zauna dan kawar da duk wani shakku da zai nuna basa zaune lafiya, yana cire kayan jikinsa ya kalleta ta madubi yace, "Har yanzu kina kan bakanki na tafiya tare dasu Mama?" Ba tare data kalleshi ba tace "kana tunanin akwai abinda zaisa na fasa ne, kayana a shirye suke ranar kawai nake jira." Gabanta ya zo ya tsaya ya kamo hannayenta suna kallon juna, kai ya girgiza mata yace "Na'ima, ke musulma ce kuma mai ilimi, nasan kinsan ba daidai bane aibata wanda ya musulunta, haka ma bai dace ak'i karb'ar yafiyar wanda ya nemi afuwa ba, hakan nasa da dama su kasa shiryiwa saboda tunanin haka, dan Allah Na'ima ki yafe min laifina wallahi ba sani da kika min da bane." Ganin ta kawar da kai gefe yasa hannu ya tallabo fuskarta yana kallo, a hankali cikin tsoro ya had'ata da jikinshi, 😁wasa fa saita fara canzawa to ni dai nayi nan, bana kallon k'aramar harka bare kuma wannan babbar harka. Kamar yanda Mamie tayi niyyar tafiya ko babu takarda hakane ta faru, ta shirya itama kuma tace wa Mammie shine yace su tafi tare danta kama mata kula da Khairat, ya gama shirya musu komai amma banda Mamie, in da itama ta shiryawa kanta komai ba tare da saninshi ba. Sun gama shirin tafiyarsu tsaf ranar talata kawai suke jira ta zo, yau *litinin* da dare Mamie na zaune matashin saurayin nan ya fad'o mata a rai, wayarta ta d'auka ta kira manager ta tambayeshi akan yaron da suka zo tare a ranar, ya fad'a mata sunanshi dama matsayinshi a ma'aikatar tare, ta kuma tambayeshi koda wata alaka tsakaninshi da Khairat yace a'a, amma ya fad'a mata abinda ya shiga tsakaninsu. Nan tace da safe ya turo mata shi kafin lokacin tashin jirginsu, bayan sunyi sallama ya kira Umar Faruk ya fad'a masa, hakan yasa ya kwana yana tunanin abinda zai faru da kuma dalilin da yasa matar ke nemanshi, haka dai ya wayi *gari* sannan ya shirya ya tafi gidan. Khairat ce zaune akan kujerarta ta kira Biba, tana zuwa tace mata ta turata ta kaita lambu tasha iska, haka akayi ta kaita can ta barota yayin da ta toshe kunnuwanta da abin sauraro tana sauraron wak'ok'i, Umar Faruk ne ya shigo gidan sai dai kafin ya shiga ciki sai wayarshi ta fara ruri, yana fito da wayar yaga Zuby ce ke kira dan haka ya d'auka ya fara tafiya ya nufi kwanar cikin gidan duk da baisan ina zata kaishi ba, a hankali yake takawa harya riski lambun dake bayan gidan, jingina yayi a bishiyar daya fara gani cikin taushin murya ya mayar da martanin abinda Zuby ta fad'a masa, "Ina sonki, ina qaunarki , na matsu ranar nan tazo domin a ranar burina na gidan duniya ya cika, na gaji da mafarkinki a kullum, ina so mu fara rayuwar gaske." Khairat dake sauraren wak'ok'i bata jin me yake fad'a, amma shi duk da yana magana ne amma yana jin wata siririyar murya na tashi a kusa dashi ana rera waka , juyawa yayi ya kashe wayar yasa aljihu tare da rumgume bishiyar ya lek'a kanshi a hankali dan ganin me wakar, yanda ya rumgume bishiyar yasa hannunshi ya d'an shafi kafad'arta hakan kuma yasa ta juyo da sauri, manyan idanunsu ne suka sarke dana juna suna kallon kallo, babu wanda baiji fad'uwar gaba ba a cikinsu amma sai suka basar. Babu wanda yace wani abu kuma babu wanda ya d'auke kanshi, Khairat ce taja tsaki tare da maida kallonta ga wayarta ta ci gaba da abinda take, yana ganin haka ya tab'e baki shima ya koma hanyar daya fito, Biba ce ta masa izinin zama sannan taje ta sanar da Mamie bak'onta ya zo. Yana cikin kallon hadadden falon yaji bud'a k'ofa, maida kallonshi yayi ga nutsatsiyar matar mai dattako, tsaye ya mike yana murmushi ita kuma ta masa izinin zama, cike da girmama juna suka gaisa kafin Mamie ta kalleshi a tsanake. Hakika Umar Faruk ba zaka kirasa da kyakyawa ba ajin farko, amma dai dole ka kirashi kyakyawa na farko a aji na biyu, manyan idanunshi masu firgita mai kallonsu da kuma saka kwarjini, haka kuma bak'i kuma yalwataccen sajenshi ma ya k'ara masa kyau, kana ganinshi zaka san jarumin namiji dan suffarshi ma ta zaratan maza ce, daga tafiyarshi kuma zaka gane ingarman dokine mai tashen k'uruciya a jika. Murmushi Mamie tayi tace "Umar Faruk, ranar ka taimakemu amma kuma saika tafi ba tare da mun maka godiya ba, kome yasa kayi haka?" D'an murmushi yayi yace "Hajia ni na taimakeku ne saboda Allah, bana buk'atar ku gode min." "Duk da haka Umar Faruk muna godiya sosai da irin taimakon daka mana, amma dan Allah tayaya akayi kasan da mutanen nan?" Kallonta yayi yace "Hajia da mun bar duk wannan maganar, tunda dai masu laifin sun shiga hannu." "Hakane, amma zan iya sanin meke tsakaninka da Khairat?" Murmushin gefen labb'a yayi yace "ba komai Hajia." "In tambayeka mana idan ba damuwa?" "Uhum, ba damuwa." "Dan Allah kana da aure?" "A'a, amma dai nakusa insha Allah." "Allah yasa alkairi." Ya amsa da "ameen, na gode." Kallonshi tayi tace "amma misali, idan nace zan da Khairat, kana ganin zaka yarda ka aureta?" Kafeta yayi da ido da tsananin mamaki, ba zai iya yi mata qarya ba kamar yanda ba zai yarda ya lalata rayuwarshi ba ta hanyar auren Khairat, ko kyauta za'a bashi ita to ba zai karb'a ba, shima da ido ya kalleta yace "kiyi hak'uri Hajia, amma gaskiya ba zan iya ba, kiyi hak'uri idan abinda na fad'a ya b'ata miki rai, ina da wacce nake so kuma hutu kawai muke jira a d'aura mana aure." Murmushin takaici tayi tace "karka damu raina bai b'ace ba, dama tunda abun nan ya faru na sawa kaina dole haka zata fara faruwa damu, nasan a yanzu ba kowa bane zai iya yarda ya aureta, amma ba komai zamu ci gaba da hak'uri har komai ya zo qarshe, kuma ina so ku sani Khairat bata da laifi, duk laifin namu ne iyayenta musamman ma ni uwa." "Shari'a ta nuna mana yanda zamu samu yaya na gari tun kafin aure, amma sai kaddarata ta zo da tangarda na kasa samar mata uban daya dace, ba komai karka damu kanka kaji." Tsaye ta mik'e tace "na gode yaro Allah ya maka albarka." Shi dai baice komai ba yana kallo ta fara tafiya kuma ta tsaya ta juyo tace "bansan ko kana buk'atar kuyi ban kwana da Khairat ba, dan baifi awa d'aya daya rage mana ba mu koma India da zama tare da mahaifiyata." Tana fad'a ta juya saboda hawayen da suka taho mata, yau gashi *halin rayuwa* yasa harta yiwa namiji tayin 'yarta a cikin wasa amma yace baya so, shi kuma jikinshi ne yayi sanyi duk yaji ba dad'i, amma kuma baiyi nadama dan ba zai yarda koda a misaline ba a dinga had'ashi da Khairat. Tashi yayi shima ya bar gidan dan baiga wani ban kwana da za suyi ba da ita, haka ya d'auki hanya yana tunanin maganganun mahaifiyar Khairat, uwar mutuniyar kirki ce amma diyar da uban sai a hankali kam , inji Umar Faruk. 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀ *MARAYU MA 'YA'YANE* 🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀🤹🏻‍♀ _A gaskiya littafin nan ya ilmantar sosai, kuma da za'a dinga yin labari irinshi to za'a samu ci gaba, my Lissa na tayaki murnar kammalashi, ubangiji ya yafe miki kurakurenki ya baki ladar fad'akarwar da ki kayi._ sai mun had'u a labari na gaba. _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣1⃣ Lokaci nayi suka fito cikin shirin tafiya, Papa na ganin Mamie ya janyeta gefe cikin rad'a yace "wai me kike shirin yi ne Na'ima, da gaske tafiya za kiyi?" Fizge hannunta tayi tace "ka rabu dani, aina fad'a maka babu abinda zai hanani tafiya wallahi, kaji na rantse." Jinjina kai yayi yace "naji, tunda kince dole zaki tafi to ki tafi, amma ki barmin 'yata zan kula da ita." Dariya tayi tace "'yarka, wallahi idan kaga nabar Khairat a hannunka to ka tabbata aure zaka mata, amma in ba haka to wallahi ba zan bar maka ita ba." Wucewa taje yi ya sake rik'eta yace "naji tunda haka kika ce, ki bar Khairat anan, na miki alk'awarin samo mata miji na gari na had'ata dashi." Kallon sama da qasa ta masa tace "idan ka samu mijin saika kirani ka fad'a min, ni kuma zan kawo maka ita da kaina." Tana fad'a tayi gaba, haka suka tafi tare ya rakasu babu mai magana har jirginsu ya tashi yana kallonsu, haka suka tashi yana ji kamar ya bisu amma tunda bai shirya hakan ba dole ya hak'ura, haka ya juya ya koma gida zuciyarshi na tafasa kamar zata fashe, yana son Na'ima kuma yasan ba zai samu mace kamarta ba, amma hallayarshi taja mashi rasata a lokacin daya fi buk'atarta. Ita kanta Mamie saida jirgi ya tashi sai taji kamar bata kyauta ba , kamata yayi ace ta hakura su rumgumi 'yarsu su maida hankali kan tarbiyarta, ba kuma wannan ne yafi d'agawa Mamie hankali ba shine ji da tayi kamar itama ta kamu da son Papa ba tare data sani ba, haka dai har suka sauka a india Mamie na hawaye, Khairat kuma na ganin haka saita dinga jin haushin Mamie saboda tana ganin ai farin ciki ya kamata tayi data rabu dashi na d'an wani lokaci, to amma ta rasa kukan miye take. *SOYAYYA KENAN*😁 Tunda suka sauka abokan arzik'i da aka saba suka fara zuwa musu sannu da zuwa, kuma sai lokacin suke ganin halin da Khairat ke ciki, haka dai ake ce musu hatsari tayi nan zasu mata addu'ar samun lafiya sannan su tafi. Haka ma dai masoyin nata Raj ba'a barshi a baya ba, a sukwane yazo domin ganin Khairat cikin farin ciki tare da shirinshi na neman aurenta a yau d'in, amma ganinta a wannan hali saiya sare masa gwiwa dole ya hak'ura, amma yayi niyyar bayyana mata k'udirinshi bada dad'ewa ba koda tana cikin wannan halin ne dan yana sonta so mai tsanani. *Daga* wannan rana sai Raj ya fara taimakawa su Mamie wajen jinyar Khairat, duk da Mamie bata so ko kad'an amma da yake mutum ne mai barkwanci da son mutane gashi da aiki ko ba'a sashi ba, hakan yasa ya shiga ran Mammie kuma ya qara girma a idon Khairat, kowace safiya saiya zo gidan ya tayasu had'a abin kari kuma da kanshi yake bawa Khairat nata , haka kuma da dare zai zo su jima suna hira da Khairat saboda kusan unguwa d'aya suke, Khairat najin dad'in haka hakan yasa yanzu harta fara canzawa yanzu tana magana sosai tana dariya in dai Raj na nan. A haka sai shakuwa ta sake shiga tsakaninsu fiye da baya, duk da raunin dake jikinta tare da rashin tafiya hakan baya hana Raj fita da ita wuraren shaqatawa, kuma hakan na mata dad'i tana d'ebe kewa sosai. *A b'angaren* Papa kuwa an duk'ufa an maida al'amura ga ubangiji, sallah kan lokaci tsayuwar dare yana neman gafarar ubangiji, azumi kullum sadaka da taimakawa marasa galihu duk wannan yanzu shine aikinshi, damuwar rashin iyalinshi na damunshi musamman Na'ima wacce yake ganin ta tafi kenan, duk kiran da yake mata bata dauka Khairat kad'ai da Mammie suke waya dasu amma banda ita, idan ka ganshi yanzu yayi kalar tausayi sosai kana ganinshi za kasan yana rayuwar kad'aici, sai ma'aikata kawai dake hidima da gidan. _Allah ya karb'i tubanmu ya yafe mana kurakurenmu._ *Bayan wata uku* Umar Faruk ne a tsakar gidansu Zuby suna hira, Zuby ce ta nunfasa tace "yaya Umar, a gaskiya kaban mamaki sosai daka iya b'oye min abu mai mahimmanci haka." Gyara zama yayi yana kallonta sosai yace "uhum, ina jinki, me nayi kuma?" Cewa tayi "yaya Umar, jiya da naje gida wajensu Mama nake jin abinda ya faru a wajen aiki, wai matar da kuke aiki a qasanta ta mareka, a gaskiya raina ya bace sosai, ganin duk kwarjinin nan naka ace mace ta daga hannu ta mareka, ai sai dai mai zarra." Shiru ya d'anyi na wani lokaci dan sai yanzu da tayi maganar ya tuna da wata Khairat, a hankali ba tare da sanin maganarshi ta fito fili ba yace "ko ya jikinta yanzu?" "Wacece?" tambayar da Zuby ta jefo masa kenan. Da sauri ya kalleta yace "a'a...ba...bb..ba komai." Dorawa tayi da "amma ai kamar itace na gani a Whatsapp ana magana akai, wai in dai har za'a dinga keta haddi yayan manya ma to ina ga talakawa da marasa 'yanci." Kallonta kawai yayi da ido, dan haka ta sake cewa "kuma naji ance har mutum hud'u ne ko, gaskiya ta ban tausayi, nikam yaya da zaka kaini gidansu ma na ganta wallahi." "Keeee." tsawar daya mata tasata zabura da k'arfi. Tsaye ya mike yana masifa "ita d'in cinema ce da za kice na kaiki ki ganta, wani abun dad'i ne ya sameta da har zaki dinga magana haka cikin shauki , to ba zan kaiki d'in ba kije da kanki saiki ganta, hada wani wai mutum hud'u, to sai akayi me dan mutum hud'u ne? zata fasa rayuwa ne ko kuma zata rasa mijin aure ne?" Yana gama fad'a kuma ya koma ya zauna yana huci, ruwan dake kusa dashi a cup ya d'auka ya kai bakinshi , kamar dirar mikiya ya tsinci muryar Zuby tace "zata rasa mijin aure, dan a mahawarar dana gani a Whatsapp, kowane namiji yana cewa shi ko kyauta ba zai aureta ba, wasu kuma suna cewa idan za'a had'a musu da kud'i da mota da gida to zasu amince, watak'ila kaine kake ganin ba komai bane, amma wannan ba k'aramar matsala bace." Kasa shan ruwan yayi ya qura mata ido, ita kuma tashi tayi ta shige d'akinsu wai ita ya d'aga mata murya akan wata banza. _Lallai ruwa sun daki babban zakara , Khairat d'in ce banza?_ Ai baiko bi ta kanta ba ya fita daga gidan shima ya hau mashin d'inshi, bai zame ko ina ba sai majalisar da manage ke zama bayan an tashi daga aiki, zaune ya samesu wasu akan tabarma wasu akan benci, gaidasu yayi cikin girmamawa dan duk ba sa'anshi, manager ne yasa takalmi ya tashi suka keb'e. "Umar Faruk lafiya na ganka cikin wannan daren?" "Eh to, lafiya lau." Shiru ya d'anyi shi kuma yana kallonshi kamar mai nazartarshi, kai ya shafa yace "manager wai dan Allah ya jikin Hajia Khairat ne? naga har yanzu babu wani labari tunda suka tafi basu dawo ba." Manager daya kafeshi da ido murmushi ne ya bayyana a fuskarshi ya dafa kafadarshi yace "Umar Faruk kenan, irin wannan damuwa haka? to ka kwantar da hankalinka, Khairat na nan lafiya dan mahaifiyarta tace min ma harta fara takawa da taimakon wani saurayinta Raj, kuma da zaran ta samu sauki sosai zata turota ta dawo gida." Da mamaki ya kalleshi yace "ta turota kuma, ita fa?" Ajiyar zuciya ya sauke yace "wannan sirrin gidan Alhaji Mani ne, bai kamata na fitar dashi ba, amma dai ka sani mahaifiyarta ba zata sake dawowa ba sai dai wani iko na ubangiji kuma." A tsanake ya kalli manager yace "hakan nada alak'a da abinda ya faru da 'yarsu kenan?" "Sosai ma, faruwar hakanne ya jawo komai." Kai Umar Faruk ya girgiza ya bawa manager hannu yace "na gode manager, ni zan wuce." Harya tafi manager ya kira sunanshi, juyowa yayi yace masa "ko dai na baka lambarta ne saika kirata kaji." Kamar wanda aka ba tsoro saiko yace "a'a a'a, ni kuma me zanyi da lambarta." Yana fad'a ya juya ya hau mashin d'inshi yana fad'in "ina ruwana da ita, tana can fa ita da masoyinta." Tafiya ya fara amma ya rasa dalilin da yasa ranshi b'acewa, da k'arfi sake fizgar mashin d'in tare da jan dogon tsaki yace "Raj d'in banza da wofi, miye matsalata dashi da zai dameni." 😛😛😛😛😛😛😛 *A wannan* lokacin Khairat jiki yayi dama sosai tafiyarta ma lafiya lau, da taimakon Raj ta fara takawa dan kullum shike rik'e da hannayenta yana koya mata tafiya harta fara sosai, yanzu dai da kaga Khairat to ta baya ce dan ba zaka tab'a cewa tayi wata larura ba. Mammie Mamie da Khairat duka suna zaune a falo suka ji ana buga kofa, Khairat ce ta tashi ta bud'e, da farin ciki ta rumgume Raj wanda ya shirya cikin pink d'in riga da bakin wando, sosai yayi kyau dan dama akwai kyau d'in, sakin juna sukayi ya shigo ciki ta rufe kofar, hannun juna suka rik'e cikin yaran india take cewa, "Yaufa kayi kyau, da wani abu ne dake faruwa?" Murmushi kawai ya mata ya mik'a mata flowers daya taho da ita ja mai kyau, karb'a tayi tace "na gode." Mamie da tunda ta ganshi ta had'e rai dan ko kad'an bata san ganinshi tare da Khairat, bata musa akan cewar yaran kirki ne ba,amma tafiyarshi da Khairat bata dace ba, saboda shine namiji kuma ba musulmi ba, d'aya bayan d'aya ya sunkuya ya tab'a qafafun Mammie da Mamie d'in dan neman tabarruki, Mammie ce tace ya zauna, kallon kallon aka shiga yi har saida Khairat tace, "Ya dai Raj?" Kai kawai ya girgiza mata alamar ba komai, Mammie da Mamie ya kalla cikin harshenshi yace "ina neman izininku akan ku bani damar neman auren Khairat." Khairat ce ta kalleshi da mamaki, kai ya jinjina mata dan haka ta taso ta dawo wurinshi ta zauna murya qasa qasa tace "kana haukane? nifa ban shirya aure ba yanzu." Hannunta ya kama ya rik'e yana mata shu'umin kallo yace "me yasa Khairat? baki sona ne?" Cikin sanyin jiki tace "ba haka bane Raj, amma ba...." 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣2⃣ Bai bari ta k'arasa ba ya rufe mata baki yana fad'in "shiiii, Khairat, in dai har kina sona, to ki tabbatar min da hakan yanzu ta hanyar saka wannan zoben, alamar munyi baiko dake." ya fad'a tare da fito da zobe daga aljihun rigarshi ya bud'e mata. Da mamaki ya kalleta tana tunanin mafita, hak'ik'a Raj shine namiji na farko da take jinshi a ranta, ganin bata da wani dalili na kin amincewa yasa tayi murmushi ta mik'a masa hannunta tace "eh, na amince." Cikin farin ciki ya fito da zoben jiki na rawa ya fara k'ok'arin saka mata, "Khairat!" Kira da Mamieta mata yasa suka kalleta a matuk'ar razane, tsaye suka mik'e suna ci gaba da kallonta, d'orawa Mamie tayi da "ashe baki da hankali Khairat, ke yanzu amince masa za kiyi ki aureshi kike nufi kome? kinsan hukuncin kuskuren da kike shirin aikatawa kuwa?" Maida kallonta tayi ga Raj da bai fahimci komai ba ta fara masa magana a harshen india duk da yanzu indiancin nata yayi rauni sosai amma haka ta dage tace masa, "Kaga Raj, kai yaron kirki ne, amma ka sani alak'arka da Khairat ba mai dorewa bace domin kuwa ita musulma ce kai kuma ba musulmi ba, addininmu kuma ya haramtawa mace musulma auren namiji da ba musulmi ba, dan Allah ina so ka fita a harkarta ka manta da ita a rayuwarka, kaje ka samu mace yar uwarka ka aura, dan Khairat ma an fitar mata da miji fad'a maka ne ba tayi ba." Duk da ta fad'i hakane danya rabu da ita, amma dai bata ji dad'in abinda ta fad'a ba saboda ba gaskiya bane, had'e hannayenta tayi tace "na rok'eka da ka tafi, ka tafi dan Allah karka sake dawowa, dan Allah." Tunda Mamie ta fara magana ya zama kamar gunki, jin ta gama fad'an abinda take son fad'a yasa ya juya ya kalli Khairat, gefen fuskarta ya shafa yayi murmushi wanda yasa hawayenshi suka fito, da qyar ya iya furta mata "zanyi kewarki Khairat, naso na sameki, amma dole na barki, ba zanso ki sab'a umarnin addinninki ba a kaina, kibi zab'in iyayenki." Yana fad'a yayi hanyar fita, da sauri Khairat tabi bayanshi, fizgowar da Mamie ta mata tasa ta fad'a saman kujera, a hassale ta tashi cikin harshen zarma (zabarmanci,😁inji k'anwata zamarmanci) ta fara magana, "Wai meye haka, me yake damunki ne, kinsan me kika aikata kuwa? aurena fa ya nema a gabanku, akan me zaki masa haka?" "Khairat, kin manta ke musulma ce, bai halatta gareki ba auren wanda ba musulmi ba." "Mamie saime, nifa zan zauna dashi bake ba, me yasa zaki min haka?" _WAI'IYAZU BILLAH_😭 A fusace ta shige d'aki ta barsu, Mamie kuma fad'awa tayi saman kujera ta fashe da kuka sosai har saida Mammie ta taso ta zauna kusanta ta dafata tace, "Na'ima kiyi hak'uri, kici gaba da yiwa Khairat addu'a, insha Allah zata canja." "Yaushe, Mama sai yaushe Khairat zata san mu iyayen tane, Mama munyi kuskure da bamu d'ora Khairat a tafarkin ilimin addini ba, yafi kowane ilimi a rayuwa, na tabbata da tayi karatu da zata san girman hukuncin iyaye sannan zata san girman zunubin da take shirin aikatawa." "A gaskiya Mama ba zan jure ba, aure kawai nake so Khairat tayi Mama, akwai matsala zamanta anan dan haka gobe zamu koma wajen mahaifinta, na gaji da ganinta a gabana Mama." Tana gama fad'a itama ta tashi ta nufi d'akinta, kwance tayi tana tunanin rayuwa da kuskurensu da kuma kuskuren da 'yarta ke cikin aikatawa, Khairat ma na d'akinta tayi kiran wayar Raj harta gaji, ganin ta aika sak'o ba amsa yasa kawai ranta ya b'ace ta fita harkarshi shima, abin sauraronta tasa a kunne tasa sanyayyen waka domin d'ebe mata kewa. *Tunda gari ya waye* Mamie taje ta ciro musu ticket kuma tayi sa'ar samun jirgin da zai tashi da yamma, tana zuwa ta shirya kayanta dana Khairat dake bacci a d'akinta, tana gamawa ganin lokaci ya fara tafiya yasa Mamie tashin Khairat. Da mik'a ta farka tare da hamma, ganin Mamie tsaye yasa ta gyara zamanta tana kallonta, "ki tashi ki shirya zamu tafi." "Ina kenan?" cewar Khairat tana saukowa daga kan gadon. "Gidan mahaifinki zamu koma?" Dariya tayi tace "kije kawai idan kinyi kewar mijinki ne, ni nafi jin dad'in zamana anan tare da kakata." Gabanta Mamieta tare tace "Khairat tare zamu tafi dake, kiyi sauri ki shirya ki fito ki sameni." "Bansan me yasa kike so ki bawa kanki wahala ba, na fad'a miki ba zanje ba." Da sauri Mamie ta fita daga d'akin ta koma falo ta bud'a jakar kayan Khairat d'in ta d'auko wata doguwar rigar atamfa ta dawo d'akin da zafinta, tana zuwa zaune ta samu Khairat akan kujerar dake gaban madubi tana kallon kanta, da k'arfi Mamie ta kamo hannunta ta tsayar da ita gabanta ta cire mata qaramar rigar dake jikinta, ganin tana kare qirjinta yasa Mamie tayi tsaki taci gaba da abinda take, saida ta barta da silip kad'ai sannan ta rataya mata wannan rigar, wani irin d'auri ne Mamie ta mata mai ban dariya sannan ta d'ora mata gyale a kafad'a dan tasan haka tafi so. Hannunta ta fizga zasu fita daga d'akin Khairat ta tirje tace "wai Mamie miye haka, nifa ba yarinya bace?" "Amma ni na haifeki, muje." ta fad'a tana janyota har suka fita. Mammie na zaune taga sun fito kamar ankorosu, tsaye ta mike tace "ku kuma lafiya, miye haka kike janta kamar yarinya?" "Fad'a mata dai kakata." cewar Khairat tana so ta kwaci hannunta. "Mama kiyi shiru, zamu tafi ne saina dawo." Jakunkunansu Mamie ta d'auka zasu fita Mammie tace "saikin dawo kuma, ina kuma yaushe, ki zo kiyi me?" Saida Mamieta bud'e k'ofar fita tace "idan na dawo za muyi magana, sai kinzo bikin gimbiyarki." Dariya Mammie tayi lokacin da taji Khairat tace "biki kuma, aure zaki min?" Haka suka fita suka shiga taxi d'in dake jiransu a k'ofar gidan, Mamie bata saki hannunta Khairat ba har saida suka shiga jirgi sannan. *Dare ya fara tafiya* suka shigo garin, suna cikin taxi Khairat na kallon gefen titi kwatsam ta hango Papanta zai shiga wani super market tare da wata wayayyar mata sun shiga ciki, da sauri Khairat ta daddab'a kafad'ar driven taxi tace ya tsaya, tsayawa yayi Mamie kuma tambayarta ta fara yi ko lafiya, fita tayi daga motar da sauri ta fita ta rufe motar ta lek'o kai tace wa Mamie "kije gida, zanje na taho miki da mijin naki." Da gudu ta tsallaka d'aya titin, zata tsallaka na biyu wani mai mota da bata kula dashi ba ya danna mata wata irin oder da saida ta zabura, cak ta tsaya tana kallon motar, ganin mai motar ya tsaya yasa ta kwada tsaki zata wuce kawai taji yace "yan mata lafiya, da matsala ne?" Hararanshi tayi tace " dallah gafara can, wai kai mai mota sai iya oder tsiya, hamago yanzu haka ma motar aro ce." Umar Faruk ne a d'aya b'angaren data tsallako zai wuce yaga kamar idonshi na mishi gizo, amma daga ganin kayan jikinta da yanda takewa mutumin nan magana yasa yasan Khairat ce da kanta ba mai kama da ita ba, tsallakowa yayi ya tsaya daga gefe yana kallonsu kamar wasu mutanen da suma har sun fara kallonsu, mai motar nan ne yace "da alama baki da tarbiya, amma tunda kika had'u dani kin gama, wallahi daga yau ba zaki sake wulak'anta wani ba." A zabure ta matso kusanshi tace "me za kayi, dukana za kayi, ko kuma kaima za kayi abinda kuka iya ne, to ka sani ba kaine farko ba?" Zaiyi magana ta mashi wata irin kyara tace "tafi dallah ni bana da lokacinka." Zata wuce ya tari gabanta ya zaro mata ido yace "ke har kin isa kice zaki ci mutunci na, kinsan ko waye ni? ke yar gidan uban waye? da alama fa karuwanci kika fito amma har kike so ki rainani, to yau sai naga uban daya d'aure miki gindi a garin nan." Waya ya fito da ita da alama kamar wata lamba yake nema, Umar Faruk ne yaga al'amarin zaiyi tsamari dan haka ya matso tare da rik'e hannun mutumin yace "sannu abokina, dan Allah kayi hak'uri ka rabu da ita, qwaqwalwarta ce ta samu matsala tunda ta samu wani hatsari." A hassale mutumin yace "ina so ne naga uban daya d'aure mata gindi a garin nan da har take wa mutane rashin kunya, ka bari kawai na koya mata hankali." "Ka koya min hankali kaga yanda zamu kare da kai, wallahi sai kayi nadaman zuwanka duniya." cewar Khairat. "Ke." mutumin ya fad'a cikin daga murya. "Wai kinsan dawa kike magana? to mune garin nan dan mune gwamnati." "Mtsssssss." wani dogon tsaki da Khairat taja. Gyara tsayuwa tayi ta rik'e k'ugu da hannu d'aya tana nunashi da d'aya hannun tace "kasan ni kuma wacece, duk kasancewarka a cikin gwamnati nasan baka kai mahaifina ba, kasan koni yar wacece? to ni yar Mani Bukar ce, kuma nasan kasanshi." Jim ya d'anyi kafin ya basar yace "to saime dan kina d'iyar Mani Bukar, cemin za kiyi ragowar sojoji, ke yanzu duk da abinda ya faru dake amma kike wannan bud'a hanci, kamar wata wacce take cike da budurci." Ranta ne ya b'ace duk da hawayen da suka taho mata, matsowa ta sakeyi daf dashi za tayi magana amma sai Umar Faruk ya d'auka ko zata mareshi kamar yanda shima ta masa, da sauri ya shiga tsakaninta dashi yana kallonta yace "waike me yake damunki ne?" Kallon sani tama Umar Faruk amma kuma tana ji ba zata iya tunashi ba, wani tsakin ta kuma ja ta bisu da harara ta wuce abinta, Umar Faruk binta yayi da kallo kafin yaga in da ta shiga shima ya juya ya hau mashin d'inshi yana tunanin maganganun da mutumin ya fad'a mata. Tana shiga ta fara waige waige ta in da za taga mahaifin nata, can ta hangoshi da wata qosashiyar mace da gani kasan ba qarya babbar macece, a hankali ta fara takawa harta tsaya bayansu basu sani ba, cikin taushin murya tace "sannu da jin dad'i." Juyowa sukayi dukansu in da jikin Papa ya d'auki rawa, matar kam a wulak'ance ta fara kallon Khairat, matsowa tayi kusan matar za tayi magana Papa ya gaggauta jan hannunta yayi gefe da ita ya fara magana cikin rad'a. "Khairat meya kawoki nan?" "Kamata yayi tambayi ne yaushe na shigo garin." "Naji yaushe kika zo?" "Papa wacece waccen matar, kenan har yanzu baka daina abinda kake ba?" Hannunta ya rik'e yace "a'a shalele, wallahi na daina duk abinda nake, na riga dana tuba da duk wani aikata zunubi, wannan matar ma ba wani abu bane tsakaninmu a yanzu, kawai tana so ta b'ata min suna ne, shi yasa nake binta a hankali." Kai ta girgiza tace "Papa, kamar ya kake binta a hankali? me take maka?" "Khairat, wannan matar tace tana d'auke da cikina, kuma ta kaini asibiti an tabbatar min da hakan, kinga dole na bi a sannu." Juyawa tayi ta kalli matar sannan ta kalli Papa tace "wannan matar bata da wani ciki, kuma yanzu zan tabbatar maka da haka." Tana fad'a ta tunkari matar, tsaye tayi gabanta tana murmushi tace "Papana ya fad'a min na kusa samun kani , rashin yarda da banyi ba yasa nace bara duba da kaina na gani." Tana fad'a ta kamo hannun matar ta fara kallon tafin hannunta wai ita tana so ta gano ciki🤣, sakin hannunta tayi tana mata kallon tuhuma, k'ara matsawa tayi kusanta ta bud'a ijiyarta tana kallo, matar kam duk tsoro ya kamata dan haka ta tsaya ma, sakinta tayi ta kalli Papa tace "babu wani ciki a tare da ita, wahalar da kai kawai take yi, da alama ma kamar ba zata iya d'aukar ciki ba." "Inji uban wa? wallahi ko banda ciki yanzu ni nasan ina haihuwa." Kallon Papa tayi tace "ka gani ko, ko makarantar koyan likitanci ban tab'a shiga ba, amma ta bayar da kanta saboda tana tunanin ni ma'aikaciyar lafiya ce." Soshe soshe matar ta fara na rashin gaskiya a hankali ta aje kwandon hannunta wanda take zuba kayan data d'auka, tafiya ta fara yi su kuma suna kallonta, saida ta d'anyi nisa ta juyo tace ma Khairat "kin kub'utar da ubanki." Murmushi ta mata tace "sai dai ki kama uban wani amma ba nawa ba." Tana fita Papa ya shafa kan Khairat yace "Allah miki albarka shalele, gashi kin kub'utar da Papanki." Tafiya suka fara yace "ina alfahari dake gimbiyata." Ba tace komai ba har suka shiga mota yana tuki har suka isa gida, zaune suka samu Mamie a falo ko hijab d'in jikinta bata cire ba haka ma kayansu na gabanta, zaune Papa yayi yace "ya kike zaune haka?" Kallon Khairat Mamie tayi tace "ki shiga ciki za muyi magana." Wucewa kawai tayi ta shiga d'akinta, wanka ta fara tana tunanin fuskar data gani, bud'e idonta tayi duk da ruwa na sauka a kanta tace "Umar Faruk ko? tabbas shine." Tab'e baki tayi ta ci gaba da wankanta harta fito ta shirya cikin dogon wando fari da pink d'in riga mai siraren hannuwa, turare kawai ta shafa ta d'auki abin sauraronta ta makala a kunne ta fara tik'ar rawa abinta. 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣3⃣ Papa ne ya gyara zama yace "ina jinki, dan da alama akwai magana sosai a bakinki." "Hakane, kuma mai mahimmanci ce maganar." "To ina jinki." Saida ta kalleshi tace "baban Khairat, gaskiya ina so ka mata aure, bana so yarinyar nan ta jawo mana wata magana, idan zai yiwu gaskiya bana so aurenta ya wuce wata d'aya." "Toh, meya faru ne haka? wani abun tayi?" "Eh, in har mukayi wasa wallahi Khairat zata iya auren wannan yaron Raj, wanda hakan kuma bai dace ba, ni kuma bana so wani abu ya faru dan yaran yanzu zasu iya yin komai akan abinda suke so, shi yasa nake so ka d'auki maganar da mahimmanci, dan a gaskiya wata d'aya ya wuce banga Khairat a d'akin mijinta ba, tofa zan koma in da na fito dan aurenka ne zai mutu." Yanda tayi maganar ya bashi dariya, amma saiya had'eta yace "Mamien Khairat kenan, yau da alama da rigima kika shigo garin nan, amma fa karki manta abinda kike so ayi kamar za'a tilastata ne akan abinda bata so." "Ba wani nan, ya zama dole ka kauda ganinka daga b'acin ranta, in ba haka ba dama babu abinda za kayi." "To naji, yanzu bara na kirata naji koda wanda take so." Yana fad'a ya fara kwalla mata kira, amma ina ta toshe kunnuwa da abin sauraro koji ba tayi, saida Papa ya tashi ya bubbuga k'ofar da qarfi sannan ta bud'e tana kallonshi, "kizo." kawai yace ya koma falon. Bayanshi ta biyo harta zauna kujera mai fuskantar tasu, ganin sun kafeta da ido yasa ta cire abin kunnuwanta tana kallonsu, Papa ne ya kalli Mamie ya kalli Khairat yace, "Shalele, mahaifiyarki ce ta zo da wata magana mai girma, kuma na goyi da bayanta, shine nace bara naji ko akwai zab'inki?" Da kai ta masa alama da me kenan, d'orawa yayi da "ina so naji ko akwai wanda kike so a cikin zuciyarki? saimu tattauna dashi." Wata shek'akk'ar dariya tayi tace "wai kun gaji dani ne da kuke son aurar dani kome?" Papa ne yace "a'a shalele, aishi aure shine darajar 'ya mace." Mamie kuma tace "ai kin kai munzalin da za'a gaji dake d'in, shekara ashirin da biyar ai ba shekara sha biyar bace." Tsaye Khairat ta mik'e tace "kaji ko, to wallahi babu wanda zai min aure ban shirya ba, kuma me yasa baki fad'a masa abinda ya faru a jiya ba, baikona fa kika dakatar." Wucewa taje tayi Papa ya kalleta yace "to baki fad'a min wanda kike so ba?" Tsaye tayi ta kalli Papa tace "ni babu wanda nake so, har yanzu ban samu wanda ya dace ba." Tana fad'a ta juya Mamie ta bita da ido tana fad'in "kaji kuma, jiya fa hannu ta mik'a wani zaisa mata zobe, amma yau tana cewa bata son kowa." Papa ta kalla dake dariya tayi tsaye tace "shikenan tunda kun mayar dani mahaukaciya." Da sauri ya tashi ya rik'o jakar data d'auka yana fad'in "haba madam, kiyi hak'uri ki bar min komai a hanuna, insha Allah za kiga auren Khairat da idonki harki saka mata albarka." Zuciyarta ce ta karye ta kalleshi tana zubar da hawaye tace "dan Allah kayi wani abu dan ganin Khairat tayi aure, wallahi ina jin tsoron faruwar wani abun marar kyau, ka sama mata miji na gari daya dace, wanda zai d'orata akan addininta sannan ta gyara rayuwarta." Hannunta Papa ya rik'e yana kallonta yace "zan iya baki zab'i?" "Zab'in me?" ta fad'a tana share hawaye. "A gaskiya Na'ima a yanzu babu abinda nake so kamar naga Khairat ta fara sabuwar rayuwa mai kyau da tsabta, in hai muna so haka ta faru sai mun had'ata da jigo, kinga kuma a duk cikin masarinta dana sani banga mai wannan nagartar ba, amma bansan ko ke zaki iya samoshi koda a cikin danginki ne?" Shiru Mamie tayi dan sosai ta gamsu da bayaninshi, amma kuma saita kasa tuna komai dan haka tace "a'a, karfa muje wajen neman na gari kuma mu had'ata da bata gari, kawai ina ganin tunda ga Mujahhid nan d'an uwanta ai sai a had'asu." "Umm hakane, to ki kwantar da hankalinki insha Allah gobe da safe zanje na samu yaya *Suleiman* sai muyi magana." "Amma kana ganin Khairat ba zata bada matsala ba? danni yarinyar nan halinta sai ita fa." "Ki barta, wannan karan dai kam zan nuna mata ni mahaifine, zan shawo kanta da yardar Allah." Cike da jin dad'i Mamie tace "gaskiya naji dad'in haka, Allah ya k'ara mana shiriya." "Ameen, ban fad'a miki bane, amma harna fara zuwa islamiyya ta manya, daga sallah magrib zuwa insha, kuma a yanzu babu abinda ke min dad'i kamar kasancewata a majlisi na ganni gaban malam ina d'aukar karatu." Cikin nuna tsatsan farin ciki Mamie ta fad'a jikinshi tace "hakan yayi kyau, gaskiya ka kyauta, Allah ubangiji ya yafe kurakurenka na baya." "Ameen." ya fad'a tare da sauke ajiyar zuciya ya sake matseta. 😎 _Daga nan dai na bar gidan nayi nawa gidan nima._ *Tunda safe* koda Papa ya gama kari ya fita bayan Mamie ta bishi da addu'ar fatan nasara, Khairat kuma na d'aki na bacci lokacin tashinta baiyi ba. Yaya Suleiman yayi matukar mamakin ganinshi a bazata haka, amma kuma farin cikin ganin d'an uwan nashi wanda yake masa wuyar gani yasa bai nuna a fuska ba har saida ya samar masa masaukin daya dace sannan, yana zuba masa lemon a cup yace "gaskiya fa ka shammaceni sosai, irin wannan bazata haka kuma da sassafe." Cikin dariya yace "gaskiya dama nasan zansha wannan maganar, wallahi kawai cewa nayi zaifi nazo da safe dan wannan lokacin ne zan iya samunka gida." "Gaskiya kam, dan ina shirin fita ma yanzu." Zaune yayi suka gaisa sosai kafin shiru ya biyo baya, yaya ne yace "kamar da magana ko Ousman? fad'i ina jinka, meke faruwa?" "Babu komai yaya, ba wata matsala bace, nazo ne akan maganar 'yarka da kuma d'ana." "Wai kana nufin Khairat da Mujahhid?" Kai ya girgiza yace "eh su, naga kamar lokaci yayi daya kamata ace mun had'asu tunda ba yara bane." Duk da yaya Suleiman ya d'anji wani abu amma dai kuma ba komai bane, cikin farin ciki yace "ranar daka saka kazo ka fad'a min, ko kuma ka zo kawai ka sanar danine dan nasa albarka a ciki?" Dariya yayi yace "yaya kenan, ai kaine uban 'ya, dan haka kai muke jira kasa mana rana." Dariya shima yayi da k'arfi yace "haba dai wasa kake, ai duk diyanka ne dan haka kasa ranar data maka kawai." Papa ne yace "amma kafin musa ranar aida munji ta bakin Mujahhid d'in ko? dan kasan yara fa, watakila bai shirya ba ko kuma yana da wani tsarin a ransa." "Haba dai Mani, yaranmu ne fa mu muka haifesu basu suka haifemu ba, kawai ka fitar mana da ranar, tunda yana da aikinyi kawai aurene ya gagara sai yawo a gari tare da abokai, idan kuma kai kana jin tsoronsu ba zaka iya ba ni saina saka ranar." Dad'i Papa yaji dan haka yace "to ba komai hakan ma ai yayi, kawai ka tsayar mana da lokacin, sai muyi fatan Allah ya nuna mana ranar da alkairi." "To tunda kace haka, yanzu mu barshi nan da wata d'aya, hakan ya maka?" Wani sabon dad'i ne ya sake kashe Papa dan jin ansa daidai da lokacin da Mamie ta diba , da sauri yace "hakan ai yayi yaya, Allah ya nuna mana ranar, Allah ya tabbatar mana da alkairinsa." "Ameen ameen, kawai kuje ku fara shirye shirye, muma tanan wajen zamu fara, duk da ma dai abun duk gidane." "Gaskiya ne yaya, kuma da wannan nake maka albishir d'in dauke muku duk wata dawainiya, hatta gida da zasu zauna a ciki ni zan bayar insha Allah." "Masha Allah, to hakan ma yayi Allah ya sanya alkairi." *A haka* suka tsayar da maganar auren Khairat da Mujahhid, tun a hanya Papa ya kira Mamie ya fad'a mata, wai zo kaga farin ciki wajen Mamie marar misaltuwa, sai dai Papa yace karta fad'ama Khairat sai zai fad'a mata yanda zata fahimta, suna gama waya Mamie na zaune kawar Khairat ta shigo da sallama, amsawa Mamie tayi cikin daure fuska saboda tasan k'awacen 'yarta da *Rashida* ba alkairi bane, cikin ladabi ta zauna gefen Mamie tace. "Mamie ina kwana?" "Lafiya lau, daga gida a ke?" Saboda jin tambayar wata iri yasa ta d'ansha jinin jikinta tace "eh Mamie daga gida nake, dama nazo ganin Khairat ne, jiya take cemin ta dawo gari." "Ina fata dai ba fita za kuyi ba ko?" "A'a Mamie, ai yanzu mun daina fita in ba da rana ba." "Kice dai kun shiga hankalinku." "Gaskiya kam Mami." Kallonta Mamie tayi tace "Rashida, me zai ku nutsu kusan cewa annabi ya faku, Rashida zaifi muku ku fara neman ilimin addini, ku koma islamiyya tunda ba'a tsufa da neman ilimi, kuma bokon nan kunyishi keda k'awarki iya gwargwado, dan Allah ku koma in da zaku san ubangijinku da yanda zaku bauta masa domin tsiranku duniya da lahira." A kunyace tace "insha Allah zamu koma Mamie, mun gode sosai." Tashi tayi tace "bara na shiga ciki, nasan mutuniyar bacci take har yanzu." "Umm." kawai Mamieta fad'a danta lura Rashida bata wani d'auki zancen da muhimmanci ba, binta tayi da kallo ganin kayan dake jikinta itama dai kamar Khairat d'in sai dai ita ta fita jiki hakan yasa matsatsin kayan ko kyau basa mata. Kwance take akan makeken gadonta rufe ruf da zanin rufa pink saboda sanyin da d'akin ya d'auka na ac, zaune tayi akan gadon ta daddab'ata tana fad'in "macho, machota tashi gani na zo." Dogon tsaki taja tana bud'e zanin daga kanta, saida ta tashi zaune sannan ma ta kalleta, jingina tayi da kan gadon ta kalleta cikin muryar bacci tace "infa gaki saime, me zaki min? hada wani zuwa ki tasheni." Shiru tayi ba amsa dan tasan ta tab'o dala ba ganmo, ganin ba tayi magana ba yasa ta sauka daga kan gadon ta nufi ban d'aki tana tattare gashinta daya bazu wanda tun tana kwance aka since matashi. Jin qarar ruwa yasa Rashida ta tabbatar wanka ta fara hakan kuma yasa ta gyara zama, dan tasan awa d'aya ce zata fito da ita daga bayin, bugu da qari itama ba zata iya barin gidan ba har saita samu abinda take so, dan in bata jira ba zata ma kanta asarar kud'i kuma tana da tabbacin zata samu. 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣4⃣ Fitowa tayi da d'aurin qirji iya cinyoyinta taja kujera ta zauna a kai tana kallon kanta a madubi, mai take so ta shafa amma tana jin k'iwa, Rashida ce ta taso ta tsaya bayanta tasa hannu tana shafar kanta tana murmushi, ta madubi ta kalleta tayi qaramin tsaki, sun jima a haka babu wanda yayi magana, saida ta gaji da miskilancinta sannan tace "me kike so?" Kallonta tayi ta madubi amma ba tayi magana ba, sake cewa tayi "kiyi magana macho, nasan wani abu kike so shi yasa kika zo." Kai ta sosa ta fara magana "eh to, wallahi macho, gidane babu kudi gashi babu kayan abinci, mun shiga wani hali saboda ba kya nan, yanzu ma banso na zo wallahi dole ce tasa na zo." Juyowa tayi ta kalleta tace "d'auko min kayana nasa." Juyawa tayi ta nufi wajen kayan nata tana hararanta ta qasan ido, da hannu ta nuna mata wanda zata d'auko mata, tana kawo mata tace "ki kira min Biba." Nan ma a qufule ta juya ta fita, Khairat ma nayin hakanne da gangan dan abotarta da Rashida bata da wata mamora, shi yasa wani lokacin take sata aikin ma da bai kamata tasa ta ba idan ta lura akwai abinda take so a wajenta. Ta riga Biba shigowa kafin itama ta shigo tace "gani Hajia." Ciki ciki tace "ki wanke hannuwanki a ban d'aki kizo ki shafa min mai." Saida ta kalleta sannan ta shiga dan wanke hannuwan, haka ta fito ta fara shafa mata man a jiki har suka ida Rashida na zaune, da taimakon Biba tasa kaya sannan ta zauna gaban madubi ta murza powder kad'ai sannan tasa Rashida ta d'aura mata d'an kwali, masha Allah tsaf ta fito cikin riga da siket d'in atamfa wacce tasha d'inki tsadadden. Saida ta gama kallon kanta a madubi sannan ta juya ta bud'a wani coffre ta d'auko poshet (post) ta tsaya gaban Rashida, budawa tayi ta d'auko kudi yan jikka goma goma sababbi guda biyar ta mika mata, tana sa hannu ta karba Khairat ta juya zata fita Rashida tayi saurin rumgumota ta baya tana fad'in, "Oh, mon chouchou, na gode sosai Allah bar min ke ta wajena." Murmushi kawai tayi ta janye kanta daga jikinta ta fice, binta tayi a baya haka ta sauka daga kan matakala kamar wata sarauniya, kai tsaye wajen cin abinci ta nufa ta zauna saman kujera, Rabi ce tayi saurin zuwa ta fara zuba mata farfesun kayan cikin rago da kuma soyayyar kaza ga kuma doya da aka mirginata cikin k'wai, fresh milk ta d'auko mata ta zuba mata sannan ta fara ci, Rashida kam an samu kud'i ko ta abincin bata bita, sallama tama Mamie sannan ta kalli Khairat tace "macho na tafi, sai mun had'u." Ba wani sosai taci ba, dan Khairat a rayuwa bata san k'iba, dan d'an kumarin dake gareta ma yanzu jinshi take a wani babbar matsala, dan haka take kula da jikinta sosai amma bata son motsa jiki saboda ragwantaka, tana kammalawa ta komo falo ta zauna kusan Mamie, hankalinta na a wayarta Mamie kuma na kallo tana d'an satar kallonta wani lokacin tana murmushi. ***************** *Umar Faruk* kuma tun jiya daya ga Khairat ya kwana cikin tunanin halin daya ganta, sam baiyi tunanin haka daga gareta ba, ya d'auka zata canza ko dan abinda ya faru da ita amma sai yaga akasin haka, ta wani b'angaren kuma haushin abinda wannan mutumin ya fad'a yake ji, da haka har safiya tayi ba tare da yayi wani baccin kirki ba, duk lokacin daya farka Khairat ce zata ziyarci tunaninshi da ganinshi. Haka kawai yaji yana burin ya sameta a wajen aiki, shiri yayi sosai cikin qananan kayanshi bak'ar riga mai dogayen hannu da wando kalar qasa, yana shiga ma'aikatar ya fara duba wajen ajiye motoci ko zaiga motarta amma babu, duk da haka bai sare ba bayan ya shiga ciki ya aje jakarshi cikin dubara da sand'a ya nufi bureaunta, lekawa yayi ta madubi amma babu kowa kamar dai yanda yake, wata ajiyar zuciya ya sauke cikin sanyin jiki ya dawo mazauninshi, yana zaunawa ya fara tambayar kanshi wai me yasa ya damu da son ganinta ne, tsaki yayi kawai ya fara aikin gabanshi. **************** Khairat ce ta 'kwalla kiran Biba, tana zuwa tace ta d'auko mata jaka a d'aki da gyale, cikin 'yan mintuna ta dawo da jaka da takalma da gyale duk kalar atamfar dake jikinta, tana sakawa tayi hanyar fita Mamie tayi saurin cewa "sai ina kuma Khairat?" "Mamie zan lek'a bureau ne naga meke faruwa acan, saina dawo." Harta wuce Mamie tace "zo mana gimbiyar Papanta." Dawowa tayi ta tsaya gabanta, tashi tayi tsaye ta shafi fuskarta tace "Allah ya miki albarka Khairat, Allah ya baki yaya na gari, Allah ya kiyaye hanya kinji ko." Cikin jin dad'i ta rumgume Mamie tace "yau dai da wayona naji addu'ar sa albarka ta fito daga bakinki, na gode Mamiena, saina dawo ba zan jima ba." Sumbatar goshin Mamie tayi ta fita cike da farin ciki yau Mamie ta mata addu'a, ita kanta Mamie sai taji ba dad'i dan in zata iya tunawa gaskiya ta jima rabon data mata addu'a irin haka. *Kuskure da iyaye mukeyi sakacin yiwa yara addu'a, wasu na ganin laifin Khairat data zama fitsararriya, amma bansa Khairat ta zama haka ba har saida na samu dalili, Mamie ta kasance mai zuciya da yanke hukunci cikin hushi, hakan ya janyo tun Khairat na qarama ta daina daina janta a jiki bare tasata a hanyar data dace, hakan kuma bai dace ba ko kad'an, yaro ko yana qarami kake masa addu'a zan sai kana masa, uwa uba kuma addu'ar na bibiyarsa ta alkairi ko akasin haka, mu kula iyaye Allah ya bamu ikon tarbiyantar da yaranmu.* Da takonta na qasaita ta shigo wajen, kallon Abba yayi kowa da komai take da kyau, Umar Faruk daya duqufa da aiki, gabanshi ne yaji ya tsinke ya fad'i hakan ya tilasta masa juyowa da k'arfi, kasa dauke idonshi yayi daga kanta, duk da ba murmushi a tare dashi amma kuma fuskarshi a sake take, ganin yanda kowa ke kallonta kamar da wani abu a jikinta yasa ta tsaya waje d'aya, sake kallon kowa tayi dake wajen ta girgiza kai tayi murmushin takaici. A hankali tace "kowa ni yake kallo saboda yanzu kuna ganin kamar na zama daban a cikin mutane, kowa so yake yaga ina cikin damuwa, ni kuma abinda nayi alk'awarin ba zan shiga ba kenan har abada." Tana fad'a ta juya a fusace ta nufi in da ta aje motarta, Umar kuma buga tebur d'in dake gabanshi yayi tare da fad'in "kai." Da gudu ya tashi yabi bayanta mutanen kuma suka bishi da kallo, Ishaq abokinshi ne yayi murmushi ya kalli na kusa dashi yace "dama ace duk soyayyar da aka fara da qiyayya to tafi zafi." "Soyayya suke dama?" cewar mutumin. "Kai ai basai an fad'a ba kasan akwai soyayya wannan wajen, watakila basu fahimci hakan ba." "Lallai ko abokinka ya d'auko dala ba gammo, to ina had'in kifi da kaska? ai wannan qarmanje ne." "Ban gane ba, ita kasan meye ra'ayinta to da za kace haka?" Cewar mutumin "ai ko ban sani ba aikinta ya nuna abokinka baya da wani girma da qima a idonta, tunda nidai banga ko kallonshi tayi ba, zaifi ka bashi shawara ma tun wuri ya fitar da abinda ke ranshi, dan wahalar banza zaisha." "Ai kuwa in dai har gaskene, to wallahi zaka sha mamaki, dan kana nan zaune za'a gayyaceka daurin aure." "Tare dani dashi da kai za'a gayyata." cewar mutumin yana kama aikin gabanshi. Tana daf da shiga mota Umar Faruk ya fito da gudu, juyawa tayi ta kalleshi ta tsaya saida ya karaso, tsaye yayi ya kuma rasa me zaiyi sai yanzu yake jin haushin abinda yayi, juyawa yayi zai koma ciki tace "kazo ka tambayeni me nake ji ne?" Juyowa yayi yace "a'a, akan me?" Dogon tsaki taja ta bud'e motarta ta shiga taja tayi gaba, shima ciki ya koma yana tsananin jin takaicin abinda ya aikata, shin me yasa yayi haka??? ***************** Tun yamma da Mujaheed ya dawo gida mahaifiyarshi ta fad'a mashi halin da ake ciki tare da zigashi akan karya yarda, bud'ar bakinshi cewa yayi "Mama bama sai kince ba, wato ni zasu rainawa wayo ko? kafin ta zama ragowa ina biyarta amma tana wulak'anta ni, su kuma sun biye mata aka su ba zasu bata wanda bata so ba, yanzu kenan sun saduda ne shine za'a kawo min ita ni d'an iska ko, to wallahi basu isa ba." Tunda mahaifinshi ya dawo da dare suka sameshi da mahaifiyar tashi akan basu son wannan maganar auren, Baban baiji dad'i ba haka sauran matanshi guda biyu sun bada tasu shawara akan Mujaheed yayi hak'uri tunda yer uwa ce, amma mahaifiyarshi tace su rufe musu baki dan ba yayansu bane, an jima ana tattaunawa har saida Mujaheed yace in dai har aka takurashi wallahi zai shiga duniya, sanin halinshi da Baban yayi wanda dama ya ake dashi yanzu ma bare ya sake shiga wata duniyar, hakan yasa yace an fasa sai dai yana jin nauyin yanda zai fukanci d'an uwanshi. Ganin baida wata mafita yasa ya kira Papa a waya ya fad'a masa yanda sukayi cikin raunin murya, a zahiri Papa ya nuna babu komai amma da suka gama waya bak'in cikinshi ya bayyana, bayan ya shigo gida shima bai iya fad'awa Mamie ba saboda gudun matsala, amma kuma ya kwanta da wani sabon shirin a ranshi, safiya kawai yake jira ta waye ya gudanar dashi. _To Papa muji alkairi._ Kamar yanda Khairat tayi niyyar ba zata bari damuwa ta samu muhalli a zuciyarta ba, tunda ta dawo take d'akinta bayan tasha bacci ta tashi da yamma, da dare kuma tana d'aki tana tik'ar rawa abinta duk dan karta damu. Ko kari Papa baiyi ba ya fita Mamie bata sani ba Khairat kuma na bacci, hanya Papa ya d'auka shi da drivenshi cikin awa d'aya suka isa fadar shugaban....fan's ku k'arasa min _(bana son tabo mukamin kowa, amma ku kuyanke hukunci ku d'auka babban Muzaffar shine qarshe a mulki baban Khairat kuma na binshi baya)._ Tarba ya samu sosai a babban falon bak'i na palace d'in shugaban , hamshakin shugaban mai dattako cikin fara'a ya kalli Papa yace "sai kuma gaka da safiyar nan, kamar da wata matsala ko?" "Ba wata matsala shugaba, kawai dai nazo mu gaisane." "To da kyau, ya al'amura kuma da fama da jama'a?" "Alhamdulillah, ya naku k'ok'arin?" "Alhamdulillah." Shiru ne ya d'an biyo baya kafin shugaban yace "ya yarinyata da jiki, taji sauk'i ko? dan har yanzu bamu sake komawa ba." Dariya yayi yace "shugaba ai dan mun kwana biyu bamu had'u ba, amma Khairat taji sauk'i sosai." "Ah to alhamdulillah." Papa ne yace "ina Muzaffar? na kwana biyu ban ganshi ba." "Muzaffar ai yau kwananshi uku baya nan, na turashi saudi arabia dan halartar wani taro na qarawa juna sani akan yanda za'a inganta rayuwar matasa." "Da kyau shugaba, in da kake birgeni kenan, kowane abu kana azashi a muhallinshi, Allah ya taimaka ya dawo dashi lafiya." "Ameen ameen, fatanmu dai Allah ya mana mai kyau." Wani shirun ne ya sake biyo baya kafin shugaba yace "'yata dai tak'i yarona, da yanzu mun gama da maganarsu." Cikin dariya Papa yace "ah haba shugaba, taya zata k'i d'anmu, yanzu haka ma maganar aurensu ya kawoni, dan nayi tunani zamanta a gida haka yayi yawa sosai, kuma tunda suna fahimtar junansu naga zaifi kawai mu had'asu." Gyara zama yayi a cikin lunstumemiyar kujerar yana fara'a yace "haba dai, kai amma naji dad'i sosai da maganar nan." D'orawa yayi da "Muzaffar zaiyi farin ciki da wannan magana, gaskiya naji dad'i sosai, danni kaina burina bai wuce naga yayi aure ba." "Hakane shugaba, dan haka yanzu wuk'a da nama na hannunku, kasa lokacin da kaga ya maka." "Kuma dai? dad'in ai saiya mana yawa." "A'a wallahi baya komai, idan kunsa ranar ku fad'a mana, iyakarmu addu'a kawai." "Umm, to yanda mai zai hana asa nan da wata d'aya, tunda kaga akwai wani babban taro da za ayi 15 ga watan da za'a shiga, kuma dole mu dasu yaran duka zamu halarceshi, kaga zaifi dad'i suje a matsayin ma'aurata, koya ka gani?" "Hakan ma yayi daidai yallab'ai, Allah ya nuna mana lokacin da alkairi." A haka dai Papa ya baro gidan cikin farin ciki, take kuma shugaba ya dannawa Muzaffar kira, yana d'auka daga d'aya b'angaren yace "Papana ya kake?" "Daidai yarona, albishirinka?" "Nasan baka min albishir marar dad'i, goro fari tas Papana." "Yanzun nan Mani ya fita daga nan, kuma bai bar nan ba saida muka tsayar da aurenku kai da Khairat." "Wow, da gaske Papa? kai amma naji dad'i sosai, Papa yaushe kuka saka?" "Nan da wata d'aya, aiya maka ko?" "Sosai ma Papa, gashi dai Allah yayi zaifita zama mijin Khairat, to dan Allah Papa kuyi duk abinda ya dace kafin na dawo." "Karka damu yarona, yanzu zan shiga ciki muyi magana da mamarka akan yanda za'a tafiyar da komai." "yawwa Papana, a fara shirya komai kafin nazo, idan na zo zamu ci gaba da shiri, dan dole bikina da Khairat ya amsa duk gari a samu labarinshi, saboda kaga fa babbar yarinya ce nima kuma haka." "To shikenan karka damu." A haka suma sukayi sallama, haka ma a ciki ya fad'a ma mahaifiyar Muzaffar, sosai itama tayi farin ciki da alamarin dan a rayuwarta tana son bariki da tsare kai, hakan yasa Khairat ke birgeta sosai, dan lokuta da dama suna had'uwa a wasu tarurruka ta wakilci mahaifinta ita kuma ta wakilci shugaba, hakan yasa take sha'awar aurenta da d'anta. Lokacin da Papa ya dawo Mamie ta gama karinta tana tunanin in da ya tafi bata sani ba, ganinshi yasa ta mike tana tambayar lafiya, saida ya zauna yace ta zauna, zaune tayi tana kallonshi kafin yace "daga gidan shugaba nake." "Shugaba kuma? lafiya, wani abunne ya faru?" "Lafiya lau, akan auren Khairat ne." "Auren Khairat kuma? amma ba'a fasa ba?" "Eh, an fasa Mujaheed sai Muzaffar." "Muzaffar kuma, da gaske Alhaji." "Sosai ma, kawai ke dai kici gaba da shirye shirye, Khairat kuma zan fad'a mata nan da kwana biyu idan muka ga komai na tafiya daidai." "To Allah ubangiji ya sanya alkairi, Allah ya nuna mana ranar." Suna gama maganar Khairat ta fito da riga da wando farare tas ta zauna, "ina kwananku?" Kallon juna sukayi dan haka bata tab'a faruwa ba, amsawa sukayi Papa ya dora da "shalele kin tashi lafiya?" "Lafiya lau, Biba." ta d'ora da kiran Biba a qarshe. Da sauri Biba ta fito ta zube gabanta, cikin yauki tace "ki kawo min abinci na." "To Hajia." ta fad'a tare da tashi. Anan ta kawo mata ta fara cin abincin Papa kuma fita yayi gabatar da harkokinshi, Mamie ce tace "ki kammala cin abincin ki shirya zamu tafi dake gidan *Safiya*." Kallonta tayi tace "Mamie nifa kinsan bana son zuwa gidan nan, wannan d'an iskan yaron da yake min maganar banza wai yana sona, bana son ganinshi ma." Dariya Mamie tayi tace "ki shirya muje kedai, kinsan na jima banje ba, kuma yanzu nasan ba zai miki maganar soyayya ba." Kallon Mamie tayi danta fahimci me take nufi da abinda ta fad'a, maida kallonta tayi ga abincinta tana tunanin yanda za tayi rayuwa a cikin mutanen da take kewaye dasu ba tare data iya tuna abinda ya faru da ita ba. Da qyar Mamie ta lallabata ta shiga danta shirya, saida ta d'auki awa d'aya kafin ta shirya ta fito Mamie harta gaji da jira, a motar Mamie suka tafi tare da driventa suka nufi unguwar *yantala* (gidan Safiya diyace ga magajiyar mamar Na'ima, ma'ana cousine d'inta.), da sallama Mamie ta shiga gidan sab'anin Khairat dake binta kawai, da farin ciki matar ta taresu sai dai Khairat fuskarta a had'e take saboda hayaniyar gidan tayi yawa, saboda matan gidan hud'une yara kuma manya da qanana barkatai, haka suka shiga ciki suka zauna, matar ce ta fara gaishe da Khairat kafin tace "ina wuni." Wata matashiyar budurwa ce ta shigo ta kawo musu ruwa, Mamie ce tasha ita kuma ko kallo, dama Mamie ta mik'a mata girgiza kai tayi tana b'ata fuska, ganin Mamie na janyo hirar da zata sa su jima yasa ta mik'e tsaye tace "Mamie ki sameni a mota, ba zan iya zama cikin zafin nan ba." Safiya ce tace "gaskiyarki kam akwai fa zafi." Kallonta kawai tayi ta fice a soron gidan suka had'u da *Aqilu*, wucewa taje yi ya tare gabanta yana fad'in "ya dai, yau kece a gidan?" "Dallah matsa min a hanya." "Ina zuwa mana, magana nake so muyi." "Kar kace zaka min maganar banzan daka saba, dan bana da lokaci." Wata irin dariya yayi yace "wai maganar so kike nufi, ai wannan tsohon yayi ne, abinda nake son fad'a miki yanzu kuma shine, dan in gaya miki cewa na janye son da nake miki ne, dan ba zan...." Bai k'arasa ba tace "shashasha." Wucewa tayi ta barshi nan tsaye kafin ya ida shiga ciki.... 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana)_🤜🤛 *RABBANA ATINA FI-DUNIYA HASANA, WAFIL AKHIRATI HASANA, WAK'INA AZABAN-NAR.* 1⃣5⃣ Ba jimawa Mamie ta fito ta sameta a mota, suna fara tafiya ta kalli Mamie tace "kin fad'i gaskiya, Aqilu yace baya sona yanzu." Kallonta tayi tace "Khairat karfa ki fahimcini ba daidai ba." Murmushi tayi kawai ta fito da abin sauraronta ta manne kunnuwanta suka ci gaba da tafiya, suna isa gida ta nufi d'akinta bata kuma sake fitowa ba sai da aka fara kiran sallah magrib, har tayi zaune Mamie tace "ki tashi kiyi alwala kizo muyi sallah." Cike da nuna rashin jin dad'i tayi shiru, a tsawace Mamie tace "dake nake magana kina jina kinyi shiru." Ganin ta tashi ta wuce cikin kasala Mamie ta dora da fad'in "kuma wallahi ya zama na qarshe da zan miki magana akan sallah, inba rainin wayo ba kamarki shekara ashirin da biyar amma ba zaki iya gaishe da unangijiki ba sai kinga dama." *Wallahi a zamanin nan da muke ciki, matasanmu musamman yan mata bamu cika tsayar da sallah ba, musamman idan sunyi kwalliya a fuskarsu ba'a son asa ruwa a wanke, ya kamata muji tsoron Allah mu gane saida sallah ne muke iya banbanta kanmu da kafirai, Allah ka bamu ikon kyautata ibadunka, Allah kasa mu zama masu tsayar da sallah domin samun sassauk'an hisabi, Allah kasa mu tsayar da sallah domin ta zama abokiyar zamanmu a qabari dan haskaka makwancinmu.* *Da sallah ne muke cika cikakki musulmi, idan sallanmu tayi kyaune ake kyautata mana zaton sauk'in hisabi, sallah itace take tayamu zama a qabarinmu kafin lokacin da za'a tashi qiyama, sannan mai tsayar da sallah ko a cikin al'uma zaka ga fuskarshi na annuri, sannan hadisi ne ingantance cewar wuta bata tab'a duk wata gab'a da take samun ruwan alwala, wannan 'yar qaramar tunatarwa ce badan na fiku sani ba.*👏 Babu wata matsala a game da alwalarta sai dai a game da sallah kam akwai yar mishkila, saboda cikin minti biyu ta gama sallah ta fito falo, hakan yayi daidai da fitowar Papa zashi makaranta, ganin littafi a hannunshi yasa tace "Papa sai ina kuma?" Kallonta yayi yace "majlisin malam zani d'aukar karatu." "Toh , Papa karatu aka koma?" "Eh 'yata, kuma kema kin kusa komawa insha Allah." Wata dariya tayi ta nufi fridge tana fad'in "wasa kake Papa, haka dani na shiga makaranta." Papa ma wucewa yayi dan lokaci nayi yana fad'in "ba'a girma da neman ilimi, tunda ki kaga na fara zuwa to kema ki shirya dan kin kusa." Yau ma dai kamar kusan kullum ita kad'ai taci abinci bayan iyayenta sunci, tana kammalawa ta koma d'aki tana chat tana sauraron waqoqi har dare yayi sosai tana bacci cikin kwanciyar hankali. Mamie ce ta shigo d'akin ta zauna kusa da ita, ta jima tana kallonta tana murmushi kafin ta tofa mata addu'a ta sumbaci goshinta, zani taja mata ta rufeta ta tashi saida ta kashe mata wutar d'akin kafin ta fita, tun fil'azal Khairat bata bacci da duhu a d'aki hakan yasa ma bata kashewa. Kusan abune daya zamar mata jiki mafarkin abinda ya faru da ita, kamar a zahiri haka ta dinga tuna lokacin da take kokawa da Musa har lokacin da yayi nasarar kutsa kanshi a tsakiyar matancinta, razananniyar qarar da tayi a mafarkinta itace ta bayyana har a zahirin baccinta. "Ahhhhhhhhh, Mamiena, Papa wayyo Allah, Papa, Papa zasu kasheni, Papa gasunan fa, zasu sake min fyad'e, dan Allah kuzo ku taimakeni, Mamie, wai baki jina ne? wallahi gasu nan." Wannan duhun d'akin shi ya qara firgitata haka ta dinga kiran su Mamie da Papa, kasancewar d'akinsu a qasa yake hakan yasa basu ji da wuri ba, Mamie ce ta fara ji ta tayar da Papa, a sukwane suka shigo d'akin nata Mamie ce ta kunna wuta Papa kuma ya tunkareta, tana ganin haske ya mamaye d'akin tayi saurin rarrafowa ta nufo Papa, fad'uwa tayi wajen tahowa Papa ne yayi saurin tashinta ya rumgumata a jikinshi yana shafa kanta yana fad'in "shiiiiii, shalele, gani nan Papanki ne kinji, ya isa haka." A haka suka taka ya qarasa da ita bakin gado suka zauna yana ci gaba da fad'in "ya isa kinji gimbiya, ba kowa anan, d'ago idonki ki gani, nine Papanki da kuma Mamienki, ki nutsu kinji." A hankali kuwa ta daga ta kalli Papa sannan ta kalli Mamie dake gefenshi, da sauri ta kamo hannun Mamie ta sake fashewa da kuka tace "dan Allah Mamie ki kwanta anan, wallahi zasu iya dawowa su sake min fy......" Mamie tayi saurin rufe mata baki. A haka suka ci gaba da rarrashinta har Mamie ta d'ora kanta a qafafunta bacci ya d'auketa, a zaune Mamie ta kwana tana shafar kanta tare da mata addu'a. Suna a haka Papa ya shigo ya tashesu suyi sallah asuba, tare da Mamie sukayi sallah sannan Mamie ta sauka ta shiga madafa, Papa na zauna yana hutawa a lambu tare da linttafinshi yana bitar karatu wayarshi tayi qara, ganin mai kira yasa ya rufe littafin ya d'auka, bayan sun gama a sukwane ya shigo cikin falo yana kiran sunan Mamie. Da sauri ta fito tana fad'in "gani Alhaji, lafiya dai irin wannan kira haka?" Cikin karsashi yace "lafiya lau, albishirinki?" "Goro." ta fad'a tana masa kallon tuhuma. "Yanzu mukayi waya da shugaba, kuma tabbatar min suna so ayi komai a gama, dan haka goben nan zasu kawo lefen Khairat." Cike da tsantsar farin ciki tace "kai, Alhamdulillah, amma naji dad'in wannan albishir, Allah ya nuna mana goben yasa alkairi." "Ameen, yanzu kije ki lissafa mana duk abinda za'a buqata dan tarbar bak'i, tunda kinsan fa harkar babba ce." "Ah sosai kam, kar kaji komai, ba buk'atar kashe kud'inka, ni zan d'auki wannan nauyin insha Allah." "Kenan dai bikin Khairat na nad'e hannayena nasha kallo?" Cikin dariya tace "a'a ba duka ba, dole ai kasan zamu shiga cikin aljihunka idan biki ya matso." "To shikenan, Allah ya kaimu." 💃💃💃💃💃💃💃 Misalin 11:35 Khairat ta tashi ta fito falo, Mamie na madafa tare da masu kama mata aiki, cikin takon mai nuna magagin bacci ta shiga madafa, ma'aikatan ne suka gaisheta amma babu wanda tako kalla bare ta amsa, wajen kayan lambu ta nufa ta d'auki kokomba ta wanke ta fara kaiwa bakinta, sai lokacin ta kalli Mamie tace "ina kwana Mamie." "Lafiya k'alau, kin tashi lafiya." "Um." ta fad'a tare da fito ta koma d'akinta tayi wanka ta shirya cikin riga da siket na kanti kanta ba d'an kwali ta fito falo ta zauna, 12:30 su Mamie suka kammala abincin rana, jerawa sukayi a dinning sannan Mamie ta shiga wanka, 13:00 Papa ya shigo gidan tare da sabin masu tsaron lafiyarsa su biyu, suma da qyar ya yarda aka had'ashi dasu. "Sannu." cewar Khairat. Kallon teburin yayi sannan yace "sannu shalele, an gama abinci." Tana kallon wayarta tace "umm , sun gama." Hannunta ya kamo yana fad'in "muje ki zuba min naci gimbiya, yunwa nake ji sosai." Itama cewa tayi "amma ai ban iya zubawa ba, bari na kira Biba ko Saude su zuba maka." "A'a nike nake so ki zuba min." ya fad'a yana zaunawa. Kallonshi tayi ta kalli kwanukan abincin ajiye wayarta tayi a gefe zata d'auki plate wayar Papa tayi qara, d'auka yayi yana fad'in "hello, manager har kun karaso ne?" Jim yayi na d'an lokaci kafin yace "to ku shigo kawai ina ciki nima yanzu na shigo." Aje wayar yayi ya kalli Khairat yace "wallahi wani hazik'in matashi ne aka samu a masana'antarki, baifi wata biyar zuwa shida da fara aiki ba, amma harya fito da sanfirin takalmin da suka karb'u a duniya, shine nace manager ya kawoshi nan mu gaisa na kuma masa godiya, sannan zan shirya masa qarin girma a ma'aikatar." Ko qala ba tace ba, kwanon farar maca ta bud'a wacce tasha kwalliya da waken gwangwani, cokali ta d'auka ta fara k'walbatowa rabi na zubewa qasa rabi na shiga plate d'in, da qyar ta zuba a plate d'in har Mamie ta fito ta samesu, kwanan miya ta bud'e wacce tasha kaji daga-daga, (😁mutuniya ba) tana saka cokalin miyar ta fallatso mata sai a ido, qara ta saki tare da sakin cokalin a miyar, sake fallatsowa yayi sai kuwa a fuskarta da jikinta, zafin da taji yasa ta dinga tsala ihu tana fad'in "na k'one , na k'one, zafi Mamie ki goge min." Mamie da hankalinta ya koma kan manager da matashin saurayin nan, Umar Faruk daya tsaya ya kasa gudawa yana kallon Khairat na tsalle tsalle duk jikinta na kadawa, da qyar ya had'e yawu suka fara takawa suka zauna inda Papa ya nuna musu, sai lokacin Khairat tayi shiru ta sauke idonta akan Umar Faruk. Kallonshi take sosai shi kuma ya d'auke idonshi daga kanta, Mamie ce ta katseta da fad'in "ki zuba musu abinci mana shalele." Da sauri ta kalli Mamie, da ido ta mata alama ta zuba musu, turo baki tayi gaba tace "nifa Mamie ban iya ba, kina gani abinda ya faru yanzu na k'ona kaina." Wayarta ta d'auka ta juya zata bar wajen Papa yace "gimbiya baki zuba min ba." Lokacin data juyo idonsu suka had'u dana Umar yana mamakin abinda ta fad'a wai bata iya zuba abinci ba, to kenan ya zata dafashi??? ya tambayi kanshi. Zagayawa tayi wajen da yake zaune ta mik'a masa hannunta tace "zo." Da mamaki yake kallonta yana mamakin fitsararta, kallon Mamie da Papa tayi wanda suma ita suke kallo tayi murmushi tace "kunyarku yake ji fa." Kallonshi tayi tace "kaga ka taso magana za muyi da kai." Tana fad'a ta ja hannunshi suka nufi d'akinta, tana shirin bud'a k'ofar d'akin ta tsaya cak saboda ji da tayi ya qara matse hannunta, kasa juyowa tayi saboda yanda taji tattausan hannunshi ga kuma gabanta daya fad'i, a hankali ta fara zame hannunta daga nashi shi kuma baisan ya akayi ya kasa rik'e kanshi ba harya qara matse hannunta, saida ta raba hannunta da nashi sannan ta ta bud'e d'akin ta shiga, kallonshi tayi ganin yaki shigowa, alama ta masa da ido akan ya shigo, a hankali yake takawa yana jin bugun zuciyarshi na k'ara tsananta, da sauri ya juya ya kalleta saboda ganin ta rufe k'ofa. Gabanshi ta tsaya tace "ranar na tambayeka amma baka bani amsa ba, amma daga baya sai nayi tunani naga cewa, ai ko ban tambayeka nasan kai kana daga cikin mak'iyana, kuma kayi farin ciki da abinda ya sameni, kuma nasan ko kai ka samu dama zaka iya yin abinda wad'ancen sukayi." "To ba komai, kuma ku sani ni Khairat ba zan nuna gazawa ba, ba kuma zan nuna bana da daraja ba, kamar yanda ba zan saka damuwa a raina ba, dan haka duk mai bak'in ciki sai dai ya mutu." Wucewa tayi ban d'aki tana fad'in "zaka iya tafiya." Shi kuma ya kasa komai gaba d'aya ji yake yayi sanyi ya rasa duk kuzarinshi, binta yayi da kallo ya kasa fita, Khairat ce daga ciki ta jefo da gaba d'aya kayanta data cire harda qananan ciki saboda bata tunanin yana nan har yanzu, yana ganin haka yayi saurin juyawa zuciyarshi kamar zata fito daga qirjinshi, saurin fita yayi daga d'akin hannunshi a kan saitin zuciyarshi a hankali yake takawa yana tambayar kanshi. _Me yasa nake jin haka idan na ganta?_ _Me yasa na rasa duk wani k'arfi na dana tsaya gabanta?_ _Me yasa gabana ke fad'uwa idan na tuna koda sunanta?_ _Me yasa nake jin daban a tare da ita?_ 😛😛😛😛😛😛 _no amsa._ Khairat na sakar ma kanta ruwa ta lumshe ido, da sauri ta bud'e idonta saboda ji da tayi kamar hannun Umar Faruk a nata hannun, ajiyar zuciya ta sauke ta sake rufe ido saboda yanda ruwa ke sauka a kanta, Umar Faruk dai ta sake gani yana mata wannan kallon da fassararshi sai _my aunty Aishan Umma_, haka ta fito daga wanka wannan tunanin ya kasa barin qwaqwalwarta harta d'auki riga da wando ta saka qanana sannan ta sake fitowa. Tare suka ci abinci dasu banda Umar Faruk da ruwa kad'ai yake d'an kurb'awa suma sai Papa ya mishi magana, anan Papa ya masa godiya tare dasa albarka sannan yace "kaci gada da k'wazonka, insha Allah za kayi nasara a duk inda ka samu kanka, Umar Faruk..ko?" Cikin murmushi yace "eh, *Umar Faruk Ahmad Adam*." Da mamaki Papa ya kalleshi yace "Ahmad Adam, kai d'an malam Ahmad ne?" Shima da mamakin ya kalleshi yace "eh ni d'ansa ne." Mamie Papa ya kalla yace "Allah sarki, kinga fa yaron nan d'an malamin da nake d'aukar karatu wajenshi ne, haba shi yasa ka zama mai hazak'a da basira." Dariya Mamie tayi tace "yaron kirki ne kam, Allah ya maka albarka." Kiran daya shigo wayar Khairat ne yasa ta tashi daga wajen, Mamie ce tace "baki ci komai ba fa tun safe." Juyowa tayi tace "Muzaffar ne yake kira, ina zuwa." Mamie da Papa ne quka kalli juna suna murmushi, sabanin Umar Faruk da gabanshi ya buga ranshi kuma ya b'ace, cup d'in ruwa ya d'auka ya kifa saida ya shanye sannan ya mik'e yace "ni zan wuce, na gode." Ficewa yana jin tsanar Muzaffar a zuciyarshi ba tare da sanin shi Muzaffar d'in ba, kasa jiran manager yayi dan haka ya tari taxi ya mayar dashi ma'aikata, haka ya isa ya zauna yana kallon tafin hannunshi da Khairat ta rik'e, wani hamshak'in murmushi ya saki saboda tuna da yayi lokacin da take tsalle tana ihu, sake fashewa yayi da dariya haka kawai ya rasa dalili amma farin ciki yake ji har k'ark'ashin zuciyarshi, Ishaq daya lura da hakane ya tab'oshi ta gefe yana fad'in, "Da alama fitar nan tayi kyau ko?" B'ata fuska yayi yace "ban gane ba, kai baka san ina muka je bane?" "Na sani mana, amma naga ka cika dariya kai kad'ai." "Son gulma ko? to ba zaka ji ba." Dariya Ishaq yayi ya maida hankalinshi ga aikinshi yana fad'in "da alama ka fad'a soyayya abokina." Da k'arfi ya kalleshi yace "me? soyayya fa kace? to aini dama ba sabon shiga bane, ko ka manta ina da Zuby?" Saida Ishaq ya kalli k'wayar idonshi yace "watak'ila yanzu ne ka fad'a soyayyar gaskiya kuma wacce ta dace, idan kuma ba haka to zai iya yiwuwa yanzu ne zuciyarka ta kamu da so." "Son wa?" "Son Khairat mana." Ishaq ya fad'a. Sake kallonshi yayi dan baiyi tsammanin yaji abinda yace ba a fili, zunbur ya tashi daga wajen ya fita filin ma'aikatar, maganar Ishaq ce kawai ke dawo masa a qwaqwalwa ta cewa "son Khairat mana." A zafafe ya furta "ina, hakan ba zai yiwuba, bata dace dani ba, zuciyata ba zata tab'a min wannan rashin adalcin ba." _Aikin gama ya gama_😛. *Team Khairat, ku fito muyi rawa*💃💃💃 Daga yanda Muzaffar yake wa Khairat magana yasa ta fahimci akwai wani dake faruwa, musamman da yace ya matsu gobe tayi a kawo kaya a tabbatar mishi ita tashi ce, kashe wayar tayi ta dawo falon lokacin manager ma harya tafi, tsaye tayi gabansu tana kallonsu tace "me yake faruwa? me Muzaffar yake fad'a?" Papa ne yace "kinga shalele ki zauna kici abincinki , an jima za muyi magana." Cikin d'aga murya tace "wane naci abinci bayan abinda wannan mahaukacin yake fad'a, kawai ku fad'a min koma miye naji." Mamie ce ta d'aga murya itama ta tashi tsaye tace "Khairat!!! mu kuke d'agawa murya? kece kika haifemu ko mune muka haufeki? idan bamu fad'a miki ba me za kiyi?" Kallon Mamie tayi fuska ba annuri tace "maganar aure yake, kuma nasan kinsan babu wanda zai min aure ba tare da ina so ba, idan alk'awarina kuka mishi to ku janye danni ba 'yar roba bace da za'a min haka." Zata wuce Mamie ta fizgota da k'arfi za tayi magana Khairat ta fizge hannunta da k'arfi tana fad'in "ki sake ni, karki sake tab'ani, ki fita a harkarta." Duk da qoqarin b'oye hawayenta kasawa tayi saida kukan ya k'wace mata ta fara magana cikin kuka "na sani kuma dake iyayena kuna ganin yanzu bana da wata kima da daraja ta 'ya mace, inba haka ba babu ta yadda zaku fara min maganar aure ba tare da sanina ba.: Wucewa tayi ta barsu nan Papa kuma ya kalli Mamie cikin b'acin rai yace "....😁 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Wallahi har qasan raina ina jin dad'in addu'arki sister Alawiyyah, gaskiya ke ta dabance, samun fan's irinki abin alfahari ne kuma burin kowace marubuciya, duk da soyayyar da kike nuna min bata isa ba saida kika nunawa my Heenat d'ina itama tata soyayyar, lallai muna yinki over, luv u dear.😘_ _My aunty *Aishan Umma* ina mik'a godiyata sosai a gareki, kinsa naji cewar ni mai sa'a ce a rayuwa😊 muna alfahari dake a matsayin shugabar k'ungiyarmu._ *Welcome Back my 🅱K.*🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣6⃣ "Wai me yasa kike wa yarinyar nan haka, akan me zaki dinga d'aga mata murya, me yasa kika cika b'acin rai ne Na'ima?" "Au, nice ma na daga mata murya kenan? kai yanzu baka ga abinda tayi ba? wai me yasa kake hakane? Khairat fa 'yarmu ce mu muka haifeta ba ita ta haifemu ba, to akan me zata dinga tsaya gabanmu haka tana fad'a mana abinda ranta yake so?" Tsaye ya mike yace "koma dai miye kinsan muna da laifi, kamar Khairat ace mun tsayar da maganar aurenta ba tare da saninta ba a wannan qarnin da muke ciki, kinga dole ranta ya b'ace." D'akin Khairat d'in ya nufa yana ci gaba da mita, tundada ta shiga d'aki ta kwanta kan gado tana kuka, jin kanta na sarawa yasa tasan yanzu zai fara mata azababben ciwon daya saba, tashi tayi da nufin d'auko magani tasha amma bata kai ga wajen ba jiri ya d'ebeta ya yadda, rintsegudu ido tayi ta dafe kanta sosai tana fad'in "wayyo Allah kaina, kaina zai fashe, kaina Papa ciwo yake, dan Allah kazo kai kad'ai ke sona, Papa kaina zai fashe, wayyo, ahhhh, wash." Papa na shigowa ya ganta kwance a qasa, da gudu ya k'arasa wajenta yana tambayar "shalele lafiya, meya faru, kanne ke ciwo halan?" Kamata yayi ta tashi ya taimakata ta zauna akan gado yana fad'in "wallahi shi yasa bana qaunar abinda zai b'ata miki rai saboda irin haka." Da sauri ya nufi wajen maganinta ya d'auko ya kawo mata tare da ruwa ya taimaka mata tasha, kwantar da ita yayi yana fad'in "kwanta ki huta kinji." Kai ta girgiza har yanzu hannunta na saman kanta tana matsewa tace "dan Allah Papa ka d'aure min kaina fashewa zaiyi, ka taimaka ka d'aure min dan Allah." Ya tashi kenan zai bud'a kayanta Mamie ta shigo d'akin, wata harara ya dalla mata dan ranshi ya b'ace sosai, kayan ya bud'a ya d'auko wani qaramin gyalenta ya dawo ya zauna kusa da ita ya d'aure mata kan sosai, sake cewa tayi ya d'aure mata sosai, shi kuma yana ganin ya d'aureshi qwarai haka ya sake tamke mata kan, duk da haka ba sauk'i Mamie dake tsaye tana kallon yanda jijiyoyin kanta suka fito sai harbawa suke kai kasan ba qaramar azaba take ji ba, cikin muryar kuka tace "dan Allah Alhaji ko zamu fita da yarinyar nan waje ne, kasan fa babu kyau ciwon kai ga 'ya mace? gaskiya ni ina jin tsoro." Wata tsawa Papa ya daka mata ba tare da saninshi ba "dallah rufe min baki, duk waya janyo yanzu in ba ke ba, ke wai har abada ba zaki iya mu'amulantar yarinya da kyakywar mu'amula ba, sai hushi kawai na banza da wofi, to idan kika kasheta ai kinga saiki huta, kinsan dai ba zaki sake haihuwa ba har abada dan mahaifar ma baki da ita, ni kuma wallahi aure zanyi da ba zan zauna ba magaji ba." Kasa hak'ura tayi da abinda ya fad'a saida tace " to kayi auren mana saime? nace saime idan kayi aure? namiji goma aiba uba goma bane, wato ka lalata min rayuwa yanzu kuma burinka kenan na rasa 'yar tawa guda d'aya kai kuma kayi aure, to wallahi baka isa ba, yanda ka b'ata min rayuwa kaima a haka zaka tabbata ba d'a ba jika." Tsaye ya mike "ni kike fad'awa haka Na'ima, waike me yasa baki da kunya? yanzu a gaban 'yarki kike fad'a min haka? kenan tarbiya ce kike so ta d'auka a haka?" "Kai tarbiyarce kake so ta d'auka daka fad'a min abinda ka fad'a min, kasan kaine silar lalacewar mahaifata, to miye na fad'a min wai zan kashe 'yata?" "Dallah ni kimin shiru a wajen nan kona tattakaki." "Naki nayi shiru, kayi abinda za kayi mana, an fad'a maka tsoronka nake ji? aini dama nasan ba tuban gaske za kayi ba, kawai dai parpaganda ce irin taku 'yan siyasa." Tatsssss, Papa ya d'auketa da gigitancen mari yana fad'in "ke har kin isa kici mutunci na, wallahi bari gani ina d'aga miki qafa, ruwane suka daki babban zakara wallahi, idan kuma kinfi son in dawo Mani na nada to mu zuba dani dake." Dauke hannu tayi daga kunci tace "ka dawo Mani mana dama ai baka canza ba, kuma da kake maganar mutunci, kai har mutuncine da kai da za'a ci? kuma wallahi ka sake dukana ramawa zanyi, tunda ni ba jaka bace." Nunata yayi da hannu yace "kici albarkacin 'yarki dake kwance a wurin n...." bai k'arasa ba saboda ganin Khairat zaune tana kallonsu kamar ba mai ciwon kan nan ba. Kunya ce ta tureshi dan baiji dad'in abinda ya faru ba ko kad'an, kawai ta kaishi bangone, zai zauna a kusa da ita kenan ta fashe da kuka tace "karka zauna, dan Allah ku fitar min daga d'aki, ku barni zanci gaba da ratuwata a haka, ba zaku tab'a sauyawa ba saboda ya riga daya zama jikinku, ba zan iya zama daku na minti d'aya ba ba tare da kun samu sab'ani ba, ku fita dan Allah, zan kula da kaina ko bakwa nan." Papa ne ya sake marairaicewa yace "shalele ki saurare ni kiji." "Bana son jin komai, ku fita kawai." Jiki a sanyaye suka fita, amma tana jinsu ko nisa ba suyi ba Papa ya fara tuhumar Mamie akan ita ta janyo komai, haka suka jima suna wannan fad'an harya fita ya bar gidan, Khairat kam turmutsutsu ta dinga yi saman gado tana tusa kanta pillow saboda rad'ad'in da yake mata. *Wallahi yan uwa akwai iyayen da basa iya rik'e b'acin ransu, ko a ina ko a gaban waye idan ransu ya b'ace sai suyi musayar yawu, wallahi iyaye muji tsoron Allah, dan dole zamu tsaya a gabansa kuma mu amsatambayoyi.* *Yana da kyau ace ke uwa mace kina da hak'uri fiye dana namiji , domin kece mai tarbiyar yara maza da mata, idan ranshi ya b'ace ke kiyi hak'uri ki taushi naki b'acin ran, yara tun suna qanana suna lura da zamantakewar iyayensu kuma hakan nada tasiri a rayuwarsu sosai, wannan d'an qaramin jan hankali ne, Allah ya bamu ikon kiyayewa, ameen.* ***************** Umar Faruk ne da Zuby suke waya, amma shirunshi yayi yawa ba kamar kullum ba, tunanin Khairat da lokacin data rik'e hannunshi kawai yake yi, ga kuma tuna abinda Ishaq ya fad'a, a hankali ya saki wani tattausan murmushi daya bayyanar da kywunshi, sannu sannu ya bud'a bakinshi ya furta kalmar " *shalele*". Wani murmushin ya koma saki, muryar Zuby ce ta katseshi da tace "yau kuma sabon sunan na samu?" Dawowa yayi tunaninshi, cikin rashin gaskiya yace "e..e...eh mana." Shi kuma harga Allah sunan daya ji Papa y kira Khairat dashi ne ya maimaita, cikin sauri yace "am kina ji? zan sake kiranki." Yana fad'a ya kashe wayar tare da fad'awa duniyar tunani, ya jima a wannan halin kafin ya fara magana da kanshi "haba Umar Faruk, ka dawo hankalinka mana, wannan fa bata dace kai ba ko kad'an, me yasa kake damun kanka a kanta? ko ka manta wacece ita? kai da ita fa kamar mota da jirgin sama ne." "Kai kana son mace mai kunya, ita kuma bata da kunya, kai kana son mace mai kamun kai da aji, ita kuma sai ajin amma ba kamun kai, kana son samun mace wacce zata kula maka da mutuncinta ko bayan idonka, amma ita ko a gaban idonka ma zata zubar maka dashi bare kuma bayan idonka, kana son mace mai ilimin addini, amma baka da tabbacin sahihancin addininta, kai namijine mai kishi, ita kuma ta riga da tayi tallar surar jikinta a waje kowa ya gani, bugu da qari baka da tabbacin ita d'in saliha ce tun ma kafin a mata fyad'e, dan haka ka fita a harkarta daga tunaninta ma haka." 🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂ Sai dare ciwon kan ya lafa mata amma kuma bata fito ko falo ba bare farfajiyar gidan, tana d'aki zamanta tana sauraran waqoqinta, Papa ma yayi yayi ta fito taci abinci amma tak'i, dole sai nan aka kawo mata shima bata ci wani mai yawa ba sosai kamar yanda ta saba, daga nan kuma bacci ya d'auketa. *Washe gari* gidan an tashi anata qoqarin shirin tarbar bak'i, Khairat na bacci Papa yasa Mamie ta tasheta, dan dole tasan halin da ake ciki, tana bud'a ido taga Mamie kawai ta tashi ta shiga ban d'aki tayi wanka, ta jima kafin ta fito ta shirya cikin rigar shadda dan fita take so tayi daga gidan, falo ta fito da gyalenta a kafad'a da jakarta a hannu, tana shirin kaiwa k'ofa Mamie ta fito daga d'akin Papa, a hanzarce tace "Khairat." Tsayawa tayi amma jiyo ba, Mamie ce tace "Papanki ke kiranki?" Saida ta sauke ajiyar zuciya sannan ta juyo bata yarda sun had'a ido da ita ba kawai ta nufi d'akin Papan. Kamar yanda bata saba ba haka yanzu ma ta shiga d'akin ba sallama, zaune tayi bakin gado saboda Papa na zaune a d'aya daga cikin kujerun d'akin, kallonshi take tana jiran taji me zaice Mamie itama ta shigo ta zauna gefenta, babu wanda ya kalli wani bare suyi magana har Papa ya gyara murya yace.... "Khairat." Jin yanda ya kira sunanta kuma yayi shiru yasa dole ta amsa da "na'am." Kallonta yayi yace "waye ni a wajenki?" Da mamaki ta kalleshi tace "mahaifina." "Da kyau." Nuna Mamie yayi yace "wannan kuma wacece ita?" Kallon Mamie tayi tace "mahaifiyata ce." Nan ma jinjina kai yayi yace "yayi kyau." Sannan ya d'ora da "a tunani da hankalin da Allah ya miki Khairat, nasan kinsan iyaye suna da daraja sosai, hakane?" "Hakane." "Shin kina ganin mun kai matsayin da zamu iya yanke miki hukunci daya shafi rayuwarki ba tare da saninki ba, ko kuwa dai dole sai mun nemi izininki kafin mu nuna mu iyayenki ne?" "Zaku iya mana, idan ba zai tauyeni ba." "Ba wannan nake son ji ba Khairat, zamu iya ko ba zamu iya ba?" "Zaku iya." "To Alhamdulillah." "Khairat, yau za'a kawo kayan lefenki daga gidansu Muzaffar, mun amince a matsayinmu na iyayenki, kuma muna da yak'ini akan ba zaki bamu kunya ba." Tsaye ta mik'e tayi wata dariyar yan daba tace "nasan dama za ayi haka, yanzu me kuka daukeni da har zaku yanke wannan hukuncin a kaina? taya zaku had'ani da mutumin da tsarina da nashi ma daban ne? ni bana son Muzaffar kuma ba zan aureshi." Jakarta ta dauka zata fita Papa ya daka mata tsawar da tasa ta tsaya wuri d'aya "ke Khairat, ina magana kina magana, maza wuce ki zauna magana nake dake." Sum sum sum ta koma ta zauna Papa ya dora da "a tunani mummunar kalma bata tab'a shiga tsakanina dake ba, amma ki sani Khairat idan har kika shirya bani kunya da tozartani, to hakika zaki fara jin kalma marar dad'i ta fara fitowa daga bakina kuma a kanki, bana fatan na tsine miki albarka, amma dai ba zaki ji dad'in abinda zai fito daga bakina ba, ke ba yarinya bace kin isa aure har kin wuce ma, burinmu shine mu kaiki d'akin mijinki kema." "Khairat, dubi mahaifiyarki ki gani." Kallon Mamie tayi ta kalli Papa shi kuma yace "burinta kawai taga aurenki, kullum cikin fargaba take a kanki, saboda yanda take son taga kinyi aure Khairat har rabuwa tayi dani kuma ta dawo, yanzu haka mahaifiyarki wata d'aya ta bani dan na aurar dake, idan kuma ba haka ba to zamu rabu kuma rabuwa ta har abada, yanzu ki fad'a min Khairat." "Shin kina son muci gaba da zama ni da mahaifiyarki, ko kuma kinfi son mu rabu?" Shiru tayi tana tunanin mafita, tabbas bata son Muzaffar saboda basu dace ba, amma kuma ba zata yarda iyayenta su rabu ba saboda maganar aurenta, dan haka ta samawa kanta mafita, a hankali ta kalli Papa tace "in dai wannan shi zai saku farin ciki, tona amince." Tana fad'a ta sake d'aukar jakarta zata fita Mamie tace "da gaske kike Khairat?" Kura mata ido tayi tana kallon tsantsan farin cikin dake fuskar Mamie kafin tace "eh Mamie, na amince." Juyawa tayi Papa yace " ina zaki je kuma?" Danne zuciyarta tayi ta qaqaro murmushi tace "yau fa za'a kawo kayana Papa, ai bai kamata na zauna gida ba har sai kowa ya ganni." Dariya suka saka mata dukansu itama ta wuce tana dariyar, yayin da suka bita dasa albarka, tana fita motarta ta shiga ta fara tuk'i kuma Mamie ta kirata, tana d'auka tace mata "shalelen Papa, dama cewa nayi me zai hana kije gidansu *Hibba*, kinga saiku zauna acan tunda mahaifiyarta ma nanan zuwa nan d'in." "Ok, zanje." tana fad'a ta kashe wayar Mamie kuma tayi murmushi. A hanya ta kira k'awayenta *Rashida, Sarina, Farida, Mamy* akan su sameta gidansu Hibba, duka suka amsa kiranta dan sun san akwai labari, hannun riga sukayi da Mamar Hibba hakan yasa basu gaisa ba, kafin su Rashida suzo ta fad'a mata abinda ke faruwa, dan ita kad'ai ke bata shawarar data dace, yanzu ma sake jadadda mata tayi tabi iyayenta, sannan ta nunawa Muzaffar kamar tana sonshi har tayi nasarar samun soyayyarshi ta gaskiya, tunda shi ya fad'a da bakinshi ko da ranar darensu na farko ne bai damu ba dan sun rabu, haka ta bata shawarwari masu kyau, sannan su Rashida suka zo. Tana fad'a musu za'a kawo kayanta suka saka shewa da murna dan sun san babban bidiri ne, nan suka wuni har Muzaffar ma ya kirata yana tambayarta abubuwa da zasu shirya, kamar yanda Hibba ta bata shawara akan tayi dan ta b'oye sirrin zuciyarya sosai, ta fad'a mishi bata gida za suyi shawara da k'awayenta idan taje gida saita fad'a masa yanda sukayi dasu, a haka sukayi sallama su kuma suka ci gaba da shirye shiryensu. *A gida* kuwa Mamie farin ciki take sosai hakan yasa suke ta kujuba kujuba, 'yan uwa mak'ota da mutanen arzik'i tuni suka cika gidan, hada hada kawai ake an soya na soyawa , an gasa na gasawa , an dafa na dafawa , an motsa na motsawa haka ma na jik'awa an jik'a. *16:35* unguwar ta shaida bak'i sun shigo cikinta, jiniya kawai kake ji na motocin matan manya uwa uba ga mahaifiyar Muzaffar da kanta tace ba za'a barta a baya (abinka ga 'yan bariki.😁), motoci ne ba adadi suka tunkaro k'ofar gidan kama daga na matan manya da abokan arzik'i, sai kuma na abokan Muzaffar duk da baya gari amma sun masa kara, abinfa ba'a cewa komai ba'a kuma ga komai ba, saida masu tsaron lafiya suka fara bud'e motoci manyan mata na fitowa daga ciki. Dala tayi kuka a wajen harka ta girma ce akayi sosai, sai dai wata matashiyar mota kyakyawa wacce aka shiga da ita har farfajiyar gidan, masu tsaronne suka dinga fito da akwatina kowace mak'il da kaya d'aya d'aya har dozin biyu da rabi, ga kuma wannan mota da aka azo akan lefan. Ciki aka shiga masu gulma nayi masu saka albarka na sakawa masu d'aukar photuna suna d'auka, acan kuwa na hango muku Mamar Mujaheed 🤣ta rumgume jakarta tana kallon manyan mata suna yagar kaji da qafafun rak'umi 😁, haka dai aka ga abin arzik'i tari guda sannan aka sake tsayar da ranar kwana ashirin da biyar ya rage. ************** Tunda Khairat ta dawo gida taga kayan ita kanta taji dad'i, dan burinta kenan ta samu babban mutum ta aura, bata wani kalli kayan duka ba kwai ta shiga d'aki tayi wanka tasa kayan bacci sannan ta kwanta dan bacci take ji. *Washe gari* da safe kiran Muzaffar ne ya tasheta, cikin magagin bacci ta d'auka ta aza a kunne da fad'in "hello." "Amaryata, kuma uwar gidana, ina fatan kin tashi lafiya?" Sai lokacin ma ta tuna shine fa wanda zata aura, zaune tayi tace "lafiya lau, ya kake?" "In dai kina cikin k'oshin lafiya, to ai nima haka nake." Tashi tayi ta fara rage kayan jikinta tace "ok, to yanzu zaka min uzuri na shiga bayi, dan tashina kenan." Cikin shagwab'a yace mata "amma fa muryarki nake so naji." A hassale tace "muryar lafiya, tashina fa kenan, so kake nayi fitsarin anan? haba nifa bana son irin haka." Ji tayi ya fashe da dariya yana fad'in "ashe fitsari kike ji, kinga kuwa da zaran munyi aure, da kaina zan dinga jaye miki fitsarin nan😛." Da sauri ta wani qaqaro amai tana fad'in "kai, wannan qazamtar fa? kaga sai an jima." Kashe wayar tayi ta cilla saman gado tayi bayin da gudu, ko wanka ba tayi ba ta fito kai tsaye falo ta nufa, binsu take da kallo ganin mata zaune suna kallon kayan lefen, cikin risunawa suka ce "sannu da fitowa Hajia." Kai kawai ta daga musu ta nufi madafa, had'uwa sukayi da Mamie da kula abinci a hannunta, "yawwa dama yanzu zanje na tasoki , zo muje to ga abincinki." Hannunta ta kamo suka dawo falo suka zauna, buda kula tayi wani b'ata rai Khairat tayi tace "wannan fa? Mamie karfa zaki fara min wannan tashin hankalin ne? wallahi ba zan iya ba." Dariya sukayi Mamie kuma tace "kwanciyar hankali dai Khairat, wannan shine gudumuwar da zan iya baki, dan nima shi kakarki ta bani." Diba Mamie tayi tasa mata a baki, da qyar ta had'e tana b'ata rai sannan tace "haba Mamie ba dad'i ba." "Yi hak'uri kinji shalelen Papa, ki saba da cinta kullum, kuma wannan fa had'in tattabaru ne, sai an jima zan miki na kaza." Haka Mamie ta dinga bata tana rarrashinta har saida ta cinye wanda aka zuba mata sannan ta tashi ta shiga wanka. *Tofa daga wannan rana* Khairat aka shiga sahun masu kurbe kurbe da tamne tamne, duk abinda Mamie zata had'a mata baya wuce na kayan itatuwa saboda sunfi lafiya, wannan kazar da tattabaru namiji da mace kad'ai ake hadawa da wasu sinadarin wajen dahuwarsu, abinka ga lafiyayya sai hakan ya d'an fara damunta saboda wasu itatuwa sun k'ara mata k'arfin sha'awa wanda da bata da ita, wasu kuma suna saukar mata da ni'ima. Kowace safiya take jan foyer wajen gyaran jiki cikin k'ank'anin lokaci ta koma kamar sabuwar haihuwa, kuma haka ake kullum ba'a daina ba, yan mata da samari sun had'u sun tattauna abinda zasuyi, daga ciki akwai arabian night wanda ango yake bala'in son partyn , sai indian night wato b'angarenmu ba yan india😁, sai kuma party wanda za'a gayyaci kowa da kowa, sai cocktail daya zama kamar al'ada. Kasancewar Khairat ta karanci zane hakan yasa ma ta zana kalar abayar da zata saka a arabian night d'in, amma kayan indian night Mammie tawa magana aka fara aiko mata da photuna ta zaba sannan Mammie zata taho dasu. *Shirye shirye sunyi nisa sosai, kuma ango ya dawo sai dai Khairat tak'i yarda su had'u, hakan kuma ya dameshi dan haka ya fara tunanin ko da matsala ne. Yau ta kama ranar *Asabar* kwana bakwai ya rage a daura aurensu, shiryawa yayi kawai yace shi zai tafi ya gant, mamarshi ce tace "Allah ya kiyaye hanya, amma dan Allah banda saurin hushi." "Haba Mama, ina kusan zama angonta kuma zanyi hushi." Yana fad'a yasa kai tare da rakiyar masu tsaron lafiyarsa sai gidansu Khairat.... _FAN'S JIHADI, ku kawo kud'in ankonku , dan yau zan siyo tawa, kuma babu wanda za muma alfarma ya shiga idan baya da anko musamman 'yan team d'in Umar Faruk, dan zasu iya b'ata mana taro.😊😁😎_ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣7⃣ Babu kowa a falon kasancewar sanyin safiya ce, Mamie yau bata fito wajen girki ba, sai masu aikin kad'ai suke abinsu, ganin babu kowa yasa shi sallama da k'arfi, da sauri Saude ta fito ganin ko wanene yasata zube qasa tana gaisheshi, saida yayi qaramin tsaki sannan yace "ina Mamie?" Murya na rawa tace "tana d'akinta bata fito ba." "Khairat fa?" "Itama bacci take." Kamar mai ciwon baki yace "ok, jeki." Tashi tayi ta nufi madafa tana fad'in "ikon Allah kenan, sai kuma Allah ya had'ata da daidai ita." Shima sama ya haura d'akin Khairat, a hankali ya bud'a k'ofar yana kallon gadon da yake da tabbacin tana nan, (kunsan mutuniyar dama ba kwana take da manyan kaya ba) hakan yasa Muzaffar ya kusa kallon rabin sadakinshi😂, saboda wata irin riga ce bata da maraba da bras, sai kuma wandon rigar kad'an ya wuce mazaunanta, takowa yayi harya tsaya gaf da ita yana had'iye yawu masu nauyin gaske, da qyar ya lumshe idonshi sannan ya sake bud'ewa ya saukesu a kanta, hannu ya kai zai daddab'ata ta bud'e ido tare da juyawa, karaf idonsu suka sark'e dana juna, a zabure ta tashi zaune taja dara ta rufe jikinta tana mashi kallon tuhuma. "Wannan wane irin jahilci ne, miye haka Muzaffar, ya zaka shigo min har cikin d'aki kana tab'ani?" K'ara matsowa yayi yana fad'in "kinga Khairat dan Allah kiyi shiru, karki tara min jama'a, wallahi bada wata manufa na tai tab'aki ba." "Dallah ni kamin shiru, ka fice min daga d'aki." "Haba Khairat w...." katseshi tayi da fad'in "dallah ni nace k...." kuma sai tayi shiru saboda tuna abinda Hibba tace mata. Hararanshi tayi ta turo baki gaba tace "to dan Allah kawai ka shigo min haka duk ka bani tsoro." Ajiyar zuciya ya sauke yace "kiyi hak'uri kinji. " "To naji, wai mema ya kawoka nan? bayan nace maka ba zamu had'u ba har sai an fara shirya shiryen bikinmu." "Kiyi hak'uri my Khairiri, wallahi na kasa hak'ura ne shi yasa, matuk'ar so nake na ganki sosai." "To naji ni dai yanzu ka fita ka jirani falo zanyi wanka na fito." Cikin wani shu'umin kallo yace "to muje na miki wankan mana." Pillow ta dauka ta jefa masa tare da masa kallon kai shashasha kuma hamago ne, amma da yake hamagon ne na gaske saiya kasa fahimtar kallon, hannu ya mik'o mata tare da sake fad'in "kizo na rakaki to idan ba zaki yarda na miki wankan ba." Saida ta had'e fuska sannan ta mik'a masa hannunta ta sauko daga kan gadon, ci gaba yayi da k'arewa surarta kallo ita kuma ko a jikinta, har saida ya kaita bakin ban d'akin sannan yayi murmushi yana cewa "insha Allah nan da rana kamar ta yau kin zama tawa, kuma daga wannan ranar ni zan dinga miki wanka." Itama murmushin tayi tace "zaka dinga min, ko zamu dinga yi tare?" Sunkuyawa yayi yace "yanda kike so gimbiya." "To ka jirani falo ina zuwa." Tana shiga shima ya bar gidan gaba d'aya ba tare daya jirata ba dan akwai abubuwa gabanshi, itama kuma ta jima bata fito ba bayan ta shirya ta fito falo, bata sameshi ba kuma bata damu ba, harkokin gabanta ta shiga yi bayan Mamie ta had'a mata kayanta tasha nasha taci naci, foyer ta nufa wajen gyaran jiki kamar kullum. *************** Cikin farin ciki ya fito daga gida zuwa wajen aikinshi, tunda ya shiga yaga gungun su Ishaq sunata hira, saida ya tsaya bayanshi bai sani ba ya kai masa duka yana fad'in "iskancin banza, wajen neman kud'in naku kuka mayar kamar kasuwa?" Dariya Ishaq yayi lokacin daya juyo ya kamo hannunsa yace "kai haba zo ka gani kaima." Matsowa yayi shi kuma ya d'auko wata had'add'iyar shadda gizna kalar ruwan qasa ya bashi, hannu yasa ya karb'a yana kallo yace "na miye wannan?" Saida ya kalleshi yace "ankon Hajia Khairat ne ta aiko manager ya kawo, kuma tace duk wanda bai siya ba to yasan sauran, dan tace tana buk'atar ganin kowa dake wajen nan ya hallara duka shagulgulan da za ayi." D'orawa yayi da "kuma kasan halinta dai, k'aramin aikinta ta tsige mutum daga aikin nan, dan haka kayi sauri ka siya dan kwana hud'u ya rage a fara shagulgulan bikin." Wata uwar harara ya zabga masa tare da jan tsaki ya cilla masa shaddar a qirji ya fita ya bar wajen, saida ya hau mashin d'inshi ya tambayi kanshi "ina kuma zaka je?" "Gida." inji wata zuciyar. Ai kuwa gida ya nufa da tunanin samun sauki, yana shiga a soro ya aje mashin d'in ya shiga ciki, duk da mutanen daya gani a farfajiyar gidan bai kula kowa ba yana shirin shiga d'aki mahaifiyarshi tace... "Kai Umar faruk, lafiya ka dawo gida yanzu?" A wahalce ya kalli Mamar yace "ba komai Mama, bana jin dad'i ne." Zai wuce ta sake cewa "Umar faruk, ashe yarinyar nan za tayi aure wacce kuke aiki a masana'antarta, shine kuma baka fad'a ba, kuma kaga ko mahaifinka bana tunanin ua sani dan daya fad'a min." Rai b'ace ya kalli Mamar yace "Mama kuma waya fad'a miki maganar nan?" Kallon budurwar dake gefenta tayi tace " *Ruk'ayya* ce." A zafafe ya kalleta yace "ke kuma gidan uban wa kika ji?" ya tambaya a harahen zarma. Tuni Ruk'ayya ta fara rawar jiki saboda tsoro tace "wallahi yaya Umar nima a Whatsapp ne na gani ana d'ora photonta da akwati talatin da makullin mota,amma ni bansan komai ba." Sama da qasa ya harareta ya rangada dogon tsaki sannan ya kalli Mama yace "wallahi shi yasa banso aka bar yarinyar nan ta rik'e wayar nan ba, kawai salon yara su lalace." D'akinshi ya wuce zuciyarshi kamar zata kama da wuta, wani irin haushin kanshi ne yake ji daya takura kanshi akan tunanin wata banzar Khairat (a cewarshi), bai sake fita ba har saida Ishaq yazo gida ya sameshi da yamma. Gaishe da matan gidan yayi kafin ya d'ora ma Mama da "Mama mutumin kuwa yana ciki?" "Yana ciki Ishaq, yana sabon d'akinshi." Dariya yayi ya mike yana fad'in "mutumin fa ba dama, kamar gobene auren nan." Itama dariyar tayi tace "ka barshi kawai, a doleshi k'uryar d'aki yake so a fitar masa, kuma wuri ba zai isa ba, in dai baso yake na fita daga d'akina ba dan yayi k'uryar d'akin." "A'a Mama ki barshi, dole zai hak'ura ai." Yana shiga ya sameshi cikin falon d'akin wanda ke shafe kayane kawai babu, falon babba ne sosai amma babu wani d'aki a ciki, d'an k'aramin kewayene daga waje sai matsakaiciyar ban d'aki , gaisawa sukayi Ishaq ya d'ora da "kai haka ake? kawai saika sa kai kayi gaba kuma baka komawa, shi yasa ai na fad'a musu wallahi son yarinyar nan kake, dan inba...." Katseshi yayi da fad'in "kai kai kai, dakata dan Allah, wacece nake so d'in?" "Khairat mana." "Mtssss, yanzu wannan sakaryar kake had'ani da ita, wannan mahaukaciyar yarinyar? gaskiya ka cuceni Ishaq, wallahi da zan san zuciyata na sonta, toda babu abinda zai hanani hukunta kaina ta hanyar da tafi kowace hanya zafi." "Wace hanya kenan?" cewar Ishaq. Shiru ya masa ya ci gaba da kallon d'akin shi kuma yace "to aini banga wani aibunta ba yarinyar, kaifa kasan *wacece ita*." "Sanin wacece ita yasa ba zan iya yarda na bari zuciyata ta fara sonta ba, da bansan ita yar d'an giya bace ko kuma manemin mata, da ace bansan ita fiysararriyace wace bata d'auki cud'anya da maza ba a bakin komai, da ace bansan ita mai wulak'anta mutane bace, da ace bansan tana soyayya da arne ba, sannan da bansan itace yarinyar da namiji majiya k'arfi guda biyar suka sauke sha'awarsu a kanta ba, to da zan iya tunaninta." Da mamaki Ishaq ke kallonshi dan b'acin rai ne kawai ya gani a idonshi da tafasar zuciya, girgiza kai yayi yace "wallahi wannan ba Umar Faruk d'ina bane, tabbas akwai abinda ke damunka kuma baka shirya fad'a min ba, Umar d'in dana sani yana da ilimin addini dana zamantakewar rayuwa, wannan maganganun bai kamata su fito daga bakinka ba, amma saboda b'acin ran da kake ciki yasa ka fad'esu, amma duk da haka ni ban yarda baka son Khairat ba, sai in har ka siyi ankon bikinta kuma ka halarci taron sannan na yarda." "Wannan shi zai tabbatar maka bana sonta?" "Sosai ma." "Muje, muje ka rakani na siyo yanzun nan." Kamar wasa Umar faruk ya shiga d'akinshi ya k'wamuso kud'ad'enshi suka fita, tare suka siye kuma suka biya suka bada d'inki, Umar harda siyan takalmi 😏kaji sai kace shine angon. Saida dare yayi suka dawo gida, dama kuma gida biyu ne ya raba gidansu, k'arar mashin d'inshi yasa Baba dake zaune a d'akinshi dake farkon shigowa gidan yasa ya kira sunansa , bayan ya shigo nan ma dai maganar d'aya ce akan aure Khairat ne, sai dai shi Baba Papa ne yazo da kanshi ya gayyaci malaminshi a matsayin wanda zai wakilceshi ya bada auren Khairat, a tsorace Umar Faruk ya d'ago kai yace "Baba, wai kai zaka d'aura auren?" "Eh, da wata matsalane?" "A'a, zan iya shiga ciki? kaina ke ciwo." "Ba damuwa kaje, amma ka sani dole zaku je wannan d'aurin auren, na fad'awa duka yan uwanka maza masu wayo , zamu tafi tare daku." "K....kkk....kuma dai?" cewar Umar faruk. "Eh, akwai damuwa ne?" "A'a, saida safe." Da qyar yakai kansa d'aki yayi kwance yana ji kamar yayi kuka, amma kuma yana tambayar kansa to kukun me kenan zaiyi😆😆😆. ***************** *Komai* na tafiya yanda suke tsarashi a haka kuma Khairat ta fara d'aukan haske saboda k'unshi da gyaran kai mai masifar kyau da aka yanyara mata gwanin sha'awa, ranar *laraba* aka fara da indian night, a ranar an rak'ashe sosai shagali yayi shagali, yayin da ya tara dubban mutane manyan yara da manyan mata, kusan kowa yayi qoqarin yin shigar indiawa, amma kana ganin amarya zaka ganeta saboda kayan data d'auka jar kala da golden, riga da siket ne hannayenta sun sauko akan damatsenta amma ta kamata sosai, sai k'aton siket d'in da yake jan qasa yasha duwatsu ga walk'iya, mayafin kayan ne aka d'ora mata akai, ba laifi gana gani zasu birgeka dan had'insu yayi, sai dai duk kyan Muzaffar Khairat ta takeshi ta shanye, haka akayita walima har aka buk'aci da amarya da ango su shigo fili su d'an taka, sai lokacin kad'ai nida ma chérie Hakeema da sister Chappa muka tsagaita da rawa muka ba Khairat d'inmu fili dan munsan tanan b'angaren gwanace ta qarshe. Ai kuwa bata bamu kunya ba, dan kuwa wata waqa ce aka baza mata d'aya daga cikin film d'in *dilwale* mai taken *janam janam*, Muzaffar tsaye yayi amma fa amarya ta taka ba laifi sai lik'i da tafi da aka dinga mata, a haka aka tashi taron ango ya maida amarya gida shima suka wuce gida kowa yayi baccin gajiya. _Har yanzu kunkumina ciwo yake😂 can naga yan team d'in Umar faruk ta taga suna lek'enmu muna yagar kaji, ah to ai dama na fad'a muku dan babu alfarma a wannan ranar_. *Washe gari* ma sabon shiri aka d'auka na arabian night, abayar da Khairat ta zanawa kanta ta saka, sosai rigar ta dace da ita, dogayen hannuwa kuma matsatsu hakama ta kamata wajen qirki abinda yayi kunkuminta, sai dai daga nan kuma saita bud'e sosai har tana jan qasa a baya, kwalliya akama rigar sosai ga d'an kwallinta ma, tana d'orawa ta fito kamar balarabiyar gasken, dogayen takalmi aka d'auko mata zata saka kawai taga ba zata iya ba, in da take ajiyar takalmin ta bud'a sai idonta ya sauka akan wasu tapet masu kyau masu kamar na maza , murmusawa tayi data tuna ranar farko da manager ya shigo tare da Umar Faruk suka gabatar mata da takalmin kuma tace su bar mata su, tana sawa suka tsaya a qafarta d'aram gwanin sha'awa dasu, haka suka nufi hall d'in taron amma idon Khairat sun kasa barin takalmin nan, yau ma haka akayi wannan taro aka ci aka sha baja baja (an samu na banza ba), 22:15 kowa yasan in da dare ya masa, sai dai tun kafin abar taron photon amarya da ango suka rigasu fita daga wajen, masu d'orawa a fecebook, Whatsapp, Instagram, kai da sauransu, cikin qanqanin lokaci sai photunan suka shiga duniya, maganganu iri iri wasu na yaba dacewarsu, wasu na yaba kyawun matar, wasu na yaba kyawun namijin, wasu na fad'in ai an mata fyad'e, yayin da maza suka fara tabka mahawara a shafukan sada zumunta iri iri, wasu na cewa ya kyauta kuma yayi jarumta tare da *Jihadi*, wasu kuma suna ganin ba zasu iya ba kuma shima da yayi bai birgesu ba. *Al'amarin aure kenan, dole sai ace nan yayi daidai, nan baiyi daidai ba, mutum d'ari na iya maganar aurenka, amma da wuya ka samu goma da zasu ce Allah dai ya sanya albarka, kashi saba'in masu kushewa ne, ashirin masu yabawa, goma ne masu addu'ar fatan zaman lafiya, Allah ka rabamu da sharrin mutane da aljanu , Allah ka bamu ikon yin komai da kai.👏* A cikin haka Allah ya had'a Umar Faruk da videon Khairat a Indian night tana rak'ashewarta, wanda anan ma mahawarar ake , wai idan kaine ya za kayi azo party amaryarka na wannan rawar kamar baindian gaskiya, wasu na fad'in kafin a d'aura auren zasu ce sun fasa, wasu kuma na cewa aiba komai bane zamani ne, yayin da Umar Faruk ya sake jin haushin Khairat sosai a zuciyarshi, tunanin yake yanda zaije partyn gobe da aka ce dole suje kuma gashi manager ya rok'esu akan suje danshi. Photo d'aya ya zubawa idanu shine in da take cikin abaya ta yane kanta, meuk-up d'in da tasha ta sake canza mata kammani tayi bala'in kyau, saika santa zaka iya ganeta abinka ga farar fata, da alama bata san an d'auki photon ba saboda babu murmushi a fuskarta kuma bata kallon mai d'aukarta, kanta na kallon qasa baka iya ganin idonta sai golden da pink d'in eyshadow d'in dake saman idon, zoom d'in photon yayi yana kallon kyawun fuskarta, a hankali furta "dama labarina dake gajere ne, gashi ya datse tun bamu kai ko ina ba." da kallon wannan photo har bacci ya d'aukeshi. A b'angaren Khairat kuwa har tayi shirin kwanciya bacci Mamie ta shigo da 'yan tame tamenta, tun kafin tayi magana Khairat tace "ohh Mamie, wai dan Allah abun nan ba zai qare bane? nifa wallahi na gaji da shan kayan nan suna takura min." Cikin dariya Mamie tace "kiyi hak'uri kinji, keda nake tunanin na had'a miki su idan ki kaje can kiyita anfani da kayanki." "Wa, ni? ba zan iya Mamie, na yanzu ma wallahi komawa za kiyi dasu." Kafad'arta ta dafa tace "Khairat, burin kowace uwace, taga yarta tayi rayuwar farin a gidanta, kiyi hak'uri nasan ba zaki ji dad'i ba amma ya zama dole na tuna miki, 'yata, akwai wani abu mai mahimmaci da kika rasa wanda ba zaki iya yiwa mijinki tink'aho dashi ba, amma duk da haka ina so naga kin samu kyautar da ake samu a daren farko." "Kinsan wace irin kyauta ce?" A hankali Khairat ta girgiza kai alamar a'a, murmushi tayi tace "wasu na bada kyautar kud'i, kadara ko tasa albarka, amma ni ina so a daren farkonki , mijinki ya mallaka miki kanshi ke kad'ai, ina so ya mallaka miki zuciyarshi ki zama mai alhakin kula da ita, duk abubuwan da kika ga ina baki, wannan ne sirrinsu, ki rik'esu da kyau su zama sirrinki, duk in da mijinki zaije to wallahi zai dawo matuk'ar kin rik'esu, natural ne ga lafiya a jiki ga dad'i a baki, kuma zasu dinga tsumaa jikinki koda kin zama raguwar mace, to zasu jima a jikinki ba tare da kin rage d'and'ano ba, idan kuma kina yi akai akai, to kullum d'and'anonki zai dinga haukata mijinki tamkar qaramin yaro ." Kumatunta ta dafa tace "kinji ko 'yar albarka?" Kai ta sake girgiza alamar eh, Mamie na bata ta amsa ta kifa kai saida ta shanye sannan ta ajiye cup d'in Mamie ta d'auka sukayi sallama ta bar d'akin zuciyarta fari qal. *Mamie nima na rik'e sirrin nan, shi yasa ban fad'a musu ba😎, nifa har kyautar yaran da zan haifa aka min😁.* *Washe gari* haka aka tashi da sabuwar hada hada kasancewar gobe d'aurin aure, bak'i na nesa dana kusa sun hallara kuma kowa na shirin tafiya partyn da za ayi na kowa da kowa, yamma nayi aka fara tafiya bayan wankan da amarya ta d'auka cikin shadda irinta ango, sunyi masifar kyau masha Allah, yau kam hall d'in cika yayi sosai dansu Umar Faruk ma na hangosu da sauran ma'aikatan, da qyar ake iya ganin amarya da ango saboda masu d'auka da waya nayi masu camera ma nayi, haka ake taro har mc ya kira amarya da ango suka yanka babban cake d'in da aka masa siffar amarya da ango , suka ba junansu a baki sannan suka shigo fili suka fara d'an rausayawa, naira tayi kuka domin wasu kamar a cikin shara suka deb'ota yanda suke zubawa ango da amarya, Umar Faruk ya kasa d'auke idonshi akan Khairat amma da kallonshi ya kai ga Muzaffar, 🤣sai naga ya bishi da harara da dogon tsaki, wannan tsakin ne ya ishi Ishaq yace su tafi su tafi tunda dai an gama ai, ko ruwa baisha ba bare jus sai Ishaq yayo oder abinshi a leda ya taho dasu. *Can naga yan team d'in Umar Faruk suna kokawa wajen d'aukar kwalban jus d'aya, amma da yake team d'in Khairat akwai imani, haka muka cika musu jakunkunansu da kayan k'walam😁* _Grp JIHADI FAN'S._ _Grp Queen Bee_ _Grp Qanin miji fan's_ _Grp Nida yayah Al'ameen 1 & 2_ _Grp Beneficiale writers_ _Grp yan Baiwa_ _Grp sharhi da tambayoyi_ _Grp Na baki rayuwata_ _Grp BK fan's_ _Grp Raheenat m kk fan's_ _Grp Online writers_ _Ummu Fatima conversation_ _Grp Mom sultan novels 1_ _Grp rayuwar gidan kawuna_ *Hak'ik'a kun min kara, dan kun cashe sosai fiye da tunani na.* 🤝🤝🤝🥰 *ANA TARE FAN'S* ****************** Koda ya shigo gida kai tsaye d'akin mahaifiyarshi ya nufa sai dai tuni sunyi nisa a bacci, kamar yanda ya sani dama ko yayi dare to abincinshi na gefen mahaifiyarshi, kwanan ya d'auka ya zauna kusa da ita ya fara ci yana kallonta tana baccinta, sai dai baici mai yawa ba ya barshi ya fito daga d'akin, d'akinshi ya shiga ya cire kayanshi ya fito zai shiga wanka, yayanshi ne *Abbakar* ya shigo shima bayan ya yiwa mashin d'inshi wajen zama, hannu ya bashi suka gaisa yana fad'in "yadai abokina, ina ka shiga ne haka?" Cikin sanyin jiki Umar Faruk yace "wallahi abokina ina nan, kai dai ka b'ace, waccen matar ta b'oyeka." Nunashi yayi da hannu yace "kai ka fita idona, ina ruwanta kuma." Bokitin ya d'auka ya nufi ban d'akin yana fad'in "idan ka shiga kace mata na dawa ta zo ta gaisheni." "Lallai ma, sai dai ka kama layi to harta gama dani, kasan ance in ana dara fidda uwa ake." Baice komai ba saboda harya fara cire kayan jikinshi, yana fitowa kuma yayi alwala ya shiga d'akinshi, doguwar riga yasa ya kabbara sallah ya fara nafilfili har saida kiran sallah asuba ya riski kunnuwanshi sannan ya dakata, fitowa yayi saboda jin motsin mutane sun tashi suma , tare suka nufi masallaci da yan uwanshi da kuma mahaifinsu, bayan sun idar da sallah suka dawo gida, kuma kamar yanda mahaifin nasu ya koya musu wasu karatun littafi mai girma suka fara, wasu kuma tasbihi da hailala da kuma istigfari, Umar Faruk ma karatu yayi saida 06:00 tayi sannan ya rufe ya d'an kwanta kafin k'arfe 09:00 auren Khairat. *Daga gobe ne fa*💃 ******************** *Yau ne fa*😂 Yau ta kama ranar *asabar* ranar d'aurin aure, Umariri ma 😂baiyi qasa a gwiwa ba wajen shiryawa kamar yanda yaga yayanshi Abbakar da k'annanshi guda biyu *Usman da Aliyu* suna yi dan cika umarnin mahaifinsu, wani abun mamaki shine, haka kawai Umar Faruk kejin wani nishad'i da farin ciki na baibaye mishi zuciya, ga murmushi mai matuk'ar tsada daya kasa barin fuskarshi, duk da yana d'an jin fad'uwar gaba da kuma tsoro, amma dai yafi farin ciki hakan kuma yasa ya ta'alak'ashi da karatun da yayi ne dan yafi komai samarwa mutum da nutsuwa. Cikin wata shaddarshi gizna fara ya shirya wacce suka d'inkata a bikin abokinsu , kasancewar ba mutum ne mai sha'awar manyan kaya ba yasa tun ranar bai kuma sawa ba, kamar yau ne ya fara saka shaddar saboda yanda take d'aukar ido, dogayen hannuwa ne da ita da kuma wasu da aka aza daga iya kafad'u hakan zaisa kayi tunanin rigar ninki biyu ce, bak'ar hula takalmi qafa ciki bak'ak'e da agogo ya d'aura kamar dai yanda aikin rigar yake, shi kanshi yasan ya had'u masha Allah sai tafiya kawai. Yana fitowa ya samu duka sun shirya suna tsakiyar gidan, rufe d'aki yayi ya kallesu yace "muje ko." Duka da kallo suka bishi saboda ganin bak'on al'amari a tare dashi, ganin kallon yayi yawa yasa Umar faruk sake cewa "muje ko." Baba ne yace "wai Umar faruk kaine da wani murmushin haka mai tsada, meya faru ne haka kake farin ciki?" Murmushin kawai ya ci gaba dayi ba tare da yace komai ba, Abbakar ne yace "wannan farin cikin dai akwai wani abu a qasa gaskiya, mutumin da kullum fuska a had'e." Cikin dariya yace "dan Allah ni ku wuce mu tafi, lokaci fa tafiya yake." *Saratu* matar Abbakar dake zaune tare dasu Mama a tsakar gidan ce tace "wannan sauri da kake Allah yasa ba wani abun kake shiryawa ba." Kallonta yayi yace "baki iya gaida miji ba amma kin iya katsa landa, to me zan shirya ni kuma?" Cike da zolaya tace "tona sani ko amaryar zaka sace , ko kuma kasa a d'aura auren da kai." Dariya duka aka saka saishi daya ce "wata d'iyar robace da kike tunanin haka ta faru?" Mama ce tace "yarinya fa tsadane da ita tunda ita ta...." sai kuma tayi shiru. Ke Ruk'ayya uwar d'umi sai kika ce "ita ta tallabeshi da mari fa duk wannan d'acin da yake mana a gida." Da gudu tayi d'aki saboda biyota da yayi duk da kiranshi da Mama keyi saida yakai , yana shiga ya tallabeta da marin itama😂 sannan ya kama kunnenta ya murd'e yace "wallahi na sake jin bakinki manya na magana, saina lahira ya fiki jin dad'i." Kuka take sosai shi kuma yana fitowa ya kalli Saratu yace "ki shirya tarban sabuwar amarya." Fita sukayi suka hau taxi dukansu suka nufi d'aurin auren, dandazon jama'a manya da qanana masu mulki masu sarauta, masu kud'i na nesa dana kusa ga kuma bak'i daga k'asashe da dama na gida dana waje, ganin irin d'ubbin jama'a yasa Umar Faruk jin haushi ma ya kamashi, haka dai suka samu suka kutsa tare da mahaifinsu harya shiga babban masallacin dake d'an nesa da gidan su kuma suka tsaya daga bakin masallacin. Unguwar *Presidetielle* tank'am take da mutane har lokacin da shugaban...ya iso wajen, haka aka bud'a masa hanya jami'an dake tare dashi suna kakkareshi harya shiga cikin masallacin, bayan sun gaisa da mutane suka fara qoqarin abinda ya tayasu a wajen, duk da haka Umar faruk baya jin komai sai wannan d'an fad'uwar gaban wanda farin ciki yafi yawa a ciki, Ishaq ma zolayarshi kawai yake manager kuma yana musu dariya. ******************** *A b'angaren* Muzaffar ma farin ciki yake da d'okin zuwa wajen d'aurin auren, ya gama shirinsa tsaf ya d'auki babbar rigarshi zai saka amininshi da suke kira da *Basta* ya kalleshi yace "sai farin ciki kake da zumud'i zaka samu Khairat, amma mu kuma bak'in ciki muke dan koba komai munsan mun kusa rasaka kenan har abada." Cike da mamaki yace " Basta, yanzu dama bak'in cikin aurena da Khairat kake? amma gaskiya ka bani mamaki." "Ba haka bane abokina, ina nufin ina bak'in cikin rasaka da za muyi." "Ban gane ba, rasani kamar yaya?" "Nasan kasan komai game da Khairat, amma sai gashi ka yarda da aurenta kamar wanda mata quka k'are a gari, baka tsaya kayi bincike ba bare ka tabbatar da lafiyarta, haba abokina kayi tunani mana ka gani, kai da kanka ka fad'a min mahaifin yarinyar nan ne yaje ya samu mahaifinka da maganar aurenku, kenan akwai wani abu a qasa." Shiru ya d'anyi yana tunani sai dai bai iya tunani komai ba, a hankali ya tambayeshi "kamar me kenan?" Shu'umin murmushi yayi yace "kasan ko suwaye suka mata fyad'e, ai kuwa ba zata rasa cuta mai karya garkuwar jiki ba, ko kuma dai wata cutar ko kuma ciki." "Ciki kuma? amma ai ba yau bane aka mata fyad'e, wata nawa aka d'auka da cikin ya kasa bayyana har yanzu?" "Kai baka san mata ba wallahi, amma idan baka yarda da abinda na fad'a maka ba , to ga wuri nan." Yana fad'a ya fita ya barshi dan yasan zaifi yin tunani da kyau, haka ne kuwa ya faru ya jima yana tunanin abinda ya fad'a har lokaci ya tafi sosai, agogon daya kalla yasa shi d'aukar wayarshi saboda ganin 08:57, shugaba ya kira yana d'auka cikin sauri yace "Papa an d'aura auren?" Murya qasa qasa cikin dariya yace "wai saurin me kake? harna bayar da sadakinka fa, d'aurawa kawai za ayi." "To a dakatar da d'aurin auren." "Me , kasan me kake fad'a kuwa? akan me za'a dakatar?" _Hummmmm Haleemat addu'arki ta kama mu._ "Papa kawai a dakatar da auren nan wallahi na fasa." "Wai kasan me kake fad'a kuwa, baka da hankali ne? yanzu haka fa d'aura auren nan ne za ayi." "To ni dai nine za'a d'aurawa auren, kuma nace na fasa dan haka ba zanyi ba." Shugaba ne ya saci kallon Papa da bakinshi ke bud'e sannan tasa babbar rigarshi ya goge zufa, aje wayar yayi yana kallon mutane malam ne yace "to zamu iya farawa yanzu." Shirun da shugaban yayi yasa aka fara shirin d'aura aure, sannu sannu murya na rawa yace "a dakatar da d'aurin auren." Kallonshi akayi amma babu wanda yayi magana , "Muzaffar ne ya kirani yanzu, kuma yace a dakatar da auren." Papa ne da gabanshi ya fara dukan uku uku yace "a dakatar kamar ya, gaba d'aya za'a dakatar ko kuma na wani d'an lokaci?" "Eh to, nidai yace min a dakatar ya fasa baya so." Da sauri Papa ya dafe kanshi, yana jin mutanen cikin masallacin na hayaniya amma bai iya cewa komai ba, kusan minti ashirin aka d'auka wasu na waje sun fara qaguwa akan meke faruwa, na cikin masallacin ne da suka tabbatar ba za'a d'aura ba suka fara fitowa, shugaba ma kallon Papa yayi yace "kayi hak'uri Mani, wallahi bansan meya faru ba,amma idan na koma gida zanji meye matsalar." A wulak'ance Papa ya kalleshi yace "ba damuwa, ba saika takurashi ba, allah zai kawo mana d'auki." Fita shima yayi ya rage daga Papa da malam sai yaya Suleiman da sauran k'annan Papa, su Umar Faruk dake tsaye k'ofar masallacin ne suka shigo ciki, wajen malam suka nufa suna tambayar lafiya har yanzu ba a d'aura auren ba, a raunane malam yace musu "yaran ne ya fasa." Kallon kallo suka shiga yi suma har muryar Papa ta daki kunnuwansu yana fad'in "bansan me zance mata ba, tafi kowa damuwa da auren nan, tana matuk'ar son ganin Khairat tayi aure, yanzu gashi ba lafiya ne da ita ba, watak'ila idan na fad'a mata hawan jininta ya tashi, Khairat ma na fama da rashin lafiya, itama zata iya shiga matsala duk da dai nasan biyayya ta mana ta yarda zata aureshi." A hankali ya furta "Allah ka kawo mana agaji." sai kuma kuka ya k'wace mishi, ganin haka yasa hankalin Umar faruk tashi babba na kuka a gaban idonshi, akan abinda zai iya taimaka masa, dole ne ma yayi wannan *Jihadin* kodan ceton mutunci da rayukan wasu, watak'ila kuma labarinshi da Khairat dama baizo qarshe ba, kuma zai iya yiyuwa akwai wani *b'oyayyen al'amari* dasu basu sonshi ba . Matsowa yayi kusan Papa ya rik'e hannayenshi yace "yallab'ai, ni ba kowa bane, kuma ba d'an kowa ba, bansan ko zaka iya bani auren 'yarka ba." Take farin ciki ya lullub'e Papa ya rumgume Umar faruk yana ci gaba da kuka, godiya kawai yake masa yayin da mutane suke mamaki malam kuma yana farin ciki haka ma 'yan uwanshi. Anan take aka d'aura auren *UMAR FARUQ AHMAD ADAM* da *KHAIRAT MANI BUKAR* Papa da kanshi ya wakilci Umar Faruk, anan ango ya tattara duk abinda yake da aka biya sadaki, malam kuma ya wakilci Khairat. _Farin ciki_💃💃🤝barkanmu 'yan uwa, musha biki lafiya. 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *ALHAMDULILLAH KASIRAN, ALHAMDULILLAH ALA KULLI HAL* _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣8⃣ Ana gama d'aurin aure sai kuma labari yasha bam bam, amma a wajen Papa farin cikine zalla yake saboda faruwar hakan, Papa ne ya keb'e da ango da Abbakar da kuma Baba yana tambayar lokacin da zata tare, Umar Faruk dai cewa yayi duk lokacin da suka shirya, amma Baba yace a basu sati d'aya, sosai Papa yaji dad'i ya kuma ce ya bawa Umar Faruk kyautar gidan da zasu zauna da kuma mota, murmushi Umar faruk yayi yace "wallahi bana buk'atar komai, shi yasa ma na fad'a maka koni waye dan matsayinmu ba d'aya bane, ba zan bar gidanmu ba, kuma ina da wajen da zan ajiyeta, idan kuma taga hakan bai mata ba, toni banda matsala tun kafin tafiya tayi nisa zan iya sss..." Bai k'arasa ba saboda taushe mishi baki da Abbakar yayi, Papa ne yace "ba komai Umar faruk, ai ba sai ankai ga haka ba, ko rumbu ka ajeta dole ai zata zauna, mudai muna godiya sosai." Papa ne yama Umar faruk iso a cikin gida yaga sauran iyaye da kakannin Khairat ya gaishesu, abinka ga idan Allah ya aiko abu, duk uwayen masu hankali idan suka kalli Umar Faruk sai suji ya kwanta musu a rai saboda hankali nutsuwa da kunya, haka suka kamo hanyar komawa gida yana wasi wasi yana ji kamar yayi kuskure hukuncin daya d'auka. ****************** *Khairat* na d'aki tare da k'awayenta tanti (aunty) Safiya ta shigo ta fita da ita bayan ta rufeta ruf da daren amare bleue wacce ta mata kyau, babban falon da Papa ke sauke manyan bak'inshi suka shiga, duk da kanta na qasa kuma cikin dara amma saida taga yawan mutanen dake d'akin, gaba d'aya kannan da yayun mahaifinta ne, Mamie kuma dama ita d'aya ce ga iyayenta, hakan yasa sai Safiya da *Ramlatou* itama cousine d'inta ce, sai kuma matar margayi babansu Papa da kuma Mammie, zaunar da ita tayi a tsakiyarsu sannan itama ta zauna. *Nan fa* aka fara sambado ma Khairat nasihoji ta ko ina bayan sun fad'a mata yanzu ita ba budurwa bace mai aure ce, kuma ita ba matar Muzaffar bace, matar *Umar Faruk ce*, an jawo mata ayoyi hadisai da kuma karatun *duniya*, sosai nasihar ta shiga jikin Khairat sai gata da kuka tare da bawa kowa dake wurin hak'uri na ayafi juna, dan duk rashin kunyarta bata kai tama mutanen dake wajen ba saboda girma da matsayinsu gareta, haka suka bita da sa albarka bayan ta musu alk'awarin bin Umar Faruk sau da qafa, tanti Safiya ce ta mayar da ita d'akinta. Tunda ta zauna ta fara wani sabon kuka dan babu yanda za tayi ne kawai ta amsa musu, amma ko kad'an Umar Faruk baya da tsari irin na mazan da take so (a cewarta fa)😎, gashi kuma baya da komai hasalima a qarqashinta yake samu, to tayaya zata rik'eshi a matsayin miji, gaskiya zata hak'ura taje gidanshi danta musu biyayya, amma dole zata dawo dan rainine ma a had'ata da wani wai Umar Faruk, haka dai bayan 'yan d'aurin aure sunsha lagwadarsu wasu har sun tafi da guziri, aka fara biki gadan gadan aka sha casu sosai. Tun yamma mutane suka fara watsewa zuwa dare kuma babu kowa sai bak'i da suka zo, kowa ya kwanta dan yayi bacci ya huta gajiya amma banda Khairat dake tunanin yanda rayuwar aurenta zata kasance, yanda taga safe haka taga rana ba tare data rintsa ba, kiran sallah asuba kad'ai yasa ta tashi tayi alwala tayi sallah sannan ta kwanta rama baccin da bata samu tayi ba. ****************** *A b'angaren* Umar Faruk kuma suna shiga gida yanda duk suka shiga da kazar kazar amma banda shi yasa mahaifiyarshi ta fara tambayar lafiya, fad'a mata yayi ita da yan uwanta (matanshi guda biyu) su sameshi d'akinshi, ba b'ata lokaci suka hallara tare da Abbakar da Umariri😂, nan Baba ya fad'a musu abinda ya faru sannan ya d'ora da "wannan na tabbata itace k'addarar yaranku, kuma wannan abun *rubutatten al'amarine* da ubangiji ya rubutashi tun kafin a samar dashi kanshi Umar d'in, dan haka ku shirya tarbar sarakuwarku ban da rana irin ta yau insha Allah, sannan ku saka musu albarka." Saida suka gama jimami sannan mahaifiyarshi ta sauke ajiyar zuciya tace "gaskiyane malam, kuma insha Allah ba za'a samu matsala daga garemu ba, kuma muna musu fatan alkairi Allah ya basu zaman lafiya." "Ameen ameen." cewar malam kafin ya kalli sauran yace "ku kuma me zaku ce?" Tab'e baki *Sa'a* tayi tace "ah to me zamu ce, tunda kun riga da kun gama yanke hukuncinku." Mik'ewa tayi ta kama hannun *Maimuna* tana fad'in "nifa ba zan iya zama wajen nan ba." Itama Maimuna saida suka mike ta kalli Umar Faruk da kanshi ke qasa shi abin duniya ma ya dameshi tace "wallahi dai kayi abin kunya, in banda kwad'ayin dukiya ta uban yarinyar nan, ince kaine nan kazo kwanan baya kana huci akan ta mareka kuma ka rama, shine yanzu dan tsabar rashin zuciya wai kai uban taimako ka taimaketa, kai yanzu ba abin kunya bane a wajenka ace ka auri macen da wasu garada suka raga?" Sa'a ce tace "ke rabu dashi dan Allah, yana tunanin zai samu abin duniya shi yasa, amma ka sani ba lallai ka mori abinda za'a baka ba, dan cutar da waccen ya guje ma kai zata sama, wannan itace k'addararka." Bushewa sukayi da dariya suka tafa hannu suka wuce abinsu, ba sabon abu bane wannan dan haka babu wanda ya dama a cikinsu, Baba ne yace "Umar Faruk." D'agowa yayi ido jawur kamar zai fashe da kuka yace "na'am Baba." "Kayi hak'uri kaji, wallahi Allah ba zai barka haka kawai ba saiya dafa mata, kuma ni nayi farin ciki da abinda kayi, kuma nayi alfahari da kai a matsayin D'ana, Allah ya maka albarka." "Ameen Baba." Mama ce tace "to a ina zasu tare?" Baba ne ya kalli Umar Faruk d'in shima kallonshi yayi, cikin muryar tausayi yace "Mama ba zan iya barin gidan nan ba, idan sunga nan ya musu, to su kawota idan kuma ba haka ba, to gaskiya sai dai mu rabu, danni dama kawai saboda na fitar dasu daga halin da zasu shiga nayi." Mama ce tace "haba Umar Faruk, me yasa zaka fara maganar rabuwarku tun yanzu, bana so ka daina, kuma ba komai ai sai a qarasa gyara abinda ya rage, idan har ya musu saisu kawota nan d'in." Abbakar ne yace "Mama, saida fa mahaifinta yace zai bashi gida da mota, amma yaron nan da taurin kai yak'i amincewa." Umar Faruk ne yace "idan na amince na amsa kenan me nayi? me kake so al'umma suce a kaina? na aureta saboda dukiya? to wallahi babu abinda mahaifinta zai bani a duniyar nan na amsa, ni taimako nayi *jihadi* nayi na auri 'yarsa, dan haka bana buk'atar komai daga gareshi." Tashi yayi ya fita daga d'akin Baba kuma ya kalli Abbakar yace "nifa naji dad'i da bai karbi komai ba, dan yanayin haka jama'a za suce dama abinda yasa yayi taimakon kenan, duk da bansan yarinyar ba nasan dai tana da rawar kai, kana ganin idan ya amshi wani abu daga mahaifinta zata yarda ya tank'warata a matsayinshi na mijinta?" A hankali Abbakar yace "kuma hakane gaskiya, zata rainashi ne ma." Mama ce tace "nidai wallahi a tsorace nake, dan zamanshi da yarinyar nan fa akwai matsala." "Wace irin matsala kuma?" cewar Baba. "Kaifa kasan halin Umar Faruk da zuciyar tsiya, ina jin tsoron yanda zasu zauna gaskiya ba tare da sun samu matsala ba." "Kinga dan Allah, ki cire tsoro a ranki sannan ki bishi da addu'a, insha Allah komai zaiyi daidai." "To Allah ya yarda." Baba ne ya sake cewa "yanzu to me zaku shirya? biki za kuyi ko walima." "Kuma dai?" inji Mama. Cikin dariya Baba yace "ban gane kuma dai ba? kina ganin zamu zauna hakane ba muyi komai ba bayan amaryar da muka samu a sauk'ak'e, kema kinsan dole za muyi koda walima ce mu godewa Allah." Abbakar ne yace "ina ga ayi walimar zaifi, kunga sai ayi wa'azi ma tare da musu addu'ar zaman lafiya." Mama ce tace "gaskiya kam shawarar tayi, to yaushe kenan?" Baba ne yace "ayi ranar juma'a, tana gobe zata tare." "To Allah ya nuna mana." "Ameen." Baba da Abbakar suka amsa. Suna fitowa Abbakar yaga matarshi a tsakar gidan tana shirin d'ora abincin rana , saida ya tsaya gabanta yace "ashe haka bakinki keda k'arfi, lallai Allah ya miki baiwa, tunda gashi abinda kika fad'a ya faru." Duk da gabanta ya fad'i dan bata fahimceshi ba haka tace "lafiya, meya faru, mena fad'a kuma?" Murmushi yayi yace "da zamu fita ba kince Umar faruk zai sace amarya ba ko a d'aura dashi?" Dafe qirji tayi da k'arfi tace "me Umar d'in yayi?" Dariya yayi ya nufi kewayensu dake kusa da d'akin amaryar Umar Zuby😂yana fad'in "dashi muka d'aura auren." Wata irin bud'a ta rangada data sashi tsayawa cak yana kallonta, wato ita farin cikinta ma harya kai haka, wucewa yayi ita kuma da gudu ta lek'a d'akin Umar daya cire kayan jikinshi ya kwanta, amma ganinshi ba riga yasa ta dawo baya ta koma ga aikinta. Umar Faruk kuma in banda tunanin irin kuskuren da yayi babu abinda yake, ji yake kamar fa ya sauke ma kanshi nauyin daya d'auka ya aza ba tare da an tilastashi ba. Tunda kannanshi suka dawo daga islamiyya aka fad'a musu suma dai murna suke yayansu yayi aure, nan kuma Mama ta siyo goro ta bawa yaran suka dinga rabawa makota ana fad'a musu Umar ne yayi aure, haka ma a waya Mama tasa Rukayya da Ali suna kiran yan uwa suna fad'a musu, wani yaji dad'i wani yaji haushi, dan ma ba'a fad'a musu wacece amaryar, duk da a kurarran lokaci ne amma zama lafiya da mutane da Mama keyi yayi tasiri sosai a yau, dan gidan turuwa aka dinga yi ana zuwa tayasu murna, Umar Faruk kuma ganin ba za'a barshi ya huta ba yasa ya sake shiri ya fita zuwa gidansu Ishaq dake kusa dasu. ***************** Tunda Ruk'ayya ta kira tanti *Ma'u* (Mamar Zuby) ta fad'a mata ta fara bala'i tun a waya, ganin haka yasa Ruk'ayya kashe wayar taci gaba da kiran wasu, duk da haka bata hakura ci gaba tayi da masifa ita kad'ai Zuby kuma da taji meya faru kuka ta fashe dashi, Mama ko nata bala'i ko sauraronta ba tayi ba, jin kukan nata yayi yawa yasa tace, "Dan ubanki rufe min baki kafin inci uwaki , yar banza kawai duk bake kika jawo ba, Umar Faruk wace irin jaraba ce baiyi ba ki bari ayi aurenku amma kika k'i yarda, waike sai kin gama jarabawarki, to yanzu gashi nan ya samu dama kuma yayi anfani da damarsa, yanzu kafin wata biyu yayi a d'aura aurenki dashi ita lokacin ta fara laulayin ciki, kinga ta riga ta tsere miki." Zaby na jin haka ta sake fashewa da kuka tace "na shiga uku Mama, yanzu Umar faruk saiya had'a jikinshi da wannan tsohuwar kilakin." "To me zai hana, macece fa kuma shi namiji, namijin ma rik'akk'e. "Wayyo Allah, dan Allah Mama ki taimaka min wallahi ba zan iya jura rasa Umar Faruk ba, Mama kinsan ina sonshi sosai, bana so wata ta rab'eshi ma bare harya had'a jikinshi da wata." "Uwarki ma, yo wane irin taimako zan miki? ai kin riga da kin cuci kanki." "Dan Allah Mama kiyi hak'uri." kwance tayi tana kuka hakan yasa taji ba dad'i, tadata tayi ta zauna tace "kwantar da hankalinki kinji, Umar fa d'an uwanki ne kuma naki ke kad'ai, sai kinso ne zaki bashi dama harya kusanci wacce karuwar sauran sojawa (da yake Zuby ta fad'awa Mama komai akan Khairat d'in tun ranar da Umar ya d'aga mata murya akanta.)." "Kamar ya Mama, ban fahimta ba?" Murmushi tayi tace "idan da zaki yarda da sai nace a d'aura aurenki dashi ranar juma'a da za ayi walima, to daga nan fa sai labari ya fara shan bambam." Murmushi ne ya bayyana kan fuskarta tace "da gaske Mama, kina ganin Umar zai yarda ya aureni ranar juma'a?" "Umar Faruk d'in banza, ni uwanshi nake iko dasu, dan haka kwantar da hankalinki tsaf za'a d'aura aukenku." "Wallahi Mama na amince, danni bana so na rabu dashi." "Ba zaku rabu ba, amma fa ki sani ba zaki tare a gidansa ba har sai munga kamun ludayinshi a matsayinshi na me mata biyu, kinga zaki samu damar raba tsakaninsu ta zaman da za kiyi anan, sauran karatun kuma na biya miki shi daga baya." Alk'awari ta mata gobe za taje gidan ta sanar dasu halin da Zuby take ciki, dan haka kawai a d'aura musu aure. 🤔🤔🤔 _Mata biyu_ ********************* *Muzaffar* manyan duniya😂 wallahi dariya yake bani,😎 abokananshi na zuwa gidan suka fara balbaleshi da masifa, wannan bai dameshi kamar da wani yace "dallah ku rabu dashi, tunda shi bai aureta ai wani ya aureta ko." Da firgici ya kalleshi yace "me kace, wani fa ya aureta?" "Kwarai, wani ne a cikin taron auren yayi *jihadi* ya rufa mata asirin da kai kake kokarin tona mata, kuma yanzu Khairat ta zama *matar Umar Faruk*, dan haka zaifi maka kaje ka samu mahaifinta danya biyaka duk abinda ka kashe a kanta." "Kutumar uba, wane dan haune ya auri *matata*? wallahi k'aryane , babu wanda ya isa ya auri Khairat ina raye, na riga dana tsara rayuwata da ita kuma ita kad'ai nake tunani, dan haka dole a kwance wannan auren." Ire iren irin wannan magnganun yake tayi duk suka watse suka barshi yana sambatu, bai tab'a tunanin yana son Khairat haka ba sai yau daya rasata, dafe kai yayi da hannu yace "na shiga uku, Basta ka cuceni, gashi banma san ina kake ba yanzu, Allah ya tsine maka albarka shege tsinanne."😛 Yan uwa da iyayenshi takaicine ya hanasu zuwa inda yake, haka baki kowa ya tattara kayanshi ya koma inda ya fito rai a b'ace, shi kuma damuwa ta mishi yawa saida ya zubar da hawaye kad'ai yaji dama dama, haka ya wuni cikin d'akinshi bai fita ba bai kuma cire kayan jikinshi ba har yayi bacci dasu tare da daukar dangana da komai daya kashe akan Khairat amma ba da ita kanta ba, dan har yanzu yana ji zai iya samunta tunda a tunaninshi tana sonshi. _A banza man kare_😏 ****************** Umar Faruk na baccin da bai jima da d'aukarshi ba k'aninshi *Sa'ad* ya shigo ya tasheshi wai tanti Ma'u na kiranshi, gabanshi ne ya shiga fad'uwa dan sai lokacin ya tuna wata aba wai ita Zuby, haka ya tashi ya sanya doguwar riga ya fito yana tunanin idan aka daura aurenshi da Zuby ya zama *mijin mace biyu* kenan, zaune ya samesu a d'akin Mama tare da Baba, wata harara masa tace "sannu ango." K'asa ya zauna yana shafa kansa yace "ina kwana." "Humm." cewar tantin tana kallonsa. Gyara zama tayi ta kalli su Baba tace "to ni dama ba wani abu bane ya kawoni sai maganar Umar faruk da Zubeida." Rudududu yaji kayan cikinshi sun kada , yawu ya had'e ya daga kai ya kalleta, ci gaba tayi da "tun jiya da Zuby taji abinda ke faruwa ta daga hakakinta da nawa, har yau kuka take tak'i ci tak'i sha, daren jiya da zazzabi ta kwana gashi yau ma tak'i hakura, maganarta d'aya shine zata rasa Umar Faruk, shine nace to da a tsaya haka me zai hana a daura musu aure? tunda dai dama an gama komai lokaci kawai ake jira, hakan zaisa ta samu tabbacin ba zata rasashi ba, amma shawara ce ya kuka gani?" Mama da Baba tausayin Zuby ne ya kamasu saboda dole za taji ba dad'i saboda shak'uwar dake tsakaninsu, da firgici ya kalleta yana tunanin girman maganar data zo da ita, a ranshi ne yace "ni kum gidan uban wa zan kai mace biyu a wannan qarnin, a zanyi dasu?" _Umariri kenan,😂kafi kowa sanin yanda za kayi dasu idan ka gansu gabanka._ Baba ya amshi tayin data zo dashi yace ba matsala, kuma za'a d'aura auren ranar juma'a, ita kuma tace ba yanzu zata tare ba sai bayan ta gama karatun, haka tanti ta koma gida cikin farin ciki Umar kuma ya kalli Baba yace "amma Baba, mata biyu a lokaci d'aya, duka ni d'in nawa nake da zan auri mace biyu, kuma idan suka tare ina zan ajesu? gaskiya Baba nauyin yamin yawa ba zan iya ba." "Haba Umar faruk, da jarumta fa akasan mai wannan sunan, karka bari mana mata su baka tsoro da wuri haka, zaka iya da yardar Allah, kuma Allah zai baka yanda za kayi dasu insha Allah, zai dubi zuciyarka ya taimaka maka wajen d'aukar nauyin ko wacce." "Maganar wuri kuma da kake, ai abune mai sauki, tunda itama Zubeida ba yanzu zata tare ba, kaga ita Khairat d'in dake uwar gida saika ajeta acan b'angaren daka gyara, d'akinka na yanzu kuma da muke tunanin saka k'annanka a ciki idan ka tashi, sai a gyara Zubeida ta shiga ciki, abinda zasu ci kuma wannan Allah ba zai hanasu ba, nasan za kayi k'ok'arin yin adalci a tsakaninsu, kuma zamu maka addu'a Allah ya baka ikon yin adalci a tsakaninsu." Mama ce tace "Allah ma ya yardar maka kafin lokacin da Zubeida zata tare ka mallaki naka gidan na kanka." Kallon Mama yayi yace "mallakar gida a wata biyu Mama?" "Eh mana, kana wasa da yin Allah ne?" "A'a." yana fad'a ya tashi jiki ba kwari ya shiga wanka ya fito ya shirya cikin qananan kaya, fita yayi ya gidansu Ishaq ya sameshi kwance yana bacci, ware hannu yayi ya kai masa duka, a tsorace ya farka yana ganinshi yace... 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 1⃣9⃣ "Umar Faruk! miye haka dan Allah?" "Dallah malam tashi, wato kai duk girgizar qasarnan da ake baka ji kana nan kana bacci, ni ina can cikin ibtila'i kai kuma hutawa ma kake." Gyara zamanshi yayi yana murza ido yana fad'in "lafiya, meya faru?" Saida ya zauna shima akan katifa sannan yace "akwai matsala fa mutumina." "Matsala tame kuma?" Kallonshi yayi yace "maganar yaran nan ne mana." Bushewa da dariya Ishaq yayi yace "ai koda kace yaran nan na fahimci da matarka da kuma budurwarka kake, dan kasan mu maza ko mace ta girmemu muna so muce mata yarinya." Harara ya cilla masa yace "toni fad'a min a cikinsu wacece ta girme min? ka daina ganin wannan da kabri ga kuma tsayi, wallahi ba zata wuce ashirin da uku zuwa da biyar ba." "Humm, nidai yanzu fad'a min me yake faruwa da kace akwai matsala? danni bana tunanin abin nan zai fara damunka tun yanzu, tunda Zuby nanan tafe." "To ai akan Zuby d'in ne, tanti fa tazo gida kuma sun gama magana akan za'a sake wani d'aurin auren ranar juma'ar nan." "Juma'a kuma? amma me yasa zasu mai dashi juma'a? bayan wata biyu ne nan gaba." "Kaima kasan halin tanti, wallahi ni nasan dagangan tayi haka, kawai akwai bala'in da suke so su kunno min shi yasa tayi haka." "Ai kuwa in hakane wallahi saika tashi tsaye, ka nuna musu kai namiji ne na gaske, dan inba haka ba sai kazo ka rasa yanda za kayi, wata rana ka kwana d'akina wata rana kuma kaje wajen Mama kana hawaye." "Wa? ni Umar zanyi kuka akan mace tamin wani abu, ai kaima kasan halina, duk wacce tamin ba daidai ba wallahi daidai nake da ita, tsaf zan zane yarinya." Dariya Ishaq yayi yace "sai dai Zuby, amma Khairat ba zata daku a hannunka ba." "Wai wasa kake dani ko? gani kake tafi k'arfina ne? ai kuwa za kasha mamaki, dan sai nasa yarinyar nan tayi laushi fiye da tunaninka." "Allah yasa, dan in haka ta faru kaine za kafi kowa cin moriyar hakan." "Kai, karfa ka d'auka wata rayuwar jin dad'i zanyi da ita, taimak...." Ishaq ya katseshi da "bana son cika baki mutumina, bari ya shigo tukun muga iya gudun ruwanka, nasan mata kuma zata iya canza maka tunani cikin qanqanin lokaci, dan haka bari har naga tafiyar taku sannan." "Ai kuwa zaka gani." Tashi Ishaq yayi ya d'auki doguwar rigarshi yasa ya d'auki maclean da brush zai fita yace "ka jira na fito saina rakaka wajen amarsu." Dan k'uwa ya masa yace "amaryo ba amarsu ba." Yana ganin ya shiga shima ya fito zai tafiyarsa ya had'u da Baban Ishaq zai fita shima, har k'asa ya zube ya gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska tare dasa masa albarka, sannan ya d'ora "jiya sai mu kaji abin alkairi, gaskiya ka kyauta Allah ya maka albarka ya taimakeka a duka al'amuranka, saura wannan sakaran shima kasa ya samu mata yayi aure." Dariya kawai yayi ya tashi tsaye shima tsohon ya wuce, saida ya koma gida ya d'auki mashin d'inshi sai dai bansan ina ma zashi ba, yau *lahadi* yau ne dama suke hutu a wajen aiki, mashin d'inshi ya tuk'a bai zame ko ina ba sai gidansu Zuby. Taji dad'in ganinshi amma kishi yasa ta kasa bayyanawa, d'aki ta shige ta barshi zaune gaban tanti, ganin haka yasa tantin tace "tashi ka wuce ka sameta mana, gidan ai ba bak'onka bane." Yana wucewa ta bishi da harara, zaune ya sameta a bakin gado ta had'e hannaye, zaune yayi kusanta yana kallon fuskarta, sun jima a haka kafin ya sake kallonta yace "amaryata hushi take dani?" Da mamaki ta kalleshi tace "lallai ma yaya Umar, yanzu daga d'aura auren naka shine harka kaini matsayin amarya tun ma bata tare ba a gidanka? lallai da matsala." Shima dai da mamakin ya bita da kallo, taushe zuciyarshi yayi yace "ko da ita ko ba ita, ke amaryata ce kuma kinsan haka." Hawaye ne suka ciko idonta ta kalleshi tace "wallahi yaya Umar ni dama tun ranar daka d'aga min murya akan banzan yarinyar nan nasan kana sonta, kawai raina min hankali kayi ka nuna ba komai, shine yanzu wai za'a ce ta zama matarka ta farko bani ba, bayan lokacin da muka d'auka muna tare da kai, wallahi kaci amanata yaya Umar, tunda muke da kai ban tab'a kallon wani a matsayin saurayi ba na kare maka kaina,amma shine kai ka kasa hakan, dama ku maza h......" "Dakata dan Allah." ya katseta. "Mu maza me? mayaudara ko maciya amana? kinga ki hukuntani ni kad'ai saboda ni miki laifi, amma karya shafi kowa, sannan ni kaina bana jin abinda nayi laifine, saboda ni namiji kuma *mijin mace hud'u*, saboda nayi ta farko kuma zan aureki a matsayin ta biyu ni banga wani aibu a ciki ba." "Sannan kinsan abinda ke tsakanina da ita, so bashi ya sani nayi abinda nayi ba." Cike da rashin wayo tace "ba wani nan wallahi, idan da gaske taimakonta kake son yi, meya hana ka rok'i yaya Abbakar ya aureta, ko kuma shi Baban ya aurrr." Qamewa tayi ta rintse ido tana jiran taji saukar hannun, Umar faruk kam daya d'aga hannu zai wanketa da mari tsayawa yayi saboda tunawa a cikin gidansu yake, nunata yayi da hannu yace "maganar data shafi ni dake, karki sake saka iyayenmu a ciki, idan ba haka ba ranki zai dinga b'acewa." D'orawa yayi da "karki kuskura kice zaki raina min mata bare iyayena, ita ke gaba dake kuma dole ki bita in har kina son zama dani, in kuma ba haka ba to mu hak'ura da junanmu, dan duk abinda zai shafi mutuncina bana k'aunarshi, a yanzu kuma itace tabbas d'ita tunda ta shiga hannuna , kuma kare mutuncinta yana wuyana ne, dan haka ki kiyaye, sannan idan kin shirya aurena to ki shirya dabarun zama dani lafiya." Yana fad'a ya fito daga d'akin yayi wa tanti sallama yayi gaba ranshi na quna , wai tun yanzu kenan za'a fara caza masa kai, sai lokacin kuma ya dinga tunano abinda ya fad'a mata akan Khairat, duk da ba sonta yake ba amma yaji dad'i dan ko ba komai dai dole ya kare mutuncin kowace a cikinsu idan har suka zama nasa dukansu. ***************** Khairat na bacci ka tasheta saboda bak'i na shirin tafiya, sallama suka dinga mata ana sake mata addu'a Allah ya bada zaman lafiya, ita kuma tana yak'e tana amsawa da ameen ameen 😁, har suka gama tafiya ya rage sai Mammie a gidan, bayan sallah azahar suka tafi da Hibba salon aka cire mata akaihun data saka dogaye da kuma gyaran da aka mata aka aka gyara mata aka mata kitso manya, bayan la'asar suka dawo gida tayi wanka tayi sallah taci abinci, ita da kakarta sai farin ciki suna hira cikin nishad'i. *Bayan sallah magrib* Papa ya tafi masallaci d'aukar karatu, kamar kullum saida sukayi sallah isha'i aka sallami kowa, anan Baba ya tsayar da Papa ya fad'a masa maganar auren Umar faruk, farin ciki Papa yayi tare dasa albarka kuma yace zasu halarci d'aurin aure insha Allah. Bayan yazo gida ya fad'a ma Mamie da Mammie, Mamie ce kawai tace "Allah ya basu zaman lafiya ya basu hak'urin zama da junansu, a fad'a mata kawai tasan halin da ake ciki." "A'a." cewar Papa sannan ya d'ora da "ba hurumin mu bane, ki bari mijinta zai fad'a mata da kanshi, shi yasan ta yanda zai tarota." "To shikenan, amma ni dai wallahi ina son yaron nan sosai, dan nasan shi kad'ai ne zai iya tafiyar da Khairat a matsayin miji, kuma ina ji a jikina zata gyaru ta dalilinshi ne insha Allah." Papa ne yace "nima yaron ai ya kwanta min a rai sosai, dan ba kowa bane zai iya yin *jihadin* da yayi." "Sosai kam, dan da yanzu bamu san halin da muke ciki ba dukanmu, nadai tabbatar bama cikin yanayin dad'i." cewar Mammie. Dariya Mamie tayi tace "ai yaron kirki ne kuma ya samu tarbiya, tunda ba shine karo na farko ba daya taimakemu." "Kin sanshi dama? wane irin taimako yayi mana?" inji Papa. "Shine fa yaron daya je asibiti yana son ganinka, wanda ni na fito na ganshi kuma shiya fad'a min inda aka samu masu laifin nan, kaga ba danshi ba da yanzu muna nan tare dasu." "Allahu Akbar, lallai ya mana taimako, babu abinda zamu saka masa dashi sai dai addu'a da fatan alkairi, Allah kuma yasa kar yarinyar nan ta bamu kunya." Mamie ce tace "ameen, amma dai nasan zaiyi wuya a samu sauk'in al'amari daga wajen Khairat." Mammie ce tace "ba zata bada matsala ba insha Allah." "Allah yasa." Suka amsa da "ameen." ******************** *Haka* aka dinga tafiyar da rayuwar ba dad'i ba wuya, Khairat rayuwarta take kamar babu auren kowa a kanta, sai dai Mamie ta hanata fita ko k'ofar gida, itama kuma bata damu ba tunda tana sakewa a cikin gidan, zuwan Mammie ya sata farin ciki sosai kullum suna tare suna shirmensu kamar yanda suka saba. Sai dai kuma har yau basu had'u da Umar Faruk ba, kamar yanda basa da lambar juna bare wani ya kira wani, sau d'aya yazo da sassafe tana bacci, yace agaisheta kawai zai dawo har yau kuma bai koma ba. ***************** Umar Faruk ma shirye shiryen wani sabon auren yake tayi hakan yasa ma baya da lokacin kanshi sosai, sai dare yayi kuma sai Khairat ta sallamo mishi ta hanashi bacci, tunaninta na takura masa yana hanashi sukuni sosai, wani lokaci har yakan manta da Zuby a rayuwarshi saboda katutun da Khairat tayi a zuciyarshi. *Kwana hud'u* yau da auren, Mamie ta tura Mamar Hibba da tanti Safiya gidansu Umar Faruk ganin d'akin Khairat, su kad'ai ne ta yarda dasu da kuma hallayarsu shi yasa ma ta turasu su kad'ai, sunje cikin aminci kuma sun dawo cikin farin ciki saboda tarbar da aka musu, sun fad'ama Mamie komai akan gidan dama d'akin inda tanti Safiya ta qara da cewa "gaskiya rayuwa dai ta mai qaramin k'arfi, to wannan d'akin na Khairat ya ishi bawa rayuwa kuma cikin farin ciki." Sai dai Mamar Hibba tace "amma ko kad'an kayan da aka saka mata a d'akin Muzaffar ba za suyi a wannan d'akin ba." Hakan yasa Mamie turawa aka d'auko kayan Khairat daga gidansu Muzaffar aka sasu kasuwa, a take kuma aka siyo mata wasu sabbi yan zamani masu bala'in kyau, *ranar alhamis* aka mata jere a d'akinta, masha Allah yayi kyau sosai duk da d'aki d'aya ne amma zai birge, haka yan gidan suka lek'a suka ga d'aki yayi tsaf dashi, ga kayan kallo da aka lak'a mata panka da k'aramar fridge, matasan kujeru ne aka aza a d'an k'aramin farfajiyar kewayenta , sai babbar kujera a cikin d'akin ta zaman mutun uku, saman wradrob kam cike yake da manyan darori da bargo , ciki kuma bayan kayan jiki sai kwanoni da sauran kayan aikin gida, a kusa da taga ma wasu darorin ne aka jerasu har suna kusan tab'a rufin d'akin saboda yawa, haka aka rufe d'akin ana jiran asabar tayi maishi ta shiga. Duk wani abu da Muzaffar ya kawo saida Khairat ta tabbatar ta mayar masashi a cikin akwatinshi, duk wani abu data d'inka saida tasa aka nemo irinshi sannan tasa aka mayar masa, kamar dai yanda yayi itama motoci ta samu suka kai kayan har gidansu, had'e kuma da makullin motarshi, tunda yaga haka ya tabbatar da aikin Khairat ne ma'ana tayi hushi kenan, bai k'ara tsinkewa da al'amarin ba saida ya bud'e k'aramar motar ya samu goron daya bada da kuma enveloppe, yana bud'awa yaga kud'i ne a ciki kamar yanda ya bada, sai kuma k'aramar takadar data rubuta wasik'a da harshen french cewar, _"Bani ba kai, ba kai bani har abada, yunk'urin sake shigowa rayuwata a karo na biyu, daidai yake da yak'in duniya na uku, dan ba shakka yak'i ne zai b'arke tsakanin gidanmu da gidanku, *K'ARAMIN MUTUM* kawai._ Hawayen da yaji suna son zubo mashi yasa ya koma cikin gida ranshi b'ace, hamshak'iyar mahaifiyarshi dake zaune a d'akinta tana waya ya fad'a saman jikinta yana kuka, kashe wayar tayi tare da tureshi daga jikinta cikin jin haushi tace "dallah ni dagani shashasha kawai, kasan kana sonta uban wa ya aikeka d'aukar zigar aboki ana daf da d'aura aurenka? kawai saboda rashin tunani da lissafi saika yarda da abinda ya fad'a, yanzu gashi har yau bai sake zuwa inda kake ba, tunda burinshi ya cika." Ganin mahaifiyar tashi ma ta d'auki zafi yasa ta tashi ya fita ya koma b'angarenshi zuciyarshi kamar zata buga. **************** Tun ranar Umar Faruk bai sake zuwa gidansu Zuby ba bai kuma kirata ba, shirin d'aurin auren kawai yake yi amma sam ya daina jinta a cikin ranshi, musamman idan ya tuna abinda ta fad'a masa, haka kawai yake jin ba dad'i idan ya tunata yafi farin ciki kawai idan yana tunanin Khairat wacce yake da yak'inin ko sau d'aya bata tab'a tunaninshi ba. *Yau juma'a* gidan an tashi da shirye shirye da kimtse kimtse, kamar yanda muka sani lokaci na gudu, dan-danan sai aka fara tafiya masallaci, bayan gama sallah kuma aka sake d'aurawa Umar Faruk wani auren, *Umar Faruk Ahmad Adam* da *Zubeida Hamza*, daga masallaci gidan wani abokinshi *Abdul Azeez* suka wuce inda akasha gara tare da tayashi murna, Ishaq dai dariya yake masa duk lokacin da suka had'a ido dashi saboda tamke fuskar da yayi, bidiri sosai abokanshi suka shirya wanda ya kaisu har magrib, suna sallah kuma suka dawo gida inda aka fara shirin walima. Shiryawa yayi cikin wata sabuwar shadda ruwan toka had'e da takalma sai dai bai d'ora hula ba, yana fitowa ya samu taro harya fara cika, Abdul Azeez ne ya takura masa ya rakashi asibiti yanzu aka kirashi ankai kakarsu ba lafiya, jin uzurinshi kuma tunda bai nemi kowa ba saishi yasa suka shiga mota suka tafi. **************** *Amarya Khairat* ce zaune a falo a saman qafafun Mammie tana latsa wayarta, kirane ya shigo ta d'auka da "hello macho." "Gamu a k'ofar gidanku." cewar Rashida. "Gidan namu kuma mak'abarta ne da ba zaku shigo ba?" "Kinga kedai ki fito." "Wai lafiya, meya faru ne?" "Kai Khairat, kina b'ata mana lokaci fa, asibiti zamu wuce tare da Farida muke." "To naji ina zuwa." Mik'ewa tayi daga jikin Mammie ta d'auki kallabin doguwar bleue rigarta ta d'ora a kai tace ma Mammie "su Rashida ne waje wai asibiti zasu, bara naje naji kiran me suke min." Tana fita Mamie ta fito cikin shirin tarban Papa, zaune tayi tana fad'in "ina ta shiga kuma?" "Wai Rashida ta kirata suna k'ofar gida." Zunbur Mamie ta tashi tace "Rashida? na shiga uku, nifa bana qaunar yarinyar nan, wallahi ita ke qara lalata min yarinya." K'ofa ta nufa Mammie na kiran "ina kuma za kije? yanzu zata dawo fa." K'ofa ta nufa tana fad'awa mai gadi "kai duba min Khairat, maza ce nace ta shigo ciki." A cewar mai gadin "a'a Hajia ai har sun tafi." "Sun tafi ina kuma?" "Wallahi Hajia ban sani ba, taxi daice suka shiga." Dafe kai Mamie tayi tace "na shiga, ina zasu je kuma? me zan fad'awa mahaifinta?" Dawowa tayi tace "Mama kin gani ko? Khairat bata nan wai sun fita." Kafin Mammie tayi magana ta d'auki wayarta ta fara kiranta, Khairat kuma da tana fita ta samesu a cikin taxi Rashida ce tace "yawwa zo muje." Ta fad'a tana matsa mata nufin ta zauna, "ina kuma zanje bayan kinsan ba'a barina fita?" "Kinga asibiti zamu je k'anan Farida ne ba lafiya, dazu aka kaishi ya k'one da ruwan zafi, kizo muje yanzu zamu dawo daga nan sai muyi magana." Hannunta ta janyo ta fad'a cikin taxi d'in suka ja suka tafi, ba suyi nisa ba kuma kiran Mamie ya shigo wayarta, tana d'auka Mamie tace "kina ina?" "Mamie ina bisa hanya za muje asibiti ne yanzu zan dawo." Da sauri Mamie tace "amma kinsan ba kya fita ko ina ko? me yasa zaki fita haka kawai, idan mahaifinki ya dawo ya zance masa?" "Dan Allah Mamie karki damu, ba jimawa zanyi ba." Tana fad'a ta kashe wayar ta kalli Rashida tace "wace magana za muyi?" Kallon juna sukayi kafin Rashida tace "am Khairat, wallahi mutuminki yana cikin wani hali, yana buk'atar taimakonki sosai." "Wane mutumin nawa?" ta fad'a tana kau da kai. Farida ce tace "Muzaffar mana, kinga yanda ya koma saboda damuwa, wallahi sai addabarmu yake wai mu taimaka masa." "Yanzu dama akan maganar waccen banzan ne kuka saka na baro gidanmu ba tare da izinin kowa ba? kinga tsayar da mai taxin nan na koma gida in dai wannan ce maganar." Rik'eta sukayi suna fad'in "kinga shikenan to, ba zamu sake miki maganarshi ba, yi hak'uri." Harara tabi kowace a cikinsu tana fad'in "aikin banza kawai, mutumin daya ci min mutunci har zaku wani zomin da maganarsa , shi bai fad'a muku ba komai tsakanina dashi ba, ko sile baya bina bare ya takura min, mak'uddan kud'ad'e na kashe wajen biyanshi abinda ya min." Babu wanda sake magana har suka isa asibitin suka duba yaron da qafarshi ce kad'ai ta k'one sannan suka tashi zasu koma, bayan mahaifiyar Farida ta gargad'eta akan ta kula da gida da sauran k'annanta, fitowa sukayi suka tsaya a bakin titi suna jiran samun taxi. *Umar faruk* ne suka fito zasu tafi suma sun shiga mota suka tayar, bakin titi suka tsaya suna so kai kawon motoci ya tsagaita su samu su hau titi suma, a cikin waige waigen da suke sai kuwa Abdul Azeez yace "masha Allah, abokina da alama nima lokacin aurena ya kusa, domin kuwa naga wacce tamin." Haka kawai sai Umar Faruk yaji gabanshi ya fad'i, daurewa yayi yace "toh , wace mai sa'ar ce wannan?" "Gatanan gabanka kan gani." Sai lokacin Umar faruk ya kai kallonshi ga yan mata ukun dake tsaye, hakan yayi daidai da Khairat ta juyo saboda motar dake bayansu ba haskesu sosai, saida ya rintse ido saboda takaici da bak'in ciki, sam fitowa bada izininshi bai dameshi ba kamar rigar dake jikinta. Duk da bata kamata ba amma da yake tana da 'yar k'iba kuma yadin rigar yadine mai bin jiki, hakan yasa ya hango shatin kwanciyar pants d'inta da kuma bras d'inta, ga kuma kallabin k'aramin hakan yasa gashinta ya fito har ya kusan rufe shatin bras d'inta, duk da dai baida tabbacin gashin kanta ne, ranshi ya b'ace sosai musamman da abokin nashi ya haskesu da mota yana mata kallon k'wak'waf, dan suma k'awayen nata duk shigar tasu babu mai dama dama a cikinsu. A fusace ya fita daga motar ya tsaya bayanta ba tare da yayi magana ba, jin kamar mutum a bayanta yasa ta juyo dan ganin wane d'an rainin wayone, a take gabansu ya tsinke ya fad'i sai kallon kallo da sukewa juna, kasa magana tayi dan har cikin zuciyarta taji bata ji dad'in ganin daya mata a haka ba, kasa d'auke idonta tayi daga kanshi shima kuma haka. Rashida ce tace "macho, kin sanshi ne?" Had'iye yawu tayi ta kalli Rashida, muryarshi ta dawo da ita da yace "wuce muje." Kallonshi tayi amma wani irin bala'in kwarjini daya mata sai yasa ta nuna su Rashida da hannu, wani sabon kallo daya mata da idonshi fuskar nan ba hasken annuri ya sake cewa "wuce muje gida." "Amma ai....." "Nace ki wuce mu tafi ko." tsawar daya mata yasa ta kama hanya ba shiri , ganin haka yasa yabi bayanta ya bud'e mata bayan motar ta shiga, tana kallonsu Rashida suka wuce suka barsu, su kuma mamaki suke ko wanene shi, Farida ce tace "nifa ina tunanin ko shine mijin nata." "In kuwa shine gaskiya yarinyar nan mai sa'a ce, danni kin sanni fa ina son namiji irin wacce wallahi, da irinsu sunfi dad'in harka. Farida ce tace "ki daibi a sannu, dan kinsan yarinyar can ta fiki akuyanci, mijinta kuma yafi k'arfinki." ****************** Tunda suka d'auki hanya babu wanda yace tak , tafiya kawai suke Abdul Azeez kuma da kanshi ke kulle bai samu damar magana, dan yasan tabbas akwai wani abu a qasa saboda yanda yaga Umar faruk ya mu'amulanci Khairat d'in yasan ba sanin yanzu bane a tsakaninsu, Khairat kam tayi iya k'ok'arinta wajen ganin gabanta ya daina fad'uwa amma ta kasa, kamar yanda Umar faruk kejin haushinta da takaicin aurenta da yayi, a haka suka isa gida da kanshi ya fito ya bud'e mata k'ofar ta fito babu wanda ya kalli wani, izuwa yanzu kuma Abdul Azeez ya gane kuskure yayi dan ko ba'a fad'a ba wannan itace 'yar Mani Bukar. Wucewa tayi zata shiga shima yabi bayanta, tana daf da shiga gidan yace "kina haukane da kika da wannan kayan a jikinki, sannan da izinin wa kika fita?" A hassale ta juyo tace "..... 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 😭😭😭😭😭😭😭😭 _ALLAH KA SHIRYA MANA YARANMU MAZA DA MATA, ALLAH KA BAMU IKON TARBIYANTAR DASU, AL'AMARIN NAN YA FARA BANI TSORO WALLAHI, YARA QANANA SUN D'AUKI D'ABI'A MARAR KYAU, WASU GANI SUKE WASU KUMA YIN KANSU NE KAWAI, ALLAH UBANGIJI KA KARE MANA 'YA'YANMU DAGA B'ATA GARIN ABOKAI, ALLAH KA BAMU IKON KIYAYE DUK WANI ABU DA ZAI HASKU A IDON 'YA'YANMU HAR SUYI SHA'AWAR KWAIKWAYA._👏👏 😭😭😭😭😭😭😭😭 2⃣0⃣ "Ban gane ba, me kake nufi, me kayan jikina sukayi, wai ikone zaka min tun ban tare gidan naka ba? ina ruwanka da kayan jikina to? kana da matsala da hakan ne? karfa kace zaka rainani saboda kaji ance an daura mana aure, wallahi ba dauka zanyi ba kaji na fad'a maka, haka kawai zaka wani tsareni harda tambayar wai da izinin wa na fita, bayan a gidan mu nake har zaka min wannan tambayar, ko kana ganin iyayena basu da ikon da zasu bani damar fita? to in dai kai zan dinga tambaya kafin na fita da sai dai karna fita har abada, dan ba zan iya qasqantar da kaina har haka ba, kuma wallahi ka fita idona, kar kace zaka sake min irin tsawar da kamin d'azu musamman a cikin mutane, in kuma ba haka ba." K'wafa tayi mai k'arfin gaske ta juya zata shiga gida, wata fizgowa ya mata saida ta kai mashi karo a qirji, turata yayi ta kaima bango karo ya mata runfa da faffad'an jikinshi, kafeta yayi da ido sunyi ja saboda zafin maganganunta fuska a d'aure ba alamar wasa cikin dakakkiyar murya yace "waye ni?" Cike da tsiwa tace "waye fa daya wuce d'aya daga cikin gama garin mutane." Rufe ido yayi ya sake maimaita "waye ni nace?" Kallonshi tayi da ido tace "Umar....Faruk mana." "Nace waye ni a wajenki?" tsawar daya mata har saida mai gadi ya leko, amma ganin Khairat da angonta yasa ya koma, ita kam yanda muryarshi ta daki k'ok'on kanta yasa ta zabura da k'arfi tare da fashewa da qara har wayarta ta sub'uce ta fad'i, hannayenshi yasa a jikin bango kamar zai rumgumeta ya sake tsareta da ido yace "ina jiran amsarki." A hankali ta daga idonta ta kalleshi amma sai hawaye suka zubo mata, kau da kai tayi ta sauke ajiyar zuciya ba tace komai ba, sake matso da kanshi yayi daf da fuskarta yace "zamu kwana anan in har baki fad'a min ba." Cikin daga murya da jin zafi tace "to waye kai? me kake so nace? so kake nace *mijina*? to naji kaine *Umar faruk mijina*, shikenan? to kauce min a hanya zan wuce." Wani d'an iskan murmushi yayi mai kama da kuka tare da fad'in "humm." kafin yace "daga yau ina so na dinga jin muryarki k'asa da tawa, idan kuma kika bari k'uruciya da hauka irin naki yasa kika d'aga min murya, to ki kuka da kanki, dan zan miki abinda kaf a tarihi babu wanda ya kwatanta yi miki shi." Sunkuyawa yayi ya d'auki wayarta ya dangwara mata a hannu sannan ya juya ya shiga mota tana kallonshi har suka b'acema ganinta, juyawa tayi ta shiga gida kamar zata tashi sama, har Papa na falo suna jiran dawowarta, a tare suka mik'e ganin ta shigo da sauri tana share hawaye, Papa ne ya fara tambayar "shalele lafiya, meya faru kike kuka." Mammie ma d'orawa tayi da "shalele meya sameki, wani abu aka miki?" Kallonsu tayi cikin muryar kuka tace "karku damu ba komai." "Ya zaki ce ba komai? bayan kin fita cikin farin ciki kin dawo kina kuka, kuma an fad'a min wad'ancen yan iskan yaran ne suka fita dake." Ganin zasu takurata yasa tace "Mamie ba komai fa, tare dashi muke." "Shi wa?" cewar Papa. Turo baki tayi gaba tace "Umar Faruk." Fuska kowa ya saki yana murmushi har Mammie tace "to kuma a waje kika baroshi?" "Harya tafi." ta fad'a tana wucewa d'akinta. _Abinka ga manya_ duk sai sukayi tunanin ko zaman da tayi na sati d'aya ne yasa ya gagara hak'uri, shi yasa suka fita ya d'an rage zafi, 😂 masu hangen nesa kenan, wannan hasashen naku ba yau ba ba kuma gobe ba. Cikin b'acin rai da bak'in cikin abinda Umar Faruk ya mata ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin rigar bacci doguwa, dole ta toshe kunnuwanta da abin sauraro danta rage zafi. ******************* Tunda suka d'auki hanya babu wanda yayi magana, amma saboda ya nuna masa baisan komai ba yasa Abdul Azeez cewa " *wacece ita*?" Kamar ba zai amsa ba amma kuma ba tare daya kalleshi ba yace " *matata ce*" Shiru yayi dan duk wata magana da zaiyi yanzu zai iya janyo b'acin rai fiye da yanzu, har suka isa babu wanda ya sake magana, suna zuwa tuni taro yayi taro *ustaz Khalid* nata bada wuta, nan ya fara gaishe da malamanshi da uwaye da kuma kakanni , tare da sake miki gargad'i da nasiha akan rik'e adalci da gaskiya, wuri ya samu ya zauna kamar mai sauraron abinda ake amma a gaskiyar lamarin ba haka bane, harya fara hango irin rayuwar da zaiyi a tsakanin d'akin Khairat da d'akin Zuby, Zuby akwai k'arancin wayo, Khairat kuma da wayonta zata b'ata maka rai, amma dole ya d'auki matakin gyara tun kafin lokaci ya k'ure masa. **************** Zuby ce tsakiyar aunyt's d'inta guda uku, sun gama zigata tare da hure mata kunne, sun cire mata soyayya da tausayin Umar Faruk a ranta tun kafin aje ko ina, tilasta mata sukayi ta kurashi ta bashi hak'uri akan abinda ta masa, saboda akwai wani magani da suka siya mata, kuma dole aiki dashi sai suna shiri dan suna son ya kusanceta, wayar ta d'auka ta kirashi lokacin yana tsaka da tunani, yayi mamakin ganin kiranta sosai dan abune da bai tab'a faruwa ba suyi fad'a ta kirashi sai dai shi ya kira, dauka yayi baice komai ba, cikin taushin murya tace, "Amincin Allah ya tabbata a gareka angona yayah Umar." Nauyayyan ajiyan zuciya ya sauke yace "amincin Allah ya tabbata a gereki." Cikin shagwab'a tace "kenan ba zan samu ko wane irin suna daga gareka ba?" Murmushi tayi yace "ina tsoron nace amaryata kuma kiyi hushi ne." Cike da wayencewa tace "ba komai yayah Umar, ka kirani amarya zan amsa, tunda aunty Khairat ta rigani zama taka." "A'a, har yanzu fa babu wacce ta shigo hannuna, dukanku dai ina jira ku gama wainani sannan ku shigo gidan." Haushi ne ya kamata danta lura soma yake Khairat ta shigo gidan bayan yace taimako yayi, shi kuma baya so ne ya bada wata k'ofa da zata sa Zuby ta raina Khairat musamman ace ta dalilinshi, koba komai itama matarshi ce kuma uwar gida, a dak'ile tace "dama na kirane na baka hak'uri abisa abinda ya faru, dan Allah ka yafe min ba zan sake ba." "Ba komai k'anwata, ya wuce ai." "Na gode, saida safe, dan naji kana cikin jama'a." "Saida safe." ya fad'a suka tsinke kiran. Haka taro ya tashi lafiya bayan addu'o'in da aka zuba musu, dare yayi kowa ya kwanta amma banda Umar Faruk, a qarshema d'akin Khairat ya bud'e ya shiga, fitilar d'akin ya kunna a hankali ya dinga sauke numfashi saboda wani baqaraken k'amshi dake shigar hancinshi, had'e yake da kamshin turaren wuta da kuma turaukan dake zube a saman coiffeuse da mayuka har babu wurin aza wani abun, bin d'akin yake da kallo ko ina yana kallon irin kayan da aka cika d'akin dashi, wai nan danma yana ba'a samu irin wurin da ake so bane, kusan komai na d'akin pink couleur ne hakan yasa yace "da alama shine couleur préféré (best coulor) d'inta." A sannu yake tunanin ranar daya fara shiga d'akinta yana fad'in "girman d'akinta shine kaso d'aya na bisa ukun gidan nan, girman gadonta kuma d'akin nan ba zai daukeshi ba, duk da banga ban d'akinta ba, amma na tabbata ta kusa girman d'akin nan." Ajiyar zuciya ya sauke tare da sakin murmushi yace "taya zata iya rayuwa a d'akin nan? bayan gashi tagar dake akwai ma kaya sun rufeta, taya zata iya rayuwa da wannan pankar? bayan acan ac take kunnawa , taya zata iya rayuwa a gidan nan da mutane haka? bayan ita acan ita kad'aice ba k'ane ba k'anwa ba yaya ba aunty." _Wannan itace rayuwar daya kamata ta fara kota koyi hankali_ ******************** *A b'angaren* tunda aka tashi da safe ta tashi jiki ba k'wari, gashi Mamie ta kira mai kitso amma sam tace bata so, ayi juyin duniya tace ba taso dole aka barta, da qyar ta bari aka mata jan lalle tunda waccen ya goge dan jikinta baya da kama lalle, duk da mutanen da suka zo dan rakiyar amarya Papa yace sam bashi ba wannan bidi'a, dan haka da kanshi zai kai yarshi gidanta tare da rakiyar kakanninta. Abin yama Khairat yawa dan haka tun yamma ta fara kuka, amma sai tace musu kukan rabuwa ne dasu, haka akayi magrib akayi isha'i, ba wani shiri tayi ba atamfa ce ta zabga riga da zane d'inki simple, kasancewar bata tab'a saka zane simple ba saiya mata kyau d'as, Mammie da Hajia *Maryama* ne suka kamata Papa da kanshi ya tuk'a mota suka nufi gidan amarya bayan d'an jan kunne da Mamie ta sake mata, sai bayan fitarsu Mamie kuma ta fashe da kuka saboda tunanin rayuwar da yarta za tayi a gidan yawa. Kasancewar a gidan Baba Papa ya koyi *sunna* hakan yasa basu tarar da wasu 'yan tarban amarya ba bare abincinsu, mutanen gidan ne kawai kuma yara na islamiyyar dare dan haka sai uwayen, tarba aka musu sosai tare da Baba aka musu iso zuwa d'akinta, Papa ne ya kama hannun Khairat ya zaunar da ita bakin gado sannan ya zauna zauna kujerar dake kallonta, su Mammie ma zaune sukayi kusa da ita kafin Papa ya kalli Baba yace "surukin namu yana nan? ina so zan d'anyi magana dashi." "Ba damuwa, ina jin ai baiyi nisa ba, bara na dubo muku shi." Baba ya fad'a tare da fita waje. A gidansu Ishaq aka kira Umar Faruk tun saman hanya gabanshi ke faduwa, haka ya shigo cikin gidan har kuma d'akin, Papa ne ya masa nuni daya zauna kusa da Khairat, kallon Papan yayi ya kalli wajen da zai zauna sannan ya matsa a hankali ya tsoma k'ugunshi, duk da fuskarta a rufe take da mayafi amma sai yake ji a jikinshi hararanshi take, kuma kuwa hakane😂dan bayan harara harda murgud'a baki da gunaguni. Papa ne ya fara da "Umar Faruk, ga Khairat nan, mun kawo maka ita, kuma amana muka baka, muna fatan zaka rik'e mana ita abisa gaskiya da amana, Umar Faruk na yarda da kai, bana jin akwai ranar da zata zo ka bud'i baki ka gorantawa Khairat akan taimakon daka mana, ka sani Umar Faruk akwai ranar da Allah zai tashemu kuma ya tambayemu yanda muka zauna da iyalenmu , kayi adalci a tsakanin matanka domin hakan ne kad'ai zaisa ka samu rabo a ranar gobe k'iyama, kasan wani abu Umar Faruk, ba wai gaggawar aurar da Khairat bane muke da har yasa muka baka ita a waccen ranar, kawai dai na yarda da tsatson daka fito, kuma ina da yak'ini akan tarbiyar daka samu, ina son Khairat sosai fiye da komai a duniya, domin ita kad'ai na mallaka, bawai ina son zamanta anan bane dan nasan dole kafin ta saba zata sha wuya, amma darasin da zata koya a zamanta anan d'in shine yafi min komai dad'i, dan nasan *tarayyarku* zata zamar mana alkairi." "Daga qarshe kuma, ina sake jaddada muku da kuyi hak'uri da junanku, Umar Faruk, akwai abinda ya kamata ka sani a game da Khairat, tana fama da wata muguwar rashin lafiya wacce idan ta taso mata takan shiga tsakanin halin rayuwa da mutuwa, duk da ince kusan nine silar wannan rashin lafiyar, amma dai a yanzu ina fatan kai ka zama maganin wannan cutar, wacce damuwa da kad'aici ne suka janyo mata ita, da fatan zaku zauna lafiya, Allah ya muku albarka, Allah ya baka abinda zaka ciyar da matanka, Allah kuma ya baka ikon yin adalci a tsakaninsu." "Ameen." mutanen d'akin suka amsa dashi. "Insha Allahu Baba zanyi k'ok'arina wajen kawar da kowace damuwa a tare da ita." cewar Umar Faruk yana satar kallonta. Murmushi Papa yayi yace "Allah ya baka iko , ke kuma baki ce komai ba?" inji Papa yana kallon Khairat. A hankali ta d'ago da kanta tana d'aga mayafinta tare da kafe Umar Faruk da ido, shima ita ya kalla amma ganin kallon da take masa bana arzik'i ne yasa ya kawar da kanshi, maida kallonta tayi ga Papa tace "nayi muku alk'awarin zama dashi...." sai kuma tayi shiru ta sake kallonshi, sai dai shima a lokacin ya kafeta da ido yana jiran yaji me za tace, ba tare data d'auke kai daga gareshi ba tace "har abada." Wani irin farin cikine Umar Faruk yaji ya mamayeshi ba tare da yasan dalili ba, su kaka kuma hak'uri dai suka sake jaddaja musu suyi da junansu, nan suka tashi zasu tafi Umar ma ya mik'e dan rakasu, da gudu Khairat ta k'arasa ta rumgume Papa ta fashe da kuka, nan ya shiga rarrashi da ban magana tare da k'ok'arin yakiceta a jikinshi amma ta cije , a lokacin kuma Mammie ta janyo hannun Umar Faruk ba tare da kowa ya gani ba ta bashi magungunan Khairat tace masa, "Wannan sune maganinta idan ciwonta ya tashi, ina fata zaka zamar mata waraka , a k'arshe ma ku jefar da maganin saboda rashin anfaninshi gareku." Kai ya girgiza yana mamakin wane irin ciwo ne, ko dai aljanu gareta? ya tambayi kanshi, murmushi yayi ya rik'e hannun Mammie yace "na miki alk'awarin haka, insha Allah." Lokacin kuma muryar Baba ta dawo dasu yana fad'in "kai Umar Faruk, kamata dan Allah su samu su tafi." Kallon Baban nashi yayi yana tunanin ta yanda zai fara rik'eta, wasu yawu ya had'iya tare da yin k'unar bak'in wake yayi kansu zai b'anb'areta, ita kuma tunda taji ance ya rik'eta ta sake sark'afe Papa tare da lab'ewa bayanshi tana fad'in "ni wallahi ba zan zauna, kawai ku tafi dani, wannan fa mugune ba imanine dashi ba." Papa ne ya kalli Umar Faruk da yayi tsaye yana sauraronta yace "dan Allah ka rik'e matarka kaji." A hankali ya matso ya fara k'ok'arin b'anb'areta daga jikin Papan, da taimakon Papan ya samu suka rabata dashi, da sauri Papa ya bar d'akin tare dasu Mammie, tana ganin haka ta sake fashewa da kuka tana fizge kanta tana so ta fita, shi kuma rik'eta yayi sosai hakan yasa take k'ok'arin zubawa a guje, da k'arfi ya sake jawota ta fad'o kanshi ya matseta sosai a jikinshi, sake volume tayi tana kukan shi kuma sai wutarshi ta d'auke d'uf , a hankali taji yana shafa bayanta yana fad'a mata wani "shiiiiiiii, ya isa haka to." kamar yarinya k'arama, da sauri ta janye jikinta ta fad'a saman gado ta kwanta tana ci gaba da kukanta , shi kuma tab'e baki yayi ya fita daga d'akin sai gidansu Ishaq. Umar Faruk bai dawo gidan ba saida *23:30* tayi sannan, yana shigowa ya shiga d'akinshi ya cire kayan sannan ya shiga wanka a ban d'akinsu ta tsakar gidan, yana fitowa kuma ya sake shiga d'akin a shirya cikin doguwar riga fara qal duk kai da kawon nan yayi shine cikin sand'a kar Baba yaji, sannan ya fito ya nufi d'akin amarya. _Kuzo mu raka ango siyan baki_😂😁 Yana shigowa ya sameta yanda ya barta sai ajiyar zuciya take saukewa a hankali alamar bacci ya d'auketa, kashe mata wutar d'akin yayi ya fita ya rufe k'ofar tare da rufe gaba d'aya kewaye sannan ya koma d'akin tuzurai 😁Umariri kenan. Ya jima baiyi bacci ba suna waya da amarya Zuby wacce take farin ciki take ganin kamar ta hanashi gabatar da daren farkonshi , nikam nace 😏 _kin rako mata duniya dai, lokacin da zai yishi ma sai kin shigo gidan_, suna gama waya kuma saiya d'auro alwala ya fara jera nafilfili har asuba, kiran farko ya bud'e k'ofa a hankali danya koma d'akin amarya ya tasheta, amma ina duk hanzarinshi Baba ya rigashi , domin kuwa yana bud'e k'ofar sai kuwa Baba a bakin panpo yana d'ibar ruwa a buta , cike da kunya da sanyin jiki ya nufi d'akin ya bud'e ya shiga ciki, tana nan har yanzu kwanciyarta kawai ta gyara, saida ya gama kallon qafafunta da suka sha lalle suka yi tsaf dasu sannan ya tab'a qafar, a hankali ta fara motsawa harta tashi zaune ta wartsake sosai, kau da kai yayi yana shan k'amshi yace "ki tashi kiyi sallah, lokaci yayi." Wata muguwar harara ta dalla masa tare da juya baki, qasa da sama ya kalleta sannan ya wuce abinshi, har tayi kwance kuma taji gumi ma ya isheta, tashi tayi ta cire mayafin jikinta da d'an kwali sannan ta mik'e ta cire rigar atamfar sannan ta d'auki t-shirt matsatsa mai k'ananan hannuwa tasa, bata cire zanin ba dashi ta fito d'an k'aramin kewayen nata, duk da duhun asuba saida ta gama kallon ko ina, tabb', wai itace zata rayuwa a wannan gidan, hayaniyar da take ji yasa ta lek'a ta gajeruwar katangar saboda ta fita tsayi, kai komo kawai mutanen gidan keyi yara da manya sunata alwala, da mamaki take kallon mutanen da ko ganinta ba suyi ba, a ranta tace "duk mutanen gidan ne wannan kamar ana biki, lallai ma.", a qalla sunkai ashirin kosu haura ashirin, kujerun da aka jera a wajen ta zauna duk da fitsarin da take ji amma tana so ya zo ya nuna mata ban d'akin. Ana gama sallah suka kamo hanyar zuwa gidan, a hanya kuma Baba saida yama Umar Faruk fad'a akan abinda yayi, anan take ya bada hak'uri tare da alk'awarin kiyaye gaba, suna shigowa Baba ya tsaya d'akinshi na soro, Abbakar yayi kewayenshi dake had'e da nasu Umar, su Usman ma suka shiga d'akinsu dake kusa da kewayen iyayensu mata, saida ya shiga tsohon d'aki ya had'a kaf abin buk'atarshi dan tarewa d'akin amarya sannan ya fito da kaya nik'i nik'i, yana shigowa ya tsaya kallonta ganinta zaune da alama ba tayi sallah ba. "Kinyi sallah?" tambayar daya wurga mata kenan. Tashi tayi daga kishingid'ar da yayi ta fara rabka hannuwa tana jujjuyasu tana fad'in "toh malam, ina zanyi sallah? ka nuna min inda zan kama koda ruwa ma bare nayi alwala, naga gidan naku har yanzu bak'in da suka zo biki basu tafi ba, to ina zan fita bansan kowa ba." Ya gane akwai cin zarafi a maganarta, amma saiya dake ya nuna mata da hannu yace "ga ban d'akin nan." Yana fad'a ya wuce da kayanshi ya shige d'akin ya ajesu a inda yaga wuri kafin yayi zaune yana tilarwar karatu, tunda ta lek'a taga matsatsan bayin ta fito ta sameshi d'akin tace "wai malam me kake nufi? waccen abar itace wurin wanka, da komai da komai?" "Itace, idan zaki shiga ki shiga, idan ba zaki shiga ba ki zauna a haka matsalarki ce." ya fad'a ba tare daya kalleta ba. Cikin d'aga murya tace "inaaa, wallahi ba zan iya ba, to wannan idan na shiga zan iya tsayuwa ma kuwa? tunda ni dai ba gajera bace, uwa uba kuma kai, ya za kayi kenan?" "Babu ruwanki dani." ya fad'a a daqile. "To dama me yayi ruwan nawa da kai, ni dai ka samo min gurin da zanyi wanka a wale , amma ba wannan kurkukun ba." Tana fad'a ta koma gado ta zauna, ganin da gaske take kuma gari na haske yasa yace "ki tashi kiyi sallah, in yaso kyazo kici gaba da zaman har sarkin zama ya sameki." "Ba zanyi ba har sai nayi wanka." "Ki tashi nace." duk da jin amon muryarshi ba wasa amma bata tashi ba. A zafafe ya taso yayo kanta yana fad'in "dake fa nake magana kina jina kinyi shiru, zaki tashi ko saina b'allaki?" Gabanta ya tsaya yana kallonta itama kuma shi take kallo, tsaye ta mik'e fuska a had'e tace "wai me? dukana za kayi? hahaha, kai dai kasan da ganina wallahi ba zan daku gareka ba, dan ba zan tsaya sanya ba wajen zage k'arfina mu daku da kai ba, idan kuma hakan ya gagara tofa akwai k'ungiyoyi da dama masu kare hakk'in mata, wallahi tsaf zansa a d'aure min kai." Saida ya shafi kansa yace "idan harna tashi dukanki, to ki sani dukan da zan miki bama zaki iya tuna meya faru dake ba bare har kiyi k'arata ba, shi yasa nake so ki bini a hankali mu zauna lafiya." "Yanzu wuce kiyi sallah, dan akan wasa da sallah wallahi sai ajimu dake a kaf garin nan." Ba yanda ta iya dole ta wuce ta shiga ban d'akin ta kama ruwa sannan ta fito tayi alwala ta koma d'akin, saida ta jima kafin ta samu hijab d'in da Mamie ta d'inka mata sabbi sannan ta d'auki sallaya zata shinfid'a ta kallesa da harara tace "ina ne gabas?" A tunaninshi iskanci ne kawai amma ta sani dan haka yace "ki kalleni kiyi sallahn." Ai kuwa shinfid'awa tayi tana kallonshi ta kabbara sallah, ganin da gaske take sallaceshi za tayi yasa yayi saurin cewa "wai ke bahaguwar inace, yanzu nan shine gabas? dallah malama can zaki kalla." Wata hararar ta sake banka masa sannan ta juya ta daidaita ta ci gaba da sallahta, tun daga sallah ya fahimci akwai matsala kuma yayi niyyar gyara mata, tana idawa shi kuma ya shiga wanka kasancewar akwai k'aramin panpo ciki, yana fitowa ya samu ta koma kan gado tayi kwance, gashi yana so ya canza amma ya kasa, lura da tayi da hakan yasa ta tab'e baki ta juya masa baya tana fad'in "me zan kalla a jikin? sai kace wata mayya." Bai kulata ba harya gama shirinsa cikin jan raiga mai dogayen hannu da bak'in wando da takalma qafa ciki bak'ak'e, yayi kyau sosai sai turarenshi daya fesa sannan ya juya zai fita daga d'akin dan yau babu aiki , saurin juyowa tana fad'in, "Kaga malam, wannan shirgin kayan naka ka tattaresu daga nan, ka bud'a armoire (drower) nan na qarshe akwai wuri ka zubasu." Ajiyar zuciya ya sauke mai k'arfi kafin ya fara d'iban kayan yana jerawa, duk kayan saida ya samar musu matsuguni sannan ya rufe, ya sake juyawa zai fita kenan Ruk'ayya ta rabka sallama daga k'ofar d'akin.... *Me kuka ce fan's a game da zaman nan*😁 _Ina sonku masoyana , addu'o'inku ma kad'ai sun ishemu farin ciki._ Allah barmu daku.💐 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _My 🅱K, ina tayaki murnar kammala wannan novel mai suna, 💘 *NA BAKI RAYUWATA* 💘, wallahi Allah har cikin raina nake ji kamar na gani da idona a lokacin mutuwar Affan, sosai wannan labarin ya shigeni dan saida na zubar da hawaye na gaske😭, Allah yasa wannan fad'akarwa da ki kayi taje inda muke so kuma ayi anfani da darasin ciki, Allah ya baki ladar tare da sakamakon gidan aljanna, Allah kuma ya qara miki lafiya sai mun jiki a next novel._ *ina yinki tawan.* _My Seeya, barka da fara sabon novel mai suna *QADDARATA*, daga jin sunan kasan zai bada kala dan kowa da tashi qaddarar, Allah ya baki ikon kammalashi lafiya kamar yanda kika fara lafiya, fatan nasara my see see._😘 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 2⃣1⃣ "Wa'alaiki salam, Ruk'ayya shigo." cewar Umar Faruk. Wata sallamar ta sake yi tare da bud'a labulan d'akin ta shigo, saida ta sunkuya ta aje kwanukan dake hannunta sannan ta d'ago tace " ina kwana yah Umar, ina kwana aunty Khairat." ta fad'a tana kallonta. Umar Faruk dai ya amsa amma banda Khairat da take tunanin itace matar tashi, jin bata amsa ba yasa ta kalli Umar Faruk tace "dama Mama ce tace na kawo muku abin karinku." Juyawa tayi ta fita Umar Faruk kuma yace "na gode." Kwanukan ya d'auka a aza saman karamin tebur d'in dake tsakanin gado da doguwar kujerar nan sannan ya zauna yana kallonta, ita kam ta d'aure fuska dan haushin Ruk'ayya taji sosai, ganin shirun ba zai gyarashi ba yasa yace "ki taso ki zuba mana abinci muci." Cikin jin zafi tace "nice zan zuba maka abincin? to kar Allah yasa kaci, ni kaga nayi kama da masu zuba abinci, ka tab'a jin koda labari cewa an ganni ina zuba abinci ko a gidanmu, ai kaima ka gani ranar, dan haka in zaka zuba ka zuba kaci." Shiru ya d'anyi na dakiku kafin ya tashi inda yaga tarin kayan anfani ya d'auko plate da cokali guda biyu ya zo ya fara zubawa, saida ya gama ya kalleta yace "ki taso kici." Sai lokacin ta juyo ta kalleshi, plate d'in ta kalla ganin malku ne (naman kan rago) yasa ta yamutsa fuska tace "wacece? ni zanci wannan abun? bana cin a wannan lokacin, kawai kaci abunka." Banza yayi da ita kawai ya d'auki bred ya fara ci, yana cikin ci yaji tace "wannan itace matar taka?" Cak ya tsaya daga kai lomar da zaiyi, cikin rashin fahimta ya kalleta amma sai tace "wallahi ban tab'a tunanin zan iya auren mutumin da bai min alk'awarin zama dani ba ni kad'ai, amma sai gashi wai na auri mai mata, mtssss, rayuwa kenan." Shi kam tunani yake ko bata san jiya ne aka daura masa auren ba, to kenan iyayenta basu fad'a mata ba kome? ji yayi abincin ya fita a ransa kawai ya fita ya wanke hannu ya dawo d'akin, zaune ya sake yi a inda ya tashi yana kallonta yace "wannan ba *matata* bace, kanwata ce, jiya ne aka daura aurena kuma bata tare ba sai nan da wata biyu." Kallonshi tayi amma saboda harbawar da zuciyarta keyi yasa ta kau da kai tana guna guni, ganin ba za tayi magana yasa ya mik'e ya d'auki turare ya fesa a hannayenshi sannan ya fice ya barta. Wani bala'in haushinshi take ji dama matar duk da bata ganta ba, ta jima cikin d'akin har rana ta take sosai sannan ta mik'e ta nufi waje, tana fitowa daga 'karamin kewayen nata ta ja ta tsaya tana 'kerewa gidan kallo, yana da girma amma yawan mutanen gidan yasa duk an matseshi , duk yara na islamiyya sai Ruk'ayya kad'ai dake k'ok'arin hura wuta dan d'ora abincin rana, sai kuma Saratu dake kamata da alama a tare ake girkin , iyayen kuma su uku suna zaune duk da dai biyu sun had'e kai waje d'aya, ta jima tsaye babu wanda ya lura da ita har saida haushi ya kamata yanda Ruk'ayya keson wutar ta kama amma tak'i kunnuwa. Cikin d'aga murya tace "waike dan Allah ba zaki bar hura wutar nan bane, duk kibi kin cika mutane da hayak'i, wai dama da ice kuke d'ori? tabb'." Sai lokacin kowa dake wajen ya kalleta, Ruk'ayya ma juyowa tayi sai dai kafin tayi magana ke Mama Maimuna sai kika ce "kaji kuma wani iyayi , to in tabar hura wutar dame za ayi d'orin kenan, ko kin tanadar mata wani abun ne? kiji rashin kunya kai." Mama Sa'a ce tace "ah to dai ganin min hanya, mu za'a yiwa fitsara anan." Takowa Khairat ta fara yi saida tazo har gabansu ta tsaya tace "daku nake magana? kunji nace kune da kuka samin baki? to karku sake min irin haka in baso kuke na muku rashin mutunci ba, ku in banda ma qaddara kun isa ku ganni cikin gidan nan bare har kumin katsalandan a harkata." K'wafa tayi ta juya zata wuce Sa'a tace "ke mu kike wa rashin kunya? kinsan komu su waye? muma fa iyayen Umar Faruk ne." "Saime? idan ku iyayenshi ne nace saime? na shiga harkarku ne? ko kuma shi yace ku dinga shiga tawa sabgar? to bana so." Tana fad'a ta juya su Mama da Saratu kam mamaki ma ya gama kashesu daga inda suke, sun d'auka ta tafi ne amma sai suka ga ta sake fitowa da wayarta a hannu da da d'aya daga cikin kujerun nan, ta zauna a bakin k'ofar shiga b'angaren nata, waya take sai dai basa jin me take fad'a, Ruk'ayya dai ta samu wutarta ta kama bayan wuya da tasha ta fara aikinta gadan gadan, su Mama Sa'a kuma sai satar kallonta suke daga nan amma baki ya mutu murus, a qalla awa d'aya aka d'auka tana zaune ta d'auki wayarta ta kara a kunne saboda kiran daya shigo, tana d'auka tace "ok ina zuwa." ta kashe wayar. Mik'ewa tayi ta nufi hanyar da take tsinkayan mutane na wucewa ba kallabi a kanta sai wannan k'aramar rigar da zane ta fita, a k'ofar gidan ta tsaya wasu samari ne guda biyu, "yawwa ku shigo dashi." ta fad'a tana komawa cikin gidan, Umar Faruk dama ba wane wurin yaje ba suna k'ofar gida shida Ishaq da wasu abokansu su hud'u, ji yayi kamar zai fashe daya tsinkayeta amma ya zaiyi, sharewa kawai yayi ya basar, suna shiga gidan ta kalli Ruk'ayya tace "ki nuna musu inda zasu aje miki." Kowa da mamaki yake kallonta da samarin nan saboda ganinsu sun shigo da cuisinière mai guda hud'u da kuma butalin gas 5kilo, duk da suna cikin zulumin abinda tayi saida kowa yayi farin ciki, sai dai mahaifiyar Umar Faruk najin d'ard'ar, da ba lallai malam ya amince ba, nan Ruk'ayya ta nuna musu cikin wata rufa suka had'a mata shi sannan suka juya inda Khairat ke tsaye, dama ta shiga d'aki ta fito kudi ta mika musu masu yawa sukayi godiya suka tafi, itama d'akin ta koma tayi kwance Ruk'ayya da Saratu kam ai sai suka mayar da tukanansu sama cikin jin dad'i, ai sai suka manta da rashin kunyar da tayi, yayin da Mama Sa'a da Mama Maimuna suka waro ido suke tunanin sunci arzik'i dan haka su kwantar da kai kawai. Yara na dawowa kowa baki bud'e sai farin ciki, nan suka rankaya suka nufi d'akin dan ganin amarya, suna zuwa sun sameta ta kasa bacci tunda ta shiga zafi ya dameta duk da pankar data aje gabanta, binsu take da wani kallon tsana da qyama suma yaran kallonta suke saboda kallon da take musu, ganin sunyi zaune wasu qasa wasu akan kujera yasa tace "ku kuma fa daga ina?" Mai wayon cikin ne yace "ina kwana aunty amarya, mu kannan yah Umar ne, jiya bamu ganki ba kuma kuma da safe muka tafi islamiyya, shine yanzu muka zo mu ganki." "Tofa." ta fad'a a wahalce. Sauka tayi daga kan gadon ta nufi wata coffre ta bud'a ta d'auko chocolat tazo ta bawa kowa d'aya d'aya, haba ai da gudu aka fita ana murna ana ji wannan amarya mai ja ce, 😂haba kudai baku sani ba, dan ita ta basu ne dansu tafi su barta, suna fita cikin farin ciki suka had'u da Umar ya shigo gidan shima, cike da murna sukayi kanshi Zeinab na fad'in "yah Umar, kalla aunty amarya ta bamu." Fuskarta ya shafa yace "ince dai kun mata godiya?" Shiru sukayi suka kalli juna dan sun manta, ai da gudu suka sake komawa shi kuma ya nufi wajen Ruk'ayya da Saratu dake girki baki bud'e har sun kusa kammalawa, "wannan fa 'yan mata?" Saratu ce ta harareshi tace "na fad'a maka ka daina kirana yan mata fa." "To naji na daina, ina kuka samu wannan?" "Aunty Khairat ce tasa aka kawo mana." cewar Ruk'ayya. Baice komai ba sai juyawa da yayi ya nufi b'angaren nasu ya rasa wane hali zuciyarshi ke ciki, farin ciki ko k'unci, yaran na fitowa shi kuma ya shiga, tana ganinshi ta sauko daga kan gadon tana fad'in "yawwa, dama kai nake jira dan Allah ka nuna min inda zanyi wanka, tun jira rabona da wanka fa." Kallon kwanukan daya ci abincin safe yayi yace "amma aina nuna miki ban d'akin, watak'ila dama wankan bai dameki ba shi yasa kike so ki d'ora laifin ga ban d'akin." "Humm, nida nake shiga cikin baho cike da ruwa nayi link'ayata son raina, shine zaka nuna min wannan banzan douche d'in kace wai a ciki zanyi wankan, kaima kasan ba zai yiwu ba wallahi, koka nuna min inda zanyi, ko kuma na tub'e a tsakar gidan nan nayi wanka na dan nan ne kad'ai zai isheni , in yaso sai kace ma kowa ya rufe idonshi." "Kije kiyi mana ga wajen nan, inkin fasa ba sunanki Khairat ba." Yana fad'a ya juya ya bar d'akin saboda rashin sanin wacece Khairat, bayanshi ta biyo ya dauka shi take bi hakan yasa ya tsaya yana kallonta, wuceshi tayi ta fito tsakar gidan ta fara kalle kalle, Ruk'ayya ce ta hanga tana kashe wuta da alama ta gama, "ke." ta kira Ruk'ayya dashi. Kallonta Ruk'ayya tayi tace "na'am." "Zo nan." da sauri ta taho ta tsaya gabanta, babban bokiti nake so ki cika minshi da ruwa ki aje min nan, saiki fad'awa iyayenku su koma d'aki zanyi wanka." Da mamaki fal a fuskarta ta kalli Umar Faruk dake bayansu, ce mata yayi "kije kici gaba da aikinki." Wucewa tayi Khairat kuma ta kalleshi tace "aini ba musaka bace zan iya da kaina." Kewayen nasu ta shiga ta samu bokiti ta fito da nufin d'ebo ruwa a bakin panpo kawai ya rik'e hannunta yace "ke mahaukaciyar inace ne? me yasa baki da h...." Bai k'arasa ba tace "wallahi karka kuskura ka k'ara kirana bana da hankali ko mahaukaciya, wai ka mantani ne da kake fad'a min haka, ko dan kaga ana kiranka da mijina shi yasa, to bana so wallahi kaji na fad'a maka." Fizge hannunta tayi zata wuce yayi saurin tare gabanta yace "kinga saurareni, kiyi hak'uri ki shiga nan kiyi wankan , daga baya zansa a gyara miki tunda ba kya so, kinji?" Zuyawa tayi ta kalli douche d'in sannan ta kalleshi tace "idan ma baka gyara ba wallahi ni zansa a gyara, kawai douche sai kace gidan b'eraye." Wucewa tayi ta fad'a douche d'in ta cire kaya ta cillo kamar yanda ta saba, rigar data jefo qarshe sai a fuskar Umar Faruk da zai shiga d'akin, a hankali ya janye rigar ya kalli sauran kayan pants bras da zanin, sunkuyawa yayi ya kwashesu ya shiga dasu d'akin ya aje mata, ruwa ta makama jikinta ta d'auki sabulu ashe bata d'auko ba ta d'auka douche d'inta ce wacce ke akwai komai da komai, cikin d'aga murya tace "ka d'auko min sabulu." Shirun da taji yasa ta sake bud'a murya tace "ka d'auki min sabulu, kona fito na d'auka." Tun maganar farko ya jita ya kuma tashi d'auka, jin abinda ta fad'a a qarshe yasa yana fitowa daga d'akin yana b'are sabulun a cikin kwalishin yace "kizo ki d'auka mana." Yana daf da kaiwa bakin douche d'in ita kuma ta zuro da kai za tayi magana, da sauri ta dage qirjinta saboda bayyanar da yayi tare da komawa ciki tayi shiru, yana ganin haka ya juya bayanshi ya mik'a mata sabulun yana fad'in "gashi." Amsa tayi sannan ta fara wankan shi kuma ya fita daga gidan, Ruk'ayya ya turo ta d'auki kwanunan ta wanke sannan ta zubo musu wani abincin ta kawo ta aje, duk lokacin Ruk'ayya na mamakin irin wankan da take data jima haka, amma a b'angaren Khairat fad'a da guna guni kawai take rusawa daga cikin douche d'in, sai gashi ta fito ba tare da tayi abinda ta saba yi ba, ta fito daga wanka cikin minti sha biyar zuwa ashirin, d'aki ta shiga ta fara shiri tana ci gaba da masifa akan douche d'in. K'aramar riga ce mai siraran hannaye ta kamata sosai duk ta fito mata da mamanta , sai kuma jan siket data d'ora a saman rigar har kusa da qirkinta, a bud'e yake siket d'in sai dai iya gwiwa ya tsaya mata, raba gashinta tayi gida biyu tasa k'ananan chouchou (ribom) ta d'aureshi, bata wani kwalliya ba sai turare data shafa ta kuma fesa sannan ta d'auki wayarta tasa takalma ta fito farfajiyar gidan. Wata kujerar ta d'auka ta aza 'kofar kewayen nasu ta zauna dan zafi ya isheta, daga yaran har iyaye satar kallonta kawai suke babu wanda yayi magana, mahaifiyar Umar Faruk kuma tana so tayi magana amma tana jin tsoron wulak'ancin da zata mata, waqa tasa a wayar ta fara biyarta tana rausaya daga zaune, mak'ota da yan uwa suka fara shigowa ganin amarya, amma duk wanda ya shigo saiya nufi wajen mahaifiyar Umar Faruk ya zauna yana tambayar ina amarya, da an nuna masa Khairat saiya tashi yana addu'a Allah ya kyauta, a qarshe da taga kowa ita yake kallo, aje wayar tayi ta zuba tagumin rainin hankali tana bin kowa da ido itama, hakan yasa gidan yayi shiru sai magana qasa qasa. Baba da Abbakar ne suka taho zasu shigo gidan ganinsu yasa Umar Faruk ya biyosu suka shigo, da sallama suka shigo amma ta Umar Faruk saita tsaya saboda ganin Khairat da wannan kayan a jikinta, Abbakar ma dai duk'e kai yayi qasa ya nufi inda mahaifiyarsu take zaune ya tsugunna, Baba ma haka ya k'araso jiki ba k'wari saboda ya riga daya shigo, kamar wanda k'wai ya fashema a ciki Umar Faruk ya tako ya nufi wajenta, yana kaiwa cikin zafin nama ya finciko hannunta yayi cikin d'akin da ita. Qarar da tayi lokacin daya fizgi hannunta yasa Baba ya kalli Mama yace "kinga, tashi dan Allah kira minshi, sai yayi b'anna yaron nan kin sanshi da bak'ar zuciya, karya lahanta 'yar mutane." Da sauri ta tashi ta nufi d'akin nasu, suna shiga ya jefata saman gado cikin b'acin rai, zaiyi magana ta rigashi da cewa "meye haka wai, kana haukane? ni sa'arka ce da zaka min wannan pigar kazar mahaukaciyar." "Mtssssss." tsaki tayi ta fito daga d'akin zata sake komawa inda take, shi kuma dama tsakin yafi bashi ma haushi, da azama ya biyota ya cakumo hannunta ya juyo da ita da k'arfi, wani irin zafine daya ratsata saboda rik'on daya mata yasa ta janye hannunta daga gareshi hawaye fal idonta, kasancewar shima yayi niyyar sakinta yasa ta fad'a saman kujerun dake wajen, kuma bata fad'a da kyau ba kawai sai kujerar ta wuntsila da ita ta fad'i qasa, qara ta saki mai k'arfin gaske hakan yasa Baba dake can tsaye hankalinshi ya sake tashi, Mama kuma ta karasa danno kai ciki, samu tayi Khairat na kokarin tashi tsaye hakan yasa ta kamata ta tashi tana kallon Umar Faruk, "meye haka Umar Faruk, kana lafiya kuwa?" Kallon matar Khairat tayi tace "kece mahaifiyarshi?" Kai kawai Mama ta d'aga mata, kallon bayan hannunta tayi da har gurin ya karce jini ya fara fitowa saboda hannun ya had'u da bango, maida hawayenta tayi ta fizge hannunta daga Mama kawai ta koma d'aki, Mama kuma harara ta bishi da ita tace "ai saika fito mahaifinka na nemanka." Juyawa tayi zata fita ya kamo hannunta ya rik'e ya marairaice yace "wallahi Mama ban mata komai ba, dan Allah ki fad'awa malam." Wucewa tayi ta barshi kawai dole ya biyo bayanta, da hannu Baba kawai ya masa alama ya boyoshi d'akinshi, cikin sanyin jiki ya bishi d'akin suka zauna, cikin hikima Baba ya dinga mashi nasiha da gargadi har a qarshe ya dora da "ba haka ake ba Umar Faruk, a matsayinka na namiji, dole akwai bukatar kafi matanka hak'uri, saboda su matane kuma masu rauni , mace zata iya yin abu, kai a ganinka waouta tayi amma ita sai tace kuskure ne, dan haka dole ka dinga hak'uri wannan zuciyar taka ka dinga tausarta, musamman kai daka fara da mata biyu, duk ranar da Allah ya had'aku zama gida d'aya, dole zaka gane ba kada wayo dan dole sai sun gwara maka kai, nasan ka sani dan kai shedane akan zaman da nake da iyayenku, dan haka dan Allah bana son wannan yawan hushi da zafin zuciya, ka rage kaji ko?" "To Baba, insha Allah zan gyara." "To Allah yasa, yanzu kaje ka bata hak'uri dan Allah, sannan ka mata godiya akan d'awainiyar da tayi, dan mahaifiyarka ta fad'a min, tashi kaje Allah ya maka albarka." "Ameen Baba, na gode ." A haka ya tashi ya tunkari b'angaren nasu yana tunanin ya bata hak'uri kamar yanda Baba yace, ko kuma dai ya shareta kawai. _Ya kuka ce? kuna ganin zai bada hak'uri, ko kuma zaiyi taurin kai?_😎😏 *Ina barar addu'arku yan uwa, Allah yaba mahaifiyata lafiya, tana jin jiki, yer uwata ma na fama da tasku na rayuwar aure, gidan miji da tsangwamar kishiya , plss ku tayamu da addu'a.* _I love you sis Alawiyya._😘❤ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *ALLAH KA KYAUTATA MAKOMARMU*👏😭 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 2⃣2⃣ Da sallama ya shiga ya sameta zaune a tsakiyar gado tana share hawaye, har ga Allah har zuciyarshi yaji ba dad'i kuma yaji bai kyauta ba, bata amsa sallamar ba harya zauna kan kujera yana kallonta, hannunta na dama da yake fitar da jini ya gani, shi kanshi baisan lokacin daya zaburo ba yayo kanta yana fad'in "subhanallah, kinga jini kike fitarwa." Zai kama hannun tayi saurin janye hannunta ta d'aga masa hannu tana fad'in " karka kuskura ka tab'ani, mugu kawai azzalumi, wallahi Allah saika sakeni na koma gidanmu, ba zan iya zaman wannan takaicin ba." Wani tafarfasa yaji zuciyarshi nayi tare da bugawa da k'arfi, wajen kayanshi ya nufa ya bud'e ya d'auko wani magani pommade ya bud'e ya lak'ata a hannunshi ya matso zai shafa mata, tsaye ta mik'e akan gadon tana fad'in "nace karka tab'ani ko, ko ana dole ne? ban son taimakon naka." Danya nuna mata ba damuwa yayi da ita ba kawai ya cilla mata maganin a jiki yace "idan kinga dama ki shafa da kanki, yarinya sai taurin kan tsiya." "Nice yarinyar? Umar Faruk ni kake fad'ama yarinya? lallai *zaka gane kurenka* wallahi." Zaune tayi akan gado shi kuma ya matso kusanta yace "yaushe aka haifeki to?" Sama da qasa ta wurga masa harara tare da jan tsaki, bata daidaita bakinta ba ya kama labb'an nata ya matse sosai wanda yayi silar sake fito da wasu hawayen daga idonta saboda masifar zafi, duk da idonta daya ga sunyi ja saida ya qara murd'e bakin yace "zaki sake min tsaki?" Rintse idonta tayi sosai hawaye na zuba, sake murd'ewa yayi yana fad'in "za kiyi magana ko saina cire bakin? fad'a min naji zaki sake hararata ko tsaki?" Kasa magana tayi saboda ya rik'e bakin sosai, cikin fashewa da kuka ta girgiza masa kai a hankali cike da takaici, shima harara ya dalla mata ya saki bakin yana fad'in "marar kunyar banza kawai, wallahi ki yarda na sake gani kiga yanda zamu kwashe dake." Zaune yayi akan kujera ya fara zuba abincin da Ruk'ayya ta kawo ta aje, ita kam hannu tasa ta dafe bakinta gam tana kallonshi, had'a ido da sukayi yasa ta sake banka masa wata hararar, danya tsorata yasa ya taso da azama yana fad'in "baki daddara ba kenan? bari kiga yanda zanyi dake." Da gudu ta wuntsila daga kan gadon tayi d'aya b'angaren tana nunashi da hannu tace "wallahi ka matso kusa dani zan illataka." Murmushi kawai yayi ya koma ya zauna ya gama zuba abinci ya kalleta har yanzu tana tsaye yace "kizo kici abinci." "Ni ba komai nake ci ba, ina da tsari na." Tab'e baki yayi ya fara cin abincin, amma bai kai ko ina ba sai wata zuciyar tace masa "da safe ma bata ci komai ba, a hakane Umar Faruk zaka tafiyar da iyalinka? kai kaci ita kuma baka damu da taci ko karta ci ba." Ajiye cokalin yayi ya kalleta yace "ki fad'a min me zaki ci?" Sai lokacin ta zauna bakin gadon tana fad'in "karka damu dani, ka d'auka zamana a gidan nan kamar naje k'auyen kakanni na ziyara ne, dan haka zan kula da kaina." " *Khairat*." Saida taji gabanta ya buga tare da sanyin jiki saboda yanda ya kira sunanta, bata kalleshi sai dai tana sauraro taji me zaice, ganin bata kallonshi yasa kawai ya qyaleta shima, saida ya gama cin abincinshi sannan ya tashi ya fita ko kallonta baiyi ba, ita kuma tana ganin ya fita ta sake kama bakinta saboda har yanzu zafi yake mata sannan ta bishi da harara tace "mugu kawai." sake haye gadon tayi ta kwanta, taso tayi bacci amma ina zafi da matsatsi sun hanata, dole tashi tayi ta sake fitowa farfajiyar gidan, lokacin wasu na d'aki wasu na tsakar gidan, zaune tayi dan har yanzu kujerar na nan inda take. Usman ne ya doso cikin gidan, da matuk'ar mamaki yake kallonta ganin bak'uwar hallita a gidansu, ko kad'an baya tunanin matar Umar Faruk ta kasance haka, cike da fara'a yace "sannu ko." Da hannu ta masa alamar yazo, ba musu kam kamar sakarai ya nufi wajenta, tsaye yayi gabanta yayin da mutanen dake wajen kallo ya koma kansu, rik'e hab'a tayi ta tangale hannu da kujerar tana kallonshi tace "kana da abin hawa?" "Eh, ina da moto." "Da kyau, aikenka zanyi restaurant ka siyo min abinci." "Ke kuma awa?" ya fad'a yana mata tuhumammen kallo. Mik'ewa tayi tsaye tace "ka bari idan wanda nake zaune dominshi yazo ya fad'a maka koni wacece, amma yanzu ka fara zuwa aiken nawa." D'akin data nufa ya tabbatar masa matar Umar Faruk ce, kuma wannan itace Khairat, kai kawai ya girgiza ya juya ya kalli mahaifiyarshi da yasan sarkin surutu ce amma tayi shiru, tunkararta yayi ya tsugunna gabanta yana fad'in "Mama, ita kuma haka take?" "Kai, tashi kaje abinda ta saka bana son surutu, kuma kayi sauri ka dawo." cewar Mama Sa'a tana yi tana kallon k'ofar da Khairat zata fito. Fitowa tayi amma ganinshi gaban wacce take tunanin mahaifiyarshi ce yasa tayi zaune saman kujerar tana jiranshi, da k'arfi Mama Sa'a ta turoshi ya dawo gaban Khairat ya tsaya, jikka goma guda uku ta bashi ta fad'a masa abinda take so, wucewa yayi yana tsananin mamaki akan abincin da zata ci zaka kashe duk wannan kud'in, lallai yaran nan iyayensu sun kwashe mana kud'i suna facaka yanda suke so😎 inji Usman fa😂. Ta jima tana jiranshi amma bai dawo ba, har saida ranta ya gama b'acewa taji abinda take so d'in ya fita a ranta, ta tashi kenan zata shiga d'aki Usman ya danno kai cikin gidan, wani wawan tsaki taja tare da nunashi tace "saika zauna kaci ai, ni bana so." Shigewa tayi d'akin shi kuma ya tsaya da leda a hannu yana kallon k'ofar, da gudu gudu Mama Sa'a ta taso ta karb'i ledar zata shiga d'akin Usman yace "canjin fa." Dawowa tayi ta karb'a ta wuce d'akin Khairat mahaifiyar Umar Faruk na kallonta tana jin tsoron abinda zai biyo baya, da sallama ta shiga cike da ladabi🤔 sau hud'u tayi sallama ana biyar ne Khairat tace "ki shigo." Da murmushi ta shigo tana k'arewa d'akin kallo tana ji kamar ace d'akin tane ko kuma na 'ya'yanta mata masu aure, aje wayarta tayi tana kallonta cike da tsana da wulak'anci amma ita bata damu ba, ledar ta mik'o mata tana fad'in "gashi 'yata , kiyi hak'uri kici kinji, kinsan yaran yanzu sai hak'uri, inka aikesu sai sun b'ata lokaci kafin su dawo, amma na miki alk'awarin ba zai sake ba daga yau." Gatse gatse Khairat tace "baki ji me nace mishi bane? nace yaci idan kuma ba zai ci ba, ke kici ko kuma ku zubar a shara, amma ni na gama da babin wannan kuma, zaki iya tafiya." Ba tare data damu ba ta sake murmushi ta mik'o mata kud'in tace "to ga canjinki." "Suma ku rik'e bana so." ta fad'a tana maida abin sauraronta a kunne. Da dariya cike da farin ciki ta juya ta fita, amma abin mamaki saita d'auki kwano ta juyo abincin ta zauna Usman da sauran yaran dake nan suna kallo da mahaifiyar Umar Faruk ta fara ci tana fad'in "harkar arzik'i aida mutanen arzik'i ake yinta." Usman da haushi ya kamashi ficewa yayi daga gidan, ita kam ko a jikinta cin abinta tayi tasha ruwa saura ta bawa yara, amma kasancewar sun samu tarbiya sai basu karb'a ba suka ce sun k'oshi, masifa ta fara tana fad'in "yara an koya muku bak'in hali tun kuna k'anananku, to ku aje kar Allah yasa ku ci d'in ." Kud'inta kuma bata bari ma kowa ya gani ba, ko abokiyar cin mushen nata dan dama tana d'aki tana bacci. ****************** Mamie da Papa sosai suke cikin damuwar rashin 'yar gudaliyarsu, haka duk suke zama shiru kowa da abinda yake tunanin a kanta, haka ma ma'aikatan gidan suna damuwa ta b'angaren kyauta da taimako, amma ta b'angaren wulak'anci da yawan aiki kuma suna farin ciki da hakan, amma dai kam tabbas suna kewarta saboda ita kad'aice 'ya a wajensu. ******************* Ana gama sallah isha'i Umar Faruk ya shigo gidan danya shirya saboda yace ma Zuby yana nan zuwa, da sallama ya shigo tare da leda a hannunshi, bata amsa ba kuma bata kalleshi ba sai ayabarta data d'auko a fridge take ci tana korawa da fresh milk, aje ledar yayi saman tebur ya d'auki maclean da brush ya shiga wanka, ya d'an d'auki lokaci kafin ya fito sanye da dogon wando fari da kuma towel ya rufe jikinshi dashi, ya jima tsaye yana shafawa yana fesawa kafin ya fara k'ok'arin saka kaya, ganin yana zame wandon daga jikinshi yasa Khairat saukowa daga kan gadon da duk ta ya mutseshi ta fito a d'an kewayen nasu ta zauna, saida ta daidaici ya gama shiryawa sannan ta shigo, gaban madubi ta ganshi yana daidaita hularshi, da kuma waya a kunnenshi ya danneta da kafad'a. Muryarshi taji qasa qasa yana fad'in "to ki shirya min kanki, dan gani nan zuwa yanzu, kinga tunda aka d'aura mana aure bamu had'u ba." Shiru ya d'anyi sannan yace "ok to, sai nazo." Juyowa yayi yaga Khairat tsaye tana kallonshi, wuceta kawai yayi yana sa wayarshi aljihu sannan yasa takalmi ya d'auki leda d'aya a cikin wanda ya aje ya kalleta yace "wannan taki ce." Juyawa da yayi zai fita yasa Khairat tayi saurin cewa "wannan fa ta wacece?" "Zubeida, amaryata." Kai tsaye kuma ya fita daga gidan ba tare daya sake kulata ba, tab'a ledar tayi taji kaza ce😋(ina sonki kaza), a hankali ta fara d'aga qafafunta harta koma kan gado, sai dai ta rasa meke damunta da taji zuciyarta na mata k'unci duk taji ba dad'i, haka ta rasa me za tayi gaba d'aya kalmar Zubeida amaryata ta tsaya mata a rai, daga ta dafe baki saita dafe goshi ko kuma k'ugu, a hankali ta lumshe idonta amma sai tayi saurin bud'ewa saboda jin hawaye sun zubo mata, hannu tasa ta share ta tashi ta shiga 'yar k'aramar douche d'in ta cire kayan jikinta ta jefosu kamar yanda ta saba ta fara wanka, saida ta gama ta fito kuma ashe babu towel, kamar yanda tayi da rana haka ma yanzu tayi, da gudu ta fito ta shigo d'akin sannan tayi shirin bacci, rigace mai 'yan hannuwa sai wandon dogo har qasa amma bai kamata ba sannan ta kwanta, bacci ne ya gagareta saboda zafi fitowa tayi farfajiyar gidan, kowa yayi shinfid'arsa ya d'aura gidan sauro ya kwanta, kewayenta ta koma ta zauna akan kujera tana sauraron waqoqi daga nan kuma bacci ya d'auketa zuciyarta na tsananta bugawa, gashi tunanin Umar da Zuby ya kasa barin qawqwalwarta. **************** Tunda yace zaizo tanti Ma'u tayi farin ciki Zuby kuma ta shiga wanka, tun kafin ta fito kuma Umar yazo, koda ta fito mahaifiyar tata harta had'a mata 'yan tame tame da tsarabe tsarabe, saida tayi kwalliya sosai ta shirya cikin riga da siket na shadda sannan Mama ta zaunar da ita bakin gado ita kuma tana tsaye ta mik'a mata roba mai cike da nono da magunguna masu k'arfin gaske ta shanye, wani farin magani ta bata tace "tashi ki matsashi a gabanki." Tashi tayi kamar yanda tace haka tayi sannan ta aje mata kaskon wuta ta zuba wani turaren tace ta sake tsugunnawa, gyara jikinta tayi sannan Mama tace "kina jina ko? kiyi duk abinda kika san zaija hankalinki ya kwanta dake, dan wannan abinda kika gani bana wasa bane, nasan dai duk gaggawarshi bai riga ya kusanci waccen karuwar ba, dan haka kar kiyi wasa da wannan damar." Ganin Zuby tayi qasa da kanta alamar kunya yasa tace "to kuma miye na kunya? nifa uwarki ce dan haka karki damu." A sanyaye ta kalleta tace "wallahi Mama tsoro nake ji, gabana ma fad'uwa yake." "Saboda me? mijinki ne fa, kasheki zaiyi? keni nama ci uwaki idan kika b'ata min rai, to in banda abinki kowace mace ba saida tazo wannan gurin ba kafin nan ta wuce, muma duk bata haka muka sameku ba." Shirun da tayi yasa tace "maza wuce kije yana jiranki." Lemon da Mama tasa aka siyo mata ta d'auka ta fito ta shiga d'akin da aka gyara mata ta zauna kafin lokacin tariyarta, zaune yake akan k'atuwar katifar dake tsakiyar d'akin, k'ura mata ido yayi harta zauna kusa daf dashi duk da irin ruwan da take jin gabanta na fitarwa, sosai ta masa kyau kasancewarta siririya kuma kayan sunbi jikinta, ga kwalliyar da tayi sosai hakan yasa ta masa kyau. Wani kashe ido ne da tayi yasa jin tsikar jikinshi ta tashi had'e da fad'uwar gaba, itace tayi k'arfin halin cewa "sannu da zuwa angona, na barka kana ta jirana ko? kayi hak'uri to na tsaya maka shirine." Cikin wani irin yanayi da shi kad'ai yasan me yake ji yace "ba komai, ai girmanki ne." Lemon ta d'auka ta bud'e sannan ta kai masa a baki tana sake rikirkitashi da wani sabon kallon, kurb'a d'aya yayi ya kau da kansa gefe tare da d'auko ledar daya shigo da ita mai d'auke da kaza da kuma lemuka masu sanyi, bata yayi ta karb'a tana fad'in "meye kuma?" "Ki diba ki gani mana, kazar amarcinki ce." Ya fad'a yana dariya, ita kam gabanta ne ya fad'i dan haka tace "na shiga uku, nifa bana son cin kazar nan." "Me yasa?" ya fad'a yana kallonta. Cikin tsoro tace "wallahi ina ji k'awayena suka fad'a wai duk wanda yaci kazar nan, to shima dole sai an...." kuma sai tayi shiru. "Ina jinki, kina tunanin na saka wani abu ne a ciki?" "A'a, kawai dai ance idan kaci kaima zaka biya." Cike da zolaya yace "ke kuma biyanne kike jin bak'in ciki ko?" Tuna abinda Mama ta fad'a mata yasa ta fad'a jikinshi tare dasa hannunta ta shafo qirjinshi amma ba tace komai ba, tunda ta fara shafarshi ta kwance masa lissafi ido ya rufe yana sauraronta, bata daina ba saima botir d'inshi data b'alle ta zura hannu tana shafoshi, cikin wata rikitaciyar murya ya kira sunanta da, "Z..u....beid...a." D'ago kan da tayi ta kalleshi tana marmad'a ido yasa ya sake fita hayyacinshi, a hankali ya had'a bakinshi da nata ya fara tsotsa, tun yana aika sak'on a hankali harya fara da sauri sauri, sai kuwa ya kwantar da ita akan katifar ya hau samanta ya cire hularsa da riga da.....🙊BK za tace waya aikeni. Umar Faruk dai ya manta da ina yake sai faman aiki yake, rana ta farko daya fara sanin 'ya mace kenan, shaye shayen da Zuby tayi yasa Umar Faruk bai sarara mata ba ko kad'an, hakan ya janyo ya mata babbar k'ofa😂shiga gari, wacce ba lallai Khairat nada ita ba, ya jima sosai kafin ya d'agawa Zuby k'afa , kwance yayi yana kallon sama yana sauke numfashi duk da gumin daya had'a, Zuby na ganin haka ta yunk'ura ta tashi zaune ta d'auki rigarta ta yab'a tare da saka siket d'inta ta mik'e zata fita, da sauri ya tashi ya d'auki wandonshi qarami ya saka ya rik'ota yana fad'in "ina zaki je haka Zubeida, miye haka?" Cikin layi da shan wahala tace "dan Allah ka k'yaleni na tafi, wallahi ciwo nake ji, zanje wajen Mama ta taimaka min." Tare gabanta yayi yace "haba Zuby, ya kike nema ki tona min asiri? ki bari dan Allah ki gyara jikinki, karki fita haka." Zip d'in rigarta ya saka mata tare da bata d'an kwalinta ta d'aura sannan ya saka nashi kayan shima, sallama ya mata ya bar gidan dan ba zai iya had'a ido da Mama ba, haka ya bar gidan gabanshi fad'uwa kawai yake kamar bai samu nutsuwa ba, a haka harya isa gida. Zuby na shiga d'aki ta fad'a saman gado, da sauri Mama ta d'auko babban roba da ruwan d'umin data d'ora musu tunda ta kara kunne a k'ofar d'akin taji nishi da sambatun Umar Faruk da kuma kukan Zuby ta dafasu , da taimakonta ta samu ta gasa jikinta sannan tayi wanka kafin baccin wahala ya d'auketa.😂 ****************** 00:30 ya shigo da mashin d'inshi a cikin gidan bayan ya kasheshi yanda Baba ba zaiji ba, yana daidaita zaman mashi d'in yana sad'af sad'af zai shiga ciki muryar Baba ta daki kunnuwanshi da kiran sunan "Umar Faruk." Rintse ido yayi sosai yana jin bugu zuciyarshi na qaruwa, a hankali ya juyo ya kalli Baba dake qofar d'akinshi, kallon da yake masa yasashi zubewa k'asa ya durk'usa yana sauraran Baba. "Umar Faruk, ya ina yabanka sallah zaka kasa alwala, kai da kanka Umar Faruk, yanzu ka kyauta kenan? to waima daga ina kake?" Yana shafa kai cikin rashin gaskiya yace "kayi hak'uri Baba, daga gidansu tanti Ma'u nake." "Au, yanzu acan kayi dare kenan haka? Umar Faruk yanzu yarinyar mutane daka bari fa? ya kayi da ita?" Shiru yayi ba magana dan haka Baba yace "to kaje ka bata hak'uri, dan kamar ka d'auki kwananta ne ka kaiwa wata, ko ban tambayeka ba nasan akwai abinda ya shiga tsakaninka da Zubeida, dan yanayinka ya nuna hakan, ka tashi ka ka b'ace min da gani, kuma wallahi ka kiyaye shiga hakk'in matanka, dan mugun kamu Allah zai maka." yana fad'a ya shiga d'akinshi ya barshi. Jiki ba k'wari haka ya tashi yana k'arewa kanshi kallo dan baya so ya shiga da wannan yanayin da Baba yace ya gani a tare dashi, kallon ahlin nashi yayi da sukayi nisa a bacci, k'ofar kewayen nasu a bud'e take haka ma wuta ba'a kashe ba, yana dosa kai ciki ya tsaya cak saboda ganin Khairat zaune akan kujera harta langab'e kamar zata fad'i, ga abin sauraronta a kunne wayar kuma ta fad'a a d'aya saman kujerar, abinda ya d'aga mashi hankali shine yawan motsin da take saboda sauron dake ta cizonta sai sosar jiki take, a hankali ya sunkuya daf da ita ya saka hannayenshi ya ..... _Kuna ganin d'aukar zaiyi, ko kuma me zai mata.?_ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 2⃣3⃣ Hannu yasa ya zare abin sauraron daga kunnenta ya d'auki wayar ya kashe, a hankali ya daddab'a hannunta kafin yayi na biyu kuma ta bud'a ido, zunbur ta tashi tsaye tana zare ido sai kuma ta fara sosar jiki kamar mai k'yaya, jin gaba d'aya jikinta ya d'auki rad'ad'i na cizon sauro yasa ta lab'e baki kamar jaririya ta fashe da kuka tana ci gaba da sosar duk inda take jin kyaikayi, Umar Faruk kuma mutuwa yayi da kallonta cike da birgewa yanda tayi kalar yara, wani murmushi ya saki ya nufi kayanta data jefo lokacin da za tayi wanka ya d'auke ya shiga dasu d'aki, jim kad'an ya fito ya fad'a douche danya tsarkake kanshi, kallon juna sukayi ita kuma ta wurga masa harara da tsaki dan sai lokacin ta tuna rabuwarsu dashi, douche ya shiga ita kuma ta shige d'akin amma ta kasa komawa ta kwanta. Fitowa yayi cikin doguwar riga ya sameta zaune tana kukan shagwab'arta, zaune yayi akan kujerar yana kallonta, ganin har yanzu sosar jiki take yasa ya taso a hankali ya zauna bakin gadon tare da sauke ajiyar zuciya, waigawa yayi ya kalleta cikin taushin murya yace "Khairat." Cikin kukan shagwab'a ta fara magana "wallahi Allah ni dai ka mayar dani gidanmu, ba zan iya zama anan ba sauro ma kasheni zaiyi, dan Allah ka taimaka ka bani izini na tafi gidanmu." Ta sake fashewa da wani kukan, "Khairat." ya sake kiran sunanta. Kallonshi tayi dan haka yace "tashi kiyi alwala kizo." "Ni ina maganar ka kaini gida, kai kuma kana maganar naje nayi alwala." ta fad'a a matuk'ar harzuk'e. "Ki tashi kiyi abinda nace." ya fad'a yana komawa kujerar. Saboda ibada ne yasa ta tashi ta fita ta d'auro alwala ta dawo ta sameshi, tunda ta fita ya duba ledar daya aje tana nan yanda take, yana ganinta ya tashi ya shinfid'a sallaya yace "kisa hijab d'inki ki tsaya bayana." "Meye kuma haka?" ta tambaya tana kallonshi. Kallon daya mata yasa ta d'auki hijab d'in ta saka ta tsaya daga gefenshi a bayanshi, kabbara sallah sukayi, raka'a biyu sukayi tare da jimawa zaune Umar Faruk yana jero musu addu'a, suna sallamewa zaune yayi sosai tare da juyowa ya kalleta, cikin nutsuwa da hikima ya fara magana, "Khairat, da farko na d'auka labarina dake gajeran labari ne, amma daga ranar da zuciyata ta yanke min hukuncin na amince da aurenki, saina yarda labarinmu dogone, hak'ik'a aurena dake Allah ya qaddara faruwarsa bamu ba, idan har za ayi maganar gaskiya, to kin wuce tsarin aurena, matsayinki da nawa ba d'aya bane, amma duk da haka sai kuma Allah ya hukunta aure tsakanina dake, hakan na nufin akwai abinda Allah ya tsara mana a rayuwarmu, dan haka zaifi mu jira hukuncin ubangiji, amma maganar saki ki daina ba kyau, sannan ina so kiyi hak'uri dan nasan na b'ata miki sosai saboda aurenki da nayi, amma dan Allah Khairat ki bani dama na cika alk'awarin dana d'aukarwa iyayenki ta hanyar samar maki ingantacciyar ruyuwar da suke miki fata da kuma burin samu." "Khairat akwai tambayoyin da nake son yi miki a game da addininki , kuma ina fatan zaki amsa minsu kamar yanda suke, ina so na d'ora miki daga inda kika tsaya, dan haka ina son fara sanin yanda kike tsarkake kanki, domin kuwa saida tsarki ne zaka fuskanci ubangijinki, idan har kina wankan tsarki kamar yanda aka koyar to alhamdulillah, dan haka ina jinki ki fad'a min." Hannu ta zura a cikin hijab d'inta ta d'an sosa damtsenta da duk k'urajen sauro suka fito mata, shiru tayi kamar bada ita yake ba, hakan yasa yace "Khairat dake nake fa." "Toni me zance maka? kana ganin sauro duk ya b'ata min jikina, ya kake so nayi." Tsaye ta mik'e ta cire hijab d'in tana shirin hayewa gado taji ya rik'e qafarta, juyowa tayi tace "dallah sakeni malam." "Ki dawo magana muke." ya fad'a ya matuk'ar tsaurare. Tana turo baki gaba ta koma ta zauna shi kuma yana bin hannayenta da kallo, saiya ji tausayinta saboda duk fatarta tayi ja sai shatin cizon sauro a jikinta. D'orawa yayi da "ina jinki." Ajiyar zuciya ta sauke tana kallonshi tace "bansan me zance maka ba, zan fad'a maka rabona da islamiyya tun ina 'yar shekara bakwai, ko kuma zan fad'a maka ni bansan komai ba, abinda na koya daga wankan tsarki a wa'azi naji a gurin malamai da dama, duk da sunce wankan akwai wanda zaka iya zuba ruwa tun daga samanka har qafafunka tare da cud'a jikinka ma ya hallata , to amma ni hankalina yafi kwanciya ga wanda yake tare da alwala, dan haka ni shi nake yi." "Ina so nasan yanda kike yinshi." Kallonshi tayi tace "wai dan Allah ba zaka bari harda safe ba, yanzu bacci nake ji ga wannan masifar sauron." "Ina jinki." yayi maganar ba wasa. Hararanshi tayi taja tsaki, da sauri ya kalleta ya kai hannu zai kamo bakinta ta tuno da karonsu da rana, da sauri ta jaye daga wajen tayi baya tana fad'in "to naji zan fad'a maka." "Nakan fara da niyyar yin wanka sannan na tanadi ruwana masu tsarki da tsarkakewa, sannan na wanke gabana da kyau ta yanda duk wata qazanta zata fita har izuwa gwiwoyina zuwa cibiya, sannan nasa sabulu na wanke hannayena da kyau, sannan na fara d'aura alwala sau d'aya d'aya har saina zo shafar kai, ana so ya samu ruwa sosai sannan na k'walk'wale kunnuwana, daga nan kuma zan fara wanke barin damana tun daga sama har qasa, sannan na koma barin hagu shima tun daga sama har qasa, sannan na wanke qafar dama sai kuma ta hagu, wankana ya kammala kuma idan lokacin sallah yayi ma zan iya yin sallah dashi in dai har banyi wanka da sabulu ba, to yanzu zan iya kwantawa *malam Umar Faruk mai tambayar wankan tsarki*?" Yaji dad'i sosai da har wankanta ya zamana yanda sunna ta koyar ne, dan haka ya dinga mata tambayoyi tun daga lokacin daka gama alwala har lokacin da zaka shiga sallah, kuma cikin ikon ubangiji ta amsa saboda tambayoyi ne masu sauk'i, abu d'aya shine ko hizib d'aya ba zata iya karanta maka ba daga farko zuwa qarshe, dan haka Umar Faruk yace "karki damu, in dai har zaki bani goyon baya, to kema zaki samu hasken qwaqwalwa dana zuciya, ina so zan fara miki karatu daga gobe daga inda nake ganin ya kamata a d'oraki, kuma ina so kisa abin a ranki ta yanda ko bana nan zaki iya tambayar wani ko wata, a cikin gidan nan Khairat ko *Fateema, da Alqasim* kika tambaya zasu iya d'oraki daga hizib d'aya zuwa talatin, dan haka kije ki kwanta gobe insha Allah zan fara miki da littafin *AL'AKHDARI, HUSNUL MUSLIM, KHAMSUNA HADITH, DA KUMA LITTAFI MAI TSAKI DAGA HIZIB D'AYA ZUWA GOMA*, idan har kika saka abin a ranki to Allah zai taimakeki cikin sauk'i ki dinga fahimtar abinda kike koya, saida safe." Ya fad'a yana tashi tsaye tare da kabbara wata sallah, duk da taga sallah yake amma bai hanata cewa ba "na d'auka ba zan tab'a samun hasken rayuwa ba, ina son sanin addinina sosai, amma duk lokacin da nayi yunkurin zuwa inda za'a koyar dani, sai k'awayena da zuciyata su nuna min na wuce wannan wurin ko kad'an ba ajina bane, kuma ma ai ina da ilimi na zamani ga wayewa ga kuma kudi, sai dai na manta dashi ilimi ba'a tsufa da nemanshi, kuma wannan ilimi saida shine zan samu tsira ranar gobe qiyama, insha Allah zan koya kuma lokacin ya kusa zuwa da zanje gaban Mamie na karanta mata sura mai tsayi wacce za tasa tayi mamaki harma ta saka min albarka." Tana fad'a ita kuma tayi kwance a gado sai dai ina bacci bai samu ba, kiran sallah ne ya daki kunnuwansu dan haka Khairat taji wani sabon shauk'i a game da son ibada ya shigeta, tun kafin ya sallame ta tashi ta fita tayi alwala, zata shigo d'aki shi kuma zai fita masallaci, tsaye tayi ta fita sannan ta shigo saida ta fara da *salatul fijir* sannan tayi sallah, tun bata tashi ba bacci ya fara fizgarta daga nan, jingina tayi da gado kawai ta dunk'ule cikin hijab ta fara gyangyad'i, a haka Umar Faruk ya shigo ya sameta, zaune yayi yana tasbihi yana kallon fuskarta, murmushi kawai ke bayyana a fuskar tashi saboda tuna tambayoyin daya mata kuma ta amsa, ga kuma abinda yaji tace a game da son karatun, a cikin ranshi yace "taya zan bata hak'uri kenan?" Bai samu amsa ba kuma bai daina kallonta ba har gari haske yana kallon yanda take bacci kuma ko motsawa ba tayi ba, a sama sama yake iya jin hayaniya a tsakar gidan, dan haka ya d'auka ko masifa ce dasu Mama Sa'a suka saba da ita, hayaniyar ce ke sake yin sama ga kuma kuka da yake ji wanda yake tunanin na *Yusuf* ne d'an Abbakar, wannan kukan ne yasa Khairat bud'a ido ta sauke akan Umar faruk dake kallonta, zaune tayi da kyau tana mike qafafu tana murza ido shi kuma tuni ya d'auke kai daga kallonta, jin kukan da hayaniyar mutane yasa ta kalli Umar Faruk tace "waiku gidanku ba kwa baccin safe ne? suna damuna fa." Kafin yayi magana ta mike tsaye ta cire hijab zata kwanta kenan taji ana kiran sunan Umar Faruk, da sauri ya fita daga d'akin tana binshi da harara da jin haushin mutanen gidan da basa barin bacci, da azama ya sake shigowa taga yana lalabar aljihun rigarshi daya cire jiya, yana d'aukar makulli yace "zanje na dawo." "Ina?" ta fad'a dan taga tashin hankali a idonshi. Yana barin d'akin yake fad'in "zamu kai Yusuf asibiti." Jin haka yasa Khairat biyo bayanshi da sauri itama ko kallabi bata d'ora a kai ba bare takalma, Yusuf na rik'e a hannun Abbakar sai kuka yake Umar Faruk kuma yana gaba danya fitar da moto, duk kowa yayi cirko cirko Ruk'ayya ce Khairat ta dafa tace "meya sameshi." Saida ta kalli kayan jikinta sannan tace "wallahi wata 'yar k'aramar lula ce mai kamar ball ya samu yake wasa da ita, shine ya saka a hanci ta shige masa, kuma gata ana gani amma tak'i fitowa." Jin haka yasa Khairat rugawa a guje ta tari gaban Abbakar ta finciko Yusuf daga gareshi ta zaune dashi a qasa ba tare data damu ba, ganin haka sai kowa ya matso inda take duka suka rufesu suna kallon ikon Allah, Umar Faruk ma zai fitar da moto yaga kuma an taru dan haka ya dawo shima, amma abin mamaki da bai tab'a tunanin ko a mafarki ya faru bane ya faru, Khairat ya gani duk da hawaye da miyo ga majina data b'ata fuskar Yusuf bai hanata saka bakinta a hancinshi ba a inda babu lular tana busawa, sosai take busawa kafin ta d'ago kai ta kalli Abbakar tace "ace duk yawankun nan kun kasa taimaka mishi, sai wani maganar asibiti kuke." Sake maida bakinta tayi da k'arfi tana busawa, sai kuwa lular nan tayi b'ul ta fito daga hancin Yusuf, wata irin sa'ida da salama da yaron yaji yasashi saurin rumgume Khairat ya manna kanta a qirjinta dake k'yam dashi yana hararan Umar Faruk daga nan😉, d'an shafa kanshi tayi sannan ta mik'awa Abbakar shi yana amsa ya kalleta sosai yace "mun gode sosai k'anwata." Mik'ewa tayi amma sai Saratu ta rik'e hannayenta duka biyu ta had'e tana kuka tace "na gode sosai yer uwa, tashin hankalin dana shiga yasa na manta ta yanda zan fara taimaka masa, na gode sosai." "Ba komai." ta fad'a kamar dai wacce aka saka dole, kakkab'e wandonta tayi ta juya ta nufi kewayenta kowa kuma na binta da kallo saboda abinda tayi babu wanda yayi tsammanin yinshi, saida kowa ya kama harkar gabansa Umar Faruk na tsaye, daga baya yaji an dafa kafad'arshi, juyawa yayi sai yaga Mama ce, murmushi yayi zai wuce yaji Mama tace "zuciyarta mai kyau ce, tana da abinda ba kowa yake dashi ba, wato *tausayi da taimako*, duk wanda yake da wannan halayen to mai imani ne shi, d'an duhun dake cikin rayuwarta nake so naga ga yaye matashi ka mayeshi da da haske , kaje Allah ya muku albarka." Wucewa Mama tayi shima kuma ya nufi kewayen yana jin wani irin nishadi da farin ciki na lullub'e zuciyarshi, yana shiga ya ganta ta d'ibi ruwa tanata wanke baki wai ita majina, murmushi kawai yayi ya shiga d'aki, tana shiga itama tayi zaune tare da d'aukar wayarta tana aika kira, ba jimawa aka d'auka a daqile tace "ka kawo min mota ina jiranka." Duk da wanda ta kira yaso ya tambayi gidan nata, amma ta riga data kashe wayar, Umar Faruk kuma tashi yayi ya shiga wanka, koda ya fito ta tashi zata shiga itama tace masa "aiki zanje, idan ka rigani zuwa kace Habiba ta share min bureau (office)." Tana fad'a ta wuce abinta shi kuma yayi shiru yana tunanin kuma ta yanda zaiyi ya dakatar da ita, harta cire kayan jikinta sai kuma taji wani irin sanyi ya lullub'eta, dafa wuyanta tayi sai taji zafi ruf, tsaki tayi dan tasan sauron nanne kawai ya zuba mata zazzabi dan haka ta d'auko kayanta a hannu ta manta da inda take rayuwa yanzu, duk da ta raumgume kayan amma dai kallo d'aya zaka mata kasan babu komai a jikinta, tana dosowa zata shiga Umar Faruk ya bud'e labule zai fita gaida iyayensu, da sauri ta durk'ushe qasa ta rintse ido tare da rufe fuska da kayan, kasa gaba yayi sai baya da yayi ya dawo cikin d'akin ya fad'a saman kujera kamar an turashi, yana hangenta ta labule bata tashi ba yasa ya tashi ya d'auki towel d'inta daya gani rataye ya bud'e ya cilla mata a jiki, sai lokacin ta mik'e ta d'aurashi sannan ta shigo, zaune tayi ta sake d'aukar waya ta danna wani kiran, kasalance tace , "Kina asibiti ne?" Shiru alamar tana saurare kafin tace "wallahi zazzab'i ne ke son rufeni, zanzo yanzu." Aje wayar tayi duk yana kallonta amma baice komai ba, tashi tayi ta bud'a kayanta ta d'auko doguwar rigar atamfa ta saka tabi jikinta sosai kuma ta mata kyau, d'an kwali ta d'aura sannan ta d'auki qaramin mayafin daya dace da kayan ta aza a kafad'a, poshet (post) d'inta ta d'auka ta bud'a wata jakar ta d'ibi kud'i ta zuba a ciki sannan ta d'auki wayarta tasa takalmi ta d'auki turare ta feshe jiki dashi, takowa tayi har gabanshi ta tsaya tace "idan driver Mamie ya kawo min motar ka karb'a ka aje min ni zan hau taxi." Zata fice yace "ki saka hijab d'inki." Juyowa tayi tace "iko? wai iko kake so ka min? to ban tab'a fita dashi ba ba kuma zan fara yau ba." Tsaye ya mik'e yana fad'in "kuma dole kisan cewa da dah da yanzu ba d'aya bane, wallahi ke baki isa ki zubar min da mutunci ba, idan kika fita a haka to mamaki da zulumi ne zasu hana mutanen unguwar nan samun shak'at, ace surukar malam Ahmad a haka, ina ba dani za ayi wannan fitsarar ba." "Wato ma nice fitsararriya ko? to ba zanyi ba naga me za kayi, idan kuma zaka tursasani ne na gani." Sallamar Ruk'ayya ce yauma tasa ya amsa tare da bata izinin shiga, yau ma gaishesu tayi sai dai Umar Faruk kad'ai ya amsa kamar dai jiya, aje kwanukan tayi ta fita abinta Khairat kuma ta juya har zata fita kuma ta tsaya ta sake kallonshi tace "idan iko kake so kaima a matsayinka na namiji, toka bari har figaggiyar matarka ta shigo gidan saika mulketa, amma bani ba *Hajia Khairat*." Gyara tsayuwa tayi tace "duk da bana da ilimin addini, amma ka sani na kare mutuncina, kuma duk da bana da sani akai amma nasan abinda kayi jiya baka kyauta ba, ka raba dare a wajen amaryarka, kuma daga yanda ka shiga wanka a wannan tsohon daren ya tabbatar min da wani abu ya faru, amma karka damu na yafe maka badan komai ba saboda ni ba sonka nake ba, kuma bana qaunarka kamar yanda ba son auranka nake ba." Bakinshi ne ya mutu dan haka dole yayi shiru yana kallo harta fita daga gidan, mutanen dake tsakar gidan kuma kowa kasa motsi yayi yana kallonta harta fita, sai dai Mamar Umar Faruk tayi niyyar fad'a mata gaskiya dan wannan ba abu bane mai yiwuwa, malam ma dake k'ofar gida suna tattaunawa da mak'otanshi yana ganinta ya d'auke kai dan karya nuna ma ya santa, amma dai shima dole yaji a ranshi zai tsawatar mata da kanshi, bata sha wahalar samun taxi ba ta d'auketa kai tsaye sai asibitin kud'i asibitin da suke da familly docteurn su, *Clinique d'an magori* kai tsaye bureaun docteur d'in ta shiga, kasancewar suna ganema juna sosai yasa ta kwantar da ita ta saka mata sérum (drip), tana kwance amma suna hira baka ce Khairat ce ba mai ganin dama kafin tayi magana. ***************** Tana fita shima ya fito ya fara shiga d'akin Mama Maimuna ya gaisheta saboda shine farko, kuma an nuna musu duka iyayensu ne dan haka d'aya ne, yana fitowa kuma ya shiga na Mama Sa'a, abin mamaki shine cewa da tayi "Umar Faruk ya 'yata, da fatan dai ta tashi lafiya?" Kallonta ya d'anyi a fakaice sannan yace "da sauk'i Mama, dan yanzu haka ma ta tafi asibiti, zazzab'ine ya rufeta." "Ayya, Allah sarki yarinyar kirki, Allah ya bata lafiya." "Ameen Mama." "Ai Umar Faruk kayi dacen mata wallahi, Allah dai ya baku zaman lafiya." "Ameen Mama." ya fad'a a d'arare. Yana fita daga nan ma d'akin mahaifiyarshi ya nufa, bayan sun gaisa ne tace "Umar Faruk ina ne matarka ta fita tunda safe haka? kuma kana kallonta ta fita da wannan kayan, kuma naga duka yaushe ne tazo da har zata fara fita." "Kuyi hak'uri Mama, duk ni naja muku, amma insha Allah zan d'auki mataki akan hakan." "To shikenan, amma dai banda duka ko wannan muguntar taka ka kama bakin mutum ka murd'e ko mintsini, ka mata cikin ruwan sanyi harta fahimta." Cikin dariya yace "to Mama." Daga nan kuma yayi d'akin Baba kuma ya sameshi yana karin kummalo, kuma Abbakar da Aliyu ma duk sunje gaisheshi, a tare ya musu nasihar daya saba na suji tsoron Allah su kyautata ibadarsu, sannan su guji d'aukar hakk'in wanda Allah ya had'asu zama dashi kona minti d'aya ne, daga nan kuma ya sallamesu suka tafi Umar faruk yayi tunanin sai Baba ya masa magana amma yaji shiru, yana fitowa yaga motarta a k'ofar gida, fita yayi suka gaisa da driver wanda Mamie ta fad'a masa unguwar shi kuma yayi tambaya, makullin ya amsa driver kuma ya koma dan ya hau taxi, shima d'aki ya dawo ya aje mata makullin sannan ya zuba abinci ya ci, Ruk'ayya ya tura ta gyara d'akin ta kuma d'auko kwanuka da kazar da bata ci ba. _Kuna wulak'anta min kaza fa😒_ Tunda ya nufi wajen aiki yake tunanin yanda mutane zasu kalleshi, kuma kam hakane ya faru dan yana shiga suka dinga zuwa suna masa wai barka, da qyar ya zauna mazauninshi Ishaq ya zuro kai yace "mutumina ina amaryar, ba dai ka hana ta fito ba? Wata harara ya wurga masa yayi banza dashi, dan tunaninshi na gareta yana so yaji ya take a yanzun, gashi kuma baya da lambar wayarta, dubara ce ta fad'o masa daya tuna manager, kai tsaye bureaunshi ya nufa, yana bashi izinin shiga ya shiga ya samu wuri ya zauna, kai fa fara sosawa ya kasa magana. Ganin haka yasa manager cewa "angon Hajiarmu, ya kuma kayi shiru? ina Hajiar tamu take? ko dai har yanzu baku gama cin amarcin bane?" Wani tarr yayi da ido yace "kai manager, amarci fa? da Hajiar taku ? kamar dai ka mantata, nifa kaga ba wannan ne ya kawoni ba, lambarta ma nazo ka bani ina so zan kira." "Me!? lambarta fa? kwananka nawa a matsayin mijinta? amma kace baka da lambar wayarta? anya Umar faruk." Shiru yayi kawai yana jira ya bashi, ba yanda ya iya shima dole ya bashi lambar sannan ya fito yana doka mata kira, tunda taga lambar ta shigo wayarta taji gabanta ya fad'i ba gaira ba dalili, gashi kuma lambar sassauk'a hakan yasa ta birgeta, saida ta tsinke ya sake kira sannan ta d'auka, shiru dukansu sukayi kafin shi yace, "Hello." Lumshe ido tayi saboda yanda muryarshi ta daki kunnuwanta cikin nutsuwa, "hello." tace a matuk'ar sanyaye. Shima dafe qirji yayi saboda wani irin bugawa da yaji yayi, da qyar yace "kina ina?" "Mai gida kenan, ina asibiti har yanzu, sérum aka saka min." Cike da nuna kulawa yace "subhanallah, amma kuma shine baki kira ba?" "Dame zan kira? bana da lambarka ai, kuma kaima nasan yanzu ka samu tawa." "Amma ai na samu, ki fad'a min inda kike yanzu zanzo." "Ina Clinic d'an magori." tana fad'a ta kashe wayar, shi kuma yabi wayar da kallo. Fita yayi ya hau mashin d'inshi ya koma gida sannan ya d'auki motarta ya tafi da ita dan ba zai dawo ba sai tare da ita 😂kasan kuma ba zata hau *Utu utu* ba. _Kuna ganin zata yarda ta taho tare dashi a motarta, ko kuma shi zai dawo a qafane ya kai mata motar kenan?_😂 _Luv u sis Alawiyya_😘 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ ```My Meelat, wannan page taki ce ke kad'ai, i love you.``` 2⃣4⃣ Saida ya kirata ta kwatanta mishi wajen da take, yana kaiwa kofar d'akin docteur d'in ta fito danta basu wuri, gaisawa sukayi kafin ta fice tana yaba mijin na Khairat, koba komai a yanda ta ganshi tasan zaiyi wuya Khairat ta rainashi, kallon juna sukayi lokaci d'aya kuma suka d'auke idonsu, zaune yayi bakin gadon ita kuma ta nad'e qafafunta, kallon ruwan yayi yaga harma sun kusa qarewa, shiru sukayi babu mai magana har wayarshi tayi qara, yana ganin Zuby ce sai yaji wani haushi ya kamashi, tunawa da yayi abinda ya faru, amma kuma sai yaji tausayinta a wani b'angaren ganin yanayin daya barota, muryar Khairat ce ta katse masa shiru da "ka d'auka mana, ko sai tayi hushi, zaifi maka ka lallab'ata dan ita kad'ai gareka." D'auka yayi baice mata komai ba, a daqile yake amsa gaisuwarta, da qyar yace mata "ya kike, da fatan kinji sauk'i?" Zuby dake gaban Mama tana kallonta tace "da sauk'i dai, amma fa har yanzu ina jin ciwo." "Ayya, sannu kinji, zai bari insha Allah, yanzu ki kashe waya zan kiraki ina wani wuri ne." "Ina kenan yah Umar?" Saida ya kalli Khairat ta gefen ido sannan ya rage sautin murya yace "ina asibiti." "Subhanallah, wake asibiti yah Umar?" Wannan karan kallon idon Khairat yayi wacce take latsa wayarta sai dai zuciyarta bugawa take da k'arfi, haushi take ji yana taso mata tana ji kamar ta bugeshi tare da wayar, sannan yace "auntynki ce ba lafiya, amma yanzu zamu koma gida serum d'in ta kusa qarewa." Zaro ido tayi ta kalli Mama sai kuma tace "tana kusanka ne?" "Eh, wani abu ne?" "A'a, ka gaisheta." "Zata ji." "Yah Umar. " ta kira sunanshi. "Na'am." ya amsa yana kallon Khairat. "Sumbata nake so kamin wacce baka min ba jiya ka tafiyarka, kuma na d'auka zaka kirani amma baka kira ba." Umar Faruk kam mamaki ne yasa yace "sumbata kuma?" Da sauri Khairat ta d'ago ta kalleshi, sai kuma ta mayar da kanta k'asa. "Eh, ko ban cancanci sumbar bane duk da jiya ne darenmu na farko?" Qasa yayi da murya yace "kinga zan kiraki anjima." "Wallahi ban yarda ni saika min." ta fad'a cikin shagwab'a harda kukanta. A hankali ya tashi ya fita bakin k'ofar d'akin ya danna mata sumbar sannan ya kashe wayar, sai dai kuma Khairat tajishi hakan ya qara harzuk'ata. Tana aje wayar tace "shikenan Mama, na shiga uku, wallahi harta fara laulayi." _Ke👀👀👀 laulayin lafiya._ "Meya faru, meya ce miki?" cewar Mama kamar zata had'eta. "Waifa suna asibiti bata lafiya, kinsan dai ba haka kawai za tayi rashin lafiya ba, gashi abinda muke gudu ya faru, kuma ni na riga na bashi kaina tun ban tare ba." 😛😛😛😛😛 _FAN'S JIHADI sukace ke kika jiyo_ Ajiyar zuciya Mama ta sauke tace "to kin gani, wallahi ba zan iya wannan kayan takaicin ba, dan haka shiryawa za kiyi kawai ki tare gidansa kema, in yaso duk abinda suke ayi a gabanki, dan zai iya mantawa dake anan d'in, yana can ya samu mai kud'i kenan ya fita harkarki, dan haka ki koma can ki zauna duk abinda suka ci kema kici wanda sukasha kema kisha, kinji ko?" "Amma fa Mama ba...." "Amma me? dan ubanki ana nuna miki annabi kina rintse ido, duk abinda nake yi ba saboda ke bane nake yinshi, dan haka ki fara shiri wallahi kin kusa komawa gidanki." Tashi tayi ta barta ita kuma ta koma ta kwanta dan har yanzu ba dad'in jikinta take ji ba, dan ba qaramar wahala tasha ba abinka ga sabbin shiga. ****************** Ran Khairat a matuk'ar b'ace ba tare data kalleshi ba tace "ka kira min *Sadiya* tazo ta cire min na koma gida." "Ki bari ta qarasa mana." ya fad'a yana kallon ruwan. Bata san me yake damunta ba amma bata kosan had'a ido dashi, a zafafe tasa d'aya hannun ta janye sirinjin daga hannunta hakan kuma yasa jini ya fito tunda bata cire yanda akeyi ba, kallonta kawai yake ita kuma ta d'auki mayafinta ta laga a kafad'a tasa takalmi tayi hanyar fita, da kallo ya bita yana k'ok'arin kiran sunanta. "Khai...k.k..." tuni ta fita dan haka ya biyota da sauri, har zai tari gabanta saiya tuna lokacin data maresa,😁( ba kyau), cak ya tsaya sai kuma ya fara binta a baya har suka fita, Sadiya ce taga fitarsu a ranta tace "Allah ya had'aka sai hak'uri." Tana fita farfajiyar ta tsaya saboda ganin motarta, juyowa tayi ta kalleshi lokacin daya tsaya gabanta, hannu ta tara masa tace " bani makullin motata." D'ago hannu yayi zai mik'a mata sai dai kuma baya so ya bata, da k'arfi ta fizgi makullin tana fad'in "ka bani nan, ko taka ce?" Tana karb'a ta dalla masa harara tace "inma kanayi ne dan naji haushi to ba zanji ba, da kai da matarka baku isheni kallo ba, kana k'ok'arin kaci mutuncina a gaban k'aramar yarinya saboda kaga damata, to kaje ka had'iyeta mana iyakar sumba , ba shikenan ba saiku huta." Motar ta nufa ta bud'e ta shiga ta tako da k'arfinta tayi kwana domin ta hau kan titi, saida ta tsaya inda yake ta zuge galss tace "ka tari taxi ta mayar da kai inda ka fito." Rik'e kugu yayi da hannu d'aya d'ayan kuma ya rik'e wuya, yana so ya fahimci wani abu amma ya kasa, to duk miye na wannan harzuk'ar? qarasawa yayi gaban titi ya tari taxi yace ya mayar dashi ma'aikata, abin mamaki shine baijin komai dan gane da abinda ta masa, ranshi bai b'ace ba kuma baijin haushinta, to me yasa?😉ka tambayi Hasfat A A, haka ya koma jiki ba k'wari wata zuciyar na raya mishi ya dinga taka tsantsan ya daina waya da Zuby a gabanta, wata zuciyar tace masa to akan me? ai matarka ce, haka dai har yamma tayi ya tashi ya nufi gida yana tunanin yau kuma wacce zai isko. *************** Da qyar takai kanta shagon wani *Saminou* saboda jiri dan dama ba'a tashi lokaci d'aya idan aka gama sérum, kuma gashi ba wani abu bane a cikinta, tana zuwa ta paka motar anan, fad'a mishi da tayi bata jin dad'i yasa ya shiga motar ya tukata ya kaita gida, tare suka fita ya bata makullin motar a shiga gida shi kuma ya hau acaba ya mayar dashi, ganin layin da take yasa suka fara tunanin ko shaye shaye take, Ruk'ayya ce ta taso da Umar Faruk ya bata makullin d'akin ta bud'e mata sannan ta shiga, da k'arfi ta fad'a saman gado ta fashe da kuka tana fad'in "wayyo Mamie, zuciyata zafi take, ji nake kamar zata fasa qirjina ta fito, dan Allah Papa kazo ka d'aukeni mu kuma gida." Ruk'ayya da taji haka yasa ta shigo a hankali ta fara cewa "aunty Khairat, lafiyarki k'alau? me yake damunki? ko baki da lafiya ne?" Da qyar tayi zaune tana kallonta hawaye na ci gaba da zuba mata tace "ki bud'a fridge akwai madara a ciki ki d'auko min nasha." Da sauri ta juya ta d'auko ta kawo mata saida ta bud'e murfin sannan ta bata ta kifa kai, saida ta shanye duka sannan ta jefar da kwalin , Ruk'ayya kuma d'aukar kwalin tayi ta rik'e ta sake tsayawa gabanta tana kallonta tace "aunty kina buk'atar wani abun?" Saida ta goge hawayen dake fuskarta cikin shagwab'a tace "kin iya dafa indomie?" _Ko dai kin manta ba Umariri bane?_ "Eh, aunty Khairat na iya." ta fad'a cikin ladabi. Nuna mata tayi da hannu tace "ki bud'a coffre d'in nan akwai indomie, ki d'auki guda biyu ki dafa min, idan akwai k'wai ki had'a min dashi guda uku." "Ai kuwa aunty babu k'wai, sai dai in za'a siyo ne?" "Yanzu babu kwai a gidan nan? to jeki dafa hakanan kawai." Tana fad'a ta kwanta saboda jiri, d'aukar indomin tayi ta fita nan ta fara dafa mata, cikin k'ank'anin lokaci ta gama ta kawo mata kuma taji dad'inta sosai, hakan yasa ta kalli Ruk'ayya tace "ke ba kamar yayanki ba, kina da kirki." "Shima yana da kirki aunty Khairat, kawai dai baki fahimceshi bane." "Ke mugu ne fa, k'etar tsiyace dashi." Yar qaramar dariya Ruk'ayya tayi tace "ba zance miki a'a ba, yaya kam akwai zafi kuma akwai salon k'eta, amma kuma in dai har zaka dinga jin maganarsa sannan baka rainashi ba, to gaskiya zaku zauna lafiya dashi." Cike da basarwa tace "ok, kije, idan na fita zan siyo k'wan saiku aje." Tashi tayi tana fad'in "to aunty Khairat, an gode." **************** Yana shigowa gidan tanti Ma'u ya samu tare da Mama suna hira, har qasa ya tsugunna ya gaishesu sai dai bai bari sun had'a ido da tantin ba, dan yasan tasan me yayi kuma tana kallonshi da abun, Mama ce tace masa "akan maganar tarewar Zubeida ne, ta yarda ta dawo gidan mijinta ta zauna itama tayi karatunta." Kallon Mama yayi ya kuma kalli tantin, tanti Ma'u ce ta katseshi da "ko dai baka shirya tariyarta bane, kafi son ka dinga zuwan can gida kana....." "Na amince tanti, yaushe ne?" ya katseta dan yaga zata tona mishi asiri, ita kuma dama ba ruwa bane a idonta, dan haka ba komai bane a wajenta danta fad'a kowa yaji. "Nan da kwana uku ne." ta fad'a a kausashe. Tashi yayi ya nufi kewayen nasu yana mamakin canzawarsu, tunda ya tunkari d'akin yaji kid' na tashi, can cikin mak'oshi yayi sallama dan haka ma bata ji ba, shiga kawai yayi tare da tsayawa k'ofar d'akin yana kallonta tana tiqar rawarta, kayan jikinta su suka d'aga masa hankali tare da tayar masa da wata kafirar sha'awa da bai tab'a jin irinta ba a rayuwarsa, iya cinyoyinta wandon yake sai rigar da ba za'a kirata da bras ba haka kuma bata fi bras girma ba, rintse idonshi yayi sosai ya cije labb'enshi , bud'e ido yayi ya sake saukesu a kanta, da k'arfi ta juyo hakan yasa gashinta dake sake saida ya tashi sama shima ya juya sosai, duk da ganinshi da tayi ba tayi wani yunk'urin kare jikinta ba sai dai dakatar da rawar da tayi, gumin data had'a yasa ta fara takowa itama da nufin fita, tsaye tayi saboda ya tare hanyar fitar kuma har yanzu idonshi na kanta ya kasa d'aukewa , hannayenta ta d'aga tana tattare gashinta tana kallonshi tace, "Ka bani hanya zan wuce." Ganin ya kasa gusawa kuma har yanzu kallonta yake yasa ta matso daf dashi ta d'aga kanta tana kallonshi saboda ya fita tsawo sosai, wani mayan kallo ta masa tana murmushi tace "yadai, kana jin wani abu ne?" Da sauri ya dawo hayyacinshi hakan yasa girgiza kai, wani murmushin ta sake yi tace "hakan yafi maka." Saida tayi kamar zata fad'a jikinshi kafin ta samu ta wuce saboda ya kasa matsawa a hanyar, takalmi tasa ta shiga douche tayi wanka duk da ta d'auki lokaci hakan yasa ma Umar Faruk tafiya masallaci saboda idan ya tsaya jiranta zai b'ata lokaci, harya dawo bata shirya ba sai d'aurin qirji daya sameta dashi tana shirin saka kaya, bai sake kallonta ba harya saka doguwar rigarshi zai shiga wanka tace "kayi hak'uri fa, d'azu na baroka acan wajen." ta fad'a tana dariya. Kallonta yayi kawai yace "hmmmm, ya jikin naki?" Saida ta nufo wajenshi ta bud'e fridge ta d'auki ruwa sannan ta fara bud'ewa tana fad'in "da sauki, amma dai ba zaka sake bari na kwana a cikin sauron nan ba ko? dan nan gaba nasan mutuwa zanyi." Sallamar tanti Ma'u ce ta katsesu ta shigo ganin amarya, Umar Faruk ne ya leko yana fad'in "tanti shigo mana." Khairat kuma wajen kayanta ta nufa ta fara neman wanda zata saka har tanti Ma'u ta shigo, Umar Faruk ne ya bata wajen zama amma Khairat ko kallo, cikin taushin murya yace "Khairat, wannan itace magajiyar Mama kuma mahaifiyar Zubeida." "Oho , ina wuni Mama, ya Zubeida? fatan tana lafiya?" "Um , lafiya lau." Tana fad'a ta tashi tace "Umar ni zan wuce, zaka zo ganin matar taka?" Saida ya kalli Khairat yace "eh tanti zanzo." Tanti Ma'u kam mutanen nan ne da bakinsu baya da linzamin, kawai sai cewa tayi "da alama karuwancin harya fara tasiri a kanka, tunda gashi har saika kalleta kafin ka yanke hukunci." Labule ta bud'a zata fita Khairat ta rufe wajen kayanta ta matso tana fad'in "yadai tsohuwa, me kika ce? sai naji kamar kince karuwanci ko?" "Eh, haka nace, ko k'arya nayi ba karuwar bace ke? me ake kiran mace irinki inba karuwa ba? ke kar kice zaki min fitsara dan wallahi ba mutunci ne dani ba, ba zan duba cewa ke sarakuwata bace ko kuma kishiyar 'yata, tsaf zan kwab'e kayana na dakeki son raina." Dariya kawai Khairat tayi, kasancewar ba mai son hayaniya bace hakan yasa kawai tace "bansan me kika sani akaina ba da har kike kirana da karuwa, amma ga dukkan alama 'yarki kike tayawa kishi tunma bata shigo gidan ba, to ba komai kije, amma ki sani ni Khairat da karuwa ce, wallahi da Umar Faruk bai kusanci 'yarki ba a daren jiya, ki dinga sanin me kike fad'a dan baki san me za'a fad'a miki ba idon kin b'arota da zafi, Umar Faruk kuma gashi nan ki d'auka ki kaiwa 'yarki, amma nasan saiya dawo gareni, koba haka ba...... *Faruk*?" Ta fad'a tana fad'awa jikinshi tare da shafo fuskarshi, tsikar jikinta ne ta tashi haka shima, a take yaji zufa na tsattsafo masa, ba abinda ya masa dad'i kamar kiransa da tayi da *Faruk* dan babu wanda ya tab'a kiranshi da haka sai yau, bai iya cewa komai ba saboda mamaki, tanti Ma'u kuma cewa tayi "ke dai wallahi anyi tsinanniya marar kunya, yanzu a gabana kike rik'eshi haka kamar wata uwarki ce ta haifeshi." "To wace kunya kuma? mijina ne fa, nan da qananin lokaci ma cikinshi zaki gani jikina." duk tayi maganar ne tana sake cukwikuye Umar Faruk. "Mtsssss, Allah ya wadaranki 'yar iska kawai, wato kinzo kin samu wuri harda mik'e qafa, kamar ba kece yar d'an siyasan nan ba da ba'a fadanshi da alkhairi , ke da gani nasan baki samu tarbiyya ba daga wajenki uwarki, kuma nasan hakan ba zai rasa nasaba da tasu rashin tarbiyyar suma iyayen naki." D'agawa tayi daga jikin Umar Faruk tace "ke tsohuwa, kifa kama girmanki, ba mutunci ne dani ba wallahi saina zubar miki da...." Yayi saurin saka hannunshi ya rufe mata baki yana kallon tanti yana fad'in "dan Allah tanti kiyi hak'uri ki tafi, nace zanzo." "A'a, saketa ka barta ta fad'i abinda take son fad'a danta nuna min ita yar zamani ce, da wallahi nima saina nuna miki ni tsohuwar zamani ce, wai har wani cika baki kike zaki raba Umar Faruk da Zubeida ko? to bismillah, idan kika fasa raba tsakanin nasu ke ba *'yar halak* bace, baki haihu cikin uwarki da ubanki ba, shed'aniya kawai marar kunya." Jin abun na tanti wuce ya gona da iri yasa ya dafa kafadunta ya fitar da ita daga d'akin, Khairat kuma kanta ne taji yana sarawa da k'arfi sosai ga qirjinta da take jin yana d'an zafi ga kuma dukan da yake mata, hannu biyu tasa ta dafe kanta sosai ta rintse ido dan kamar saukar guduma take ji a cikin qoqon kanta, da qyar Umar Faruk ya fita da tanti daga gidan ya had'ata da Aliyou dake kofar gida yace ya rakata ta shiga taxi, wannan masifa data dinga yi yasa mahaifiyar Umar Faruk itama kanta ya fara sarawa saboda hawan jini ne da ita, ko kad'an bata qaunar hayaniya koya take. Mikewa tayi da qyar badan tana ganin gabanta ba ta fara bud'a duk wani abinda take ganin za'a aje abu ciki mai mahimmanci kota samu taga maganinta, tana cikin dubawa Umar Faruk ya dawo d'akin, binta yake da kallo saboda ganin tana abu kamar makauniya dan ba daidai ba ma take tafiya, ganinshi a bayanta yasa ta dago hannunta dafe da kai tana ganin dishi dishi ta fara masa magana cikin yanayin matukar shan wahala, "Dan....Allah ka tai ....maka min, a cikin kayan nan ka ....duba min...ma...ga...maga." Bata qarasa ba tayi luuu ta fad'i kasa, da gudu Umar Faruk yayo kanta ya zube qasa ya fara kiran sunanta, shiru bata amsa ba, cike da damuwa yace "na shiga uku, tanti ta kwanto min bala'i, yanzu gashi bansan meye matsalar ba, ya zanyi da ita?" Tashi yayi da sauri ya d'auki ruwan data aje akan fridge yazo ya zuba a hannu ya fara shafa mata a fuska, da qyar ta farfad'o sai dai da wani sabon ciwon kan, da kuka ta farka tare da saka hannaye biyu akai tana fad'in, "Kaina zai fashe, ka taimaka dan Allah ka d'aure min, zai fashe, kaina zai tarwatse, ciwo yake min sosai, dan Allah ka d'aure minshi *Faruk*." "Kanki ne ke ciwo?" ya tambaya cike da tausayi. Itama cikin kuka tace "qirjina ma fashewa zaiyi, amma nafi jin ciwon kan nan, dan Allah ka taimaka min ka samo abu ka d'aure minshi." Rufe ido yayi lokaci d'aya kuma ya bud'e ya saukesu a kanta, tsaye yayi tare da sungumarta ya rumguma a jikinshi, yanda ta kwantar da kanta a qirjinshiya yasa hankalinshi ya sake tsananta tashi, domin kuwa tsaf yake jiyo yanda jijiyoyin kanta ke harbawa, a hankali yake takawa da ita harya direta akan gado, ya qura mata ido yana ganin jijiyoyinta duk sun fito, alamu ne qarara suka bayyana masa irin wahalar da take ciki, haka kawai sai yaji inama ciwon ya koma kansa, koba komai zai fita juriya da hak'uri, gyara zamanshi yayi a kan gadon yasa hannayenshi biyu ya fara shafa kanta daga farkon inda take aza goshinta wajen sallah, har zuwa inda gashinta ya tsaya kusa da kunne, ya jima yana shafa mata kamar yana wasa jin haka kuma yasa Khairat shako wuyar rigarshi cikin azaba da rad'ad'i ta bud'e ido danta masa magana amma sai taga dishi dishin ma har yafi d'azu, dan haka ta d'ago kanta ta kai bakinta har saman hanshinshi sannan tace "ka d'aure min kaina nace, ko so kake na mutu? mugu kawai azzalumi." Shidai baice qala ba harta saki wuyan rigarshi, yana cikin shafa mata ya matse daidai inda gashinta ya tsaya sosai da yatsa biyu, wata siririyar qara tare da zabura ta cakumi rigarshi ta shige qirjinshi tana rik'e hannunshi daya matse mata kai da k'arfi sosai, k'ok'arin k'wace hannunshi take dan ba qaramin matsa ya mata ba, shi kuma ya rik'e sosai hakan yasa ta kasa k'watar kanta, turmutsutsu kawai take a jikinshi tana zubar da hawaye, gashi tana rok'on ya saketa amma bata jin muryarta na fita, da qyar yayi dauriya ya k'arasa addu'o'in da yake karanta mata saboda yanda take had'a jikinshi da nata tana murzawa, ba tare daya d'auke yatsunshi ba yaja yatsun nashi da k'arfi har saida ya diresu akan inda take aza goshinta wajen sallah sannan ya saketa, tana jin wani sauk'i ya zirnyarceta ta fad'a saman pillow tana sauke numfashi amma idonta rufe, sai lokacin taji kan yana mata sauk'i sosai sai kuma taji qirjinta kamar zai tsage, hannaye ta d'ora akai tana murzawa, ganin haka yasa ya d'auke hannayenta yace "bara na taimaka miki, shima zai bari da yardar Allah." Kallonta yake yana tunanin yanda zaiyi wannan taimakon, kiran sallah isha'i ne ya riske kunnuwanshi, a hankali ya fara k'ok'arin sauka daga kan gado amma sai yaga ta dunk'ule waje d'aya tana dafe qirjinta sosai, wani sauk'ak'ak'en numfashiya sauke sannan ya dawo ya zauna, gyara mata kwanciyarta yayi ta mik'e sosai kamar wata gawa sannan ya d'auke hannayenta daga qirjinta, "um um, Umar faruk, karka fara." cewar wani b'angare na zuciyarshi. "Ba komai, matarka ce ai, ka d'auka yanzu ma wani *Jihadi* ne za kayi, domin tana cikin halin rayuwa ne da mutuwa." "Hummmmmmm." cewar Umar Faruk. A hankali ya kai hannu ya sab'ule d'aurin qirjin dake jikinta, wata 'yar k'aramar numfashi yaja tare da saka tafikan hannayenshi ya rufe fuskarshi, ba k'aramin rikita mashi lissafi sukayi ba, kasancewar Allah ya horesu gasu kuma b'ul b'ul dasu kamar na mai k'aramin ciki, jawur suke har sunfi fatarta haske uwa uba kuma kan😎, kamar wani abu ya cijesu saboda yanda suke jawur dasu kamar an sulb'esu, gasu giri giri suke babu alamar kunya a idonsu😉👀, bud'e idonshi yayi ya sauke a fuskarta sai dai idonta a rufe suke, da alama bata ma cikin hayyacinta, "k'uk'ut." ya had'iye yawu kafin ya kai hannunshi da tuni suka fara karkarwa ga gumi dake tsattsafo masa, dan tuni ya shiga masifa network kuma ya kawo service, awazarta duka biyu ya soka hannayenshi a qarqashi ya tallabosu, wata irin bank'arewa tayi ta tusa masa qirkinta a nashi qirjin saboda masifar zafin da taji, kwantar da ita yayi saita kuma tasowa tana kara 'kwak'umeshi, sake mayar da ita yayi yana fad'in "ki tsaya mana, bana son mugunta fa." _To wai fan's, me Umar Faruk ke nufi da baya son mugunta, mema aka masa na muguntar?_ Nan ma dai addu'a ya mata ya tofa mata sannan ya rabu da ita yana ji yana gani jam'i ya wuceshi, sauka yayi daga gadon ya bud'a wajen kayanta ya d'auko wata rigar bacci da wandonta silip ya aje mata yana fad'in "ki tashi ki saka." Sai dai bansan Khairat azabar ciwon kai yasa ji da ganinta sun d'auke ba na wucen gadi , ko alamar taji ma ba tayi ba hakan yasa ya d'auki kayan ya warware rigar yana kallo........ _Me kuka ce?😁 zai saka ne ko kuma dai yaya zaiyi?_💁 💋luv u my Meelat.👄 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *Sadaukarwa ga* _Fateema_ momyn Dady _Maman tasleem_ _Bismmilahir-rahman-rahim_ _Allahumma antas- salam, wa minkas-salam, tabarakta ya zuljalali wal-ikram._ *Astagfirullah wa atubu ilaikh.* 2⃣5⃣ Kamar zai fita daga d'akin kuma saiya kashe wutar d'akin ya dawo da rigar a hannunshi, duk da ba'a gani amma haka ya lalabata ya qarasa zame towel d'in, wandon ya d'auka ya fara saka mata sannan ya zura mata rigar, saida ya tabbatar komai yayi daidai sannan ya kunna hasken d'akin, daga inda yake ya kalleta ganin kayan sun mata d'as gwanin kyau, fita yayi daga d'akin danya tafi masallaci sai dai kuma yasan alwalarshi ta karye dole saiya d'anyi wanka😂 ko sama sama ne😛, haka kam akayi saida yayi wanka ya fito ya bud'a kayanshi zai ciro wasu kayan ya saka kawai yaga maganin da kakarta ta bashi, a hankali ya fara tuna maganganun iyayenta dama kakarta d'in, hakan yasa ya ya fad'a a fili "kenan wannan ne abinda ke damunta? to me yake janyo mata shi?" Maganar kaka ya sake tarowa baya kawai sai yace "uhum, kenan b'acin rai da damuwa ne kamar yanda mahaifinta ya fad'a? ikon Allah." Maida kallonshi yayi gareta tana bacci hankali nutse, shiryawa yayi ya aje magungunan kusa da ita ya fita ya nufi masallaci, shi kad'ai yayi sallah shi sannan ya hau mashin d'inshi ya d'an fita, baifi awa d'aya ba kuma ya dawo, har yanzu bacci take dan haka ya fito da clé USB daya siyo ya mak'ala a tv ya jona ya fara sauraren k'ira'o'in, wannan karatun ne ya tasheta yana ganin haka ya taso zunbur yayi kanta, tana dafe da kanta ta fara k'ok'arin bud'e idonta, a kanshi ta saukesu tana kallonshi, saida ta saisaita kanta sannan ta kalli d'akin da kyau ta kuma kalli jikinta, da sauri ta dafe qirjinta ta kalleshi a tsorace. "Ba wannan kayan bane jikina, waya canza min kayana?" ta tambaya tana kallonshi. "Dank'ari." cewar Umar Faruk. Da sauri ta sauka daga kan gadon tana fad'in "waya canza min kayan jikina, ka fad'a min gaskiya Faruk, kaine? yanzu kenan ka kalleni saboda kaga bana cikin hayyacina? kamin adalci kenan? saboda kawai kana mijina." "Kinga dan Allah, bafa abinda kike tunani bane, ba..ni ba...bane ba sauya miki kaya." Kafeshi tayi da ido tace "kalleni." Kallonta kam yayi sai dai gaba d'aya gabansu dukan uku uku yake, a hankali tace "ka rantse ba kai bane, ni kuma saina yarda." Shiru ya d'anyi kafin yace "kiyi hak'uri, ni na canza miki, amma...." "Amma me? baka kalleni ba za kace?" Kuka ta saka da k'arfin gaske harda bubbuga qafafu tana fad'in "shikenan ya gama dani wallahi, ace kamar wannan yaron ne zai saka min kaya a jikina, shikenan ta qare miki Khairat, baki da bakin magana kuma tunda haka ta faru, nan gaba kuma kusantarki zaiyi daga nan kuma saiki d'auki cikinshi sannan ki haifeshi , bayan nan kuma saiya...." Da sauri Umar Faruk ya janyo k'ugunta ya had'e da nashi ya d'ora yatsarshi akan labb'ata suna kallon juna, wani yanayi yake ji dashi kad'ai yasan me yake ji, dakewa yayi ya kama gashinta ya fara wasa dashi kamar gaske harda murmushi kafin yace mata "kiyi shiru, bana so mutanen dake waje su d'auka wani abu ne nake miki, dan haka kuskure ne, ki cire wannan tunanin a qwaqwalwarki dan haka ba zata faru ba, ni Umar Faruk ba zan iya had'a jikina da naki ba." "Saboda me? ni karuwa ce? kaima haka kake gani? amma me yasa ka aureni to?" Ganin hawaye sun cika idonta sai kuma ta bashi tausayi sosai, a hankali ba tare daya raba jikinshi ba yace "ni ba haka nake nufi ba, kawai dai ba zan iya had'a jikina da naki bane, saboda ina da matuk'ar kishi." Qasa tayi da idonta tace "kenan yanzu da ice ka had'a jikinka? ko kuma kana nufin daga wannan had'awar da kayi yanzu ne ba zaka sake had'awa ba?" Sakinta yayi yace "daga wannan ba zan sake ba." Har zai wuce tace "baka ji mena fad'awa mahaifiyar matarka ba kenan? idan naso Faruk zaka zama nawa, idan nayi niyya zaka zama kamar raqumi da akala sai yanda nayi da kai, ka daina cika baki." "Hummm, ba wani cika baki, ina da yarda da kaina ne shi yasa." "Ka tabbata?" "Qwarai ma kuwa." "Ok, zamu gani, ni kuma zan ruguje wannan yarda da kai d'in." "Kinga maganinki nan ki d'auka kisha yafi miki mahimmanci." Juyawa tayi inda ya nuna mata ta kalla, maido kallonta tayi gareshi tace "ina ka samu magani na?" "Matata ce ta bani." Wani irin murd'awar kayan ciki taji lokaci d'aya kuma zuciyarta ta turnuk'o, a dake tace "wace matar taka? ba dai wannan d'iyar masifafiyar matar ba?" Dariya ce ta kama Umar Faruk, karo na farko da Khairat taga dariyarshi, kafeshi tayi da ido harya tsagaita yace "wannan ta dabance , duk cikin matan nawa babu mai qaunata kamar ita, shi yasa nima na mata waje na musamman a zuciyata." Duk da Khairat ta fahimci Umar faruk zaiyi dad'in zama kuma kamar yanda Ruk'ayya tace ta fad'a ne, amma kuma wani bala'i da taji ne a zuciyarta yasa ta rasa meke damunta, haka kawai taji bata so yana danganta kanshi da kowace mace a duniya, ba tare daya ankara ba Khairat ta kai masa duka a qirji harda fad'in "aisai kaje gaka gata ku cinye junanku." Juyawa tayi zata haye gado tana fad'in "aikin banza kawai, ni gidanmu ma zan koma." Da k'arfi taji ya janyota har saida ta fad'a qirjinshi, kafe juna sukayi da ido na d'an lokaci kafin yayi k'arfin halin cewa "meye wannan nake gani a idonki?" Tsaki tayi mai k'arfi ta janye kanta daga jikinshi, fizgota yayi niyyar yin sai kuma, "Assalama alaikum." sallamar Ruk'ayya ta katsesu. "Shigo Ruk'ayya." cewar Umariri😁. Shigowa tayi tana aje kwanukan Khairat tace "kina zuwa a lokacin da bai dace ba fa." Ruk'ayya dai sakin ido tayi tana kallonta, har zata fita kuma tace "kina ji? ki dafa min." A hankali Ruk'ayya ta tako ta zo ta d'auki indomien inda ta d'auka d'azu sannan ta fita tana guna guni, kwance tayi akan gado ta d'auki wayarta ta fara kiran lambar Mamie, muryarshi taji yace "ki daure ki dinga suturta jikinta koda gaban mace ne 'yar uwarki." Hannu d'aya ta rumgume a qirji ta mike qafafunta tana girgizawa tana murmushi tace "to meye a ciki, naga jikina ne ba bana ka ba, kuma kace baka qaunarshi ba zaka tab'a had'ashi da jikinka ba, to miye na damuwa?" Muryar Mamie ta daki kunnuwanta dan haka tace "Mamie ya kike, shine kun manta dani ko kirana ba kuyi ba?" Shiru tayi kafin tace "ba wani nan, kudai kuna can kuna soyayyarku da Papa, tunda yanzu babu kowa a gabanku, dama nice kuma kun kawar dani." Turo baki tayi cikin shagwab'a tace "wallahi Mamie nayi kewar Papa, nan fa gaba d'aya ba dad'i, yau fa har zazzab'i ya kamani, amma dai da sauki." Nan suka dinga hira har Ruk'ayya ta shigo ta kawo mata sannan ta kashe wayar, sauka tayi daga kan gadon ta zauna kujerar da Umar Faruk ke cin abinci harda turashi take da k'ugu tana fad'in "duk kabi ka matse waje kai kad'ai." Plate d'in imdomin ta ta aza ta fara ci itama, satar kallon hannunta yake wanda suka sha jan lalle, tana ci tana kallonshi ta wutsiyar ido tana kuma tunanin abubuwan da matar nan ta fad'a mata, alwashi taci saita saka matar nan tayi nadamar abinda ta mata, to amma tayaya? dole saita samu kusanci da Umar Faruk, to shima tayaya? abu mai sauk'i, namiji neshi ke kuma macce, kawai ki samu kusanci dashi, a hankali ta juya ta kalleshi, caraf idonsu suka had'u, kallon baka da hankali ta masa yayin da shi kuma ya bita da harara, tunawa da plan d'inta yasa ta turo baki gaba cikin sigar shagwab'a ta d'an mangareshi da kanta, hannu tasa ta debo lomar indomie ta nufi bakinshi da ita, ganin yana mata kallon rashin fahimta yasa ta sake langab'e kai tace "bud'a bakinka mana." Kai ya gurgiza mata alamar a'a, a bakinta ta saka lomar ba tare data kallesa ba tace "hum, kama daina kallona haka." Wata sallamar ce ta katsesu daga k'ofar kewayen nasu, Umar faruk ne ya fita jim kad'an ya dawo, tsaye yayi a kanta yace "ki canza kaya Baba nasan ganinmu." "Meya faru?" ta tambaya. "Ki tashi, duk litinin ana zama wajenshi da wannan lokacin." "Me ake tattaunawa?" "Oh, Khairat, kiyi abinda nace mana." "To bari na gama cin abinci na." Ba yanda ya iya saida ta gama sannan ta wanke hannu ta d'auki doguwar riga tasa ta d'auki kallabi ta yafa, yana kallonta yace "hijab zaki saka." "A'a, nifa bana iya zama dashi, kuma ba kace wajen Baba ne zamu ba." Hijab d'inta da take sallah ya d'auka ya matso kusanta ya gyarashi , bai b'ata lokaci ba wajen saka mata, k'ok'arin 'kwacewa tayi ya mata wani jan kallo dole ta tsaya, gaba ya sata suka fita daga d'akin bayan ya rufe, suna daf da shiga d'akin Baba inda gaba d'aya mutanen gidan suke, hannunta Umar Faruk ya kama ya gyarawa yatsunsu waje d'aya tare da murzawa har suka shiga yayin da yayi sallama, amma suna shiga ya saki hannunta suka samu wuri suka zauna, tunda ya rik'e hannunta taji wani *baqon yanayi* a tare da ita da bata tab'a jin irinshi ba, kamar yanda shima abubuwan da yaji sunfi k'arfin wasa, dan saida ya tuna da maganar Ishaq cewar *wataqila yanzu ne ya fara soyayar gaskiya.* Kallon kowa take yayin da su kuma suke sauraran nasihar da Baba ke musu akan rik'o da zumunci, sun jima sosai kafin Baba yaba Zeinab damar rufe musu taron da addu'a, sosai yarinyar ta shiga ran Khairat saboda ganinta bata fi yar shekara bakwai ba, amma sink'i sink'i addu'o'i na fitowa daga bakinta, haka suka tashi suka fito, kowa makwancinshi ya nufa sai Umar Faruk daya kalli Khairat yace "muje kiga Mama." Binshi kawai tayi suka nufi d'akin Mama, da sallama ya shiga ita kuma tun k'ofar d'akin take kalle kalle har suka shiga, zaune yayi kusa da Mama dake kwance amma ganinsu tare yasa ta tashi zaune tana fad'in "ah, ashe tare kuke da 'yata." Sai lokacin ta d'anyi zaune akan kujera tana kallon d'akin da kyau, k'aramar panka take kallo a ganinta ba zata musu komai ba, muryar Umar Faruk ce ta katse yana fad'in "ya jikin Mama?" Kallon Mama tayi tace "dama baku da lafiya ne?" "A'a 'yata, ai nama ji sauk'i." Umar Faruk ta kalla dan haka yace "hawan jininsu ne ya tashi, amma sunsha maganinsu." "Wane irin magani, kuma baku kaita asibiti ba?" "Eh, akwai maganin da aka rubuta musu, to shine suke anfani dashi." cewar Ruk'ayya dake gyara shinfid'a. "Amma ai hakan bai dace ba, me zai hana ku dinga kaita asibiti duk lokacin da bata jin dad'i? amma zama da ciwo ana shan magani barkatai." Tsam ta mik'e daga kujerar ta durk'usa kusan Mama ta tallabota ta zauna daidai, kallon Ruk'ayya tayi tace "ki bani hijab d'insu." Ba tace komai ba sai hijab d'in data mik'o mata, saka mata tayi sannan tayi tsaye tana ciccib'ar Mama tana fad'in "muje asibiti Mama, lafiyarki tafi komai mahimmanci, kuma suma kansu yayanki nasan sun san da haka, amma babu mai fasahar kaiki asibiti, sai sun rasaki kuma za kiga sunfi kowa damuwa da kuka." Kallonta kawai Umar Faruk da Ruk'ayya da sauran yaran suke, tsaye yayi yana fad'in "ba wai bamu damu bane, muma muna...." "Dan Allah kayi shiru, ni ba tambayarka nayi ba." Mama ce tace "'yata dama kin barshi wallahi, naji sauk'i ai da dama jikin ba kamar d'azu ba." "A'a Mama muje kawai, sai dai kuma ko kina so ki nuna min ni ba 'yarki bace." Suna fitowa farfajiyar gidan ta kalli Umar Faruk tace "ka rik'e Mama, zan d'auko makullin mota." Tana fitowa kuma da makullin da post d'inta ta kuwa haka ta rik'e Mama har suka fita inda Baba ya fito da su tafi tare amma Khairat tace kawai yayi zamanshi, tare da Umar Faruk suka tafi suna gaba ita dashi tana tuk'i, Mama na baya in banda addu'a da qaunar Khairat babu abinda take ji, bata san kuma me yasa ba amma taji daga haka son sarakuwar tata ya kamata, suna zuwa asibitin da taje da safe docteur Sadiya ta tafi sai wani docteur d'in, cikin qwarewa ya duba Mama kuma ya fad'a musu jininta ya hau, allura aka mata na saukar da hawan jinin sannan aka rubuta wasu magunguna masu matuk'ar tsadar gaske, ita ta biya kud'in sannan suka kamo hanyar gida, saida ta tsaya babban pharmacie ta siyo duka magungunan sannan suka tafi gida dare yayi sosai lokacin. Har d'aki suka kai Mama ta kwanta Khairat taja zanin rufa ta rufeta, gefen fuskar Mama ta shafa tace "kiyi bacci Mama, dan Allah banda damuwa da tunani, ki more baccinki babu mai takuraki." Mik'ewa tayi tana fad'in "saida safe Mama." Hannunta taji ta rik'e hakan yasa ta koma ta durk'usa tana kallonta, cike da jin dad'i da tsantsar qauna Mama tace "na gode yata, ubangiji ya saka miki da mafificin alkairinsa, Allah ya kareki daga sharrin masharranta, Allah ya baki abinda kike so, Allah ya saka miki da gidan aljanna, Allah ya albarkaci rayuwarki da zuri'arki baki d'aya, Allah ya sakawa iyayenki da alkairi, Allah ya kareki daga bakin duniya, Allah....." Rufe bakinta Khairat tayi ta fashe da kuka ta fad'a jikin Mama ta rumgume, saida tayi mai isarta ba wanda ya bata hak'uri kafin ta d'ago ta share hawayenta ta rik'e hannun Mama sosai tace "Mama, kin kusa kasheni da farin ciki saboda wannan addu'ar taki, tunda nake a rayuwata ban tab'a jin addu'a irin wannan ba, ko mahaifiyar data haifeni bata tab'a kwatanta yimin irin wannan addu'ar ba, Mama nice da godiya bake ba, ina da yak'inin wannan addu'ar taki ba zata fad'i k'asa banza ba, a yanzun nan sai nake ji kamar ni 'yar aljanna ce kuma zan gama da duniya lafiya, Mama Allah ya bar mana ke, kuma nayi alk'awarin zama a gidan nan har qarshen rayuwata in dai har zan dinga samun irin wannan addu'a a wajenki." Tana fad'a ta bar d'akin tana kuka, Umar Faruk ma bayanta yabi bayan sunyi sallama da Mama, yana shiga ya sameta kamar ba ita bace mai kukan nan harta murje idonta tayi kwance, sai dai abinda Umar Faruk bai sani ba ta rufe ido ne amma addu'a Mama ce ke yawo a qwaqwalwarta, kashe wutar d'akin yayi bayan yayi shirin kwanciya sannan ya kwanta a saman kujera, zunbur ta tashi zaune tana lalubar wayarta ta kunna haske, a daqile tace "malam nifa bana bacci a cikin duhu, ka kunna fitilar mana in dai ba wani abu bane a ranka." Wayarshi ce a hannunshi yana duba kiran da Zuby tayi bai d'aga ba, ba tare daya kalleta ba yace "ni kuma gashi bana bacci a cikin haske, ya kenan za ayi?" _To fan's ne zasu bamu shawara, ya kuka ce akashe ko a barta kunne?_ _Idan an kashe akwai d'an dannau mai taushe mutun cikin dare😎😂, idan an bari kuma shed'anun aljanu na anfani da hasken su cutar da bil'adama._ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *_Masoyana💖, kune abin alfahari na, ina matuk'ar ji daku fiye da tunaninku, fatana Rabbi ya bar qauna tare da soyayya, nasan ba zamu iya had'uwa daku ba dukanku, amma ina fatan Allah ya sadamu da alkairinsa sannan ya taramu a aljannatul-firdausi._*👏👏 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 2⃣6⃣ Wajen makunnin ta nufa tana shirin kunnawa yayi saurin tare gabanta, d'auke idonshi yayi daga nata saboda masha Allah akwai girma kamar idon Barbie ga kuma kyau da yalwataccen gashi, "dan Allah ka matsa min na kunna, bana iya bacci a cikin duhu, tsoro nake ji." Da kanshi ya nuna mata gado yace "kije kiyi addu'a saiki kwanta, babu abinda zai sameki da yardar Allah." "Ba zaka gane ba, dan Allah..." bata qarasa ba saboda hannunta data kai ta kunna wutar shi kuma ya rik'e. Janye hannunta tayi tana sauke ajiyar zuciya tace "shikenan, kar Allah yasa ka kunna, amma wallahi naji hannun mutum a jikina ana lalubata, to zaka sha mamaki dan saina fasa maka kai wallahi." Dariya ce ta subece masa komawa yayi kawai ya kwanta, harta kwanta itama amma data rufe ido saita ga su Musa a idonta, sosai ta rintse ido amma duk da haka bata daina gani ba, bud'e idon tayi taga duhu sosai, zaune tayi ta kalli wajen da Umar Faruk yake tace "malam nasan ba kayi bacci ba, dan Allah ka taimaka ka kunna ko hasken fitalar wayarka ne." "Wayarki fa?" ya fad'a cikin taushin murya. "Haka kawai zan kunna harsken wayata har safe, ai tunda ka hana a kunna wallahi na wayarka zaka kunna." "To zan gani, wayata ce kota wani." "Kaji kamar mai wata wayar million d'aya, wallahi saika kunnata ko kuma." Ta fad'a tana saukowa daga kan gadon, jin tahowarta yasa ya tashi zaune yana fad'in "ko kuma me?" "Gani nan ai a aikace zan nuna maka." Da hasken wayarta taga wayar tashi akan qaramin teburin dake tsakanin gadon da kujerar da yake, tunkararta tayi gadan gadan tare da kai hannu zata d'auka, da sauri ya d'auki wayar tare da ajeta bayanshi ya rumgume hannaye yace "ki d'auka idan ke jan wuyace." "Dan Allah ka bani, wallahi bana iya bacci a duhu, kuma gashi dare keyi har yanzu banyi bacci ba, zanfa maka kuka wallahi ko kuma na fad'awa Mama." "Wace Mamar?" ya tambaya. "Mamank...." kuma kawai sai tace "Mamana." Kallonta yayi dan ya mata tambayar ne dan yaji me zata ce, a hankali ya zura hannu ya d'auko wayar ya mik'o mata kamar sakarai, hararanshi tayi tace "ka kunna mana, meye saika wani bani a hannuna." Baiyi magana ba kuma bai bar mik'a mata ba, cike da haushi tasa hannu ta karb'a ta kunna fitilar, murmushi tayi ta kalleshi tace "kaga tasirina ya fara aiki a kanka, tun ma ba'a je ko ina ba kenan." Zaune yayi yana fad'in "ke bani wayata, tasirin me? kin d'auka dabararki ce tasa na baki?" Juyowa tayi tana kallon qwayar idonshi ta soka wayar a cikin rigarta tsakiyar mamanta sannan ta rik'e k'ugu tace "kazo ka d'auka idan ka isa." Murgud'a baki tayi ta koma gado ta haye tare da fitowa da wayar ta aje gefenta, baki sake ta barshi yana kallonta har bacci ya d'auketa, saida ya tabbatar tayi nisa sannan ya taso zauna bakin gadon yana kallon fuskarta, baisan menene asalin abinda yake ji ba, sai dai yana ji kamar a yanzu haka baya so ta masa nisa, to amma me yasa? *my aunt Aishan Umma* ce zata baka amsa a gaba, wata irin nutsuwa ce yake ji tana sauko masa, ga kuma taimakon da tawa mahaifiyarshi wanda yafi komai faranta masa rai, ya jima a wajen sosai yana tunani akanta kafin ya tashi ya koma wajenshi, ko bacci bai d'aukeshi ba yaji Khairat ta farka a tsorace. Da sauri ya dawo kanta yana kallonta, numfashi kawai take saukewa kamar wacce tayi tseren gudu, a hankali ya furta "Khairat, lafiya? meya faru dake?" Kallonshi tayi a firgice sai kuma ta rufe bakinta da hannu tana fashewa da kuka, wata nauyayyen ajiyar zuciya ya sauke ya kau da kansa danya lura tana da saurin kuka akan komai, sake cewa yayi "Khairat, meya faru?" Share hawayenta tayi tana kallonshi tace "ba komai, kaje ka kwanta kawai." "Ya zaki ce ba komai? bayan ga komai nan ya faru." "To me kake so nace? na fad'a maka bana son duhu, sune ke sake zuwa min duk da qoqarina nasan ganin na manta komai, fyad'e ba abu bane mai sauk'i, amma duk da haka ina so na manta dan nayi rayuwata ba tare da damuwa ba, naso na zama marar tsoro da fargaba, amma su sun saka na zama mai tsoro, sunsa min fargaban da bana iya sakewa a kowane lokaci, kullum ji nake kamar zasu qara dawowa gareni ne." Hawaye ta goge tace "ka kwanta kawai." tana fad'a ta koma ta kwanta ta bashi baya. "Tashi zaune." yanda ya fad'a yasa ta tashi ba tare da gardama ba. "Kiyi addu'a kafin ki kwanta." Kallonshi tayi kuma lokaci d'aya ta dauke idonta, a hankali yace "baki iya bane?" Nanma shiru tayi kawai sai yace "to ki d'aga hannayenki, saiki dinga fad'ar duk abinda na fad'a, kinji?" Yanda yace tayi, *ayatul kursiyu* ya fara karantawa sannan *ammana rasul*, kafin suka karanta *falaq* da *nas* sannan ya karanta mata *Allahuma aslaftu nafsi ilaikh, wa fawadhatu amri ilaikh, wa wajahtu wajhi ilaikh, wa aljahtu zahri ilaikh, ragabatan wa rahabatan ilaikh, lamalja'a wala manja minka illa ilaikh, amantu bi kitabikal-lazi anzalta wabi nabiyikal-lazi arsalta.* "Ki shafe jikinki." ya fad'a. Shafawa tayi sannan ta koma ta kwanta, a hankali ya tashi yana sake nanata kalmar fyad'e a bakinshi, karo na farko daya ji haushin masu laifi kuma yaji inama shiya d'auki mataki akansu , wutar d'akin ya kunna tare da komawa shima ya kwanta, ganin haske yasa ta kashe na wayarsa sannan ta sake rufe ido sai bacci. ****************** Koda tanti ta koma gida tasa Zuby ta kira mata sauran 'yan uwanta a waya kasancewar duka matane 'ya'yanta guda hud'u, nan fa ta fad'a musu matar Umar Faruk taci mutuncinta tare da fad'a musu qudirin Khairat, nan fa suka fara zaginta suna aibatata tare da cin alwashin fitar da ita daga gidan, sannan suka qara kitsama Zuby wani sabon shiri a kanta tare da alk'awarta mata sabon had'in magani na musamman domin yaqar Khairat. Sai dai tanti ita burinta ya wuce nasu dan haka safiya ma take jira kawai tayi, danta lura yarinyar dole sai an had'a da malamai. ****************** Tunda Khairat take a gaba d'aya tsawon rayuwarta, bata tab'a bacci mai dad'in na yau ba, bata tab'a jin natsuwa da farin ciki ba a cikin bacci kamar yau, gashi kuma ubangijinta ya nuna mata wani abu da ko kad'an bai firgitata ba saboda nutsuwar data farka da ita, a baccinta Allah ya haska mata tanti Ma'u tana matuk'ar biyarta da sharri , sai dai ta rasa waye kuma me yasa ya fad'a mata cewar ta rik'e addu'a tafi komai mahimmanci, koda Umar Faruk ya tasheta tayi sallah zaune tayi ta murje idonta kafin yace mata "ki fad'i abinda zan fad'a." Kai ta jinjina alamar tana sauraro, *Alhamdulillahi lazi ahyana, ba'ada ma'ama tana wa'ilaihir-nushur.* Nanma fad'a tayi kafin ta shafa ta sauka daga kan gadon shi kuma ya nufi masallaci, har tayi alwala tazo ta kabbara sallah tana tunanin akan me matar nan zata nemeta da sharri, shin akan yarta ne ko kuma akan abinda ya faru tsakaninsu? da qyar ta saita nutsuwarta ta samu tayi sallah tana gamawa kuma ko hijab bata cire ba ta zauna bakin gado, a hankali take tunano addu'a da Umar Faruk ya fad'a mata jiya, tana haka kuma ya shigo d'akin. Kayanshi ya bud'a ya d'auko duk litattafan daya fad'a jiya sannan ya zauna akan kujera, kallonta yayi yace "dawo nan ki zauna." Ba musu tayi yanda yace, littafi mai tsarki ya bata sannan yace ta bud'e, a farko ta bud'e sannan ya fara biya mata daga qananan surori har guda goma, kallonshi tayi jin daga nan yake tsayawa yasa tace "to wai meka d'aukeni, iya haka zaka tsaya min? kaga ni qara min kawai ai zan iya." "Da farko dai ina so ki d'aukeni a matsayin malaminki, dan ta hakane za kiga haske da albarka a karatun, sannan ki girmamani domin samun sauk'i, sai kuma jin maganata a duk lokacin dana miki, kin fahimta?" "In dai sai nayi haka zan samu albarka a karatuna, to na shirya zama dalib'a 'yar shekara biyar a gaban malaminta." "Da kyau." ya fad'a kafin yace "idan kina so na qara miki, ki fad'a min wanda na fad'a miki sannan." Gyara zama tayi kamar zata kwanta jikinshi sannan ta d'ora yatsarta a littafin ta fara biya masa, duk da a cikin salon koyo take karatun, amma abin abin birgewa da sha'awa, bakinta yake kallo wanda take motsashi a hankali tana biya karatun domin gudun kar tayi sauri tayi b'ata kuma, sosai Umar Faruk ya girgiza domin kaf a cikin waje d'aya kawai ya mata gyara, shima kuma ta fad'a ne ba daidai ba, murmushi yayi har hak'oransa suka fito fili yace "kinyi qoqari sosai, kuma ina fatan zaki kasance haka, har ranar da zaki hardace al'Qur-ani a kanki." Wata irin lallausan dariya tayi data tafi da imanin Umar Faruk dan bai tab'a ganin irinta ba a fuskarta, cike da jin dad'i tace "nima zan hardace a kaina, na zama kamar k'anwar nan taka?" "Zama ki fita in har kika saka kanki." "To shikenan qara d'ora min wani." ta fad'a cike da zumud'i. Nan ya sake dora mata har suka kai suratul *Qari'a* sannan yace ta rufe littafin tare da cewa "ki tabbatar kin kawosu gobe, idan ba haka ba kuma." "Idan ba haka ba me?" ta tambaya tana kallonshi. "Zaki sha bulala ne, saboda ke dalib'a ce." Wata dariya ta kece da ita mai qarfi kafin tace "ai bama zaka fara ba kaima, dan kasan zamu iya dakuwa da kai." Kunnanta ya kama ba zato ba tammani ya murd'e fuska a had'e yace "ni kike fad'awa haka? anya kina neman albarka kuwa?" Hannayenshi ta kama duka biyu tana rokon ya saketa tana fad'in "dan Allah kayi hak'uri wallahi ba zan sake ba malam, dan Allah kasa min albarka ko nayi saurin fahimta." Sakinta yayi yana tunanin ya samu hanyar da zaibi da ita cikin sauk'i dan haka yace "idan akayiwa malam laifi har qasa ake duk'awa a bashi hak'uri, dan haka ki fara in dai har da gaske dalib'a ce mai neman albarka." Ita kuma yanzun nan taji a ranta bata da wani buri daya wuce na karatu, musamman da taji wai yau itace take karatun littafi mai tsarki haka, shaukin abin ya shigeta sosai dan haka bako tunani ta zube qasa ta kamo hannunshi ta rik'e tana murzawa ba tare dama tasan me take yi ba tace "naji to kayi hak'uri dan Allah, ba zan sake ba, nidai ina sonna samu albarkar karatuna." Shima biye mata yayi ya dinga murza tattausan hannunta yace "ba albarkata kad'ai kike buqata ba, akwai ta iyayenki, dama mutanen da kike zaune dasu." Cikin mamaki tace "wai har suma?" "Eh, basu cancanci saka miki albarka bane?" Cikin turo baki tace "toya zanyi?" Mik'ewa tayi yace "yanzu zaki fara ai." Ta qasan ido ta harareshi kafin tace "toya zanyi yanzun?" Wani shu'umin murmushi yayi ya tashi tsaye yace "biyoni muje." Saida suka fita sun nufi d'akin Mama Maimuna yace "za muje ne mu gaida iyayenmu, sai kice kina neman albarkarsu." Kallonshi tayi kamar zata fashe da kuka tace "zafa ka rusa min jiji da kaina, gaskiya ba zan iya ba." "Shikenan, koma ki zauna, amma ki sani za kiyita karatu bakya fahimta, saboda ba albarkar manya a ciki." Bubbuga k'afafu tayi cikin shagwab'a ta kutsa kai d'akin Mama Maimuna, ganinta kawai tayi ta fad'o mata dan haka ta tsorata, da sallama ya shiga sosai ya gaisheta duk idonshi na kan Khairat da har yanzu ta b'ata rai, da ido ya mata alama kafin ta fahimta ta kalli Mama Maimuna tace "ina...kwana, an tashi lafiya, ina neman albarka dan Allah ki saka min." Mama Maimuna mamaki ne ya hanata magana, saida Khairat ta sake cewa "ba zaki samin bane kome?" Kai ta girgiza da sauri tace "a'a 'yata, kin tashi lafiya? Allah ya miki albarka." "To na gode, sai an jima." tana fad'a ta tashi ta fita shi kuma ya mata sallama ya fita. Kewayensu ta nufa shi kuma ya janyo hijab d'inta ya nuna mata kewayen Mama Sa'a, ciki suka shiga amma Mama Sa'a harda rumgume Khairat tanata wasar baki tana gaisheta, haushi ne yasa Khairat yin shiru ta kasa gaisheta, danta lura irin mutanen nan ne masu shishigi, Umar Faruk kad'ai ya gaisheta kuma yanawa Khairat alama da ido akan tarbiyar gaisheta amma tak'i, fitowa sukayi suka shiga d'akin Mamanshi, suna shiga da sauri ta qarasa ta durk'usa gaban Mama tana rik'o hannunta da fad'in "Mama ya jikinki?" Cikin sakin fuska tace "da sauk'i 'yata, kin tashi lafiya." "Ina kwana aunty Khairat." murayr duka yaran dake d'akin ta daki kunnuwanta. D'an murmushin gefen labb'a kawai ta musu kafin suka juya kan Umar Faruk suka ce "ina kwana yah Umar." "Lafiya lau, kun tashi lafiya?" "Lafiya lau." suka amsa. "Mama kinsha maganinki?" cewar Khairat. "A'a 'yata, yanzu dai zanci abinci sai nasha." Juyawa tayi ta kalli Ruk'ayya dake shirin fita tace "har yanzu baku gama bane?" "Eh aunty Khairat, yanzu ma zan d'ora." "Me? yanzu fa? kuma Mama ta zauna tana jiranki? me yasa ne wai kuke haka? kamar dai baku damu da ita ba." Mtsssss, taja tsaki tare da tashi rai bace ta fita daga d'akin har tana karo da Abbakar da Saratu da zasu shigo suma, wayarta ta d'auko ta dawo d'akin tana ci gaba da kira amma ba'a d'auka, saida ta aika kira na hud'u sannan mutumin ya d'auka jiki na rawa, tana jin ya d'auka tace "ka kyauta, amma yanzu bata kai nake ba, ka gaggauta had'a min duk wani abinda kake dashi yanzu, amma karka saka arom (d'and'ano) a ciki na mai tension ne, da zaran ga kama ka kirani." "To Hajia." ya fad'a ta kashe wayar. Umar Faruk ta kalla wanda suma dukansu kallonta suke tace "dan Allah ka d'auki makullin motata kaje *riva side* ka karb'owa Mama abinci." Fita tayi shi kuma yabi bayanta, makullin ta d'auka ta bashi ta bud'a post d'inta ta d'auki kud'i ta bashi, kai ya girgiza mata yace "ki barshi zan biya." "Kai kayi magana a maka oder koni? kaine ka sani koni nayi niyya? dan haka karb'i kawai." Karb'a yayi ya cire doguwar rigarshi ya sake kayan sannan ya fita, yana fita ita kuma ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin riga da siket na shadda, kwalliya tayi sosai kafin ta d'ora gyale a kafad'a ta d'auki jaka da takalmi, wayarta ta d'auka da nufin kiranshi sai gashi ya shigo, hannu kawai ta tara masa ya bata makullin sannan ta fita. Bayanta yabi amma sai yaga ta shiga d'akin Mama, Mama ce kad'ai a d'akin dan haka ta sake zubewa qasa tace "ga abinci nan kici Mama, sannan ki saka min albarka zan fita wajen aiki." "Allah yayi albarka yata ,daga yanzu har zuwa fitar numfashina na qarshe sanya albarkata ba zai tab'a nesanta dake ba." "Na gode Mama." ta fad'a tana yunk'urin tashi. Hannunta Mama ta rik'e tace " 'yata." Komawa tayi yanda take tace "na'am Mama, akwai abinda kike sone?" "A'a 'yata, ina so na fad'a miki wani abu." "Ina jinki Mama." " 'Yata, wannan kayan na jikinki, bai kamata ki fita dasu ba a matsayinki na matar aure, ki sani Allah ya umarcemu damu dinga rufe jikinmu a duk lokacin da zamu fita daga cikin gidajenmu, kuma hakan nada alfanu sosai, hakan da zaki fita baiyi ba sannan shi kanshi mijinki zaiji ba dad'i, yata, ina so ki zama salihar mace kuma yar aljanna, amma fa ki sani ba'a zama salihar mace a haka, dan Allah yata ki kare mutuncinki ko dan gudun sake faruwar abinda ya faru dake a baya, ki kame kanki ba kowa jaki da alade bane ya kamata ace sunga surar jikinki, idan zai yiwu ki gwada saka hijab ki gani, na tabbata zai miki kyau, dan sutura ce mai rufa asirin mace tare da qara mata kwarjina da haiba." Murmushi Khairat tayi ta sake makale hannun Mama tace "na gode Mama, kullum mahaifiyata na fad'a min na dinga rufe jikina, yau kema gashi kin fad'a min, hakan na nuna irin soyayyar da kike min." Tsaye ta mik'e tace "ina zuwa Mama." Nan ta bar jakarta ta fita ta koma d'akinsu, cikin hijabban da Mama tasa aka d'inka mata ta d'auko kalar aikin shaddarta ruwan qasa, tana saka hijab d'in ta kalli kanta a madubi, wani murmushi ta saki ganin yanda ya d'auki jikinta ga hannayenta da suka fito ya tsaya iya gwiwarta, fita tayi daga d'akin ta koma na Mama, su Mama Sa'a mamaki ne ya kamasu ganin tana safa da marwa a d'akin, tana shiga Umar Faruk da Mama suka sakar mata ido, tsaye tayi gaban Mama tace "Mama haka yayi, nayi kyau?" "Yata fad'ar kyan da ki kayi ma bata bakine , Allah ya kareki." "Ameen Mama, na gode saina dawo." Tana fad'a ta d'auki jakarta ta bar d'akin ko kallon Umar Faruk, tana fita ta d'auki hanya amma saboda rashin sabo yasa taji kamar an d'aureta , kasa jurewa tayi hakan yasa ta cire ta ajeshi saman kujera harta isa ma'aikatar, d'aukar hijab d'in tayi ta saka ta d'auki jakarta sannan ta fito, da gudu massinger yazo ya tareta yana gaisheta, hannu kawai ta d'aga masa tayi gaba, tunda ta shiga idon kowa ke kanta suna gaisheta da mamaki, kowa da abinda yake sak'awa a ransa, Khairat a wajen aiki tunda safe haka gashi ko Umar Faruk d'in bai zo ba, sannan da sabuwar shiga, harta tunkari office d'inta, dago ido Habiba tayi amma saita saukesu ba tare data mik'e tsaye ba kamar yanda ta saba, saida Khairat ta tsaya gaban tebur d'in tana kallonta, k'amshin turaren da taji ya tabbatar mata Khairat ce, a zabure ta tashi tsaye tana fad'in, "Kiyi hak'uri Hajia, wallahi ban...ban ganeki bane." "Wato *arniya kafira* yau ta shigo da hijabi, shi yasa har zaki kasa ganeni? dama wad'ancen shashanshun sun bini da ido, shine kema zaki min fitsara." Wucewa tayi mazauninta tana shiga ta zauna kuma ta cire hijab d'in ta rataye, a gaba d'aya ma'aikatar kuma maganganu aka d'auka, wasu na ganin Umar Faruk yayi namijin qoqari da har ya iya canza Khairat a qanqanin lokaci haka, wasu kuma na mamakin ta yanda ya iya juyata harta zama haka. _FAN'S ya kuka ce? nifa sai nake ganin kamar qoqarin na Mama ne ba Umar Faruk ba._ Abun mamaki jakarta naga ta d'auka kawai ta fito da littafin da Umar Faruk ya bata, budawa tayi ta fara karatunta a hankali daki daki , dan bata so gobe ya tambayeta ta kasa fad'a mashi, kodan gudun bulala.🤪 _Shin kuna ganin zai iya dukanta idan ta kasa kawo karatun daya koya mata?_ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 2⃣7⃣ Tunda ta fita ya bita da ido, Mama ce tayi murmushi tace "tana da taushin zuciya, cikin sauk'i zata dinga fahimtarka in dai kana binta a hankali." Shiru yayi shi dai abinda kawai yake ji a zuciyarshi yake so ya gano ko menene, "ka tashi kaje ka shirya karka makara kuma." muryar Mama ta katseshi. Tashi yayi cikin sanyin jiki ya fara shiri harya gama, tsaye yayi bakin madubi yana b'alla mab'allan rigarshi tare da wani hamshak'in murmushi a fuskarshi, yana gamawa ya makala agogo sannan ya d'auki jakarshi ya rataya zai fice, rigar baccin data cire da asuba ya gani akan gado ya d'auka, rufe fuskarshi yayi da riga yana shak'ar wani tattausan k'amshi da ba zaka tab'a jinshi ba in har ba shak'a kayi ba a kusa, aje rigar yayi amma har yanzu ya kasa daina wannan tsadaddan murmushin, ko kari baiyi ba kawai ya fita saboda ji da yake yana so ya kusanta da ita, wayarshi ya d'auka akan tebur har zaisa aljihun riga kuma saiya k'ura mata ido, tunawa yayi da wajen da wayar ta shiga jiya, wani murmushi ne ya sake sub'uce masa hakan yasa ya mannawa wayar sumba tare da mannata a qirji, haka ya d'auki hanya cike da sabon yanayi a tare dashi da sabon farin ciki, yana shiga yau ma dai haka gaisheshi wasu keyi cike da girmamawa wasu kuma tsabar izgilanci ne kawai, zaune yayi ya fara abinda ya kawo, alk'alami ya d'auka da farar takarda ya fara zana wani sabon sanfirin takalmin, ji yake yana so yaje wajenta amma kuma yana jin fargaba, jin ya kasa samun sukuni yasa kawai ya tashi ya nufi wajenta zuciyarshi na d'ard'ar na abinda zata masa ko zai tarar. Koda Habiba ta ganshi ta tashi ta bud'e masa k'ofar tare da gaisheshi, shiga yayi cikin sakin fuska amma saiya tsaya cak yana kallon Khairat, chocolat a hannu tana sha sai kuma littafinta data duqufa da karatu, d'ago kai tayi tana ganinshi ta saki murmushi tare da fad'in "yawwa, qaraso mana." K'arasawa yayi zauna kujera yana kallonta, tasowa tayi daga kujerarta ta zauna kujerar kusa dashi ta aje littafin tace "bara na karanta maka kaji, saika sake d'ora min wani." "Anan d'in?" "Eh miye to, ba bureau na bane?" Basarwa yayi kamar ba ganinta ne ya kawoshi ba ya mike tsaye yace "ba zan iya ba, kuma shine kika cire hijab d'in ko? ai za muje gida saina fad'awa Mama ta janye sawar albarkarta." Juyawa da yayi zai fita yasa tayi saurin tashi da nufin ta riko hannunshi, sam bata kula da inda ta rik'e ba sai zuba take tana fad'in "dan Allah malam kayi hak'uri karka fad'a mata, wallahi na daina daga yau, kuma rashin saboda ya janyo haka, kaima kasan ai ba zan yaudari Mama ba, dan Allah karka fad'a mata." Da k'arfi ya fizgota ta fad'a jikinshi yana mata wani kafirin kallo mai kashe jiki yace "to cire hannunki." Ido ta bud'o tace "a ina?" Raba jikinsu yayi ita kuma ta kai kallonta ga hannun nata, d'aya hannun tasa ta rufe baki ganin ceinture (belt) d'inshi ne ta cakumo, hannu biyu tasa ta rufe fuskarta saboda kunya, shi kanshi dariya ce ta kubce masa hakan yasa ya juya ya fita, zaune tayi tana mamakin abinda tayi kuma ba tare da tasan tayi ba, shi kuma yana mamakin wasu b'oyayyin halayen Khairat da sai yanzu ne suke fitowa, dan kunyar data nuna taji ma ya masa dad'i sosai, misalin *10:00* Khairat tasa aka tattara kowa dake ma'aikatar suka shiga meeting, saida ta saka hijab d'inta sannan ta fita, anan ta fad'a musu zangon shekara yazo qarshe, dan haka ana buk'atar kowa ya fito da nasa sabon sanfirin domin aga bajintar kowa, sallamarsu tayi sai kuma manager da accountant da suka tsaya suka yi wani lissafi sannan suka tashi suma, tana fitowa jakarta kawai ta d'auko ta kama hanya zata fita, dan dama aikinta ba jimawa take ba. Tunda ta fito kowa ke kallonta kamar wacce tayi wani mugun abu, ranta ne ya bace harta tsaya ta fara kallon kowa zata fara zazzaga masifa, sai kuma taga kowa yasha jinin jikinshi saboda ganin zata koma musu Khairat d'in ta asali, lokacin ne ta fahimci dalilin kallon nata, hakan yasa ta saki murmushi a fuskarta sannan ta fara takawa cikin rangwad'a ta tsaya bayan teburin Umar Faruk, duk da yaji alamar akwai mutum a bayanshi, duk da turarenta ya bayyana mishi ita amma baisa ya juyo ya kalleta, cike da tsantsar shagwab'a da bubbuga qafafu Khairat tace "shine ma zaka wani kyaleni ko ka juyo ka kalleni, ni wallahi zanyi hushi da kai." Mamaki ne yasa ya juyo dan ganin dawa take, qara waro ido yayi tare da dage giranshi sama, kasa magana yayi saboda kowa na wajen kallonsu suke, sake shagwab'ewa tayi ta fara kukan sakuwa tace "uhum uhum uhum, wallahi Allah saina fad'awa Mama mana." Kunyar data fara basa ne yasa ya mik'e tsaye yana kallonta cikin mamaki yace "ya dai, me yake damunki ne?" "Gida zan tafi wajen Mamie, shine nazo kamin sumbatata ta ban kwana." "Sumba kuma?" ya fad'a da k'arfi har mutanen suka sake sakar musu ido. Lab'e baki ta sake yi tana "uhum uhum uhum uhum uhum uhum uhum." Zaiyi magana kuma saiya d'an kalli mutanen da wutsiyar ido, ganin yanda hankalin kowa ke kansu yasa ya zura hannu ya janyota yana fad'in "oh mon bébé, meya faru ne waya tab'a min ke?" ya fad'a yana shafar fuskarta. Kamar zata janye hannunta kuma saita goge ido kamar mai hawayen gaske tana magana cikin shagwab'a tace "toni sumbata nake jira." Wasu yawu ya had'iye danshi dai ba zai iya ba kome za tayi, kallonshi tayi ta fahimceshi dan haka ta nuna mutanen tana fad'in "wai kunyarsu kake jine? su d'in fa duka yaranka ne, tunda shugabarsu ma a qarqashinka take." Saida ta d'an d'aga qafafunta ta kai bakinta daidai kunnenshi saboda ya fita tsayi sannan tace "ko ba wannan ne burinka ba? ace Umar Faruk mijin Hajia Khairat." Sai kuma ta sake tsayawa yanda take tana murmushi tana kallon fuskarshi, ganin zai b'ata mata lokaci yasa ta kalli idonshi tace "wato zaka iya yiwa waccen figaggiyar matar taka sumba a waya, amma ni gani gaka ma ba zaka iya ba ko? to bara ka gani." Sake d'aga qafafunta tayi ta daidaita tsawonsu tare da d'ora bakinta akan nashi bakin, ji kake muahhhhh😘 ta sumbaceshi, daga cikin wasu mutanen dake wajen ne sai kuwa suka saka tapi tare da shewa, yayin da Khairat kunyar abinda tayi ta lullub'eta, ficewa tayi ba tare da sun had'a ido ba ta bar wajen, ta jima zaune kafin ta tayar da mota ta tafi, tun tana tunanin dalilin da yasa tayi haka, har dai ta fara sakin murmushi da ba tasan dalilin yinshi ba, wannan ce sumbatarta ta farko, dan ko Raj dake ba musulmi ba bata tab'a yarda ya sumbaceta a baki ba, haka ma su Musa da suka keta mata haddi babu wanda ya damu da bakinta, da wani irin sabon farin ciki daya lullub'e zuciyarta ta isa *marina market score*, siyayya tayi mai yawan gaske kayan abinci da kuma kayan mak'ulashe saboda kanta, a bayan mota aka saka mata daga nan kuma gida ta nufa wajen Mamie. *************** Tunda ta d'ora labb'anta akan nashi ya sandare tare da lumshe ido, ba komai ya tafi dashi ba kamar taushin labb'anta, ga kuma wani sabon k'amshin turare daya baibaye hancinshi, harta fita bai iya zaunawa ba har saida Ishaq ya janyo rigarshi yana dariya yace "sabon shiga kenan, kai yanzu bizou (kiss) ne ya sukurkutar da kai haka? tofa wannan inaga har yanzu ba wani labari tsakaninku ko? dan inaga ranar da kaje bakin boda, tofa sai dai mutanadi makarar da zamu saka gawarka." Duk da ya zauna amma hankalinshi baya jikinshi, sake tab'ashi Ishaq yayi yace "kai, ko dai ka zaucene, sumbata ce fa." A hankali ba tare daya kalleshi ba yace "ya danganta dawa ya sumbaceka, wannan ta dabance Ishaq, ba zaka gane ba." "Wow." ya fad'a tare da dogara hannayenshi akan teburin dake gabanshi ya tusa hannayenshi a cikin sumar kanshi, bakinshi har kunne yayin da hakoranshi suka kasa b'oyuwa, wani irin sanyi ne yake ji yana shigarshi a hankali, zuciyarshi kuma na qara narkuwa akan wani abu da take so sosai, sai dai bai yarda son Khairat bane take. _Zama kayi magana Umariri_😉 **************** Da sauri mai gadi ya bud'e mata k'ofar ta shiga, tun kafin ta fito kuma yaja ya tsaya gabanta yana fara gaisheta tun kafin ta fito, qafafu ta zuro kafin ta qarasa fitowa, "barka da zuwa Hajia, sannunki da zuwa uwargijiyata, 'yar Alhaji da Hajia, 'ya d'aya tilo kuma farin ciki da sanyin idaniyar gidan mai gidanmu, takawarki lafiya yar albarka jikar arzik'i, sannu da zuwa." Hannu ta d'aga masa tana kallonshi tace "baka tab'a min irin wannan kirarin ba, halan da wani abu a qasa?" Kai ya d'an sosa amma baice komai ba, "humm, nasan dama da wani abu, dan banza bata kai zomo kasuwa, ka jira na shiga ciki na fito." Tana fad'a ta wuce shi kuma ya sake rakata da wasu kirarin, saida yaga ta shige yaja baki yayi shiru yana mamaki Hajia Khairat da hijabi, lallai mijin nan mai sa'a ne, kuma da alama zai juyata yanda yake so. Mammie ce zaune a falo ita kad'ai tana kallo, da gudu ta qarasa ta rumgumeta tana fad'in "Mammie na." Rumgumeta tayi itama tana fad'in "lah, Khairat d'ina, ashe kece?" D'ago kanta tayi tana gyara zama tace "nice Mammie, kema baki ganeni ba saboda nasa hijab?" "Ah haba, ni na isa na kasa gane 'yar gudaliyata, kawai dai gani nayi kin qara min kyau da haske." Kumatunta ta kama taja suna dariya tace "kin ganki tsohuwar nan, wato harda haske na qara, bayan duhun da nayi saboda bala'in zafi da cizon sauro." Dariya Mammie tayi cike da zolaya tace "ba wani nan, kinje kin manta dani kina kwasar amarcinki, yanzu zaki ce wai zafi da sauro , kedai sai dai in kin samo min wani d'an gudaliya ne kawai." Fashewa tayi da kukan shagwab'a tana fad'in "lah Mammie, d'an gudaliya fa, tun yanzu? wallahi ba dani ba, Mammie yana da mata fa." "Eh na sani ai, amma ina ruwanki da matarshi? ke daban ita daban." "Humm, Mammie baki sani ba fa, wallahi ni ba sona yake ba ita kawai yake so." Hannu tasa ta rufe mata baki tace "bana so, karna sake jin haka daga bakinki, shiya tab'a fad'a miki baya sonki?" "To Mammie saima ya fad'a, jiya ma fa cemin yayi ba zai tab'a had...." Mammie ta rufe mata baki, kai ta girgiza tace "Khairat, kefa yanzu ba yarinya bace, kamata yayi ace kina rik'e sirrinki, musamman irin wannan sirrin mai tsada, ki sani duk abinda ya faru tsakaninki da mijinki to bai hallata ki fad'eshi koda ga mahaifiyarki bace bare kuma waninta, dan haka bana so na sake ji kinji yar albarka." Hannayenta ta matse sosai tace "naji Mammie ba zai sake ba, kinga yanzu nima na fara sauyawa, ina so na zama 'yar aljanna." Muryar Mamie ce ta katsesu da cewa "nayi hushi dake, tun d'azu nake jiyo muryarki amma kin kasa zuwa inda nake." Yanda take maganar da shagwab'a ne yasa Khairat yin dariya tace "kiyi hak'uri Mamie, ina nan tare da wannan tsohuwar k'awar tawa." Hannaye Mamie ta bud'e alamar Khairat ta taho, abinda Khairat d'in ba tayi tunani bane hakan yasa da mamaki ta tashi ta tafi, tana zuwa Mamie ta rumgumeta sosai a jikinta tana fad'in "nayi kewarki sosai 'yata." "Nima haka Mamie, ina Papa?" ta fad'a tare da tashi daga jikinta. Hannunta ta kamo tace "Papanki ya tashi *Germany* amma yace ba zai jima ba." "Ta'bb, yanzu shine har Papa yayi tafiya ban sani ba? lallai gidan nan kun daina sona." Mamie data qura mata idone tace "Khairat, wannan sabuwar shigar fa?" Saida ta cire hijab d'in tace "wallahi Mamie mahaifiyar Faruk ce tace na dinga rufe jikina, matar tana da kirki gaskiya ga yiwa mutum addu'a a kullum." Duk da Mamie ta gano kuskurenta anan take amma bata nuna ba, murmushi tayi tace "Alhamdulillah, ashe 'yata ta kusa zama salihar mace itama." "Eh Mamie, kuma ma yanzu har karatu na fara, Faruk ke koyar dani, wallahi Mammie baki ji dad'in dake akwai ba idan kana karatu." "Alhamdulillah, ashe yaron ya kusa canza min yarinta ta yanda ba zan ganeta ba nan gaba? to Allah ya mishi albarka, ke kuma Allah ya baki sa'a ya taimakeki a karatunki." "Ameen Mamiena." ta fad'a tana sake rumgumeta. Mamie ce tace "to amma daga ina haka? kina ganin ba kiyi saurin fara fita ba kuwa?" "Mamie daga wajen aiki nake fa, kuma shima na baroshi acan." "Amma kin fad'a masa?" cewar Mammie. "Eh, nace masa zanzo gida." "To ya mutanen gidan, ba wata matsala dai ko? inji Mamie. "Eh to, bana shiga sabgar kowa, amma akwai kishiyar mamanshi tana da zakewa, amma ba komai zan gyara mata zama." "A'a." "A'a." Mammie da Mamie suka had'a baki a tare ,Mamie ce ta d'ora da "haba yarinyar kirki, 'yar aljanna, aiba girmanki bane wannan, ki rabu da ita kawai, kinji?" "Shikenan." tayi maganar tana gyara zama. Su kuma kallon juna sukayi saboda mamakin canzawar Khairat, magana d'aya tak Khairat tace to ko shikenan, tab', dole ma mu nemi yaron nan mu qara gode masa, saboda wannan namijin k'ok'ari da yayi, a kwana uku rak ya gyara musu 'yarsu cewar Mamie. Saude da Biba da kuma Baraka masu aikinsu ne suka fito suka gaisheta, ba yabo ba fallasa ta amsa suka koma ciki ana mamakin Hajia Khairat. Mamie ce ta kira Papa ta bashi Khairat d'in suka gaisa, anan kuma yake fad'a mata lallai lallai ta shirya tare da mijinta zasu zo Germany suma nan da kwana biyar tare dasu Mammie da Mamie, dad'i taji sosai saboda zata keta hazo, anan ta wuni gida sam tama manta da wani gidan aurenta, ji take kamar ta tsaya a inda take ba tare data koma waccen kurkukun ba. ****************** Yamma sosai Mammie ta iza qeyarta zuwa gidanta, haka ta tafi ba dan rai naso ba, tana zuwa ana kiran sallah dan haka koda ta shiga gidan wasu na alwala wasu sun tafi masallaci, sai dai ganin moton Umar Faruk ya tabbatar mata ya dawo, tana shiga ta tub'e ta shiga wanka sai dai bata jima ba ta fito saboda yanzu tana son yin sallah akan lokaci, cikin gaggawa ta shirya amma saboda qananan kaya ne saita dora doguwar riga a sama sannan ta saka hijab, harta kammala sallah bai shigo ba har qaramar kwalliya tayi sannan ta d'auki hula (hana sallah) ta zatsa akai, wata k'atuwar chocolat ta d'auka ta d'auka ta fara sha ga kuma k'atuwar loli pop d'inta a hannu, abin sauraronta ta dasa a kunne ta fara biyar waqar Zaho mai taken *Allo* tare da rausaya. Da sallama tare da d'aga labulen ya shigo, baiyi mamaki ba saima birgeshi da tayi , bak'in dogon wando da farar riga mai hannuwa sai bak'ar hula itama, kamar ita ta rera waqar ga kuma yanda take tafiyar da kowace gab'a ta jikinta cikin qwarewa, shiga yayi ya zauna dan sunyi ido takwas takwas dashi amma bata nuna ta damu ba, a cikin takon rawa ta bud'a jakarta ta d'auki makulli ta mik"o masa ya karb'a yana kallonta da mamaki, ta jima kafin tace "akwai kaya a mota a deb'osu." Duk tana maganar ne tana girgiza rawarta, hararanta yayi da fad'in "waye zai d'auko?" Nunashi tayi da hannu tana ci gaba da abinda take , cilla mkullin yayi a saman gado harya kusan bugeta, cire abin sauraron tayi tana kallonshi tace "ni kake so na kwaso to?" "Eh, saboda ke kika siyo." D'aga kafad'u tayi alamar ba matsala, fita tayi daga d'akin ta zura takalmi harta kai k'ofar fita daga kewayen yayi saurin fitowa yace "ke." Duk da taji amma bata saurareshi ba, wucewa tayi ta kuma yi sa'ar ganin Aliyu da Usman sun shigo, da sauri ta mik'a musu makullin tana fad'in "yawwa karb'i nan, akwai kaya a cikin mota ku fito dasu saiku shiga dasu madafar gidan nan." Suna karb'a suka fita ita kuma kawai tasa kai ta shiga d'akin Mama dan ganin jikinta, duk da saurin da yake ya rik'ota tuni ta shige, dafe kai yayi yace "duk kaine ka jawo Umar Faruk, da kayi abinda tace daba haka ba." Mama na zaune duka yaranta suka ga ta shigo, gaisheta sukayi qasa qasa kamar yanda ba wanda ta amsa ma, zaune tayi kad'an tace "Mama ya jikinki?" "Da sauk'i sosai 'yata, ya kike?" "To yayi kyau, kinsha magani?" "Eh nasha." Mama ta fad'a tunda taga ba kowace magana take amsawa ba. Tashi kawai tayi ta kalli Ruk'ayya dake koyar da k'annanta karatu tace "akwai kaya za'a shigo dasu." "Mama saida safe, Allah qara lafiya." "Ameen 'yata saida safe." Tan a fitowa suka ci karo da Umar Faruk dake sauraronsu, wucewa kawai tayi a lokacin kuma su Aliyu suka fara shigowa da kayan, saida suka gama duka sannan Aliyu yayi sallama ya bawa Umar Faruk makullin, mutanen gidan ne suka fito suna tambayar ina za'a da kayan, Zeinab aka aika ta tambayo tana fitowa ta fad'a musu wai nasu ne, kowa dai yayi farin ciki amma banda Baba. Umar Faruk yasa aka kira masa, bayan ya fito yace dashi da ita su sameshi d'akinshi, ba b'ata lokaci suka hallara bayan yasa tasa dogon hijab, zaune suke gaban Baba ya fara da " 'yata, munga abin arzik'i da kika mana kuma mun gode, amma sai nake ganin da kinbar bawa kanki wahala haka, tunda cikin ikon Allah muna ci muna sha kuma muna rayuwa cikin rufin asiri, dan haka ba buk'atar ki dinga bawa kanki wahala." Kallon Baba tayi ido tsaye tace "Baba, karka wahalar da kanka, in har nima d'aya ce daga cikin 'ya'yanka, to inada damar da zan taimaka maka, bawai inayi bane saboda wani abu, haka kawai nake ganin ya dace na taimakawa duk wanda yake tare dani, a shekarunka mune ya kamata ace muna ciyar da kai da d'aukar duk wata d'awainiyarka, dan haka kamin addu'a kawai bawai magana akan na daina ba, dan hakan a cikin jinina yake zaiyi yuwa na daina." Tunda ta fara magana Umar Faruk ya saki baki yana kallonta, mamaki yake irin yanda take girmama iyayenshi kamar dai ta sansu, yana mamaki shin dama haka hallayarta take ko kuwa dai wani abu take nufi, muryar Baba ce ta katseshi da yace "to yata Allah ya miki albarka, amma duk da haka dai ki bari, tunda kinga dama bani bane nake ciyar da gidan nan a yanzu, Umar Faruk ne da yayanshi Abbakar." "Baba, ai nima 'yarka ce yanzu, koba komai ka haifeni, bugu da qari kuma kuma ni matar Faruk ce, ina da damar da zai iya taimakawa mijina." Tana fad'a tabar d'akin ba tare data bi ta kansu ba, shima dai bayanta yabi dan kawai ji yake kamar tana masa nisa ne a kowane tako, suna shiga ta cire hijab d'in ta d'auko littafinta ta zauna kusa da Faruk, "Dan Allah ka biya min wani." ta fad'a a tausashe. "Khairat." Umar Faruk ya kira sunanta yana kallon idonta yayin da zuciyarsa ke azalzalarsa Alan sonta. Shiru tayi tana kallonshi itama amma kawai saiya basar daga abinda yaso fad'a mata, dan a ganinshi ba abu bane mai yiwuwa, sam ba zai lamunci hakan ba. Kawai karatun sukayi tare da fara karanta husnul muslim saboda ta iya addu'o'i shima sosai ta maida hankalinta akai har suka gama, sallah isha'i ce ta fitar dashi bayan ya dawo kuma Ruk'ayya ta kawo abinci, sam Khairat bata ci ba sai karatunta daya d'auke mata hankali. *Me kuka ce fan's, ya fad'i abinda ke ransa ko yayi shiru.*??? 💃💃💃💃💃💃💃 _Na gode 'yan uwa, naji dad'in addu'arku tare da fatan alkairi, ku sani Sameera na yinku sosai, kuma sister's d'ina ma sunce suna godiya._ _Ban d'auka zaku samu Jihadi ba a yau, amma farin cikin da nake ciki yasa na qoqarta na qarasa muku typing d'in nan, wannan page baki d'aya na bawa k'annaina ita, *Ameera* da *Haleema*, wallahi ina sonku 'yan uwana abin alfaharina._ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 2⃣8⃣ Shima wani littafi ya bud'a ya fara karantawa, ya jima sosai kafin ya aje ya tashi yayi wanka ya fito ya fara shiryawa, ganin zai saka kaya yasa Khairat sauka daga kan gadon zata fita, tana saukowa tari gabanta yana mata wani irin kallo yana warware rigar dake hannunshi zai saka, giftashi tayi zata wuce ya sake tareta, numfashi ta sauke ta kalleshi fuska ba annuri tace "meye matsalar?" Saida yaja wani dogon numfashin kafin yace "d'azu kin sumbaceni, me yasa?" "Me yasa baka tambaya ba tun acan sai yanzu?" "Nan ne ya kamata muyi maganar." "To idan ka gama saka kayan na dawo sai muyi magana." Zata fice ya janyo hannunta, wani kallo da sukawa junansu lokaci d'aya kuma Khairat ta d'auke idonta, cikin kissa da mazantaka Umar Faruk ya rumgumo kugunta ya had'a da nashi yasa hannunshi d'aya ya cire hular dake kanta ya fara wasa da gashinta, kafeta yayi da ido akan yasa ta kasa kallonshi, qirjinshi kawai take kallo gabanta na faduwa sai dai kuma shima tana jin yanda zuciyarshi ke bugawa saboda hannunta na kan saitin zuciyarshi, a hankali ya sunkuyo da kanshi ya kalli fuskarta, ganin tayi quri da ido tana kallon qirjinshi yasa ya hura mata iska a ido, da sauri ta lumshesu kai tsaye kuma ta bud'e ta kalleshi, saida ta had'e yawu masu daci sannan tace "me ka keyi haka, ka manta meka fad'a jiya?" Wani shu'umin murmushi yayi yace "ke kika tab'oni ai, akan me kika sumbaceni? dan haka ramawa zanyi." A k'arfi ta kwaci kanta tayi baya ta nunashi da hannu tana fad'in "karma ka fara wallahi, karka dauka nayi ne dan jin dad'i, kawai ni nayi ne saboda mutanen dake wurin, idan kuma kace zaka tab'ani harka sumbaceni, wallahi...." "Ba sai kin qarasa ba." ya katseta da sauri. D'orawa yayi da "meye na rantsuwa, karki wahalar da kanki, kece zaki kwana a ciki danni ina da mata, yanzu haka ma wajenta zanje." Wani dammm, taji gabanta yayi amma saita dake tace "to ina ruwana da matarka ni, kuma wallahi kaje ka kai mata kwana na, to ban yafe ba." Busehewa yayi da dariya yace "zaki yafe, tunda ke kika ja komai." Duk da ganin ya zame towel d'in jikinshi sai qaramin wandon dake jikinshi baisa ta daina fad'ar abinda take fad'a ba ta rufe ido sai masifa take "wallahi ba zan yafe ba ko mutuwa za kayi, haka kawai ka mayar dani wata ballagaza kana cin amanata, toni ba sakarya bace wallahi, kuma kaje daga kai har matarka zaku shigo hannuna, aikin banza kawai kace waini na janyo komai, ba wani nan dama kana so kawai baka samu damar tafiya bane inda za'a baka." Yana cikin d'aure belt d'inshi ya kalleta yace "kema ai nasan kinji wani abu a lokacin, watak'ila har yanzu kina jin shauk'i tunda mutum ce ke, sai dai ko in kina da k'arancin isassar lafiya." "Kuutt, ni d'in ce ma banda lafiya? wallahi lafiyata k'alau ni, sai dai in kaine baka da lafiyar." "Ni ai dama bance miki bana da ba, ke dai nake tunanin ba kyada ita." "Wallahi ina so da." ta fad'a tana juya baki. "Kin tabbatar?" "Eh." nan ma tayi maganar tana zabga masa harara. Matsowa yayi kusanta yace "kenan kema kinji wani abu d'azu." "A'a, a'a wallahi ni babu abinda naji." Saida ya b'alla botir d'in rigarshi yace "to in kina so na yarda babu abinda ki kaji, ki bani dama na bincika da kaina saina gane, amma in ba haka ba to qarya kika fad'a kina b'oye wani abu a ranki." Babbar yatsarta tasa a bakinta tana kallonshi tana tunani, fito da yatsar tayi tace "ka rantse babu cuta a ciki." "Cutar me kuma? gani gaki fa, kuma a gabanki za ayi gwajin." "Na amince to." ta fad'a da gyara tsayuwarta. Matsowa ya sakeyi kusanta yana fad'in "ok, bani minti d'aya tak ya isa na gano gaskiyar komai." Kafin tayi magana taji bakin Umar Faruk a nata bakin, "ahhhh." kuma sai tayi shiru tare da lumshe ido. Shi kanshi ji yake kamar bashi ba dan bai shirya yin hakan ba, zuciyarshi kawai yaji tana izashi akan yin komai, bayanta yake shafa a hankali yana latsawa har lokacin daya zura tafikan hannayenshi ta cikin rigarta, bras dake jikinta ya balle ba tare daya cireta ba yakai hannayenshi a mamanta, jin yanda yake shafasu ne yasa Khairat qamqame Umar Faruk sosai tare da turo masa gabanta, shi kanshi sake fita hayyacinshi yayi yanda yaji gaban tsam tsam dashi kamar an hura mata iska, wani numfarfashi yake saukewa yana ji yana so yakai wata gab'a da baisan ko zai iya jarumtar hakan ba. _Wannan abu yafi qarfina_🏃‍♀🏃‍♀🏃‍♀ Yanda ta qamqameshi tare da cabko harshenshi ta fara tsutsa yasa gaba d'aya ya rasa wanene shi me kuma yake yi, biye mata yayi suka fad'a kan gado, harya fara shirin rabata da rigarta sai kuma ya tuna minti d'aya ne gareshi, a zabure ya tashi tsaye yana gyara jikinsa da saisaita nutsuwarsa, Khairat ma a firgice ta tashi zaune tana ganin an fara cire mab'allan rigarta tayi saurin rufe qirjinta tare da duk'e kanta qasa, kasa had'a ido sukayi harya d'aga qafafunshi ya bar gidan. Yana fita ta shafi gashin kanta tace "oh Allah na." Kasa motsawa tayi daga wajen tana tunani har bacci ya fara fizgarta, daga nan kuma ta kwanta sai bacci. *************** Yana fita daga nan siyayya yayi ta yan kayan motsa baki ya wuce gidansu Zuby, dan tun ranar daya rabata da budurcinta bai sake komawa ba, bai samu tanti a gidan ba sai Zuby kad'ai, yayi mamakin rashin tanti a gida a wannan lokacin amma ya zaiyi, da gudu Zuby ta qaraso ta rumgumeshi, shima rumgumeta yayi dan dama a tafashe yake, amma abin mamaki shine, abinda yaso yaji bashi yaji ba, ga dukkan alama ba tayi wanka ba kodan bata san da zuwanshi bane oho, a hankali ya raba jikinta da nashi yana murmushin yak'e, "sannu da zuwa yah Umar, shine ko ka sanar dani kana zuwa?" "Ina so na miki bazata ne." ya fad'a suna nufa d'akin da aka ware mata. Tsaye yayi yana kallon d'akin ganinshi a yamutse, da hannu ya nuna mata yace "meye haka Zubeid? na d'auka nan shine muhallinki." "Eh yah Umar, ai an fara tattare min kayana ne gobe za'a kaisu can gida ayi gyara d'akin, jibi kuma saina tare." ta k'arashe maganar da jin kunya. Ya karb'i uzurinta hakan yasa ya bata ledar hannunshi yana fad'in "ya jikinki." "Kai yah Umar, yayi sauk'i fa." ta fad'a cikin rufe fuska. Hannunta ya kamo ya sake rumgumeta a jikinshi cikin sanyayen muryar da baima san yana da ita ba yace "kinyi kewata kuwa?" Cike da jin kunya tace "eh mana yah Umar." "Kenan....zaki sake...bani wani abu ne?" Cikin tsoro ta bud'e baki tace "yah Umar, ba yanzu ba gaskiya, ka bari saina dawo gidanka." Cikin shagwab'ar da tunda yake a rayuwa bai tab'a irinta ba yace "kenan tsoro kike ji? zafi ke akwai ne har yanzu?" "Eh to yah Umar, akwai zafi kuma akwai wahala, amma dai ba sosai ba." Sakinta yayi yace "shikenan to na hak'ura harki shigo hannuna." Kafin tayi wata magana yace "ni zan koma gida, ki gaida tanti idan ta dawo." "Yah ko zama ba kayi ba fa?" "Karki damu, ki gaisheta kawai." Sallama sukayi ya fita, fitarshi kuma tanti ta tsinkayeshi sai dai shi bai ganta ba, tun daga soron gidan ta fara kiran "Zuby, Zuby, ke kina ina fito fad'a min waccen mara mutuncin me yazo ya miki, injin dai baki yarda dashi ba? dan na lura yaron nan so yake saina mashi rashin mutunci." Zuby dake tsaye tana kallonta tare da sauraronta ne tace "kai Mama, bafa abinda ya kawoshi kenan ba, kawai yazo ganina ne." "Aina d'auka iskancin ne ya kawoshi." Dorawa tayi da "kinga abinda nake fad'a miki ko, tunda ki kayi aure nake fad'a miki ki saba da yawon wanka amma ba kyaji, yanzu gashi ya miki zuwan bazata, ke ko kunya baki ji ba?" Ganin zata maida bala'in a kanta yasa ta shigewarta d'akin ta d'auki ledar tsirenta ta fara ci, shigowa tayi tana ganinta ta fizge ledar tana fad'in "shegiya matsiyaciya , wato ke kad'ai zaki ci saboda baki da mutunci." Fita tayi da ledar Zuby kuma ta bita tana fad'in "wai Mama me yake damunki ne, to kema ke kad'ai zaki ci, dan Allah ki bani kayana." _Ganin uwa da d'iya zasu botsare akan ledar tsire yasa na fito,danni ba wajen kuka na bane, da kaza ce😁 da sunga sabon tashin hankali *amma fa shima ina sonshi, musamman na madugu mai nama*._😂maman Dady. ************* Ishaq ya samu a kofar gida dan haka ya tsaya suka gaisa, "kaga mijin mace biyu, matashin yaro mai sa'a a duniya, wanda ya fara da zankad'a zankad"an mata a lokaci guda, kai Umar Faruk ina fatan Allah ya bani irin taka." "Idan ka gama shiriritar ni zan shiga ciki dan bana da lokacinka." "Humm, ba wata shiririta, kai dai kawai kace za kaje ne tana jiranka, aini na gama sanin komai wallahi." Kashe motan yayi yace "me kenan?" "Kuma, ka manta dazu a ma'aikata kun nuna mana sanfiri a fili mun gani." Duka ya kai masa ya goce yana fad'in "kaifa d'an iska ne wallahi, to an fad'a maka sone ya kawo hakan? kawai tayi ne saboda ire irenku 'yan gulma." "Kaiba wani nan wallahi, kawai kuna cikin shauk'i ne." "To naji, saime kuma?" Dariya yayi yace "halan daga wajen Zuby kake?" "Eh, daga can nake, da wata matsala ne?" Rik'e kan mashin d'inshi yayi yace "kaii , amma fa Umar Faruk kana more rayuwa wallahi, ace ko ina jin dad'i ne ya baibayeka, ka fita daga gida kabar santaleliyar lace kaje wajen wata santaleliyar, gashi kuma zaka sake shiga ciki waje wata zankad'aziyar." "Allah ya shiryaka Ishaq, wallahi kayi sauri kayi aure, inba haka ba zaka mutu." "Miye zai kasheni to?" "Ba zaka sani ba inba matakin ka kai ba." Tayar da mashin d'in yayi zai wuce cikin gida Ishaq yace "za kasha mamaki idan na fad'a maka wacce nake so." Hararanshi yayi yace "ya wuce kace Ruk'ayya kake so, banza kawai dake tsoron fad'an abinda ke ransa." Da k'arfi ya rik'e moton yana fad'in "waye ke tsoro d'in? naga ai bani kad'ai bane ya kasa fad'a, kaima ka kasa fad'a." Sake kashe moton yayi yace "wa wai? ni kake nufi? ai kasan ni tuni na wuce wajen wallahi." "Qarya kake, domin soyayyarka ta gaskiya yanzu ne ta fara." "Me yasa kake sha'awar mayar dani baya, kasan sau nawa ina fad'awa Zuby kalmar so? yafi sau dubu." Sosai Ishaq ya kalleshi tare da nuna ba wasa a abinda zai fad'a yace "saboda ba ainihin sonta kake ba, Khairat itace wacce zuciyarka ta kamu da sonta, watak'ila ka fahimci hakan, ko kuma ka sani kana take sanin ne, amma ka sani tun fil'azal dama Zuby ba sonta kake ba, kawai sone na 'yan uwantaka da kuma shak'uwa." "Kasan me kake fad'a? kaifa kasan Zuby da Khairat, kuma kasan matsayin kowace a zuciyata, to me yasa kake so ka nuna bana qaunar Zuby?" Rumgume hannayenshi yace "sanin haka ma yasa nace maka Khairat itace masoyiyar zuciyarka, amma ba Zuby ba, kayi tunani hakan haka da kanka zaka fahimci gaskiyar da kake b'oyewa, kayi tunani da kyau zuciyarka zata bayyana maka alamomin a fili wanda take fad'awa a duk lokacin da tayi tozali da Khairat." Ajiyar zuciya ya sauke yace "haka dai kace, ni saida safe." Dariya yayi shi kuma yace "hakane ma." *************** Saida ya shiga yaga Baba ya mishi sallama haka ma d'akin Mama sannan ya wuce d'akin, ganinta kwance tana bacci yasa ya cire kayan jikinshi ya watsa ruwa ya sauya kayan bacci sannan ya zauna makwacinshi, remonte ya dauka ya kunna qira'a ya fara biya. Sautin k'ira'ar daya kunnane yasa ta farka, saida ta murje ido sannan ta zuro da qafafunta ta sauko daga kan gadon duk yana kallonta, tana kallonshi taji haushi ya lullubeta wato ya dawo daga wajen matarshi, hararanshi tayi ta bud'a ma'ajiyar kayanta ta d'auko qaramin wando iya cinya da rigarshi hannayen sun d'an sauko zuwa damtse, yana kallo ta cire rigarta sai bras d'in daya b'alle mata ko gyarawa ba tayi ba, juyowa tayi sai kuwa sukayi ido takwas takwas, hararanshi tayi ta juya ta zage bras d'in ta d'auki rigar baccin ta saka, juyawa tayi ta sake kallonshi tace "zan saka wando fa." "Miye nawa a ciki to?" ya fad'a yana d'auke kai daga barin kallonta. "Ka rufe idonka to." ta fad'a a kaurare. "Nak'i d'in, idan zaki saka ki saka, kuma ma ai naga ke ba lafiya ne dake ba." ya fad'a kamar bashi ke maganar ba. Da hannu a nunashi tace "kai, karka qara cemin bana da lafiya, Allah ranka zai b'ace." "An fad'a d'in, inga b'acin ran dan Allah." "To ka sake cemin banda lafiya ka gani." "To kina da lafiyar ne? aini ba zan tabbatar ba har sai jarabaki na gani." "Hahahahaha, kaji yaro, waini zai mayar shashasha mahaukaciya, to an fad'a maka ni d'in yar shekara goma ce da zaka mayar dani abar wasarka, to bari kaji, inma wani abu kake nema a wajena ka sani ba zaka samu ba, ka jira amaryarka tazo sai kuje ku cinye kanku, tunda naga ita d'in marar aji ce da har zata bada kanta tun bata tare ba." Maida kanshi yayi ça tv yace "kedai kiyi fatan kar Umar Faruk ya buk'aceki, dan hakan na faruwa to ki sani kin zama sorry." "Dan Allah Faruk ka buk'aceni, ni kuma a lokacin zan nuna maka nawa d'anyan kan." "To waima me kake tunanin zaka min? tausheni ta k'arfi kamin fyad'e." Saida ya kalleta yace "kina ganin ba zan iya bane?" Cike da raini tace "hmm, jarumtarka bata kai can ba." Tana fad'a ta juya ta fara zuge dogon wandonta, bata kai ga cirewa ba taji an hankad'ata saman gadon ta fad'a, kafin taga wanda yayi aika aikar kuma aka tausheta , duk da dai ta gane Umar Faruk ne amma bata fahimci yanayinshi ba, had'e hannayenta yayi da katifar ya taushe tare da sakar mata gaba d'aya nauyinshi, taushe mata qafafu yayi da nashi qafafu sannan ya had'a goshinsu wuri d'aya yana kallon qwayar idonta, yunk'urawa tayi da nufin ta tashi amma taji ko matsawa ta kasa yi dan ba qaramar matsa ya mata ba, bata san lokacin da hawaye suka zubo mata ba suka fara gangarowa ta kunnuwanta, da qyar take fitar da numfashi sama sama ga zuciyarta dake barazanar fitowa waje, tausar daya mata yasa yake iya jiyo bugawar da zuciyarta keyi, cikin muryar kuka tace, "Dan Allah Faruk ka d'agani, wallahi ni ba dakai nake ba, ina jin tsoron abinda za'a aikata, zaka iya jimin ciwo kamar yanda suma suka min." Wani mugun tausayinta ne ya rufeshi dan take qwaqwalwarshi ta hasko mashi photonta kwance a gadon asibiti bata san inda kanta yake ba, basarwa yayi ya mata kallon ki shiga hankalinki sannan yace "wannan sanfiri ne na nuna miki, idan kika qara qalubalantar mazantaka ta, to zan wuce inda bakya zato kuma nayi kaca kaca dake." Da sauri tace "wallahi ba zan qara ba, wanda nayi ma na tuba." D'agata yayi ya koma mazauninshi yana fad'in "sai tsoron tsiya amma kuma ba hus, hada wani wai zaka jimin ciwo, ko ciwon me zanji ma wacce ke a bud...." Sai kuma yayi shiru dan yasan ba lallai maganar ta mata dad'in ji ba, ba abinda bata jiba hakan yasa ta share qwallanta tace "eh naji, nasan idan ka kusanceni ba zan galabaita ba, amma kuma nasan dole zansan ka shigeni, saboda na yarda da kaina, kuma nasan cika bakin ba zai rasa nasaba da waccen figaggiyar matar taka ba, ita dake budurwa ai banga kayi sammakon zuwa kai mata d'auki ba." Saida ta sauke numfashi sannan tace "wallahi ka sake cin zarafin matsayina saina had'aka da mahaifinka ya shiga tsakaninmu." Bata damu dashi ba ta zage wandon ta saka na bacci sannan ta kwanta, tunowa da addu'a yasa ta tashi ta kalleshi tace "ka taimaka ka koya min addu'ar kwanciya bacci." A wulak'ance ya kalleta tare da harara, itama hararar ta banka masa had'e da juya baki , tasowa yayi yazo kan gadon ita kuma tana ganinshi ta wuntsila ta sauka, ta kan gadon ya taka ya ritsata saboda bata da hanyar bi, hannu ya kai zai shak'o bakinta ita kuma tasa hannu ta rufe bakin tana fad'in "na tuba, wallahi mantawa nayi ba zan sake ba." Kunnenta ya kama sosai ya murd'e yana fad'in "zaki koma kenan in dai har kina mantawa." "A'a wallahi, a'a ba zan sake ba, na shiga uku kunnena , dan Allah kayi hak'uri kunnena zai cire, dan Allah Faruk kunnena." Duk tana maganar ne tana tsalle tsalle da yarfa hannaye ya saketa , "sai kinyi alk'awarin ba zaki sa...." "Nayi nayi, wallahi nayi, ba zan sake ba." ta fad'a tun bai qarasa ba. Sakinta yayi ya sake kafeta da ido yace "me sunana?" "Faruk, fa...Umar Faruk....Umar Faruk sunaka." Da k'arfi ya bugi bangon dake bayanta yace "sunana kenan na yanka, amma ba sunan daya kamata ki kirani dashi ba kenan, ina so naji sabon sunana." Kallon gefenshi tayi tana sharb'ar majina😁irinta ansha kukan nan ta fara girgiza kai tana fad'in "dan Allah ka bari zanyi tunani akai." "Me? sunan ne sai kinyi tunani? zan zubar miki da hak'ora ma." Ya fad'a kamar zai kai mata mazga, dafe kai tayi ta durk'ushe, "tashi tashi." ya fad'a yana mata alama da hannu. Tsaye ta mik'e duk tayi kalar tausayi sannan yace "ina jinki." "Malam." ta fad'a kamar zata fashe da wani kukan. "Um um, bashi nake so ba." Gashinta dake kwance kan wuyanta ta kama tana wasa dashi tana ta rarraba ido, can ta tuna ta kalleshi cikin lab'e baki tace "baby." Wata shegiyar dariya Umar faruk ya kece da ita kafin yace "baby? ki aje wannan sunan har ranar da kika shirya d'aukata a matsayin mijinki, amma ba yanzu ba." Hannunta ya janyo ya zaunar da ita a inda ta tashi yaja zanin rufa ya rufa mata sannan yace ta d'aga hannayenta suyi addu'a, haka sukayi har suka gama sannan ta shafa ta kwanta, kallonshi tayi tana mamakin izzarshi da kwarjini, ko ba tayi niyyar abu ba inda ya canza yanayinshi to dole take yi, tunawa tayi da sak'on Papa hakan yasa tace, "Ka shirya inji Papa, nan da kwana biyar za muje Germany." Kallonta yayi yace "Germany kuma? wajen me? kuma dole sai dani?" "Haka dai yace, wai tarone mai mahimmanci." "Kiyi hak'uri, gaskiya bana jin zanje." "Me yasa?" ta fad'a tana tashi zaune. "Jibi Zubeida zata tare, kinga kuwa za'a shiga hakk'inta." Rudududu, 'yan cikinta suka ya mutsa , da k'arfi tace "tariya kuma?" "Eh, da matsala ne?" A hassale ta sauko daga kan gadon ta fara nunashi da yatsa tana fad'in "..... _Me kuke tunanin za tace_? _Shin ya kamata ya bisu su tafi?_ *Kuyi hak'uri da wannan masoyana.* 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 2⃣9⃣ "Anya Faruk zaka iya zama shugaba mai adalci kuwa, waini meka d'aukeni ne? dabba ko marar anfani? ace matarka zata tare amma ni na kasa sani sai tana jibi zuwa, shima kuma bawai ka fad'a min ne ba a'a maganar dana d'auko ce tasa ka fad'a min, to wallahi ba zan yarda da wani wulak'ancin ba, kai in banda ma k'addara nida nake so na auri wanda zaimin alk'awarin ba zai tab'a min kishiya ba, sai gashi nazo na aureka, amma kuma har kake kokarin wulak'antani akan wata figaggiya, to ba zai yiwu ba wallahi, gari na wayewa zanje na samu Baba na fad'a masa duk abinda kake, na fad'a masa a rage maka nauyi d'aya dan ba zaka iya zama mijin mace biyu ba, jarumtarka bata kai can...." Shiru tayi saboda hararar daya watso mata, kallonta yake bako qyabtawa ita kuma tace "ko kasheni za kayi saina fad'a, tunda abun rainin wayo ne." Shi fa harga Allah ba wai yaki amincewa bane saboda Zuby, kawai dai baya so da wuri haka ace ya fita qasar waje kuma tare da ita, yasan zaisha maganganu da tsirfa iri iri, yafi so idan Allah ya hore masa nashi na kanshi, saiya d'auketasu keta hazo a duk inda suke so, amma ba irin haka ba kuma daya zama tarone ba wani biki ko zumunci ba, to amma ya zaiyi tunda tana barazanar fad'awa Baba, bari ya mata abinda take so kawai tunda dai laifinshi ne da bai fad'a mata ba. Shima tasowa yayi ya tsaya gabanta tare da sakin fuska ya kamo hannunta yace "me kike so nayi Baby?" Hararan wasa ta wurga masa tare da turo baki gaba tace "wacece babyn? ka nemi babynka ma tun wuri. "To naji zan nema idan lokaci yayi, yanzu fad'a min me kike so nayi da zai goge laifina?" "Sai dai in zaka yarda ka biyoni muje." ta fad'a tana d'an rausayawa. "Idan nayi haka ba zaki fad'awa Baba komai ba?" "Ba zan fad'a ba." "To na yarda za muje, amma ba zan wuce kwana biyu ba zuwa uku." "Na yarda nima." Juyawa yayi zai kwanta tace "Faruk." Juyowa yayi ya kalleta "na lura kamar baka san kusantar ahlina da kuma dukiyarmu, dan tun ranar da akace min anbaka gida da mota amma kak'i karb'a na fahimci hakan, amma ka sani iyayena ba k'ananan mutane bane da zasuyi abu kuma su goranta , haka nima duk wanda taimaka to bana iya tuna koda fuskarshi bare na tuna me nayi masa, ka saki jikinka ka babu abinda zai faru, ka d'auka kamar kaine ka biya mana kud'in jirgi, sannan kasa a ranka kamar zaka tafi cin amarci ne da uwar gidanka." Murmushi kawai ya sakar mata ya kwanta akan kujerarshi yana qara gyara kwanciya, ganin sai juye juye yake yasa ta taka har gabanshi cike da kissa ta kamo hannunshi ta tako dashi har gaban gado ta zaunar dashi, kwantar dashi tayi ta dora kanshi akan pillow kamar jariri taja zanin rufa ta rufe masa rabin jiki, haurawa tayi ta kanshi ta kwanta gefe itama taja zanin ta rufa, kallon juna suke amma ita ta rufe idonta, tunani ne take indai har kishiyarta zata tare jibi a maimakon wata biyu da akace, tofa ba zai rasa nasaba da ita ba, in kuwa hakane ya zama dole ta tashi tsaye koda bata samu soyayyar Umar Faruk ba, to ta samu koda tunaninsa ta yanda zata addabeshi, kuma ba zata samu hakan ba harsai ta kusanta kanta dashi. A hankali ta bud'a idonta sai kuwa taga ashe shima idonshi na kanta, ji yake kamar ya dinga tsotsar bakinta harya gaji da kanshi, murmushi ta masa tare da dora hannunta a bayanshi ta qara had'a jikinta da nashi, daga haka kuma bacci ya d'auketa, yayin da tabar Umariri ido bud'e abinda duniya ya isheshi, had'e cinyoyinshi kawai yake saboda ji yake kamar wani abu zai b'illo daga nan😂, saida yaga tayi nisa a bacci ya sake tausa kanta a qirjinshi yana shinshinar wani daddad'an k'amshin tuffa ga numfashinta dake fitar da k'amshin kanunfari, sannan k'amshin jikinta kuma ya rasa dame zai misaltashi ma kamar sabulu kamar turare, kai koma dai miye yana da dad'in shak'a da kwantar da hankali da kuma tayar da hankalin.....jijiya." _Kun dai gane ai_😉 Ko alama bai rintsa da idonshi ba, daf da a kira sallah asuba Umar Faruk yaji kamar zai mutu saboda bala'in abinda yake ji, ga mararshi data d'aure take ciwo ga azababben zabbab'in daya rufeshi, sake matse Khairat yayi sosai a jikinshi ya d'ago da kanta ya fara sumbatar fuskarta, a tsorace ta zabura zata mike yayi saurin sake damk'arta ya had'e bakinsu, tsotsar bakinta yake sosai yaki bata damar da zata 'kwaci kanta, dukanshi ta fara yi tana ihu sai dai ba'a jinta, abu d'aya ne ke mata yawo a tunani shine su Musa, shi kuma mafita kawai yake nema, wata cakuma daya kaiwa mamanta yasa ta zabura tare da k'amewa, dauke bakinshi yayi daga bakinta ya saukeshi kan d'aya daga mamanta ya fara tsotsa d'aya hannun kuma yana murzar d'ayan, mafita d'aya ta rage mata shine tayi ihu , ai kuwa zage damtse tayi ta rumtuma wata qara da shi kanshi saida ya tsorata, a wahalce ya dago da jajayen idanunshi cike da rauni ya tallabota gaba d'aya ya had'ata da jikinshi ya kai bakinshi cikin kunnenta yace, "Dan Allah Khairat, ki taimaka min, kefa kika tab'oni." "Ni, ni dai ka sakeni dan Allah." ta fad'a tana shirin k'watar kanta. Sake kai bakinshi yayi ga mamanta yana tsutsa ita kuma tasa hannaye tana ture kanshi da k'arfi, bille bille take sosai yanda dole ba yanda ya iya daya rabu da ita ya kife a wajen ya kwanta, ruf da ciki yayi ya tusa kanshi a pillow yana sauke numfashin wahala, tana ganin haka ta sauka daga kan gadon tana fad'in "jaraba kawai, kaine fa harda cika baki wai kai ba zaka had'a jikinka da nawa ba, kenan raina min hankali za kayi." Hannu ta dora kan qirjinta ta tab'a taji yanda suka fara mata zafi saboda bala'in matsar da suka sha, tsaki tayi kawai ta wuce douche lokacin kuma an fara kiran sallah. Har tayi wanka ta fito yana yanda yake , shiryawa tayi cikin doguwar riga ta shinfida sallaya sannan ta kai hannu ta daddab'a qafarsa tana cewa "ka tashi fa an kusa tayar da sallah." A hassale ya tashi zaune yana fad'in "karki sake tab'ani kinji na fad'a miki, muguwa mai bak'in hali." Yana fad'a ya fita ya bar dakin cikin k'arfin hali ba dan ko yana ganin inda yake takawa ba, da qyar yayi wanka shima ya fito amma saboda bala'in abinda yake ji yasa ya kasa saka kaya a jikinshi ya koma ya kwanta, abin ya dameshi sosai kuma baisan miye mafita ba tunda bai tab'a jin irin haka ba, ita kam ko a jikinta saida tayi raka'atanil fijir sannan tayi sannan ta kuma jima zaune tana addu'a da tasbihi kafin ta tashi, cire hijab d'in tayi ta nade sallayar duk tana kallonshi kuma sarai tasan miye matsalar saboda tana da wayewa ta wannan fannin, amma dai ba zata iya taimaka masa ba take ji, littafinta ta d'auko ta kwanta saman kujerarshi ta bud'a ta fara karatu, jefi jefi tana kallonshi tana basarwa, gari ya fara haske ta sake juyawa ta kalleshi ganin mutum mai ibada amma har yanzu ya kasa tashi yayi sallar farilla, aje littafin tayi ta qarasa wajenshi ta d'an daddab'a faffad'an bayanshi tana fad'in "Faruk." Bata fad'i abinda taso fad'a ba saboda jin atsakanin zafi a jikinshi, bata wani daga hankalinta ba saboda tasan a ina matsalar take, fitilar d'akin ta kashe tazo taja zanin rufa tare da haurawa kan gadon ta kwanta kusa dashi ta rufesu sosai, da qyar ta birkitoshi sannan ta rumgumeshi a jikinta sosai ta matseshi, a hankali tasa hannu ta zame rigarta daga jikinta ya zama daga ita sai pants, a hankali ta saka mashi mamanta a bakinshi kamar 👶, da qyar ya iya bud'a bakinshi ya fara tsotsar mamanta a hankali ido rufe. _Namijin duniya kenan, baka da dama_🤓 Duk da itama tana jin abin na ratsata amma dai had'e tata zalamar tayi ta dinga shafar kanshi da duk ilahirin gab'a ta jikinshi, sai waje d'aya da bata fatan hannunta ya kai can, Umar Faruk kuma da yake jin yana neman shidewa can kawai yake so takai , a hankali ta kwantar dashi tare da haye ruwan cikinshi tana murza mishi kan....kai kuyi hak'uri wannan rubutu yafi k'arfin alk'alamina. _Suturtawa_ Sosai Khairat ta samarwa Umar Faruk da nutsuwa, har inda bata so takai saida ya tilasta mata zuwa, tsorata dashi sosai saboda jin girmanshi da rik'ewarshi, take fargaba ya shigeta tare da fatan kar Allah ya kawo ranar da zai kusanceta, tun Umar Faruk na nishi da numfarfashi da ihu😁harya fara had'awa da kuka, kalamai dai ba wata tsiya ba Khairat tasha su, ita kanta ta lundu ta kuma gurzu amma bata yarda ya shigeta ba, dan irin haka take so ya fara jin banbacin salo kafin yaji banbancin hq, dan da hakane kad'ai zata zama tauraruwa itama a wajenshi, tunda tasan ta rasa abinda za tayi tink'aho dashi. *Wannan shine dalilina na saka akawa Khairat fyad'e, shifa budurci ba shine mace ba, amma wasu na ganin daka rasashi ka rasa komai, baka da martaba da qima, to ba haka abin yake ba akwai abubuwan da inka rik'esu za kafi mai budurci bakali a gurin miji, tabbas ka rasa burduci kuma ba zaice na sameta budurwa ba, amma ace ka rasa salon kwantarwa miji da hankali shine abin gudu.* Juya mashi baya tayi a lokacin shi kuma yaji nutsuwa na zuwa mishi tare da tsatsafowar zufa daga jikinshi, a hankali ya matsa kusa da ita ya rumgumeta ta baya yana sumbatar kanta, da qyar a bud'a bakinshi ya rad'a mata a kunne yace "na gode Khairat, kin taimaki rayuwata." "Khairat." ya kira sunanta, jin bata amsa ba yasa ya k'yaleta. Tashi yayi ya fad'a douche ya suburbud'a ma kanshi ruwa yayi wanka k'arfi 😂, sannan ya fito ya zura doguwar riga ya shinfida sallaya ya kabbara sallah, harya gama Khairat na yanda take itama dan haka ya tashi ya kunna mata chauf eaux (heater), har ruwan suka tafasa ya juye mata a bokiti bata motsa ba, a hankali ya rad'a mata a kunne "ki tashi kiyi wanka." Khairat ko daga nan kwance ba komai take ba illa karanta karatun rashin kunya 😂, dan inba fitar da kunyar tayi ba a yanda take ji yanzu sam ba zata sake had'a ido dashi ba, ai kuwa dai murje ido tayi ta tashi zaune kamar wacce tayi bacci, towel d'inta ta d'auka ta d'aura ta nufi douche ya bita da kallon *so* da *qauna*. Tana gama wankan ta fito ta sameshi harya shirya abinshi, itama shirin tayi lokacin Ruk'ayya ta kawo musu abin kari, har Ruk'ayya zata fita Khairat tace "idan an jima ki share mana d'akin nan." "To aunty Khairat." ta fad'a ta bar d'akin. Yau ma hijab ta dora akan shirin atamfar da tayi kuma hakan ya masa dad'i sosai, saida ta rigashi fita ta fara shiga d'akin Mama ta gaisheta sannan ta wuce wajen aiki, tun a hanya ta yanke shawarar ba zata bari kishiyarta ta k'wace miji ita kad'ai ba, dole itama ta samu. ******************* Tana cikin ayyukanta Habiba tace ana son ganinta wata k'awarta, izini ta bata ta shigo da koma wacece, jim kad'an macho ta shigo, gyara zama tayi tayi kalar rashin mutumci tana kallonta harta zauna, "meya kawoki?" Itace tambayar data mata, "kuma macho? nazo ganinki ne fa." "Hum, kinzo ganina? baki san inda nake bane?" "Kiyi hak'uri macho, wallahi ban samu damar zuwa gidanki bane, amma nida Farida da Hibba munyi shawarar zuwa insha Allah." "Ke dallah karki raina min wayo, kinga Rashida, a gaskiya na gane *tarayyata* bata da wani anfani, tunda na tare babu shegiyar data taka qafarta gidan nan, kuma tunda na ganki anan kuma a yanzu , nasan wani abu kike so, dan haka dama dai abota daku kune kuke qaruwa dani amma banda ni, dan haka ina ganin daga nan ya kamata mu raba kaya daku." Ko kad'an al'amarin bai yiwa Rashida dad'i ba, dan wata hidima ce ta taso mata kuma a gun Khairat kad'ai zata samu kudi, in wajen samari ne to dole saita bada wani abu itama kafin ta samu, "amma macho wane irin hukunci ne wannan? wallahi zamu gyara dan Allah kiyi hak'uri." Hak'uri da magiya ba irin wanda bata mata amma ta kafeta da ido ko magana tak'i tayi bare tasa ran ta hak'ura, dole ta tashi ta fita rai a bace tana dura mata ashar, ba ita kad'ai ba harda Umar Faruk da take ganin shine silar suyawarta. Tana fita ta dora kanta akan makeken tebur d'in tana hasko irin wasan da sukayi da Umariri, murmushi ta saki tana jin wani farin ciki zuciyarta na ratsata, da sauri ta lumshe ido saboda tuna irin....🙈tana tausayin kanta ranar data shiga hannunshi🤓karki damu tawan, aunty Aishan Umma tana nan tare dake.😉 _Ashe shi yasa akama Zuby babbar hanya_😂 Shima dai a b'angarenshi haka abin yake, *daren jiya* ya kasa fita a qwaqwalwarsa da zuciyarsa , murmushi ne kawai akan fuskarshi mai tsada, tunani yake wace irin nutsuwa ce to zai samu in har zai iya jin irin wannan farin cikin da kwanciyar hankali saboda taimakon data masa, ko kuwa dai mutuwa zaiyi ma gaba d'aya tsabar farin ciki da jin dad'i, _mutuwar lafiya_😏. Daga shi har ita babu wanda ya tsinana wani abun kirki har aka gama sallah azahar Khairat ta nufi gida, yauma saida ta tsaya gabanshi tace "ni zan wuce gida." Har zata wuce taji ya janyo hannunta,tana juyowa ya tashi tsaye ya manna mata kiss😘a goshi , yau ita mamaki ya shek'e shi kuma baiji komai ba saima aikin gabanshi daya kama. Fita tyi tana sakin murmushi jama'a ma dai yau basu saka musu idon nan ba kamar jiya, har taje gida bata daina tunanin Umariri ba, shima kuma dama ba wani aiki yake yi ba, tana fita ya kwanta akan tebur d'in yana murmushi tare da wasa da alk'alamin dake gabanshi. ****************** Tun fitarsu ba dad'ewa yan uwan Zuby suka zo gyaran d'aki tare da kaya, tun kafin su fara gyaran suka kalli kewayen Khairat *Uwani* tace "hum, ina zubarwa da kai mutunci ba, kewayen nan da sunan Zuby akayishi amma ku d'auka kuba wata, ai wannan rashin adalcine." *Zabba'u* ce tace "waike kina mantawa da kud'i sunfi tasiri fiye da aikin boka ko malam? ai kar kiyi mamaki kud'i suka gani fa." "Kuma fa hakane, Allah ya shiryemu to , amma ni ko duniya zaka d'auka ka bani, aiba zan qasqantar da kaina gareka ba wallahi." "Ke kika san haka ai, baki ga harda sabon abin sanhwa aka sake ba?" cewar *Zulfa'u*. Da wanna kananan maganganun suka gama gyaran, ba laifi an cika d'akin da kaya, sai dai tsari da qualitie ya banbanta dana Khairat, suna gamawa suka shekama d'akin turaren wuta sannan suka rufe, ana kiran sallah azahar sukayi alwala sukayi sallah sannan Ruk'ayya ta kawo musu abinci. Sunacin abincin Hajja Khairat ta shigo, ta tarar kowa na tsakar gidan ana cin abinci , ko kallon su Uwani ba tayi ba ta wuce wajen da Mama ke zaune tana bawa su Yusuf da Fateema abinci, gwiwoyinta ta d'ora akan taburmar da suke zaune tace "Mama sannu da gida, ya jikinki?" Cikin sakin fuska da fara'a Mama tace "jiki alhamdulillah 'yata, har kin dawo?" "Na dawo Mama, ki saka min albarka." Cikin dariya Mama tace "albarkata na tare dake 'yata a koda yaushe, kije ki huta yanzu Ruk'ayya zata kai miki abincinki." "A'a Mama, ki barshi kawai." tana fad'a ta mik'e zata wuce ciki, Uwani ce tace "koda nace, gashi dai da idona na gani." "Hum, aini da wani ne ya fad'a mana ma ba zan yarda ba wallahi." cewar Zulfa'u. "Nifa abin takaicin anan, yanda k'anwarmu zata zauna a wannan gida a wannan rayuwar takaici, taya za tayi kishi da karuwa? yake ya k'wak'walo cutarshi yazo ya mak'alawa yar uwarmu, ni shine yafi damuna." Cak Khairat ta tsaya tare da juyowa ta kalli Ruk'ayya tace "sabbin mahaukata akayi kuma a gidan?" Dariyar da Ruk'ayya ke rik'ewace ta fito za tayi magana Mama Maimuna uwar katsalandan tace "au, dama can akwai mahaukata ne a gidan?" Maida kallonta tayi gareta ba alaman wasa a tare da ita tace "kin fahimci hakan kenan?" A take kula ta kalli Uwani tace "dama ku tunaninku zaku kawo yar uwarku ne haka kawai ba tare da kun bata training d'in zama da karuwa ba? karuwar ma kamar Khairat." "In dai har baku shiryata ba, to ku ware mata d'aki dan har yanzu bata gama zaman gida ba, domin kuwa ba dad'ewa za tayi ba zata koma inda ta fito." Juyawa tayi Ruk'ayya ta taso ta d'auko makullin k'ofar ta soma bud'e mata, Zabba'u ce ta nuna ita bata da hak'uri, hakan yasa ta taso tazo har gaban Khairat tace "idan gadararki fitsari, to ki sani ni zan miki maganinta, wallahi ba yar Mani Bukar kike ba, ko kece 'yar shugaba gaba d'aya ni sai naci kutumar ub...." Tasss, kake ji Khairat ta nuna mata ta fita hauka, da hannu Khairat ta nunata tace "idan haukane a kanki ki sani asibiti ce akan Khairat, idan rashin kunya ce tak'amarki ki sani Khairat harta siyarwa take da, idan fitsara ce tink'ahonki ki sani Khairat dab'i'arta ce haka, ki yaye nan gaba idan za kiyi magana, ba dan a cikin qaddarar aurena ba akwai auren Umar Faruk, ke da baki isa ko kamata ki gani ba koda a mafarkinki , banza kawai." Da k'arfi ta zura kai ciki ciki tana shiga d'aki Ruk'ayya ta gyarashi tsaf sai kamshi yake, fad'awa tayi saman gado tana jin zuciyarta kamar zata fito, maganar kishiya na tab'a ranta sosai kuma yana dagula mata lissafi, bawai zafin maganar da Zabba'u ta fad'a baneya harzuk'ata, zafin kishi ne kawai ya rinjayeta. Nan fa sauran suka mike wai sai sunyiwa Khairat dukan tsiya, Mama Sa'a da yanzu bata san ana takurawa Khairat da kuma Mama da Saratu ne suka dinga basu hak'uri, da qyar suka rabu dasusuka bar gidan, amma dai al'amarin baima kowa dad'i ba, amma Ruk'ayya taji dad'in haka sosai tunda da farko iyayensu suka dinga ciwa mutunci. Saida ta jima kwance tana kuka kafin ta tashi ta watsa ruwa ta zura doguwar riga iya gwiwa ta d'ebo kayan marmari da biscuit da chocolat tasha ta k'oshi sannan tayi kwance, bacci bai d'auketa sai tunanin daren jiya kawai hakan yasa ta kira Ruk'ayya ta d'auko littatafanta ta fara mata wani sabon darasi, sai kiran sallah la'asarya tsayar dasu suka tashi zasuyi alwala Ruk'ayya cikin kunya tace "wallahi aunty Khairat rigarki tamin kyau." Murmushi kawai tayi ta fara alwala tace mata "idan kinyi sallah ki had'a min ordevre." "To aunty." ta fad'a ta bar wajen. Babu abinda bata siyo ba a kayan abincin data siyo musu, hakan yasa babu abinda aka buk'ata wajen had'awa, minti kusan arba'in ta dauka kafin ta kawo mata, tana zuwa ta sameta da wata riga da wando iya gwiwa kayan sai suka fi birgeta akan rigar dazu, ajewa tayi tace "aunty gashi." Zata juya ta fito tace "kinga rigar nan akan kujera." Da farin ciki ta d'auki rigar tana gwadawa a jikinta, tsayi dai Khairat ta fita amma jiki kam zasu iya zuwa daidai ko kuma Khairat ta fita da kad'an, "na gode aunty Khairat." Ko kulata ba tayi ba bare ta amsa, tana fita ita kuma ta fara cin abincinta, bayan ta kammala kuma ta sake d'aukar littafi tana karatu, *18:30* Umar Faruk ya dawo gidan, tunda ya shiga d'akin ko kallonshi ba tayi ba harya cire kaya ya shiya wanka, sai lokacin kuma wata zuciyar tace mata "to a hakane kuma kike so ki addabi tunaninshi, idan ya gane kina kishinshi zai d'auka sonshi kike kuma ya rainaki , kawai ki basar harki samu kuje Germany ku dawo wata dama ce da zata qara kusantashi dake, kuma me meye na hushin kin manta ya gama ganin komai na jikinki." Tashi tayi ta bud'a kayanshi ta d'auko wata shemise fara qal da bak'in wando slim da takalma farare slipas, tana cikin duba agogo ya shigo d'akin... _Toya kuka ce, ta saka masa da kanta? ko kuma ta barshi yasa?_ 😉😂😍😍😍 luv u guy's. *Meerah* 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣0⃣ "Yadai Hajia Khairat?" Yar qaramar harara ta watsa masa kafin ta aje kayan hannunta tace "na zab'o maka kayan da zaka saka ne." Zata koma kan gado ya rik'e hannunta, juyowa tayi suna kallon juna kafin ya fizgota ta fad'a qirjinshi yace "tunda kike cirosu, to ke zaki sakasu." Murmushin gefen labb'a tayi tace "wasa kake ko? kaima kasan abune da ba zai yiwu ba." "Me zai hanashi yiwuwa? in dai Hajia Khairat zata iya shiga zani d'aya da Umar Faruk harta bashi t...." Da sauri ta qarasa fad'awa jikinshi ta tare da toshe mishi baki, a hankali yasa hannu ya cire hannunta yana fad'in "a barni nayi magana da bakina mana." Hannunta taso janyewa tana fad'in "kasa kayan." Had'e k'ugunta da nashi yayi yana mata shu'umin kallo yace " ke zaki sakasu, idan kuma ba haka ba, zan cire na jikinki in yaso saimu saka tare." "Bama sai ankai ga haka ba, zan saka miye a ciki, naga da saffen nan babu abinda ban gani ba a jikinka, to miye na shiga matsalar." Murmushin gefen labb'a yayi yace "da yaya haka ta faru? naga har kuka ki kayi kamar wacce nama wani abu, ai in dama qarasa aikin nayi sai kiyi kukan mai lasisi, matsoraciya kawai." Qaramar rigar ciki ta (singlet) dauka ta saka masa sannan ta d'auki dogon wando ta sunkuya har qasa, shiru ta d'anyi kafin ta dago ta kalleshi tace "rayuwa kenan, a gida ina tsaye Biba ke saka min kaya, amma yau gashi ina sakawa baligi kuma k'oshashen namiji kaya, abinda ban tab'a tunani ba." "Da girmanki kike tsaye ana saka miki kaya?" "Eh mana, duk cikin ikone." D'age kai yayi sama yana magana qasa qasa "wannan ashe ba maza ba kad'ai suka gama kalleta ba harda mata, Allah kamin tsarin wuce iyaka." "Amma a haka jiya ka dinga min kuka kamar d'an dana haifa a cikina, harda wani mak'alk'ale min a jiki kanata tsotar min mama, dubi ka gani fa." Ta d'ago tare da janye rigarta qasa mamanta na hannun dama ya fito tana fad'in " kaji fa yanda suke min ciwo, har sun canza kala kamar wacce ruwan nono suka taran ma." Da sauri ta d'an janye tare da mayar da rigarta saboda hannu da Umar Faruk ya kai da nufin tab' yana fad'in "bara na gani." Sake sunkuyawa tayi ta gyara masa wandon ta rintse idonta wai ita ba zata kalleshi ba, haka ya saka wandon kafin ta mik'e ta d'auki rigar ta saka masa, tana cikin b'alla mab'allan rigar ta kalleshi tace "da bakinka kace ba zaka tab'a had'a jikinka da nawa ba, meya faru yanzu?" Basarwa kawai yayi ya huske yace "ai banyi rantsuwa ba kuma ba alk'awari nayi na bare ace kaffara ta hau kaina." Agogo ta dauka ta makala masa tare da machete d'in hannun rigarshi sannan ta d'auki turarenshi har kala biyu *Oud 24 heures* da *Gold* ta wankeshi dashi. Wayarta ta d'auko tace "mutum na farko dana farama wahalar da koni bana ma kaina, dan haka wannan kwalliyar taka ta zama cikin tarihi." K'ugunshi ta rik'e ta saita wayarta ta danna camera sweet selfie sannan ta kalleshi tace "yi murmushi mana." Maganarta ce ta bashi murmushin sai dai kuma ita yake kallo ba wayar ba harta dauka, kiran sallah magrib ne ya dawo dasu hankalinsu , fita yayi yayi alwala sannan ya nufi masallaci yana ji fa a yanzu dai kam ko ba zai kusanci Khairat ba, yana so ya zauna da ita yana kuma mamakin Khairat d'in, sam bai tab'a tsammanin haka daga gareta ba, _nima fa banyi zaton haka ba_. _FAN'S ma ba suyi tunanin haka ba da wuri, to amma dama baka sanin halin mutum saika zauna dashi._ Saida yayi sallah isha'i ya dawo itama harta gama sallah ya sameta zaune akan gado ta qurawa photonsu ido, ita kanta sai yanzu ne taga matuk'ar dacewar da sukayi da juna, ya fita tsayi da kad'an ta fishi hasken fata da kyawu , ya fiya kwarjini da izza, number daya kirata ranar da taje asibiti ta gani ana Whatsapp da ita, tura photon tayi a lokacin shima ya hau connexion, yana bud'a photon suka fara kallon juna, shima dai kura mata ido yayi kamar yanda ta qura masa , Ruk'ayya ce ta shigo ta kawo musu abinci, yau ma shi kad'ai yaci Khairat ma sam bata jin yunwa saboda abincin da taci da yamma, saida ya gama ta janyo littatafai aka fara karatu. Wajen karatu ma Khairat kwance take akan cinyarshi har suka gama, yau ma dai koda aka zo kwanciya Khairat tace dole sai kan gado zai kwanta, tuburewa yayi da qyar ta addabeshi ya yarda ya kwanta, yauma kamar safiya sosai suka galabaitar da junansu kai kace wasu masoyane dama, yau kam koda Umar Faruk ya nutsu rumgume Khairat yayi a qirjinshi har bacci ya d'aukesu. _Kuyi hak'uri fan's, wallahi abubuwa ne dayawa, ga rubutun k'angin rayuwa ga hidimar gida, dan nayi alk'awari ne yasa na cika._ *Wannan page kyauta ce ga yar uwata Djamila* 😘 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _*Jihadi* anyi nisa masoya, dan Allah masu neman tun daga farko kuyi hak'uri a kammala saiku samu document, abubuwa suna min yawa sosai yan uwa ta yanda na fara k'osawa, ina fatan zaku fahimceni, nasan ina da masoya a waje da dama ta yanda duk mai neman *Jihadi* ba daga 1 ba ko daga 0 ne ma zasu samu, dan Allah duk mai nema ya dinga tambaya a grp, bana da burin wulak'anta masoyana a duk inda suke._ _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣1⃣ Kiran sallah farko a kunnuwan Umar Faruk dan haka ya farka tare da raba jikinshi dana Khairat, saida ya d'aura towel d'inshi kafin ya tayar da ita, da sauri taja zanin rufa ta rufe qirjinta tana kallonshi, harara ya watsa mata yace "kaji yar rainin wayo, ku kwana kina min kuka yanzu kina wani rufe jiki, tome zan kalla bayan jiya komai a hannuna yake." Juyawar da yayi ya shiga douche yasa ta dafe kai da hannu tana fad'in "ohhh, shikenan ta gama qare miki Khairat, kin saki jiki dayawa da yaronki." "Zuby." wata zuciyar tace mata. Dan haka kawai ta share ta tashi itama ta d'auki towel d'inta ta d'aura ta nufi douche d'in da wani sabon salo, yana tsaka da wankan tsarki yaga ta fad'o ciki, da sauri ya mike tsaye yana fad'in "ke lafiya, meye haka kuma?" Bata kulashi ba sai towel d'in data cire ta jefoshi waje tayi tsaye tana kallonshi, kakkare jikinshi ya fara ita kuma ta d'an bugi qirjinshi tana fad'in "kaji rainin hankali, nan fa jiya kake min kuka da ihu a gidan nan, shine yanzu zaka wani rufe jiki, to me zan kalla? bayan daren jiya komai a hanuna yake ina sarrafashi." Ya fahimci ramawa tayi dan haka yace "naji to Hajia, zaki iya tafiya idan na gama kin shigo." "Tare zamuyi." ta fad'a da fara tsarkake gabanta. Ya lura kawai Khairat ta sauya fiye da tunaninshi, dan haka baya da wani zab'i daya wuce ya saki jiki suyi wankan, saida suka gama na tsarki kafin Khairat ta had'e jikinsu ta dinga shek'a musu ruwa, ganin b'annar ruwan yayi yawa yasa ya kashe panpon tare da fad'in "to a ragawa an jima ko." Towel d'inshi ya d'auka zai d'aura Khairat tayi saurin ja itama ta rufe jikinta, kallonta yayi yace "ki d'auko naki mana." "Ba buk'ata." ta fad'a tana shirin fitowa daga ciki. "Ai kuwa buk'atar ta taso." ya fad'a yana janyota. "To tsaya kaga me zai faru." Had'e k'ugunsu tayi waje d'aya ta rufesu da towel d'in sannan ta zura hannayenta a bayanshi mak'ala a wuyanshi, cire slipas d'inta tayi ta d'ora qafafunta akan nashi sannan tace "to muje." Kallon juna suke sosai har suka isa d'aki, suna shiga ta zare towel d'in daga jikinshi ta rufe nata jikin, kashe wutar d'akin yayi danya samu damar saka kaya yana fad'in "duk tabi ta kalleni haka kawai." "Me zan kalla a jikin gardi." A cikin duhu ya lalubota, ita kuma saboda ba tayi tsammaninshi ba yasa tana jin ya cakumota ta saki qara, rufe mata baki yayi a kunne ya rad'a mata "waye gardin?" Shiru tayi dan haka yasa ya tsunshi biyu ya tsamiki mazaunanta hakan yasa ta sake sakin qara, "zaki fad'a min ko saina..." Cikin shagwab'a tace "nifa da kaina nake." Sakinta yayi ya fara saka kaya cikin hanzari saboda kiran sallah da akayi, yana shiryawa ya fita itama ta shirya ta kabbara sallah, har gari ya fara haske sannan ya dawo lokacin ta fara karanta littafin Akhdari shi kawai take jira. Yana zaunawa ta d'ora hannayenta akan cinyoyinshi ta fara biya karatun, dagata yayi daga jikinshi yace "ko mage ta shafa min lafiya wajen son jiki, a hakane za kiyi karatun?" Cikin turo baki tace "kaima kana son jikine?" "To wa yak'i banza." ya fad'a yana d'auke kanshi. Bai ankara ba yaji ta finciko kanshi ta d'ora a cinyoyinta ta danna mashi qirjinta a fuska ta bud'a littafin tana fad'in "to saimu fara." "Ke sakeni dallah, so kike ki kasheni?" Sai lokacin ta kula ashe gaba d'aya qirjinta a fuskarshi yake, gyara mishi tayi amma bata bari ya d'aga kanshi ba, a haka ta biya karatunta harda wanda Ruk'ayya ta qara mata, ya jinjina mata sosai sannan ya d'ora mata wani, suna gamawa kuma ta d'auki littafi mai tsarki shima ta d'ora sannan qara dad'a mata wani, saida suka gama sannan ya dinga mata sharhi sosai akan abinda suka karanta, ta kuma fahimta tare da burin kiyaye na kiyayewa, aikata na aikatawa. Sallamar Ruk'ayya sukaji ta kawo musu abin karyawarsu, yunk'urawa yayi zai tashi ta sake danne kanshi tace "meye haka? k'anwarka ce fa." Ba yanda ya iya haka Ruk'ayya ta shigo ta samesu sai dai mamaki bai bar fuskarta ba, "ina kwananku?" ta fad'a tana kallonsu. "Lafiya lau Ruk'ayya, kin tashi lafiya?" cewar Umar dakodako ganinta baya iya yi. "Lafiya lau." ta fad'a a sanyaye. Khairat kam sai wani shafar kansa take tana kallon fuskarshi ko Ruk'ayya ma bata kalla ba harta fita daga d'akin, tana ganin ta fita ta ture masa kai tare da fad'in "malam ni d'agani dallah." Zaune yayi yace "dama bani na saki ba ai." Ganin yau a babban tray aka kawo abin karin yasa Khairat bud'awa, soyayyen k'wai ne da dankalin turawa sai kuma flas d'in shayi da kayan had'inshi , Umar Faruk ta kalla tace "baby , dan Allah ka taimaka ka had'a min shayi." Wani kallon yaushe kika haukace ya mata kafin yace "nine ma zan had'a miki?" "Eh mana, to miye a ciki?" "Akwai wani abu kam, kece fa mata ni kuma mijin, kuma nine zan had'a miki abin karyawa." "To wai miye a ciki dan Allah? dama aure ba anayi bane dan a taimaki juna? kai miji ni kuma mata, yau na buk'aci taimakonka , gobe zaka iya buk'atar nawa taimakon, dama ai hakane rayuwa." Kallonta yayi dan har ranshi yana tunanin sai tayi magana akan taimakon data masa a safiyar jiya, amma da yaji bata fad'i haka ba saiya tabbatar da abinda ta fad'a, da tace idan tayi taimako bata iya tuna ko fuskar wanda tama bare ta tuna me tayi, jinjina kai yayi ya matso domin had'a mata yace "to baby bara na had'a miki." Murmushin ka rainani ta masa tana kallonshi yana had'awa, saida ya gama ya mika mata cup d'in ta karb'a tana fad'in "naga yanda kayi, kuma insha Allah gobe ni da kaina zan had'a maka." "Au, dama baki iya bane?" "Ban iya ba." ta fad'a tana kurbar tea d'in. "Jan aiki." ya fad'a yana shirin had'awa kanshi shima. Ba tare data kalleshi ba tace "ya taso maka?" "Ya dai taso miki, kina mace baki iya had'a shayi ba? ina ga dafa abinci." "To mema zai kaini dafa abincin? gidanmu masu aiki ne keyi, anan kuma Ruk'ayya ce da waccen matar." "Au baki ma san sunanta ba?" "Ban sani ba saboda baka fad'a min ba." "Sunanta Saratu, matar yayana ce Abbakar, kuma Ruk'ayya da kike magana ai banan zata zauna ba kullum, itama za tayi aure taje gidan mijinta." "Kafin lokacin kuma figaggiyar amaryarka zata dinga dafa mana." Gyara zamanshi yayi yana fuskantarta yace "wai me yasa kike kiramin amarya da figaggiya? tunda muke ban tab'a jin kin kira sunanta ba sai figaggiya." "Saboda nasan zaiyi wuya ace ka had'a mata biyu masu kumari, dole d'aya sai tafi d'aya, saboda ni nasan kaina 'yar duma duma ce shi yasa nake tunanin ita figaggiyar ce." "Humm, Hajia rumdub'e kenan, wato ke gaki sarauniyar masu k'iba ko? to bari ki ganta zaki sha mamaki." "Fad'i ka qara fad'i, ni Hajia ce, amma Hajia Khairat ba Hajia rumdub'e ba." Hannu yasa ya juyo da kanta yace "wai da gaske Hajia ce ke?" "Kana tamtama ne?" ta fad'a fuskarta ba yabo ba fallasa dan tunda yayi maganar amaryarshi ranta ya gama b'acewa. "Ina mamaki ne, dan naga ku mata burinku da kunje qasa mai tsarki ku saka haure ta yanda da kunyi dariya zai fito yana walk'iya, amma ke naga babu ko d'aya a bakinki, ko dan kina yar zamani." _Nima dai nace hud'u zan saka idan naje, oga yace na lullub'e duka hak'oran, wai magana ce ya mayar min😁_ Hararanshi tayi tace "meka d'aukeni ni, ko wace shekara nakan je nayi ziyara a qabarin manzo (S.A.W), sau d'aya na tab'a sakawa kuma na cire na siyar." Da mamaki ya kalleta yace "siyarwa fa, rashin kud'i ki kayi?" Cike da nuna rashin kulawa da rashin tabbas tace "na manta ko waye da kuma sunanshi, na kuma manta lokaci da wajen, amma dai a lokacin ina wajen wani biki kuma babu kud'i a jikina, kuma naga mai neman taimako kawai na ciresu guda biyu na bashi ya siyar." Shayin hannunshi ya kurb'a yana kallonta, a haka har suka gama karin ita ta fara shiga wanka ta fito sannan ya shiga, koda ya fito ya sameta saye ta fito da kaya zata saka, bras ta ya d'auka yana kallo kafin yace "domin Allah kuna kyautawa , akan me kuke tauye wad'annan bayin Allah ta hanya saka musu wannan sasarin? ba zaku barsu su wataya ba." Fizge kayarta tayi tana fad'in "bani nan sarkin kicihi, ina ruwanka to? wata matar ai ba zata kallu ba idan ba wannan." "Amma ai ban dake, kefa ki dubi yanda kike." ya fad'a tare da janyota ya zame towel d'in jikinta, hannu yasa ya shafi qirjinta nata yana latsawa sannu sannu, wani caji yaji yana d'auka dan haka ya dinga lumshe ido yana fitar da numfashi sannu sannu, janye hannayenshi tayi ta fara k'ok'arin mak'ala bras, fizgeta yayi yace "wallahi ba zaki sakata ba haka kawai, barsu suma su wataya." Yanda yayi maganar yasa ta d'auki rigarta ta saka kuma ta zauna mata daram, pant ta saka tare da siket duk yana kallo, wata tamfatsetsiyar sark'a ta d'auki tare da 'yan kunnenta ta mik'a mishi ta juya tana kallon madubi tace "ka saka min." Cikin nutsuwa suka dinga kallon juna harya gama saka mata, hanckiciep (mouchoirs) d'in daya gani a saman coiffeuse ya d'auka ya janyota jikinshi, a hankali ya kaishi a bakinta zai gobe jan bakin data shafa, saurin gocewa tayi tana fad'in "a'a, miye haka?" Tsaki yayi dole taja bakinta tayi shiru saboda ganin ya b'ata rai, tana ji tana gani ya goge jan bakin tare da girar data sha wahala wajen zanawa, juyawa tayi ta kalli kanta a madubi , lab'e baki tayi ta fashe da kukan shagwab'a harda bubbuga qafafu, wucewa yayi zai saka kayanshi yace "daga yau haka zaki dinga fita ba tare da ko d'igon kwalli ba." Cak ta tsaya da kukanta ta matso kusa dashi ta koma Khairat d'inta tace "kai a wa zaka fad'a min yanda zan dinga fita? fuskar dana sakar maka na kwana biyu shine har zaka rainani haka, ko kuma dan kasan komai a tare dani, to wannan dama shine dalilin da yasa naki yarda ka kusanceni, dan nasan alfahari za kayi da hakan." Damtsenta ya fizgo da k'arfi ya had'ata da drower kayan ya matsa gaf da ita fuskar nan a had'e yace "ni a mijinki kuma mai iko dake, ki dinga kama harshenki, dan ba kowace magana Umar Faruk ke hak'urin jinta ba, yanzu nan sai kiyi nadama." Idonta ne sukayi ja suna neman kawo k'walla , cikin hassala tace "dallah ni sakeni, nak'i na kama bakin nawa naga me za kayi, kawai mutum dan ka samu dama shine kake neman rainani, wallahi saina d'aureka idan ka qara tab'a lafiyar jikina haka." Hankad'ata yayi saman gado ta fad'a yana fad'in "idan kin d'aureni ki hana nayi numfashi." Tasowa tayi daga kan gadon ganin ya saka dogon wandonshi zai saka belt, karb'a tayi ta fara mak'ala mishi belt d'in idonta qasa tak'i kallonshi, shi kuma ya kafeta da ido yana kallon hawayen dake barazanar zubowa qasa, duk da masifa ce a ranta amma bata fatan duk wani abu da zai lalata mata shiri, musamman na tafiyarsu Germany, zafin da take ji a zuciyarta karuwa kawai yake, maganar amaryarshi ta tsaya mata a rai, tunani kawai take yanzu idan amaryar tazo duk wannan abinda yake mata dainawa zaiyi, kuma zai bud'a sabon shafin soyayya shida amaryarsa , tana cikin balla maballan rigarshi hawayen da take boyewa suka zubo, da sauri ta daga idonta ta kalleshi saboda ganin yayi saurin tara hannunshi suka zuba akai, kallon kallo suka shiga yiwa juna, wasu hawayen suka qara gangaro mata yasa hannayeshi ya shareta mata, tallabo fuskarta yayi yana kallon idonta danshi a tunaninshi fad'an da sukayi ne yanzun, kai ya girgiza mata tare da cewa, "In dai ina da rai, hawayenki ba zasu sake zuba ba tare dana taresu ba, basu da farashi a duniya da zai iya fansarsu, dan Allah Khairat kiyi hak'uri idan har saboda abinda nayi yanzu ne kike kuka, haka kawai naji bana son zubar hawayen nan naki , domin kamar a birnin zuciyata suke sauka, ki share hawayenki, ni Umar Faruk nayi alk'awari daga yau daga kuma yanzu, ba zan sake b'ata min rai ba da har zaisa ki zubar da hawayenki, kinji?" ya fad'a a raunane. Kallonshi kawai take amma ta kasa gasgata abinda kunnuwanta da ke jiyo mata hakama abinda idonta ke gane mata, shirun da tayi yasa ya kama kunnuwanshi alamar ban hak'uri ya shagwab'e fuska yace "kiyi hak'uri mana Hajia Khairat." Nanma shiru ba amsa, mafita d'aya ta rage masa dan haka ya birkita idonshi yayi irin jirgen kallon nan da za kaga kamar ba kai mutum ke kallo ba amma kuma kai d'in yake kallo (kallon gora) ya zuro harshenshi waje ya mata gwalo sannan yace "dan Allah ki yafe min Hajia rumdub'e, wallahi ba zan qara ba, idan na sake ki min bulala." Yanda yayi wani iri da kuma maganar yasa Khairat bushewa da dariya tana girgiza kai, hannu ta kai ta bugi qirjinshi tare da kwance akan qirjin nashi tana ci gaba da dariya, shi kuma lek'a fuskarta yayi yana kallon kyakyawar fuskarta, ganin yanda dariya ya mata kyau amma sai dai kuma bata cika dariyar ba saboda miskilanci irin nata , kud'urawa yayi a ransa dole ya dinga sakata dariya koda basu tare, da haka kuma ta 'karasa shiryashi harda saka mishi takalma qafa ciki da agogo sannan kowa ya d'auki jakarshi suka fita tare. Hannunshi makale da nata hannun suka shiga d'akin iyayensu suna gaishe dasu, da farko yaso raba hannayen nasu amma saita cije ta sake matse hannunshi tace "ai kai ka fara." A haka suka shiga d'akin Mama rumgumewar da Khairat tama Mama yasa suka raba hannayensu , gaisawa sukayi sosai kafin suka fito, Ruk'ayya dake bayan Mama ce tace "ikon Allah, ko yaushe yah Umar ya lalace haka?" "Lalacewa kuma Ruk'ayya? matarshi ce fa." cewar Mama. Ruk'ayya ce tace "haba Mama ya rage kunya yanzu, dafa na shiga d'akinsu kwance na sameshi akan cinyarta ita kuma tana wani shafashi." "Alhamdulillah, saimu gode Allah tunda Allah ya daidaita tsakaninsu, ko kin manta lokacin baya daya wuce itace ta zabga mishi mari? kina ganin da akwai irin wannan shak'uwar ta yanzu da haka ta faru? dan haka kija bakinki kiyi shiru, kuma nan gaba idan kika kai abincin ko sun baki izinin shiga ki d'an k'ara b'ata lokaci kafin ki shiga." A d'akin Baba ma gaisawa sukayi sosai yayin da yayi farin cikin ganinsu tare, ba kamar sauran yan gidan ba da suke ganin ya canja sosai. _Haka rayuwa take dama, da iyayenta zasu ganta a yanzu za suyi farin ciki sosai na ganin ta shiryu , yayin da ku kuma kuke ganin d'anku tashi tarbiyar zata watse._ K'ok'arin hawa mashin d'inshi ya fara kawai Khairat ta janyo hannunshi ta mika mishi makullin mota tace "muje, kai zaka tuk'a matarka yau." "A'a, kije kawai." ya fad'a ba yabo ba fallasa. Ta fahimci me yake nufi dan haka tace "to sai dai muje akan mashin d'in." "Akan me?" "Akan yau tare da mijina nake so mu tafi gurin aiki." Shiru yayi yana tunani kafin ya karb'i makulli yace "muje to." Tare suka fita bayan ya bud'e itama ta bud'e ta zauna mazaunin mai zaman banza sannan shima ya shiga ya tayar suka wuce, jinshi yake duk ba dad'i amma hirar da take janshi da ita yasa ya manta komai suka ci gaba da farin cikinsu har suka isa wajen, da gudu passinger ya bud'e mazaunin matuk'in , amma ganin Umar Faruk yasa yayi tsaye yana gaisheshi, da sauri Khairat ta zagayo tana fad'in "yanzu a hakane zaka gaishe da mijina, ai dai ka rusuna shima kamar yanda kake min." Zubewa yaje yayi Umar Faruk ya rik'eshi yace yaje kawai, cikin shagwab'a ta sake mak'ala hannayensu har suka shiga ciki mutane na kwasar gaisuwa, yana kawowa mazauninshi ta saki hannunshi ita kuma tayi nata office d'in zuciyarta cike da mamaki da tambayoyin me yasa ta zama haka, me kuma yasa ta sauya haka, akan kuma wani dalili take sakin jikinta haka da Umar Faruk, amsar dai d'aya ce kawai kar Zuby ta shigo ta k'waceshi ita kad'ai, to amma akan me zata damu da kar a rabasu, *sonshi kike mana* a cewar wata zuciyar amma sai tace sam ba haka bane, rainine kawai bata so. *13:30*, Khairat ta fito zata koma gida, Umar Faruk na ganinta a ranshi yace "dole nayi wani akan aikin nan nata, kullum a wannan lokacin take komawa gida." Maganar data mishi ce ta dawo da tunaninshi "baby, ni zan wuce gida a taxi." Hannu yasa zai fito da makullin motar yana fad'in "a'a kije a taxi, ga makullin, ni saina zo tare da Ishaq." "Ka barshi kawai, aita zama taka." Tana fad'a ta bar wajen ya bita da kallo shi kuma, taxi ta d'auka ta mayar da ita gida, yau ma Ruk'ayya ce ta sake d'ora mata karatu bayan sunci abincin rana , da yamma kuma tana jin ana hayaniya gidan amma data tabbatar na tarban amaryane duk sai mutanen gidan suka dinga bata haushi, a haka ta zauna abinta har *18:30* Umar Faruk ya dawo shima. _Ma chérie Hakeema Allah ya baki lafiya._👏😔 _Kuna ganin za kuwa a kawo amaryar nan lafiya_??? *Dan Allah duk mai neman Jihadi ya dinga nema a grp, wani ko page d'aya ya rasa saiya bini private, pls ku fahimceni.* 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣2⃣ Wanka ya shiga ba tare da sun kula juna ba, saida ya shiga sannan ta tuna da tsarinta, tashi tayi yanzu ma ta fito mashi da wata watsetsiyar shadda fara qal da alama bai tab'a sakata ba, takalma agogo ta fito dasu tare da hula bak'ak'e, tana gamawa ya shigo yana tsane ruwan jikinshi, karb'ar towel d'in tayi ta fara goge masa shi kuma yana kallonta yana tunanin kodai tana da aljanu, a haka ta gama shiryashi tsaf dashi yau ma ta d'aukesu selfie sannan ya fita zuwa masallaci, harya fita ya kuma dawowa yace "wannan shirin fa na miye?" "Ba amaryarka zata zo ba anjima." ta fad'a tana kunburo baki. Murmushi kawai yayi ya fita zuciyarshi na qara kamuwa da qaunarta, ana kiran sallah itama tayi sallah sannan ta shiga wanka ta shirya cikin riga da siket masu shegen kyau na kantie sun fito mata da komai a fili, kwalliya tayi sosai tana gamawa kuma ta mayar da sallah isha'i da ake kiran, harta gama ta zauna akan kujera amma bai dawo ba, ranta na tafarfasa haushi ya gama isarta tunaninta ko yana can da motarta ma ya tafi d'aukar figaggiyar amaryarshi. *************** Tanti Ma'u ce ta tisa Zuby gaba ta bata wani kullin magani tace "wannan wanka za kiyi dashi na tsawon kwana uku, wannan kuma kisan hanyar da za kibi Umar Faruk yaci a abinci, wannan kuma na tsinnaniyar matarshi ce, a abinsha zaki zuba matashi." "Amma Mama duk na miye wannan? nifa tsoro nake ji." "Ke can dallah, wannan da kinyi aiki dashi, to ke zai dinga gani da daraja , ita kuma ta fita a ranshi, wannan kuma idan yaci a abinci, to zaki malleshi ne sai yanda ki kayi dashi, wannan kuma da tasha ita kuma, to ba haihuwa a gidan Umar Faruk har saita mutu." "Yawwa Mama na gode sosai, zanyi maganin shegiyar." *************** Umar Faruk kuma yana can ya tura abokananshi d'aukar Zuby amma yana k'ofar gida tare da Ishaq, ana cikin haka an kawo amarya suka hallaro, nanfa aka fara hayaniya aka shiga da amarya aka bud'e d'akinta aka zurata ciki, saida aka gama bidi'o'i da kwanjil kwanjil sannan mutane aka fara watsewa, anan yan uwan Zuby suka sake bata wasu sinadaran na yak'ar Khairat danta cinye gida, yayin da Zabba'u take addu'ar Allah ya had'ata da Khairat a tsakar gida ta rama marinta. Ganin har zasu tafi bata fito ba yasa suka dinga d'ura mata ashar suna habaici iri iri had'e da kiranta karuwa, to nidai lek'awa nayi d'akin Khairat d'in naga tana jinsu kuma tayi shiru. 😂 _Kun sanfa mutuniyar akwai son casu, can na hangota kwance akan kujera ta danne kunnuwa da masub'urb'ud'ar sauti tana holewarta._ Haka dai aka watse aka bar amarya da ita da halinta, sai kusan 22:45 Umar Faruk ango ya shigo, kai tsaye d'akin amarya ya nufa inda ya zuro k'eyarta gaba izuwa d'akin amarya danya ja musu kunne😂, tun a labule Khairat ta hangi tahowarshi hakan yasa ta cire abin sauraron ta aje, yana bud'e labulen tare da sallama tayi saurin fad'awa jikinshi tare da fad'in "sannu da zuwa." "Sannu." ya fad'a a wahalce saboda k'amshin turarenta ya birkita mishi lissafi. Hannunshi ta kamo suka qarasa shiga ta zaunar dashi akan kujera tare da zama akan cinyoyinshi ta sagala hannunta ta wuyanshi, cike da kissa tace "ka tafi ka barni kana can wajen amaryarka, tun yanzu harna fara kewarka." Saida ya sumbaci nonuwanta dake barazanar fitowa daga rigarta kafin ya lumshe ido yace "da gaske? ashe dama za kiyi kewata?" "Eh mana." ta fad'a tana qara bank'aro gabanta. _Hum😎 duk wacce taso ai ita take zama banza a wajen miji._ Yatsar hannunta tasa tana shafa gefan fuskarshi ta cije leb'e tana wani kakkashe masa ido tare da d'an jujjuya mazaunanta akan cinyoyinshi, hakan kuma yasa take tsokano babbar harkar daga qasa😂, ido Umar Faruk ya rufe kamar zai fashe da kuka yana fad'in "wayyo ni Ummaru na shiga uku, Khairat kasheni za kiyi fa wallahi." Matseta yayi a jikinshi ya tusa kanshi a mamanta dansu suka fi d'aukar hankalinshi, itama matse kanshi tayi tana mishi cakulkuli tana fad'in "kana mutuwa zan sake dawo da kai ai, dan yanzu na fara jin dad'in rayuwata da kai." "Kun gama iskanci na tafi, ko kuma da saura?" 😂😂😂😂😂😂 _Wa yayi maganar nan fan's_? nasan kowa zaice Zuby. Da sauri Umar Faruk ya kalli Zuby dake tsaye yama manta da ita harga Allah, "inna lillahi." ya fad'a tare da d'aga Khairat daga jikinshi ya mayar da ita ta zauna gefenshi ya zura hannu ya janyo hannun Zuby ya zaunar da ita d'aya gefenshi. Saida ya saci kallon Zuby tare da saisaita nutsuwarsa kafin yayi gyaran murya ya fara da " *KHAIRAT*." "Na'am baby." ta fad'a da dafa kafad'arsa, dan tunda ta sauke idonta akan Zuby ta fahimci akwai tazara a tsakaninsu mai yawa. "Ga Zubeida, k'anwarki, kuma ina fata zan samu had'in kanku domin ku fahimceni na fahimceku, dan ta hakane zamu samu zaman lafiya da kwanciyar hankali, Khairat, kece babba, dan haka akwai buk'atar ki kama girmanki ta yanda zaku zauna lafiya, duk da bamu jima tare ba, amma nasan kin fahimci ni ba mutum bane mai son hayaniya da tashin hankali, kamar yanda dukanku kun sanni bana d'aukan raini da rashin hankali, dan haka ina so kowace ta tsaya matsayinta, bana so naga ko naji raini a tsakaninku bare har yakai ga sa in sa ya had'aku wata rana, ina fata kin fahimceni?" Ajiyar zuciya ta sauke ta kalli Zuby tace "Allah sarki, wannan itace Zuby? karka damu baby, insha Allah ba zaka tab'a samun matsala daga gareni ba, kuma zan d'auketa kamar k'aramar k'anwata dan dama bana da kowa." "To da kyau, haka nake son ji dama." "Saike Zubeida, wannan itace Khairat kuma tana gaba dake a shekaru dama kasancewa matata, buk'atata a gareki shine ki kama kanki kema sannan ki d'auketa a matsayin yayarki, nasan Khairat, bata da hayaniya da tashin hankali, dan haka nake rokon da ki kiyaye duk wani abinda zai kawo tashin hankali a tsakaninku, Zubeida a sanin sanin dana miki ke ma...." "Ni masifafiyar ce? ai tun tuni daka fito sak ka fad'a min, da kace kasanta ita ba mai hayaniya bace, kenan nice mai hayaniya? yah Umar wai yaushe ka canza ne haka? da fari ka kirani kuma kazo kuna karuwanci a gabana, amma kuma bai isheka ba shine kake fad'a min matarka ba mai hayaniya bace, to naji saika barni da hayaniyata ni." Kallon Khairat tayi tace "ke kuma, karma kiji dad'i saboda kinji yace na d'aukeki a yayata ke kuma har kike jin dad'i, wallahi bani bake kuma bana da had'i dake da har zaki zama yar uwata, kuma ki sani tashin hankali masifa da bala'i, yanzu kika fara ganinsu cikin gidan nan, dan ba zan tab'a yarda nayi kishi da karuwa ba." A hassale Umar Faruk ya mik'e zaiyi magana Khairat ta rik'e hannunshi d'aya hannu kuma tana shafa qirjinshi tace "ya isa haka baby, ka rabu da ita mana, yarinya ce fa." Tureta Umar Faruk yayi daga jikinshi cikin jin zafi ya cabko Zuby da k'arfi ya fara magana "wacece ke Zubeida da har nake magana kina katseni, yaushe aka haifeki da har zaki d'aga murya akan yawa, fad'a min ina jinki akan me? yaushe wuyanki yayi kauri haka?" Sakinta yayi ya nuna mata kujerar yace "maza zauna malama." Jiki na rawa ta zauna kowa ya zauna wajenshi sannan yace "abinda ki kayi yanzu hauka ne, kuma bana d'aukar irin wannan, akwai kishin da zan iya yiwa mace uzuri a kanshi, amma banda irin wanda ki kayi yanzun, dan haka a kiyaye nan gaba, bana buk'atar tashin hankali da qananun maganganu, zan sab'ama duk wacce ta tayar min da tarazma a gida ba tare dana d'aga qafa ba, dan haka ku had'a kanku shine zaifi muku alkairi dani kaina, dan saida had'in kanku zan iya samun farin ciki, kwantar da hankalinku shine zai zama silar nasarata a rayuwa, da wannan nake mana fatan samun zaman lafiya." Addu'a ya dinga kwaranyowa ta fatan zaman lafiya tare da neman tsari daga shed'an daga garesu, kafin daga bisani ya d'ora da "akan maganar kwana kuma, kamar yanda muka sani ne, zan dinga yin kwana bibbiyu a d'akin ko wacce." Yana fad'a ya fita ya bar d'akin ranshi a b'ace yana tunanin abinda Zuby tayi, Khairat ma ta bishi a sannu bare kuma ita k'aramar alhaki banza a banza😂inji ni fa ba Umar Faruk ba. Juyawa Zuby tayi zata fita Khairat ta rik'e mayafinta ta tako a hankali gabanta ta tsaya, kallonta tayi sosai kafin tace "hum, wai kishiyata , kinyi wasu maganganu d'azu amma bansan ko zaki iya maimaitawa ba? nasan ma ba zaki iya ba domin karyaki zanyi, amma bari kiji in fad'a miki, ni *karuwa* ce kuma ta Umar Faruk, dan haka zan baki shawara kamar yanda na bawa mahaifiyarki, ki koyi karuwaci kema ko zaki iya samun wani kaso a zuciyar Umar Faruk, idan kuma ki kayi wasa, to ki sani kin rasashi kenan har abada, sai dai kiyi rayuwar k'unci a gidan Umar Faruk ko kuma kiyi rayuwar 'yanci a gidanku a gaban mahaifiyarki, ma'ana zawarci." Da hannu ta mata alama tace "zaki iya tafiya, idan kin fita ki turo min baby na rarrasheshi, dan kin b'ata masa rai daga zuwanki gidan." "Dama Mama ta fad'a min baki da kunya, amma ni zan koya miki hankali." cewar Zuby tana shirin fita. Rik'ota tayi tace "au, dama kuna tunanin samun karuwa da kunya ne? ai kawai ki tanadi maganin hawan jini dana ciwon kai, domin daga yau salon bugun zuciyarki zai canza." Tana fad'a ta haye gado ta kwanta ita kuma ta fita daga d'akin ta koma nata, ko kayan jikinta bata cire ba ta kwanta tana kuka saboda bak'in cikin abinda ta gani da idonta. _Ni kam nace zaki wahalar da kanki a banza._ D'akin Mama ya nufa ya samu abinci yaci kafin ya mata sallama ya komo d'akin sahiba😉, tana ganinshi ta sauko daga kan gado ta sake rumgumeshi kafin ta d'ago ta kalli fuskarshi cikin shagwab'a tace "kayi hak'uri baby, ta b'ata maka rai, muje na maka wanka to." Sake rumgumata yayi a jikinshi murya can cikin mak'oshi yace "zaki iya yimin wanka?" "Me zai hana? kaifa nawa ne." Kafeta yayi da ido harta rabashi da kayan jikinshi ta d'aura mishi towel, hannunshi ta kama dan zuwa douche ya rik'e hannunta ya fizgota ta fad'o kanshi, kallon juna suke sosai kafin ya fara magana cikin sigar tausayi kamar zaiyi kuka yace, "Khairat, dan Allah ki fad'a min me yasa kika canza daga yanda na sanki? Khairat me yasa kike min duk wannan kyautatawar? bayan nasan ba sona kike ba, Khairat dan Allah ki fad'a min me kike shiryawa a kaina? dan ina ji zuciyata zata iya bugawa idan har kika gujeni daga baya, ni kaina bansan me nake ji ba, ban kuma san me zance yake damuna ba a kanki, amma dai ina jin bugun zuciyata yana qaruwa idan ina tare dake, sannan ina shiga farin ciki idan na ganki a kusa dani, Khairat nakan ji daban a tare dani idan jikinmu ya had'u wuri d'aya, Khairat ina jin matsanancin kishi a kanki, kuma ina yawan tunaninki kamar yanda kike yawan zuwa min à qwaqwalwata, tunaninki na hanani sukuni, fuskarki takan hanani shak'at saboda yawan ganinta da nake a idona, Khairat, wasu na tunanin na kamu da sonki ne, amma ni kaina na kasa tantacewa sonki nake ko kuma ba haka bane, kinsan me yasa na kasa tantacewa?" Kai kawai ta girgiza masa shi kuma yace "domin ban tab'a shiga irin wannan yanayin ba har saida na had'u dake, a sanadinki ne na fara jin komai na canza min, Khairat, a yanzun in har zan iya fad'in gaskiyar abinda yake raina, to zan iya cewa *ina sonki*, tabbas Khairat *ina qaunarki*, bana jin zan iya rabuwa dake a yanzun, dan Allah kema karki gujeni, nasan ni talaka ne kuma ba zan iya d'aukar nauyinki ba, amma Khairat zanyi iya qoqarina wajen ganin na samar miki duk abinda kike buk'ata, Khairat zan iya bada rayuwata dan ganin walwala da farin cikinki, yanzu abu d'aya nake so naji shine, kema kina sona?" Rarraba ido ta shiga yi tare da had'iyar yawu tana k'yabta mishi ido, abinda za tace masa take tunani, koda bata sonshi tasan dai taji dad'in abinda ya fad'a yanzu, idan kuma ta fad'a mishi bata sonshi to zata rasa duk wani abu da take shiryawa, dan haka mafita d'aya ta nuna itama sonshi take, maye murmushi tayi a gurbin da mamakin kalamanshi suka bayyana sannan ta riko hannunshi sosai ta sumbata kafin tace... "Na d'auka ni kad'ai nake jin abinda nake ji a game dakai, bansan wani irin farin ciki zan nuna ba, Faruk, kayi min abubuwa da dama wanda babu wanda ya tab'a min har iyayena ma, tun daga ranar na fara jin abubuwa daban a game da kai, amma dayake shashasha ce ni, saina kasa fahimtar halin da nake ciki, sai yanzu da naga wata zata shiga tsakanina da farin cikina, naga ba zan iya hak'ura ba zaifi nima na tashi tsaye na nuna maka soyayyata a zahiri." Ajiyar zuciya ta sauke tace "Umar Faruk." Amsawa yayi ta hanyar sake kafeta da ido, dorawa tayi da " *ina sonka*, ina qaunarka, ina sonka so mai tsanani , son da babu wanda zai iya ganin qarshensa sai mahallicin sammai da qassai." Qasa yayi da kanshi yana dariya saboda wani kuntumemmen farin ciki daya tokare zuciyarshi, tabbas ya yarda yanzu ne ya fara soyayya, kuma da Khairat, hannayenta tasa ta tallabo kanshi , abin mamaki ba dariya bace kad'ai harda hawayen farin ciki, ita kanta wani farin cikin ne taji yana nuk'urk'usarta a zuciya, rumgumeshi tayi sosai suka mak'alewa juna kowa kuma hawaye yake zubarwa. _My Khairat ki yarda kawai, kema kin fad'a tarkon guy nan, auntyna Aisha, ina ga maganar team tazo qarshe, mu nemi 'yan adawa mu sasanta kanmu, dan muji dad'in farmakar Hajja Zuby._😉 Tare sukayi wanka kai kace shekararsu arba'in suna zuba love, haka suka fito a towel d'aya kowa ya shafa na shafawa ya murza na murzawa, Umar Faruk na kallon Khairat tana shafa humra takai kala bakwai wacce ta shafa, ta bayanta ya rumgumota ya shinshina wuyanta ido lumshe kafin yace "miye sirrin turarukan nan? danna lura akwai al'ajabi a tare dasu." "Ni kuma ba zan iya fad'an sirrinsu ba wa kai." "Me yasa to?" ya tambaya yana qara tusa kanshi a tsakiyar wuyanta yana shak'ar daddad'an k'amshin. Juyowa tayi da nufi d'auko kayan baccinta ta saka kawai ya sureta yayi kan gado da ita, saida ya kwantar da ita sannan ya sauka ya kashe wutar d'akin ya dawo tare da zame towel d'in jikinshi ya wurgo mata, kan jikinta ya kwanta ya fara lagudarta yana sarrafata son ranshi, to itama fa ba kwance kawai tayi ba aikin ta tayashi yi, duk da ita kanta tasa takai mak'ura kuma tana buk'atar tallafi domin gabanta ya nuna hakan, amma ba zata bari ya shigeta tun yanzu ba, tana jin ya fara bud'e mata qafafu ta tashi zaune a firgice. Janyota yayi jikinshi yace "Khairat, wallahi taimakonki kad'ai nake nema, dan Allah ki barni nayi." Cikin kukan shagwab'a tace "um um, gaskiya ni tsoro nake ji, wallahi ciwo zanji." Da sauri ya rik'ota yace "a'a Khairat, na miki alk'awarin ba zaki ji ciwo ba, wallahi a hankali zan biki." "Ka manta meya faru ne, ba qaramin rauni suka min ba fa, gaskiya ba zan yarda na sake kai kaina mahallaka ba." Janyeta yayi daga jikinshi rai b'ace ya sauka daga kan gadon, kayanshi ya bud'a ya samu doguwar riga ya zura da qaramin wando ya kwanta akan kujera, ranshi kam in yayi dubu ya b'ace dan wani irin kishin bala'i ne yaji ya taso mishi akan su Musa, kawai saiya dinga haskota kwance su kuma suna juyata son ransu, tunani yake yanzu nan wasu sun rigashi isa bakin bodar, tuk'uk'i kawai ke taso masa a zuciya har Khairat ta d'auro towel d'in tazo kusanshi, zata sunkuya kenan ya tsayar da ita ta hanyar d'aga mata hannu yace "dan Allah ki rabu dani, kije ki kwanta." Yanda yayi maganar yasa bata da wani zab'i daya wuce ta koma kan gadon tayi zaune sai kuma ta fara kuka, yana jin shashek'arta kuma duk sai hankalinshi ya watse, alk'awarin daya d'auka na ba zai bari ta zubar da hawaye ba yasa ya koma kusanta ya fara rarrashi, a cikin rarrashin yace "ke kika tsokano min kishina Khairat, dan Allah idan zai yiwu? bana so na sake jin wannan kalmar a bakinki, ina so ki manta nima kuma zanyi qoqari naga na manta, kinji ko shalelen Papa." Murmushi tayi tace "kayi hak'uri to , insha Allah ba zan sake ba." Kwanciya ya gyara mata a qirjinshi ya tofeta da addu'a sannan ya dinga daddab'ata har bacci ya d'auketa, shima ya jima kafin bacci ya d'aukeshi. _To me kuka ce fan's?_ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 💕💕💕 *My Meelat*💕💕💕 _Ina tayaki murnar zagayowar ranar haihuwarki, fatan Allah ya qaro shekaru masu albarka, *jouyeux anniversaire* My mentor._💖 _My sweet and lovely *Hawwer* , ina miki fatan qarin wasu shekarun domin sai dake bugun zuciyar Sameera ke tafiya daidai, *Happy Birhtday* my Hawwer._💖 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣3⃣ Kiran sallah asuba ne ya tashesu, alwala yayi ya nufi masallaci bayan ya biya ta d'akin Zuby ya tasheta, sallah sukayi bayan ya dawo kuma ya d'orawa Khairat karatunta, kamar kullum yau ma jinjina mata yayi sannan ya sake ninka mata wani, suna gamawa wanka ta fara yi bayan ta fito ya shiga, harya fito bata saka kaya ba hakan yasa da kanshi ya shiryata cikin riga da zani mai kamar siket na shadda, d'inkin yayi sosai gashi ya zauna mata a jikin, d'an kwali ta d'aura sannan ya saka mata sark'a da yan kunnai na zinariya kafin ta juyo ta kalleshi tana murmushi tace "nayi kyau?" Saida ya sumbaci goshinta kafin yace "ai fad'a ma b'ata lokaci ne, kin ganki kuwa? kamar k'yank'yasar yau." Dariya tayi ta rumgumeshi tare da sumbatar kumatunshi tace "ka saka min albarka to." "Allah ya miki albarkar baby." ya fad'a yana dariya. "Sakinshi tayi tana d'aukar hijab d'inta tana fad'in "yaufa ba zanje wajen aiki ba, yanzu haka salon zanje amin kitso da kuma gyaran jiki." Shima kayanshi ya fara sakawa yace "wane irin gyara kuma, kina so sai kin fara haukatani da kyawunki ne?" "To ai ba kyawu zan qara ba, gyara ne kawai." Yana gama shirinsa Ruk'ayya ta kawo masa abinci, har zata fita yace "ki kira min Zubeida." "To yaya." ta fad'a tana ficewa daga d'akin. Da kanshi ya zaunar da Khairat a gefen hagunshi jim kad'an kuma Zuby tayi sallama, da hannu ya mata alama data zauna kusanshi , saida ta duk'a har qasa tace "ina kwana yah Umar." "Lafiya kalau Zubeida, kin tashi lafiya?" "Lafiya lau." "Ya kwanan bak'unta kuma?" Sai lokacin kad'ai ta tashi daga durk'uson ta zauna inda ya nuna mata tana fad'in "yah Umar ai gidan nan ba bak'ona bane." "Kuma fa hakane." Jin shiru yasa yace "banji kin gaishe da ita ba?" D'an karatun tanutsun da tama kanta ne a daren jiya taji yana neman sub'ucewa saboda b'acin rai, cikin harare harare tace "ina kwana." ba tare data kalleta ba. Khairat kam data fita iya karatun zaman duniya saita saki fuska duk da irin k'uncin da take ji da kishin dake taso mata tace "lafiya lau yer uwa, kin tashi lafiya?" Shiru ta mata hakan yasa Umar Faruk cewa "a gaskiya ba haka nake son gani daga gareku ba, akwai bukatar ku canza tun kafin lokacina ya fara aiki." Yana fad'a ya kalli Zuby yace "kece qarama , ki zuba mana abincin." "Ruk'ayya takai min nawa a d'akina." ta fad'a a daqile. "To zan fad'a mata daga yau tare zamu dinga ci, yanzu ki zuba mana." Khairat ce tayi saurin cewa "lah baby, ka barshi ni zan zuba, ya zaka saka amarya aiki daga zuwanta." tana fad'a ta janyo kayan ta had'a musu tea kamar yanda taga Umar Faruk yayi jiya, sannan ta bud'e plate d'in soyayyan k'wai da dankalin turawa, sai kuma miyar dake cikin kwano ta naman rago, tana gamawa ta dafe qirjinta tare da sauke ajiyar zuciya, kallonta Umar Faruk yayi yace "gajiya ki kayi?" Cikin dariya ta dafa kafad'arshi ta rad'a masa cewa "wallahi na zata ba zan iya ba, na gode daka koya min jiya." Shima dariyar yayi Zuby kam ta gefen ido ta kallesu, shiya fara saka hannu kafin yace "to bismillah." Nan suka fara ci ba mai magana har suka gama, Zuby ce ta fara tashi ta fita dan zuciyarta barazanar tarwatsewa take, shima dai jakarshi ya dauka haka ma Khairat kafin suka fito a tare, saida suka shiga d'akin iyayensu suka gaishe dasu kafin suka fito suka tafi, yauma a motarta suka tafi yana tuk'awa , saida ya ajeta salon sannan ya wuce bayan tace ya bari zata koma gida a taxi. Kitso akan fara mata yayin da tasa aka makala mata sabbin akaihu, sai dai wannan karan ba masu tsayi bane sosai yan madaidaita, tasa aka lullub'esu da jan lalle mai ja sosai, bakin lalle tasa aka mata ga hannuwa kawai saboda har yanzu wanda aka mata bai gama zubuwa ba, gyaran fuska aka mata tare da gyaran gira, masha Allah kamar balarabiya ta fito, dogayen riguna ta gani masu kyau da kwalliya ta siyo har kala shida, sannan ta d'auko hanyar dawowa gida. ************* Tun fitarsu Zuby suka shiga d'aki ita da Ruk'ayya tana sank'ama mata tambayoyi ita kuma tana kakkaucewa wajen bata amsar, a qarshe kuma cewa tayi "itama tana girki ne?" "A'a, tunda tazo bata tab'a girki ba." cewar Ruk'ayya. "To kenan me take? sai dai a dafa a bata taci." "To ai kusan yanzu itace ma ke ciyar damu, tunda da kayan abincin data siyone muke anfani dasu." "Me? wai kina nufin abincin da naci ma d'azu a cikin wanda ta siyo ne?" "Qwarai kuwa." cewar Ruk'ayya cike da mata kallon baki da tunani. "Tabb', bari yah Umar d'in ya dawo, wallahi ba zan sake cin abincin wajenku ba, kayan abinci kawai zai siyo min na dinga dafa nawa nima." Cike da iya shege Ruk'ayya tace "amma da ice zaki dinga dafawa ko?" "Kawai ma bayan naga harda gas gareku." ta fad'a tana hararanta. "Toshi gas d'in dashi kika taho jiya? ai shima ita ta siyoshi, dan haka ki sake tunani ma dan wannan ba mafita bace." "Keni dallah tashi ki bani wuri." korarta tayi daga d'akin ita kuma ta kira Mama ta fad'a mata halin da ake ciki. Nan Mama tace "to bari kiji in fad'a miki, wallahi saikin tashi tsaye sosai, inba haka ba kin shiga uku a wannan gidan, kuma abinda za kiyi yanzu shine, da zaran ya dawo ki fad'a mishi ya siyo miki kayan abincinki da qaramin rechau wanda zaki dinga aiki dashi, tunda kinga nan da kwana biyar zaki fara zuwa ecole (school), kuma wallahi karki yarda ya fad'a miki wasu maganganu, ki dage saiya siya miki, kuma ki tabbatar kinyi aiki da abinda na baki jiya." "To Mama, amma ai ita bansan yanda zanyi na bata tasha ba." "Saboda ke ba mace bace? kisan duk irin dubarar da za kiyi tasha, inba haka ba wallahi data fara haihuwa kafin ke, kin shiga uku." Da haka sukayi sallama tana tunanin hanyar da za tabi wajen saka ma Khairat wannan maganin. ************** *12:15*, Khairat ta shigo gidan ba tare da sallama ba kamar yanda ta saba, ganinta da babbar leda a hannu yasa Ruk'ayya taje da sauri ta karb'i ledan tana fad'in "sannu da zuwa aunty Khairat." Saratu da Zuby na zaune waje d'aya ko kallonsu ba tayi ba, yaran ma duk suna zaune da sannu suka bita , jakarta ta bud'a ta fito da d'an qaramin kwalin chocolat taje inda yaran suke zaune duk rabawa kowa harta qare, godiya suka mata Zuby kuma ta bita da kallon banza, ita kuma ta wuce d'akinta saboda iyayen duk suna d'aki, Ruk'ayya ce ta bud'e k'ofar ta shigar mata da ledar har ciki, aje jakarta tayi tare da hijab tana kallon d'akin an kitsashi ba kamar yanda suka barshi ba, kallon Ruk'ayya tayi tace "Ruk'ayya waike ba kya gajiya da aikine, naga ko ecole ba kya zuwa sai d'ora girki da shara, a haka zaki qarene?" Cikin dariya tace "aunty kenan, ai wannan aikin shine aka saba mana dashi, duk 'yan uwana mata wanda sukayi aure saida sukayi wannan aikin, kuma karatu na gama ne shi yasa bana zuwa, na addini kad'ai Baba yake qaramin wani lokaci yah Usman ko yah Umar, amma yanzu dai mun daina da yah Umar." "Me yasa?" ta tambaya lokacin da take b'alle bras d'inta. "Tunda yayi aure ne." Towel ta d'aura a qirji ta nufi k'ofar fita tana fad'in "ki bud'a ledar nan dogayen rigunane ki d'auki wacce ta miki." "Wayyo aunty Khairat na gode sosai, Allah ya saka da alkairi." Bud'awa tayi sai dai bata tsaya zab'eba kawai ta d'auka ta fita cikin farin ciki, Zuby na ganinta taja dogon tsaki tace "aikin banza, ashe dai gulma ce tasa daga ganinta kika tashi harda wani karb'an abun hannunta kamar uwar data haifeki." B'ata rai Ruk'ayya tayi tace "Zuby, ki fito idona na rufe, ba ruwana dake baruwanki dani, kar kisa muyi abinda za'a mana dariya, tom." "Nak'i d'in marar kunya, kenan nice za kima rashin kunya dan kinga daidai muke dake? to ko kina so ko ba kya so nima matar yayanki ce, kuma na tabbata ni ya fara sani dan haka na fita kusanci dashi." Wani dogon tsaki Ruk'ayya taja kafin tace "kishin ne haryake neman haukataki , ya muna magana zaki canza mana maudu'in da muke kai." Tana fad'a bata tsaya sauraranta ba tayi d'aki ta nunawa Mama rigarta, godiya tama Khairat tare da saka albarka, dan tasan kyauta ce ta bata ba rok'a tayi ba. **************** Koda ta fito daga wanka kwalliya sosai tayi sannan ta shirya cikin d'aya d'aga cikin rigunan data siyo, nanfa ta d'auki k'yali da shek'i ga gyaran data sha, gama shirinta ba wuya kuma taji dumin Umar Faruk a tsakar gidan, d'an kwalin rigar ta yane kanta dashi ta feshe ko ina da turare sannan ta tsaya tana jiran shigowarshi. Shi kuma yana shigowa yaji wani sanyi ya ratsashi saboda ganin d'akin bud'e ya tabbatar da sanyin idaniyarshi ta dawo, Zuby ce tace "sannu da zuwa yah Umar." "Yawwa,sannu da gida." ya fad'a tare da yin sama da Fateema. "Ango kasha k'amshi." cewar Saratu. Yana kallonta yace "ke ko ba kya gajiya da tsokana, to wane k'amshi kuma?" "Au, nice zan fad'a maka wane iri? ai kai kafi kowa sani." "Kinga da surutun nan, ki tashi ki kaimin ruwan wanka zafi miki ki samu lada." Hararanshi tayi tace "bana so, sai yaune ka tuna dani kenan?" Waro ido yayi yace "lah, ladar ce ba kya so? lallai ma matar nan, gaba d'aya ba kya kula dani yanzu." "Haba Ummaru, 'yan aljanna biyu ne fa a tsakiyarka, ai kuwa kaga ba buk'atar na zama ta uku a bayansu." Wani shu'umin kallo yama Zuby wacce itama shi take kallo yace "ga d'aya nan a kusanki ma, amma ya banga d'ayar ba?" Da hannu Saratu ta nuna mishi d'aki tace "to ai kasan basan fitowa take ba, ina jin tana ciki tana shirin tarbanka, dan naji qarar ruwa alamar tana wanka kenan." Cike da zolaya yace "toke me kike anan? baki je kiyi shirin tarban naki mai gidan ba." "Ni! rufa min asiri, mu ai tsohine mun barma 'ya'ya da k'annanmu." *Irin wannan tunanin shi ke kashe mata dayawa ta hanyar nakasasu, kice ke kin tsohuwa saboda kawai kinyi haihuwa uku hud'u, mijinki kuma yana buk'atar ganinki cikin kyakyawan yanayi da shiga, koda ke kika haife duniya, wallahi saimun gyara sosai idan har muna son ganin daidai, a duniya karki yarda namiji ya rainani saboda rashin tsaffa da kama jiki, daya rainaki ta wannan hanyar kin gama shiga tara.* Wucewa kawai yayi bayan ya aje Fateema, tashi Zuby tayi tabi bayanshi hakan yasa ya juyo ya kalleta, cikin jin kunya tace "magana nake so muyi." Baice mata komai ba sai sauya akalarshi da yayi ya nufi d'akinta, yana shiga ya zauna a bakin gado ita kuma ta tsaya, kallonta yayi ganin bata zauna ba kuma ba tace komai ba, kammo hannunta yayi ya zaunar da ita akan cinyarshi d'aya tare da zura hannunshi ta bayanta ya rumgumota, d'aya hannunshi yasa ya rik'o hannunta yana wasa da yatsunta ya qurawa fuskarta ido yana kallo, ita kam kunya ce ta rufeta hakan yasa tayi qasa da kanta ta kasa had'a ido dashi, cikin taushin murya yace "ina jinki, kince za muyi magana kuma kinyi shiru." Wala-wala ta fara da ido tana tunanin yanda zai fahimceta idan ta fad'a masa, tasan halin Umar Faruk sarai, zai iya baud'ewa ya kuma bita da masifa, sumbar daya watsa mata a wuya yasa ta dawo daga tunani, hannunshi yasa cikin rigarta ya fara wasa da cinbiyarta, sake maimaita mata yayi "ki fad'a mana ina jinki." Hannu tasa tana shafa wuyanta tana fad'in "yah Umar dama, nan da kwana biyar ne zan fara zuwa ecole, to kuma ni ba wani cin abinci ba nake sosai, shine nace da zaka siyo min nawa kayan abincin saina aje." Shiru tayi tana d'an satar kallonshi dan ganin yanayinshi, shi kuma shiru yayi yana tunanin abinda ta fad'a, tabbas yasan wannan ba tunaninta bane, amma kuma ba matsala bane tunda ko Saratu itama wani lokacin ita kad'ai take abincinta, dan haka zaiyi yanda take so kodan gudun magana. Fuskarta ya shafa yace "hakan ya miki?" Kai ta d'aga alamar eh tare da fad'in "eh yah Umar." "To karki damu, an jima zan siyo miki kayan abincin, abinda ban siyo ba kuma saiki fad'a min saina baki kud'in ki qarasa siyowa." Ko kad'an ba tayi tunanin haka ba hakan yasa tayi murmushi tace da cewa "na gode yah Umar." D'agata yayi daga jikinshi ya mik'e tsaye yace "ba komai." Matso da ita yayi kusanshi yace "ba kiyi kewata ba ko?" "Kai yah Umar." ta fad'a tana rufe fuska wai ita kunya. Janye hannayen nata yayi yana kallon fuskarta yace "to naji, in dai ba kiyi kewata ba karki sumbaceni, amma idan kinyi ki sumbaci bakina." Zuro mata fuska yayi yana jiran yaji saukar sumba, a tunaninta ta ballagazar da kanta sau d'aya dan haka ba zata qara ba, dan haka kawai ta fito daga d'akin ta baroshi tana dariya, dan gani take ya fad'a tarkonta, yana ganin haka ya fito shima kai tsaye d'akin habibiya ya wuce. Da sallama ya shiga kamar yanda ya saba, amma saiya kasa shiga ciki yana kallon Khairat dake tsaye tana sakar masa tsadadden murmushi, ganin ya tsaya yasa ta karasa ta janyo hannunshi ya k'arasa shigowa ciki, saida ta sakar masa kyakyawar sumba a baki tare da wata a goshi kafin tace, "Ya kake kallona haka?" Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi kafin ya lumshe idonshi ya kuma bud'e a kanta yace "dole na kalleki, a gaskiya baby dana rasaki da nayi asara babba, sai yanzu nake qara fahimtar sa'ata a rayuwa." Wani murmushi zaka gane kurenka ta masa kafin tace "ai dukanmu ne masu sa'a a rayuwa." "Amma ba kamar ni ba." ya fad'a yana rumgumata jikinshi. "Haka dai kace." ta fad'a itama tana qara shigewa jikinshi. "Kema masallaci zaki je?" ya tambaya yana kallonta. "Meka gani to?" "Naga kema kinyi kwalliya sosai ga kuma doguwar riga, dan sau d'aya na tab'a ganinki da doguwar riga irin haka, shima a lokacin bikinki." Duka ta kai masa a qirji tana fad'in "kaji mutum wai bikina, kace bikinmu, shagali da wani ango, kuma d'aurin aure da wani ango." Dariya yayi yace "dama fa ara mishi ke nayi na wannan lokacin kawai, amma ba kiji yanda zuciyata ke tafasa ba." Da kallo ta bishi tana fad'in "ashe dama ka jima kana sona, amma shine a lokacin dana mareka ka kasa hakura saida ka rama, ba kaji yanda naji zafi ba a ranar, har saida hannunka ya kwanta a kumatuna." Dariya yayi ya fara cire kayansa yana fad'in "to ai ko yanzu idan kika min laifi ba zan tsaya wasa ba wajen zabgeki da mari, kawai dai nasan yanzu idan na mareki a kumatu , to ni kuma zanji zafin a zuciyata ne." Mak'ale masa tayi a baya tana kukan shagwab'a tace "hamago kawai, wallahi saina rama marin soyayyata daka min." Juyowa yayi da ita gabanshi yana kallonta yace "in dai zaisa kiji dad'i to na amince ki rama." Yana fad'a ya bata kumatun da nufin ta rama, Khairat kam saida ta share 'yar qwallan data taho mata dan sosai taji zafin marin daya mata a ranar, hannu ta d'aga iya k'arfinta dan dama ce ta samu da ba zata bari ta wuceta ba. Kamar saukar aradu Umar Faruk yaji saukar wani gundumemen bahagon makahon.....😂 _Wallahi kinmin daidai tawajena, hi yasa nake sonki._ *Wasu na mamakin Umar Faruk ya kwana a d'akin Khairat, to ai ban gama sati d'aya na d'akin Khairat ba, dan haka ku tayani lissafi, yau juma'a a labarin Khairat da Umar Faruk, kenan gobe asabar ne zata cika sati, lahadi kuma sai kuzo mu rakashi d'akin amarya Zubysss.😂* _Koda yake naga mutuniyar ma bata da masoya._ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bansan me zan iya cewa masoyana ba, hak'ik'a kuna sakani farin ciki, comment d'inku na nishad'antar dani, tsakanina daku sai dai ince Rabbi ya bar qauna._ 💞💕💗 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣4⃣ Kamar saukar aradu Umar Faruk yaji saukar wani gundumemen bahagon makahon kiss a kumatunshi, ji kake "Muahhhhhhhhh." 😂😂😂😂😂😂 Sakin fuskarshi tayi data rik'e tace "idan kaga hannun Khairat ya tab'a fuskarka yanzu, toka sani shafata ne za tayi." D'aukarta yayi ya dinga juyi da ita a tsakaiyar d'akin yana dariya yana fad'in "har kinsa zuciyar maza ta tsinke, na d'auka fa marina za kiyi, ashe dai sanin da nayiwa Khairat." Itama dariyar take kafin tace "kaga saukeni kaje ka shirya lokaci na tafiya." Sauketa yayi ya qarasa cire kayan jikinshi kafin ya shiga wanka, koda ya fito ta fito mishi da kayan da zai saka, da taimakonta ya shirya tsaf cikin farar shadda da hula da takalmi, kallon kanshi yayi a madubi yana qara daidaita hularshi, saurin d'auke hular tayi a kanshi ta d'ora a kanta tace "kenan ban iya sakawa ba? shine har kake gyarawa." K'ugunta ya janyo ya had'a da nashi yasa hannayenshi ya fara daidaita mata zaman hular a kanta, murmushi ya sakar mata yace "dubi madubi kiga yanda kika gama had'uwa, shi yasa nace miki ni mai sa'a ne." A tare suka kalli madubin yana bayanta ita tana gaba, wani irin bala'in kyau ne sukayi ga matuk'ar dacewa da junansu, wayarshi ya ciro a aljihu ya d'auketa photo ita kad'ai sannan ya musu tare, cire hular yayi ya mayar a kanshi yana fad'in "kinsan me zai faru?" "Saika fad'a." ta fad'a tana d'anewa a bayanshi. Goyeta yayi yana fad'in "kawai kizo muje tare, saina biya na ajeki gida wajen Mamie, idan na dawo saina biyo na d'aukoki." Da k'arfi ta wuntsilo ta sauko daga bayanshi tana fad'in "da gaske baby, Allah kuwa ina son zuwa, ina kewar Mammie." Kumatunta ya kama yace "sosai ma, tukwicin wannan kwalliyar ne na bayar." Wajen aje jakunkunanta ta nufa ta d'auko qarama ta hannu baka mai walk'iya ta saka wayarta, Umar Faruk na kallo ta bud'a wata jakar ta kwaso kud'i ko k'idayawa ba tayi ba ta zuba a jakar, kallonshi tayi tace "na shirya, zamu iya tafiya?" Da ido kawai ya mata alama sannan yace "d'auko min sallaya." D'aukowa tayi ta rik'e a hannunta, shi kuma ya kama hannunta suka fita, saida ya saki hannunta ya rufe k'ofarsu hakan kuma yayi daidai da fitowar Abbakar shima ya shirya zai tafi, Zuby da Saratu kam kallon ikon Allah suke, wato masallacin ma tare zasu tafi kome? anya Umar Faruk bai haukace ba😉 ku shinshina kuji, cikin taushin murya Khairat tace, "Baby, tunda ga yah Abbakar ai saiku tafi tare ko." Kallonta yayi ya juya ya kalli Abbakar dan baiga fitowarshi ba, cike da k'aunar juna Umar Faruk yace "abokina ka jirani saimu tafi ko?" Abbakar dake nad'e sallayar hannunshi ne yace "amma ai naga kamar tare zaku fita? taya zan shiga wannan harka ta amare." Wani wawan tsaki da Zuby taja tare da tashi tabi ta gaban Khairat ta wuce d'akinta, Umar Faruk kam ko kulata baiyi ba yace "kaga muje, dama akwai maganar da nake so muyi da kai." Saratu dake zaune acan tace "Allah yasa dai ba cewa za kayi ya qara aure ba." Kafin suyi magana Mama Sa'a tace "ke kuma shine matsalarki, kenan mu nan mutuwa mukayi da muke zaune da kishiyoyin?" Umar Faruk ne yace "rabu da ita Mama, aure ai ya zama dole yah Abbakar ya qara, tunda ita yanzu ta tsufa." "Kai tsufan lafiya, waya fad'a maka?" cewar Saratu. Saida ya kama hannun Abbakar suka nufi hanyar fita yace "da bakinki kika fad'a, ko awa d'aya ba ayi ba." Khairat ma bayansu tabi ko murmushi ba tayi ba bare dariya, Mama Sa'a kuma harda daga murya tana fad'in "saikin dawo 'yar albarka." "Mtsssss, tusa kai ba kwarjini." cewar Mama Maimuna dake zaune akan tabarma. A hassale Mama Sa'a tace "dawa kike Maimuna? ni kike fad'awa haka? ni tsararki ce da zaki shiga harkata?" "Eh, dake nake kiyi abinda za kiyi, aikin banza kawai, duk kibi kina wani nanik'ewa yarinya ita kuma tana wulak'antaki, kawai saboda tsinannan kwad'ayi." Aifa tsaye aka mik'e suka fara surfa bala'i Mama Umar Faruk dasu Saratu Ruk'ayya hak'uri kawai suke basu, dan duka mazan sun tafi masallaci Zuby kuma naji tayi banza dasu, saida suka kusan dakuwa sannan suka hak'ura kowace ta shiga d'akinta, amma duk da haka kowace na jefo magana daga d'akin nata. ************** A mota kam Abbakar da Umar Faruk hira suke sosai data shafesu, Khairat na baya tana jinsu amma tana latsa wayarta har suka isa, tare suka fita da Umar Faruk suka tsaya a k'ofar gidan, saida ya d'an saci kallon Abbakar dake mota kafin ya shafi fukarta yace "ki gaishe dasu Mamie, idan muka taso zan biyo." Cikin shagwab'a tace "amma fa nidai daka barni har zuwa dare, kaga idan ka dawo daga wajen aiki sai kazo muje." "Nak'i d'in, ina buk'atar ganinki a kusa dani." "An gama ranka shi dad'e , yanda kake so haka za ayi." Tana fad'a ta matsa kusa dashi ta sumbaci bakinshi tana kallonshi ta kece da dariya, "meye?" cewar Umar Faruk. "Ba komai, saika dawo." duk tayi maganar ne a cikin dariya tare da tura k'ofar gidan ta shiga. Mai gadi dake alwala cikin shirinshi na masallaci ya taso da nufin gaisheta ta daga masa hannu tare da tsayawa tace "kaci gaba da alwalanka, ba'a so ana tsayawa idan ana alwala, komai mahimmanci abu kar yasa ka dakatar da alwalarka, musamman ma idan abun ya shafi harkar duniya ne." Tana fad'a ta shige ciki shi kuma ya biya da kallo tare da tunanin yaushe Hajia Khairat ta zama Ustaza haka, yauma farin ciki sosai Mamie da Mammie sukayi, musamman data fad'a musu shiya kawota kuma yace zai biyo idan ya taso, hak'ik'a sunga shiriya sosai a tare da yarsu, kuma sunyi farin ciki marar misaltuwa." ************* Yana shiga mota ya tayar suka wuce, Abbakar kam kallonshi yake yana dariya, ganin dariyar tayi yawa yasa kalleshi yace "wai miye haka dan Allah? ya zaka sani a gaba kana dariya." Yanda yayi maganar yasa ya fahimci rai zai iya b'acewa dan haka yace "kalli madubi ka gani." Gyara madubin yayi ya kalli kanshi a ciki, ganin bakinshi yayi ja kamar yasa jan baki yasa ya fahimci me yake wa dariya, a lokacin kuma ya fahimci dariyar da Khairat take masa, lotus ya d'auka a motar ya goge bakinshi yana hararan Abbakar yana cin magani, girgiza Abbakar yayi yace "Umar Faruk kenan, kamar ba kai ba wallahi duk ka canza." "Kaga nifa akwai maganar da nake so muyi da kai." "Ina jinka." ya fad'a yana gyara zama. "Dama wata tafiya ce ta taso mai mahimmanci, kuma Khairat tace mahaifinta yace dole sai dai mu tafi tare, in kuma banje ba ba zasuji dad'i ba, ni kuma harna ce mata na amince, saboda akwai wani laifi da nayi mata tace zata fad'awa Baba, saboda haka yasa nace na amince, amma ni gaskiya har yanzu bana jin zan iya tafiya tare da ita haka kawai a dinga nuna ni a gari." Saida ya gama nazartarshi kafin yace "to ita dai rayuwar duniya da kake gani inka biya ta abinda mutane zasu fad'a to babu inda zaka je, sannan a matsayinka na mijinta kuma kace zaka, amma daga baya kace a'a hakan zai iya tab'a darajarka da mutuncinka a wajenta, iyayenta kuma tunda suka ce suna buk'atarka a wajen, tofa akwai buk'atar son ganinka ne a wajen, dan haka ni ina ganin kawai ka bita ku tafi tunda dai ba siyar da kai za tayi ba, matsala d'aya ce kawai nake tunanin za'a samu." "Matsalar me kenan?" "Zubeida mana, da ace kafin ta tare ne, amma a yanzu data tare kuma na lura kan yarinyar yana rawa, bai zama lallai ta amince ka tafi ba." "Nima yaya nayi wannan tunanin tun kafin kayi, amma da yake tamin alk'awarin idan har mun kwana biyu to ba zamu wuce uku ba, a lissafina ranar talata ne tafiyar ta kama, daga gobe kuma kwanan Khairat zai qare, kaga kenan a ranar da zan koma d'akinta ne za ayi tafiyar, kenan ko an shiga kwanan Zuby to kwana d'aya ne." "Eh to da sauk'i idan hakane, dan haka ka fara shiri kawai ni zanji dasu Baba, sai kuma ka nemi izinin matarka." "Izini kuma? haba dai, kamar itace mijin." "A wannan qadamin kam kusan itace, dan ka sani in bata amince ba ba zaka tafi ba, idan kuma ka tafi bada amincewarta ba, tofa ka sani ranar gobe Allah zai tsayar da kai a gabanshi." "To naji, Sheik Abbakar." "Sheik Umar Faruk dai, kuma kayi k'ok'ari kafin ku dawo kuzo mana da babban tsaraba." Dariyar da yake yasa yace "wane irin k'ok'ari kuma, wace irin tsaraba?" Cikin rad'a yace mishi "baby " Bushewa sukayi da dariya harda tapa hannu kafin Umar Faruk yace "baka da dama wallahi, taro ne fa zai kaimu ba lune da miel (honeymoon) ba." Da haka suka isa masallaci kamar wasu abokanai suna hirarsu cikin raha, saida aka gama hud'uba kafin akayi sallah daga nan kuma suka dawo tare suka komo gidansu Khairat dan d'aukarta kamar yanda yace. ***************** Suna zuwa tare suka shiga da Abbakar har ciki, a lokacin masu aiki na k'awata wajen cin abinci da kalolin girke girke, Khairat da fitowarta kenan daga d'akinta ta gama sallah ta dako da gudu ta rumgume Umar Faruk, "sannu baby , har kun taso?" Kasa aiwatar da komai yayi saboda fitowar Mamie itama daga d'aki wanda Mammie dama tana zaune a falon, abinka ga yan bariki😂 ba wanda yaji wani abu, sai Umar Faruk daya ji kunya ta rufeshi, suna shirin zubewa qasa dan kwasar gaisuwa Mamie ta qaraso da sauri ta dafa kafad'un Umar Faruk duka biyun tana fuskantarshi tace "a'a a'a, haba d'ana, ai ka wuce wannan a gidan nan, kaima fa d'an gidan nan ne." Hannunshi ta rik'e tayi hanyar wajen cin abincin dashi tana fad'in "muje ga abinci an gama kuci." Umar Faruk dai kanshi na qasa ya kasa kallonta sai Abbakar dake kallon falon irin tsari da dukiyar da aka zuba, da kanta taja mishi kujera ya zauna ita kuma mai aiki taja mata ta zauna, Khairat ma da Mammie duka sun zauna, Biba da Saude ne suka bud'a kwanukan suka fara zuba musu abincin, suna gamawa suka koma mafakarsu su kuma suka fara cin abincin. Ba ruwan Khairat haka kawai take jin son Umar Faruk na gaskiyar na shirgarta, da kanta take d'ibar abincin tana saka mishi a baki saboda taga baya ci, haka yasa ya fara diba kad'an kad'an yana ci, Khairat d'in da Mammie kuma hira suke sosai irin na kaka da jika , Abbakar dai kallon ikon Allah yake yana qara ganin girman Khairat, dan inba mai hak'uri ba babu ta yanda za ace kana rayuwa cikin wannan daular kamar a masarauta, abinci ma na rana kana cin kusan kala uku zuwa hud'u amma ka yarda ka fara rayuwa a gida kamar nasu, haka ma a wajen Umar Faruk abinda yake rayawa kenan a zuciyarshi tare da sake jaddada irin taushin zuciyar Khairat, lallai baka sanin asalin mutum saika zauna dashi sannan zaka fahimceshi. Suna kammalawa kafin su tashi Mamie ta kalli Khairat tace "ki tashi kije ki shirya kizo ku tafi." A shagwab'e ta kalli Mamie tace "to Mamie." Umar Faruk ne yace "a'a Mama, ku barta kawai ta zauna, naga kunyi kewarta sosai, idan na taso daga aiki zan biyo saina d'auketa." Cike da farin ciki ta kalleshi tace "da gaske baby? gaskiya naji dad'i." Mak'ale wuyanshi tayi tare da janyoshi kusanta ta sumbaci kumatunshi tare da fad'in "na gode baby." Mammie dake kusan Khairat ce ta zura hannu ta kama kumatunshi tace "yaron kirki, gaskiya ka kyauta, dan dama muna so muyi shirye shiryen tafiyarmu a gabanta." Ture hannunta Khairat tayi tana fad'in "kuma shine saikin tab'a min miji , nifa bana son haka." "Allah sarki, yo mijinki ko mijina? kaji min yarinya kai, kawai dan na ara mikishi saiki wani zak'e dayawa." Kallon Umar Faruk tayi ta kalli Mammie tace "zak'ewa ma nake? to ai mijin naki ne ke rawar qafa a kaina." "Kaji wani d'aurin duniya kuma, to nidai ban gani ba, kuma nasan yafi sona." "To ai gashi nan ki tambayeshi kiji." Khairat ta fad'a tana nunashi da hannu "Ba buk'ata, danni zai zab'a, bana so kiji kunya a gaban mutane." Cikin taushin murya cike da jin kunya Umar Faruk yace " gaskiya ne, za tasha a wajenki." Mammie kam bushewa tayi da dariya had'e da yiwa Khairat gwalo, turo baki tayi tana kallon Umar Faruk, shi kam kasa kallonta yayi saboda wutar tartsatsin da yake ji a kanta, haka suka mik'e gaba d'ayansu zasu tafi, bayan sunyi sallama Mammie tace "nasan dai sai mun had'u a lokacin tafiyarmu ko? "Insha Allah." ya fad'a kawai. "To Allah ya nuna mana." "Ameen." suka amsa. A hankali Khairat ta taka musu har zuwa k'ofar d'aki sannan suka tsaya, sumbatar bakinshi tayi tare da kumatunshi kafin ta kalleshi tace "Allah ya tsare, saika zo." Su Mamie dake hangensu yasa ya d'an shafi fuskarta kawai yayi gaba, suna fita suka d'auki hanya saida ya aje Abbakar gida ko shiga baiyi ba ya juya ma'aikata dan lokaci yayi sosai, sai dai zuciyarshi ta qara narkewa da tsananin son Khairat, haka ya koma duk baijin dad'in aikin saboda manyan kayan dake jikinshi, ga kuma motsi da k'amshin Khairat daya isheshi duk sanda ya motsa, ji yake kamar tana jikinshi ko kuma tana sumbatartashi, a haka dai ya gama aikin a daddafe har aka tashi. Bai wuce gida ba har saida ya tsaya ya siyawa Zuby kayan data buk'ata kafin ya wuce gida, yana isa ana kiran sallah magrib hakan yasa yana shiga d'akinta ya aje mata kayan ya fito yayi alwala cikin gaggawa ya tafi masallaci, bai dawo gidan ba har saida akayi sallah isha'i saboda lokacin qurarre ne kuma suna tare da Ishaq suna hira, suna gamawa ya shigo gidan saida ya fara shiga wajen Baba suka gaisa kafin ya shiga d'akin Mama da sauran iyayen, yana fitowa ya wuce d'akin Zuby. Ya samu tana nad'e sallayar da tayi sallah, abinda ya qona masa rai da haushi shine, d'akin dai tsaf dashi sai kamshin turaren wuta amma kayan jikinta, tun atamfar safe ce daya fita ya barta da ita ya kuma dawo ya sameta da ita, kuma yanzu ma ita dai ce, ya d'auka kafin ya dawo daga masallaci zai samu ta canza, amma ina alamu dai na ba tayi wanka ba tun na safe, zaune yayi a kukerar robar dake fuskantar gadon ya kalleta fuska ba yabo ba fallasa yace, cike da ladabi tace "sannu da zuwa." "Yawwa, sannu? ya gida?" "An gode Allah." Aje sallayar tayi ta tsaya tana kallonshi, a d'an dak'ile yace "zauna mana." Zaune tayi bakin gadon tana kallonshi shima wuyanta yake kallo dake tsattsafo da zufa , a shak'e yace "kin duba kayan?" "Eh yah, na duba." "To miye babu a ciki?" Cikin sanyin murya tace "eh to, kusan abinda babu kad'an ne gaskiya." Da d'an k'arfi yace "to yanzu kamar nawa zai isheki ki siyo abinda babun?" Nanma a ladabce tace "eh to, ko nawa ka bayar ma zai isa." D'aga gira yayi sama ya d'an zame daga kan kujerar yasa hannu aljihu ya fito da kud'i, jikka biyar biyar guda biyu ya bata yace "gashi, sai kiyi manage dashi dan kinsan nauyi dayawa ne a kaina." "An gode Allah ya saka da alkairi." ta fad'a a sanyaye. Sauran canjin ya mayar aljihu kafin ya sake gyara zama ya kalleta sosai yace "ina son yin wata muhimmiyar magana dake, ina fatan zaki bani hankalinki kuma ki fahimceni?" "Ina ji yah Umar." "Zubeida, akwai wani babban taro da aka shirya a Germany, taro ne na manyan mutane wanda zai had'a da iyalensu, mahaifin Khairat na d'aya daga ciki, kuma ya gayyaceni a matsayina na surukinsa, tafiyar zata iya d'aukanmu kwana biyu zuwa uku, shi yasa nake neman alfarmarki kwanan d'ayan, domin zai iya yiwuwa na shiga cikin kwananki domin kinsan tafiyar hali, kosu Mama basu sani ba domin ina so na kammala daku iyalina, ina fatan zaki min wannan alfarmar ki bani kwananki d'aya tak." Cikin mamakin kalamansa tace "tafiya kuma, har qasar waje, amma kuma kai yaya ka amince ka tafi? ba ka tsoron ko wani abu aka shirya maka." "Me kuma za'a shirya min? tare fa da Khairat zamu tafi." "Darammm." taji gabanta ya fad'i, cike da kasa b'oye abinda ke ranta ta mik'e tsaye tace "uhum, yanzu naji magana, kace dai tare da karuwarka zaku tafi, wato harta bud'e maka idon da har kake tunanin fara biyarta a duk inda tayi ko? yah Umar wai yaushe ka zama haka ne? gaba d'aya ka canza kamar ba kai ba, to wallahi in dai izinina ne ake nema ban yarda ba." Wata wawura daya ma hannunta har yayi qara cikin d'aga murya yace "Zubeida , akan miye ina magana dake har zaki mik'e tsaye kina min ihu, rainani ne ki kayi kome, me yasa zaki d'aga muryarki akan tawa? wai tambaya ma kike yaushe na canza? to a ranar da kika canza na canza nima, akan miye zan zaunar dake ina miki magana cikin nutsuwa ke kuma zaki d'aga min hankali, waye ya koyar dake wannan d'abi'ar? nace waye yace kizo nan ki dinga min abinda ranki yake so, waye." ya qarashe da d'aga murya tare da hankad'ata saman gado. D'orawa yayi da "kina tunanin izininki nake nema? to baki fahimta daidai ba, ni alfarma na nema kimin ta kwana d'aya wanda shima qila waqala na yishi a can, da har zaki wani ce wai baki yarda ba, to karki yarda mana saime? naga idan zamanki nake a gidan." "Ba dai alfarmar dana nema bace har tasa kika min haka, to bari ki gani yanzu zanyi maganin abin." Wayarshi ya ciro daga aljihu ya danna kira, daga d'aya b'angaren ana d'auka cike da karsashi da kashe murya tace "hello baby." Saida ya lumshe ido saboda yanda yaji har tsikar jikinshi ta tashi, saita nutsuwarsa yayi tare da sauke ajiyar zuciya kafin yace "hello, ya kike?" Cikin shagwab'a da wata shegiyar kissa tace "ba dad'i, ka tafi ka barni inata jiranka, duk da ina kewar gida amma har kasa naji gidan ya gundureni saboda kayi nesa dani, a gaskiya Faruk sai yanzu nake qara tabbatarwa cewa soyayya *had'in Allah ce*, yanzu fad'a min yaushe zaka taho?" Baisan sanda wani basaraken murmushi ya sub'uce masa ba, a hankali ya furta "zanzo, yanzu fad'a min tafiyar nan da zamuyi, kina ganin zamu iya dawowa a kwana biyu?" "Eh baby , dan a ranar da za muje ma a ranar za'a gabatar da taron, kawai dai akwai gajiyar tafiya da kuma ganin gari da zai iya kaimu kwana ukun." Yanda muryarta ke fita yasa yasa hannunshi yana shafar saitin zuciyarsa da yake jin bugunta yana canzawa , cikin basarwa yace "to a kwana biyu nake so mu dawo, ki shirya zanzo d'aukarki yanzu." Cike da zumud'i da qwarin murya danta daki dodon kunnensa tace "an gama ranka shi dad'e." Kashe wayar yayi ya maida kallonsa ga Zuby dake zaune tana sauraranshi, kallon sama da qasa ya mata yace "wai duk wanda ya samu dama ba zai tsaya wasa ba sai k'ok'arin ya dama damarsa, to in dan kwana d'aya ne ki rik'e na yafe miki bana buk'ata, zan tafi a ranar da kwanan Khairat zai zagayo, naga kuma mai hanani abinda naga dama." Wucewa yayi ya barta a zaune yana fad'in "aikin banza kawai, yara da zaran sun ganka ba kaya a jikinka saisu nemi su rainaka." Yana fita d'akin Khairat ya nufa ya bud'e da makullan wajensa ya shiga, kayansa ya cire ya shiga wanka, bai jima ba ya fito ya shirya cikin qananun kaya yayi wanka da turare kafin ya d'auki makullin mashin d'inshi dan dashi yake so ya d'auko gimbiyar. _Yaufa my Khairat utu utu zata hau._😁 ***************** Duk da yaso ta fito amma saida tasa ya sake shiga ciki ya gaishe dasu Mamie kafin ta fito, cak ta tsaya saboda ganin Dream a maimakon Renge rover😂, matsowa tayi kusanshi tace "baby, ina motar take?" Gemunshi ya tattaro ya had'e guri d'aya yana murmushi, a tunaninta so yake ya gwada soyayyar da take fad'in tana masa shi yasa ya taho da mashin d'in, ba zata bari shirinta ya watse ba dan haka ta saki murmushi ta rumgumeshi taré da sumbatar kumatunshi kafin tace, "Karo na farko a rayuwata zan hau mashin, a gaskiya soyayya za tayi dad'i akan mashin." Cikin dariya ya fara qoqarin hawa yana fad'in "saima kin hau zaki tabbatar." Rik'e rigarsa tayi tace "ka taimaka min na hau kafin ka hau." Hannun damansa ya mika mata ta rik'e sannan ta tattare rigarta kafin ta hau, yana hawa ya tayar suka d'auki hanya, tintserewa tayi da dariya ta fara masa cakulkuli tana fad'in, "Ashe haka mashin yake? gaskiya daga yau ba zan sake hawa mota ba, nima mashin zan siya sabo." "Ke ke, dan Allah ki bari, za kisa mu fad'i fa, ki bari mana, hhhhhhh." ya qarashe da dariya. Saida suka hau titi kad'ai ta rabu dashi amma fa tana makale a bayanshi tayi luf kamar mai bacci, surutu kawai take zuba masa shi dai nishadi da farin ciki ma ya hanashi magana, da sauri ta nuna masa wata babban restaurant da zasu wuce ta gabanta tace ai saiya tsaya sunci abinci. "Dan Allah me zamu tsaya muyi anan? idan yunwa kike ji muke gida sai kisa Ruk'ayya ta dafa miki duk abinda kike so." cewar Umar Faruk. Cikin raha tace "a'a ni bana jin yunwa , kawai zamu je ne a matsayin masoya kuma muci abinci." "Um um , nifa bana son shiga irin guraren nan." ya fad'a cikin shagwab'a. "Ai tare zamu shiga, in dai kana sona kawai muje." Saida ya rank'wafo bayanta ya kwantota yace "an gama ranki shi dad'e." Tsayawa yayi kamar yanda take so suka shiga babban restaurant d'in, d'aya daga cikin ma'aikatan ne suka tarbesu da kyakyawar mu'amula har suka samar musu da wajen zama, ana aka basu takardar da zasu duba abinda suke so, Khairat ce ta zaba Umar Faruk kuma yace abinda take so shi zaici, cikin k'ank'anin lokaci aka wadata gabansu da kayan tab'awa, suna ci suna hira kamar masoyan tun a ranar farko, suna daf da gamawa ma'aikacin ya dawo ya basu bill d'insu, ganin kudin da zasu biya yasa Khairat kallon Umar Faruk, shima kallonta yayi saita bawa ma'aikacin takardar ta nuna Umar Faruk tace "kaba baby zai biya." tana fad'a ta bud'a post d'inta ta d'auko kud'i ko dubawa ba tayi ba cikin dubara ba tare da kowa ya gani ba. Nufa wajen Umar Faruk ma'aikacin yayi amma sai Khairat ta rigashi isa ta sunkuya kamar ta mishi sumba ta kamo hannunshi ta dank'a masa kud'in kafin ta dago ta kalli ma'aikacin cikin harshen frensh tace "dan Allah ina zan samu douche?" Kwatanta mata yayi ta nufi wajen Umar Faruk kuma ya kalli a hannunshi yaga kud'i, karb'ar takardar bill d'in yayi sai yaga kud'in da aka rubuta ko kasheshi za ayi ba zai iya biyansu ba, sai lokacin ya fahimci abinda Khairat tayi, murmushi kawai yayi yayi kamar ya fito da kud'in daga aljihunshi ya bawa ma'aikacin, godiya yayi ya wuce Umar Faruk kuma ya maida kallonshi ta inda habibiyar zata fito. Ai kuwa sai gata dama ba abinda taje tayi kawai dan tabar wurin ne, tana zuwa ya mik'e itama post d'inta ta d'auka sannan suka wuce, suna fita waje ya kalleta yace "me yasa zaki biya? bayan nine ya dace na biya." "Ni kuma? biyan me?" Kallonta yayi yaga raina masa wayo kawai za tayi dan haka yace "daga yau bana so ki sake shiga aikin daba naki ba, wannan ba huruminki bane, yin hakan kamar kina nuna ba zan iya d'aukar nauyinki bane." Saida suka hau mashin d'in tace "duk da bana da ilimin addini, amma nasan abune mai kyau mata ta taimakawa mijinta, nice nace muzo nan badan kana so ba, taya zan bari kayi asarar mak'odan kud'ad'e har haka." Jin yayi shiru yasa ta bishi da wata kissar ta hanyar rumgumeshi ta baya tana sauke numfashi tace "kayi hak'uri to idan ranka ya b'ace, zan kiyaye anan gaba, amma ban maka alk'awari ba." Hannu ya zura ya shafi fuskarta yace "Allah ya miki albarka." Da sauri ta d'aga daga jikinshi cikin daga murya kamar ta manta inda suke tace "wayyo Allah, yau mijina ne yake saka min albarka, gaskiya na gode baby, dan Allah kayi min alk'awarin kullum zaka dinga saka min albarka, kaji?" "Nayi alk'awari." ya fad'a yana rik'e hannunta dake kan cinyarshi. A haka suka kai gida cikin nishad'i da farin ciki, saida suka shiga wanka suka fito kafin ya saka doguwar riga ya shiga yiwa iyayensu saida safe, d'akin Zuby ne ya shiga qarshe ya tarar da ita kwance tana chat a wayarta, ko kallonshi ba tayi ba saboda ta nuna masa ranta a b'ace yake, shi kuma domin ya nuna mata yana farin ciki sai yace "ni zanje na kwanta, ina fatan dai ba wani abu ko?" "Um um." ta fad'a a cikin mak'oshi. "Ok, saida safe to." yana fad'a ya wuce ya barta, ta d'auka zai rarrasheta ne koya tsaya tab'a jikinta, hakan kuma ya mata zafi sosai dan haka ma ta fara matso wasu hawaye masu zafi. Shi kam yana komawa can Khairat tasa ya manta da wata Zuby soyayya da salo ta dinga kasheshi dasu, har saida ya goge hawayen dake idonshi ya k'amk'ameta sosai yace "dan Allah Khairat ki bani dama na shiga rayuwarki shiga ta har abada, Khairat ki amince ki bani kanki mana ta hakane kad'ai zamu sake zama d'aya, dan Allah Khairat ki taimakeni , ina kusa da kaiwa k'adamin da ba zan iya rik'e kaina ba, ki taimaka ki bani kanki kafin kwananki ya qare daga gobe." Shiru tayi a qirjinshi dan sam ta manta da wani rabon kwana, basarwa tayi ta fara shafar kanshi tana fad'in "kayi hak'uri baby zan baka, d'an lokaci kad'an zaka qaramin." "Yana iya to , dole nayi hak'uri, na riga dana saba da wannan jikin naki Khairat da salonki , zaiyi yuwa na iya *rayuwa ba tare dake ba*." duk yayi maganar nan yana shafar qirjinta kamar zai ciresu. Ita kam wani murmushin gefen labb'a ta masa dan kuwa hak'arta ta cinma ruwa, kuma ko iya haka aka tsaya, to tayi nasara akan Umar Faruk. _Me kuka ce ne my fan's.???_ 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *Jan hankali* _Akwai wani kuskure da nayi amma ba kowa ya fahimta ba, sati d'aya Umar Faruk zai yiwa Zuby itama, amma na manta nake cewa kwana biyu, tun farkon labarin dama Umar Faruk ba zasuyi tafiyar nan da Khairat ba, kawai dai na kawo maganar tafiyar ne da Umar Faruk saboda ita Khairat za taje, ina fatan zaku fahimceni._ *Tunatarwa* _Akwai wasu da naji suna cewa Umar Faruk baya adalci a tsakanin Khairat da Zubeida, dalilin kuwa shine ya amince zai tafi tare da Khairat da kuma fad'an da yake yiwa Zuby, ni kuma a sanina sau biyu yawa Zuby fad'a, lokacin da tazo yana magana ta katseshi wanda kuma banga hakan a matsayin laifi ba, sai kuma daya zo mata da maganar tafiya shima ya gargad'eta ne kawai, wasu na ganin Zuby bata da anfani a labarin dan haka inda ban sakata a ciki ba._ *To kuji da kyau dalilina nayin wannan rubutun.* *1* _Ba budurci bane mace kawai._ Khairat ta rasa budurci a lokacin da namiji hud'u suka mata fyad'e, amma hakan baisa ta cire rai da rayuwar farin ciki ba, ta alk'awartawa kanta ba zata saka damuwa ba, kuma tayi nasarar hakan, bata nuna cewar ita yanzu ta zama wata daban ba kamar yanda al'uma ke kallonta. Sanin kanku ne idan akace anyiwa mace fyad'e har rasa mijin aure take, badan komai ba sai dan ana ganin kamar ta rasa kima da darajar ya mace, Eh, tabbas ta rasa budurci, amma bata rasa kima ba, domin kuwa har yanzu tana nan a sunan mace kuma mai daraja, budurci abun tattaline garemu domin mu kaishi inda ya dace, amma ba'a fad'a ba ko a *_Littafi mai tsarki_* cewar idan suka rasashi a zubar dasu ba, wannan shine manufata kuma tunanina , bai zama lallai ko dole ba maganata ta shigi kowa, amma nidai abinda na yarda dashi kawai shine🧘‍♀ _Dan mace ta rasa budurci bata rasa kima bane da zaisa a kalleta qasqantaciya_ *2* _Ba budurcinki zaisa miji ya soki ba_ Biyayya, Hak'uri, Kissa, Salo, sune matakalar farko da zata janyo miki martaba da soyayyar mijinki, *Na yarda* duk macen da bata kawo budurci gidan mijinta kimarta tana raguwa a wajenshi, amma idan kika rik'e abubuwan dana fad'a a baya, to tabbas zaki sha mamaki, qaramin misali ga wanda suke cewa Zuby bata da matsuguni a cikin labarin. Tana tink'ahon ita budurwa ce Khairat kuma akasin haka, amma meya faru? Khairat ce a zuciyar Umar Faruk, meya kawo haka? salo da kissa ta shigo dasu a al'amuranta, duk da dai da kanshi ya amshi budurcin Zuby amma yanzu ba zai iya tuna meye amya faru a wannan ranar ba, kunsan me yasa? saboda ba cikin nutsuwa hakan ta faru ba yana gidan sarakuwarshi ne , bai kuma shirya hakan ba, kawai taja hankalinsa ne, kuma yana biyan buk'atarshi ya tafi ya barta, baiga asalin miye ma budurcin ba bare gobe ya fad'a, to tambayarga da zan muku, *wa zai fad'a min me Umar Faruk zai iya fad'a a game da budurcin Zuby???*, masu ganin jan ran da Khairat takewa Umar Faruk ya isa haka a'a, ina so Khairat ta gama kama zuciyarshi da salonta sannan ya kai maqura wajen sha'awarta ta yanda zai kusanceta cike da nishad'i da son isar da sak'onshi a kanta yanda ya kamata, a ranar da zai haukace yaji ita kad'ai yake buk'ata kuma zai iya k'watar hakk'inshi koda ta k'arfi ne, a ranar ko baiga budurcinta ba ba zai d'aga hankalinshi ba, saboda ya samu nutsuwar da yake buk'atar samu a matsayinshi na namiji, dan haka 'yan uwa ku fahimci me nake son isarwa a labarin *Jihadi*. *3* _Kissa ita ke tafiya da kishiya dama miji kanshi._ Duk da Khairat najin kishin Umar Faruk amma hakan baisa ta fito da kishinta a fili ba, ko Umar Faruk d'in bata bari ya fahimci tana kishinsa ba, me yasa haka? a ganinta bai dace da ita ba kuma ba girmanta bane, da kissa take tafiyar dashi da ita kanta Zubyn. Wannan yawan tab'awa da sumbatarshi da kuka ga ina yawan sakawa yana da anfani, miye anfanin? anfanin shine, hakan zaisa ko baya tare da ita yaji kamar tana kusanshi, k'amshin jikinta zai dinga tsayawa a jikinshi ta yanda zai dinga bibiyarshi, ko bacci yake kuma zaiji tamkar ta sauke masa sumba mai kyau a kumatunshi, wannan shine dalilina na saka haka. Saboda rashin iya kissar zama da miji da kishiya , shi yasa Zuby take kasa b'oye abinda ke ranta, a qarshe kuma hakan zai iya haifar mata da matsala, ita a ganinta tunda ya karb'i budurcinta da hannunshi kuma tana da malaman tsibbu, to ta gama dashi alhalin kuma ba haka bane. *4* _iyaye sune tushen tarbiyar yaronsu._ Tun farko laifin na iyayen Khairat ne, ai a littafin *Akhdari* an fad'a cewar _"babu biyayya ga ababen hallita wajen sab'awa mahalicci."_ Na'ima (mahaifiyar Khairat) tana da damar bijirewa iyayenta saboda ta samu labarin munannen halin Usman, amma saita musu biyayya saboda gudun b'acin ransu, sanadiyar haka ta samu mijin dako addu'ar saduwa bayayi idan zai kwanta da ita, saboda kusan kullum a maye yake. Sun haifi Khairat an sakata islamiyya, amma saboda an daketa mahaifinta ya hanata zuwa gaba d'aya, mahaifiyarta kuma ta fara koyar da ita, itama kuma saboda ta daketa sai yace ta daina shiga sabgar 'yarsa , me tayi a matsayinta na uwa? saita fita harkar yarinyar da bata san meke faruwa ba. Khairat ta shiga damuwa sosai ta yanda ta zab'i zaman d'aki akan waje, bata sakewa bata fira da kowa daga tunani sai jiyo hayaniyar iyayenta a lokacin da mahaifinta ke saduwa da mamanta ko kuma yana dukanta ko kuma suna fad'a. Yarinya ce dole hakan zai tab'ata sosai, hakan ya janyo mata ciwo a qarshe aka fitar da ita wajen kakarta, itama kakar me tayi??? shagwab'a tayi ta hanyar samar mata da duk abinda take so. Duk da ta dawo kuma ta girma amma Mamie bata shiga sabgar 'yar tata saboda halinta, hakan yasa yarinyar ta tashi tsagera kuma marar kirki, amma yanzu nasan kun fahimci ainihin hallayar Khairat, *waccen hallayar dama aransu tayi ta yab'a a jiki* yanzu kuma data samu nagartaccen miji da 'yan uwa, saita fara dawowa asalin Khairat d'inta. _Ina fatan zaku fahimci sak'ona, kuma ku nutsu kuga miye zai faru a gaba, kuji ku qara ji *Ni Sameera Harouna* ban tab'a tsayar da labari ba saboda maganganun makaranta, kuma ban tab'a canza akalar labari ba saboda makaranta._ ~FATAN ALKHAIRI~ 🤝👏 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣5⃣ *ZAIZO MUKU INSHA ALLAHU.* 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Shi yasa ban tab'a tunanin tsayar da rubutu ba saboda maganar wasu, domin kuwa akwai dubbanin masoya da suke biye da kai, muna mugun tare daku insha Allah._ 😘😘😘😘😘😘😘 _Bismmilahir-rahman-rahim_ *My Amnoor, wannan kyautarki ce* Ina sonki💕 _My dotana *Khadija* Allah ya saka miki da alkairi, ina alfahari dake kuma ina qaunarki._ 3⃣5⃣ Dare yayi sosai Khairat ta farka da matsananciyar qara cike da tsoro, a kunnen Umar Faruk qara ta ratsa hakan yasa suka mik'e zaune a tare, da sauri ya janyota jikinshi yana fad'in "shiiiii, Khairat, ya isa haka, ya isa kinji, ki kwantar da hankalinki ba komai anan." Kallonshi tayi ido a kafe tana ganinshi ta fad'a jikinshi ta fashe da kuka, kanta ya dinga shafawa yana fad'in "ya isa, ya isa kiyi shiru kinji." Cikin kuka tace "sune, sune suke zuwa min a cikin bacci, Faruk ina jin tsoro, ina so na manta amma na kasa." "Kiyi hak'uri Khairat, ba zasu sake zuwa miki ba insha Allah, kar kiji tsoro, ina tare dake, kuma ba zan tab'a bari wani ko wata ya sake cutar dake ba, kinji ko? ki nutsu muna tare." A hankali ta d'ago kai ta kalleshi tace "kayi alk'awari." Saida ya sumbaci labb'anta yana murmushi yace "nayi miki alk'awari." Qara shigewa tayi jikinshi tana qara qamqameshi, ajiyar zuciya kawai take saukewa tare da shashekar kuka, bayanta yake ci gaba da shafawa har bacci ya sake d'aukarta, gyara zamansa yayi tana rumgume a jikinshi shima har baccin ya fara d'ibarsa, amma kiran sallah daya shiga kunnuwansa yasa ya bud'a ido, kallon fuskar Khairat yayi ganin yanda ta turo leb'en qasa cike da shagwab'a, a hankali ya daddab'a bayanta kafin ta bud'a ido. "A tashi, lokacin sallah yayi." ya fad'a tare da shafa kumatunta. Tashi tayi zaune shi kuma ya fita yayi alwala, kai tsaye d'akin Zuby ya nufa, saida ya bubbuga kafin ta bud'e k'ofar, tana bud'ewa ya shiga d'akin yana kallonta, itama kallonshi take kafin yace mata "kin tashi ashe?" "Eh, na tashi." "Ok, ni na tafi masallaci." Binshi kawai tayi da kallo dan ita haushi kawai yake bata, gaba d'aya sallah sukayi Umar Faruk kuma koda ya dawo d'akin Zuby ya sake komawa, kwance ya sameta akan gado hakan yasa ya haura kan gadon ya rumgumota jikinshi, duk da dai ba komai ne keda dad'in shak'ar k'amshi a jikinta ba, haka ya matseta har yana sauke numfashi kafin yace "ya kika tashi?" "Ina kwana." ta fad'a tana turo baki gaba. "Lafiya k'alau." ya fad'a yana zura hannunshi a cikin rigarta. Rik'e hannunshi tayi tace "dan Allah ka bari, bana so." "Saboda me?" ya fad'a yana kallon fuskarta. "Kawai bana jin dad'i ne." Tashi yayi zaune tare da d'agota itama tayi zaune yana kallonta yace " hushi kike dani Zubeida?" Saida ta qara had'e fuska tace "akan me zanyi hushi da kai? kawai dai bana son abinda kake min." "To me yasa ba kya so?" "Saboda bana son kana tab'a jikina kamar yanda kake tab'a waccen karuwar." Sosai kalmar karuwar nan ta shiga zuciyarshi ta fasata, bud'e idonshi yayi daga lumshewar daya musu ya kalleta yace "k'yamata kike kenan?" Wani kallon bakin cikine ta masa dan ita ba haka taso ba, kau da kanta tayi tace "ashe ma kana kusantarta, aina d'auka za kace min wallahi babu abinda ya shiga tsakaninmu ne, ashe dai ba haka bane." "Amsar tambayata?" ya fad'a a dake ba alamar wasa. "A gaskiya in dai har." kuma sai tayi shiru. "In dai har me?" "In dai har kana tab'a jikinta itama kamar yanda kake tab'a nawa, to gaskiya ina qyaqyaminka, da ba zan yarda kaje ka d'auko wata cutar da banji ba ban gani ba ka qaqaba min." Sam bai tab'a tunanin haka Zuby take ba, a yanda ya santa da ilimi na addini ya d'auka zata iya fahimtar komai cikin sauk'i, amma saiga akasin haka, ya zaiyi da ita ita haka nata salon kishin yake, janyota yayi jikinshi yana murmushi yace "ban tab'a tunanin haka ba, aina d'auka ko kina da tabbacin Umar Faruk d'inki yana da wata cutar da zaki iya d'aukarta a jikinshi, ina tunanin zaki amince ki zauna dani saboda soyayyar dake tsakaninmu." "Zan iya, idan har cutar Allah ne ya jarabeka da ita, ba wacce kai ka siyo da kud'inka ba." "Naji to, yanzu kiyi hak'uri ki yafe min laifina." D'ago kanta tayi dan dama jinta take a takure tace " ba zan iya ba, saboda har yanzu kana tare da ita, ga kuma sabon rainin wayon daka zo min dashi, waina baka kwana na kuje qasar waje, humm." Taushe zuciyarshi yayi yace "Zubeida, na d'auka zaki iya ara mana kwana uku a cikin kwanakinki, idan ki kayi duba da rayuwa yau gareka gobe ga d'an uwanka , wata rana kema buk'atar hakan zata iya taso miki, kuma ta miki alfarma." "Tabbb', Allah ya kiyaye wallahi, kenan gadin gidan zan zauna yi muku? bafa zai yiwu ba wallahi, sai dai kuma in amanata za aci kawai." Dariyar baki da hankali ya mata yace "to idan anci amanar taki saime? aiba yau na fara cin amana ba, ko kin manta ne? to idan kin manta bari na tuna miki, a kanki aka fara cin amana, domin kuwa a ranar dana kusanceki aiba kwananki bane, kwanan waccen baiwar Allah ne, amma kinsan meya faru data fahimci naci amanarta? cikin gargadi tace min, na yafe maka a yanzu, amma idan ka sake ba zan yafe ba, ke yanzu wannan matar ce ba zaki iya bawa aron kwanaki biyu zuwa uku ba?" "To ina ruwana? itama tayi ne dan neman gidin zama a wajenka , kuma lokacin da akayi ai bana gidan bare tamin kallon banza." Kallon mamaki ya mata sosai kafin yace "kenan ke ba kya neman gindin zama a wajena? ba kya fatan qara samun matsayi fiye da wanda kike da? abinda kika fad'a yanzu sai yasa naji cewar ba zaki damu da darajar mijinki ba, kinsan me yasa nace haka?" "Alk'awari na d'aukarwa Khairat cewar zamu tafi tare kuma tun kafin kizo gidan nan, nasan kinsan mahimmanci cika alk'awari da kuma alamar mai karyashi, idan na sab'a mata ban kyauta ba, kuma a matsayinta na matata ba zata iya kallona da mutunci ba, zata iya kallon mijinta mutum mara cika alk'awari kuma maqaryaci sannan munafiki, yanzu Zubeida a matsayinki na masoyiyata duk zaki so hakan ta faru, kuma ma ki rasa wacce zaki bari tawa mijinki wannan kallon sai abokiyar zamanki, hak'ik'a ina so na cika alk'awarin dana d'auka saboda tun ina qaramin yaro Baba yake fad'a mana, Babban mutum ba yana nufin girman jiki bane ko matsayi , ainihin abinda yake nufin shine, magana d'aya kuma abisa gaskiya, cika alk'awarin daka d'auka, hakan zai qara martabar addininka." Jikinta ne yayi sanyi yayin da wannan hadithn ya dinga mata yawo a qwaqwalwa, *alamomin munafiki guda uku ne, idan zaiyi magana sai yayi qarya, idan yayi alk'awari ya sab'a, idan aka amince mishi yayi ha'inci.* "A gaskiya badan tunawa da hadisin nan ba, da ba zan yarda ba, na amince ku tafi, amma da sharad'i." "Ina jinki." ya fad'a ba tare da nuna ya wani ji dad'in abinda tayi ba. "Idan kuka dawo zaka cika min sati na nima kamar kowace mace." Janyota yayi jikinshi yana sumbatarta yana fad'in "saima kin fad'a, kinsan yanda nayi kewarki kuwa?" Raba jikinta tayi da nashi tana nok'ewa, cike da karsashi yace "nifa bana son wannan kunyar, zaifi miki ki cireta dan ranar da kika shigo hannuna fa ba sauk'i." Wata kunyarce ya sake bata hakan yasa ta juya mishi baya ta kwanta tana sauke numfashi, sauka yayi daga kan gadon ya koma wajen da take ya sunkuya yace "bani sumbata a kumatu, kuma harda ta jiya zaki min." Bud'a idon tayi ta kalli qasunbarshi luf da ita, sake rufe ido tayi, haka yayi juyin duniya amma tak'i koda bud'a ido harya fita daga d'akin, yana fita ta juya ta kalleshi duk da ya fita, ajiyar zuciya ta sauke ta gyara kwanciyarta. Yana shiga d'akin Khairat ya sameta zaune bakin gado tana waya, da mamaki yake kallonta yana tunanin dawa take magana a muqu muqun safiyar nan, duk da waya take saida ta mik'e tsaye ta rumgumeshi da hannun d'aya tare da bata kumatunta alamar ya sumbata, manna mata sumba yayi ta koma ta zauna inda ta tashi, tsaye yayi gefenta ya fara bin kowace kitsonta yana tab'awa, abinda ta fad'a a wayar ya tabbatar mishi da manager ne, "Eh, idan angama had'awa kawai ka fitar mana da guda uku wanda nasu yafi na kowa, na farko za'a bashi kyautar mota da qara masa albashi , na biyu kuma za'a bashi sabon moto da qarin albashi, na uku kuma zamu bashi kayan abinci da kuma kud'i, hakan yayi ai?" Jim tayi alamar tana sauraro kafin tace "yau kam ba zan fita ba, idan ka had'a komai kayi abinda ya dace, kawai dai kana kirana a waya dan insan meke faruwa." Jim nayan dak'ik'u kafin tace "ok, saina jika." Aje wayar tayi a gefenta tare da janyo Umar faruk da har yanzu yake wasa da gashinta ta zaunar dashi, sai data dafe kumatunshi ta sumbata kafin tace "ina kwana baby, ina ka shigene haka inata jiranka?" Yana kallonta yace "na shiga wajen k'anwarki ne, kinyi kewata har haka?" Duk da taji wani abu ya soketa amma basarwa tayi tace "sosai ma, nifa bana son kana nisa dani sosai, sai naga kamar zan rasaka ne." Tana fad'a ta janyo kanshi ta kwantar a saman cinyarta ta fara shafar kansa har zuwa qasumbarsa tana fad'in "yau ba zan fita aiki ba, amma zanje na siyowa su Mamie kayan da zasu tafi dashi, kaga daga nan nima saina siyo namu, dan nasan yanzu a Germany akwai sanyi, dan haka ina buk'atar ka bani aron motarka." Shiru yayi yana kallonta yayin da zuciyarshi ke antayo mishi sink'i sink'in tambayoyi _"wai me yasa Khairat da Zubeida suka kasance ba d'aya ba? bayan kuma dukansu mata ne, me yasa Khairat tafi bashi farin ciki? sab'anin Zuby da sukayi soyayya, me yasa Khairat take son kusanci dashi sosai? ba kamar Zuby ba da bata ma son yana tab'a jikinta a koda yaushe, me yasa Khairat ta iya komai kuma cikin salo tare da iya takonta? shin wayewa ce tafi Zubeida? ko kuma ilimin bokon data fita ne? ko kuma bud'ewar ido?"_ _Bara na fan's Jihadi su baka amsar_😜 Jin yayi shiru yasa ta shafi kumatunsa tace "baby." ta fad'a cikin shagwab'a. Kallonta yayi yace "ina jinki." "Au du baka ji me nace ba? me kake tunani?" Tashi yayi daga cinyarta yace "naji, amma ai naji baki nemi izinin fitar ba." Hararan wasa ta masa tana fad'in "wato kai mai iko ko? dama an fad'a namiji ko ka girmeshi in dai har aure ya shiga tsakaninku, to ka zama abin tausayi, dan iko kuke nunawa harna fitar hankali." Da murmushi a fuskarsa yace "kuma hakan yayi ko?" Gira ta d'aga sama tace "sosai ma, tunda hukuncine da yazo daga sama yankakke." Kafin yayi magana ta gyara zama tana fuskantarshi tace "to naji zan nemi izinin." Harda gyaran murya tayi kafin ta langab'e kai tayi kalar tausayi tace "baby, dama ina neman izininka ne ina so zan fita dan na siyowa su Mamie kayan tafiyarsu, idan da hali ina so ka bani izini tare da aron makullin motarka?" Janyota yayi jikinshi yana fad'in "kaji neman izini mai kyau, gaskiya daga yanzu haka zaki dinga yi idan zaki fita." D'aga kanta tayi ta kalleshi amma wani kallo daya watsa mata yasa a hankali ta zura harshenta cikin bakinshi ta lumshe ido tare da kama harshen tana tsotsa......... saida ta gama rikirkitashi sannan ta mik'e tana gyara jikinta tace "bara na d'auko kayan karatu." Hannunta ya rik'e hakan yasa ta juyo ta kalleshi, wani marayan kallo daya mata irin kizo ki taimakeni d'in nan yasa tayi murmushi ta matso kusanshi, kasancewar yana zaune hakan yasa ta manna kanshi a qirjinta a tsakiyar mamanta tana shafa kanshi, a hankali ta d'ago dashi ta kalleshi idonshi sunyi ja tace, "Malam, lokacin karatu fa yayi." tana fad'a ta wuce d'auko litattafanta, ba yanda ya iya haka suka fara karatunsu kamar kullum. Ruk'ayya ta kawo musu abin kari kamar yanda ta saba kuma yace ta kira Zubeida, da sallama ta shigo fuskar nan a had'e ba annuri, dogon hijabi ne a jikinta yama rufe kayan dake jikinta, zaune tayi inda tasan nan zaice ta zauna, ganin sun gaisa da asuba yasa ba tayi magana ba, Umar Faruk ne ya kalleta yace "ba gaisuwa?" "Amma ai mun gaisa d'azu." ta fad'a ba tare data kalleshi ba. "Ina nufin 'yar uwarki, nasan kin karanta a hadith, cewar idan kazo ka samu mutum a wuri kaine zaka fara gaisheshi." A wulak'ance tace "ina kwana." tana hararan Khairat d'in. Khairat da ita kanta haushinta take ji itama a wulak'ance ta amsa da "lafiya lau." A haka suka fara cin abincin babu mai magana, Khairat kam yau kishinta take ji sosai, haka ma Zuby kamar zata mutu saboda ganin wai yau Umar Faruk ne ya zama nasu su biyu. Zuby da masifa ke gurgurarta ce tace "idan ba damuwa zan iya magana?" Kallonta yayi da murmushi yace "Zubeida, a zamanin 'yanci muke fa, zaki iya magana mana kina da damar hakan." "Sai nake ganin kamar hakan bai dace ba kullum a dinga dafawa ana bamu, me zai hana ka raba mana girki, kaga kenan duk lokacin da kwanan d'aya daga cikinmu ya zagayo itace da girkin ranar." Tabbas Zuby tayi gaskiya dan abinda ya kamata kenan, saida ya gyara zamansa kafin yace "gaskiya ne Zubeida, kin fad'i abinda dama dole zanyi magana akai koba yanzu ba." Kallon Khairat yayi yace "abinda ya dace ayi kenan, dan haka yanzu zaku fara girki da kanku." Waro masa ido tayi tayi magana qasa qasa sai dai baiji me tace ba saboda na kurame ne tayi, ganin Zuby ta tashi tare da fad'in "alhamdulillah, aci lafiya." tana fad'a ta bar d'akin domin kuwa burinta ya cika. Khairat na ganin haka ta gyara zama da kyau ta cire hannunta daga plate d'in tace masa "me kayi haka Faruk, so kake kaci mutuncina a gaban yarinya qarama, dan kasan ban iya komai ba shi yasa zaka amince da abinda ta fad'a? to kama sake tsari dan wallahi ba zan yarda ba, dan babu abinda zai sani yin girki koda ma na iya." "Khairat, miye abun d'aga hankali a cikin nan? kinyi sakaci tun farko kasancewarki na 'ya mace kika kasa koyan aiyukan da kinsan dole zaki yisu in dai har kinyi aure, amma duk da haka ba wata matsala tunda zaki iya koya." "Kana haukane? nice zanje koyan girki saboda kawai waccen yarinyar, nifa ba zan iya wannan wahalar ba ta girki danko a gidanmu banyi ba, kuma kai shaidane." Kallon da yake watsa mata ba tare da magana ba yasa ta mik'e ta cire rigar baccinta ta shiga wanka, tana fitowa shima ya shiga cikin sauri ya fito ya fara shiri, saida ya gama shi da ita babu mai kula wani harya d'auki jakarshi zai fita ya d'auko makullin motar ya mik'a mata, karb'a tayi ba tare data kulashi ba kafin ya fice daga gidan. Saida ya fita kuma tana shirin tana tambayar kanta me yasa tayi haka? ita da take burin ganin ta mallakeshi ta hanya mai kyau, ji tayi kuma ta kasa hak'ura kawai ta d'auki wayarta ta danna masa kira, k'in d'aga kiran yayi saboda yana kan hanya cinkoso yayi yawa, har ya kai bata daina kira ba koda yaga itace kawai saiya share yana tunanin me zata fad'a masa, da sauri ya shiga ma'aikatar ya tarar an fara taro, kamar ko wane ma'aikaci shima tsayawa yayi yana sauraron abinda manager ke fad'a, ya jima yana jawabi kafin ya gabatar da abinda ya tarasu. Nan aka fara duba sunayen mutum uku wanda zanensu yafi na kowa, na farko shine *Umar Faruk Ahmad* na biyu kuma *Abdullahi Salis* ta uku *Surayya Balarabe*, nan aka kira kowa aka bashi kyautarshi tare da musu fatan alkairi sannan aka qarfafa musu gwiwa tare ma da wanda nasu samu nasara ba, damar tafiya aka basu ba tare da sunyi aikin wannan ranar ba. ***************** Umar Faruk baya raba d'ayan biyu kan cewar aikin Khairat ne, dan shi dai yasan a tarihin masana'antar babu wanda akace an tab'a bawa kyautar mota, wannan mamakin ya hanashi tuk'a motar sai Ishaq ne ya tuk'ota shi kuma yazo a mashin d'inshi, a k'ofar gida aka paka motar su kuma suka shiga ciki Ishaq na shaidawa mutanen, murna dai ba kowa ke yi ba daga ciki harda Umar Faruk, a haka aka kira Khairat da Zuby dansu gani, suma dai babu wacce ta fito da farin cikinta a fili, Zuby tunaninta shine Khairat ce ta bashi motar raina mata hankali kawai zasuyi, Khairat kuma haushin ta kira bai d'aga bane yake damunta. Sake fita sukayi da Ishaq Umar Faruk ya goyashi a mashin ya mayar dashi ma'aikatar shi kuma ya dawo amma a hanya saida ya tsaya ya s gas guda biyu 5kl kafin ya dawo gida. _Bara nima na tab'a turancin nan._😜 _I need you prayers fan's._👏👏👏 _Me zai faru to_🤔 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Sorry fan's abisa rashin amsa comment d'inku, jikin ne sai a hankali._ _Dan Allah ku tayamu da addu'a Allah ya bawa my *BK* lafiya, ina so ta dawo muci gaba da kodimo😉, my masoyiyar BK nayi kewarki sosai, rashinki yasa nima bana jin dad'i._ _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣6⃣ Tunda yaga baiga mota a k'ofar gidan ba ya tabbatar ta fita, koda ya shigo Aliyu ne ya tarbeshi ya karb'i tukunyar gas d'in, d'aya ya bawa Zuby d'aya kuma ya aje a kewayen Khairat, shiga yayi ya rage kayan jikinshi sannan ya kwanta akan gado, wayarshi ya ciro ya fara kiran Khairat, Khairat kuma data bar wayar a mota tana cikin babban kanti tana siyayya, hakan yasa Umar Faruk cewa ta rama ne itama. *************** Har *12:40* Khairat bata dawo ba, ganin haka yasa Zuby girki d'an sassauk'an abinci ta zuba a plate ta rufe da d'aya tare da cokali ta tunkari d'akin Khairat. 😏😏😏humm, zaki jawa kanki. "Assalama alaikum." tayi sallama cikin taushin murya. "Wa'alaiki salam, shigo." ya fad'a. Bud'a labulen tayi ta zura qafafunta ta shiga, ganin Zuby yasa ya tashi zaune dan baiyi tsammanin ita bace saboda murayar daya ji, "Zubeida, kece dama?" Saida ta tsaya gabanshi tace "eh, kona koma ne baka buk'atar ganina?" "Ah haba, ni na isa." Ganin tayi zaune a bakin gadon kusa da qafafunshi tana wani yamutsa fuska yasa ya d'an qara gyara nutsuwarsa yace "ina jinki, magana zamuyi ne?" "Abinci na kawo maka, dan nasan kana jin yunwa, tunda naga ita har yanzu bata dawo daga walagigin ba." ta fad'a tana bud'a plate d'in. "Me kike nufi da abinda kika fad'a?" ya tambaya. Cikin had'e fuska tace "ka fini sani mana." Qara gyara zama yayi yace "Zubeida, ku matana ne, kuma nine mai alhakin kare mutuncin kowace daga cikinku, ya kamata kisan me zaki dinga fad'a akan Khairat, duk cin zarafin da zaki mata kamar ni kikawa , haka itama idan ta miki ni tawa, tunda kika zo gidan nan kike kiranta da sunan da bai dace ba, na miki shiru ne kawai amma naga baki gani ba, to daga yanzu bana so na sake jin kin kirata da sunan karuwa, dan ita ba karuwa bace kamar yanda kike fad'a, dan haka ki kiyaye, idan kuma abincin kika zo bani zaki iya ajewa ki tafi na gode." Cike da makirci ta fashe da kuka tana fad'in "ni dama sani baka sona yanzu, wallahi banyi tunanin haka daga gareka ba yah Umar, gaba d'aya ka canza saboda waccen matar, shine ba komai ba anfanin zamana a gidan nan in dai har baka sona." Tsaye ta mike ta fara tafiya taji ya rik'e hannunta, saukowa yayi daga kan gadon ya rumgumota jikinshi yana shafa kanta, cikin rarrashi ya fara fad'in, kiyi hak'uri, baki fahimceni bane Zubeida, ina so ki gane cewa, ke da Khairat ba zan bari wani ya cutar da d'aya ba, ko itace take fad'a miki haka abinda zanyi kenan, ke da ita duka Allah zai tsayar dani ranar gobe kuma ya tambayeni yanda na shugabanceku, Zubeida na zama mutum azzulumi da baya iya adalci tsakanin matanshi, da farko naci amanar Khairat ta hanyar kusantarki a kwananta, dan Allah ki taimaka karna sake aikata wani laifi, banyi adalci ba idan nayi shiru ina ji kina kiranta da karuwa, amma kiyi hak'uri kinji." D'ago da kanta yayi yana kallon fuskarta yace "kiyi shiru to, yanzu kije d'akinki ki zauna zanci abincin, bana son mai d'akin ta sameki anan, dan nasan yanzu tana kan hanyarrrr." Bai k'arasa ba kuma Khairat ta bud'a labulen d'akin ta shigo, daram dam, shine tsinkewar da gaban Khairat yayi ganin Zuby a qirjin Umar Faruk, bugun zuciyarta ne ya qaru ta yanda ba zata iya saisaita kanta ba, sauke idonta tayi akan Zuby ta fara takowa cikin d'akin, itama Zuby d'in ita take kallo harta aje plate d'in hannunta akan center tebur d'in d'akin, ganin yanda suke kallon juna yasa Umar Faruk cewa "Zuby ki wuce d'akinki." Saida ta gama hararan Khairat sama da qasa sannan taja dogon tsaki ta nufi hanyar fita, aikam dama zuciyar Khairat a wuya take hakan yasa ta finciko rigar Zuby ta shake sosai ta zubar da kayan hannunta harda wayarta ta mata wani jan kallo tace "dawa kike, ni Khairat ki kewa tsaki, ni kike wa tsaki? dake nake magana." Ta qarashe maganar da d'aga murya, matsowa Umar Faruk yayi da nufin magana Khairat ta daga masa hannu tace "dakata min dallah, bari na gama da ita sannan, kana kallo qaramar yarinya zata nemi taci mutunci na, akan miye zata min tsaki?bayan nice ke daidai nayi mata tunda ni na sameta a d'akina, koda yake ba laifinta bane laifinka ne, da baka kirata ba aiba zata zo, shine har zata dinga min kallon raini da iskanci, wallahi sai naji wanda ya d'aure miki gindi a gidan nan." Ta qarasa tana jinjigar Zuby dake hannunta, Zuby kam tuni idonta suka fara kawo qwalla, cikin gunguni ta rik'e hannun Khairat tace "dallah sakeni malama." Wani murmushin rainin hankali Khairat ta mata ta sake shak'ar rigarta ta jinjina tace "ki k'wace mana idan kina ganin k'arfinki yakai, tabbas gata da shagwab'a ne suka raini ne, amma ki sani ina da k'warin k'ashi da tsabagen tsagwaron k'arfi, ta yanda idan na rik'i kamarki wallahi ba zaki iya k'watar kanki ba, amma idan kinyi musu toki gwada ki gani." Qara qoqarin qwaqwale hannun Khairat tayi amma tajita jim a hannunta, sake maqale murya tayi tace "dallah nace ki sakeni ko." "Hum, bari kiji na fad'a miki, dama nasan dole za kiyi rawar kai dan tunda naga mahifiyarki na tabbatar da haka, tun ranar da kika shigo gidan nan kike min kallon bi aho amma na miki shiru, to ki sani qyaleki nake ba dan komai ba sai dan canjin da aka samu, idan kuma kika kuskura kika tayar da qwanqwanman Khairat harna dawo asalin Khairat d'ita, tofa akwai matsala dan ba lallai gidan nan su iya dani ba, kashedi na qarshe, karki bari na sake ganin qafarki cikin d'akina dan ban yarda dake ba, kamar yanda ban yarda da mahaifiyarki ba." Da kai ta mata alamar ta wuce kawai, ficewa tayi da sauri saboda hawayen dake son taho mata, kai tsaye d'akinta ta wuce ta fad'a saman gado ta fashe da kuka, duk da zuciyarta naso ta qaryata abinda take ji, amma dai tabbas ta tsorata da Khairat yau d'in nan, dan tasan gaminta da ita ba zai mata kyau ba, saida taci kukanta ta koshi sannan ta kira Mama ta fad'a mata abinda yake faruwa, fad'a sosai Mama ta mata tare da zaginta gaba da baya kafin ta sake jaddada mata tayi aiki da magungunan nan. Bud'ar bakinta cewa tayi "ai Mama maganin ne nasa a abinci nakai masa, shine fa tsinannar ta shigo." "Toki kwantar da hankalinki, nasan ai zaici abinci, da yaci kuma magana ta qare." "To Mama, sai an jima." *************** Tana fita Khairat ta wurga masa harara tana hango Zuby a qirjinshi, ta gabanshi taso wucewa amma saiya tareta, kallonshi tayi tace "matsa min a hanya." "Ba zan iya ba, saboda kina hushi dani." "Ka matsa min nace ko, inba so kake na huce a kanka ba." "In dai zaki huce na amince ki huce a kaina." K'arfinta tasa ta tureshi gefe hakan yasa yayi baya da k'arfi, amma jarumta tasa bai fad'i qasa ba, tsaye yayi sosai a gabanta a hankali ya rik'o hannunta tare da zube gwiwoyinshi a qasa ya marairaice kafin ya fara magana, "Kiyi hak'uri, nasan ke mai hak'uri ce, ki yafe min domin nasan kin yafe min laifin da yafi wannan ma, kimin uzuri danna fahimci ke mai ilimi ce, my *Khairiri* ki yafewa wannan hamagon mijin naki mana, ke alkairi ce a gareshi kamar yanda fassarar sunanki yake, duk da dai bana da laifi, amma ina neman gafararki matata, idan baki yafe min ba zan shiga tashin hankalin da nake da yak'inin ban tab'a shiga irinsa ba, domin kuwa Khairat ta zama wani b'angare na sassan jikin Umar Faruk, a yanzun yafiyarki ce zata zata tabbatar da ci gaba da farin cikin mijinki ko akasin haka, domin kuwa ba Umar Faruk in dai har ba Khairat, hushinki na second d'aya, tamkar hushin duka mutanen duniya ne a wajen Umar Faruk, ki tausaya kuma agazawa wannan bawan Allah wanda rayuwarsa ta kasance kece mahad'inta, kuma nasan ko Khairat ce ta b'atawa Umar Faruk rai, zata sunkuya har qasa sannan ta nemi afuwarsa, a lokacin kuma Umar Faruk zai rumgumo Khairat jikinsa sannan yace na yafe miki my Khairat." _Kaji mai wayo, wato ya fad'a mata abinda ya kamata tayi cikin dubara._ Inhar Khairat tace kalaman nan basu shiga sassa da b'argo da jijiyarta suka ratsa zuciyarta ba, to qarya ta fad'a hakan yasa ta sunkuya itama ta rumgumeshi tace "na yafe to, amma me yasa zata shigo min har d'aki kuma ta raina min wayo?" K'eya ya d'an sosa yace "kiyi hak'uri, abinci kawai ta kawo min." Sai lokacin ta juya ta kalli plate d'in dake aje, takawa tayi ta d'auki plate d'in ta dauka ta bud'a, tsaki tayi tare da fad'in "aikin banza kawai, inba munafirci ba meye na kawo maka abinci? bayan ba ranar girkinta bace, to ba zaka ci ba danni ban yarda da ita ba." Tana fad'a ta fita da plate d'in ta aje akan gajerar katangarsu sannan ta dawo ta fara cire kayanta, bayanta ya tsaya ya fara cire mata bras yana fad'in "naji dad'i da kika yafe min, nan gaba zan kiyaye b'acin ranki." Tana d'aure kitsonta tace "kayi nasara akan Khairat, dama wannan kalaman kad'ai Khairat take buk'ata kuma gashi ta samu maiyi mata." Da haka ta shiga wanka shi kuma ya nufi masallaci, yana dawowa kuma ya samu tana sallah, kayan data barbaza ya fara tattarewa, wanda ta cire kuma ya ninkesu ya mayar drower, tana gamawa ta taso ta sumbaci goshinshi tare da qarasa addu'arta ta fad'a a fili cewa "Allah ya dawwamar maka da farin ciki a rayuwarka." "Ameen." ya fad'a yana kallonta yace "addu'a kika min?" "Eh mana, addu'a nawa mijina." ta fad'a tana cire hijabinta. Yana kallo ta fara shafe shafe da murje murje, humra kusan kala bakwai yaga ta shafa kafin ta d'auki qaramar riga iya cinya ta saka sai pants, wasu turaren yaga ta dauka tana fesawa har kala hud'u suma kamar dai abun hauka, *pure love*, *Mid night*, *Blue dive* da kuma *love flowers*, amma fa cikin k'ank'anin lokaci d'akin ya gauraye da k'amshi mai dad'in shak'a, a hankali ta juyo tana kallonshi cikin takon d'aukar hankalitana jijjiga qirjinta ta tsaya gabanshi. Rumgumarshi tayi cikin kunne tace "me kake ji?" Dogon numfashi yaja ya gagara maidowa saboda ji yake kamar zai mutu, wani irin rikitatacen k'amshi ne mai tafiya da hankali, nanfa suka lula wata duniyar wacce Khairat ce kad'ai ta samu nutsuwa amma banda Umariri 😂, dan wata sabuwar sha'awa ce ta taso masa wacce inba fa can yakai ba ba zai samu nutsuwa ba, a haka tafi masallaci sallah asar , yana dawowa kuma ya sameta tasa kayan marmari gaba tana shan kayanta a maimakon abincin rana, zaune yayi kusanta ya d'auki ayaba yana fad'in "me zaki dafa min?" "Yaushe? wai da gaske kake? shi yasa kenan naga tukunyar gas." "Eh mana." ya fad'a tare da kai ayabar bakinta. Bud'a bakinta tayi sosai ta tsotso tana kashe masa ido, shi kanshi abinda tayi wata ma'anar ya bayar ta daban, a take yaji wani abu yana masa yawo dan haka ya rintse idonshi, cire ayabar tayi daga bakinta ba tare data d'iba ba tace "me kake so na dafa maka?" "Komai ma." ya fad'a numfashinshi na fizgarshi. Aje tuffan dake hannunta tayi ta mik'e tsaye tace "zaka sha mamaki yau, dan zaka ci abincin shalelen Papa." Canja kayan jikinta tayi ta saka riga da wando kafin tace masa "to ta ina zan fara?" Murmushi yayi a zuciyarshi kuma yace "zan kuwa sha mamaki." Kallonta yayi yace "ki fara tanadar kayan aikin, daga baya sai kiyi tunanin abinyi." "To ina suke kayan?" Dariya yayi dan da alama shima yau zai d'ana girki, fita yayi ya kira Ruk'ayya dake fama da nasu aikin, tana zuwa tace "yah Umar gani." Cewa yayi "kije ki d'auko mata duk wani abu da kika san za'a buk'ata wajen sarrafa doya da k'wai da miyar...." Sai kuma ya kalli Khairat yayi shiru, itace tace " umm , jus kawai nake buk'ata na mayonnaise da albasa." "Me zai hana ki had'a da sardines?" cewar Umar Faruk. "Um um, bana cin kifi da daddare." Kallon Ruk'ayya yayi yace "jeki kawo, ai akwai komai ko?" "Akwai yah, doya ma akwai sauran wacce ka siyo." Tana fad'a ta fito tana dariya dariya murmushi murmushi, qanqanin lokaci ta had'a mata komai a kewayenta ta tafi ta kama nata aikin, tare da Umar Faruk suka fito tana kallon kayan, rik'e k'ugu tayi ta yamutse fuska, satar kallonta yayi ya bushe da dariya ya koma ciki, "humm, dariya ko? zaka sha mamaki." Tana fad'a ta dawo d'akin wata santaleliyar wuk'a ta d'auka ta fita, d'aya daga cikin kujerun wajen ta zauna ta janyo doya ta gatsa mata wuk'ar, aikuwa sai doya ta rik'e wuk'ar Khairat ta jinjina wuk'a tak'i fitowa, haushi ne ya kamata ta taso cikin shagwab'a ta samu Umar Faruk dake shirin fita. "Eh, lallai ma malam Umariri, wato ka had'ani da aiki, shine kake qoqarin fecewa daga gidan, to muje idan ka datsa min doyar ka fita." Bata bari yace qala ba taja hannunshi sai waje, zaunar dashi tayi akan kujerar ita kuma tayi tsaye tace "to fara, dama aikin doya na maza ne irinku masu k'arfi." Shi dai in banda dariya ba abinda yake, yana tab'a wuk'ar kuma sai yaji ta biyo hannunshi, kai kawai ya girgiza ya fara sara mata ita harya gama sannan ya yunk'ura da nufin tashi, maidashi tayi zaune tana fad'in "kasan me? bara na d'auko wata wuk'ar sai naga yanda zaka fereta , dan ba zan iya ba." Tana fad'a ta koma d'akin ta d'auko wata wuk'ar, zaune tayi ta d'auki doyar tace "to fara ina kallo." "Yanzu ina namiji meye had'ina da wannan aikin? bafa wuyane dashi ba." "Ehe , kaji ka da wata magana, to miye a ciki? naga koda ma na iya ai zaka iya kama min aiki, koka manta ka fara bani tarihin rayuwar *Annabi muhammad (S.A.W)*, kuma kai ka fad'a min yana taya matanshi aikin gida, kaga kayi koyi dashi kenan." Yamutse fuska yayi yace "Allah ko?" "Eh mana, d'affak'a sunna." ta qarashe da d'aga mishi gira sama. Ferewa ya fara yi itama tana ganin yanda yake tana yi, surutu kawai take zubawa yayin da shi kuma a d'arare yake, ya matsu koya tashi dan gidansu ana ganinshi anan duk iliminsu zai tashi a banza, za ace ya zama mijin tace kawai, duk a ciki qwaya biyu kad'ai ta fere shima saida Umar ya d'auka a nuna mata yana fad'in "dubi bata feru da kyau ba." Suna gamawa ta mik'e tsaye da wuk'a a hannu tana gilmawa da ita ta gabanshi tana fad'in "gashi yanzu harka samu lada, to me zanyi a gaba?" Qarewa yayi a kujerar yana kallonta da tsoro cikin zolaya yace "wuk'a fa kike nuna ni da ita, zaki yankeni fa." "To nidai fad'a min me zanyi?" "Ki kunna wuta saiki d'ora tukunya , saiki wanke doyar ki zuba a ciki bayan kinsa ruwa saiki zuba gishiri." "Yeeeee, ashe mijina kuku ne." ta fad'a da rumgumeshi. Yanda ya fad'a tayi amma shiya kunna wutar dan kasawa tayi, suna azawa ta kuma cewa "to saime yanzu?" "Ki yanka albasa ki b'are tafarnuwa, kinga ni tafiyata zanyi." Albasa ta d'auka da nufin yankawa amma da qyar ta samu ta fitar da hancin, hannunta ya kasa tsayawa sai rawa yake, shi dai yana kallonta har yaga wuk'ar ta kubce ta daki hannunta, saida ya rigata rintse ido danji yayi kamar wuk'ar ta sauka a qahon zuciyarshi ne, ji yayi ba zai iya jura ba, hakan yasa Umar Faruk cewa "kawo na yanka miki, d'auki tafarnuwa ki b'are." Dad'i taji sosai nanta fara b'ara tafarnuwa amma fa shima ansha wahala, saboda akaihun dake hannunta duk sun rarraba tafarnuwa gashi ita kanta zafi take ji a akaihun nata, da qyar ta b'ara 'yar kad'an tace ta isa, "to ya zanyi yanzu?" ta tambayi Umar Faruk. "Ki d'auko turmi ki jajjaga." "Tu me?"😳 "Ba zan iya daka ba hannuna yayi ruwa." tana fad'a ta shiga d'aki jim kad'an sai gata da blender a hannu cikin kwalinta, bud'ewa tayi ta had'a sannan ta zuba kayan miyar gaba d'aya ta dawo d'aki ta jona a waya ta markad'asu, Umar Faruk kam cewa yayi "dama saboda irinku akayita." Gama markad'an yayi daidai da dahuwar doyan, nanfa ta d'auko passoire (abin tace macca) da roba ta aje zata sauye doyar, wani k'yale tasa ta kama tasa zata sauke amma tace tsoro take ji karta zubar, karb'a Umar Faruk yayi ya juye mata zai jiyo ya kalleta yaji saukar sumba a kumatu tana fad'in "na gode Faruk." Aifa buga k'wai a kazo, humm reader's kuzo kusha kallo wajen fasa k'wai..... _Wai nikam wa yayi girkin nan ne, *Umar Faruk* ne, ko *Khairat*???_ *Ina buk'atar addu'arku masoya.* 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _💕💕💕Je vous aime tellement.💕💕💕_ _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣7⃣ Tana bugawa da k'arfinta k'wain ya baje gaba d'aya, kallon Umar Faruk tayi da yake mata dariya yana rufe baki, fashewa tayi da kukan shagwab'a harda turmusa qafafu a qasa, tasowa yayi ya tsugunna kusanta ya dago fuskarta ya fara share mata hawayen yana fad'in "haba babyna, kiyi hak'uri ki daina kukan, kawo na fasa miki." Karb'a yayi ya fasa k'wain kafin ta zuba kayan had'i yace ta soya, a tak'aice dai haka tayi suyar rabin mai ya zube qasa rabi ya fallatsar mata a jiki rabin kuma ya qone bayan ta kammala, sauce d'in ta had'a shima da taimakon Umar Faruk har suka gama, idan ka ganta saika tausaya mata kuma ta baka dariya, saboda yanda ta had'a zufa ta ko ina biyar jikinta take, amma saboda turarukan dake jikinta yasa zufar ke fitar da k'amshi, sauke kaskon yayi daidai da fara kiran sallah, da gaggawa Umar Faruk ya shiga yayi wanka saboda duk jikinshi ya d'auki odeur d'in abinci kafin ya fito da gaggawa ya nufi masallaci. *************** Abincin da Zuby ta kawo masa kuma Ruk'ayya ce ta had'a da kayan wanke wanke zata kai wajen da zata wanke, cikin tsautsayi kwanukan suka zube qasa abincin ya b'are, Mama dake zaune saida tayi ta mata fad'a saboda ganin abinci lafiyayye ya zube, hak'uri taba Mama tare da gyara wurin kafin ta fara wanke wanken. ***************** Kasancewar Khairat yanzu ba abinda take bawa mahimmaci kamar sallah yasa ko wanka bata tsaya yi ba tayi alwala tayi sallah, tana gamawa ta fito ta zuba abinci a wasu shegun kwanukan masu kamar yan shafesu da gold ta zuba, akan tebur ta kai ta aje sannan ta d'auko carap (jug) wanda sukayi daidai da kwanukan ta aje sannan ta d'auko lemu a cikin fridge *chivita* ta juye a ciki, tana jin kiran sallah kuma ta mayar da isha'i sannan ta shiga wanka. Tana shiga Umar Faruk ya shigo gidan, zaune yake yana jiranta ta fito suci abincin yaji ko zai ciyu😂 amma shiru, yunce ke ciciyarshi saboda tun break d'in safe baici komai ba sai kayan marmari, hakan yasa ya janyo plate ya d'auki cokali ya bud'a kwanukan, lumshe ido yayi danko ba dad'i dai akwai k'amshi, jin k'arar ruwa yasa ya kalli douche d'in yace "aifa, mod'a kenan sarkin wanka, an samu randa sai nink'aya ake." Saida yasa hannu ya d'auki yankan doya d'aya ya dangwala sauce d'in yakai baki 😎😋, "tohhh, ashe dai na iya girki." Ya fad'a yana qara dangwalar wata sauce d'in, d'iba yayi ya zuba a plate ya fara ci ba k'akk'autawa, duk a zuwan shiya iya girki🙃 _karka raina mana hammata mana_, harya kusa gamawa ta fito, kallon kallo suke tana kallon plate d'in, "malam Umariri kenan, bako bismillah?" Lumshe ido yayi yace "um um, idan na gama kinci." Qara d'aure towel d'in dake qirjinta tayi ta zauna kusanshi ta d'ora hab'arta akan kafad'arshi ta rik'e damtseshi sosai tana fad'in "fad'a min na iya girki ko?" Hararanta yayi yace "kaji malama, ki kayi girki a ina? na iya dai." Cakulkuli ta masa tana fad'in "wallahi sai kace na iya girki sannan zan rabu da kai, kaji mutum duk qoqarin nan da nayi." Cikin dariya ya tuntsire baya ya kwanta saman kujeran yana kare kanshi yana fad'in "kin iya, kin iya Hajia rumdub'e." Tsalle tayi ta tashi daga wajen tace "wayyo Allah Mamie na." Ta fad'a tana d'aukar wayarta, kira ta aikawa Mamie kuma cikin sa'a ta d'auka, Mamie na d'auka cike da zumud'i Khairat tace "Mamie albishirinki?" "Goro fari tas shalelen Papa, badai kin samar min d'an jika ba?" Da k'arfi ta fad'a kan gado tayi ruf da ciki tace "kash Mamie, wane irin jika kuma yanzu? da wuri haka? nifa dan nace miki ne yau da kaina nayi girki, kuma yayi dad'i." Jim Mamie ta d'anyi dan sai yau kuma yanzu ta fahimci wani babban kuskure data tafka, amma saita basar tace "ayya, gaskiya na miki murna, to ki dage kinji ko, kuma da mijinki zai amince da saiki dinga zuwa ina koya miki? dan wannan aikina ne a matsayina na uwa." "Humm, sai yanzu kika fahimci hakan? to naji zan masa magana, idan ya amince zaki ganni, idan bai amince ba bazan zo ba, ki gaida Mammie." Tana fad'a ta kashe wayar ba tare data juyo b'angaren da Umar Faruk yake ba, dan itama sai yanzu taji kunyar kanta ace bata iya girki ba, abu d'aya taji ya shiga ranta shine ta koyi girki kota halin yaya, daga haka kuma tana tunanin nan bacci ya d'auketa saboda wahala da gajiyar da tayi. Saida ya gama ya wanke hannayenshi yazo kan gadon, saida ya tsaya bayanta ya lek'a kanshi ta fuskarta cikin kunne yace "gaskiya kin iya girki, ban tab'a cin abinci mai dad'in wannan ba." Jin shiru yasa ya sake cewa "ya ku kayi da Mama? naji kince zaki nemi izini na." Nanma shiru ba amsa, gyara kwanciyarshi yayi ya mirgino da ita gabanshi, kasak'e yayi yana kallon kyakyawar fuskarta da tayi fiyau da ita saboda ba'a shafa komai ba, towel d'inta ne ya d'an sassauto daga qirjinta, a hankali ya shafi fuskarta har zuwa qirjin nata kafin yasa bakinshi ya fara tsotsa. A cikin bacci taji manya manyan sak'onni na isketa, babu yanda ta iya data kama mishi suka shiga wata duniyar, sunyi nisa sosai kamar kullum ya fara k'ok'arin wuce gona da iri, dakatar dashi tayi amma sam baya jinta dan haka ya matseta sosai ya rad'a mata "me yasa Khairat, dan Allah ki barni, yau kad'ai ya rage min a cikin sati d'aya da zan miki." Shiru tayi saboda wata guduma data daki zuciyarta da k'arfin gaske, jerowa kanta tambayoyi ta fara yi _"yanzu shikenan daga yau ni da Umar Faruk, yanzu duk abinda yake min shi zaije yayiwa yarinyar can, yanzu duk soyayyar da yake cewa yana min da kuma nuna min da yake, daga gobe zai fara nunawa wata irinta koma fiye da ita, tunda ita ya santa 'ya mace, kenan sanfiri ne suka nuna min d'azu shi yasa na sameta a d'akina, wayyo Allah na, gashi bana da wannan abun bare na bashi kaina ko nima yayi alfahari dani, to miye abunyi yan....."_ Bata fad'a ba taji Umar Faruk na fad'in *"Allahumma janibna shaid'an, wa jannibi shaid'an ma razak'tana."* Lumshe idonta tayi hawaye suka zubo mata, ji tayi ta rasa duk wani kuzari da k'arfinta, jira kawai take yayi abinda zaiyi da ita, idan kuma ya gama ya koreta gidansu dan tasan qarshen alak'arsu ce tazo, to in kinsan haka me zai hana ki hana mishi kanki? ko dai kina son farin cikinshi ne? in kuwa hakane kema kina sonshi kenan kuma so na gaskiya. 😎😎😎😎😟😟😟😔😔😞😞😒😒😞 Bayan doguwar wahala da jarumta da *Jihadi* da kuma gumurzu da Umar Faruk yasha kafin ya samu hanyar wucewa, a qarshe dai ya samu ya wuce bayan 'yan dubaru tare da taimakon zuma da vaseline kuma yayi nasara.😂😂😂 _Hmmmmmmmm_ *KHAIRAT* dai naga kuka take, amma Umariri bansan ainihin meye yake ba dan ban fahimceshi ba sosai, kwance yake yana kallon rufin d'akin yayin da kukan Khairat ke hanashi tantance yanayin da yake ciki, jin ta qara sautin kukan ne yasa ya juyo da ita ya d'ora kanta akan qirjinshi yana shafar gashinta, ba zai iya magana ba a halin da yake ciki shi yasa yayi shiru yake daddab'ata kwai. Jin tak'i yin shiru sai rera kukan take kamar wata sabuwar amarya yasa ya fizgo nutsuwarshi ya mayar a jikinshi ya saisaita kanshi cikin murya qasan mak'oshi yace "Khairat, kinsan yanda nake jin kukan nan naki kuwa? tamkar zubar tafasasshen ruwa ne a jikina, a halin da ake ciki yanzu Khairat, kukanki shi yafi komai d'aga min hankali, dan Allah kiyi shiru ki daina kuka, nasan na rabaki da abinda yafi komai, kuma ba zan iya maido miki shi ba, amma in har hankalinki zai kwanta ne kawai idan na maido miki shi, to ki shirya yanzu, saina rama miki abinda na miki." Duk da barkwanci ya mata a qarshe, amma abinda ya fad'a shine mai mahimmanci a wajenta, yunk'urawa tayi ta tashi tayi saurin qamqame hannunshi ta rintse ido tace "washhh." Janyota yayi ta koma jikinshi yana fad'in "kiyi a hankali mana, kinfa aikatu sosai." Nanma dai bata kulashi ba sai cewa da tayi "meka karb'a daga gareni?" cikin muryar kuka harta shak'e. Saida ya lumshe ido yana shafa bayanta yace "abinda yafi daraja a wajen 'ya mace mana." Cikin shakk'ak'ar muryarta tace "ban gane ba, me kake nufi?" "Ina nufin budurcinki." Ji tayi kawai yana mata izgili ne dan haka ta tashi zaune da qyar ta fashe da sabon kuka, shi kuma kamar tana tsikara masa wani abu haka yake jin kukanta, janye hannayenta yayi yasa nashi hannayen yana goge mata hawayen, d'ago da kanta yayi yana kallon idonta duk sun kumbura sunyi ja, kai ya girgiza mata cikin rarrashi ya fara da, "Khairat, nasan me kukanki yake nufi, amma kafin nace komai ina so ki sani kuma kisa a ranki cewa, babu wani d'a namiji a duniyar nan daya tab'a sanin Khairat a matsayin 'ya mace sai mutum d'aya, mijinki na sunna, wato *Umar Faruk* ni kenan, ina so ki manta baya ki fuskanci gaba, nima kuma abinda zanyi kenan a yanzun, ki d'auka a ranki babu wani abu daya tab'a shiga tsakaninki da wani sai yau kuma dani, ina fatan kin fahimceni? kuma zaki bani goyon baya tare da mallaka min kanki ni kad'ai naci gaba da saninki har qarshen rayuwata kamar yanda ni na fara, shin kin amince zaki bani kanki ki zama tawa har abada?" Fashewa tayi da wani kukan ta rufe bakinta tana girgiza masa kai, da qyar ta fara magana cikin kuka tace "kayi hak'uri Umar Faruk ka yafe min, na kasa kawo maka abinda yafi komai mahimmanci, abinda kowane namiji yake burin samunshi a tare da iyalinshi, amma ni na kasa, na kasa Umar Faruk, ban cancanci yafiya ko soyayyarka ba, amma ka sani nima nayi iya k'ok'ari na Faruk dan ganin na kare makashi ,amma kuma sunfi k'arfi na." "Khairat, karki damu kanki da wannan, ni ba shine a gabana ba, nifa ke nake so kuma so na gaskiya nake miki, Khairat zan iya zama dake a kowane irin yanayi a kowane hali, ni zan jure rayuwa dake ba zan tab'a barinki ba Khairat duk tsanani duk wuya." Kai take girgiza masa tana fad'in "ba gaskiya bane Umar Faruk, kawai dai ka b'oyene dan karna fahimta, amma dole zaka ji ba dad'i tunda zuciya ne da kai, kuma zuciya bata da k'ashi, Umar Faruk ba zan iya cutar da kai ba, dan Allah kace na tafi gidanmu, dan nasan koba yau ba zaka goranta min haka ma 'yan uwanka, ni kuma ba zanso ranar da za'a wulak'antani ba akan abinda bani nayiwa kaina ba." "Babu wanda zai wulak'antaki Khairat, ina tare dake, wallahi wallahi Khairat ni _Umar Faruk, nayi alk'awarin ba zan tab'a bari wani ko wata ya sake cin zarafinki ba, ke matata ce kuma uwar 'ya'yana, zan iya b'atawa da kowa a kanki Khairat inhar kika cire iyayena, Khairat ki yarda dani kema ki bani kanki danni na mallaka miki kaina, kiyi yanda kike so dani Khairat, wallahi sai yanda ki kaso za kiyi dani bana da bakin magana."_ A take maganar Mamie ta fad'o mata a rai cewar tana so a daren farkonta ta samu kyauta zuviyar mijinta dashi kanshi, share hawayenta tayi danta hango tsantsar gaskiya a tare dashi, hannunshi ta kama tana d'an murmushi tace "Faruk ka yafe min, nayi maka laifi a baya , amma yanzu zan gyara kuskure na." Fuskarta ya shafa yace "wane irin laifi kuma? a iya sanina nidai babu." "Akwai Faruk." "To ina jinki." Qasa tayi da kanta cike da kunya tace "ranar dana fad'a maka kalmar so, wallahi a ranar ba daga zuciyata ta fito ba, amma yanzu na fahimci kaine wanda ya dace naso kuma kafi cancanta dani, Umar Faruk ka yafe min dan Allah, wallahi yanzu ina sonka so na gaskiya nima." Murmushi yayi tare da janyota jikinshi, "washhhh." ta fad'a saboda zafin da taji daga qasanta. Da sauri ya kalleta yace " ayya sannu, bara na d'ora miki ruwan zafi kinji." Yana fad'a ya sauka daga kan gado ya d'auko doguwar riga yana zura, wani kallo ta dinga masa hakan yasa yace "kodai na dawo ne?" "Ayi me?" ta fad'a tana kallonshi. " *Jihadi* mana." Da sauri ta juya baya tana fad'in "a'a ba dani ba, kaje kai kad'ai." Fita yayi ya d'ora mata ruwan, kafin suyi zafi kuma ya shiga wanka, sai lokacin ne ya fara jin wata irin matsannanciyar qaunar Khairat na sake ratsa kowace gab'a ta jikinshi, sonta kuma ya gauraya da numfashinshi ta yanda baya jin zai iya rayuwa babu ita, rufe ido yayi yana tunano abinda ya faru awa biyu data wuce, tabbas Khairat ta cancanci ya mallaka mata komai daya mallaka a fad'in duniya, ta cancanci ya sota fiye da yanda yake son kansa, tabbas Khairat ta bashi farin cikin da tunda yake a rayuwa bai tab'a shiga kwatankwacinshi ba, hak'ik'a in dai har haka Khairat take to zai dage da addu'a Allah ya bashi ikon yin adalci a tsakaninta da Zuby, dan Khairat da Zuby tamkar moto ne da jirgin sama, murmushi ne mai tsadar gaske a fuskarshi harya fito ya juye mata ruwan. Tuna irin wahalar da yasha yayi kafin ya samu k'ofar shiga, hakan ma yasa yayi wani tunani, anya kuwa an yiwa Khairat fyad'e, anya maza hud'u sun santa a matsayin 'ya mace, taya wacce maza hud'u suka yiwa fyad'e da k'arfi kuma take tsuke haka, me yasa, me yasa to??? D'aga kafad'a yayi yace " Umar Faruk dai a budurwa ya samu Khairat, dan haka daga yau babu wanda zai sake aibata min matata." "Gaskiya ne an mata fyad'e." cewar wani b'angare na zuciyarshi. Da sauri ya tusa hannunshi cikin kanshi saboda bala'in kishin da yaji ya taso mishi, kenan in dai har wasu sun rigashi saninta, kenan duk abinda yaji suma sunji, watak'ila ma fiye da wanda yaji tunda su sune farko, rintse ido yayi sosai zuciyarshi na tafarfasa kamar zata fito ga wani irin haushin su Musa ya kamashi. Haka kuma ya fito sam ba walwala a tare dashi, duk da ya taimaka mata ta samu ta gasa jikinta tare da tsarkake kanta, amma ta lura da sabon canji daga gareshi, daurewa kawai tayi dan tasan dole zata fuskanci wannan matsin dama, doguwar rigar bacci tasa ta kwanta zuciyarta na rawa tana ji kamar ta sake fashewa da wani kukan, juya mishi baya tayi dan tasan ko ba tayi ba shi zaiyi, bacci harya fara d'ibarta saboda wahalar da tasha kawai taji Umar Faruk ya mirgino da ita ya d'orata akan qirjinshi yana shafata tare da daddab'ata, wani farin ciki ya lullubeta hakan yasa ta qamqameshi ta fara sauke numfashi sai bacci. Ci gaba yayi da shafarta yana sumbatarta yana sake matsata a jikinshi shima har baccin ya d'aukeshi...... _Me kuka ce masoya?_ 💃💃💃 06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 💕💕💕💕💕💕💕 _My *Heenat*, my *Meelat*, my *BK*, haqiqa kun taka rawar gani a cikin rayuwar Sameera ta yanda harta kawo yanzu data zama wata tsiya, ku na dabanne a gareni kuma na musamman, ina alfahari daku mutanena._ 💞💞💞💞💞💞 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣8⃣ Ganin yanda take baccin tana sauke numfashi yasa kawai ya gyara mata kwanciyarta ya tashi ya tafi masallaci, bai jima yau dan ana sallamewa ta dawo gida, yanda ya barta haka ya sameta saida ya sake kura mata ido ya kalleta yana ji komai nata na birgeshi kuma yana da kyau kafin ya tangale kanshi da hannu ya sumbaci bakinta, a hankali Khairat ta fara bud'a ido harta sauke akan Umar Faruk, murmushi ya sakar mata tare da fad'in "barka da asuba *madame Faruk*." Itama murmushin ta sakar masa ta shafi fuskarshi tace "barka da asuba malam Faruk." Saida ya d'ora bakinshi a kumatunta yace "ya jikinki?" Zanin rufar dake jikinta taja ta rufe fuska tana murmushi, kallonta yake yace "wai kunya, to bara ki gani." Yana fad'a ya zame zanin rufar yayi sama da ita bai tsaya ko ina ba saida ya direta douche, bud'a ido tayi ta kalleshi yace mata "akwai ruwan d'umi a butar nan, nasan zasu miki anfani." Cikin shagwab'a tace "uhum uhum, nifa zafi nake ji." Sumbatar bakinta yayi yace "hak'uri za kiyi, dole kiyi anfani dasu, inba haka ba kuma." "Inba haka me?" "Kedai ki gama kawai ki fito." yana fad'a ya fita ya barta. Kafin ta dawo harya canza zanin gadon tare dana rufa, cire rigarshi yayi ya kwanta dan wani sanyin baccin ne yake jin yana ratsashi, shigowarta ce yasa ya bud'a ido, yana kallonta harta canza kaya ta fara sallah, tana gamawa kuma ta d'auko kayan karatu tazo ta hau gadon itama, a pillow d'aya kansu yake ta bud'a littafin amma fa yau an samu matsala, saboda rashin bitar karatun da ba tayi ba yasa sam ta kasa kawoshi yau, kallon da Umar Faruk ya mata yasa ta lab'e baki, fuskar nan a had'e yace "kika min kukan nan karyaki zanyi, mena miki to, tun ban dakekin ba?" Zaune ta tashi tace "yanzu saika dakeni?" "Me zai hana? ai karma kiyi tunanin zan d'aga miki qafa, dan yanzu muna matsayin malami da d'aliba ne." Za tayi magana yace "sauka qasa." Baki ta bud'e tana kallonshi, "dake fa nake magana." Bata daina kallonshi ba harta sauka tayi tsaye tana kallonshi, qare had'e rai yayi yace "aro min cazar wayarki." Juyawa tayi ta d'auko cazar ta kawo mishi, "gwiwanki qasa." ya fad'a. Da mamaki take kallonshi sai kuma ta tuna ranar data sakashi zube gwiwoyinshi qasa a office d'inta, a hankali ta sulale qasa tana ci gaba da kallonshi, sai lokacin ya kalleta ya tashi zaune, kallonta yake sosai yace "meya hana ki kawo karatunki yau?" Had'e baki tayi tana rarraba ido ta kasa magana, muryarshi taji yace "wasa kika tsaya ko?" Baki bud'e take kallonshi hakan yasa yace "rufe bakin, sannan ki bani hannunki." Mik'a masa hannu tayi tunaninta zai taimaka mata ne ta tashi zaune, harara ya wurga mata yace "tafin hannunki." Da sauri ta juya tafin hannun tana kallonshi kamar sakarya, ganin ya d'aga cazar wayarta zai tsula mata a hannu yasa tayi saurin janye hannun tayi baya da k'arfi, da azama shima ya rik'o hannunta ta dawo gabanshi, tana ganin haka tasa kuka tana fad'in "wayyo Mamie na dan Allah ki taimakeni, kayi hak'uri malam wallahi gobe zan kawoshi, dan Allah karka dakeni, banda lafiya fa." "Meya sameki?" ya fad'a fuska a had'e. Cikin turo baki tace "to ba kaine ba jiya da daddare ka...." Hannu yasa ta rufe mata baki ya zaro mata ido yace "idan har akace muna cikin ajin karatu, to zaifi miki kyau ki manta da abinda ke tsakanina dake, na fad'a miki haka tun farkon fara karatunmu, ki d'auka abinda ya faru jiya da mijinki ne, yanzu kuma kina ajine gaban malaminki." "Kin fahimta?" ya fad'a da sake zaro mata ido. "Eh, eh na fahimta." "Bani hannunki." yayi maganar yana sakin hannunta yana gyara cazar hannunshi. Yawu ta had'iye sosai ta fure ido ta bashi hannun, "ahhhhhh." Ta fashe da qara saboda cazar data ratsa hannunta, sake rintse idonta tayi sosai hawaye na zubowa taji yace "bani hannun." Gani nayi shima ya rufe ido tare da kau da kanshi sannan ya sake tsala mata a hannu, da sauri ta janye hannun tana matsashi da d'aya hannun tana kuka, jin shiru yasa ta ta bud'e ido a hankali hawaye suka sake zubowa, yana ganin ta bud'e ido ya basar ya daidaita kansa kamar baiji komai ba, alhalin ita taji zafin ne a hannu shi kuma zafin yana ratsa zuciyarshi ne, da hannu ya nuna mata gefenshi ta zauna sannan ya sake maimaita mata karutun jiya tare da qara mata kad'an. Suna gamawa ta haye gadon taja zanin rufa ta kalleshi a lokacin daya tashi yana zura rigarsa tace "in dai sunana Khairat, wallahi daga yau ba zaka sake dukana ba akan rashin kawo karatu." Dariya yayi lokacin daya saka rigar ya matso kusanta tare da manna mata sumba a goshi yace "haka ake son d'alibi ya zama, fatan alkairi madame Faruk." Tana kallonshi ya fita daga d'akin tasan wajensu Mama zaije ya gaishesu da kuma Zuby, tashi tayi itama ta canza kayan jikinta tasa hijab sannan tabi bayanshi, d'akin Mama ta fara shiga ita shi kuma d'akin Mama Sa'a, a haka suka dinga sab'ani shi zai shiga can ita ta fito, saida ta gama ta fito zata koma d'aki ta ganshi ya nufi d'akin Zuby, da sauri ta qarasa d'aki ta haye gado tayi shiru, duk qoqarinta saida taji hawaye na neman zubo mata, basarwa tayi kawai ta d'auki wayarta da abin sauraro ta danna wani indian film tana kallo. Yau ma haka ya fito daga d'akin Zuby duk da qoqarin da yayi ya rumgumeta amma ita sai tayi ta tureshi tana bata so, yana zuwa ya sake cire rigarshi ya kwanta kusan Khairat dan bacci yake so yayi sosai tunda yau lahadi ba aiki, ganin abinda take kallo yasa yace "kina jin me suke fad'a kenan? tunda naga kema 'yar garinsu ce." Murmushi kawai ta saki ba tace komai ba, zare d'aya abin sauraron yayi yasa a kunnenshi yaji indianci ne, kallonta yayi yace "ki dinga fassara min to." "To." ta fad'a tare da jinjina kai, suna rumgume da juna suna kallo tana fassara masa wani, wani kuma tayi shiru har bacci ya d'aukesu. Tun Zuby na had'a abin kari take leken kofar tana ganin takalman Umar Faruk amma shiru ba motsinsu, harta gama taci tayi wanka ta shirya, mutanen gidan suka fara kujuba kujubarsu amma su shiru kake ji, zuciyarta ce ta fara tafasa ji take kamar ta dinga aika ashar ta yanda kowa na gidan hankalinshi zai tashi. Ruk'ayya ma haka tazo ta tattara kwanukan wajen tayi wanke wanke tayi shara amma koda wasa ko lek'awa ba tayi ba bare taga meke faruwa, *10:25* Umar Faruk ya farka, saida ya fito daga wanka harya shirya kafin ya dawo wajen Khairat ya kalli fuskarta ya shafa, sumbatarta yayi a kumatu sannan ya daddab'ata. Itama wanka ta shiga ta fito tana cikin shiri kuma Umar Faruk ya shigo da leda a hannunshi, plate ya d'auka ya juye musu abincin a lokacin ta gama shiryawa sannan suka ci, suna idawa ya kalleta yace "zan fita gari, ki kula min da kanki kinji, ina sonki *alkairina*." Rumgumeshi tayi tace "nima ina sonka jarumina." "Yaushe na cancanci wannan sunan?" ya fad'a da zolaya. Cikin kunya tace " *daren jiya*." Sake qamqameta yayi sosai yace "ashe jarumtata har takai haka? ai kuwa zan qara himma." "Lahhh, idan ka qara himma zan iya mutuwa fa, wallahi ba qaramar wahala nayi ba jiyan nan." D'ago fuskarta yayi yace "ki fad'a min sirrin abinda naji jiya, danni na kasa yarda cewa wasu sun fara..." sai kuma yayi shiru. "Sun fara kafin kai?" ta qarasa masa. Kai ya d'aga mata alamar Eh, cike da tabbatarwa tace "tabbas wasu sun rugaka, amma ni bansan komai ba." Shafar jikinta ya fara tare da mata wani salo yana sumbatar wuyanta dan yaji zafin maganarta, kawai baya so ta fahimta ne, cikin rad'a yace "amma fa ni ban tabbatar ba, kawai dai nasan nasha wahala kafin na samu hanyar wucewa izuwa duniyar Khairat mai wuyar mantawa." Idonta ne suka kawo qwalla ta kalleshi a marairaice duk tayi kalar tausayi tace "dan Allah ka fad'a min gaskiya Umar Faruk, shin nima zaka iya kallona da darajar da zaka iya kallon wacce ka samu a matsayin budurwa? Umar Faruk zan shiga tashin hankali da damuwa idan ka juya min baya, ba zan iya jura rasaka ba domin kuwa haka na taso tun farko, ina samun duk abinda nake so, bana so na rasaka Umar Faruk zan iya mutuwa, wallahi mutuwa zanyi idan ka wulak'antani ko ka rabu dani, Umar Faruk mutuwa zanyi ba zan iya rayuwa ba." Ta qarashe da sulalewa qasa tana fashewa da matsanancin kuka, ita kanta bata san lokacin da take fad'an maganganun ba ta daisan kawai daga zuciyarta suke, shi kanshi ji yayi kamar zaiyi kuka amma dakkakiyar zuciyarshi ba zata bari ba , sunkuyawa yayi ya d'agota ya fara share mata hawayen kafin yace "Khairat, ki kwantar da hankalinki dan Allah ki sawa zuciyarki nutsuwa da salama, in dai har kin yarda da cewar kina samun duk abinda kike so, to ki yarda kin samu Umar Faruk, Khairat ki d'auka Umar Faruk ya zama naki, kuma ba zan tab'a juya miki baya ba saboda kin zama rayuwata nima." Cikin kuka ta kalleshi tace "ka tabbatar?" "Na tabbata Khairat, babu abinda zaisa na gujeki, muna tare har qarshen ratuwarmu." Dariya tayi tare da kamo kanshi tasa bakinta a nashi, saida taji ya fara birkicewa kafin ta barshi, cikin muryar galabaita yace "ni na wuce." Hannunshi data rik'e yasa ya juyo yana kallonta da idonshi da har sun canza, "ya dai?" ya tambaya. Langab'e kai tayi tace "ina so ne na maka kallon qarshe, dan daga yau zamu nesanta na d'an wani lokaci." Shi kam harga Allah harya manta da yau ne, marairaicewa yayi ba tare daya nuna mata rashin jin dad'in hakan ba a fili yace "da nasan haka zan samu Khairat, da banyi qasa a gwiwa ba wajen wuce wannan wurin." Cikin dariyar mugunta tace "nima da nasan haka zan sameka da jarumta, da ban yarda na baka ba ko jiya." "Ashe dai na bada tsoro." ya fad'a yana shirin ficewa daga d'akin. "Kawai ma, ba wani tsoro, kara nake maka dan kar kaji ba dad'i idan nace maka *ragon namiji*, amma ba komai da naji." Juyowa yayi yana mata wani mugun kallo, k'ofar d'akin ya tsaya ya mik'o mata hannunshi yana murmushin mugunta yace "zo baby." Ita kam da bata fahimci komai ba takawa tayi a hankali ba kamar yanda take tafiyarta ba tana d'an cije lips saboda ciwon da take ji a qafarta da qasanta, saida ta kusa kaiwa gareshi ya kauce da sauri ya shigo d'akin ya sake mik'a mata hannu yana fad'in " so nake naga kin taho kamar yanda kika saba da k'arfi." Kai kawai ta girgiza masa ta sake tahowa a hankali, bata tantance ba taji ya fizgo hannunta ta fad'a qirjinshi, wata qara ta saki da k'arfi dan ji tayi kamar qafarta ta cire hakama k'ugunta, rufe mata baki yayi yace "me kika ji?" D'agawa tayi daga jikinshi ta koma kan kujera ta zaune tana hararanshi, dariya kawai yake mata harya zo kusanta ya danna mata sumba a goshi ya tallabo fuskarta yace "ina sonki Khairat, ki kular min da kanki, saina dawo." Janyo fuskarshi tayi ta sumbaci bakinshi itama tace "ina sonka baby, ka kula min da kanka, kuma karka bari wata ta qwace mana kai." Dariya yayi yaja dogon hancinta yace "kishi ko? toni me zanyi da wata bayan Allah ya bani ku." Bye bye ya mata ya fita, gyara zama tayi ta rumgume hannayenta ta shiga duniyar tunani, da farko kishi ne ke ciciyarta na abinda ya fad'a, amma sai tayiwa kanta karatun tanutsu ta shiga tunanin sabbin hanyoyin da zata samu zuciyar Umar Faruk, dan yanzu itama sonshi take so na gaskiya, sai inda k'arfinta ya qare a kanshi. **************** Mamie ce zaune tayi tagumi Mammie ta sameta a wurin, harta zauna bata sani ba saida ta d'aga murya wajen magana, "ke, waime kike tunani?" "Na'am Mama, ba komai." "Ya za kice ba komai bayan ga komai na gani, fad'a min meke faruwa?" Ajiyar zuciya ta sauke tace "Mama, sai jiya na tuna da wani *kuskure* da nayi mai girma a rayuwa wanda ba lallai yanzu ya gyaru ba." "Wane irin kuskure ne wannan da ba zai gyaru ba?" "Mama, jiya Khairat ta kirani take fad'a min da kanta tayi girki, Mama abin takaici shine dad'i take ji saboda tayi girki d'aya tak a gidan miji, tun farko dana koya mata da duk haka bata faru ba, yanzu bansan ya za tayi ba gashi tana da kishiya, Mama nayi kuskure sosai a game da rayuwar Khairat, tabbas bamu rik'eta ba kamar yanda ubangiji yace mu kula da 'ya'yanmu ba, rashin iya girki ba qaramar matsala bace a gurin 'ya mace, shi yasa nake tunanin abinyi." Saida Mammie ta jinjina al'amarin kafin tace "akwai mafita har yanzu, duk da tayi aure ba zai hana ki jata a jikinki ba sannan ki koya mata girki." "Nima haka nace mata jiya Mama, amma kinsan halin Khairat." "Karki damu, ni zan mata magana saita fara zuwa nan kina koya mata in mijinta ya amince." "Yawwa Mama na gode." "Karki damu." *************** *16:30* Khairat na zaune tana waya da Papa, tambayarta Papa yayi ita kuma ta fara kora mishi bayani kamar haka "wallahi Papa ba komai, Faruk yana sona kuma nima ina sonshi, kuma kaga zamu zo tare dashi Germany, ina farin ciki da kasancewarmu tare, kuma kunga yana koya min karatu kullum, yanzu haka na kusa zama malama." Ko bata fad'a ba Papa yasan ta canza daga yanda ta kirashi da kunga a maimakon baya da take cewa kaga, "ai kuwa ya kyauta, da alama wannan mai sa'a ne tunda yayi sa'ar shiga zuciyar gimbiyata , dan haka ki fad'a min me kike so na masa?" "Kawai Papa kaima ka soshi, sannan ina so ka samar mishi aikin da yafi wanda yake yi a k'arkashina, saboda matakin karatunshi ya wuce nan." "An gama shalele , akwai manyan masana'antu a k'asashen waje da nake da hannun jari a ciki, idan kina so sai a samar masa d'aya daga ciki." "A'a Papa, bana son aikin da zaisa ya bar garin nan, in dama ni kad'aice da saimu tafi tare, amma mu biyu ne." "Ai yanzu anci gaba shalele, zai iya zama anan kuma yana aiki a k'ark'ashin wani ma'aikatar, computer ta isa tayi komai." "To Papa, kayi abinda ya dace kawai." haka dai suka jima suna waya kafin sukayi sallama. Sallama take ji daga k'ofar d'akin kamar muryar data sani, "shigo." shine abinda ta fad'a cikin d'aga murya. Tana bud'a labulen d'akin ta shigo Khairat ta daka tsalle tare da ihu ta rumgume Hibba, murna sukayi sosai har Hibba ta dago da ita tana fad'in cikin harshen zarma "oh Khairat, kin canza." Itama a harshen zarma ta mayar mata da "ni ai na kusa nayi hushi dake, ace sai yau zaki zo gidana." "Kiyi hak'uri Khairat, kinsan fa karatu yayi zafi, wallahi yanzu haka daga ecole nake tare da driver." "Kuma fa hakane yan jarabawa ne." ta fad'a a harshen frensh. "Zauna mana." "Ba lokaci Khairat, yanzu haka ina zuwa gida zan tarar da malamin maths yazo." Juyawa tayi Khairat tabi bayanta suka fita suna hira tana shaida mata zata zo ta wuni idan sun gama jarabawar , sai lokacin Khairat taga ashe yamma tayi sosai ita tana d'aki zaune, Zuby suka tsinkaya wajen girki ita da Ruk'ayya da Saratu suna kama mata aiki saboda yau zata karb'e Umar Faruk, sallama Hibba ta musu suka amsa cikin sakin fuska kafin ta wuce, Khairat ce ta dawo zata wuce Zuby ta bita da harara, Khairat kuma wani burin son koyan girki ne ya shiga ranta dan haka ta fara danna kiran wayar Mama daga shigarta d'aki, Zuby ma dai ji tayi itama tana fatan samun k'ugu da gaba irin na Khairat d'in masu kyau da d'aukar hankali. *************** "Mamie, ki fad'a min yaushe zan fara zuwa wajen koyan girkin?" Da mamaki Mamie tace "Khairat zaki koya? idan kin fad'awa mijinki ya amince zaki iya zuwa kowane lokaci." "Ok zan fad'a masa, zaki ganni." "Amma ba zaki bari harmu dawo ba?" "Eh Mamie saimun dawo." tana fad'a ta kashe wayar. Wayar Umar Faruk ta kira, "hello baby." ya fad'a daga b'angarenshi. "Baby ya kake? " "In dai kina lafiya, to nima haka." "Lafiya lau nake, dama magana zamuyi." "Yanzu kuma?" "Eh." "To ina zuwa." "A'a ba sai kazo ba, zamu iya yi a waya ma." "To ina jinki." "Dama Mamie ce tace me zai hana na dinga zuwa gida tana koya min girki, shine nace zan fad'a maka dan saida amincewarka zanyi komai." "Me kuwa zai hana baby, ki shirya kawai ki fara zuwa, ai farin cikina ne kuma jin dad'ina idan kika zama chief a wajen girki." "Na gode baby, saika dawo." "Muahhhhhhhh."😘 ta qarashe da sumbatarsa, saida ya lumshe ido saboda dad'i da yanda sumbar ta ratsashi. ************* Kusan magrib ya shigo gidan tare da Abbakar, d'akin Zuby ya nufa yana kallon d'akin Khairat, da shigarshi bai sameta ba sai dai k'amshin turaren wutane ya mishi maraba, ga kwanukan abinci da aka jera masa abin birgewa, fitowa yayi ya d'auki buta ya fara alwala, yana cikin yi ta fito daga douche tayi wanka, saida tazo kusanshi zata shiga d'akin tace "sannu da dawowa." "Yawwa sannu, ashe ana can ana wanka." ya fad'a lokacin da yake shafar kai. "Um, na shiga wanka." Aje butar yayi ya kalleta yace "na wuce masallaci." "A dawo lafiya, amma fa karka dad'e." ta fad'a a shagwab'e. Murmushi yayi yace "ba zan jima ba." Masallaci ya wuce itama ta shiga ciki ta fara sallah kafin ta tsalla shirin tarbar mai gidanta..... 09/08/2019 à 21:40 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Wow wow wow wow wow wow wow wow, my *Heenat* ina tayaki murnar kammala wannan zazzak'an novel d'in naki mai sunan *nida yah Al'ameen*, a gaskiya ya ilmantar tare da nishad'antarwa, babban abin birgewa shine darasin dake ciki tare da manya manyan kalaman da ki kayi anfani dasu, shi yasa a kullum nake cewa ke *uwargijiyata* ce, insha Allah zamu kammala *k'angin rayuwa*, ina sonki tawa.💞😘_ _Bismmilahir-rahman-rahim_ 3⃣9⃣ Sai bayan sallah isha'i ya dawo gidan kai tsaye d'akinta ya wuce, tana zaune da alama shi kawai take jira, tsaye tayi tana fad'in "sannu da zuwa yah Umar." "Yawwa sannu, ya gidan?" ya fad'a yana zaunawa da alamar gajiya a tare dashi. Mab'allan rigarshi ya fara cirewa yana kallonta yayin da take zuba mishi jus d'in data had'a dominshi, saida ya cire rigar ya aje gefe sannan yasa hannu ya karb'i cup d'in da take mik'a masa, "na gode, Allah ya miki albarka." ya fad'a yana murmushi. "Ameen yah Umar, nima na gode." Yana shan sanyayyen jus d'in ta kuma zuba mishi abinci har kala uku, dad'i ne ya rufeshi sosai nan fa ya bud'e ciki ya kwashi abincinshi yasha ya k'oshi kafin yayi hamdala tare da sake saka mata albarka, kallonta yayi yace "dan Allah taimaka ki had'a min ruwa zanyi wanka." "To yaya." ta fad'a tare da tashi. Tana kai masa ruwan shi kuma ya fita yaje yayi wanka, koda ya dawo ya samu harta gyara wurin kamar ba aci abinci ba, yana so ya shirya kuma gaba d'aya kayanshi ne d'akin Khairat, kallonta yayi yace "k'anwata." "Na'am yah Umar." "Wallahi kaya nake son sakewa kuma gashi duk suna can d'akin." Cikin murmushi tace "lah yah Umar, kaje ka d'auko mana." Kanta ya dafa yace "Allah ya miki albarka." "Ameen." Fita yayi ya nufi d'akin Khairat, da sallama ya shiga ya sameta kwance akan gado da kayan bacci da littafi tana karatu, tana ganinshi ta mike tsaye akan gadon ta bud'e hannayenta, da azama shima ya qarasa wajenta shima ya rumgumota ya sauko da ita yana juyawa da ita tare da aika mata sumba, saida suka jima kafin ya sauketa suna kallon juna tace "nayi kewarka na wuni d'aya kawai." "Nima haka, ya kike?" Cikin turo baki gaba tace "lafiya k'alau, ya kake?" "Tunda kina cikin k'oshin lafiya to nima haka." Sakinta yayi ya nufi wajen kayanshi ya fara dubawa, bin bayanshi tayi ta mak'ale mishi a wuya yana ci gaba da da duba kayan yana d'auka, har saida ya gama tana bayanshi a mak'ale kafin yace "to sauko ni zan tafi." Saukowa tayi tana fad'in "yanzu shikenan tafiya za kayi, ni kad'ai zan kwana?" "Idan kina so na kwana ai saina kwana." ya fad'a kamar da gaske. Da sauri tace "a'a ba dani ba, ba zaka jamin magana ba." Rumgumota yayi ya sumbaci labb'anta yace "ki kula da kanki kinji." "Insha Allah, saida safe." A hankali yake sakin hannunta yana ji kamar karsu rabu, yana fita tabi bayanshi ta rufe k'ofar d'akin, kwance tayi tasa panka gabanta saboda zufar da take ji tana fito mata, bugawar da zuciyarta take ne da kuma harbawar da jijiyar kanta keyi yasa ta d'auko maganinta tasha sannan ta koma ta kwanta amma duk da haka tunani da kewar Umar Faruk sun dameta , abun kamar wasa saita fara tunanin irin abinda ke faruwa a d'aya d'akin, a hankali saita fara kuka har saida bacci ya d'auketa. _ALLAH ka rabamu da haukan kishi, ka sausauta mana kishinmu._ A wajen ango kuma da amarya yana shiga ya sameta ta cancara wata arniyar rigar bacci, amma tana jin shigowarshi sai taji ba zata yarda ya ganta a haka ba, da sauri ta haye gado ta rufe da zanin rufa, shi kuma ya riga daya ganta sai dai ba sosai ba, aje kayan hannunshi yayi yana dariya ya mik'a mata hannu yace "zo mana." Qara rufe fuskarta tayi tace "um um yah Umar." "Taso mana, nifa mijinki ne, ina so na ganki da kyau." Yanda yayi maganar yasa ta fara janye zanin daga jikinta, da qyar ta taso ta rarrafo ta sauko ta tsaya gabanshi amma tana kare jikinta, ganin yanda yake k'are mata kallo yasa ta rufe fuska ta juya zata koma kan gado ya rik'e hannunta, kwantar da ita yayi a jikinshi yana shafar duk wata gab'a ta jikinta, jin yana d'an wuce gona da iri yasa ta fara nok'ewa tana d'an tureshi daga jikinta, cikin muryar....yace "haba Zubeida, me yasa?" Kwantar da ita yayi akan gadon ya fara sarrafata cikin k'warewar daya samu a kwanakin da yayi a d'aya d'akin, saida ya kai mak'ura yayi kwance yayin da ya rad'awa Zuby a kunne tare da kai hannunta a....... yana so ta bashi a gajin farko kafin suje mataki na gaba, sam Zuby tak'i tare da dauke hannunta da sauri saboda ita abarma tsoratata tayi ba kad'an ba, yayi juyin duniya ta masa dan zaiji dad'i sosai saboda ya d'an saba da hakan amma tak'i, (wacce ta kasa tab'awa da hannu zata iya sakawa cikin...🙈my Heenat da aunty Aisha da auntyna Meerah suna nan), haka ya tashi ya fara hak'ar rijiyar amma baije ko ina ba Zuby ta fara masa kuka tana fad'in ta gaji ya daina zai kasheta, shi kam mamakinta yake ganin darensu na farko itace taja hankalinshi, (ranar ma ai sakata a kayi bayin kanta bane), haka ya tsaya babu abinda k'arda bare ya samu nutsuwa. Duk da sunyi wanka bai hana ya matsata a jikinshi ba yana sumbatarta dan yana so ya manta da abinda zuciyarshi keta raya mishi, ma'ana yana so ya manta da Khairat a qwaqwalwarshi musamman da yake d'akin daba nata ba, Zuby kam ganin kamar zai sake takurata ne yasa ta tureshi daga gareta da k'arfinta jiki na rawa ta juya masa baya, dan harga Allah taji ya gundireta a yau d'in nan kuma tana ganin da alama zaiyi jaraba, basar da ita kawai yayi har bacci marar dad'i ya d'aukesu. ************** Kamar yanda ya zama jiki kowa na gidan yayi sallah asuba kafin suka karya, Khairat ce yau tazo d'akin Zuby domin yin kari, ba yabo ba fallasa suka gama ta koma d'akinta, a lokacin da Umar Faruk zai fita saida ya shiga d'akin Khairat, duk da abinda ya dinga mata bata ji komai ba da qyar ta lallab'ashi ya fita, a motarshi yau ya fita Khairat ma a tata motar ta fita izuwa gida. Ta samu Mammie da Mamie zasu tafi gidansu Muzaffar ganin mahaifinsu ba lafiya, a motarta ta kaisu gidan kuma suka shiga tare, zaune suke a falon Baban suna masa sannu da jiki, likita ne suka shigo tare da Muzaffar, ko kallonshi ba tayi ba yayin da shi kuma ya kasa d'auke idonshi daga kanta yana kallon yanda tayi wani b'ulb'ul da ita ta qara yin fresh da ita ta qara kyau, mamaki d'aya yake shine hijabin dake jikinta wanda kuma ya kare masa ganin muhimman abubuwan da suke birgeshi a kanta tun kafin aurenta, ganin likitan ya fara duba Baban yasa suka mishi sallama suka tafi yana binta da kallo yana d'an cije lips tare da had'e yawu. *A d'an gurguje fan's.* Kwana biyu kad'ai yayi a d'akin Zuby amma kewar Khairat ta dameshi, yafi jin dad'in zamanshi acan danko ba komai tasan yanda take tana samar masa da nutsuwa, a yanzu kam bai damu ba tabbas kunya tana da kyau ga 'ya mace, yana tunanin meye banbanci tsakanin Khairat da Zuby, koda kuwa Zuby kunya tafi Khairat kuma za'a kira Khairat da marar kunya to shidai yana son wannan rashin kunyar dan yana da tabbacin shine kad'ai keda Khairat a yanzun. Khairat ma tana kewarsa kuma tana kishinsa, amma ganin lokacin tafiyarsu yayi yasa ta gama musu shiri tsaf gari kawai take jira ya waye. Zuby kuma a nata b'angaren takura da jaraba ne kawai sukawa Umar Faruk yawa, a kwana biyun nan ya gama gubdurarta dan kullum cikin sumbata da shafe shafe yake, a cewarta komai saiya tab'a jikin mutum ita kam ba zata iya ba. Duk ya gama sallama da 'yan uwa da iyaye wayewar gari yake jira yana ganin damace da zata sake mannashi da Khairat d'inshi. *************** Yau ta kama yammacin ranar *talata*, kuma *awa* d'aya ce ta rage jirginsu ya tashi, Umar Faruk ne tsaye kofar d'akin Zuby bayan sunyi bankwana , a tsakar gidan ma duk mutanen gidan sun taru sai yara dake ecole, haka ma Ishaq yazo danshi zai saukesu aireport da motar Umar Faruk, Khairat ce ta fito cikin riga da siket na kanti masu masifar kyau sai d'an kwalin data yane kanta dashi, babbar jakarta ce a hannu da waya sai qaramin farin glass d'in dake hannunta, tsaye tayi gabanshi tana kallonshi da murmushi a fuskarta, hannunta tasa a hankali ta kamo nasa hannun ta rik'e sosai tace "mu tafi." Ajiyar zuciya ya sauke ba tare daya kalli mutanen dake wajen ba dan soyayya ta rufe masa ido, sake qamqame hannunta yayi shima kafin ya janyota suka tsaya gaban iyayensu yace "iyayena mu zamu tafi, kuyi mana fatan alkairi." Baba ne ya fara da "to Umar faruk, Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lafiya, sannan ya dawo daku lafiya, sannan a kula sosai kaji, banda wasa da sallah da kuma karatu duk da dai ba jimawa zakuyi ba." "Insha Allah Baba." Khairat ce ta d'ora da "ai dama littatafaina zan tafi dan muci gaba da karatu." Kallon Mama tayi tace "Mama zamu tafi, saimun dawo." Addu'a suka musu Khairat kuma ta rumgume duka iyayen mata tare da Ruk'ayya, tana kawowa wajen Saratu ta tsaya tana kallonta, janyo Saratu tayi jikinta ta rumgume kafin ta saketa tana kallonta tace "ku kula da Yusuf." Cikin murmushi da jin dad'i Saratu tace "insha Allah 'yer uwa, Allah ya tsare." Hannun Umar Faruk ta sake kamawa suka juya zasu fita sukayi tozali da tanti Ma'u ta shigo cikin gidan..... Kai tsaye wajen Zuby ta nufa dan tafi kusa da 'kofar shigowa, cikin rad'a tace "ke me yake faruwa a gidan?" Itama cikin rad'a tace "Mama bana fad'a miki zasuyi tafiya ba? to ai yau ne." Harara ta banka mata kafin tayi wajen da suke tsaye, Baba ta fara kallo tace "malam, da hankalinka da iliminka, amma shine ka amincewa Umar Faruk da sutafi da wannan karuwar yarinyar qasar waje." Yanda maganar bata ma kowa dad'i ba haka ma Umar Faruk, sunkuyar da kai yayi yace "dan Allah tanti ki daina kiranta karuwa, hakan ba kyau." "Kai tafi can dallah, ba dakai nake ba da mahaifinka nake, zan dawo kanka daga baya." Maida kallonta tayi ga mahaifiyar Umar Faruk tace "ke dama bana take, dan kowa ya debo shararshi kanki yake dorawa, amma ki sani za kiyi nadama inhar kika bari d'anki ya tafi tare da wannan yarinyar, danna tabbata wani mugun abu suke nufinshi dashi." Kallonta takai ga Umar Faruk tace "kai kuma, me kake nufi, kana so kace 'yata zatayi zaman gadi ne a gidan har lokacin da kuka gamo gantalinku kuka dawo sannan ka sameta? to bari kaji sam ba zai yiwu ba wallahi, kamar yanda wannan abar take matarka haka itama Zuby matarka ce, dan haka babu inda zaku je ba tare da ita ba, in kuma kace tafiya zakuyi to akwai sharad'i." "Sharad'i na farko shine, kodai ku tafi da ita, ko kuma dai kaika fasa tafiyar ka barta ita kad'ai ta tafi dan dama ita ta saba bi garinta , k'in d'aya daga cikin biyun nan, to ka sani kana tafiya nima zan tafi da Zubeida daga gidan nan, kuma yanzu basai an jima ba." Shafa wuyanshi yayi yana tunanin abinyi Baba ne yace "haba Asma'u, bai kamata irin wannan magaganun na fitowa daga bakinki ba, kefa babba ce zaki iya jawa kanki raini a wajen 'ya'yan cikinki, da amincewata ne Umar Faruk zaiyi tafiyar nan, kuma ina da tabbacin babu abinda zai faru, tunda Umar Faruk namiji ne ita kuma mace, dan haka ki dubi girman Allah ki barsu su tafi." Cikin d'aga murya irin na marasa nutsuwa tace "iyee , yau ake shirin yinta fa a gidan nan, lallai abin duniya ya rufe muku ido, inba haka ba kai yanzu har wani alfahari kake saboda d'anka zaiyi tafiya da wannan, ko kunya baka ji ba dan Allah malam?" Mama ce tayi k'arfin halin cewa "babu wani son abin duniya kamar yanda ba kwad'ayi bane, mu mutane masu girmama mutane da suka karramasu, alk'awari ma abune mai girma shi yasa muka amince su tafi tare, badan komai ba sai dan ya cika alk'awarin daya dauka, dan haka Umar Faruk zai tafi domin shima yanzu d'aya ne daga cikin dangin Khairat, danko yanzu bama cire rai kan cewar Khairat na d'auke da cikin Umar Faruk, kinga kuwa sun riga da sun zama d'aya, zaifi kyau ki barsu sutafi ba tare da rai ya b'ace ba, Zubeida kuma naga ai koba auren Umar Faruk a kanta ainan gidansu ne, dan gidan nan ba bakonta ba zata iya zama koba Umar Faruk, kuma da kike cewa zaki taf da ita saida izinin Umar Faruk Zubeida zata bar gidan nan." Umar Faruk najin haka yaja hannun Khairat zasu wuce tanti ta sake shiga gabansu tana fad'in "wallahi idan kaga ka fita daga gidan toka tabbata ka bani takardar Zubeida." Zuby na jin haka ta matso kusan mahaifiyarta ta dafa kafad'arta tace "Mama, ki daina dan Allah, karki rabani da mijina." "Ke rufe min baki, duk danwa nake abun? badan ke ba." Sake maida kallonta tayi garesu tace "kaga kaifa nake jira." "Tanti...." hannu Khairat ta d'aga masa. Kallon agogon hannunta tayi ganin lokaci yasa ta mak'ala glass d'inta a fuska wanda ya qara mata kyau, kallon idon Umar Faruk tayi tana murmushi tace "kayi hak'uri Faruk, ka zauna da iyalinka tare da matarka, ina cikin farin ciki kasancewarmu tare, bana so raina b'ace bare na b'ata ran wani, ni zan tafi." Tana fad'a ta d'an d'aga qafafunta ta shafi fuskarshi tare da manna masa sumbata mai kyau a baki harda tsotsawa tayi kafin ta sakeshi a hankali suna kallon juna, kallon tanti Ma'u tayi fuska a had'e tace "ki tabbatar kun raba tsakanina da Umar Faruk kafin na dawo, idan kuma bakuyi ba, to ki sani al'amarin ba sauk'i dan dawowar ba zata muku dad'i ba." Tana fad'a ta fara raba hannunta dana Umar Faruk wanda ya rik'e hannunta gam amma ya kasa magana saboda mutanen dake wajen, a lokacin data qarasa zare hannunta daga nashi saida ya rufe ido saboda bugawar da zuciyarshi tayi , ganin tana tafiya da gaske yasa murya qasa qasa yace "Khairat." Duk da ba kowa yaji kiran daya mata ba amma saida ta juyo dan itama zuciyarta bugawar take, bye bye kawai ta masa ta wuce tare da Ishaq ya tafi kaita aireport dansu Mamie suna jiransu. Yana ganin b'acewarta ya juya da sauri ya nufi d'akin Mama, da shigarshi ya fad'a kan gado ya fashe da kuka danshi ji yake kamar ta rabu dashi kenan. Itama a mota cire glass tayi ta fara kuka Ishaq sai baice komai ba har suka isa, saida ta gyara fuskarta kafin ta bud'a murfin zata fita kuma ta tsaya, kallonshi tayi tace "Ishaq ko?" "Eh Hajia." "Dan Allah ka fahimtar da Umar Faruk banyi haka dan b'ata masa rai ba, na fahimci hakan ne kawai maslaha, inba haka nayi ba lallai ya hakura da tafiya dani ba saboda yamin alk'awari, bana so na zama silar samun matsala tsakaninsu, ka kula min dashi, karka bari ya shiga damuwa dan inada tabbacin son da yake min na hak'ik'a ne." Tana fad'a ta bar motar bata jira me zaice ba, ta samu su Mammie na tsumayinta kuma suna daf da tashi, ai kuwa babu b'ata lokaci suka tashi duk da tambayar da suke mata ina Umar Faruk amma babu amsa, taga kawai take kallo hawaye nabin fuskarta danta riga data tsara yanda tafiyarsu zata kasance tare da bada armashi, a haka dai har suka sauka manyan jami'ai ne suka d'aukosu a filin jirgin kamar yanda shugaban qasar ya tsara kuma ake zuwa tarbar kowane babban bak'on. Babban hotel ne aka kamawa manyan bak'in kowa da nashi d'aki mai kyau da 'kawa , kai tsaye Khairat d'akinta ta wuce zata shiga wanka saida taji inama suna tare da tare zasuyi wankan, haka ta fito ta shirya sannan suka fita wajen cin abinci tare da manyan mutane.... _Kar kuce bakuji dad'i ba da basu tafi tare ba, hakan ma nada nashi fa'idar._ 😍😍😍 09/08/2019 à 21:40 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 💞💞💞💞💞💞💞 *my BK* 💕💕💕💕💕💕💕 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣0⃣ Kallonta ake sosai saboda ganin shirin da tayi, doguwar riga ce ja mai kyan gaske da hannaye iya gwiwa, amma saita b'ata tsarin ta hanyar d'ora qaramin hijab wanda ya rufe mata wuya, kujera kawai taja ta zauna ba tare data kula dasu ba, abinci suke ci har lokacin da idonta ya sauka akan teburin da Muzaffar ke zaune wanda ya kasa komai sai kallonta, wata tattausa harara ta jefa masa kafin ta d'auke kanta, a haka suka gama kowa ya tashi dan komawa masaukinshi, Khairat na daf da shiga d'akinta taji an rik'e hannunta. Da mamaki ta juyo tana ganin Muzaffar ta qara had'e rai tace "malam miye haka? sakeni dallah, ko ka manta ni matar aure ce?" Wani murmushi ya mata yace "matar aure, to saime, ina mijin naki yake? ko dai shima ya kasa zama dake ne ya korok....." Shak'ar wuyar rigarshi da tayi yasa yayi shiru, kamar zata sumbaci fuskarshi ta matso sannan tace "karka sake ka fad'i maganar banza a kaina ko mijina, danshi ba jahili bane irinka." Sakinshi tayi ta bud'a d'akin da makullin da aka basu ta shiga ta kuma maida k'ofar ta rufe, yana kallonta ya jima kafin ya koma nashi d'akin yana mamakin yanda Khairat ta sake mulmujewa bayan yasan wanda ta aura ba mai kud'i bane, ga kyau data qara sai yaji sabon kishi da qaunarta sun mamayeshi, tana shiga ta cire doguwar rigar ta d'auki wata qaramar riga shara shara ta saka wacce ta tsaya iya k'ugunta, daga ita sai pant ta kwanta akan gadon ta d'auki waya ta dannawa Umar Faruk kira. ************* Mama na ganin ya shiga d'akin itama tabi bayanshi, cikin tashin hankali da mamaki Mama ta qarasa kusa dashi ta dafa kafad'arshi, shiru bai d'ago ba amma saiya tsayar da rera kukan da yake, d'an daddab'a kafad'arshi tayi tare da cewa "Umar Faruk." Tashi yayi zaune yayi qasa da kanshi yana goge fuskarshi kafin yace cikin muryar kuka "na'am." Hab'arshi ta kamo ta mayar da kallonshi kan fuskarta tace "hawaye a idon namiji, meya faru Umar Faruk, meya saka zubar da hawaye haka, saboda ta tafi ne?" Wasu hawayen ne yaji sun sake malalo mishi a fuska, hakalin Mama ne ya rubanya tashi da sauri tasa hannu ta share mishi tana fad'in "Subhanallah, dan Allah ka daina, kana tayar min da hankali mana, ka fad'a min meye damuwar." Sake goge hawayen yayi ya saisaita nutsuwarsa sannan yace "Mama ban tab'a sanin a baya baso nake ba sai yanzu, ban tab'a sanin cewa Zuby ina mata son yan uwantaka bane saida Khairat ta shigo rayuwata,Mama ji nake kamar ta tafi da rayuwata ne, bansan me yasa naji na kasa tausar zuciyata ba, amma tunani nake kamar ta tafi kenan ba zata dawo gareni ba, wallahi Mama bana jin dad'i gaba d'aya, Mama ki taimaka min dan haka, ki taimaka min Mama." Ya qarashe da fad'awa kan cinyar Mama da bai tab'a yin hakan ba tunda ya mallaki hankalin kanshi, cike da tausayinshi da qauna ta fara shafashi tana fad'in "kayi hak'uri babban mutum, bana son kukan nan kaji, insha Allah Khairat zata dawo, nasan ba zata wuce kwanan ukun da kuka d'iba ba dan na yarda da ita, maganar Zuby kuma Umar Faruk ni dama nasan babu soyayyarta a cikin zuciyarka, saboda ban tab'a jin kalmar so daga bakinka ba izuwa Zubeida, ba kai kace kana sonta ba mune muka hadaku, kuma cikin sa'a kuka mana biyayya baku bijire ba, ba zanyi mamaki ba dan yanzu ka samu masoyiyar zuciyarka, kamar yanda nake da yakinin ba zaka tab'a fifita Khairat akan Zubeida ba, saboda na yarda da kai kuma na yarda da tarbiyar da muka baka, bugu da qari kuma kana da zuciyar da zaka iya boye abinda kake so kuma kana da zuciyar da zaka iya son mak'iyinka ma, dan haka abu d'aya nake so da kai yanzu shine, ka cire wannan damuwar ka kuma kwantar da hankalinka ta yanda hakan ba zai shafi Zubeida ba, kaji ko?" D'agowa yayi ya sake goge fuskarshi yace "to Mama, insha Allah zanyi yanda ki kace." "Yawwa Umar Faruk, yanzu ka tashi kayi alwala, nasan yanzu an kira sallah saika tafi masallaci." "To." kawai ya fad'a ya fita yayi alwala sannan ya bar gidan, lokacin tanti tabar gidan kowa ma ya kama gabanshi Zuby ma na d'aki tana kuka, ko kallon d'akinta baiyi ba dan maganar gaskiya ji yake baya son ganinta, yana fita yaji wayarshi na kururuwa, ganin bak'uwar number yasa ya saki murmushin gefen labb'a tare da d'agawa ya d'ora a kunne. Cikin sanyayyen murya tace "baby, ya kake?" Lumshe ido yayi yana jin wani irin dad'i da sanyi yana ratsashi, a hankali ya furta "banda lafiya, saboda kin tafi kin barni." Rufe ido tayi kafin tace "kayi hak'uri, hakan ne kawai maslaha, amma ai zan dawo da wuri." Takawa ya fara yi a hankali yana fad'in "baby kin tafi kin barni da sonki, Khairat, sai yau ne na qara tabbatar da irin son da nake miki, yaune na samu tabbacin gazawar da zanyi idan na rasaki, Khairat dan Allah karki rabu dani ki zauna tare dani hakan ne kad'ai zai sani farin ciki, sannan kiyi sauri ki dawo gareni dan a gaskiya ba zan iya farin ciki ba alhalin kina nesa dani." Hawaye ne suka fara bin fuskarta sai taji kamar ta samu kanta a gabanshi, cikin kuka tace "karka damu Faruk, ba zan iya rabuwa da kai ba nima, ina sonka kuma babu abinda zai rabu insha Allah, yanzu ka rufe idonka." Cikin murmushi kamar yana gabanta ya rufe ido, a hankali ta furta "je t'aime (i love you), prend bien soin de toi (ka kula da kanka)." Kasa bud'a ido yayi saboda farin ciki, jin ana gaf da tayar da sallah yasa yace "baby, zan shiga masallaci." "Kayi mana addu'a baby." "Wace iri?" "Um, ka mana addu'a Allah ya barmu tare, Allah kuma ya tsone idon mak'iyanmu, bizou." tana fad'a ta kashe kiran. Masallaci ya shiga sukayi sallah magrib bai fita ba har akayi isha'i sannan suka fita tare da Ishaq yaje gidansu, number da Khairat ta kira ya fara kira amma bata shiga, Ishaq ne ke kallonshi ganin ya aje wayar gefe cikin fushi yasa Ishaq gyara zama yace "kasan wani ma? Hajia Khairat fa ta bani sak'o wajenka." Da sauri ya kalleshi yace "me tace dan Allah?" "Um, tace nace kayi hak'uri, tasan za kaji ba dad'i rashin tafiyarku tare, amma dai ita maslaha ce tayi a ganinta, kuma bata son shiga tsakaninka da danginka, sannan wai..." sai yayi shiru yana kallonshi. "Sannan me?" ya tambaya cike da zumud'in son jin abinda zai fad'a. Hararanshi yayi kafin yace "waina kula mata da kai, kamar wani qaramin yaro, ko kuma ni d'in yaronka ne." Fashewa yayi da dariya ya d'auki pillow ya rumgume amma ya kasa magana, duka Ishaq yakai masa yana fad'in "mijin Hajia, kaifa yanzu nan bala'in sonta kake ko?" "Kana mamakin hakan ne? ai yanzu bana jin zan iya numfashi idan babu wannan Hajiar taku, bansan ya akayi sonta yamin mugun kamu ba haka, amma dai ina qaunarta fiye da yanda nake qaunar kaina." "Amma dai sai nake ganin zaifi kyau ka dinga sassautawa tare da b'oyewa, tunda kaga ba ita kad'ai gareka ba akwai wata, zaka iya shiga hakk'in d'ayar, hakan kuma kasan zai iya halakar da kai." Ajiyar zuciya ya sauke yace "hakane abokina, yanzu haka ji nake inama ace ina da hali, da zanbi Khairat ne har inda take, haka kuma yanzu haka ji nake bana son ganin Zubeida da mahaifiyarta, saboda da bata fad'awa tanti ba da bata zo gidan ba, amma dai duk da abinda nake ji a kanta zanyi qoqari naga na b'oye hakan, ba kuma zan tab'a tauyeta ba insha Allah, dan bana so na tashi a ranar gobe da shanyayyen barin jiki, a matsayin wanda bai adalci a tsakanin matanshi." Sun jima suna hira kafin ya tashi ya shiga gidan kai tsaye kuma d'akin Zuby ya shiga, zaune ya sameta akan kujera ta zuba tagumi idonta jawur alamar tasha kuka, cikin sanyin jiki ya zauna kusa da ita yana kallonta yace "Zubeida." Kallonshi tayi tace "na'am." "Meya faru, kuka kike?" Kai kawai ta girgiza masa, kasantuwar baya son doguwar magana yasa ya janyota jikinshi ya kwantar da ita yana daddab'ata, duk da tana jikinshi amma hankalinshi baya wajen gaba d'aya, tunanin 'yar qaramar rayuwar da sukayi da Khairat da irin farin cikin daya samu a tare da ita, jin yanda yake ta shafarta yasa ta d'aga daga jikinshi tana fad'in "bara na zuba maka abinci." Bata jira maganarsa ba ta fara zubawa, shima kuma baisan ta fad'a ba, harta gama zubawa ta juyo ta kalleshi da nufin magana amma saita tsaya tana kallonshi, da mamaki ta fara kallonshi ganin yayi kamar gunki murmushi kad'ai ke bayyana a fuskarshi, ga dukkan alama yayi nisa a tunani, a hankali ta d'an kai hannunta a hannunshi ta bubbuga, da sauri ya zabura yana kallonta, "kaci abinci." kawai ta fad'a. "A'a, bana....." ganin ba zai kyauta ba yasa kuma yace "to." Gyara zamanshi yayi ya fara cin abincin badan yana jin dad'in abincin ba, da qyar ya d'an tuttura badan yaci mai yawa ba ya barshi, tashi yayi ya shiga wanka koda ya dawo ta gyara wajen, kayan bacci yasa ya fita wajen Baba sukayi saida safe hakama Mama da sauran iyayensu, saida ya tsaya kofar d'akin Khairat yana ji kamar ya shiga amma ganin ba zai kyauta ba yasa ya koma d'akin, koda yaje ya samu harta kwanta ta duk'unk'une kamar mai bacci. Jiki a sanyaye ya kwanta gefenta zuciyarshi na hasko mishi daren farkonshi da Khairat, a hankali ya gyara kwanciyarshi yana sakin murmushi, rumgume hannayenshi yayi ya rufe ido kamar mai bacci, amma abinda yake tunani yana gaf da zautar da tunaninshi, jin shiru bai tab'ata ba yasa ya bud'a ido ta juyo ta kalleshi, da matuk'ar mamaki ta kalleshi ganin ya juya mata baya shima kamar yanda tayi, duk da hakan bai mata dad'i ba amma ba zata iya masa magana ba ita, dan haka ta shereshi itama kawai tayi baccinta, shi kuma saida ya raba dare biyu kafin bacci ya d'aukeshi wanda rabinsa duk mafarkin Khairat ne a ciki. ************** Tana zaune akan gado ta shiga Internet tana duba yanda ake girki Mamie ta shigo, zaune tayi gefenta tana kallonta tace "hutawa ake?" "Eh Mamie, ina duba yanda ake girki ne." "Toh , to ina ganin ko zamu fara ne tun daga nan, tunda naga kina son koyon girkin da wuri." Da sauri ta aje wayarta ta rik'e hannun Mamie tace "eh Mamie, dan Allah mu fara." Dariya tayi ta shafi kumatunta tace "karki damu zamu fara, tunda zamane kawai zamuyi kafin isowar sauran bakin, amma kafin nan ki fad'a min, me yasa baku taho tare da Umar Faruk ba? bayan nasan an shirya tafiyar dashi." "Mamie, an samu matsala ne, wannan masifaffar matar ce ta hana mu taho tare." "Wace mata ce wannan?" Cikin yamutsa fuska tace "wannan mahaifiyar matar tashi mana." "To shikenan, bara na samo abin rubutu saimu fara kafin mu koma gida muyi a aikace." Fita Mamie tayi bayan wani lokaci ta dawo da littafin rubutu da alk'alami, zaune Mamie tayi tace "to ga wannan, zan dinga fad'a miki sai kina rubutawa." Kamar wasan yara kuwa sai suka fara, sun jima Mamie na fad'a mata tare da fayyace mata komai kwatta kwatta kafin suka tashi yin sallah. *A gurguje fan's* A kwana *uku* _Need your prayers_ 09/08/2019 à 21:40 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣1⃣ A kwana ukun nan Khairat da Mamie ba suda abinda suke daya wuce koya mata girki, indai har suna zaune basu tafi abinda ya kawosu ba to aikinsu kenan, idan kuma ba tare da Mamie ba to Khairat na d'aki tana kallon yanda ake wasu kalolin girkin a Internet, gaba d'aya basu cika waya da Umar Faruk ba ,domin kuwa sam baya son shiga hakk'in Zuby, idan yana wajen aiki kad'ai suke samun yin waya a nutse sai kuma tsakanin sallah magrib da isha'i, da anyi sallah isha'i kuma gida yake shiga kuma baya fita a wannan lokacin, hakan yaba Khairat damar koyan abubuwa da dama a wajen Mamie a wannan 'yan kwanakin, kamar yanda a wannan kwanakin ne ta qara tabbatar da irin son da take ma Umar Faruk, tunaninshi na hanata sakewa sosai kamar yanda maganganunshi ke hanata walawa, hakan yasa ta matsu ta koma dan tana kewarshi sosai kuma tana so ta faranta masa fiye da baya. A ranar da duka bak'i suka hallara anyi abinda ya tarasu bayan gabatar da kai da kowa yayi, sai lokacin Khairat taji haushin rashin tafiyarsu tare da Umar Faruk a lokacin data gabatar da kanta a matsayin mai aure, amma mijinta bai samu halartar taron ba, sab'anin kowa daya gabatar da iyalenshi gaba d'aya, haka ma Muzaffar ya gabatar da kanshi a matsayin shi kad'ai (single) 😂, a haka dai aka gabatar da taron cikin farin ciki tare da qarawa juna ilimi, inda shuwagabannin suka keb'e domin tattaunawa, yaran mata ma haka maza ma haka, su Khairat ma sun tattauna ta yanda zasu bawa iyayensu gudummuwa domin ci gaban siyasarsu, anan aka watse tare da tunanin safiya ta waye kowa ya hau jirginshi su koma gida. **************** Sam rayuwar babu dad'i tunda Khairat ta tafi, duk ya zama wani silent dashi kamar ba mai kazar kazar d'in nan ba, yana matuk'ar buk'atar wasu abubuwa amma ya kasa samu a wajen Zuby, yana buk'atar jin sumba daga wajen Khairat da wasanni da kuma yawon surutunta da wayan tab'a jikinshi, a yanzu hakan ne kawai ke d'awainiya dashi, dan lokuta da dama sai yaji kamar tana masa magana ko kuma ta sumbaceshi, turarenta kuma yanzu haka su yake fesawa a jikinshi, kamar yanda kullum saiya shiga d'akin da sunan zai d'auko wani abu, haka zai kwanta akan gadon ya d'auki kayanta yana shak'ar k'amshinsu hakan ne kad'ai ke masa dad'i. Yayi iya qoqarinshi wajen ganin ya manta da hakan ya kuma mayar da hankalinshi akan Zuby, amma abin yaci tura kuma Zuby ta bada gudumuwa wajen hakan, wani lokacin haka zai daure ya fara sumabatarta saita dinga janyewa tana nuna bata so, baisan me yasa take haka ba amma dai shima ya gaji, dan gaba d'aya tunaninshi dama na wani wajen, duk da baya tauyeta ta ko wane b'angare, amma fa tunani da murmushi ne sukafi yawa a cikin al'amuranshi yanzun, dan ko abinci bai cika ci ya k'oshi ba." A yanzun Zuby ta fahimci hankalinshi na kan Khairat, hakan kuma ba qaramin b'ata mata yayi ba, ta fad'awa Mama amma tace ta rabu dashi karta yarda ta nuna masa tana damuwa da halin da yake ciki, da kanshi zai dawo ya nemeta tunda itace a gabanshi yanzun, wannan shawara da Mama ta bata bata anfaneta da komai ba sai k'unci, shareshin da tayi yasa shima zuciya ta d'ebeshi ya shareta, idan ya shigo kwanciyarshi kawai yake yayi karatu daga nan bacci ya daukeshi, sam ya daina nemanta tsakaninshi da ita kawai gaisuwa, sai maganar ci abinci ko sannu da zuwa, duk da hakan na damunta amma bata nuna masa, kuma gashi an horeta akan karta kulashi ita shine zai kulata, shi kuma yana ganin ai shine namiji kuma yayi iya qoqarinsa amma bata bashi had'in kai, hasali ma nuna ya gundureta take shi kuma baya jin dad'in hakan. Ana cikin hakane kuma ta koma école, shike ajeta kafin ya wuce wajen aiki, kasancewar ranar juma'a ce hakan yasa ya biyo ya daukota, kuma tun safe ta fajimci yana cikin farin ciki, kuma tasan yana farin ciki ne saboda yau kwana uku, a lissafinta yau Khairat zata dawo, to amma ba komai tazo duk da haka ai kwananta bai qare ba, a fa tunaninta. Har yamma Umar Faruk na gwada kiran wayar Khairat amma bata shiga, hankalinshi ne ya fara tashi amma daya tuna dama ita ke kiransa bashi ba saiya kwantar da hankalinsa. *************** Tashin dare jirginsu zaiyi, tare take da Mammie da Mamie da Papa zasu shiga acessaire (lift), mutane suka samu sun shiga, ganin sai sun jira yasa Khairat kama hannu Mammie cike da karsashi tace "kawai muje a matakalar haba, kinga saimu motsa jiki." "Ke ke, rabu dani dan Allah, ba zan iya ba, jiri nake gani idan na hau." haka Mammie ke fad'a tana bin bayan Khairat data ja hannunta. Haka suka fara takawa a hankali, ganin yanda Mammie ke rik'e da wajen take takawa a hankali yasa Khairat sakin hannunta ta fara takawa da sauri tana sauka tana fad'in "saimun shekara bamu kai qasa ba in muka bi ta taki." Tana kusa da sauka taji qarar Mammie, da sauri ta juyo ganin Mammieta fad'i qasa yasa ta jefar da jakar hannunta ta ruga a guje ta qarasa, "Mammie, lafiya, meya faru ne Papa?" Suna cikin jajen abinda ya faru saiga ambulance har ankira musu saboda anan ba wasa da lafiya, babban asibiti mai kyau aka kaisu, bayan duba Mammie aka basu izinin zasu iya tafiya, amma tana buk'atar hutu sannan ba'a so ta taka qafarta, kuma gashi bayanta ma ya bugu shima an d'orata akan magani, wayar Umar faruk ta fara kira danta fad'a masa halin da ake ciki, bugu d'aya biyu ana uku aka d'auka. "Hello baby." cewar Khairat cikin taushin murya. A gadarance Zuby tace "baby dai, waye babyn to, ke yanzu wannan ya miki kama da qaramin yaro? to yana hutawa kuma yace baya buk'atar takurawa bare a tasheshi daga bacci, dan haka ya bani ikon na d'aga wayar duk wani qare da jaki daya bugu masa." Tana fad'a ta kashe wayar ta aje tana dariyar mugunta, da sallama ya shigo d'akin yayi wanka tare da d'auro alwala, bai kula da komai ya fara shirinshi tana zaune tana kallonshi, har saida ya gama shirinsa cikin wani farin yadi shara shara mai kyau wanda ya amshi jikinshi, machette ya d'auka tare da hula da agogo ya nufi inda Zuby take ya bata, karb'a tayi tana kallonshi shima ita yake kallo. "Me zan maka dasu?" ta fad'a cikin rashin fahimta. "Ke yanzu har saina fad'a miki me za kiyi? saka min za kiyi to, tunda naga ke baki tab'a tunanin tayani shiri ba bare nasa ran wata rana zaki min shirin da kanki ma." Aje kayan tayi a saman gado tace "oho, kana fad'a min yanda waccen karuwar take maka ne? to ba zan iya ba, saika jira idan tazo saita maka har wanka ma idan kana so." Wata irin tafarfasa yaji zuciyarshi nayi, a qufule yace "Zubeida na fad'a miki karna sake jin kin kirata da karuwa ko, kuma idan ma karuwar ce ai tawace, dan haka karna sake ji, idan ba zaki iya abinda na saki ba ki bari amma ba sai kin fad'a min magana ba." Tsaki yayi ya d'auki kayanshi ya fara mak'alawa ita kuma ta d'ora da "ba zan daina kiranta karuwa ba tunda ai karuwar ce, dama kasan ina da haushinka wallahi shiru kawai na maka, bansan dame waccen karuwar ta fini ba da har kafi sonta a kaina ba." Rintse ido yayi yace "karki sake fad'a mata karuwa." "Saina fad'a d'in, me zaka min?" Wata zuciyar ce ta d'ebeshi ya kifeta da wani marin da saida ta fad'a kan gado, duk da ta fashe da qara amma sam bata ji ba saboda jinta ya d'auke, da hannu ya nunata yace "wannan ba d'abi'arki bace, ki sake hali inhar kina so mu zauna lafiya dake, ke kinfi kowa sani na bana d'aukar raini, amma na lura dake tun ranar da kika ganni ba kaya a gabanki, kika rainani ko kuma nace aka saki kika rainani, to wallahi ba zan d'auka ba, ke kinsan waye Umar Faruk." Ko sallaya bai d'auka ba ya fita ya bar gidan, kuka ta dinga rerawa har Ruk'ayya dai taji abin yayi yawa ta shigo ta sameta, daga tsaye ta dafa kafad'arta tace "Zuby, yaya ne ko?" Shiru tayi dan haka tace "dan Allah kiyi hak'uri ki daina kuka, idan Mama taji ba za taji dad'i ba kema kin sani, kuma ya kamata ki dinga bin yah Umar a hankali, tunda ke kinsan halinshi da zuciya da hushi ga kuma saurin hannu, dan Allah ki daina kukan nan kiyi shiru ki rabu dashi." Ko motsawa ba tayi ba bare ta amsa mata, dan haka ta fita daga d'akin tana mamakin Zuby, dan bata santa da haka ba kuma duk da bata shiga harkarsu, amma dai ta d'an fahimci akwai matsala a tare da ita, dan ko zaune suke tsakar gida yah Umar ya shigo, sai dai ya wuce d'aki shi kad'ai ita kuma sai dai tace sannu da zuwa daga nan inda take zaune, ba zata tashi ba inba wani babba yace ta tashi ba, haka ko d'akin ta shiga idan suna tare, sai dai ta sameta ita akan gado shi akan kujera, koshi a kujera ita akan gado sam ba zaka gansu kusa da juna ba, sab'anin Khairat da zata samesu daf da juna wani lokaci ma ko qafafunshi akan jikin Khairat d'in ko ita nata qafafun, da wannan tunanin dai ta shiga harkar gabanta. *************** Yana fita ya fad'a mota dan yanzu ya barwa Aliyu motonshi, kasa tayar da motar yayi saboda zafin da zuciyarshi take, ji yake kamar ya d'auki mataki marar dad'i akan Zuby, danshi baya son matsala ko kad'an, ganin yake akan me Zuby da quruciyarta zata lalata kanta ta zama kamar wata tsohuwa, yana nan inda yake wayarshi ta sake ruri, yana dubawa yaga farin cikinshi ce, itama kuma ta maido kiran ne dan bata yarda da abinda Zuby ta fad'a ba, yana ganin lambar ya d'auka jiki sanyaye ya d'ora a kunne. Shiru tayi saboda tana so ta tabbatar dawa ya d'auki wayar yanzu, jin shiru yasa yace "Hello." Jin amon muryarshi ba karsashi ba kamar yanda ya saba ba yasa tace "baby, meya faru, waya tab'a min kai ne?" D'auke wayar yayi daga kunne ya kalla sannan ya sake mayar da ita yana fad'in "me kika gani?" "Baka cikin farin ciki, ni kuma ba haka nake so ba, fad'a min waya tab'a min kayana, yanzu shima ranshi ya b'ace." Wata tambaya ce zuciyarshi ta wurgo mishi _"anya kuwa Zuby itama tana sonka?"_ Basarwa yayi yace "tabbas, bana cikin farin ciki, amma ki barshi kawai." "Haba dai, bana da hankali ne da zan barka a wannan halin, kaga ina zuwa, yanzu kayi connecté kaga abin mamaki." "A'a Khairat, ba yanzu ba, masallaci zanje yanzu." Cikin d'aga murya da raha tace "a'a ban yarda ba, kawai kayi abinda nace, ba zan tab'a barinka kaje masallaci cikin b'acin rai ba." "To naji." ya fad'a ba annashuwa a tare dashi." Yana d'orawa Khairat ta kirashi appel vidéo, d'auka yayi amma a take ya lumshe idonshi, ganin haka yasa Khairat bushewa da dariya tace "bud'e ido malam Umar Faruk." Bud'e ido yayi ya sauke akan qirjinta daya fito yayi fam, saboda wata qaramar bras ce tasa wacce ta matse qirjinta ya fito sama, sai kuma qaramin wando iya cinyarta shima, ga gashinta data baza a bayanta ba zaka tab'a rabata da larabawa ba ko india, d'an yatsanta tasa tana yawo dashi akan fuskarta harta saukar dashi akan bakinta sannan tasa yatsu biyar ta sumbata tare da kashe mishi ido ta kuma watsa mishi sumbatar. Wani irin narkewa yayi a kujerar motar yana d'an cije lips yana marairaicewa kamar zai fashe da kuka, ganin ta fara kamashi yasa ta tashi tsaye ta aje wayar yanda suke kallon juna da kyau ta fara taka rawa irinta india cikin qwarewa da iyawa tana rera wak'ar *humsafar*. _Mere tu sare savere._ _Baho me tere tehre._ _Mere tu sare shave._ _Mere sat nahi hai_ Da irin haka ta dinga karairaya jikinta tana rawa (in baku manta ba gogagiyar 'yar rawa ce ko a india), saida ta gama ta koma ta kwanta Umar Faruk kuma wata azababbiyar sha'awarta ce ta taso mishi, da qyar ya fizgi muryarshi yace "baby....yaushe...zaki dawo..gareni?" Kafin ta bashi amsa wayarshi ta d'auke babu caji, dole ya hak'ura ya lik'a wayar a cajin dake motar a haka ya tayar da mota ya matsa k'ofar gidansu Ishaq ya fito suka wuce , duk da ya shiga farin ciki, amma kuma ta barshi da ciwo. Haka yaje masallaci ya dawo ba qwarin jiki, saida Ishaq ya shiga gida ya fito suka sake wucewa wajen aiki tare, babu abinda yayi sai ganin Khairat a wannan yanayin, shi dai kawai ya sani koma karuwanci ne Khairat ke masa, to tabbas yana son wannan karuwancin, a haka suka tashi yana tunanin idan ya koma zai sameta tazo, amma kash yaje ba Khairat, hakan yasa tunda yayi sallah magrib ya fara kiran wayarta amma shiru. Khairat kam na d'akin Mammie suna hira har saida tayi bacci, sannan kowa ya koma d'akinshi, tana zuwa kuma bacci itama ya d'auketa.... ************** Saida safe yana wajen aiki ta kirashi take fad'a masa abinda ya faru, cikin rashin jin dad'i yace "ayya, dan Allah ki gaishe min da amaryar, kice ina mata sannu." "Zan fad'a mata insha Allah." "Yanzu kenan yaushe zaki dawo?" "Ai tare zamu taho idan taji sauk'i." "To, ya zanyi? sai hak'uri, Allah dai ya bata lafiya." "Ameen." ************* Mamie kuma naci gaba da koya mata girki da kalan jus da wasu abubuwan tab'awa, a haka suka qara kwana biyu kuma a ranar suka sake shirin tafiya, Khairat ce ta fita tace zatayi siyayya kafin su wuce... _Me kuka ce fan's?_ 😍😍😍 14/08/2019 à 15:32 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣2⃣ Tunda ya shigo haka ya gama duk abinda ya saba amma babu wanda ya kula wani tsakaninshi da Zuby, ganin babu ko plate akan tebur yasa shima ya shareta bai mata maganar abinci ba, akan kujerar ya kwanta yana latsa wayarshi, a hankali yake duba photunan da suka d'auka da Khairat musamman wanda take sanye da hularsa, haka ake kwance abinshi har gari ya waye. Washe gari ma tare suke shiri da ita amma babu mai kallon wani, har saida suka gama ta d'auki jakarta zata fita a daqile yace " haka zaki fita baki karya ba?" Saida ta harareshi tace "kana da matsala da cin abinci nane? " "A'a, kije." Yana fad'a yayi wuf ya fita daga d'akin ya barta tana rufewa, kosu Mama bata kalla ba ta wuce, su kuma da kallo suka bita yayin da sukansu suke tunanin, yaushe Zuby ta zama haka marar kunya, suda suke zaton wuta a maqera sai kuma su ganta a masaqa, k'ofar gidan ta sameshi ya paka motar da alama ita yake jira, d'auke kai tayi ta kama hanya ta nufi bakin titi, kallon kan bala'i ya bita dashi😂 da tsananin mamaki, yana kallo harta kai bakin titi tana jiran taxi, kai ya girgiza ya taka motar da k'arfi, yana kaiwa kusanta ya kawar da kanshi kamar baisan da wata halitta ba a wurin ya wuce, ganin ya wuce yasa ta bishi da kallo baki bud'e, dan tunaninta zai biyota ne kuma ya bata hak'uri, a ranta tace "anya Mama ta bani shawara mai kyau, karfa na tsaya jan aji da hauka Umar Faruk ya sub'uce min." Da qyar ta samu taxi hakan yasa taje a makare, ta kuma yi niyyar idan aka tashi kai tsaye gida zata je ta fad'awa Mama, dan ba zata iya da wannan shawarar ba, gashi duk da ta saka mishi magani a abincin amma bata ga wani canji ba, kuma itama tayi wanka da wanda aka bata amma shiru, na wajen Khairat ne kawai ya rage tayi aiki dashi, kuma duk kusantar da yake mata bai nuna yana wani jin dad'in da zai iya kasheshi, a tak'aice dai bata ga wani anfanin abubuwan da take yi ba. ************ *13:20* ta shiga gida, zaune ta samu Mama akan tabarma tana cin wake da shinkafa, jefar da jakarta tayi har tana neman buge Mama sannan ta zauna tana cire hijab da d'an kwali, Mama kallonta take harta d'auki ruwa tasha kafin ta aje tace "Mama, akwai matsala fa?" Cikin harara Mama tace "to ke kuma dan ubanki, baki gajiya da matsala ne, me kuma ya faru yanzun?" Cikin turo baki tace "Mama, sam shawarar da kika bani ba tayi ba, haka ma wannan magungunan naki babu abinda suka qara mana, yanzu haka maganar da nake miki yah Umar jiya marina yayi, kuma har yanzu bama magana ko kulani baiyi ba." "Mtsssss." shine dogon tsakin da Mama tayi. "To shine me, dama wannan ce matsalar, waike yaushe zakiyi hankali? kina mace amma sam ba kyada aji da kama kai, to yanzu me kike so na miki da kika zo nan so kike nace kije ki masa magana ko? to kiji yarinya, kamar yanda nace karki yarda ki kulashi, ki barshi zaiyi ya gaji ya dawo gareki , kuma karki qara cewa magungunan dana baki basuyi ba, sai dai in kece ki kayi ba daidai ba." "Mama, wallahi duka nayi yanda ya dace, kawai dai ba sa'a ne wallahi, nifa gaba d'aya na rasa me yake damun yah Umar, wallahi ni harma na fara tsanarshi, kwata kwata bana son zaman gidanshi ma duk na fara takura." "Ke! fita idona wallahi, ke kinsan me kike fad'a kuwa? to kima cire wannan tunanin a ranki, dan aurenki dashi mutu ka raba ne takalmin kaza, wallahi kina gidanshi har sai yayi kud'i kuma mun moreshi." Da mamaki tace "kud'i kuma Mama, an fad'a miki zaiyi kud'i ne?" "Ke kuma a tunaninki nan zai zauna baiyi kud'i ba? "Aina jima da sanin zaiyi kud'i, shi yasa ma na shiga na fita na had'aku aure." "Tohh, lallai, nidai yanzu kawai kisan ya za kiyi dani wallahi, danni rainin hankalinshi ya fara isata." Cikin sassauta murya Mama tace "yana kusantarki kuma?" Cikin jin kunya tace "Mama fa tun ranar da waccen karuwar ta tafi bai qara neman wani abu wajena ba." "Bai nema ba kodai baki bashi ba?" ta fad'a cikin d'aga murya. Sosai kai tayi tace "eh to, amma aike kika ce na dinga jan aji, kuma ni wallahi bana ma son yana kusantata, saboda...." "Saboda me?" Cikin yamutsa fuska tace "kefa Mama baki sanshi ba, wallahi jaraba ce dashi, baya da aiki sai lagudar mutum, gashi inya fara baya dainawa sai yaga ya maka liqis, gashi da tsinannan k'arfi, ga...." *Wal'iyazu billah, towana miji asiri irin haka, abin yayi muni yan uwa, kuma ace uwar ta kasa kwab'arta , nidai ba zan iya fad'a ba gaskiya* 😏 "To kinsan me za ayi? yanzu zan sake komawa wajen malam na fad'a mishi komai, ina tabbatar miki wannan karan, ba sauk'i a al'amarin dan aiki zansa yayi sosai." Shiru tayi hakan yasa Mama cewa "waini ke kad'ai ke zuwa ecole d'in?" "A'a Mama, shi yake kaini, yaune na tafiyata saboda bama magana." "Da motar tashi yake kaiki ko motar waccen karuwar?" "Haba Mama, nice zan shiga motarta, da tashi muke zuwa." "Hum, aini fa wannan tsinnaniyar motar ma saina sa an faffasata kafin ta dawo." "Mama rufa min asiri, jiya fa saboda nace mata karuwa ne ya mareni , idan kin fasa mata mota kuma sai dai ya sakeni, dan wallahi na fahimci yafi sonta a kaina." "Ai kuwa za kiga me zanyi, kuma wallahi saina raba tsakaninsu, ni na fad'a miki wannan maganar." Kiran Umar Faruk ne ya shigo wayarta, dan yaje gida abazata bai sameta gidan ba, hakan yasan ya kira dan yaji ina taje.... _Kafin muji me za tace mishi, zamu waiwaya baya muji tarihin mahaifiyarsu Zuby ._ *WAIWAYE ADON TAFIYA* *Fatima* shine sunan mahaifiyarsu wato kakarsu Umar Faruk, mahaifinsu kuma *Mamman*, sun haifi yara biyar hud'u mata *Khadija, Asma'u, Maryama, Zeinabu* sai kuma autansu namiji mai sunan *muhammad Sani*, yaran sun samu tarbiya da kuma ilimi na boko da addini, kasancewar mahaifinsu yasan anfanin ilimi, kuma cikin ikon Allah sun sameshi yanda ya kamata, sai dai matan basa wani zuzzurfan karatu ake aurar dasu. Suka yaran suna aiki da tarbiyar da iyayensu suka basu amma banda Asma'u, tun tana yarinya iyayensu suka fahimci bata da kirki kamar sauran yaransu, sam bata da ragowa ga yan uwanta gata da masifar fad'an tsiya, ga kuma son kud'i da tijara akansu, saboda son kudinta yasa ta kasa fitar da mijin aure har saida ta samu zabinta , a lokacin kuma har qanwarta Zeinabu ta isa aure, dan haka aka had'asu tare aka aurar dasu. *Hamza* shine wanda wannan hau ta fad'a ma, a waccen zamanin yana d'aya daga cikin masu kud'in da ake ji dasu, amma aurenshi da Asma'u saiya zama silar tarwatsewar komai, ta samu ragama da akalarshi tana juyawa yanda ranta yake so, bata d'aga masa qafa ba wajen rabashi da yan uwanshi dama mahaifiyarshi d'aya da yake da ita a duniya, hatta fita sai taga dama take bari ya fita, hakan yayi sanadiyar raba alak'arshi da abokan harkokinshi mak'ota da abokan arzik'i, sannu sannu kuma sai arzik'inshi ya fara durk'ushewa sakamakon yawan bani bani da take masa kuma bata bari ya fita ya nema, a hankali sai abubuwa suka fara canza musu har takai ya fara siyar da k'adarorinshi daya mallaka. A lokacin kuma ciwo yaci qarfin mahaifiyarshi, amma babu kud'in da zai iya siya mata koda magani bare ya kaita asibiti, da qyar Asma'u ta bashi izinin zuwa yaga mahaifiyarshi bayan dogon rarrashin daya mata, yana zuwa kuma ya makara dan sai gawarta ya samu, ya girgiza sosai da mutuwar mahaifiyarshi, amma rashin imani na Asma'u bata barshi ya qarasa jimamin rashin mahaifiyarshi ba ta fara azabtar dashi ta wata sabuwar hanyar, a lokacin ta fito da wani sabon salo ta hanyar d'ora mishi duk aikin gida, saboda kawai yanzu ba yada komai, kuma duk abin nan da ake akan idon 'ya'yansu mata guda uku da Allah ya basu, ko sau d'aya bata tab'a tunanin yayanta mata bane kuma zasu iya koyi da ita, haka take azabtar dashi yaran kuma na gani kuma dukansu basu damu ba, dan dama tana d'orasu ne akan turbarta. Kasancewar suna nesa da gida yasa iyayenta da 'yan uwanta basu riga sun fahimci halin da take ciki ba, a ranar da suka samu labari mahaufiyarsu tayi tattaki izuwa gidan, anan kuma idanta ya gane mata tabbas, danta samu Hamza ya tak'ark'are yana sharar gida, ran Fateema ya b'aci sosai kuma taji kunyar abinda ta gani, amma abin takaici shine, koda ta fara mata magana akan abinda take saita mik'e ta fara zuba rashin mutunci da fad'a, cike da quna Fateema tace, "Yanzu Asma'u ni kike fad'awa wannan maganar, ni kike kallo kike fad'a min wai na takura miki? Cike da rashin kunya tace "eh mana, na fad'a miki, gidana fa kika zo, kuma naga mijina ne ba mijinki ba, to miye a ciki? nifa ba zan iya wannan banzar rayuwar ba irin taku, kana zaune gidan miji bakin ciki da takaicin namiji ya kasheka , ai muna gani tun muna qanana irin rayuwar da kike a gidan mahaifinmu, hawan jinin da kike fama dashi ma ai duk shine sila, shine kike so nima na zauna ya qaqaba min, wannan da kike gani namiji shima, kuma dana bashi dama babu abinda zai hana yamin tsiyarsu irinta maza." Cikin sanyin murya tace "naji, tunda haka kika zab'arwa kanki, ga hanyar nan, kuma duniya ta isheki riga da zanin d'aurawa." Qarasa mata tayi da "harda d'an kwali ma." "Haka kika ce? shikenan kije , amma ki sani akwai ranar qin dillanci, akwai ranar da za kiyi nadama, bansan ko zamu riski lokacin ba, amma dai nasan tabbas zata zo, kuma ki sani daga yau ba zan qara shiga sabgarki ba." "To saime, nace saime dan baki shiga sabgar tawa ba? hakan ma yafi min dad'i, yanzu ne kuma zan sake watayawa yanda nake so, dan haka tafi nono fari, danni ko baki kika min ba kamani zaiyi ba." duk tayi maganar ne tana murgud'a baki. "Haka kike gani, ai kuwa da zan miki wallahi ba zaki kai ko ina ba, amma ina jin tsoron karki qara lalacewa." "Kiyi mana, wallahi babu abinda zai sameni, ina yin duk abinda nake so kamar yanda nake samun duk abinda nake so, dan haka babu abinda bakinki zaimin ." "Haka ki kace?" "Eh, haka nace." "Shikenan kije , kije kya gani." "Wallahi sai dai naga alkairi." Juyawa tayi ta bar gidan rai b'ace tare da tunanin yaushe Asma'u ta zama haka, da wannan tunanin takai gida kuma ta kwanta bacci ba tare data fad'awa mahaifinsu ba, dan tasan inta fad'a masa toshi zai tsine mata ne ba tare da b'ata lokaci ba. Babu wanda yasan me zai faru a gaba, badan haka ba da Fateema ta janye mugun bakin data ma Asma'u tun kafin ta kwanta bacci, domin kuwa wannan baccin data kwanta bacci ne na qarshe, baccin da babu tashi sai lokacin da aka busa qaho na biyu. Haka lokaci yaja sosai babu abinda ya sauya a game da al'amarin Hamza, har suka aurar da *Salamatu* wacce suke kira da Uwani, da kuma Zulfa'u ya rage Zabba'u, lokacin kuma aka samu cikin Zuby amma sam Asma'u bata bari Hamza ya sani ba, domin kuwa cikin ba nashi bane na abokinshi ne, kuma hakan ta faru ne lokacin da abokin yazo gidan domin sanin meke faruwa ya daina fita, daga ranar suka qulla wannan alaqar kuma tana jin dad'in haka saboda yana sakar mata kud'i masu yawa, sai dai ta manta da ciki d'an dumane dole wata rana zai fito kuma ta haifeshi. A ranar da Hamza yaga cikin kuwa, ya sameta ne d'akinta kwance da kayan bacci, anan yaga cikin dake jikinta d'an wata shida zuwa bakwai wanda take b'oyewa kullum, "Me zan gani haka Asma'u?" ya fad'a yana sake kallon cikin gidan nata. Cikin baccin daya fara d'aukarta taji muryarshi, a zabure ta tashi zaune tana d'aukar hijabin da take ajewa saboda gudun irin haka, cike da dakiya tace "mefa kake gani, miye haka zaka shigo min d'aki a wannan daren?" "Asma'u, ciki fa nake gani a jikinki, ko kuma kina so kice min wannan ba cikin mutum bane? "Ciki kuma, a ina?" Da hannu ya nunata amma ya kasa fad'ar komai saboda yanda zuciyarshi ke bugawa, ya jima yana nuna hannun amma baice qala ba, daga haka kuma ya fad'i qasa wanwar , fashewa tayi da qara hakan yasa Zabba'u fitowa daga d'akinsu, nan dai aka samu aka kaishi asibiti amma ina lokaci yayi Hamza, shima nan aka tabbatar musu da zuciyarshi ce ta buga, Asma'u bata ji mutuwarshi ba saboda lasisi ne ya bata ci gaba da harkarta, bayan wattani kuma ta haifi Zuby kuma samu kulawar mahaifinta wanda mutane sukewa kallon aminin mahaifinta, sai dai tunda akayi arba'in d'in Zuby shima Alhaji *Bala* ya fita sabgarta, da farko tayi yunkurin tona musu asiri, amma sai Bala ya nuna mata ya fita zama d'an iska, domin kuwa cewa yayi taje ta fad'a, shi namiji ne bai gudun abinda mutane zasu ce, bayan tunani da tayi saita fahimci ita zata jefa kanta rijiya, dan haka taja bakinta tayi shiru. Sai dai rayuwar ta sauya musu sosai, dan abinda zasu ci wani lokacin wuya yake musu, wani lokacin ma saita d'an kula maza kafin ta samu abinda zata ciyar da Zuby da kanta, rufi asiri d'aya shine su Zulfa'u suna taimaka musu wani lokacin, a haka rayuwa ta tafi har girma ya risketa tare da yarta Zubeida. Ranar wata *litinin* Zuby ta taso daga école, a qasa take tafiya ga rana ga yunwa, Umar Faruk ne ya b'illo akan hanyar da take, nan dai suka gaisa kuma ya d'auketa ya rage mata hanya, suna zuwa gida kamar yanda ya zama saban Mama zama k'ofar gida a bakin bishiya, yauma nan take zaune daga ita sai kallabin dake kanta, saida ya sauka daga kan mashin d'in ya gaisheta sosai kafin ya tashi ya tafi, Zuby kuma tuni dama tayi cikin gida bata ko kulata ba, bin kowannensu tayi da kallo tana girgiza kai, har zuciyarta taji sun birgeta kuma sun dace da juna, hakan yasa tayi tunanin had'a aurensu, sai dai kuma Umar Faruk talaka ne haka ma mahaifinshi, amma ba zata aiwatar da komai ba har saita nemi shawarar malam sannan. Ba tayi qasa a gwiwa ba wajen zuwa wajen malam tare da fad'a mishi abinda ya kaita, bud'ar bakin malam cewa yayi "tabbas, wannan yaron zaiyi arzik'i, kuma arzik'in zaizo ta sanadiyar matarshi ne ta farko." "Ban gane matarshi ta farko ba, kana nufin ba yata kad'ai zai aura ba, kuma wacce zai aura farko itace silar arzik'inshi, to wacece ita.?" Rarraba ido yayi, dan na farko ma yayi qarfin hali ne ya fad'a da d'an abinda shed'anu suka nuna mishi, duk da yasan ba lallai gaskiya bane, amma saboda ita d'in abokiyar harka ce ba zaiso mutuncinshi ya zube ba, dan haka yace "haba Ma'u, ai 'yar taki nake nufi." A wulak'ance tace "ka tabbata?" "K'warai ma kuwa, ai kisan yanda za ayi ki hadasu, dan arzik'inshi na tattare da ita, yarinyar akwai qashin arzik'i." "Gado tayi gaba da baya." ta fad'a tana yamutsa fuska. A lokacin da taje ma iyayen Umar Faruk da maganar basu ce komai ba sai fatan alkairi, haka ma Umar Faruk da aka fad'a mishi, bud'ar bakinshi cewa yayi "Allah ya sanya alkairi." "Ameen, Allah ya maka albarka." cewar Mama "Ameen." Daga wannan rana ne sai Asma'u take turo Zuby gidan tazo har takanyi sati biyu wani lokacin, shakuwa ta shiga tsakaninsu duk da dai Umar Faruk baya jin komai a zuciyarshi a game da ita, amma a lokacin da girma ya qara zuwa masa ya sake mallakar hankalin kanshi, a lokacin yana da shekara *30* sai buk'atar aure ta kamashi, amma sam Zuby tak'i amincewa tace saita samu certificat d'inta na (BEPC) sannan suyi aure, dole ya hak'ura tunda baida wacce yake so kuma baya da ra'ayin yin mata biyu a cikin qananin lokaci da kuma qarancin shekarunshi. *Wannan* ne dalilin da yasa tanti ta tsani Khairat ba tare da wani dalili ba, ta yarda d'ari bisa d'ari akan abinda malam ya fad'a ,musamman da tasan Khairat 'yar babban mutum ce, tasan ba makawa sai yayi kud'i ta silarta, hakan yasa ma tayi gaggawar shigo da Zuby gidan. *WANNAN KENAN* 😍😍😍😍😍 *_CIGABAN LABARI_* Tana d'auka yace " ina kika je?" Cikin gunaguni da harare tace "ina gida wajen Mama." "Da izinin wa kika je?" "Toh , wajen mahaifiyar tawa ma da zanzo saina fad'a maka? to da izinina nazo." Da qyar ya taushi zuciyarshi yace "naji, na miki uzuria karo na farko, amma ki sani kika sake maimaita irin haka, wallahi ranki idan yayi dubu zai b'ace, sannan, ki gaggauta dawowa gida nan da minti talatin ina jiranki." Yana fad'a ya kashe wayar ita kuma ta kalli Mama tace "kiji rainin wayo." Shiru Mama ta mata ganin haka yasa ta tashi ta kimtsa nata yanata sukayi sallama ta kama hanya, dan nisan dake tsakani ma zai iya d'aukarta minti talatin d'in, da qyar ta samu taxi ta hau, koda taje bata samu Umar a gidan ba, hakan kuma ya mata dad'i sosai. ************* B'angaren Khairat kuma tana babban shagon siyayya , kud'i kawai take kashewa yayin da take tuna iya mutanen dake cikin qwaqwalwarta take siya musu kaya, ta jima sosai kafin ta fita ta d'auki hanyar komawa masaukinsu, tana zuwa su Mammie ita suke jira , dan haka basu b'ata lokaci ba wajen isa filin jirgi kuma suka tashi da izinin Allah suka sauka lafiya. _Me kuma zai faru yanzu? my Hajja fa ta dawo._ *Kamar yanda na fad'a, babu abinda zai tsayar dani rubutu idan harna fara rubutawa,amma fa akwai yiwuwar na dakatar da rubuta _Jihadi_ na d'an wani lokaci, danna lura kamar kun fara gajiya da comment, comment bawai yana nufin a turo maka💃 tsalle ko🤸‍♂talar qafafu ba, ko striker dake cinye data, tabbas muna jin dad'in addu'a, amma mutum yayi sharhi akai shine zai baka tabbacin an karanta abinda ka rubuta d'in, so idan kun gyara zanci gaba, idan ba haka ba😎bana da matsala, zan sawake ma kaina ta hanyar ajiyeshi gefe ko kuma na dinga turawa masu so na fita daga duk grp d'in da basa comment.* _Ina muku barka da sallah, Allah ya nuna mana ta bad'i, Allah ya karb'i ibadunmu , Allah ya gafarta mana zunabanmu, Allah yasa muna cikin bayin da aka 'yanta._👏 *Ameen ya Hayyu ya Qayyum.* 14/08/2019 à 15:32 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *Sufa iyaye girmane dasu, samun Zuby bata hanyar aure ba yana d'aya daga cikin kamun da bakin mahaifiyar Asma'u ya fara mata, kuma wannan ba abun mamaki bane danni naga irin haka da idona.*😎 _Muje zuwa masoya masu fahimta_😉 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣3⃣ Driven gida ne ya kawo Khairat saboda shiya d'aukosu daga filin jirgi, saida ya shigar mata da kayan cikin gidan kafin ya wuce, nanfa yara suka mata ca suna mata sannu da zuwa, haka ma manya sannu suke mata cikin murna, jin ana sallah isha'i a masallaci yasa Khairat kallon duka mutanen wajen cikin farin ciki tace "zanje nayi sallah, amma kumin alk'awarin ba zaku fad'awa Faruk ba." Fateema da Zeinab ne suka amsa da "munyi aunty." Kumatunsu ta shafa tace "da kyau 'yan mata, zan wuce, idan na fito zan baku tsarabarku." Wucewa tayi Ruk'ayya tabi bayanta da kayanta, tana shiga d'akin taga yasha gyara, kallon Ruk'ayya tayi tace "kece ko?" Cikin dariya tace "eh aunty, ai naga bakya son k'azanta, shi yasa nake shigowa ina gyarawa duk da ba kya nan." "Kin kyauta." ta fad'a tana shirin fitowa yin alwala. "Amma fa aunty naga sai farin ciki kike, kodai da wani abu ne?" cewar Ruk'ayya. Cak Khairat ta tsaya amma bata juyo ba, ajiyar zuciya ta sauke mai nauyin gaske, ita kanta haka take ji tana farin ciki, kuma baya rasa nasaba da kusanto da kanta da tayi wajen Umar Faruk, ba tare data juyo ba kuma ta wuce ta fad'a 'yar qaramar toilet d'insu, koda ta fito bata samu Ruk'ayya ba, a haka ta kabbara sallah kuma harta kammala Umar Faruk basu shigo ba. Jakar data zuba tsarabara ciki ta janyo ta fito da ita tsakar gidan, fitowarta yayi daidai da fitowar Zuby daga d'aki itama, kallon juna sukayi Zuby kuma ta bita da harara, Khairat kuma binta tayi da kallon zan kamaki a hannuna, wajensu Mama ta nufa inda suke zaune akan tabarma, zaune tayi itama tana cire hijab d'in jikinta danya d'an takurata sannan ta bud'e jakar, kayan kanti ne masu kyau da qualitie wanda ta siyowa Zeinab, Fateema, Yusuf, Ubaidullah, Bilal, Abdul rahaman, bawa kowa tayi sai lokacin ta fahimci ba kowa ya samu ba, dan dama ba wani sanin yaran tayi ba tayi anfani da ganinsu ne yau da gobe, kallon sauran tayi tace "ayya, kuyi hak'uri kunji, insha Allah kuma zan siyo muku naku." Mama Sa'a kuma cewa tayi "haba, aiba komai ba, wannan ma an gode wallahi, Allah yashi albarka." Mama kuma dad'i taji sosai saboda ganin anyi daidai, dan Bilal d'ane ga Mama Maimuna kuma ya samu, Abdul rahaman d' ga Mama Sa'a kuma shima ya samu, Zeinab kuma 'yarta ce itama kuma ta samu, sai Fateema da Yusuf yayan Abbakar, suna cikin godiya kuma saiga takalma ta fiddo ta bawa Mama Sa'a Mama Maimuna da kuma Mama, suna da kyau kuma basu da tudu ko kad'an, nanma godiyar suka fara sai kuma ga wasu kayan masu kyau tabawa Ruk'ayya har kala uku, wata agogo ta fito da ita mai shegen kyau qirar rolex ta bawa Mama Sa'a da tafi kusa da ita tace "wannan na Baba ne." Kafin tayi magana Khairat ta fito da wata agogon qirar gucci ta fata tabawa Saratu tace "na mijinki ne wannan." Sannan ta bita da wasu had'add'un turare kala uku tace naki ne wannan." "Kai, amma na gode sosai yer uwa, irin wannan tsaraba haka." Sallamar Aliyu da Usman ce ta katsesu, 'karasowa sukayi Usman na fad'in "matar yaya, yaushe garin?" A harshen zarma ta amsa mishi da "ana sallah na shigo." "Sannu da zuwa, ya hanya?" cewarsu gaba d'aya. "Lafiya lau." ta fad'a tana mika musu wasu kwalaye wanda ko a cikin bacci aka basu zasu san na miye, Aliyu ne ya waro ido yace " Iphone7, ta mece aunty?" "Naku ne." ta fad'a ba tare data kallesu ba. Su kuma mamaki ne ya hanasu karb'a, saida ta juyo tace "baku sone?" Da sauri Aliyu ya karb'a yana fad'in "ah haba aunty, mu mun isa? mun gode Allah saka da alkairi." Karb'a yayi duka ya mik'awa Usman d'aya, amma sai Usman yace "na gode, amma gaskiya ni bana so, wannan ma ta isheni." Ba tare da damuwa ba Khairat ta kalli Aliyu tace "ok , ka bawa maiso ko cikin abokanka." Mamaki ne ya cika kowa dake wajen, Usman d'in ne yace "kud'i fa kika saka kika siyo saboda ni, me yasa ba zaki aje ba koki siyar?" Wani d'an murmushi tayi mai sauti tace "ba wakai ba na siyo, na siyo ne wa mutanen da nake rayuwa dasu, tunda baka so ai ba za'a rasa maiso ba." Gyara zama tayi tana kallonshi tace "da farko na shigo gidan nan ne a matsayin bana son d'an uwanku , duk da haka kuma zan iya sadaukar da komai nawa dominku, yanzu kuma da nake son Faruk, ina ji zan iya taimaka muku da k'arfina ma ba iya dukiyata ba kad'ai, ko zaku kasheni ba zan daina muku alkairi ba domin kuwa a jinina yake, haka ma kome za'a fad'a ba zan daina taimakawa mutane ba." Tana fad'a ta tashi zata wuce d'aki Mama Sa'a tace "dan Allah yata kiyi hak'uri, karki bi ta abinda ya fad'a." Juyowa tayi za tayi magana idonta ya sauka akan Zuby dake k'ofar d'akinta zaune, shiru tayi ta wuce d'aki tana ji kamar bata kyauta ba da bata bawa Zuby komai ba, domin kuwa kishiya aina mak'iya bace, coiffeuse d'inta ta kalla, da sauri ta qwala kiran sunan Ruk'ayya, tana shigowa ta d'auki wasu turaruka wanda suke birgeta har guda biyu ta bata tace "ki kaiwa Zubeida." Da mamaki Ruk'ayya tace "amma aunty sai naga kamar naki, me yasa zaki batasu?" Cikin d'an murmushi tace "Ruk'ayya, wannan ba komai bane danna bawa Zubeida wannan, itafa kishiyata ce bawai mak'iyata ba, zan iya bata fiye da wannan ma musamman idan ta buqata ko kuma naga buqatar hakan ta kamata." "To aunty." ta fad'a tare da fita daga d'akin. Tana bud'a labulen suka ci karo da Umar Faruk wanda labarin zuwanta ya sameshi tun a tsakar gidan, rab'awa tayi ta wuceshi shi kuma ya shiga ciki, Khairat na ganinshi ta daka tsalle tare da qara ta nad'e a jikinshi,shima rumgumeta yayi sosai a jikinshi yana juyi da ita a tsakiyar d'akin yana dariya, cikin murna take fad'in "nayi kewarka sosai baby, nayi kewarka, nayi farin cikin ganinka sosai." Sauketa yayi da nufin ya mata magana amma saita had'e bakinsu waje d'aya, shima bai tsaya b'ata lokaci ba wajen biye mata suka lula wata duniyar, sunyi nisa sosai a duniyarsu suka ji wata hayaniya a tsakar gidan, dakatawa sukayi Umar Faruk kam fad'awa yayi akan gado yana sauke numfashi, ita kuma gyara rigarta tayi ta lek'o daga d'akin, jin hayaniyar ba qarama bace yasa ta qarasa fitowa, tsakar gidan ta fito tana kallon Zuby dake masifa wai Khairat ta bata turare bayan ta mata sihiri a ciki, su Mama ne ke bata hak'uri da ban baki, amma ganin haka sai yasa ta buga kwalaben a qasa suka watse a banza, ganin hakane yasa Khairat nufa wajen Mama ta kama hannunta har saida ta shigar da ita d'aki sannan ta zaunar da ita tace "ki zauna ki huta Mama, dan Allah kada ki kulata, nima kuma ba zan kula ba." Bata jira me Mama za tace ba ta fita daga d'akin, tana fitowa ma kai tsaye d'akinta ta nufa tana fad'in "dan Allah duk mai aikinyi yaje yayi." D'aki ta nufa Zuby kuma tace "hum, wato an mayar dani mahaukaciya, to bari kiji wallahi sihiri da qulubotanki ba zai tab'a kamani ba, kuma ni dake mu zuba mu gani shege ka fasa." Juyowa Khairat tayi ta kalleta tace "ke, ni bana da lokacinki, yanzun lokacin mijina ne, idan kuma kin shirya masifa dani to ki bari har gobe, kinsan me yasa nace har gobe? domin kuwa gobe ranar aikina ne, kuma ko wannan uwar taki bata isa ta b'ata min abinda nayi niyyar shiryawa ba, dan haka ki aje masifarki har goben." Wucewa tayi ba tare data kula kowa ba, suna ganin shigarta kusan kowa ma ya watse, Mama ta kaiwa Baba agohonshi kuma yayi godiya sosai, haka ma Abbakar shima yayi godiya, a kwance ta sameshi dan haka ta kwanta kanshi ta fara sumbatarshi. Saida suka kusa shiga duniyar da ba zan iya binsu ba sannan suka tsaya, Khairat ce tace "baby." "Um." ya fad'a cikin maqoshi. "Har yanzu ba kace komai ba." Saida ya janyota jikinshi ya d'ora hannunshi akan mazaunanta yana shafawa yace "me zance? bayan kin hanani fad'ar komai." "Duk da haka kace wani abu." Saida ya sake mannata a jiki yace "to da fatan kinzo lafiya? ya hanya yasu Mama?" Saida ta sumbaci kumatunshi tace "lafiya lau, yana sameka?" A sanyaye yace "lafiya lau." Kallonshi tayi hakan yasa numfashinsu ke gyauraya tace "Faruk ina qaunarka, ina sonka fiye da raina, sonka yamin mugun kamun da ba zan iya kub'uta ba, kuma na fahimci hakan ne a tazarar da muka samu na kwana biyar, dan Allah baby ka zauna dani har qarshen rayuwarmu." "Baby, ba zan iya rabuwa dake ba nima, ina sonki kuma ina qaunarki, rabuwa dake kamar rabuwa da numfashina ne, dan haka babu maganar rabuwa." Shigewa tayi jikinshi suka sake dunk'ulewa suna sauke numfashi, tunawa da Zuby yasa Umar Faruk tashi zaune yana d'aukar rigarshi yana sakawa, fahimta da Khairat tayi yasa ba tace komai ba harya gama saka kayanshi, saukowa tayi itama tana fad'in "yanzu sai yaushe zaka zama nawa? wallahi ina buqatarka kusa dani" Kumatunta ya shafa yace "nima haka baby , amma ai gobe ne." Turo baki tayi gaba kafin tace "to yanzu me kake so na dafa maka gobe?" Cike da zolaya yace "wai harkin gogene?" "Sosai ,kana tamtama?" "A'a, ina dai mamaki ne." "To fad'i me kake sha'awar ci gobe?" "Tuwan shinkafa." "Ai kuwa zaka ci insha Allah." Sumbatar kumatunta yayi yace "gobe zai sauke miki gajiyar tafiya, ki kula min da kanki." "Um, kodai ka saukar min da wata gajiyar ba, saida safe." ta fad'a tana d'aga masa hannu. Yana fita itama ta fito ta shiga wanka kafin ta fito tayi shirin kwanciya, da tunanin gobe bacci ya d'auketa saida asuba. ************** Koda Umar Faruk ya shigo da nufin tashin Khairat tayi sallah ya samu har tayi alwala zata kabbara raka'atanil fijir, murmushi ta sakar masa tace "baby, ina kwana, ka tashi lafiya?" Wani sanyi yaji yana ratsashi na musamman kafin ya shafi kumatunta yace "lafiya lau, fatan kin tashi lafiya." "Tunda dai kana cikin k'oshin lafiya, to nima haka." "To, ni zan wuce masallaci." "Saika dawo baby." Juyawa yayi zai fita yana bud'a labulen tace "baby." Juyowa yayi ya kalleta, cikin wani kallon dake kashe jiki tace masa " *ana uhibbuka khasiran*." Murmushi ne ya bayyana a fuskarshi wanda ya bayyana haqoranshi a fili, kallonta kawai yake yayin da qwaqwalwarshi ke zuwa mishi da tunani kala kala a game da ita, ya jima a haka kafin yace " *ihubbuki* Sumbatar hannunta tayi ta jefa mishi kafin ya fita, haka ya tafi masallaci yana jin wani irin nishad'i da farin ciki na lullub'eshi , yana zuwa masallaci kuma saiya samu Malam baya jin dad'i dan haka yace ya jagoranci sallar saboda Abbakar bai riga yazo ba, haka yaja sallah cikin farin ciki da nutsuwa, kuma ya sake gazgatawa sallah cikin tsantsar nutsuwa wani lokacin yakan danganta da irin yanayin da kake ciki. Khairat na gama sallah bata kwanta ba, saida ta zagaya ta gaishe da iyayen gidan kafin ta shigo d'aki ta cire hijab ta fara....... _Meta fara to?_ *Dad'in comment d'inku ya sani sake muku posting duk da na fita unguwa, samun posting sau biyu ya danganta da yawan comment d'inku, dan gaskiya yau na samu comment sosai, kuma kuyi hak'uri da rashin maidawa saboda ina muku typing d'in ne.* _Luv u guy's_😍 17/08/2019 à 20:13 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣4⃣ Zanin gado ta fara canzawa abinda kuma bata tab'a yiba kenan tunda take a rayuwarta, tana gamawa ta d'anyi goge goge duk da ba datti ke akwai ba, tana gamawa tayi shara sama sama itama dai da wuya tayi ta dan bata tab'a yiba, turaren tsintsiya da kuma na wuta ta jona a kuran tayi, sannan ta had'a da airfreshner ta feshe d'akin dashi, zaman kujerar d'akin ta canza tare da qaramin teburin dake d'akin, hakan yasa kujerun dake waje suka samu matsugunni a d'akin, a gajiye ta shiga wanka ta fito, tsaye take tana tsane ruwan jikinta tare da gashin kanta data wanke. ****************** Koda ya dawo daga masallaci yace wa Zuby "zanje muyi karatu, kinsan tayi tafiya, ya kamata muci gaba." A lokacin da take saka wasu littafin a jakar makarantarta ne ta kalleshi wulak'ance tace "wacece?" A dake yace "Khairat mana." Tashi tayi ta fara cire hijabin jikinta tana fad'in "oho, karatu dai, wane irin karatu kenan?." Shiru yayi kawai bai tankata ba harta fara sarrafa abin karyawa, zaune yake yana tilawar karatu amma hankalinshi na kan Khairat, a haka harya yayi shirin tafiya wajen aiki, Zuby ma ta shirya tsaf zaune tayi ta fara karyawa, kallonta yayi yace "ki jira 'yar uwarki mana." Wani irin yamutsa fuska tayi kamar taga kashi tace "ban dafa da ita ba, kuma gashi ban dafa da kai ba bare ka bata naka, in kuma zaka tuk'eni ne na amayar da wanda naci saina gani, tunda dama kafi sonta a kaina." "Zubeida wai me yasa kike hakane, me yasa kika sauya gaba d'aya, wannan wane irin kishine kike nunawa haka? me zai hana kiyi koyi da 'yar uwarki, itafa ya kamata ta nuna kishi a matsayinta na wacce kika sameta a gidan, amma ba tayi ba saboda tasan bata da wani dalili nayin kishi a game dake, me zai hana kema kiyi wannan tunanin." A hassale ta mik'e tsaye tace " eh mana, ai bata da dalilin yin kishi dani ne shi yasa, kasan me yasa? saboda tun fil'azal tare muke da kai, kuma a tare ta samemu ana shirin aurenmu, kenan sai tayi kishi dani saboda kawai ita jahila ce bata san ciwon kanta ba? to wallahi kaji ba zaka tab'a samun kwanciyar hankali ba tunda ka nuna kafi sonta a kaina, bakai ba kwanciyar hankali tunda nasan wacece ka had'ani da ita, karuwa, karuwa, babu yanda zanyi naci gaba da zama karuwa a gidan nan da karuwa, kamar yanda na haramta maka kaina dan ba zan yarda ka had'ani da jaraba ba wallahi ina zaman zamana." Zaune ta koma tana cin abincin tana gunguni, nunata yayi da yatsa yace "sai dai ki rasa kwanciyar hankali amma bani ba, na fad'a muku tun farko, wallahi babu wacce ta isa ta tayar min da hankali, kuma na kasa maganinta, bansan ko kinsan auren zobe ba? to idan kin sani ko shine aka min daku wallahi zan tsigeku daga gareni, dan ba'a haifi matar da zata rainani ba, ke kinyi, amma ki sani ina raga miki ne saboda darajar iyayenmu, wallahi wallahi Zubeida kika kaini bango, tofa ki sani abinda ba kiyi tsammaninshi bane zai faru." D'aukar jakarshi yayi ya wuce yana fad'in "haka kawai ki mayar dani mahaukaci, aure da tarewa cikin qanqanin lokaci, amma kina neman kisani yin abinda za'a dinga yi dani a gari, iskanci kawai." Kai tsaye d'akin Khairat ya shiga, yana zuwa ya sameta tana goge ruwan jikinta, aje jakarshi yayi akan kujera yana kallon gyaran d'akin da tayi, yana qarasawa ya rumgumota ta baya, juyowa tayi tare da rumgumeshi tana fad'in "sannu da zuwa baby." Kallonta yayi yace "ke ki kayi aikin nan?" Cike da murmushi tace "ni nayi, kana mamaki ko? nima nayi mamaki da nayi aikin nan, yau kuma na sake tabbatarwa so zai iya sa komai, dan a yanzu ina jin zan iya zama da kai a kowane irin yanayi." Rumgumeta yayi cike da qaunarta da kuma tausayinta da yaji ya lullub'eshi a take har idonshi sun kawo ruwa yace "zaki iya zama dani a kowane hali Khairat? " "Zan iya Faruk, wallahi har zuciyata nake fad'a maka haka, a yanzun zan iya zama da kai koda a cikin rijiya ne, Faruk ina sonka so mai tsanani, son da ba zan iya fassara makashi ba, kuma a game da hidimar gidanka, to a shirye Hajia Khairat take wajen shanye kowace irin wahala, badan komai ba sai dan farin cikin mijina abin alfaharina kuma uban 'ya'yana." Kafin yayi magana kuma ta daga qafafunta ta kaima tsayinshi, a hankali ta d'ora bakinta tana sumbatar wuyanshi tare da d'an tsotsawa, rufe ido yayi yana murmushi harya fara qyqyata dariya, rumgumeta yayi sosai ya rad'a mata a kunne "ina sonki Khairat, kina sani farin ciki sosai, ina fatan Allah ya barmu tare har abada, Khairat zan iya rayuwa dake ko babu 'ya'ya." Kallonshi tayi da sauri tace "da gaske? kaga ni kuma ina so na haihu, na samu yar mace domin na d'orata akan tarbiyar da kuka d'orani kai da Mama." Murmushi yayi yace "ashe kina son yara, in kuwa hakane yau d'in nan saina baki ajiyarsu." Waro ido tayi tace "harsu nawa to?" D'aure fuska yayi yace "da uku uku mana, dan kiyi saurin gamawa." Fashewa tayi da dariya tace..... _Kuna ganin zai iya?_😉 _Sorry fan's, wlh wani aiki ya taso min bazata, shi yasa kuka jini shiru, kuyi hak'uri da wannan._ 17/08/2019 à 20:13 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣5⃣ "Zaka iya kuwa?" Wani kallo ya mata yace "kina qalubalantar mazantakata kenan? to bara kiga sanfiri." Yana fad'a ya sungumeta ya dire kan gado, da zafi sosai yake aika mata da wasu gunduma gunduman sak'onni, yana daf da shiga wata sabuwar duniyar Khairat ta dakatar dashi, da qyar ta samu suka daidaita nutsuwarsu kafin ta kalleshi tana dariya tace "nifa duk da haka ban yarda zaka iya ba." Lumshe idonshi kawai yayi yana shak'ar k'amshin daya gauraya d'akin, yunwar data ji ce tasa ta sauka daga kan gadon ta bud'a drower ta d'auki riga iya gwiwa ta zura ta fesa turaruka sannan ta bud'a wajen ajiyarta, gâteau (cake) ta d'auko da chacolat ta aje akan tebur sannan ta d'auko jus mai sanyi tare da kayan marmari duk ta tule gabanta sannan tazo wajen Umar Faruk da har yanzu yake kwance ido rufe, hannayenshi ta kamo ta tayar dashi zaune sannan ta d'auki rigarshi ta saka mishi ta sauko dashi daga kan gadon duk yana kallonta, a ranshi kuma addu'a kawai yake mata akan Allah ya sata farin ciki kamar yanda take sakashi, kumatunshi ta dafa tace "to naji, yanzu ka samu dai ka fita ko nima nayi abinda ke gabana." Saida ya sauke ajiyar zuciya yace "to, nine fa mijin Hajia Khairat, ko kuma nace madame Khairat, idan naso ma zan iya zamana tare dake." Shafa cikinshi tayi tace "da fatan dai ka cika minshi sosai, dan naga bai taso ba." Dariya yayi yace "kina so kiga ya taso ne kamar mai cikin wata hud'u ko biyar? aike ya kamata naga haka gareki, a lokacin da kika fara kula min da 'yan ukuna." Turo baki tayi gaba tace "nidai ba wasu 'yan ukun da zan haifo maka, ina son d'aya d'aya dai, yanzu dai zo kaci ko kayan marmari ne saika wuce." Baya so ya nuna baici komai ba daga wajen Zuby hakan yasa yace "a'a, nifa bana buk'atar cin komai saboda na k'oshi." Wata yar ledata d'auko mai kyau ta bud'a ta d'auki wannan qaton cake d'in ta saka mishi a ciki tare da chocolat, sannan ta rufe ta bashi jakar tace "wannan kyautace daga gareni, bana so ka manta dani duk inda za kaje, ina so kayi anfani dasu." tana fad'a ta sumbaceshi. Rumgumeta yayi yace "ki kula min da kanki sosai." "Zanyi, kaima ka kula min da kanka, kuma banda kallon 'yan mata." Dariya yayi yana sakinta yace "ni kuma me zan kalla a jikin wasu, bayan inada ku." Murmushi tayi tana kallonshi harya d'aga mata hannu zai fita tace "kayi sauri ka dawo fa karka jima, kasan yau zan maka girki da kaina." Cikin dariya yace "oho, kina so na dawo da wuri kenan saboda na tayaki aikin ko?" Itama cikin dariyar tace "a'a a'a, aini zanyi da kaina, kai kawai zaka ci ne kuma kasha sannan kayi kwance kayi bacci." D'an hararan wasa ya mata yace "bacci kuma, kema kinsan ai ina bala'in kewarki, tun ranar da kika d'and'ana min zumarki wacce ta haukatar dani kuma har yanzu ta kasa sakina, dan haka yau ki shirya sam ba zan d'aga miki qafa ba." Dariya kawai take ba tace komai ba harya fita shima yana dariya, saida yaga Zuby zata fito da niyyar shan iska a tsakar gidan sannan ya tuna ma da wata hallita Zuby da kuma b'acin ran daya fito dashi daga d'akinta, yanda ta d'auke kai daga barin kallonshi yasa shima ya wuce bai kulata ba, haka ya wuce wajen abokanshi zuciyarshi fal da farin ciki. ************ Zaune tayi tasha kayan marmarin nan sosai, da haka ta koshi kafin ta d'auki littafi ta fara tilawar karatunta, ta jima sosai a wurin har lokacin sallah azahar, saida tayi sallah sannan ta kira Ruk'ayya ta d'ebo mata shinkafa, jik'ata tayi sannan Ruk'ayya tasa aka qarasa had'o mata kayan miya, lemon kankana ta fara had'awa tasa a fridge kafin ta shiga aikinta gadan gadan, duk da Ruk'ayya taso taimaka mata amma tace a'a ita za tayi da kanta, tana cikin yi Umar Faruk ya kirata, tana d'auka yace, "Baby, ya kike?" "Lafiya lau baby, ya aiki?" "Alhamdulillah, ya zaman gida?" "Ina jin dad'i, saboda ina rayuwa a gidanka." 'Waike, kullum maganganunki masu dad'i ne?" "Aiki nane saka nishad'i, kuma aikin office d'ina ne samar maka da farin ciki mai d'orewa indai ina da rai da kuma lafiya." "To na gode, kuma ina fata nima Allah ya bani ikon sakaki farin ciki na har abada, yanzu kinsan me nake so?" "Ka fad'a kawai, ni kuma aikina ne cikawa." Saida yayi murmushi kamar yana gabanta yace "fura nake so ki dama min, kisa Ruk'ayya ta kawo miki, amma nafi son ki dama da hannunki, akwai abokanaina da zamu zo tare dasu, ko zan iya samu?" "Ka d'auka an gama ranka shi dad'e, zaka samu yanda kake so insha Allah." "Kina ganin zaki iya damun fura?" "Ban tab'a ba, amma yau zan fara saboda kai." "To shikenan, Allah ya miki albarka." "Ameen baby, na gode." Da haka suka kashe wayar, aiki yayi aiki Khairat nata bada himma, da kanta ta tuk'a tuwon kuma tayi miyar agushi da nama mai had'e da kifi k'anana, saida ta kammala dasu a lokacin gida duk ya dau k'amshi tako ina kafin ta d'auki fura da nufin damawa, duk iya qoqarinta kasa damawa tayi saboda ta riga data gaji ga kuma wahala da rashin iyawa, wata dabara ce ta fad'o mata, a blender tasa ta markad'ata haka ma da ayaba tasa ta markada ta juye a cikin furar , zuma tasa a ciki da kuma dagen kwakwa (yaghourt mai kwakwa), fridge tasa sannan ta feshe d'aki da turare haka ma gado saida ta d'auki turarenta ta fesa mishi. *Wannan wani had'in damun fura ne, ku jaraba ku gani* Wani bala'en'en had'in kayan marmari ne da Mamie ta koya mata tayi tasa a fridge, da zaran yayi sanyi za tasha *emergency* kenan mai qara martaba da kima da qauna da soyayya da kuma nishad'i, hmmmm, yau fa Umar Faruk zaka gane kurenka, tana gamawa ta fad'a wanka. Shiryawa tayi cikin riga da siket na shadda daka gani kasan taji kud'i, uwa uba kuma d'inkin, sarkar zinariya ta d'ora akai sannan ta cab'a kwalliya ta fitar hankali, sakin gashinta tayi ta shafeshi da mayuka da turaren kai tare da kashe d'aurin d'an kwali, dogayen takalmi ta saka saida ta tabbatar ta gama da komai sannan ta zauna jiran Umar Faruk, kamar ya san ta gama da komai kuwa sai gashi ya shigo, "Assalama alai." bai qarasa ba saboda rumgumewar da Khairat ta masa..... Yanda ta fad'a kan qirjinshi da k'arfi yasashi cewa "Khairat, zaki kayar dani fa wata rana." Kallonshi tayi tace "sannu da zuwa." Kasa amsawa yayi yana kallon kwanukan abincin data shirya akan table, ga k'amshin dake tashi daga d'akin gwanin dad'i, kallonta yayi yace "kinsha aiki ko?" Kai ta girgiza masa alamar eh, kumatunta ya shafa yace "ayyah, sannu, bara na dawo daga masallaci na miki tausa." Dariya tayi ta kamo hannunshi ta fara cire mishi kayan jikinshi, da haka kuma ta shigar dashi douche ta sakar masa ruwa ta fara wankeshi soso da sabulu, cikin towel ta sakashi ta fito dashi, bakin gado ta zaunar dashi ta shafeshi da mai, ta d'auko kayan da zata saka mishi aka fara kiran sallah, cikin gaggawa ta saka mishi ta fesheshi da turare sannan ta mishi bye bye ya tafi masallaci. Zuby da taga fitarshi da qyar takai kanta d'aki tana tunani kala kala, wato itace ya raina shi yasa ma ko wanka bayayi a wannan lokacin in yana d'akinta, qwafa tayi tace "zaizo ya sameni, wallahi saiya gane bashi da wayo, kuma ina nan akan bakana, sai dai ka gaji ka bani hak'uri akan marin daka min amma badai ni ba." _HAMAGIYA_😏 Kamar yanda saba saida yayi sallah isha'i kafin ya shigo tare da Ishaq da abokinshi Abdul da kuma Noura, saida ya fara shiga wajen Baba sannan wajensu Mama, daga nan kuma d'akin Zuby ya nufa, yana shiga ya sameta zaune tana latsa wayarta, "assalama alaiki." Shiru bata amsa ba kuma bata kalleshi ba, zaune yayi kusa da ita yace "ya gida?" Ko kallonshi ba tayi ba tace "ba gashi nan ba kana cikinshi, koda wani abu ne kuma?" Kallonta yayi yana jin kamar ya maketa da duka, amma saiya daure yace "Zubeida, yanzu kina ganin haka shine daidai, kina ganin ya kamata ace ana samun wannan matsalar a tsakaninmu, me yasa kike haka, idan wani abu na miki ki fad'a min? ni ba fad'uwa bane a gareni danna baki hak'uri." A kauce ta kalleshi tace "au, wai baka ma san meka min ba, ka duba fa ka gani." Ta fad'a tana nuna mishi kumcinta inda ya mara tana fad'in "ka duba ka gani, har yanzu akwai shatin hannunka a lokacin daka mareni saboda kawai na fad'i sunan daya dace da waccen matar taka , amma shine kake nuna babu abinda ya faru ma." Tsaye ya mik'e yana fad'in "in dan wannan ne to kiyi hak'uri, yanzu ki tashi muje kuci abinci." "Humm, kaje kaci ni ba zanci ba, dan ba zan iya cin abincinta ba, kai dai da aka saba barbad'a maka kana ci kaje kaci." Wata yar sisiriyar dariya yayi yace "idan mutum yana abu to baya da yarda da kanshi, haka zai dinga ma kowa kallon zargi yana ganin shima yana abinda yake yi , amma duk da haka ki tashi muje, danke baki isa ki canzamin tsari ba." Tunda ya fara magana gabanta ke fad'uwa, tunaninta ko yaga abinda take, basarwa tayi tace "na fad'a maka ba zanci ba kaje kai kaci." "Zaki tashi ko saina takaki a wajen nan." tsawar daya mata ce tasa ta tashi tsaye bata shirya ba. _Ni kam nace, Khairat ma taji wannan tsawar bare ke_😏 Hijabi ta dauka tana gunguni tasa ta wuce shi kuma yana binta da harara, tsaye taga su Ishaq amma bata kulasu ba ta wuce kewayen Khairat tana turo baki gaba, bayanta yabi shima saida suka shiga ta tsaya shi kuma ya shiga da sallama, tashi tayi daga zaunen da take tana fad'in "sannu da zuwa." Yana mata murmushi yace "sannu uwar gidana, ana hutawa." Wani dad'i ne taji ya kasheta wanda yasa ta fara shafar qirjinshi tana murmushi, d'orawa yayi da "bak'inki sun iso." Sakinshi tayi tace "to bara na fitar musu da kujerun nan, koya ka gani?" "Ai yanda ki kayi shine daidai." Kujera ta d'auka yace "a'a, bari wannan aikina ne." matsowa yayi kusan kunnenta yace "na sani kun kinmin ajiya anan." Murmushi kawai tayi shi kuma ya fitar da kujerun ya aje sannan ya fita da qaramin tebur d'in shima, kwanukan abincin ta fito dasu a lokacin taga Zuby tsaye, da murmushi ta kalli Zuby tace "sannu 'yar uwa." Saida ta harara sama da qasanta taja dogon tsaki da yasa Umar Faruk kallonta, banza sukayi da ita shi kuma ya shigo dasu Ishaq, hijabi Khairat ta d'auko abinda Umar Faruk baiyi tunani ba, sawa tayi sannan ta fito ta samesu zaune tace "sannunku da zuwa." "Yawwa, sannu madame, ya gida? "Lafiya lau, ya qoqari?" "An gode Allah." Umar faruk ne ya kalli Zuby saboda jin tak'i magana, amma abin takaici saita wurga mishi harara, d'auke kanshi yayi yana murmushin yak'e, muryar Khairat ce ta katse mishi shiru da fad'in "ya aiyuka?" "Alhamdulillah, ya fama da ango?" cewar Abdul. "Kallon wanda yayi maganar tayi sannan ta kalli Zuby dake hararansu tace "yar uwa kinji fa, wai fama, ba wani fama da muke dashi, shifa kamar jariri ne a hannunmu." Tuntsirwa sukayi da dariya Ishaq ya d'ora da " ashe mutumin an shiga hannun mata." D'an matsowa Khairat tayi zata zuba abincin sukaji muryar Zuby tace "aikin banza kawai." tana fad'a ta wuce ta koma inda ta fito. Dakewa Umar Faruk yayi ya d'agawa Khairat hannu yace "a'a baby, barshi zan zuba, kije ki huta yau duk kibi kin gajiyar min da kanki." D'agowa tayi tana kallonshi tana murmushi tace "da babu kaine a ciki sai nace na gaji, amma hidimarka ba zata tab'a gajiyar dani, domin kowace matsowa da zanyi wajen aikinka , to a cikin lada nake, haka ka fad'a min a cikin karatunmu, ka barni na qarasa samun ladata baby." Sumbatar yatsunshi yayi ya jefa mata, kuma harga Allah yaji dad'in abinda ta fad'a shi yasa yayi hakan, murmushi tayi ta kanne masa ido d'aya sannan ta fara zuba abincin, jus d'in data had'a ta d'auko cikin wata juge mai kyau da cup d'inta ta zuba musu, haka ma furar data dama wacce tayi kyau ko a ido ta zuba musu kafin ta kalli Umar Faruk tace "aci lafiya." "Mun gode, Allah ya miki albarka." cewar Umar Faruk. Saida ta d'an sunkuya kamar zata duk'a har qasa sannan tace "ameen, na gode." sannan ta koma d'aki. Tana shiga ta zauna kan doguwar kujera tana jin yanda suke surutu tare da yabawa girkin da suke ci, dad'i taji tare da sake qudurawa zata sake gogewa wajen girki, har saida suka gama suka tashi tafiya sannan Umar Faruk yace ta fito suyi sallama, fitowa tayi sukace "madame mun gode, Allah ya saka da alkairi, girki fa yayi ba dama, muna muku fatan alkairi Allah ya bar qauna." "Ameen, mune da godiya ai da kuka zo inda muke." Juyawa sukayi zasu fita Khairat ta kalli kan tebur d'in tace "wa ya bar makulli?" Juyowa sukayi da sauri Noura ya d'auka yana fad'in "Lah, nawa ne." Wani dundu Umar Faruk ya sakar masa a baya yana fad'in "munafiki, harda cewa kaika koshi ba zaka ci dayawa ba, shine harda mantuwa." Fashewa sukayi da dariya suka fita, ita kuma d'aki ta koma ta cire kayan jikinta ta shiga douche ta watsa ruwa sama sama cikin sauri ta fito, rigar bacci ta fara d'aukowa ta saka sannan ta shafe jikinta da turare, yanzu ma sakin gashinta tayi ya bazu a bayanta, powder kad'ai ta shafa da lips mai k'amshi sannan ta d'auko had'in da tayi ta zauna harta shanye Umar Faruk bai shigo ba, bonbon (sweet) ta d'auka tasa a bakinta saiga Umariri an shigo... 17/08/2019 à 20:13 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣6⃣ Tsakiyar gado ta kwanta tana tsutsar alawar bakinta cikin wani irin salo, hannu ta mik'a masa alamar yazo, ganin haka yasa ya huri iska kafin ya juya ya fita, k'ofa ya rufe sannan ya shigo d'akin tare da rufe k'ofar, mab'allan rigarshi ya fara cirewa shima yana aika mata da wani kallon, kashe wuta yayi ya haura kan gadon ya mata runfa, bakinshi yakai ga nata ya fara tsutsa, alawar bakinta suka fara wasa da ita suna tsutsa a tare.... _Hmmmmmm, sai ana sayawa fa, inba haka ba yanzu sai kaji ana cewa kaza kaza_ Basu rintsa ba a tsawon dare, raya sunna kawai suke suna gajiyar da kawunansu, duk da Khairat takai maqura ta kuma gaji, amma haka ta daure ta kasa nuna mishi gajiyarta, tare sukayi wanka sukayi alwala suka fito, da kanshi yasa mata kayan sannan yasa nashi, sumbatar goshinta yayi yace "zan tafi masallaci, amma ba zan jima ba zan dawo." A wahalce ta kalleshi tace "saika dawo." "Ok." ya fad'a ya sake sumbatar goshinta ya d'ora da "Ina sonki alkairina." **************** K1mar yanda ya fad'a bai jima ba, yana zuwa suka koma kan gado tana rik'e da littafi, harta fara bud'awa dansu d'ora karutunsu ya karb'a ya aje yana fad'in "kinga kawo, yau dai kawai mu hak'ura da karatun, so nake kiyi bacci sosai." Janyota yayi jikinshi sosai itama kuma ta qara rumgumeshi qam a jikinta, babu jimawa bacci ya d'auketa, yana ganin tayi bacci ya zame jikinshi daga nata a hankali ya fita daga d'akin, d'akin Zuby ya shiga ya sameta zaune tana duba littafinta na école, yanzun ma bata amsa sallamarshi ba, a tak'aice shima yace "kin tashi lafiya?" A qwalla ta d'auki second ashirin kafin ta amsa da "lafiya." Taushe zuciyarshi yayi da k'arfi yace "idan kin shirya kimin magana na saukeki." Jin tayi shiru yasa ya kalleta, idonsu ne suka had'u tana wurga masa harara, ranshi ne yaji yakai qololuwa wajen b'aci, cikin zafin nama ya fizgo hannunta tare da mannata a bango ya taushe, k'ashin dake wuyan hannunta ya matse sosai yana fad'in "wa kike harara, dawa kike nace?" Tuni idonta suka kawo ruwa, kasa magana tayi hakan yasashi sanya yatsunshi biyu ya janye rigarta ya kaisu ga cikinta ya tsamuka, wata qara ta saki tare da fashewa da kuka lokaci d'aya, "ni kike harara, zaki fad'a min ko saina cire fatarki?" Cikin fashewa da kuka tace "dan Allah kayi hak'uri yah Umar, wallahi ba zan sake ba, akwai zafi wallahi dan Allah ka sakeni." Sakinta yayi yana hararanta yace "na sake gani wallahi ranki zaiyi mugun b'aci , tunda na lura ba zaman lafiya kike nema dani ba, kuma na fad'a miki kimin magana kafin ki tafi." Fita yayi ya barta a tsaye tana kuka, saida ta gaji dan kanta sannan ta d'auki wayarta ta dannawa Mama kira, saida tayi kusan kira biyar ana shida Mama ta d'auka dan tana bacci ita, cikin muryar kuka tace "Mama wallahi yah Umar baya sona yanzu, waccen karuwar duk ta d'auke mishi hankali, ni Mama kawai ki raba auren nan wallahi ba zan iya ba, ni na gaji da wannan bak'in cikin." "Me kuma ya faru yanzu da safiyar nan?" cewar Mama cikin magagin bacci. "Mama yanzu haka fa saida ya sani kuka, ni kawai nace miki na gani kisa ya sakeni kawai." "Kinga, kinsan me zai faru yanzu?" "A'a." cewar Zub. "To an jima idan kika tashi daga école, ki biyo ta gidana muje tare dake wajen malam saiki fad'a mishi komai da bakinki, kinji ko." Tsagaita kukan tayi tace "amma fa Mama bana da kud'i ni, ya zanyi nazo nan." "Karki damu kizo kedai, ni zan biya komai." Cikin farin ciki tace "to Mama, sai nazo." "Yawwa, ki daina kuka kinji, ki rabu dashi da 'yar iskar yarinyar, duk zanyi maganinsu wallahi, kuma wannan karan harda uwayen da yan uwanshi duk zan had'a." "To Mama na gode, sai nazo d'in." Da haka sukayi sallama ta fara shirin tafiya ecole cikin uniforme d'inta, tana gamawa ta fito ko abinda zata ci bata tsaya had'awa ba ta fito, Ruk'ayya ta samu tana wanke wanke tace "Ruk'ayya, kije ki fad'awa yah Umar na shirya." "To." Ruk'ayya ta fad'a ta wuce, Mama dake d'aki zaune tana jinsu tana mamakin yanda Zuby ko sau d'aya bata tab'a taka qafarta ba ta shiga d'akin da sunan tazo gaisheta, sai dai idan taje suna hira da Ruk'ayya, bare kuma sauran iyayen, tana zaunawa tsakar gida dasu dai suyi hira amma babu wanda take shiga ta gaisheshi. Ruk'ayya kam tsaye take a k'ofar d'akin tana sallama, jin shiru yasa ta d'an had'a da bubbuga k'ofar, a tare suka motsa saishi ya sake mayar da kanta akan pillow yace "shiiii , koma ki kwanta baby, zan duba na gani." Sake gyara kwanciya tayi shi kuma ya bud'e k'ofar, cike da ladabi tace "ina kwana yah Umar." "Lafiya lau Ruk'ayya, yadai?" "Zuby ce tace na maka magana." "Ok, kice ina zuwa." "To." ta fada ta sunkuya ta tattare kayan da Khairat tayi aiki dasu jiya danta wanke sannan ta juya ta fita. Tana tsaye saiga Umar Faruk ya fito da doguwar riga da makullin mota a hannu, ganin ya nufi hanyar waje yasa tabi bayanshi, saida ya shiga ya tayar da motar sannan ta shiga suka d'auki hanya, babu mai magana har sukayi nisa, Umar Faruk ne yace "ya karatun naki?" Cikin turo baki tace "lafiya lau." "Yayi kyau, babu wani abu da yake d'aure miki kai kuma?" "Babu." Bai sake mata magana ba harya sauketa, suna tsayawa tayi wuf ta fita daga motar ko kallonshi, ita ala dole ranta a b'ace yake, girgiza kai yayi kawai ya wucewarshi, restaurant d'in da Khairat ta tab'a sashi amsowa Mama abinci ya biya, oder abinci ya musu sannan ya wuce gidan yana tunano daren jiya, murmushi kawai yake saki yana jin farin ciki har zuciyarshi, tabbas da yana da arziki daya mallakawa Khairat duk abinda yake dashi kyauta, dan abinda yaji jiya yafi k'arfin tunaninshi, abune daya kusan zautar dashi ya kusa sashi haukacewa, baisan dame zai iya misalta dad'i da farin cikin daya ji ba, amma dai yasan inhar haka zasu kasance, to daf yake daya haukace ko zuciyarshi ta buga saboda farin ciki, da haka ya isa gida kai tsaye d'akinta ya wuce, cak yaja ya tsaya saboda ganin Khairat wacce koda taga ya fita itama ta tashi da gaggawa ta shiga wanka, cikin riga da wando tayi sauk'akk'an kwalliya tana suyar qwai. Cikin k'agaggen fara'a ta rumgumeshi cikin taushin murya tace "sannu da zuwa." "Yawwa sannu, amma me yasa zaki wahalar min da kanki, kinga abin kari fa na siyo." Kasa magana tayi sai langab'ewa da take kamar wacce tasha wani abu, kallon fuskarta yayi yana dariyar mugunta yace "yadai baby na ganki sukuku dake haka?" Sakinshi tayi ta koma kujerarta ta zauna tana juya qwan tana fad'in "ba komai, kawai dai bacci ne bai isheni ba." Karb'ar cokalin hannunta yayi ya durk'usa yana fad'in "kije ki kwanta to zan qarasa." A hankali tace "da gaske?" "Eh, na hutar dake da abinda ke cikinki." Tashi tayi tana hamma tana murzar ido tace "babu komai a cikina sai hanji." Binta yayi da kallo harta shiga d'aki, akan doguwar kujera ta kwanta bacci harya sake d'aukarta sai gashi ya shigo ya gama had'a komai, had'awa yayi da wanda ya siyo sannan ya tasheta suka ci, ganin lokaci ya tafi yasa Khairat nuna mishi agogo da hannu, kallo yayi ya kalleta yace "me?" "Lokaci ya tafi, ka tashi ka shirya karka makara fa." Cike da zolaya yace "to saime, naga nine mijin Hajia Khairat, babu wanda zai tuhumeni, kuma ma ai ina gida tare ina kula da ita." "Kenan yau ba zaka fita ba?" ta tambaya. Cike da kwonkwonto yace "umm , ina tunanin kamar haka dai." Duka ta kai masa a qirji tana fad'in "tashi ni babu ruwana, abinda ma na kusa siyar da compagnie." Kallonta yayi yace" saboda me?" Saida ta dauke ido daga kallonshi tace "ina so ne na zauna tare dakai nayi bautar aure." "Ke." ya fad'a da k'arfi tare da d'orawa da "rufa min asiri, kina so ki sani a bakin duniya ne? to bana ciki nidai." Murmushi kawai tayi tace "dan Allah ka tashi ka shirya kazo ka tafi." "Na makara fa, kina so naje manager ya hukuntani ne?" "Aiko yana hukunta kowa banda mijin Hajia Khairat, koya kace?" Da murmushi yace "kuma fa hakane tawa, ban biyar." ya fad'a tare da bata hannu, hannun ta bashi itama suka bige kafin ya mik'e yana fad'in "ina da sa'a fa dana zama mijin Hajia." Da murmushi kawai ta bishi tana sake kishingid'a akan kujerar, sauke idonta tayi akan gado tana tunano daren jiya, ajiyar zuciya ta sauke tana mai jin farin ciki da Allah ya bata miji kamar Umar Faruk, mijin da zai iya wayar gari yana d'ebe maka kewa ba tare da gajiya ba, ga salo masu rikita mutum bugu da qari baya da qyanqyami, zai iya kai bakinshi ko ina na mace, da tunanin nan Umar Faruk ya fito ya sameta, tashi tayi duk da a gajiye take haka ta tayashi shiryawa cikin bleue riga da bak'in wando, kayanta ta nufa ta bud'a sai gata da wasu kwali a hannu guda uku, ajewa tayi akan gado ta bud'a babban, wasu shegun takalmi ne suka bayyana qafa ciki masu masifar kyau, maganar tsada ma an ajeshi gefe, da kanta ta duk'a har qasa bayan ta zaunar dashi akan gado ta fara saka mishi takalmin, da mamaki yake kallonta yace "wannan fa?" "Tsarabarka ce, ko ka d'auka zan iya bawa kowa tsaraba banda kai?" Duk tayi maganar ne tana saka mishi takalmin, da kai kawai ya mata alamar a'a, tana gam saka mishi ta dago ta d'auki d'aya kwalin ta bud'e, wata tanfatsetsiyar agogo ce ta fito itama, nan ta makala mishi kafin ta d'auki kwalin d'aya ta bashi a hannunshi, kallo yake da matuk'ar mamaki kafin yace "Khairat, ki rik'e wannan ba zan iya karb'arta ba." Rai bace ta kalleshi tace "me yasa kuke min haka, gani kuke ni macece bai kamata ina haka ba, ko kuma kuna tunanin wata rana zan goranta muku ne kana mijina na baka abu kak'i amsa wa kake so nama? nifa na d'auka ni dakai d'aya ne, amma shine zaka nuna min ba haka bane, haka qaninka shima na mishi kyauta amma yak'i karb'a, shikenan kaima idan bakya so kaje ka jefa a cikin shara, amma ni na riga na siyo ba kuma zan tab'a amsarta ba." Ajiyar zuciya ya sauke ya sake kallon kwalin mai d'auke da photon tsaleliyar waya qirar *IPhone XMAX*, tsaye ya mik'e ya rumgumeta yace "shikenan to daina fushin." Tana cikin qirjinshi tace "ka karb'a?" Saida ya qara matseta yace "dole na ai, da kai da kaya ai duk mallakar wuya ne." Duka ta kai masa suka fashe da dariya tana fad'in "hamago, nice ya kamata nace haka ba kai ba." Cikin kunnenta ya rad'a mata " ai Umar Faruk mallakar Khairat ne, sai yanda taso za tayi dashi, kinga kuwa ai dani da hannayena na karb'ar kyauta daga gareki duk naki ne." Dariya ta sake yi tace "na ganoka fa, kana nufin dani da abinda na mallaka duka naka ne, shi yasa ma ka karb'a." Kumatunta yaja yace "mai basira kenan." Da qyar suka rabu ya tafi wajen aiki, ita kuma ta koma ta kwanta bacci danya tabbatar mata ba zai dawo da rana ba, aikinshi yake hankali kwance cike da farin ciki da nutsuwa, bayan sallah azahar saiga wani babban kira a wayarshi, ya zai gani inba Papa ba, da girmamawa ya d'auka suka gaisa, nan Papa yace yana son ganinshi inba damuwa, nan ya aje komai dake gabanshi ya tafi kiran mai gida kuma suruki. *Bayan yaje gidan* Papa yake sanar dashi wani compagnie a qasar *Las vegas* dake *America* suna neman zakakurin matashin mai aikin zane irinshi, dan haka in yana son aiki toya shirya zuwa qarar Las vegas domin tattaunawa dasu, kuma tattaunawar ba zata wuce gobe ba, dan haka idan ya amince compagnie ya d'auki nauyin tafiyarshi da dawowarshi, wannan shine sharad'in farko, Umar Faruk ya d'auka kawai alfarma ce Papa ya mishi kasancewarshi surukinshi, hakan yasa ya amince kuma ya kama hanyar gida cike da zumud'in fad'awa Khairat abinda ake ciki, sai dai baisan ita tayi silar samun wannan aikin nashi ba. Su Mama ya samu a tsakar gidan dukansu suna d'an tab'a hira sama sama, saida ya zauna ya fad'a musu komai dake faruwa, mahaifiyarshi dai kam tayi farin ciki, amma banda sauran iyayen nasu da suke ganin ci gabanshi na qara kusantoshi, addu'a Mama ta mishi kafin ya tashi ya nufi d'akin Khairat yana sake kallon k'ofar Zuby dake rufe, yana tunani a ranshi har yanzu bata dawo ba kenan, qwafa yayi a cikin ranshi kafi ya shiga d'akin da sallama, littafi ne a hannunta tana karatu tana ganinshi ta taso ta tarbeshi, "albishirinki?" "Goro." ta fad'a a harshen zarma kamar yanda shima yayi. A harshen zarma dai fad'a mata komai, rashin mamaki da tayi yasa yayi zargin wani abu, kallonta yayi yace "alkairina, kodai aikinki ne." Zaunar dashi tayi tana kallonshi tace "kayi hak'uri Umar Faruk, ba lallai ina so na canza qaddarar ubangiji a kanka bane, amma ina so naga kaji dad'i kaima, ba dole sai kayi aiki da compagnien ba harna tsawon lokaci, amma idan ka samu wani abu mai tsoka kaima zaka iya tsayawa da qafafunka, wannan shine burina a kanka, ina so naga ka tsaya da qafarka saboda kana basira da ilimin daka wuce ka zauna qarqashin wani, amma ka yafe min idan nayi ba daidai ba." "Shawara mai kyau, hakan kuma zai bani damar kin rattab'a hannu akan aiki dasu na dindindin." "Hakane." ta fad'a tana murmushi. Rumgumeta yayi yace "na gode Khairat." a zuciyarshi kuma cewa yayi " da farko na d'auka *Jihadi* nayi na aureki , amma yanzu komai na fitowa fili cewar, kece silar arzik'ina a duniya, kuma kece farin ciki da kwanciyar hankalina." D'orawa da "ki shirya, dan tare zamu tafi dake ki nuna min gari." Cikin dariya ta kalleshi tace "shirme." "Allah kuwa nake fad'a miki." ya fad'a yana dariya. _Wannan karan naga uban daya isa ya hana tafiyar nan._ ***************** Koda Zuby taje gida basu tsaya komai ba suka wuce wajen malam, nan Zuby ta fad'a mishi abinda ke faruwa, tambayarta yayi me take so a mata? cewa tayi asa Umar Faruk ya tsaneta harya saketa ma, nan yace msu "aikinku mai sauki ne, kuma zai yiwu, amma harsai kun samo wani abu daya zama na ita Khairat d'in ne, bi ma'ana abinda take sawa a jikinta koma menene, dashi za'a had'a laqanin da zai tsaneta, zaku iya?" Mama ce ta karb'e da "zamu iya mana malam, aiba wuyane da aikin ba." "A shikenan, kuyi qoqari ku kawo cikin kwana biyu ko uku, dan a gaggauta yin komai." "To malam, kar kaji komai za'a kawo." Da haka suka baro wajen malam Zuby tayi gida Mama ma tayi hanyar gida, da tunanin yanda za ayi ta samu abun Khairat taje gida, ganin motar Umar Faruk ba qaramin tsinkewa 'yan cikinta sukayi ba, da qyar ta shiga gidan tana d'an sunnewa, ganin baya tsakar gidan yasa ta fara gaggawar bud'a d'akinta ba tare data kula da mutanen tsakar gidan ba, suma babu wanda ya mata magana dan sunga abinta iskanci ne da raini, tana shiga tayi saurin cire kayanta tayi zaune gabanta na fad'uwa tana tunanin hukuncin da zai mata. Ana sallah la'asar ya fito, koda d'akin bud'e bai kula da tsiyarta ba yayi alwala ya wuce masallaci, bai kuma dawo ba sai bayan sallah isha'i, lokacin Khairat ta sake daddaga abinci mai rai da lafiya, saida ta zubo min a babban kula tace na kawawa _Team Khairat_ amma na taho akan hanya nayi tuntube tuwon ya zube, daga nan na zaune na qarasa cinye wanda yayi saura tare da kazar dake sama😋 kunsan dai akwai aminci tsakaninmu da kaza, yau ma kamar jiya sunci sunsha kuma sunyi farin ciki tare da raya darensu, yayin da Zuby haushi kamar zai kasheta, dan da yaje mata saida safe bai mata wata maganar kirki ba, hakan kuma ya qara b'ata mata rai, amma dai kuma ba zata iya bayar da hak'uri ba a tunaninta, shi kuma a nashi b'angaren yana ganin saita bashi hak'uri ta kuma gane kurenta sannan. _Me kuka ce mutanena?_ 😍😍😍 17/08/2019 à 20:13 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣7⃣ Kamar kullum gaba d'aya sun taru a d'akin Baba inda yake musu nasiha akan kyautatawa, saida aka gama kamar kullum ana shirin tashi Umar Faruk yayi gyaran murya yace "am, ina da magana, dan Allah ku zauna." Gyara zama kowa yayi Baba yace "muna jinka Umar Faruk." "Dama akan maganar aikin dana samu ne, acan compagnie suna buk'atar naje gobe domin tattaunawa dani, kamar yanda na fad'a muku wannan aikin Khairat ce silar samar minshi, kuma ni babu inda na tab'a zuwa na qasar waje, kasancewarta wacce tasan wajen yasa nake tunanin tafiya tare da ita, amma shawara ce bansan ku me kuka gani ba?" Baba ne yace "Umar Faruk, kaima fa yanzu magidanci ne, ba komai bane zaka nemi shawararmu akai, indai har kana ganin hakan ba matsala kuma shine daidai, ai saimu muku fatan alkairi." "Na gode Baba." ya fad'a kafin ya d'ora da "dama wannan ce maganar, na gode." Tashi kowa yayi zai fita Zuby kam ta kasa tashi, ganin Umar Faruk zai fita yasa Zuby kallon Baba tace "ina da magana nima." Juyowa Umar Faruk yayi ya kalleta, kallonshi tayi itama tace "ka dawo ka zauna." Zaunawa yayi Mama ma zata fice Zuby tace "Mama kema ki zauna." Saida kowa ya fita Baba ya kalli Zuby yace "ina jinki Zubeida, ina fatan dai ba wata matsala bace?" Tana kallon Umar Faruk tace "gaskiya ni ba'a min adalci ba, na fahimci yana son yin tafiya da ita, to ba komai su tafi, amma kafin su tafi ya fad'a min à wane matsayi nake, dan wallahi ba zan iya zaman gadi ba a gidan nan haka kawai." Da mamaki duka suke kallonta kafin Umar Faruk yace "Zubeida wane irin rashin adalci nake miki?" Shiru tayi harya sake maimaitawa da "Zubeida fad'a min, mena miki na rashin adalci." Cikin turo baki tace "ai duk mai ido yasan baka adalci a tsakaninmu, domin kuwa ko ranar aikina ne idan ka shiga d'akinta saika jima kafin ka fito, kuma inhar ka shiga d'akinta to sai dai ka fito da fara'a da murmushi a fuskarka, sab'anin d'akina idan ka shigo sai kayi duk abinda za kayi ka b'ata min ran sannan kaima ka fito cikin b'acin rai, bugu da qari ita cikin kayan abincin su Mama take diba tana aiki dasu, ni kuma ka siyo min wanda basu kai basu kawo ba, dad'in dad'awa kuma duk da nasan ita yar mai kud'i ce, amma na tabbata daga cikin suturun da take sakawa akwai wanda kai ka matasu na lefenta, yah Umar idan nace zan dinga zayyano maka rashin adalcin da kake ba zai k'idayu ba." Murmushin takaici yayi na gefen labb'a, dan yaso a kamashi da laifi danya b'ata hak'uri, amma kash ta kasa bayar da hujjar da zai d'auki laifin a kanshi, saida ya qara gyara zamanshi yace "da kin fad'i wani abu daban ba wannan ba, amma tunda haka ki kace bara na fad'a miki abinda yayi daidai da abinda kika fad'a." "Da farko kince idan na shiga d'akin Khairat nakan jima ban fito ba kuma ina fitowa da fara'a, ba zan iya ce miki komai ba, amma ina baki shawara ki samu wata qawarki da kika yarda da ita ki tambayeta me yake janyo hakan, na tabbata zata fad'a miki gaskiya, na biyu kuma maganar abinci, to kiji in fad'a miki, wannan kayan abincin da kika gani wallahi ko Baba baya da iko akansu kamar yanda Khairat take da iko akansu, kinsan me yasa? saboda itace ta siyesu, kuma bata tab'a kulasu ba sai ranar dake kika kawo shawarar kowace ta dinga girki da kanta, Zubeida idan akwai wanda akawa rashin adalci to Khairat ce, domin kuwa a lokacin dana siyo miki kayan abincin nan ita ban siyo mata ba, sannan na d'auki kud'i na qara muki dasu, duk da haka sisin kwabo ban bata ba dan nasan ba zata karb'a ba, tunda ta shigo gidan nan zan iya fad'a miki adadin da taci abincin gidan nan, kinga kenan ita akawa rashin adalci, na uku kuma kince sutura, to kijini da kyau Zubeida, ni banwa Khairat lefe ba kece nayiwa lefe, tunda nake da ita zani d'aya na atamfa bai shiga tsakani na da ita ba, kin ganni a matsayin mijin Khairat? wallahi har yanzu idan banda wurin kwanciya da ruwan gidan nan, banga wani abu da Khairat ke anfani dashi ba wanda zan iya cewa nawa ne, sannan atamfar da Khairat ke sawa a jikinta ma kad'ai tafi k'arfin arzik'ina, bare kuma kudin d'inkinta har azo ga shadda ko less, maganar sarka da d'an kunnai ma mu barta, har yanzu babu tsaiyar dana tsinanawa baiwar Allah nan a matsayina na mijinta, hasali ma nine ke qaruwa da ita tako ina, a yanzun burina bai wuce na samu hanyar da zan saka mata da alkairin data min ba, dan duk wanda zai bawa ahalinka abinda zasu ci ya kuma dinga kyautata musu, to tabbas shi masoyinka ne na gaskiya, musamman ita da bata damu da dukiyarta ba, ita dai burinta kawai ta kyautatawa wanda yake tare da ita, ba tayi dan gobe ta fad'a tayi maka, sannan idan tayi ba'a karb'a ba tana jin zafi, domin kuwa ita alheri a cikin jininta yake kamar yanda ma'anar sunanta yake, dan haka ina baki shawara Zubeida, ki cire komai a ranki ki rumgumi yer uwarki, wallahi babu komai a zuciyarta a game dake, ko sau d'aya bata tab'a nuna min kishinta a kanki ba, ina fatan za kiyi anfani da shawarata, kuma ki yafe min idan na fad'i abinda ya b'ata miki rai." Mik'ewa yayi da fad'in "saida safenku." danshi baiga abinda zai sashi b'ata lokacinshi ba akan banzan shirmen Zuby. Mama da Baba ma sun gamsu da abinda ya fad'a dan haka sukayi shiru harta tashi ta koma d'akinta, yana shiga d'aki Khairat ya sameta zauna tana tunani akan karatun da Baba ya musu, dan a cikin kyautatawar daya musu magana akai, akwai kyautatawa iyaye, ita kuma tana tunanin yanda ta zauna da nata iyayen, ji tayi tana so ta basu hak'uri akan yanda ta mu'mulancesu a baya, zaune yayi kusanta ya janyota jikinshi yana fad'in "yadai, meya faru." "Ba komai." ta fad'a tana shafa jikinshi. "Kin tabbata?" "Um." Dago kanta yayi ya kalli fuskarta, turo baki yayi gaba kamar yaro ya langab'e kai yace " ban yarda ba gaskiya, akwai wanda ya tab'a min baby, fad'a min meya faru.? Qara langab'ewa tayi tace " ba komai fa." "To indai hakane kiyi dariya na gani." D'an murmushin yaqe tayi tace "nifa bacci nake ji." Tana fad'a ta kwanta tare da jan zanin rufa, Umar Faruk a ranshi cewa yayi "baiwar Allah, ko tana tunanin abinda ya faru ne wanda ya tsayar dani? koma dai meye dole nima na saki farin ciki kamar yanda kema kike sakani farin ciki, wannan itace damar da nake da wajen saka miki da alkairi." Hayeta yayi ya fara mata cakulkuli yana fad'in "ba zan iya komai ba sai naga dariyarki." Ai kuwa dariya ta fara qyalqyalawa daga haka kuma suka lula duniyarsu ta maji dad'i...... ************** Tunda asuba koda Khairat tayi sallah ta fara shirya musu kayansu tare da shirya kanta , Umar Faruk kuma saida ya shiga d'akunan iyayensu suka gaisa tare da d'akin Zuby, haka yayi sallama har sau uku amma ko qala ba tace ba, sannan ya qara da "kin tashi lafiya?" Nanma shiru ba amsa, fita kawai yayi daga d'akin, yana zuwa shima shiryawa yayi a lokacin kuma Khairat ta gama abin karyawa, suna gama break suka fito cikin shirinsu, duka iyayen nasu na zaune dan haka suka qarasa suka musu sallama, sun tashi kenan zasu wuce Zuby ta fito tana rufe d'aki itama zata wuce école, ganin ko kallon kowa ba tayi ba ta kama hanyar fita yasa Umar Faruk binta da sauri, a soro ya sameta ya rik'e yana fad'in "ki jira mu saukeki." Fizge hannunta tayi tace "rabu dani bana so." Ganin Khairat ta taho kuma ko Khairat ba zaiso ta rainashi ba yasa ya wurga mata wata harara, shiru tayi tana sauke numfashi ,wucewa yayi suka bi bayanshi amma abin mamaki, da hanzari Zuby ta zagaya ta zauna a gidan gaba, kallonta yayi zaiyi magana kawai yaga Khairat ta bud'a mazauninshi ta zauna, saida ta daidaita zamanta sannan ta fizgo makullin hannunshi fuskarta a had'e itama ba alamar wasa, jin tayiwa motar key yasa ya bud'a gidan baya ya zauna ya rufe yana fad'in "Allah gani gareka, ashe dama haka mata biyu suke, da zaran sun had'u sai an caza maka qwaqwalwa." Gyara madubi Khairat tayi ta kalleshi tace "baby ka shirya?" Gintse dariyarshi yayi ya sunne kai qasa, Zuby kuma qoqarin bud'ewa ta farayi danta fita, Khairat na ganin haka ta fizgi motar da iya k'arfinta a zuciyarta tana fad'in "uban daya kawoki gidan gaba." Titi suka hau Umar Faruk na kallon kowace daga baya, Khairat na tuk'i hankali kwance Zuby kuma tayi tsaki yafi dubu , amma jin sun qyaleta yasa tace "aikin banza, barewa ai ba tayi gudu ba d'anta yayi rarrafe, an gada wajen uba dole a nuna hali." Ba tare data kalleta ba tace "na fad'a miki ki daina saka iyaye a maganar data shafemu , bai zama lallai abinda zai fito a bakina ya miki dad'i ba, amma kika b'ata min rai yanzun nan saina had'a motar nan da bango." Sai lokacin ta kalleta duk da tana tuki tace "bana tsoron mutuwa, dan Mama tace ni yar aljanna ce, bugu da qari ina tare da babyna, zanyi farin ciki mu mutu tare, idan kin shirya biyarmu to." "To an fad'a miki ina tsoron mutuwa ne? ai gwara na mutu ma da zama dake a matsayin kishiya wallahi, inkin fasa hadamu da bango bakya tsoron Allah daya halicceki." "Kin shirya mutuwa kenan?" cewar Khairat. "Shege ka fasa, d'an halak sai yanka." Da sauri Khairat ta kalleta tace "a'a malama, ki daina sako mana wannan kalmar anan, ni dai 'yar halak ce." "Kenan nice shegiyar?" "To ai ba kama garesu ba, kuma ba'a rubuta a goshinki ba bare na karanta, kinga kenan ba zan iya sani ba." "In haka kike tunani, toki d'auka ni yar babanki ce." Umar Faruk ne yayi saurin cewa "ya isa haka to, karna sake jin bakinku, inba haka ba rai zai b'ace." Khairat kuma gani tayi aita kaita qasa, dan haka tace "ina aiki na masu hankali, amma idan haukana ya motsa to akwai matsala, ki kiyaye bakinki kafin kiji abinda zai iya tarwatsa miki lissafi." Tsaki Zuby tayi ta rumgume hannaye har suka isa ecole d'insu, saida ta juya ta kalli Umar Faruk sannan ta kalli Khairat tace "na gode Allah, ni ba 'yar d'an giya bace." Tana fad'a ta fita ta bar motar, Khairat binta tayi da kallo lokaci d'aya hawaye suka soma zubo mata, fitowa Umar Faruk yayi ya bud'e inda take zaune, saida ya kama hannunta ya fito da ita sannan ta zagaya ta zauna inda Zuby ta tashi, saida suka fara tafiya jin tana shashek'ar kuka yasa ya fara tausarta da kalamai masu sanyi, ba tayi shiru ba har saida taga yayi parking a k'ofar gidansu sannan, zata fita ya rik'e hannunta suka kalli juna, d'aure fuska yayi yace, "Ki maye fara'a a gurbin d'aure fuskar nan." Cikin muryar kuka tace "amma fa kaji abinda yarinyar nan ta fad'a min." "Naji, kuma kamar yanda ki kace kina da hankali, to ina so ki nuna min ke mai ilimi ce, kuma naji dad'i da kika qyaleta." Share fuskarta tayi kafin suka fita suka nufi cikin gidan, sun samu Papa da Mamie suna hira a falo, da gudu Khairat ta fad'a jikin Papa tana dariya, saida suka gama murnar ganin juna sannan Papa yace "shalelen Papa, ashe har yanzu baki girma ba? na dauka kin girmi hakan yanzu." Turo baki tayi gaba tace "Papa wane irin girma kuma, nifa kamar autace a gareku, babu wani gabana kuma babu bayana, to in banyi ba wa zai muku." Mamie ce ta juyo da fuskarta ta kama kumatunta tana fad'in "banga laifinka ba, kiyi yanda kike so shalelen Papanta." Murmushi tayi tace "Mamie ina kwana?" "Lafiya lau Khairat, ina mai gidan naki?" Kallon kofar da suka shigo tayi danta nuna musu Umar Faruk, ganinshi tayi durk'ushe yana gaishe da Papa, ajiyar zuciya tayi ta tashi ta kama Umar Faruk ta zaunar dashi kan kujerar da dukansu suke tana fad'in "kaifa yanzu d'an gidane, bamu da wani dangi daya fika, yanzu kaine babban d'ansu bani ba, ka d'auka na baro Mama da Babana can gidan, yanzu kuma nazo gidanku ne kaima." Murmushi Umar Faruk yayi yana jin maganganunta na sake dawo masa a qwaqwalwa, Mamie ce ta dora da "gaskiya ne kam, ya kamata ka saki jikinka, muma iyayenka ne." Papa ne yace "wai harka shirya kenan?" Cike da ladabi yace "eh Alhaji." Khairat ce ta katsesu da fad'in "Alhaji kuma, Baban nawa? ni wallahi ban yarda ba, kace Papa kaima, inba haka ba, tam." Papa ne yace "dan Allah ki rabu dashi." Maida kallonshi yayi ga Umar Faruk yace "to amma kuma na ganku tare, kana nufin da ita zaka je?" Nanma cikin ladabi yace "eh, saboda bansan garin ba shi yasa nace muje tare." "To, da yake tana da biza ba matsala, amma ai ba jimawa zakuyi ba." Kwance Khairat tayi akan kafad'ar Papa tace "Papa ba zamu wuce kwana biyu ba." "To Allah yasa." Papa ne ya d'ora da "ya kamata ku wuce lokaci na tafiya." Kukan shagwab'a Khairat tasa tana fad'in "Papa korarmu kake, shikenan idan naje ma ba zan dawo ba, zan zauna acan ni da baby." Saida Papa ya kama kumatunta yace "da kuwa kin ganmu nida mahaifiyarki, dan kinsan ba zamu iya jurar zama nesa dake ba." Gyara zama Khairat tayi dama a tsakiyarsu take ta kamo hannayensu ta had'e wuri d'aya tana kallonsu tace "Papa, Mamie, a cikin karatun dana koya a gidansu Faruk, na fahimci girma da matsayin iyaye, iyayena ku yafe min, domin a jiya ne na gane kuskure na, nasan ban saku farin ciki ba, kuma ban zama 'ya ta gari a gareku ba, dan haka ina neman afuwarku tare dasa albarkarku, kuma nayi alk'awari insha Allah zan zama d'iya mai tarbiya a gareku, ba zan sake muku rashin kunya ba, dan Allah ku yafe min iyayena." ta qarashe da fashewa da kuka. Kusan a tare suka rumgumota a jikinsu, kuka suke sosai yayin da Mamie take kuka tana fad'in "Khairat mun yafe miki, kuma inda mai laifi, to mune iyayenki, munja miki abubuwa da dama a rayuwarki, muma muna neman afuwarki , dan ko kad'an bamu baki tarbiyar data dace ba." "A'a Mamie, kunyi iya qoqarinku, nice kawai ban maida hankali ba, ku yafe min dan Allah." Papa ne yasa hannu ya share mata hawaye yace "Khairat ba laifinki bane, komai nine silarshi, nine silar faruwar komai, inada damar da zan iya gyara halina tun lokacin da nake da quruciyata , amma na kasa gyarawa harna auri mahaifiyarki bada son ranta ba, amma kuma duk da haka ban gyara ba, ganin an haifa min 'ya mace ma baisa nayi tunanin komai ba na saduda , a haka naci gaba da shek'e ayata , harsai ranar da aka ci zarafin sannan na gane kurakuraina dana tafka wanda ba zasu tab'a gyaruwa har abada, nasan a baya wasu suna kiranki da 'yar d'an giya ko kuma shugaba marar adalci, wasu ma suna kiranki da 'yar mazinaci , amma ki sani wannan sunayen dane, yanzu na daina komai, siyaya ma ajeta zanyi da yardar Allah." Da qyar Umar Faruk ya rarrashesu sannan akasa driver ya kaisu aireport ya dawo da motar, ba b'ata lokaci jirginsu ya tashi da ikon Allah kuma suka sauka da izinin ubangiji..... Mota aka turo ta d'aukesu, kai tsaye babban hotel aka saukesu, wanka suka shiga koda suka fito an kawo musu abinci, suna gama ci kuma aka d'aukesu izuwa compagnie da suka zo dominshi, babban compagnie ne mai dubbanin ma'aikata, d'aki na musamman aka shiga dasu domin tattaunawar, manyan mutane ne guda biyu suke zaune suna zaman jiran zuwansu , suna ganinsu suka mik'e saboda girmamawa tare da bawa Umar Faruk hannu, suna gaisawa d'aya dattijon ya bawa Khairat hannu dansu ba wani abu bane a wajensu, saboda ne yasa Khairat mik'a mishi hannu itama da nufin su gaisa, amma jan kallon da Umar Faruk ya mata yasa yan cikinta murd'awa, tabbas Umar Faruk nada kwarjini kuma tana shakkarshi, da sauri ta janye hannunta a daidai lokacin da mutumin ke neman rik'e hannunta, kallon Umar Faruk sukayi kawai suka basar, da hannu suka nuna musu su zauna, nan suka zauna suka tattauna akan abinda ya kawosu, duk da ya fad'a musu ba zaiyi aiki dasu ba na dindindin amma sun amince, dansu burinsu kawai shima su mori basirarshi, dan qirqirarshi da aka nuna musu yayi matuk'ar birgesu , abinda yaba Umar Faruk mamaki shine, bill da suka bashi kuma sukace ya rubuta adadin kud'in da yake so su dinga biyanshi , da taimakon Khairat ya rubuta adadin da yake bukata, anan suka sallameshi bayan sun bashi sabuwar computer wacce zai dinga musu aiki da ita, sannan aka ce jibi jirginsu zai kuma tashi, kai tsaye aka sake mayar dasu masaukinsu, saida suka huta sukayi bacci sannan suka shirya suka fita ganin gari, Khairat ce ke zagayawa dashi ko ina duk da itama ba wani sanin garin tayi ba sosai, a haka suka dinga shaqatawa har dare yayi sai dai lokacin kowace sallah suka samu wuri Umar Faruk yajasu , taxi suka tare ta kaisu masaukinsu, suna zuwa wanka sukayi suka ci abinci sannan suka kwanta. *Asuba ta gari* Washe gari ma koda suka shirya fita sukayi cikin qananan kayan sanyi, wuraren shaqatawa suke je sukayi farin ciki abinsu tare da d'aukar photuna , saida dare yayi yauma suka kamo hanyar masaukinsu, kafin su hau titi akwai tafiya kuma gashi wajen babu mutane, Khairat ce ta qamqameshi tace "baby nifa tsoro nake ji." "Tsoro, kina tare dani d'in?" Sunkuyawa yayi yace "hau na goyaki to." ko qarasawa baiyi ba Khairat ta haye bayanshi, tafiya suke a hankali suna hira qasa qasa, dan Khairat gabanta kawai ke fad'uwa tana ji akwai matsala, amma dai bata san me zai faru ba, suna cikin tafiya kawai wasu samari su shida dake gefen hanyar suka fito tare da tare musu gaba, a hankali Khairat ta sauko daga bayan Umar Faruk tana kallonsu cike da tsoro, hannunta Umar Faruk ya kama da nufi su wuce danshi ko d'ar bai jiba a zuciyarshi , d'aya hannu tasa ta rik'e hannunshi tana girgiza kai, kallonta yayi yaga tsoro fal a idonta da fuskarta, fuskantarta yayi ya dafa kumatunta yana fad'in "baby, kalloni nan, kwantar da hankalinki, babu abinda zai faru ina tare dake, ki nutsu kinji, kar kiji tsoro." Kai ta girgiza da sauri hawaye na zuba a idonta dan duk gani take zasu mata abinda su Musa suka mata ne, qara rik'e hannayenshi tayi tana fad'in "dan Allah Faruk kazo mu canza hanya, wallahi tsoro nake ji, bana son abinda ya faru dani a baya yanzu ma ya sake faruwa, zan iya kashe kaina in haka ta faru, dan Allah kazo mu canza hanya, wannan basu da imani 'yan shaye shaye ne kawai." "A'a Khairat bab......." bai qarasa ba yaji saukar abu a kanshi, qarar da Khairat tayi yasa d'aya daga cikin matasan ya fizgota a jikinshi tare da rufe mata baki, duk da girman bugun da suka mishi akai bai fad'i ba, sai dafe kai da yayi yana lumshe ido, kallon matashin daya rik'e Khairat yayi yana murmushin takaici, kamar mai ciwon baki yace "saketa, in kana son kanka da lafiya." Biyu daga cikin samarin sun fahimci me yace a harshen frensh dan haka suka fad'a musu me yace dansu sunfi jin english, wurga Khairat yayi ga d'aya daga cikinsu, shima rik'eta yayi har yana shafar jikinta, ganin haka yasa Umar Faruk yin kukan kura kan samarin , cikin sauk'i yayi nasarar k'wace madakin dake hannun d'aya daga ciki, nan fa ya soma dukansu kamar Allah ya aikoshi , wani ne yayi nasarar dukanshi ta baya ba tare daya lura ba, qara dafe kai yayi yana ganin dishi dishi ga jiri na d'ibarshi, tangal tangal ya ya fara yana shirin fad'uwa, da gudu Khairat ta rik'eshi ya fad'a kanta, tana daddab'ashi d'aya daga ciki ya finciko gashin kanta yana fad'in "ina kud'i suke? kud'i muke so." Cikin kuka da d'aga murya tace "babu kud'i a jikinmu, mu bak'i ne." Rigar sanyinta yaja da k'arfi harta fita ya rage sai qaramar rigarta ta ciki, hannunta ya kamo da k'arfi ta mik'e tsaye yayin da Umar Faruk ya qarasa fad'uwa qasa yana fad'in " idan baku da kud'i, ai kina da kadara, dan haka zamu je dake mu fanshe kud'inmu." Kururuwa kawai take tana qara tana dukanshi, a hankali Umar Faruk ya bud'a idonshi ya kalli inda suke nufa da ita, wani d'aki dake gefen suka jefata a ciki suka rufe, baya baya take ja d'aya na biyanta yana rage kayan jikinshi, qara ta qurma da k'arfi wacce tasa Umar Faruk mik'ewa zunbur, ai kuwa tunkarar d'akin yayi cikin wani sabon k'arfi da yake ji yana zuwa mishi, qafa yasa ya dinga bugun k'ofar, ana uku kuwa ta bud'e, yanzun ma dai saida aka kai ruwa rana kafin yayi nasara a kansu, wanda ya fara fitar da kayanshi ne Umar Faruk ya shak'e mishi wuya cikin zafin rai yana fad'in "me kayi niyyar aikatawa a kanta, fyad'e, shin kasan me iyali yake nufi, kasan me ake cewa mata, kasan me mutum zaiji idan akace an yiwa matarshi fyad'e a gaban idonka, shin kasan me zai ji?" Ya qarashe da had'a kanshi da bango, zubewa yayi kamar ba rai a jiki, tsorata da Khairat tayi yasa ta kama hannun Umar Faruk da sauri suka fito daga d'akin, Khairat har had'awa take da gudu gudu, yayin da Umar Faruk zuciyarshi ke bugawa da k'arfi yake jin inama yaci naman yaran nan d'anye , dan wani sabon tsumi suka tayar masa tare da tuna su Musa, cikin sauk'i suka samu taxi suka koma masaukinsu , suna daf da shiga Umar Faruk ya lura da rigar dake jikinta, cire rigar sanyinshi yayi ya mik'a mata ta saka sannan suka wuce d'akinsu, cike da tsoro da fargaba Khairat tasa key ta murzawa k'ofar d'akin, tana juyowa taji saukar wani azababben marin daya sa ta fad'i gefe d'aya.... _Tohhhhhh, me kuka ce yan uwa?_ 20/08/2019 à 14:26 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣8⃣ Dafe kunci tayi lokacin data kwamtsa qara dan a bazata marin yazo mata, da'gowa tayi ta kalli Umar Faruk ba tare data tashi daga fad'uwar da tayi ba, za tayi magana kuma ya sunkuya yasa hannu ya shako wuyanta rai b'ace ya had'ata da bango yana fad'in, "Ke mahaukaciyar inace, ke wace irin sakarya ce, au dama haka ake miki fyad'en, ba kya iya kare kanki sai dai kawai ki dinga kuka, me kike tunanin zai faru idan da sun sake maimaita abinda ya faru a baya, ni sakarai saina sake hak'urin zama dake? sam ba zai yiwu ba wallahi, da kin bari haka ta faru dana rabu dake, danni ba sakarai bane da zan zauna ina qarasa ragowar 'yan iskan gari." Hannun daya shak'e mata wuya dashi ta kam tana so ta kwaci kanta, idonta duk sun fito ta rasa shed'a cikin wahala da fafutukar neman rayuwa tace "Fa...faru.k, ka...k..ka sakeni, zan..... zaka...kasheni.." Sakinta yayi ya tashi ya fara cire kayan jikinshi ya shiga douche, binshi tayi da wahalallen kallo tana kallon jinin dake bin kanshi, da qyar ta rarrafa ta rakub'e qasan gado tana kuka, tana nan harya fito d'aure da towel ya shirya cikin gajeran wando ko riga bai saka ba, wani hankciep ya d'auka ya d'aure kanshi kafin ya bud'a wata drower ya d'auko paracétamol, wanda ake ajewa saboda irin haka dama yasha sannan ya zauna akan kujera, matuk'a ranshi a b'ace yake dan haka ko kallonta baiyi ba, kuka take amma babu mai rarrashi sai dai ta juya ta saci kallon Umar Faruk, amma shi ko kulata baya yi, share hawayenta tayi ta tashi ta zagaya inda yake ta tsaya, d'ago da jajayen idonshi yayi ya wurga mata harara, jiki na rawa tayi saurin zube gwiwoyinta qasa, a hankali ta qara satar kallonshi, ganin yanda ya kafeta da ido ba annuri fuskarshi yasa ta sake fashewa da kuka, wani dogon tsaki yaja ya kawar da kai gefe yace "kije ki kwanta bana son kukan nan, idan kuma ba haka ba ranki zai qara b'aci." Cikin fashewa da sabon kuka tace "dan Allah Faruk kayi hak'uri, wallahi bana da laifi, ya kamata ka...." Cikin d'aga murya yace "kije ki kwanta nace ko." Tashi tayi ba yanda ta iya, ko kayan jikinta bata cire ba taja zanin rufa ta rufe tana shashek'ar kuka, kusan minti ashiri babu mai magana sai jiniyar kukanta, cikin dakkakiyar murya yace "ki rufe min bakin nan fa." Hannu tasa ta rufe bakinta tana fitar da sautin kukan a hankali, jin tak'i yin shiru yasa ya taso yazo gabanta yace "nace kiyi shiru, amma saboda kin rainani kin k'i kiyi shiru ko? to tashi zaune." Tashi tayi zaune taja zanin rufa ta rufe bakinta tana kallonshi tace "kayi hak'uri na daina." Kan gadon ya hau ya jingina ya mik'e qafafunshi yaja zanin rufa ya d'auki wayarshi ya fara dannawa, kallonshi take ganin baya kulata daga haka har bacci ya d'auketa daga zaune, jin yanda take sauke numfashi yasa ya d'an juya ya kalleta, ganin tana bacci yasa ya aje wayar gefe ya gyara mata kwanciyarta, kallon fuskarta yake sosai yana jin sonta na qara huda mushi zuciya, wani b'angare kuma tunanin abinda ya faru a baya da wanda yaso faruwa yau ne yake, a ranshi yace "wallahi Khairat zan kashe duk wanda ya sake keta miki haddi, haka kema zan iya kashe kaina danna huta, ki kiyaye kuma ki kare min mutuncinki." Haka suka tashi suka shirya dan komawa qasarsu amma babu mai magana, Khairat har gaisheshi tayi amma bai amsa ba, kuma a haka har suka hau jirgi, suna cikin jirgi Khairat ta kalleshi cikin taushin murya tace "baby, dan Allah ka daina fushi dani, bana da laifi a cikin al'amarin nan, ba zan iya shiga qasarmu ba alhalin kana fushi dani, dan Allah ka yafe min." Kallonta yake kamar ba zaiyi magana ba ita kuma tana sunne kai, hannayenshi ya bud'e mata alamar ta taho, saida tayi murmushi kafin ta fad'a jikinshi ya rumgumeta, wasu hawaye ne suka taho mata tace "Faruk ina sonka, dan Allah karka hukuntani ta hanyar nesanta kanka dani, ba zan iya jura ba." Saida ya sumbaci kanta yace "kiyi hak'uri baby, rai nane kawai ya b'ace, amma nima ba'a son raina nayi ba, amma ba zan sake maimaitawa ba, nima ki yafe min kinji." D'ago ido tayi ta kalleshi tace "ba zan yafe ba, sai munje gida na rama sannan zan huce." Kallon idonta yayi yace "kina so na mutu ko?" "A'a." ta fad'a cikin taushin murya. "To karki fara ramawa, dan zaki gane mijinki ragone idan ki kayi haka." "Ba wani nan, bayan jiya ka nuna min zaka iya acting as sadaukin jarumi." Nanma qwayar idonta ya kalla yace "zan iya komai a kanki Khairat, na fad'a miki zan iya indai akan sonki ne." "Ina sonka." ta fad'a tana qara qwaqwumeshi. Sun sauka lafiya kuma taxi ya kaisu gidansu Papa, bayan Umar Faruk da Papa sun tattauna sannan ya d'auki motarshi suka tafi gida, tun a k'ofar gida yara suka fito suka tarbesu, haka suka shiga cikin gidan ana musu sannu da zuwa, Ruk'ayya ce ta karb'i kayansu da makulli ta bud'e ta shigar musu da kayan, Zuby ce ta fito daga wanka zata shiga d'aki, kallon kallo sukayi da Umar Faruk dan Khairat harta shiga d'aki, "sannu da zuwa." Ta fad'a kawai tasa kai d'aki, ganin ta shige yasa shima ya wuce d'aki, Khairat ya samu harta shiga wanka dan haka ya fito ya shiga d'aya douche d'in dan yayi wanka, doguwar riga kawai Zuby ta saka ta fito dan tayi alwala dan an fara kiran sallah, ganin yara maza sun fita k'ofar gida suna alwala iyayen kuma sunyi sun shiga d'aki, kusan dai gidan ya d'anyi shiru hakan yasa ta tuna da aikin da malam ya basu, aje butar hannunta tayi ta lallab'a a hankali ta shiga d'aki Khairat, tana shiga idonta ya sauka akan gado, jaka waya da kuma mouchoir (hankciep) ta gani akan gadon, da sauri ta d'auki mouchoir d'in dan a ganinta zaifi zama qaramin abu wanda ba za'a gane ba, sai dai kash, sark'ar da Khairat ta cire ce ta rufe da mouchoir d'in, kuma wajen d'auka da sauri yasa yan kunnai suka fad'i qasa saita had'a da sarqar ba tare data lura ba. Da sauri ta shiga d'aki ta kira wayar Mama, a lokacin kuma Umar Faruk ya fito ya shiga d'akin Zuby baiko kulata ba yasa kaya ya fita masallaci, saida taga ya fita sannan tace wa Mama "Mama na samo abinda malam yace." "Yawwa yar albarka, amma tayaya sun dawo ne?" "Eh Mama." ta fad'a tana warware mouchoir d'in danta kalla, ido ta waro tace "Mama, sarqa ce fa a ciki." "Sarqa kuma, ita kika d'auko?" "A'a Mama, ina ga cikin mouchoir d'in take." "To kinga ki ajesu , zanzo gidan an jima saina kaiwa malam d'in." "To Mama." daga haka sukayi sallama, kallon sarqar take sosai qarama mai kyan gaske, wani babban dutsi ne ya qawata sarqar, ajewa tayi ta jira zuwan Mama. Khairat na fitowa ta shirya cikin doguwar riga sannan ta rama duk wata sallar dake kanta kafin ta cire doguwar riga tasa riga da wando, jakarta ta d'auka ta fara cire kayan ciki tana mayar da komai mazauninshi, kan mouchoir ta aza hannu sai taji ba komai, kallon wajen tayi amma dai taga ba komai, wajen dressing miror ta nufa danta duba sai taji ta taka abu a qafarta, "ashhhh." ta fad'a tare da d'auke qafarta ta duba wajen. Da mamaki tasa hannu ta d'auki 'yan kunnai dake qasa zube, duba gadon ta farayi amma sam bata gani ba, aje 'yan kunnai kawai tayi ta kwanta da littafinta a hannu tana karatu, sai dai tana tunanin yanda akayi abinda ta aje anan ta kuma rasashi. *************** Bayan sallah la'asar Mama tazo gidan ta karb'a, a lokacin Khairat na d'akinta bata sanma da zuwanta ba, koda Mama taga sarqar tace zata kaita kasuwa ta siyar, dan ba zai yiwu a mayar da ita ba kuma da alama za tayi tsada, dan haka daga nan wajen malam ta nufa takai mishi mouchoir d'in, kasancewar magrib ta gabato yasa ta koma gida da niyyar gobe zata kai sarqar kasuwa ta siyar. **************** Har Khairat ta fara bacci Umar Faruk ya shigo d'akinta, bai yarda ya tasheta ba dan yasan tana tare da gajiya, a hankali ya lallaba ya sumbaci goshinta sannan ya sake gyara mata rufa, dauke littafin dake qirjinta yayi ya daga hannayenshi ya tofa addu'o'i sannan ya shafa mata a jiki, ficewa yayi ya rufe mata d'akin sannan ya koma d'akin Zuby, da qyar Zuby ta amince da Umar Faruk ta bashi hakk'inshi, abin takaici kuma banbaci ne nesa tsakaninta da Khairat, ba yanda ya iya dole yana da hankalin da zai iya banbace dad'i da akasin haka, yana mamakin yanda yake samun Khairat kullum kamar budurwa kullum, dan kullum saita zubar da hawaye idan zai shigeta, amma Zuby ya kasa tantance meye ma yake ji a tare da ita, koda ya samu ya tsarkake kanshi bai kwanta ba, karatu ya dinga yi har dare ya raba kafin ya kabbara sallah, nanma saida aka kira sallah sannan ya nufi d'akin Khairat, koda ya shiga ya samu har tayi alwala, dad'i yaji sosai bayan ta gaisheshi sannan ya wuce masallaci. Da safe kuma basu samu damar karatu ba saboda yana d'akin Zuby yana bacci, Ruk'ayya ta samu ta d'ora mata karatun, suna gamawa kuma Mamie ta kirata danta mata ya gajiya, suna cikin magana Khairat tace " Mamie, jiya fa na jefar da sarqata." "Wace sarqar kuma?" cewar Mamie. "Mamie sarqata ta *diamond*." Waro ido Mamie tayi kamar tana gabanta tace "diamond d'inki, garin yaya Khairat, me yasa kike da sakaci ne haka, sarqar milyoyin kudade zaki saki har a d'auke?" Cikin katse hanzari tace "Mamie, sarqa cefa, kuma ta b'ata, ya zanyi to? dan Allah karki damu kanki, zan siye wata insha Allah." "Humm, haka za kice mana, dan kinsan kina tambayar mahaifinki ko million nawa ne zai baki shi yasa." "Mamie, to idan bai bani ba wa zaiba? ni kad'ai ya haifa a duniya, nice mai gadon komai nasa, ai yafi naci tun muna kan lokacinmu." "To naji, yanzu ki aje yan kunnan, zan kira *Alpha* da *Maiga* na fad'a musu idan sun samu koda mai kama da 'yan kunnan su kawo min, dan nasan halinki zaki iya yin banza dasu." "To Mamie, amma nidai da baki bawa kanki wahala ba." "Kiyi yanda nace kawai." "To Mamie." tana fad'a ta kashe wayar, Mammie ce ta kalli Mamie ta tambayeta meya faru, nan ta fad'a mata abinda ke faruwa, a take Mamie ta kira Alpha da Maiga ta kula tura musu photon sarqar da yan kunnan lokacin da aka siyesu. **************** Tun Mama nakan hanyar zuwa kasuwa take kiran wayar malam amma yak'i d'agawa, ta alaqanta hakan da yawan abubuwa, shi kuma ya ya kasa d'auka ne saboda sam babu nasara a aikinsu, danya riga daya gama fahimtar indai har Khairat na cikin gidan nan to babu abinda zai iya yi mata, saboda tsaron dake cikin gidan, ana yawan karanta Qur'ani musamman suratul Baqara, dan haka dole dai su sake shawara. Mama na zuwa kasuwa ta zarce wajen wani babban mai harkar sarqoqi mai suna Alpha 😂😂😂, (wallahi dariya take bani), yana ganin sarqar yace "gaskiya Hajia kinzo da babbar harka, amma ki d'an jirani zansa a duba kota qwarai ce ko jabu." Tana wasar baki tace "ba komai ai, nasan ma ta qwarai ce." kuma ta fad'i hakane ba tare da sanin wace irin sarqar take rik'e da ita ba. Yana shiga daga cikin shagon ya kira Mamie ya fad'a mata irin sarqarce komai da komai, amma babu yan kunnai "bani minti biyu zan kiraka." cewar Mamie. Tana kashewa ta kira Khairat ta fad'a mata, shiru Khairat tayi tana tunani, mamaki take sosai ta yanda akayi sarqarta ta fita daga gidan, duk da dai ba tabbaci amma tana so tasan waya samu sarqar, da sauri tace "Mamie, kice ya rik'e matar karya bari taje ko ina." "To." Mamie ta fad'a tare da kashe wayar, ba b'ata lokaci Khairat ta dannawa *Abdul waid* kira, tare sukayi makaranta abokinta ne sosai kuma gendarme ne, yana d'auka yace, "Marar mutunci, ashe zaki tuna dani harki kirani?" Dariya tayi dan indai sun had'u sai haka ta faru, cewa tayi "petit frère, ya kake?" "Ba zaki daina cemin qannanki ba ko? har yanzu kina nan da shegen san girma, ke mutum koya baki shekara arba'in kina iya kiranshi qannanki." "Saboda nasan na girmeka ne shi yasa." "To naji, ya akayi yanzu? kwana biyu kin b'ace." "Wallahi da dama, amma yanzu akwai matsala." "Meya faru?" "Shekara d'aya data wuce akwai wani diamond dana siya, to shine jiya bayan na dawo daga las vegas na ajeshi, kawai na fito ban sameshi ba, amma abun mamaki yanzu Alpha ya kirani wai wata mace tazo da irin sarqar zata siyar." "Subhanallah, yanzu me kike so ayi?" "Um , ina so nasan matar kuma ya akayi sarqar taje hannunta, nasan zaiyi wuya ace ba sarqata bace, tunda ga 'yan kunnan a hanuna." Kamar yana gabanta yace "an gama ranki shi dad'e, za ayi yanda kike so baby." Da sauri tace "kai bana san iskanci, wannan sunan yanzu mijina kad'ai keda damar kirana dashi." "Ke tafi can marar mutunci, ai dama jira nake na had'u dake wallahi sai anyi yak'in duniya na uku, wai yarinyar nan dan kin rainani kawai sai dai naji kinyi aure a gari, ba sanarwa ba kira ki fad'awa mutane, amma ba komai nine kika tsana ai, tunda *Ma'aruf* yace da kanki kika kira kika fad'a musu." "Ai ban kiraka bane saboda baka damu dani ba, wata na kusan hud'u ina jinya amma baka tab'a zuwa ka dubani ba." Shiru yayi kafin yace "kiyi hak'uri Khairat, wallahi nima labari na samu akan abinda ya faru dake, amma lokacin bana gari." "Kaga ni ka dameni da surutu, kaje da sauri dan Allah ku qwamuso min matar nan." Dariya yayi yace "baki da dama, kina nan yanda kike har yanzu." "Kai wallahi ba kamar da ba, yanzu in fad'a maka inka ganni ba zaka ganeni ba, yanzu fa da hijabi nake fita." Bushewa yayi da dariya lokacin da suka shiga mota shida jami'ai guda biyu suka nufi kasuwa yana fad'in "Allah ya shirya minke Khairat, yanzu fad'a min adresse d'in mai shagon?" "Ba matsala zan turo maka, amma fa bana so kayi saurin fad'an sunana." "No wahala baby, za ayi yanda kike so." "Kai, zanci..., wallahi ka kiyaye ni fa, mijina zai shek'ek'a idan yaji" Tana fad'a ta kashe wayar ta tura masa d'à adresse d'in, Mamie ta kira ta fad'a mata yanda ake ciki, tana d'an duba karatun da Ruk'ayya ta d'ora mata Umar Faruk ya shigo d'akin da sallama, tashi tayita tarbeshi suka gaisa, tambayarshi tayi da "ba zaka fita yau ba?" Saida ya shafi qasumbarshi yace cike da kasala yace "yau kam bana jin dad'in jikina, amma kuma ina so na fita, gashi kuma na makara sosai." Itama gemunshi ta shafa tace "bara kaga yanda za ayi." Wayarta ta d'auka ta dannawa manager kira, cike da girmamawa ya gaisheta kafin ta d'ora da "manager ayi mana uzuri nida Faruk, kasan jiya muka shigo." "Ah haba Hajia, ai girmanku ne, ba komai wallahi." Kashe wayar tayi ta kalleshi tace "kaje ka sake kwantawa." Ba gardama ya sake mikewa ya fita ya koma d'akin Zuby, yana tafiya kuma sai taji hawaye sun zubo mata, sharewa kawai tayi taci gaba da karatunta. *************** Alpha ne ya d'anja Mama da hira yace mata "Hajia saifa kin jira an kawo min kud'i daga banki." Baki Mama ta bud'e tace "wai dama darajarta har takai haka?" "Hajia dama baki san darajarta ba." "A'a ba haka nake nufi ba, kasan mu tsofaffi ba ruwanmu." Murmushi yayi yace "Hajia diamond kike d'auke da ita fa." "Diamond?" cewar Mama da ita k'arfinta, hakan kuma yayi daidai da isowar su Abdul Waid, cikin d'aure fuska Abdul Waid ya sauko daga mota yana zarewa Mama ido, "kece wacce zaki siyar da sarqar?" Mama da jiki ya ya fara rawa ga fad'uwar gaba da tsinkewar yan ciki tace "a'a.....a..a.., ba...b.ni." Kallon Alpha yayi yace "mun samu rahoton anzo siyar da sarqa nan wajen, shin zamu iya sanin gaskiya." Sarqar ya bashi tare da fad'a mishi komai, ba sauki al'amarin suka tusa Mama cikin mota suka tafi da ita, suna zuwa suka garqameta suka rufe sannan ya kira Khairat ya fad'a mata, duk da bata san ko wacece ba cewa tayi "kawai ta fad'a muku yanda ta samu sarqar." _Ma'u ho_😂 *************** Sai kusan la'asar labari ya riski Zuby da mutanen gidan, gaba d'aya Zuby ta ishi gidan da kuka da jiniya , da qyar Umar Faruk ya lallab'ata yace zaije yaji miye matsalar😂😂 (wlh dariya kawai ke sub'uce min), koda yaje kuwa aka fad'a mishi abinda ake ciki, amma kuma Mama tak'i fad'in yanda akayi ta samu sarqar, abu kamar wasa haka labari ta fara karad'e dangi da mutan gari. Khairat na jin abinda ke faruwa tayi mamaki sosai, to taya sarqarta taje hannun Mama? wannan itace tambayar da take wa kanta, dan haka taci alwashin sai Mama ta wahala ta kuma gane kurenta tare da fad'in yanda akayi sarqarta taje hannunta, gidan babu wanda yayi bacci a daren saboda kukan da Zuby keyi, a haka safiya tayi Zuby ta shirya dan tafiya ganin Mama. Saida Umar Faruk ya matsa mata ta samu taci abinci, suna shirin fita daga gidan jiri ya d'ebeta ta fad'i, a firgice Umar Faruk ya d'auketa yana kiran sunanta, d'akin Mama ya kaita ya kwanta aka shafa mata ruwa ta farka, bayan qanqanin lokaci kuma zazzab'i ya rufeta, duk da haka matsawa tayi saita tafi dan haka Umar Faruk ya d'auketa suka tafi, koda taga halin da Mama ke ciki ma sabon shafin kuka ta bud'a, da qyar Umar Faruk ya fito da ita daga wajen, suna hanya yaga tana rawar sanyi sosai dan haka ya wuce da ita asibiti. Ana dubata aka tabbatar mishi tana d'auke da qaramin cikin da ba zai juri wahala ba, ji yayi kamar almara hakan yasa saida suka shiga mota ya rufe ido na d'an wani lokaci, yana bud'ewa ya saki murmushi yana fad'in "Alhamdulillah Allah, Allah kaine Allah, ina godiya abisa ni'imominka a gareni." Aifa ranar Zuby na jikin Umar Faruk, duk da masifar shagwab'a da kukan da take haka ya taushe ya had'iye, a ranar ko saida safe bata bari yama duka muten gidan ba bare kuma Khairat, Khairat kam ganin shiru yasa ta maida hankali ga tilawar karatunta, amma fa da taga dare yayi sosai kuma ta tabbatar ba zai shigo ba saida ta zubar da hawaye, a haka asuba tayi saida ya samu ya dawo daga masallaci kad'ai ya wuce d'akin Khairat har safiya tayi, yana shiga ya sameta kwance akan kujera da littafin *Hisnul muslim* tana karanta addu'o'i, a wahalce ta tashi zaune tana fad'in, "Sannu da zuwa." "Yawwa sannu." ya fad'a yana zaunawa kusa da ita, kallonta yayi yace "kin tashi lafiya?" "Lafiya lau." ta fad'a a tak'aice, janyota yayi jikinshi yace "yadai, me yake damunki." "Ba komai." Tashi tayi zaune ta kalleshi tace "Faruk, da zuciya d'aya nake zaune da kowa a gidan nan, zan iya sadaukar da komai nawa dan taimakawa marar k'arfi, amma duk da son taimakona a gaskiya bana son sata, bansan tayaya sarqata ta shiga hannun mahaifiyar matarka ba, amma dai nasan ta sameta ne da taimakon wani na kusa dani, ma'ana wanda yake cikin gidan nan, ni nasa aka maka wanda ya d'auka min sarqar, amma gaskiya da farko bansan ita bace." Katse mata magana yayi da "da kuma ki kasan itace me ki kayi?" "Banyi komai ba." "Ai kuwa na d'auka za kisa a fitar da ita ne ,kodan matsayinta a gareni." "A'a Faruk, ina so nasan yanda ta samu, dan nasan b'arawona, hakan na nufin akwai mai son cutar dani, ba kuma zan lamunci hakan ba." Gyara zama yayi yana kallonta yace "dan Allah Khairat kiyi hak'uri kisa a fitar da ita basai kowa yaji ba, na miki alk'awarin hakan ba zata sake faruwa ba insha Allah." Tsaye ta mike ta aje littafin hannunta tana fad'in "kayi hak'uri, gaskiya ba zan iya ba, dole nasan meya faru, kuma fa maganar milyoyin kud'ad'e ake, taya kake tunanin zanyi wasa haka." Shima tsaye yayi yace "kenan kina so kice ba zaki iya fito da ita ba?" "Eh, haka nake nufi." ta fad'a ba tare data kalleshi ba. "In kuwa hakane baki cika masoyiyar gaskiya ba, na dauka zaki iya yin komai saboda ni, ashe ba haka bane." Yana fad'a ya fita ya bar d'akin, ko kallonshi ba tayi ba itama taci gaba da harkokinta, shiryawa tayi bata kula kowa ba itama ta tafi office danta samu salama, taji dad'in tafiya domin ta manta da duk wasu matsaloli, sai dai damuwar d'aya shine rashin zuwan Umar Faruk aiki, da yamma ta fito dan tafiya gida amma motarta tak'i tashi, kiran Umar Faruk tayi a bugu d'aya ya d'auka, nanta fad'a masa abinda ke faruwa, saida ya shiga gida ya d'auko makullin motarshi danya tafi d'aukarta, Zuby ce ta shagwab'e sai dai ya zauna bata so ya fita, ganin ba zata barshi ya tafi ba yasa yace sutafi tare. Koda suka isa Khairat bata damu ba tunda yau ba itace dashi ba, gidan baya ta bud'a ta zauna lokacin har mai gyara yazo duba motarta, suna fara tafiya tace "sannunku." Umar Faruk kad'ai yace "sannu, ya aiki? kinga yau banzo ba ko?" "To ai naga amarci kake ci har yanzu." Karaf Zuby tace"bai kai yaci amarcin bane kome?" Ajiyar zuciya kawai ta sauke, tsaki tayi ita kuma tana habaice habaice har tana fad'in "wataqila itama tana kurb'awa kamar gyatuminta." Murmushi Khairat tayi tace "zanyi farin ciki ace kurb'awa nake, koba komai shan giya sai mai kud'i, amma halin b'era, ina fatan Allah yamin tsari dashi." Zuby zatayi magana Umar Faruk ya daka mata tsawa yace "karki sake naji bakinki, wallahi idan na sake jin makamancin haka a tsakaninku har takai ga sanya iyaye, wallahi zaku gane kuskurenku." Qwafa yayi mai k'arfin gaske, shiru sukayi suka ci gaba da tafiya, daf da wani babban shago Khairat tace "dan Allah baby inba damuwa ka ajeni nan zan duba wani abu." D'an qaramin tsaki yayi yana paka motar yana fad'in "bana so magrib ta sameni akan hanya." "Ba zan jima ba baby." Ganin Zuby na kallon shagon yasa yace "ko kema zaki shiga?" "Eh, madara nake so." ta fad'a cikin shagwab'a. Hannu yasa ya shafi sumar kanshi sannan ya bud'e murfin yace "fito muje." Fita sukayi suka rufawa Khairat baya, a tare suke duba kayan yayin da Khairat keta cika kwando da kaya, suna gamawa suka zo wajen biyan kud'i, ana lissafi kayan daga baya sukaji ance, "Hajia Khairat." Juyowa tayi amma wanda ta gani yasa mamaki ya bayyana a fuskarta fal, da farin ciki ta nunashi tana dariya tace "Alhaji.... 20/08/2019 à 14:26 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 4⃣9⃣ "Alhaji Bala, kaine?" Cike da girmamawa ya matso inda take ya sunkuya yana gaisheta "Hajia ina wuni." "Haba dan Allah ka tashi mana." "Haba Hajia, aini ba butulu bane, wallahi uwata kad'ai nafi girmamawa a duniyar nan kafin ke, duk da dai nasan nayi laifi, amma ina neman afuwa Hajia, ke babbace kina bawa komai baya komai girmanshi, musamman ga irinmu talakawanki." "Alhaji Bala, matsalata dakai fa kenan, wasa mutum da kurantashi, to ya kwana biyu ya iyali?" "Lafiya qalau Hajia, ya harkoki ya kuma fama damu?" Bata amsa ba sai nuna masa Umar Faruk da tayi tana fad'in "am Bala, ga mijina nasan baka san nayi aure ba, ga kuma yar uwata abokiyar zamana." Hannu Umar Faruk ya mika masa amma saiya nemi zube gwiwoyinshi qasa danya gaisheshi, da sauri ya rik'eshi yana fad'in "haba haba, ya haka kuma? kaifa babbane." "Barni Alhaji na gaisheka, aiko karen Hajia Khairat dole samu girmamawa daga gareni, bare kuma kai mijinta." Cikin jin haushi Zuby ta juyo danta fita daga wajen, idonta ne ya sauka kan Alhaji Bala, wucewa tayi dan bata sanshi ba shi kuma ya santa farin sani, binta yayi da kallo harta b'acewa ganinshi, hannu Umar Faruk ya ya sake bashi suka gaisa sannan sukayi sallama, ledojin ya d'auka harda na Khairat ya wuce dan yau dad'i yake ji ya mata hidima, kallon Alhaji Bala tayi tace "mu zamu wuce, sai kwana biyu." "Am Hajia." ya fad'a a hankali. Kallonshi tayi shi kuma ya d'ora da "Hajia ki kace waccen abokiyar zamanki ce?" "Eh." ta fad'a a tak'aice. Shiru yayi yana girgiza kai, da mamaki tace "lafiya ko, kasanta ne?" Shiru yayi yasa babbar rigarshi ya shafe zufa, d'an hararanshi tayi tace "He Bala, nasanka fa, ka fad'a min gaskiya, kardai itama tana cikin yan matanka." A tsorace ya kalleta yace "A'a Hajia , wallahi na jima da daina wannan harkar, wannan d'in indai sunanta Zubeida kuma ya ga Asma'u, to tabbas *d'iyata ce*." "Me, 'yarka fa, tayaya?" "Kamar yanda kika sani bana iya b'oye miki komai, domin kuwa badan taimakonki ba da yanzu ina bara akan titi, wannan da kika gani 'yata ce ta cikina, kuma bata hanyar aure muka sameta ba." Bai qara komai ba daga hakan, kuma itama bata tambayi komai ba suka rabu, a mota kallon Zuby kawai take tana mamaki, Zuby kam cikin rawar kai tace "da auranka ma saika nuna halin, wannan jaraba dame..." Bata qarasa ba Umar Faruk ya taka burki da k'arfi yana harara, cikin zare ido yace "wallahi tallahi zan zubar miki da hoqoran gaba, kinji dai na rantse ko? tom." Tayar da mota yayi suka d'auki hanya, duk da haka Zuby bata daddara ba suna daf da shiga gida saida ta bangaji Khairat da k'arfi ta wuce, bugu da qari ta d'ora da "yar mashayi kawai, in banda qaddara me zai had'ani had'a kafada dake." Yanzu kam Khairat takai maqura ba zata iya jura ba, kamar mai tab'in hankali haka ta zubar da kayan hannunta ta shak'o wuyan Zuby, kafin ma Zuby ta fahimci meya faru Khairat ta dasata a qasa tabi kanta da duka , ihu ta fara tana kiran sunan Umar Faruk dake gyara parking d'in mota, sosai Khairat take bugun bakinta harya fara fitar da jini, gashi girman jiki ba d'aya ba ta kasa qwatar kanta, jin kururuwa ne yasa mutanen dake d'aki duk suka firfito, da azama kowa yayi soro ya fara qoqarin rabasu, lokacin kuma Umar Faruk ya shigo, sosai ta rik'e rigar Zuby harta keta mata rigar, janyota Umar Faruk yayi a lokacin Zuby itama ta rik'e rigarta sosai, hakan yasa zip d'in rigar cirewa har rigar ta zame daga jikinta, ganin haka yasa mazan wajen komawa mafakarsu suka bar mata, cike da takaici da b'acin rai Umar Faruk ya fizgi hannun Khairat daga wuyan rigar Zuby yana fad'in "ba zaki saketa ba?" "Ba zan saketa ba, wallahi saina ci uwar yarinyar nan, akan me zata rainani, ni tsararta ce?" duk tayi maganar nan cikin neman d'aukewar numfashi. Duk maganganun da mutanen wajen keyi ko jinsu basuyi, da k'arfi ya b'abb'are hannayensu ya nuna Zuby yace "wuce ciki." Juyawa tayi tana kuka tana d'yangasa qafa tana tofar da jinin dake bakinta, Khairat ma a tsawace yace "maza wuce ciki." A hassale ta qarasa zame rigarta ta jefar ta wuce nata kewayen, zaune tayi akan kujera saboda makullin na cikin jaka kuma ta jefar da ita, Zuby na kaiwa qofar d'aki ta durk'ushe tana dafa ciki tana qara tsananta kukanta, da sauri kuma sukayi kanta ana tambayar lafiya, Mama ce da Saratu suka kamata danta shiga ciki, sake lanqwashewa tayi tana dafe ciki, Mama Sa'a ce ta kalli Umar Faruk tace "Umar Faruk tana da ciki ne?" Kai kawai ya d'aga mata alamar eh, Mama Maimuna ce ta qara da "Allah yasa dai ba b'ari za tayi ba." Jin haka yasa Zuby sake fashewa da kuka tana kiran cikinta cikinta, a hanzarce yace "to Mama mu tafi asibiti mana." "A'a bari dai mu gani." cewar Mamanshi, d'orawa tayi da "bud'e mana d'akin." Umar Faruk d'in ne ya bud'e musu d'aki suka kwantar da ita akan gado, duk wannan murqususus da take har yanzu shiru ba alamar jini ko wani abu, da qyar suka rarrasheta tare da bata baki, sannan Mama ta dora "in ki kaji wata matsala kiyi sauri ki fad'a masa kinji." Bata amsa ba su kuma suka kama bansu, tashin hankali Umar Faruk ya ganshi a daren nan, kuka kawai take tana fad'in cikinta, sam bata barshi yayi bacci ba, kuma duk kururuwar nan da take akan kunnan Khairat dake cika tana batsewa, duk yanda taso tayi banza dasu abin ya gagara saida ta zubar da hawayen bak'in ciki ,itama dai ba tayi wani bacci ba sai karatunta data kwana tanayi. Tunda asuba Zuby ta fahimci illar da Khairat ta mata, kallon kanta tayi a madubi taga yanda bakinta ya kumbura, ga masifar ciwon da hannunta keyi ko motsashi bata son yi, a haka Umar Faruk ya dawo daga masallaci ya sameta ba tayi sallah ba, nuna mishi hannun tayi yana gani ya kece da dariya yace "wallahi gotaki tayi, kawo na gyara miki." Cike da jin haushi ta bashi hannu danya gyara mata, amma yana tab'awa ta fara ihu da kururuwa tana qwaqwumeshi, taji jiki sosai yayin da Umar Faruk yaki sakin hannun har saida ya gyara mata dan gwanine a wannan fannin , hawaye majina da yawu babu wanda bata had'a ba, saida ya shafa mata magani kafin ta kwanta na d'an lokaci shi kuma ya fita gaishe da iyayensu daga nan ya wuce d'akin Khairat. Tsaye ya sameta gaban madubi tana shiryawa, dan wajen aiki take so ta tafi da wuri dan zaman gidan Umar Faruk ya fara fitar mata akai, sam akwai abinda ba zata d'auka ba ko daga wajen Umar Faruk d'in ne bare banzar matarshi, a daqile ta amsa sallamarshi ba tare data kalleshi ba, takawa yayi har yaje inda take ya kwanta akan bayanta wanda Allah ya wadatashi da tarin nama, hannu yake kaiwa cikin rigarta yana tattausa ko ina na jikinta yana sauke numfashi, yayin da wata sabuwar kewarta ke qara mamayeshi, shiru ta masa tana ci gaba da shirinta harta juyo da nufin d'aukar d'an kwalinta ta d'aura, janye jikinta tayi daga nashi ta d'auki d'an kwalin ta d'aura ta d'auki hijab ta saka, jakarta ta d'auka tasa takalmi zata fita ta rik'e hannunta, marairaicewa yayi yace "bako gaisuwa, me yayi zafi haka, kuma ina zaki je da safiyar nan? koni gani a gida ban fara shirin fita ba saike." "Saboda kana da qarancin abinyi ne shi yasa, ni kuma akwai abubuwa masu mahimmanci dake gabana wanda suka fi zaman haka." Janyota yayi ta fad'a qirjinshi Kutsawa yayi cikin hijabint ya manna kanshi a tsakiyar wuyanta yana sumbata, qoqarin fito dashi ta fara yi amma ya cije, jin ya fara birkicewa har yana neman zare mata rigar yasa ta turoshi da k'arfi ya fad'a kan gado, gyara jikinta tayi zata wuce ta kalleshi tace "Khairat fa ba tayi shiryuwar da zaka raina mata hankali ba, ina da 'yancin da zan iya qwatarwa kaina 'yancina da kaina, kuma wallahi ko kaine ka d'aukar min abu zan iya nuna maka b'acin raina, kamar yanda ko kai ka b'ata min ba zan gagara nuna maka hushina ba." Banka masa harara tayi ta wuce abinta, wani irin iska ya furzar yana jin ba dad'i, tashi yayi ya koma d'akin Zuby ya samu tana bacci , shiryawa yayi shima kawai yabi bayan Khairat ba tare damu daya tashi Zuby ba, abin mamaki da d'aure kai shine, umarni da Khairat ta bawa Habeeba kan cewar bata son ganin kowa, kuma haka akayi Umar Faruk ma yazo ganinta Habeeba tace yayi hak'uri Hajia tace tana aiki, bai wani ja da tsayi ba dan yasan jiya ta dawo Khairat d'inta, kuma zai iya jawa Habeeba matsala a nata aikin inhar ya shiga da k'arfi, haka ya koma ya zauna mazauninsa ya kasa yin komai sai tunani da rashin walwala, abinda ya qara d'aga maishi hankali shine har suka tashi kowa ya kama hanyar gida Khairat bata fito ba, wacce bata iya rabin wuni a wajen, saida yaga har Habeeba ta tafi sannan ya nufi office d'in nata. K'ofar rufe take dan haka ya dinga bubbugawa yana kiran sunanta, saida ta gama had'a kayanta zata fita tazo ta bud'e k'ofar, yana shiga ita kuma ta fito ta kama hanya, da gudu ya biyota kamar wani matashin zaki ya tari gabanta, yanda suka had'a ido yasa ya d'auke idonshi daga kallonta, wani tartsatsi yaji da rabon daya jishi tun zamanin shed'an na d'an qauye , ma'ana tun tana Khairat d'inta ta ainihin, kasa magana yayi ya kuma kasa kallonta, rab'ashi tayi ta wuce abinta tana fita ta shiga motarta ta kama hanyar gida a lokacin ana sallah magrib. *Muje da sauri 'yan uwa* A kwana biyu abubuwa sun faru, daga ciki akwai jinya da Zuby tayi da kuma zuwansu Zulfa'u gidan, sunzo suka tayar da hayaniya akan cewar sai sun d'aukar mata fansa, ganin basu samu wannan damar ba yasa suka ce zasu kai qararta, duk ban maganar da Umar Faruk ya dinga yi basu ji ba, har saida ya fad'a musu itace tasa aka kama Mama, kuma in suka kai qararta tofa magana zata iya yin girman da ba za'a iya tsayar dashi ba, sai lokacin sukayi shiru da bakinsu suka bar maganar qararta, a kwanankin nan aka hana kowa ganin Mama dake d'aure wacce wahalar duniya ta isheta, kuma a kwana biyun nan Umar Faruk ya had'a Khairat da Zuby ya musu qwaqwaran kashedi, ya kuma fad'a musu zai iya rabuwa da kowace in suka sake mishi tashin hankali a gida, kuma yaja kunnan Zuby sosai aka fita harkar Khairat, ya kuma nuna musu rashin jin dad'i akan haka sosai, a lokacin ne Khairat tace, "Ka fad'a mata ta daina aibatani, wani yana da asali na qwarai, amma wani asalinshi ko waiwayarshi ba'a so ayi, kace ta bini a sannu inhar bata so na b'allo mata ruwan da ba zata iya taresu ba, wallahi wallahi tayi wasa saina tona mata asiri kuma na tonawa mahaifiyarta, mummunan aikin da mahaifiyarta aikata shekarun baya, to ni nan Khairat zan fallasa wannan ajiyayyan sirrin marar dad'in ji, tana wasa dani sosai kuma tana yawan fad'an bak'ar magana akan mahaifina, ni ba zan raina asalinta ba duk da nasan ita wacece, amma dai taci gaba da harzuqani to zata tsinci kanta a wahalalliyar rayuwa, tana wasa da ajina, bata san matsayi da girmana ya wuce duk inda take tunani ba, idan naso yanzun nan zan iya canza miki wajen zama, ba kuma wajen zama kad'ai ba harda sunan uba ma." Tana fad'a kuma ta koma d'akinta ta barsu cike da juyayin maganganunta... Umar Faruk ne ya kalli Zuby yace "kin gani ko, kinga abinda halinki ya ja miki, Zuby kin kasa gane cin zarafin mutum ba dad'i bare kuma iyaye, baiwar Allah nan ko kallonki ba tayi ba tare da dalili ba, amma ke kullum burinki kici zarafinta, ire irenku ne kuke saka wanda suka tuba su koma ga ci gaba da aikata laifukansu na baya, kuma irinku kuke saka wanda ba musulmi ba shakku da tamtama akan ya shiga addinin ko karya shiga, na tabbata mahaifinta yayi tuban gaskiya, amma ke sai tozartata kike ta hanyar anfani da kurakuran mahaifinta na baya, kin manta da cewa d'an adam ajizinie, yanzu gashi bakinki yaja miki kinci dukan tsiya harta kaiki ga jinya, abinda nake so na fad'a miki yanzu shine, Khairat ta dage ba zata saka a saki Mama ba har saita san yanda akayi ta samu sarqar, bana zarginki , amma dai ina fatan Allah yasa babu hannunki a ciki, dan in haka ta faru a gaskiya zanji kunya, dan ko babu aure a tsakaninmu, mu yan uwane na jini, dan haka abinda ya shafeki ya shafeni, kuma inya tabbata akwai hannunki a ciki babu abinda zan iya yi miki, dan maganar milyoyi ake, ni kuma ba zansa kaina a matsala ba saboda haukanki, gashi yanzu kinsha shegen duka a banza a wofi saboda shegiyar masifarki, ina fatan zaki kiyaye gaba." Cikin kukan iskanci ta fara magana "lallai ma yah Umar, yanzu duk da abinda tamin amma ba tayi laifi ba?shine zaka d'ora min laifi, shikenan na gode." D'akinta ta koma tana tunanin mafita akan Mama, shima d'akin Khairat ya nufa dan yau yana d'akinta ne, samunta yayi ta juya baya ta yanda baya iya ganin fuskarta, da alama har tayi shirin kwanciya bacci ne danta rufe da zanin rufa, saida yayi wanka yayi shirin kwanciya kafin ya haura kan gadon, jikinshi ne ya bashi akwai matsala dan tunawa da yanda Khairat ke tarbanshi idan ya shigo d'akinta, tabbatarwa da yayi ba za'a iya rik'e kanshi ba yasa ya rumgumeta ta baya yan shinshinar k'amshinta, shiru tayi kamar mai bacci sai dai tana ji kamar hawaye zasu taho mata, juyowa yayi da ita ya fara sumbatarta, tureshi tayi daga jikinta ta tashi zaune, a raunane ya kalleta yace... "Haba baby, laifin me nayi kike min wannan hukuncin? na dauka ban cancanci haka daga gareki ba." Cikin d'aure fuska tace "wannan shine *kuskuren da nayi*, ba kuma zan sake maimaitashi ba." Hannunta ya kama ya rik'e yana sumbata yace "amma ai bana da laifi ko, me yasa za'a zab'i hukuntani to?" "Baka da laifi kake cewa? taya za kace baka da laifi, bayan kana magana na fito da surukarka daga magarqama, bayan kana jin irin iskancin da matarka take min amma ban tab'a ganin ka d'auki matakin daya dace ba, kuma a hakane kake cewa baka da laifi." Saida ta mayar da hawayen da suka zubo mata sannan tace "naji ni mahaifina yana shan giya kuma yana neman mata, amma ai yanzu ya daina kuma ya tuba ga Allah, duk da haka ina son mahaifina kuma ba zan lamunci cin zarafinshi ba a gabana, kuma ko yanzu ta fad'i bak'ar magana a kanshi, wallahi saina karyata." Juya mishi baya ta sakeyi ta kwanta ta rufe, lalabarta ya fara yi amma ta juyo ta nunashi da hannu tace "bana so ka takura min, raina a b'ace yake har yanzu." Cikin rawar murya yace "K..ha..ira...t, dan Allah karki min haka a wannan lokacin, Khairat ina neman taimako da tallafinki, wallahi zan iya shiga wani hali in ki kak'i kulani, dan Allah Khairat." Banza tayi dashi haka ya dinga lallab'a amma ta shereshi, sam kasa bacci yayi ya fara karatu amma ya cije mishi, sai daf da asuba ya kabbara sallah ana kiran sallah kuma ya nufi masallaci, itama tana gama sallah d'akin Mama taje Ruk'ayya ta d'ora mata karatunta, suna gamawa ta fito ta shiga d'akin Mama Maimuna sa Mama Sa'a ta gaishesu, zata shiga kewayenta Zuby ta fito daga d'akinta da kumburin hannu har yanzu bai gama warkewa ba, tsaki taja tace "aikin kawai, sai iyayi da kurin tsiya kamar ba *Jihadi* akayi ba aka aureki." Cak Khairat taja ta tsaya tare da juyowa ta kalleta, yayi daidai da shigowar Umar Faruk tare dasu Abbakar Aliyu da Usman, kasa tausar zuciyarta tayi saida hawaye suka wanke mata fuska, kallon Umar Faruk tayi ta d'an matso kusa dashi tace "Faruk, kai ka fad'a mata Jihadi ne kayi ka aureni?" Kai ya girgiza mata yace "karki saurareta Khairat, kema kinsan ba zan tab'a fad'a mata haka ba, kawai tana so ta b'ata miki rai ne." Jin haka yasa Zuby jin dad'i tace "kai yah Umar kaji tsoron Allah, yanzu ka manta da abinda ka fad'a min jiya kafin ka shiga d'akinta? tabb'." Ta fad'a tare da tab'e baki, matsawa yayi Faruk yayi wajenta zaiyi magana saisu Mama suka fito, Baba ne shima yace "me yake faruwa ne kuma?" Karaf Zuby tace "jiya nefa yace min shi jihadi yayi ya auri Khairat, daga na fad'a yanzu shine kuma yake cewa qarya nake yi." Jin abinda ta fad'a kowa ya fara tamtama akan abinda ta fad'a, Khairat da kuka ya qwace mata ne ta matso kusan Umar Faruk tace "dan Allah Faruk ka sakeni, ka sakeni na koma gidanmu, wallahi ba zan iya jurar wannan wulaqancin ba saboda ban saba ba, da nasan *jihadi* kayi ka aureni wallahi da ban shigo gidanka ba, dan Allah ka sakeni." Rud'ewa yayi ya rik'o hannayenta yace " Khairat karki yarda da abinda ta fad'a, wallahi bana daga cikin irin wannan mazan, ban tab'a magana mai kama da wannan ba da ita, Khairat ba zan iya sakinki ba." Fizge hannayenta tayi cikin daga murya tace "qarya kake, ba zan sake yarda dakai ba Faruk, kai mugu ne azzalumi kuma marar adalci, wallahi na tsaneka na tsani ganinka, ba zan tab'a yafe maka ba abisa cutar dani da kayi." Juyawa tayi da k'arfi zata shiga d'aki taji muryar Usman yace "kar kiyi haka kema, inhar za abi maganar gaskiya ai Umar Faruk jihadi yayi, amma kuma na tabbata bashi ya fad'a mata haka ba, kawai tana son rabaku ne." Murmushin takaici tayi tace "ok , amma ai idan bai fad'a mata ba ai kai ya fad'a maka, tunda gashi ka sake maimata min jihadi yayi ya aureni." Zata wuce Umar Faruk ya rik'o hijabinta, juyowa tayi a hankali ta kalleshi saita ganshi akan gwiwoyinshi yana zubar da hawaye, kasa magana yayi saboda tafarfasar da zuciyarshi keyi, haushi ne ya kama Ruk'ayya saboda soyayyar dake tsakanin 'yan uwa, rufe ido tayi ta matso kusanshi ta raba hannunshi da hijabin Khairat ta d'agashi tana fad'in "ka barta ta tafi mana yah Umar, saime, zaka kasa rayuwa ne? ai kowa yasan jihadi kayi ka aureta , dan babu wanda zai iya auren macen da namiji hud'u suka yiwa fyad'e." Kallonta Khairat tayi sosai hawaye na safa da marwa a fuskarta, juyawa tayi ta wuce d'akinta Umar Faruk kuma a hassale ya d'auke Ruk'ayya da mari, sannan ya juya ya kalli Usman yace "ba dan ka sulhunta tsakanina da ita ba ka fad'i abinda ka fad'a." Zuby ya nuna da hannu yace "kin jima kina yimin abinda ki kaga dama ina qlayeki, kiji da kyau, wallahi Khairat ta bar gidan tare zaku fita, bawai saboda sonta da nake ba sai dan qazafi da qaryar da kika min." D'akin Khairat ya nufa yaci karo da ita da akwatin kayanta ta zubo wanda ya sawwaqa, rik'e akwatin yayi yana fad'in "dan Allah Khairat karki tafi, wallahi tallahi babu wanda na tab'a fad'a ma haka, rabamu kawai suke so suyi." Mama ce ta qarasa inda suke itama cikin taushin murya tace " 'yata, kiyi hak'uri dan Allah karki sauraresu, babu gaskiya a cikin wannan maganar na tabbata." "Mama, bana so kiga rashin kyautatawata , dan Allah ki barni na tafi." "A'a Khairat, haka bai dace ba, dan Allah kiyi hak'uri ki koma d'akin mijinki." Baba ne ya matso shima yace "ki koma d'akinki kinji, zan daidaita komai." "Kuyi hak'uri, ba zan iya zama ba gaskiya, indai har canzi gaba da zama dashi, to zan dinga jin kaina a matsayin wacce ta kasa samun mijin aure, saida Umar Faruk ya taimaka yayi *jihadi* ya aureta, kusan kowa da abinda yake kira da jihadinsa, amma aurena shine *Jihadi* _Umar Faruk_." Fizge jakarta tayi ta wuce abinta, motarta ta shiga ta wuce gida tana kuka, daga nan Umar Faruk yace Zuby ma ta had'a ta bar mishi gida ba zai iya zama da ita ba tana mishi haka, Baba ma baiji dad'i ba shi yasa babu ma wanda bashi hak'uri, itama tana kuka ta had'a yan kayanta, zata fita Mama ta tausaya mata tace ta koma d'akinta da zama, saboda Mamanta ba tanan kuma gata da cikinshi, taji dad'in haka sosai da haka take jin basu rabu ba tunda dama ba sakinta yayi ba. ************** A gigice su Mamie ke tambayarta amma ta kasa magana sai kuka, kiran Papa Mamie tayi yazo shima saida yayi lallab'a da dubara ta fad'a masa abinda ya faru, a take Mamie da Mammie suka fahimci kawai sharrin kishiya ne, nan suka dinga bata magana tare da sake koya mata wasu sabbin salon na shanye makircin kishiya kowace iri ce ,sannan suka ce ta koma gidanta, nanfa tace ba zata koma ba ita ba zata sake zaman gidanshi ba, zuwa yamma kanta ya fara mata azababben ciwo, gashi kuma maganinta na can gidan. ************** Umar Faruk nayin sallah la'asar ya d'auki makullin mota ya nufi gidansu tare da Baba, Papa ne ya tarbesu a masaukin bak'inshi, bayan sun gaisa malam ya fad'a mishi abinda ya kawosu, cikin nuna dattako Papa yace "ba komai malam, dan kunyi saurin zuwa ma dani zan mayar da ita da kaina, amma ku jira ni zan taho muku da ita insha Allah." Takalmi Papa yasa ya tunkari d'akin Khairat yana tunanin rage mata daular da take samu, dan yana ganin kamar harda sakewar da take samu yasa haka, yana shiga d'akin ya sameta kwance, a tak'aice yace "tashi ga mijinki nan yazo ki tashi ku tafi." Tashi tayi zaune tace "a'a Papa babu inda zanje, kawai kace ya tafi ni bana son ganinshi." Rai had'e Papa ya kalleta ya tara mata hannu yace "ban makullin motarki." "Motata kuma?" "Eh." "Amma Pap...." tswar daya mata yasa tayi shiru, d'orawa yayi da "ki bani makullinki kuma ki tashi ki wuce." Mamaki ne ya hanata magana, dan ko a mafarki haka bata tab'a faruwa ba, tashi tayi a hassale ta fita daga d'akin ta sauka qasa, fitowa Papa yayi ya musu magana sannan suka wuce tare suna godiya, Khairat kuma kamar zata qurma ihu komai ya mata zafi har suka kai gida..... 20/08/2019 à 14:26 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣0⃣ Bayan tafiyarsu Mamie take fad'awa Papa batun b'atan sarqarta da kuma kama matar, cikin b'acin rai Papa yace "yanzu yarinyar nan har takai matsayin da zata iya sakawa a d'aure mutum kuma ma mace, to ba zan d'auki wannan iskancin ba, jiya ba yau bace dan haka gobe nan zansa a fitar da ita." Yana komawa d'akinshi yasa aka kulle duk wani asusun baki da Khairat ke dashi, bawai dan wani abu ba sai dan ta d'and'ana rayuwar rashi hakan zaisa ta qara hankali, haka ma ya kira manager da accountant ya gargad'esu, duk da ayukan da suka masa yawa yayi qoqari ya d'orawa kansa wani nauyin, ta yanda babu sisin kwabon da zata fita daga ma'aikatar ba tare da saninshi ba, da haka kuma yake burin ganin gobe. *************** Zuby na k'ofar d'akin Mama su Khairat suka shigo, baki bud'e take kallonsu harta shiga d'akinta, rufe baki tayi tace "jaraba ba zata rabu dashi ba cikin sauk'i." Khairat na shiga d'aki ta d'auki maganinta tasha na ciwon kai sannan ta kwanta, ganin tak'i kulashi yasa ya fita daga gidan, bai dawo ba saida yayi sallah isha'i, a lokacin suka shigo tare da Ruk'ayya da Mama, sallama sukayi ta amsa tare da cewa "shigo." saboda taga babu wanda ya shigo. Shiga sukayi da wata sabuwar sallama, zaune sukayi akan kujera Umar Faruk kuma akan gado, Mama ce tace "Khairat, nazo na sake baki hak'uri ne akan abinda ya faru, kiyi hak'uri kinji, insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba." Zaune tayi bakin gadon ta kalli Mama tace "Mama ba komai, komai ya wuce ai tunda gani na dawo." Wani kallo da tabi Ruk'ayya dashi yasa cikin Ruk'ayya murd'awa, a hankali ta sauka daga kan kujerar ta durk'usa ta rik'e rigar Khairat tace "dan Allah aunty Khairat kiyi hak'uri ki yafe min, wallahi ba nayi haka ba danna tozartaki ba, raina ne naji baimin dad'i ba da naga yah Umar na kuka, amma wallahi ina sonki aunty Khairat kuma ina son zamanki da yah Umar, dan Allah kiyi hak'uri." ta qarashe da fashewa da kuka. Allah sarki Khairat da taushin zuciya, hannun Ruk'ayya ta kama ta zaunar da ita kusa da ita tace "shikenan Ruk'ayya, komai ya wuce, ban fahimceki bane da farko saboda bana da d'an uwa ko 'yar uwa, amma yanzu da kika fad'a min na fahimta, ba komai wallahi." Ruk'ayya ce tasa hannu ta share mata hawayen da suka zubo mata tana fad'in "dan Allah aunty ki daina kuka, wallahi ni daga yau ma na koma qanwarki, bani ba yah Umar zan d'aukeshi a matsayin mijin yayata ne kawai, kin amince?" Ta fad'a tana nunata da hannu, murmushi tayi da yasa hawaye suka qara zubowa tace "Ruk'ayya waye zaik'i d'an uwa, da ina ni kad'ai yanzu kuma na samu qanwa." Tashi Mama tayi ta fita tana goge qwalla dan wani irin tausayin yarinyar taji sosai har zuciyarta, Umar Faruk kusan qwallan yayi yayin da qaunarta ke qara ratsashi, fita yayi ya barsu Ruk'ayya kuma ta gyara mata kayan da suka zube a lokacin da take shirin tafiya gida, sunayi kuma suna hira har Khairat ta fad'a mata zata fara zuwa wajen koyan girki, da farin ciki Ruk'ayya tace "gaskiya kam aunty Khairat ya kamata, kuma kinga nima munyi magana da Mama akan zan shiga, amma tace na bari har aurena ya taso saina fara zuwa." "Ah haba, indai kina so kawai kishirya gobe muje muji yanda abubuwan suke." Shiru tayi ba tayi magana ba, tana mamakin hali irin na Khairat, katseta tayi da cewa "ki shirya kinji, zan miki magana." "To." ta fad'a cikin sanyin jiki, ta jima sosai suna hira har saida taji sallamar Umar Faruk sannan ta mata saida safe, yana shigowa kayanshi ya cire ya shiga wanka, koda ya fito yana shiryawa Khairat itama ta shiga wankan, cikin doguwar rigar bacci ta shirya mai kyau fara tas sannan ta kwanta, kallon qeyarta Umar Faruk yayi danta juya masa bayane , cikin taushin murya yace "Khairat, kiyi hak'uri abis....." "Ya isa haka, nace komai ya wuce." ta katseshi, murmushi yayi ya d'ora kanshi a tsakiyar wuyanta yace "indai hakane me yasa zaki bawa mijinki baya, kin manta hakan babu kyau?" Juyowa tayi ta sauke idonta a kanshi tace "to na juyo, hakan yayi?" Murmushi ya sake yi yakai bakinshi a hankali zai sumbaceta, da sauri tasa hannunta tsakiyar bakinsu, b'ata rai yayi yana kallonta, ba alamar wasa tace "kayi hak'uri Faruk, bana so ka sake neman wani abu a gareni, dan ba zan iya baka ka, ina ji har yanzu kamar ban cika cikakakkiyar mace ba, domin kuwa ana kallona a matsayin wacce ka taimaka." Janye hannunta yayi yana kallon qwayar idonta yakai bakinshi a hankali harya had'e bakinsu, saida ya gaji da tsutsa ya saki ya kalleta da idonshi harsun canza kala yace "ki bani dama ta qarshe na nuna miki kece wacce zuciyata take so, dama d'aya tak nake so ki sake bani Khairat, ni kuma zan nuna miki matsayinki a wajena ya wuce yanda kike tunani." Kallonshi kawai take da ido ta kasa magana, ganin haka yasa ya sake lulawa da ita wata duniyar, saida ya jima yana lashe ko ina kafin ya fara shirin gangarawa , kallon fuskarta yayi cikin siririn haske daya bayyana a d'akin, yana ganin yanda ta rintse ido sosai hawaye na zubowa ta kama damtsenshi sosai ta rik'e, yana danna kai ciki ta saki wata tausassan qara, harshenshi yasa ya dinga lashe hawayen fuskarta yana ci gaba da daidaitawa kansa zama, numfashinshi na fizgarshi yana neman shid'ewa sai hawaye dake zubo mishi yana qara matseta a jikinshi sosai yana sauke numfashi da qyar, tausayinta ne ya sake kamashi ganin kullum sai taji wannan azabar, kuma har yanzu ya kasa gane dalilin haka, kuma har yau yana mamakin yanda bata bud'ewa. Bakinshi yakai a kunnanta yana fad'in "Allah ya miki albarka alkairina, Allah ya biyaki da gidan aljanna, Allah ya tashemu a aljannatul firdaussi, ina sonki Khairat, ina qaunarki Khairat, wallahi ba zan iya rayuwa babu ke ba, Khairat ki tausaya min karki kasheni dan Allah, wallahi ina so na zauna dake har qarshen rayuwata, Khairat ki fad'a min abinda kike so a duniyar nan, ni kuma nayi alk'awarin yi mikishi ko menene a duniyar nan, Allah ya saka miki da alkairi baby." 😎😎😎 *Ba magana* ****************** Shiryawa Khairat tayi tace ma Umar Faruk "nida Ruk'ayya zamu je wani wuri, ina neman izininka." "Wani wuri bashi da suna?" ya fad'a yana tsefe sumar kanshi. Matsowa tayi kusa dashi tace "da zaka taimaka saika ajemu , tunda motata na gida." Juyowa yayi yana kallonta yace "muje to." juyawa tayi zata wuce ya janyo hannunta ta fad'a jikinshi, rumgumeta yayi tare da sumbatar kanta, wani numfashi yake saukewa ido lumshe yana tuno....jiya (kun gane ai), d'agota yayi daga jikinshi ya kalli fuskarta yana dafe kumatunta yace " ina qaunarki *bugun zuciyata*." Kallonshi kawai tayi ta janye jikinta daga nashi ta fita, bayanta yabi ita kuma tama Ruk'ayya magana suka tafi tare, akan hanya ya nuna mata aikin daya fara na d'aya compagnie sai dai baiyi komai ba, kallonshi tayi tace "meya janyo haka to?" Kallonta yayi ya d'an cije gefen lips d'inshi yace "kwana biyu kin daina bani kulawa, wannan ne yasa Umar Faruk rasa duk wani kuzarinshi." ya qarashe tare da kanne mata ido. Harara ta cilla mishi tana kallon computer bata sake mishi magana ba, suna daf da isa wajen kiran Papa ya shigo wayarta, d'auka tayi Papa yace "ki sameni a gendarmerie yanzun nan." D'if ya kashe wayar, kallon Umar Faruk tayi za tayi magana wayarshi tayi qara shima, daga yanda yace "ok Alhaji insha Allah." yasa ta gane Papa ne. Ajiyar zuciya ta sauke ta aje computer ta rumgume hannayenta tana kallon titi, tana tunanin me zai faru, shima baice da ita komai ba suka d'auki hanya...... _Bara muji meya faru bayan fitarsu_ ************* Abdul waid ne yayi irin durk'ushin nan nakan tafikan qafafu da kulki a hannunshi yana zarewa Mama ido, a nutse yace "Mama, Mama, Mama, sau uku ko? ina ganin girmanki shi yasa ban dakeki ba tunda kika zo nan, amma yanzu kin kaini bango mafita d'aya itace nasa a lallasa minke, in kuma baki son a dargajeki to ki fad'a mana yanda akayi kika samu sarqar tunda kince bake kika d'auko ba." Cikin rawar jiki da tsoro dan ganin ba sauk'i a al'amarin yasa tace "a'a yi hak'uri zan fad'a, wallahi zan fad'a maka gaskiya." "Ina jinki Mama." Cikin kuka tace " 'yata ce, sunanta Zubeida, wallahi ita ta d'auko bani ba." Zunbur ya mik'e tsaye yace "bani adresse d'inta?" Had'e hannaye tayi tace "dan Allah kamin rai yaro karka tona mata asiri, wallahi tana da aure kuma tana da kishiya, idan maganar nan ta fita wallahi aurenta zai iya mutuwa, nima kuma zan iya mutuwa." A tsawace yace "tasan da auren nata kuma tayi sata, mu aurenta bai damemu ba, aikinmu kawai mukeyi, ki bani kwatancen gidanta." ya fad'a da sake d'aga murya. Cikin kuka ta fad'a musu takwacen gidan malam, fitarsu Khairat ba wuya motar jami'ai tazo gidan, guba biyu daga ciki ne suka kutsa kai cikin gidan, a lokacin Zuby na zaune tana gurgurar tsamiya, saida gabanta ya fad'i data gansu, idon jami'in akan Mama Sa'a yace "sannu ko, dan Allah Zubeida muke tambaya a gidan nan?" Ba Zuby ba har Mama Sa'a saida kayan cikinta suka murd'a, a duburbuce take kallonshi tana kallon Zuby da ido ya raina fata , cikin d'aga murya yace "Hajia dake muke magana kinyi shiru." "Gata nan, wallahi gata nan, bani bace." cewar Mama Sa'a cikin harshen zarma, dan dama shi tafi iyawa. Ganin sun tunkari inda Zuby take yasa Mama Sa'a tashi da dugu ta shige d'akinta, tun basu qarasa wajenta ba ta fashe da kuka tana kiran sunan Mama ta fito ta taimaketa, Saratu Mama da Mama Maimuna ne duk suka fito, Mama kad'ai tayi k'arfin halin tambayar "bayin Allah lafiya, me tayi?" Shirun da sukawa Mama yasa dole taja baki tayi shiru, tsawa d'aya suka mata ta tashi ta d'auki hijabi tasa suka wuce, cikin qanqanin lokaci sai gata a prison (cell) tare da Mama, hannu ta d'ora a kai tana fad'in... "Na shiga uku Mama kin cuceni, yanzu da wane ido kike so na kalli yah Umar, haka kawai kinja mana abin kunya, akan me zaki fad'i sunana kamar ba 'yar da kika haifa ba?" Tsaye Mama ta mik'e tace "wallahi ubanki zaki ci idan baki min shiru ba, mahaukaciya kawai, dan ubanki ke ba banza ki kayi dani ba anan d'in kina can kina iskanci, shine ni kuma saina rufa miki asiri, to mu shirya d'aukar hukuncin da za'a mana, danna gama lura yarinyar nan 'yar akuya ce, ba zata tab'a sawa a fitar damu ba." Kuka ta sake fashewa dashi tana fad'in "haka kawai na jawa kaina, yanzu ya zanyi da cikin dake jikina? kina nufin zanyi rainon cikine a magarqama kome? wallahi ni dai ban yafe ba." Kwaf, Mama takai mata bugu a baki tana fad'in "ubanwa kike cewa baki yafe ba, ni Zubeida, ni?" Murgud'a baki tayi ta kawar da kanta, suna haka Khairat suka qaraso, nan ta samu Papa ya hakimce yana jiran zuwanta, masu tsaron lafiyarsa ne suka sara mata alamar gaisuwa kafin ta zauna, bayan sun zauna Abdul waid yace "Khairat dama yanzu nake tunanin kiranki , saboda an samu wanda ta d'auki sarqar." Kallon Umar Faruk tayi ta maida kallonta ga Abdul waid tace "an sameta, wacece, tana ina?" Papa ne ya katsesu da "bana kiraki bane danna saurari haka, ina baki umarni da ki janye qarar nan sannan kisa a rufe qarar, wannan ba girmanki bane." Kallon Papa tayi tace "amma P..." "Amma me, kiyi yanda nace kawai." Furzar da iskan bakinta tayi ta kalli Abdul waid da ido kawai ta masa alama, kai ya d'an jinjina yace "an gama." Da mamaki Umar Faruk ya kalleta, shi girma da ikonta ne kawai ke qara bashi mamaki, wata takarda ya bata tasa hannu sannan ya kalli wani jami'i yace "ka fito dasu." Da mamaki duka suke kallonsu kowa da abinda yake ayyanawa a ranshi, har suka tsaya gabansu cike da kunya dan sun kasa d'aga kai su kallesu, da qyar Umar Faruk yace "Zubeida, dama da ha...." Papa ne yace "tunda kun sansu , kuyi hak'uri ku koma gida, bai kamata kuyi magana anan ba." Kai kawai Khairat ke girgizawa yayin da Ruk'ayya ta rik'e baki, tsaye ta mik'e ta nunasu da hannu tace "na tabbata izuwa yanzu kun gama fahimtar abin kunyar da ku kayi, kunci albarkacin mahaifina wallahi, badan haka ba da sai kun gane shayi zalla ruwane, amma duk da haka nasan kun gane wacece ni, kuma in halinku ne nasan zaku koma, a wannan lokacin kuma zan muku d'aurin da goro ma saiya fiku kyan gani, daga qarshe kuma dole za'a shiga tsakanina daku, danna tabbatar ba alkairi kuke nema dani ba, kamar yanda jikina ke bani ba kun d'auki sarqar bane dan kawai ku siyar, ina fatan zaku gyara halinku in kuma hakan yaci tura to da fatan zaku kiyaye qara yiwa Khairat sata a karo na biyu." Da harara ta bisu tare da tsaki ta fice daga wajen, Abdul waid ne ya bawa Umar Faruk sarqar yasa aljihu, bin bayanta sukayi shi da Ruk'ayya, Papa ma tashi yayi ya wuce da qyar suka rarrafa suka fita daga wajen, tun a bakin titi Zuby ta fad'awa Mama abinda ya faru bayan tafiyar Khairat gida, a wahalce Mama tace "muje gidana." Taxi suka hau ta ajesu gidan Mama, suna shiga sukayi zaune kamar kayan wanki suna jajantawa kansu, Mama ce tace "ashe haka yarinyar nan take?" "Humm, ai bata da mutunci ko kad'an." Kafin Mama tayi magana Zuby tace "bama wannan ba, nifa akwai wasu maganganu da yarinyar ta fad'a min a ranar sun d'aure min kai sosai, amma nasan ke zaki sansu." "Wace magana?" cewar Mama tana neman cire riga dan tayi wanka. Maganganun da Khairat ta fad'a mata ta maimaita mata, cak Mama ta tsaya da cire rigar da take, da sauri ta juyo ta kalli Zuby ta kafeta da ido, ta kasa d'auke idonta kuma ta kasa magana, saida Zuby ta d'aga murya tace "Mama." Zabura tayi ta sake kafeta da ido, "lafiya Mama?" A hankali ta girgiza kai tace "ba komai, bara na fito daga wanka saiki tafi gidanki." Harta d'ibi ruwa ta shiga bayi jikinta ba qwari, saida ta fara kwararawa kanta ruwa ta dawo hayyacinta, *wacece Khairat, ya akayi tasan sirrin dako 'yan uwanta basu sani ba, taya tasan wannan sirrin? shine dai kad'ai nasan abinda na aikata wanda nake tsoron duniya ta sani, inba shi ba me Khairat take nufi???* wannan sune tambayoyin da takewa kanta harta fito daga wanka, Zuby ma tattarawa tayi ta kama hanyar gida, da sand'a ta shiga gidan dan ba zata iya had'a ido da kowa ba, d'akin Mama ta nufa kai tsaye ta samu ta kwanta. Khairat kuma daga nan gida suka dawo saboda takaici da zulumin abun, Ruk'ayya da Umar Faruk kuma babu wanda ya fad'i maganar a gida, d'aki take kwance tana karatu dan yanzu shi kad'ai ne ke cireta damuwa. Ana sallah magrib kuma Mama tasa Zuby ta shirya tace ta koma d'akinta, ba gardama ta shiga ta hakimce tana sabgar gabanta, Umar Faruk na shigowa bayan sallah isha'i yaga d'akin bud'e da alama qarara tana ciki, wata shegiyar qwafa yayi ya cire belt d'inshi ya tunkari d'akin........ _Wallahi nima gidana zanje, wannan hushi haka Umar Faruk_😂 *Kuyi hak'uri da rashin cika alk'awari da nayi jiya, hakan ya faru ne saboda daukewar da wata tayi ina cikin typing.* 23/08/2019 à 12:51 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *Allah Ka qara mana tsoronka* _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣1⃣ Daf da zai shiga d'akin Mama ta kira sunanshi, juyowa yayi yaga Mama tsaye a k'ofar d'aki, b'oye belt d'in yayi ya nufi wajen Mama, sunkuyawa yayi har qasa yana fad'in "gani Mama." Saida ta shiga d'aki yabi bayanta daga tsaye tace masa "na mayar maka da matarka, dan Allah bana son jin wata hayaniya, kayi hak'uri da duk abinda ya faru, kaji?" Jim ya d'anyi kafin yace "shikenan Mama." Tsaye ya mik'e zai fita ta sake cewa "azumi ke tahowa,amma banga kana shirin tarbansa ba kamar yanda kake kowace shekara." Ajiyar zuciya ya sauke yace "ina tune Mama, insha Allah za'a fara gudunar da komai kamar yanda ake kullum." "To shikenan, Allah yayi albarka." "Ameen, saida safenku." ya fito daga d'akin. Saida ya harari d'akin ya wuce d'akin Khairat, tunda ba za'a barshi ya mata shegen duka ba, gwara ko hukunci ya mata wanda zata san ta b'ata masa rai, tsakiyar gado take ta mike qafafu ta jingina bayanta ta rufe da zanin rufa tana karatu ya shigo, bayan amsa sallamarshi ta bishi da "sannu da zuwa." "Sannu." kawai ya fad'a ya fara cire kayan jikinshi, douche ya shiga yayi wanka sannan ya fito, wando iya gwiwa yasa ya feshe jikinshi da turare ya haura kan gadon, computernshi dake gefe ya d'auka ya fara aikinsa, ganin shiru babu mai magana yasa Khairat cewa "baka jin yunwa ne?" "Ya zanyi idan ma ina ji, wa nake da da zai bani abinci naci?" shine abinda ya fad'a ba tare daya kalleta ba. Jaye zanin rufan tayi ta fita daga d'akin, tununya ta d'ora a gas sannan ta shigo ta d'auki indomie ta dora mishi, ba jimawa ta gama dafawa ta juye a plate ta kawo masa, saida ta janyo tebur d'in har gabanshi ta aje masa, ruwa ta d'auko da lemu mai sanyi ta aje masa, kallonshi tayi ganin ko kallonta bayayi tace "bismillah yallab'ai." Abinda bata sani ba, kaf kai da kawowarta a idonshi tayashi, ya kuma kalleta ne da idon rahama da qauna, aje computer yayi ya sauko da qafafunshi, cokalin ya d'auka yana kallonta yace "kefa?" Kai kawai ta girgiza alamar a'a, fuska a d'aure ya janyo hannunta ya zaunar da ita akan cinyarshi, kafeta yayi da ido yace "me yasa ba zaki ci ba?" "Naci abinci tare da Ruk'ayya." ta fad'a tana kawar da kai. Hannu yasa ya juyo da hab'arta yana kallon fuskarta yace "Khairat, bansan da wane baki zan baki hak'uri ba, amma ina baki hak'uri daga gaba d'aya zuciyata." Kallonshi tayi cike da yanga tace "manta kawai ya wuce, hakan da sukayi aiya nuna nice a samansu." D'an lumshe ido yayi kafin ya bud'e ya fara cin indomien ba tare daya d'agata daga cinyarshi ba, yana ci tana shafar qasumbarshi kamar daga sama sukaji qarar Zuby....... Tsakin da Umar Faruk yayi yasa Khairat kallonshi tace "yadai, kasan meya faru ne? kaje ka duba." "Meye fa idan ba iskanci ba." ya fada yana ci gaba da cin abincinshi, itama sherewa tayi saida yaji hayaniyar mutane sannan ya d'auki singlet yasa ya fito, ganin mutane a k'ofar d'akin nata yasa ya qarasa cike da takon izza, Mama na ganinshi tace "ka d'auko makullin mota ka kaita asibiti, ina jin fa tayi b'arine." Ba zaice yaji dad'i ba amma dai yasan baiji zafin barewar cikinta, dan a halin yanzu baya ma buqatar had'a zuri'a da Zuby, juyawa yayi a kasalance ya koma d'akin Khairat ya sanyo doguwar riga ya d'auko makulli ya fito, Khairat ma dai lek'owa tayi taga tanata birgima tana dafe ciki, sosai taji tausayinta lokacin da Mama Sa'a da Mama suka kamata zasu fita taga jini ya b'ata mata jiki, cike da rashin jin dad'i ta girgiza kai ta koma d'akinta, tana komawa d'aki ta kwanta ruf da ciki ta janyo computer Umar Faruk tana kallon aikin daya fara, kamar da wasa saita fara dora mishi tata fasahar zanen, bata daina ba har saida ta gama, kallon sabon sanfurin zanen takalman tayi tayi dariya, dan a ganinta babu abinda zaiyi dashi, bacci ne ya fara fizgarta har tana gwara kai ga computer, sulalewa tayi ta aza kanta daf da computer yayin da hannunta ke saman ceybor d'in, cikin kuskure saiko Khairat ta aika da sakon a shafin yanar gizo na compagnien da yake ma aikin. ************* Koda suka je ma wankin ciki aka ma Zuby dan ciki kam ya b'are, duk wasu kudade da aka caza saida ya biya sannan yace zai koma gida, tunda dai ance saida safe a sallmeta, Mama bata hanashi ba tunda babu abinda ya rage Zuby kuma bacci take, amma koda aka kira Mama aka fad'a mata ta garzayo tazo, abin mamaki ko kallon Mama ba tayi ba wai ita tana hushi saboda bata je ta ganota ba, haka ma Umar Faruk bata kulashi ba kamar yanda shima bai kulata ba, Mama Sa'a kad'ai ta tambaya yanda ake ciki, ana fad'a mata tace su tafi gida ita zata zauna wajenta, hakan kuma ba qaramin dad'i ya musu ba, dan haka Umar Faruk ya dawo dasu. ***************** A hankali ya shiga d'akin da sallama d'auke a bakinshi, da murmushi ya qarasa wajenta ya zura hannu zai gyara mata kwanciya, cak ya tsaya yana kallon computer dake gabanta da tsananin mamaki, d'aukar computer yayi danya tabbatar da abinda idonshi ke gane mishi, ai kuwa dai gaskiya idonshi ya nuna mishi, sanfurin daya aika an karba kuma ana tayashi murna, tare da turo mishi adadin wasu manyan kud'ad'e a account d'in daya bud'e bada dad'ewa ba, da sauri ya janyo sak'on daya tura ya gani, nan yaga sanfurin da aka tura, shi dai yasan bashi bane kallon Khairat yayi dake bacci abinta, dariya yayi ya aje computer kamar daga sama Khairat taji an d'auketa sama, cikin dubara ya azata bayanta yana juyi da ita tsakiyar d'akin, "Wai miye haka Faruk?" Fad'a mata yayi abinda ake ciki, itama murna ta tayashi kafin yasa tayi alwala suka dinga jera nafilfili har zuwa sallah asuba, yau kam sunyi karatu kuma yayi mamakin yanda bakinta ya fad'a sosai akan karatun, qara mata yayi sannan suka shirya dan tafiya wajen aiki, amma shi dole zai fara biyawa asibiti, suna hanya ya kalleta yace "saina biya asibiti fa." "Ba komai." ta fad'a tana kallon gefen hanya. Ba b'ata lokaci suka isa asibitin, a tare suka shiga ciki kafad'unsu na gugar juna, da sallama Umar Faruk suka shiga sab'anin Khairat data d'auke kai, tsaye tayi kofar d'akin ko kallonsu ba tayi ba, Umar Faruk d'in ne kad'ai ya zauna bakin gadon suna gaisawa, gaba d'aya sama sama suke gaisuwar dan kowa da abinda ke ranshi, Zabba'u ce tazo shigowa d'akin, ganin Khairat a k'ofar yasa ta shirya ta taqarqare ta bankad'e Khairat har saida ta fad'a bayan Umar Faruk dake kusanta, yar qaramar qara tayi tare da maqale wuyanshi sosai, jin a jikinshi ta fad'a yasa ta canza rik'on da tayi masa dà salon shafa, kanta ta zuro ta wuyanshi tana kallon Mama da Zuby da suke fuskantarta, kashe musu ido d'aya tayi kafin ta d'ago tana kallon Zabba'u wacce ke tsaye Umar Faruk ma kallonta yake, murmushi ta mata tace "sannu." Kamar jira take sai kuwa ta shak'i wuyan hijabin Khairat ba tare data shirya ba, kamar Umar Faruk ta shaka sai kuwa yayi zunbur ya mike tare da qwaqwale hannunta ya nunata da yatsa yace "karki sake dora hannunki akan matata, marar kunya kawai, meta miki to? bayan turowan da ki kayi mata bai isheki ba saikin ci mutuncinta a gabana, to ki kiyaye ni wallahi." Juyawa yayi ya kalli Zuby dake zaune tana kurb'an pure water yace "nasan ai kinsan laifinki, kiyi qoqari kada ki bari wani ya sake jaza miki sabon laifin." "Kai Umar Faruk, kana cikin hankalinka kuwa, dama abinda kazo fad'a mata kenan, kuma dan wulak'anci shine saida wannan zaka zo ganinta? kawai dan kana so kaci zarafinmu." cewar Mama. A kaurare yace "hmm , Tanti, naci zarafinku fa ki kace? ai kune kuka gama cin zarafina." "Mu kuma, wai yaushe ka zama marar kunya fitsararre ne? nidai ba haka na sanka ba." Saida ya rik'e hannun Khairat cikin nashi yana murmushi yace "tun ranar dana samu soyayyar gaskiya, ranar na fara banbance tsakanin qarya da gaskiya, kuma ranar na fara sanin asalin masoyiyata, ranar dana samu wacce ta dace da rayuwata, matsayina, mafarkina, da kuma burina." Hannunta Umar Faruk yaja zasu wuce ta juya ta kalli Mama ta sake kashe mata ido, wayarta ce ta sub'uce daga hannunta ta fad'i qasa hakan yasa Umar Faruk sakinta ta sunkuya ta d'auka, da murmushin mugunta ta sunkuya ta d'auki wayar tana d'agowa ta d'ora wayar a kunne kamar da gaske tana fad'in " Hello, Bala , ka sameni office za muyi magana da kai, eh akan maganar nan ba, ok saika zo." D'auke wayar tayi tare da juyawa ta kalli Mama data sake baki da kunne tana saurarenta, wata kafirar dariya tayi ta juyo tare da gimtse bakinta dan kar Umar Faruk ya gani, bakin k'ofar kuma suka had'e da wata matashiyar likita mai sunan *Jamila* , da farin ciki suka mik'awa juna hannu ita da Khairat suka rumgume juna, sosai suka gaisa ana gaisuwar yaushe gamo saboda an jima ba'a had'u ba, saida sukayi musayan lamba sannan suka fita, dariya na takura mata saboda yanayin da taga Mama, suna cikin tafiya Umar Faruk yace "waye Bala kuma?" Gimtsewa tayi tace "ba komai." ta fad'a. "Ban yarda ba." ya fad'a yana kallonta. A tak'aice tace "wannan Alhajin da muka had'u dashi ranar." "Waye shi?" ya sake tambaya. Cikin qosawa tace "ba komai fa, idan da wani abu ma ai lokaci zaiyi da zaka ji." Wayarta ta fiddo ta fara aikawa Jamila sak'o kamar haka " k'awata naso na miki magana tun acan, amma muna buqatar sirri." Maido mata tayi da fad'in "k'awata baki da dama, ina fatan dai ta samu?" "Sosai kuwa, wata alfarma nake nema a wajenki idan zan samu?" "Fad'i kawai, kinsan umarninki abin bine." "Na gode, aiki nake so kimin akan yarinyar nan dake qarqashin kulawarki." "Ina jinki." "Ina so ne ki rik'esu har nan da kwana biyu." "Me yasa, meye tsakaninki da ita?" Maida mata tayi da "ita d'in kishiyata ce, kuma tana min kallon raini, ni kuma bana so, ina so tasan wacece ni." "Shegiya qawata, ashe zaki iya zama da kishiya? aina d'auka baki da ra'ayin auren mai mata, amma karki damu ba zai gagara ba insha Allah." "Na gode qawata, zaki ji nauyi a lalitarki." "Da kyau qawata, shi yasa nake sonki wallahi." Suna gama message Khairat ta fara qoqarin tura mata da kud'i, ganin an nuna mata ba zata iya cire kud'i ba yasa tace "ban gane ba, wannan wane salon iskancin ne kuma?" Kallonta Umar Faruk yayi yace "meya faru?" "Kud'i zanyi transfert yanzu ana nuna min ba zan iya fitar dako sisi ba." "Wataqila kin cinye wajen siyan sweet da kayan jiki." cewarshi ba tare daya kalleta ba. "Haba dai, kasan nawa ke cikin asusu nan kuwa?" Wayarshi ya fito da ita ya kalleta tare da bata wayar yace "ki turawa duk wanda kike so kuma ko nawa ki kayi niyyar turawa." "A'a ka barshi kawai, zanje bankin naji meye matsalar." Murmushin gefen labb'a yayi yana kallonta yace "wane banki kike ajiya?" "Bank centrale." ta bashi amsa. Nanma wani murmushin yayi ya fara danna wayarsa , 'yan daqiqu ya fara magana " mutumina ya kake?" Jim yayi yana sauraro kafin yace "lafiya lau wallahi, dan Allah kana aikine yau?" Nanma shiru kafin yace "zan turo maka da lambar wani asusu ina so nasan nawa ne a ciki, dan ana so a cire kud'i bayayi, ina so nasan meye matsalar." Jim ya d'auke wayar daga kunnanshi ya bata wayar yace tasa lambar asusun, tura mishi yayi bayan wasu mintina ya sake kira, nan ya fad'a masa mai girma Mani Bukar ne yasa aka rufe asusun, take ya fad'awa Khairat yanda ake ciki, waya ta ciro tana dannawa Umar Faruk yace "me za kiyi?" "Papa zan kira." ta fad'a a tak'aice. Fizge wayar yayi yace "ba yanzu ba, tunda ki kaga sunyi haka to da dalili, ki sarara musu dan Allah." Dole ta hak'ura badan taso ba, da haka suka isa ma'aikatar, kowa mazauninshi ya nufa amma Khairat ta kasa samun sukuni saboda abinda Papa yayi, bata tab'uka komai ba har lokacin tashinsu yayi, tare da Umar Faruk suka koma gida, alwala yayi ya wuce masallaci, saida yayi sallah isha'i ya dawo kai tsaye wanka ya shiga, tunda Khairat taga haka tayi niyyar babu inda zaije, dan haka yana gama shiryawa ya rumgumeta yace "zanje asibiti na dawo." "Saika dawo." ta fad'a a qasan maqoshi. Zai tafi ta rik'e hannunshi...... _Anya kuwa zai tafi?_ 23/08/2019 à 12:51 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣2⃣ Ta had'e bakinsu waje d'aya, salonta ta fara masa wanda yasa ya manta komai dake gabansa ya biye mata, take ta lula dashi wata duniya har suka fad'a kan gado, nan dai naji ya fara karanto wannan addu'ar mai kayar min da gaba, da gudu na fito daga d'akin na barosu🏃‍♀🏃‍♀🏃‍♀. *************** Tun bayan fitarsu Khairat Mama tasa gyalenta ta goge gumi, a ranta kuma tace "nifa nayi mamaki, tabbas yarinyar nan tasan Alhaji Bala, to amma meye tsakaninsu da ita da har take kiranshi da Bala haka ba girmamawa? kodai itama karuwarsa ce, wata zuciyar ta fad'a mata." Zuby ce ta katse mata tunani da "ni dan Allah suzo su sallamemu naje gida, wanka ma nake so nayi." Kallonta tayi amma ba tace komai ba, Zabba'u ce tace "kiyi hak'uri mana zasu sallameki ai." Sai lokacin Mama tace "nima dai na matsu, dan yanzun haka akwai abinda ya taso min mai mahimmanci." Zuby ce tace "Mama badai wajen malam zaki koma ba?" A fusace tace "eh wajenshi zan koma saime? ba dole naje ba, ke baki ga abinda ya faru bane kuma yake shirin faruwa." "Kamar me kenan?" cewar Zuby. "Mtsssss." tsaki kawai tayi ta shareta Zabba'u ce tace "to ai qwara aje wajen malam, dan ina tsoron kar karuwar can tasa miki hannu a cikin zubewar cikin nan." Kallonta Zuby tayi tace "kuma fa hakane, gaskiya kam." "Ah to fad'a mata." cewar Mama. Jamila ce ta shigo ta fad'a musu tana buqatar sake murmurewa , dan haka sai nan da kwana biyu zasu sallameta , da farko fad'a Mama tayi saboda ba zata iya zama waje d'aya ba haka, amma da Zabba'u tace "ku kwantar da hankalinku mana, wannan ma ai hanyar samun kud'i ce a hannun yah Umar." "Shegiya, kuma fa hakane wallahi." cewar Mama tana dariya. _Allah ya shiryeku_ Zuba ido suke da dare suka Umar Faruk amma shiru, sai Saratu da Abbakar Baba dasu Mama ma duka sunzo amma banda shi, tun lokacin Zuby ta fara damuwa tare da kuka tana fad'in Khairat ce ta hanashi zuwa, haka dai su Uwani da suka zo suma aka rarrasheta. _Tukunna ma Zuby, ke kika tsokano min qawata._ **************** Da safe ma saida Khairat tayi abinda yasa suka makara, hakan yasa dole suka wuce wurin aiki ba tare daya biya asibiti ba, a ma'aikatar ma bata barshi ba, basu fi minti talatin da zuwa ba tasa Habeeba ta kira matashi, yana shigowa ta taso tasa makulli a k'ofar ta zaunar dashi akan kujera, qafafunshi ta zauna ta b'alle masa botir d'in riga, yanda ta rikirkitashi yasa ya cire mata tata rigar itama, duk da a tsorace take dan bata manta wahalar da tasha ba, amma haka ta daure suka dinga....duk da komai bai faru ba amma anji jiki sosai kuma ankai maqura. A daddafe suka kai yamma suka koma gida, kamar kullum alwala yayi ya tafi masallaci sai bayan sallah isha'i ya dawo, wanka yayi cike da kasala ya fara shiri, tun bai qarasa ba Khairat ta sauko daga kan gado ta nufi hanyar fita, yana kallonta ta madubi yana b'alla mab'allan rigarshi, saida ta saci kallonshi ta gefen ido taga yana kallonta ta madubi sannan ta dafe kai da fad'in "ahhhhh, washhh kaina." Da sauri ya juyo yayi kanta ya rik'ota yana fad'in "baby lafiya, meya faru ne?" Cikin lumshe ido da kasallaliyar murya hannunta dafe da kai tace "kaina ne kemin ciwo, harna fara ganin jiri." "Ayya, sannu, zoki kwanta to." ya fad'a yana nufa da ita kan gado, a yamutse tace "karka damu kanka, zai bari yanzu." "Ke lafiya kike? bana da hankali ne zan barki a wannan halin, kinsan yanda nake jinki kuwa?" Kafin tayi magana ya nufi da ita kan gado ya kwantar da ita yace "bara na samo miki magani." Shiru tayi harya bud'a drower ya fito da maganin ya d'auko ruwa ya d'agata yasa mata maganin a baki tare da kai mata ruwa, bata bari ya wuce ba ta maidoshi a jikin Umar Faruk kamar wacce ke aman gaske, rik'e rigarshi tayi ta sake yunquro wani aman kamar gaske, ganin babu abinda ya fito daga bakinta yasa ta koma ta kwanta, kallonta yake harya cire rigar yasa ya goge mata bakinta a tunaninshi amai tayi, fitar da rigar yayi ya dawo da abin gogewa ya goge na kan gado, gefenta ya zauna ya d'ora kanta akan cinyarshi yana shafarta yace "tun yaushe kike jin haka amma baki fad'a min ba?" Da qyar kamar marar lafiya tace "ban jima da jin haka ba." Lek'o fuskarta yayi yace " to me yake damunki, kodai akwai ajiyata ne anan?" ya qarashe da dafa cikinta. Shiru tayi ta rufe ido ta nuna bacci harya d'auketa, jin shiru yasa ya sake kallon fuskarta, ganin tana bacci yasa yace "to, ke kuma naki mai bacci ne." Tana jin haka ta bud'a ido tayi murmushi tana d'aga ido tana kallonshi dan tasan ba ganinta zaiyi ba, murmushin gefen labb'a tayi a ranta tace "kad'an kika gani Zuby kike ko uwar wa, zaku san dani kuke magana." Daga haka kuma har baccin gaske ya d'auketa, saida yaga ta jima tana baccin sannan ya gyara mata kwanciya, lokacin dare yayi sosai dan haka ya kabbara sallah... *************** Ganin shiru yau ma yasa Mama fita tace za taje ta dawo, haka ta bar Zuby ita da Zulfa'u a asibiti, daga nan kuma wajen malam ta nufa. A gaban malam take ta fad'a mishi abinda ya faru tun washe garin ranar data bar wajenshi har izuwa yau, kwantar mata da hankali yayi kafin ya d'ora da "ke dai kinsan komai game da gidan nan, matsalar da aka samu a game da aikinmu shine wannan tsaron dake cikin gidan, abu d'aya da zakiyi yanzu shine, da zaran yarinyar ta fita daga gidan ki gaggauta kirana ki fad'a min, ta haka zamu samu sauk'in yin nasara a kanta." "To amma malam aiba gidanmu guda ba, taya zansan ta fita?" " xYarki ba gidan take ba? ki fad'a mata ita saita fad'a miki idan ta fita." "To shikenan malam, za ayi komai." da haka ta baro wajen malam ta dawo asibiti, koda ta tambaya yazo akace a'a, masifa ta fara asibitin tana fad'in ya rainata ma. ************ Shi kuma yana gida ko fitar baiyi bama shima mutan gida sai kula da Khairat ake , dan gaba d'aya ya fad'a musu bata da lafiya, kowa na tunanin itama ciki ne a kwasa,shi yasa kowa ke bada gudumuwarshi , sai bayan sallah azahar ta nuna ta warware babu abinda ke damunta, amma duk da haka Umar Faruk bai barta har saida akayi sallah magrib, a lokacin ne Khairat ta buk'aci Zuby ta dawo gida, sai dai tana jin kunyar tama Jamila magana ba tare data tura mata kud'in nan ba, dan haka ta kalli Umar Faruk tace, "Baby." "Na'am baby, me d'an baba yake so?" Murmushi tayi tace "ba komai, maganar kud'in nan ne da zan tura, ina buqatarsu ne kuma bansan me nawa Papa ba ya rufe min asusu na." Wayarshi ya mik'a mata yace "gashi kisa lambar saiki aika." Karb'a tayi kuwa ta tura iya wanda tayi niyyar tura mata, ganin hankalinshi baya kanta yasa ta duba lambobin daya kira ko suka kirashi, cikin sauk'i ta samu lambar Zuby a wayar, saida ta d'auka a wayarta sannan ta bashi wayar, fita yayi dan sallah isha'i dan rabon daya dawo irin wannan lokacin harya manta, saida tayi sallah tana zauna ta dannawa Jamila kira tace a sallami Zuby, saboda taji nauyi a lalita yasa yace "an gama hajiyata." Suna gama waya ta kira lambar Zuby, Zuby na zauna taga baquwar lamba, d'auka tayi ba tayi magana ba, "Hello." Yanda muryar ta daki kunnanta yasa har saida gabanta ya fad'i, kafin tace wani abu Khairat tace "Zubeida, kiyi hak'uri da rashin ganin mijina a asibiti, kar kiga laifinshi indai kina da wayo, mahaifiyarki ce ta fara tsokanoni, a qarshe kuma sai kika nuna min kina so mu fara siyasa a cikin zaman namu , da wannan nake so na nuna miki cewar, ni jinin siyasa ce kuma na gajeta ne ba kamar ke ba da tsinta kawai ki kayi a hanya, bara na nuna miki kad'an daga cikin ikona, yanzun nan za'a sallameki daga asibiti, dan nasan kuna tunanin an ajeku ne kawai, to nice nan nasa aka rik'eku, zai iya yiwuwa ba ara miki mijina yazo ya d'aukoki, bye bye." Tana kashe wayar ta tuntsire da dariya tana fad'in "waya fad'a miki barno gabas take, turnuqu fad'an iblisai, yaro bai gani ba balle ya raba, da uwarki ma a shirye nake nayi kishi bare kuma ke." 🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂ Cike da jin haushi Zuby ta buga wayar a qasa ta fashe, a tsorace Mama ta kalleta tace "ke lafiya, meye haka dan ubanki?" Kallon Mama tayi zatayi magana sai kuma ta fashe da kuka, da qyar ta tsagaita da kukan ta fad'awa Mama abinda tace mata, dafa kafad'arta tayi tace "kwantar da hankalinki, zamu je gidan ai wallahi sai Umar Faruk d'in ya raina kansa." Tana cikin daddab'ata wani namiji ya shigo shiya sallamesu, tattara kaya sukayi suka fito daga cikin asibitin...... ************** Lambar Jamila ta kira amma kafin ta d'auka saita katse kiran, hakan yasa Jamila maido kiran kuma ta dauka, cewa tayi tayi hak'uri ba ita taje kira ba, *anya ba wani abu a game da kiran nan* suna kashe kiran tun kafin ya shigo Khairat ta kirashi a waya, yana d'auka tayi fuska tace "dama qawar nan tawace ta kirani waina fad'a maka kaje ka d'auko marar lafiyarka, an sallamesu kuma sun kasa samunka a waya." "Amma ai wayata a kunne take." ya fad'a da d'an mamaki. "To nidai haka ta fad'a min, kaje kawai saika dawo." "Ok to, ki kula min da kanki da babyna." "Ina babyn yake?" cewar Khairat. Dariya yayi yace "bari na dawo zan nuna mikishi." "Allah ya tsare, saika dawo." "Ameen." ya amsa ya shiga mota dan dama da makullinshi a aljihu, ita kuma goge kiran da tawa Zuby tayi da wanda tama Jamila, amma bata goge wanda Jamilar ta mata ba da wanda tama Umar Faruk. ************ A k'ofar asibitin ya samesu suna jiran taxi, tsayawa yayi gabansu harya fito, "sannunku." kawai ya fad'a, kayansu ya d'auka yasa ciki sannan ya shiga ya zauna yana jiran shigowarsu, saida suka gama wainashi sannan suka shiga motar, Zuby ce gaba Mama baya sunyi nisa babu mai magana, shirun ne yayi yawa yasa Mama cewa, "Umar Faruk, ina kallonka mai hankali, amma gashi kana nuna min ba haka ba, me yasa kake haka?" "Me nayi tanti?" ya tambaya cike da gadara. "Yanzu yaushe rabon da kazo asibitin nan? saika nuna mana kai ka auri karuwa, gaba d'aya tabi ta shanyeka ta hanaka komai, inba ka sakar mata fuska ba har tana da ikon da zata kira Zuby tana fad'a mata magana, har za tace wai zata ara mata kai kazo ka d'auketa, shi yasa kazo kenan?" D'an juyowa yayi ya kalli Mama yace "Khairat d'in ce ta kira Zubeida?" "Eh mana, ko qarya zan mata?" "A'a, ni bance ba, amma da mamaki." "To shikenan, kaimu gidan saika tambayeta a gabanmu kaji." "To." ya fad'a a tak'aice. Suna zuwa gida ya shigo da kayansu, nan aka fara musu sannu da zuwa har Mama Sa'a da Mama sukace "shirin tafiya muke yanzu kam, amma gashi an muku sallamar dare." "Ki tambayi karuwar surukarki, ita tasan yanda akayi tasa aka rik'emu sai yanzu kuma tasa aka sallamemu." Kallonta Umar Faruk yayi yace "tanti ba karuwa ba dai, Khairat sunanta, idan kuma sunan na miki wuyane zaki iya kiranta da alkairi." 😂😂😂😂 "Ubanka." ta fad'a cikin hushi harda mishi da hannu. Gimtse fuska yayi Mama kuma tace "ka fito da munafukar mana ta fad'a a gabanku kuji." Juyawa yayi ya nufi d'akin ya sameta zaune tana karatun littafi mai tsarki, daga qofar ya tsaya yace "kizo dan Allah." Da kai ta masa alamar to, hijabi tasa sannan ta biyo bayanshi, ganin kowa cirko cirko yasa ta tsaya kusanshi tana kallon Zuby tana fad'in "yar uwa, yanzu kuka shigo, ya jikin naki?" Kallonta Zuby kawai take Mama ce kad'ai ta samu damar yin tsaki, Umar Faruk ne ya kalleta yace "alkairina, akan me kika kira Zuby kika fad'a mata magana har kina cewa zaki ara mata ni." Da sauri ta bud'e baki tana kallon kowa dake wajen da tsantsar mamaki, cike da rainin hankali tace "baby, nice na kira Zuby, akan me kuwa zan kirata, ina na samu lambarta ma?" Maida kallonta tayi ga Zuby tace "ni d'in na kiraki, tunda muke na tab'a kiranki ne? wallahi kuji tsoron Allah ku tuna zaku mutu fa." Mama da Zuby kasa magana sukayi sai Umar Faruk ne yace "kin gani tanti, na fad'a muku dama da mamaki, babu ruwanta da sabgar kowa." Zuby ce dake dafe da cikinta tace "kece za kiji tsoron Allah munafuka kawai, kina nufin zaki qaryata mahaifiyata ne? ai wayarta nanan a duba kiran za'a gani. " Ta qarasa da kallon Umar Faruk, kallon daya ma Khairat ne yasa ta nuna mishi d'aki tace "tana d'aki, ka d'auko da kanka ka duba." D'akin ya nufa Khairat kuma ta kalli Mama tace "da kike cewa mahaifiyarki zata min qarya, ita littafi mai tsarki ce da ba za tayi qarya ba, ta aikata laifin daya fi na qarya ma bare kuma wannan." Kallon Mama Zuby tayi ta kalli Khairat tace "me tayi? ki daina kwalo kwalo ki fito ki fad'a mana in kina da gaskiya." Matsawa kusan Zuby tayi tace "Ina ruwanki to da zaki ce ta fad'a, karna sake jin bakinki." Fitowar Umar Faruk yasa sukayi shiru suna kallonshi, saida ya gama duba kiran sannan ya bawa Zuby wayar yace "duba ki gani, kiran da qawarta ta mata ne ta fad'a mata naje na d'aukoku, sai kuma kirana da tayi ta fad'a min, amma duk da haka kike neman d'ora mata laifi." Saida Khairat ta maqale hannunshi ta d'ora kanta akan kafad'arshi tana kallon Zuby tace "Allah yasa zata gane idan ba asarar kud'inku ku keyi ba kuna zuba mata ecole d'in." Mama Ruk'ayya Mama Sa'a Umar Faruk harma da Mama Maimuna dariya suka saka, aida bak'in ciki ya taso mata sai kuwa ta buga wayar qasa itama, a take wayar ta fashe ita kuma ta dora "sai dai dukanmu muyi asara, shegiya kawai." Juyawa tayi zata nufi d'akinta Khairat tace "wallahi ina rabaki da yawan kiran wani shege, zafa ki iya jin kunya a qarshen al'amarin, kuma waya da kika fasa mijinki ne zai biyani." Maida kallonta tayi ga Mama tace "ki fad'a mata komai ko zata daina kirana shegiya, inba haka ba wallahi da kaina zan fad'a mata komai." Itama d'akinta ta shige ta barsu nan, Umar Faruk kuma daukar wayar yayi yaga ta fashe sosai, yanzu dole saiya siyi sabuwa😁😉, haka dai Mama ta fita ba nasara Zuby kuma wanka ta samu tayi ta kwanta, d'akin Zuby ya kwana bayan ya gargadeta sosai tare da ja mata kunne, nan ta fad'a mishi itama wayarta ta fashe, cewa yayi "ke kika fasa wayarki saboda b'acin rai, kuma kika fasa ta mutane, dan haka karki d'auka zan siyo miki tsadaddar waya ce, wacce kika fasa ita zan siyo miki." "Kenan itama zaka siyo mata wacce na fasa ne?" ta fad'a tana kallonshi. "Sosai kuwa, wannan ai shine adalcin da kike cewa bana yi." A haka sukayi bacci suna nesa da juna, da safe kuma ba wayoyinsu kad'ai ya siyo ba harda kayan d'inkinsu na sallah, dana gaba d'aya sauran mutanen da yasan yana musu.... _Indai Zuby ce nasan yanzu ma za tace wani abun ne_ 23/08/2019 à 12:51 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣3⃣ Da safe Umar Faruk ya bawa kowa kud'in d'inki tare da damar tafiya kai d'inki, Khairat kuma yace ta zauna ta huta tunda bata da lafiya karta wahalar masa da babynsa, saida ya fita tace "na shiga uku nikam na jawa kaina." Zuby ta zuba ido tana so taga Khairat ta fita kai d'inki danta kira ta fad'a, ganin shiru bata da niyyar fita yasa itama ta fita kai nata, kuma harta dawo bata ga alamar Khairat ta fita ba, dole ta hak'ura ta cire rai amma dai tasan dole zata fita koba yau ba tunda uwar yawo ce. Saida Umar Faruk ya dawo yace Khairat ta shirya ya kaita, cewa tayi ya bari har ranar data karb'i girki saisu tafi, bai mata musu ba ya barta dan tayi tunanin abinda shi baiyi tunaninshi ba. *Bayan kwana uku* ranar litinin kuma a ranar aka tashi da azumi, a ranar Khairat tasha wahala sosai dan saida ta tafi aiki ta dawo misalin 12:00, wanka kawai tayi da sallah ta fara aiki saboda abinda take sonyi yana dayawa, duk da ta fara da wuri kuma Ruk'ayya dasu Fateema Zeinab duk sun kama mata saida ta gaji sosai, an soya an dafa an motsa haka tayi shirye shirye sosai domin taya mijinta tarban wannan watan, koda suka gama wanka kad'ai ta fito aka sha ruwa, Umar Faruk kuma dama duka mazan sai an gama sallah isha'i suke shigowa dan daga gidan ake fitar musu da wasu daga cikin kayan shan ruwan. Tunda ya shiga d'akin yaga abubuwan ci da sha zube kala kala ya saki baki, saida ta zaunar dashi ta fara taimaka masa sannan yace "babyna wai duk ke ki kayi wannan abun, yaushe kika zama babban qwararriyar Mai girki ne?" "Idan ka gama ci zaka san ranar." Hannunta ya kamo ya zaunar da ita akan cinyarshi yana kallon fuskarta yace "kenan kin wahalar min da babyna ko? gaskiya ni bana son haka, daga yau ba zaki sake aikin nan ba, kibar komai su Ruk'ayya zasu yi." A raunane ta kalleshi tace "baby nifa bana da komai, ka daina tunanin inada ciki fa, bana da komai." Ta qarashe da shagwab'ewa, sumbatar kumatunta yayi yace "idan ke baki tabbatar ba ni na tabbatar." "Tayaya?" ta fad'a tana kallonshi. "Zan nuna miki anjima." ya fad'a yana kallon tarin kwanukan dake gabanshi. Azumi ake yayin da abubuwa sukayi dama, sai dai kullum da dramar da za ayi tsakanin Zuby da Khairat, wani lokacin dramarsu tana bawa mutanen gidan dariya, danko Baba ya gani yakan dara saboda yanda Khairat ta bala'in raina qurar Zuby, a hankalce da dubara da salo take fad'a mata magana, a qarshe sai dai ta shiga d'aki tana kuka, kullum cikin waya suke da Mama tana fad'a mata abinda ke faruwa gidan, Mama kuma tana cewa tayi hak'uri watan azumi take jira ya qare suci gaba daga inda suka tsaya, ta mata alk'awarin dole wata rana gidan zai zama mallakinta, a haka kad'ai take jin sanyi a ranta, duk da qoqarin da Umar Faruk keyi akanta bata ganinshi, Allah ya sani ya saba da irin rainon Khairat hakan yasa idan yazo d'akinta yake sa ran samun irinsu, amma sam baya samun damar hakan kuma idan ya buqaci ta bashi jikinta kawai shiya juyata bata yarda, dan haka ya gama lura ita d'in mace ce da bata damu da wasanni ba, ita dai kawai kaje mata lokaci d'aya, abin haushi kuma da an fara haqar rijiyar sai tace ta gaji ko gaba d'aya ba'a haqa ba, zuwa yanzu kam badan haqqinta ne ba daya daina kusantarta , tunda dama ba wani abu yake jiba (😂 a dauri kashi ko a b'ata igiya), ita kanta idan ta zauna tana jinjinawa qoqarinshi, matsalar d'aya shine tana ganin kamar yafi nunawa Khairat soyayya, alhalin Khairat ko bai tab'a jikinta ba ita zata kai ga jikinshi, hakan yasa take ganin kamar yafi sonta ne. *Kwana sha biyar* da fara azumi Papa yayi aike gidan, mota guda aka aiko ta dinga sauke kayan abinci babu abinda babu, bugu da qari harda shaddodi da atamfofi, saida aka gama shigowa dasu kuma driver ya ciro enveloppe ya bawa Mama yace abawa malam inji mai girma baban Khairat, godiya dai kan anshata kuma shima yaji tukuici sosai, Khairat ma na d'aki bata san me ake ba, tana can tunanin bayin Allah da take taimakawa ya dameta, bata san a wane hali suke ba yanzun, gashi yanzu mahaifin nata na mata wuyar samu ko a waya saboda waya da harkoki suka masa, sai lokacin Fateema ta shigo ta kirata, fita tayi taga kayan ta tayasu murna. *A gurguje fan's* Haka suke tafiyar wa rayuwar, idan yana d'akin Khairat yana farin ciki, idan yana d'akin Zuby qorafi da fad'a suke takura masa, haka kuma har yanzu zaman na Khairat da Zuby ba dad'i, yayin da Khairat keta qunsawa Zuby baqin ciki kala kala, kullum da sabon tuggun da take zuwa mata dashi, kuma har yanzu sun kasa samun nasara a kanta saboda sau d'aya ta fita taje gida wajensu Papa tare da Umar Faruk, har yanzu bata sake fita ba har Umar Faruk d'in kanshi yana fad'in taje takai d'inkinta amma tak'i takai, kuma tak'i tafiya ne saboda tana da d'inkin da zata iya sakawa ranar sallah, gashi kuma Zuby har yanzu ta kasa sakewa da Umar Faruk kamar ba mijinta ba, (mutan da). Alhamdulillah rayuwa sauyawa take, Umar Faruk alert kawai yake ji hankali kwance, ga kuma albashin aikinshi shima yana samu, da wannan yanzun haka ya fara qoqarin kafa kanshi ta hanyar kama wani babban shago yana zuba takalma da jakunkuna wanda ake bugawa a wannan compagnie dana Khairat, duk da dai burinshi shine shima ya samu nashi ma'aikatar da zai fara buga nashi takalmin, komai na tafiya daidai saboda yana samun albashi mai tsoka sosai, da wannan arzik'in Umar Faruk ya fara bunqasa. *RANAR JAJIBIR* Saniya Umar Faruk ya yanka ya rabawa masara qarfi, bayan ya wadatan gidan da kaji😋da zabi, bayan sallah la'asar ya shiga d'akin Khairat ya samu tana kuka abinda ya jima bai gani ba a tare da ita, bayan rarrashinta da yayi ya tambayi me yake faruwa, cikin muryar kuka ta fara magana "Faruk bansan ya zanyi ba, bansan me nawa Papa ba ya hanani samun kud'i tako ina, Faruk ina jin kunyar su Mama saboda na kasa musu komai a bikin sallah, akwai mutane da dama wanda nice ke taimaka musu a wannan lokacin, nasan wasu zasu je gida nemana su samu bana nan, wasu kuma kirana a waya amma kunya ta kasa na d'auka dan babu abinda zan iya yi musu, dan Allah kaje ka bawa Papa hak'uri ka fad'a mishi ya taimakawa duk mutanen da yasan ina taimakawa, wallahi bana jin dad'i." Rumgumeta yayi jikinshi yace "yanzu akan haka kike zubar min da hawayenki? nifa na tabbatar babu abinda kika yiwa Papa, wataqila wani horo ne yake so ya miki, amma karki damu zan bashi hak'uri insha Allah, yanzu ki fad'a min nawa zai isheki biyan duk buqatun nan da kika zayyana?" Girgiza kai tayi tace "a'a Faruk, ka barshi kawai, ba zan yarda ka tauyeni ba akan me zan yarda ka tauye wata, da ni kad'ai gareka zan iya fad'a maka haka tun tuni, kuma kud'i ne masu yawan gaske dani kaina bansan nawa nake kashewa ba a kowane wata, ka barshi kawai." "Kenan har yanzu bamu zaman d'ayan da komai nawa naki ne, kuma komai naki nawa ne?" "Ba haka nake nufi ba, amma dai..." "Amma me? dan haka dole ki fad'a min." "Wallahi ni ban sani ba, kawai ka barshi kamar yanda na fad'a maka, zanfi jin dad'i idan ka gano min laifin da nawa Papa." Tabbatarwa da yayi ba zata fad'a ba yasa ya tashi ya bud'a wradrob d'inshi ya d'auko daurin kud'i yazo ya mik'a mata, kallonshi tayi ta fara girgiza kai hakan yasa ya d'aure fuska yace "ranki fa zai b'ace." Turo baki tayi gaba ba tare data karb'a ba, d'aga hannu yayi kamar zai mazgeta yana fad'in "zan gabjeki wallahi." Da sauri taja baya tana fizgo kud'in daga hannunshi, "nifa wallahi bana ssss.." bata qarasa ba Yusuf ya shigo d'akin da sallama cikin murya irinta yara, amsawa sukayi Umar Faruk ya d'aukeshi yana fad'in "babban mutum ya dai, ya azumin?" Baiko kulashi ba sai Khairat da yake kallo yana fad'in "aunty Mama na ciyanki." Cikin dariya ta aje kud'in hannunta akan gado ta tara hannu ta amsheshi duk da ba qarami bane tana fad'in "Mama ke kirana?" "Eh." ya fad'a, hanyar fita ta nufa tana fad'in "to muje." Umar Faruk ma bayansu yabi shima, suna fita suka samu Papa ne yanzu ma yayi aike, naman jajibir ne mai tarin waya da kuma kud'in cefane na sallah, yaron da aka aikone ya kalli Khairat ya bata enveloppe biyu yace "Alhaji ne yace abaki keda yar uwarki." Bata tankasa ba harya fita su Umar Faruk yabi bayanshi dan bashi tukuici, kallon enveloppe d'in tayi taga d'aya sunanta ne a baya da signature d'in mahaifinta, d'aya kuma sunan Zuby ne nanma da sa hannun Papa, tasan akwai dalilin da yasa ya saka suna, ba kuma zai wuce adadin kud'in ne ya banbanta ba shi yasa ya raba musu, da Yusuf a jikinta ta qarasa inda su Zuby ke aiki ita dasu Saratu ta mik'a mata ba tare data mata magana ba, a wulaqance ta kalleta tace, "Miye wannan d'in?" Itama a daqile tace "ki karb'a mana saiki duba ki gani." Saida taja tsaki ta karb'a tana kallon sunan da aka rubuta, kallonta tayi tace "wai miye wannan iskancin?" A hassale Khairat tace "ba iskanci bane, mahaifina ne yace a baki, kuma na tabbata yayi hakane saboda yana kallonki a matsayin 'yarsa kamar ni." Wani tsaki tayi kafin tayi dariya irinta daba tace "kiji wani rainin hankali, to an fad'a miki bana da hankali ne ko kuma sakara ce ni? to bari kiji wallahi asirinku ba zaiyi tasiri a kaina ba, kuma koba komai Allah ya kiyayeni naci kud"'in haram kud'in da bansan ta wace hanya aka samesu ba." Muryar Umar Faruk ce ta katsesu yana fad'in "waike me yasa baki da hankali ne, le kullum inba tsokano abinda za ayi tashin hankali ki kayi ba hankalinki baya kwantawa, gidan nan sai kace ni kad'ai ne mai mata kullum a masifa nake kuma duk saboda ke, ko kad'an ke baki d'auki iyaye a wata tsiya ba shi yasa baka jin kunyar aibata na kowa, to wallahi na gaji da wannan iskancin naki, nakai maqura ta qarshe dan haka ba zan sake yarda ba, ya zama karo na qarshe da zan sake jin kina mata rashin kunya, ke inma banda raina mutane da ki kayi ba itace gaba dake ba a komai, amma kuma tana hak'uri dake bata miki cin kashin dake kike mata, to wallahi kashedi ne na qarshe wannan, in baki ji bari ba zaki ji a jikinki ma ba hoho ba, yar rainin hankali kawai." Yana fad'a ya juya ya fita daga gidan, Khairat ma da yau takai maqura matsowa tayi kusan Zuby tace "ina da yaqini akan mahaifina cewa baya tab'a anfani da dukiyar daba tasa ba, sanin kowa ne da arziqinshi ya shiga siyasa, bawai yayi kud'i bane bayan ya fara siyasa, kin jima kina cin zarafina amma ina d'aga miki qafa, ki sani yau kin kaini qarshen da ba zan iya hak'ura ba, ya zama dole na nuna miki kuskurenki Zubeida, dole ki gane baki da wayo a duniyar nan, wallahi saina nuna miki banbancin dake tsakanina dake, Zubeida inhar bansa kinji kunyar mutanen gari ba ki canza min suna, Zubeida inhar gobe bansan kin kasa kallon kowa na gidan nan ba kice ni ba yar Na'ima bace, Zubeida inhar bansa kika kika tuhumi mahaifiyarki ba kice da zina Mani Bukar ya haifeni, wallahi gobe i warhaka ba zaki gane halin da kike ciki ba wannan alk'awarina ne." Aje Yusuf tayi tasa hannu ta share hawayen da suka taho mata masu zafi tana kallon Zubyn, da k'arfi ta fizge enveloppe d'in dake hannnunta ta nunata da ita tace "saina sa kin fahimci haramcinki tafi haramcin da kike tunanin kud'in nan na d'auke dashi insha Allah, wallahi zaki gani za kuma ki gane kurenki, daga gobe zaki fara tunani kafin ki zagi asalin mutum ko ki masa rashin kunya, banza kawai da baki san inda duniya tasa gaba ba." Tana fad'a ta juya ta shiga d'aki, aje enveloppe d'in hannunta tayi ta d'auki wayarta ta dannawa Bala kira, yana d'auka cike da girmamawa yace "ranki shi dad'e, barka da warhaka." A tak'aice tace "barka Bala." "Hajia ya hidima damu , ya k'ishin ruwa?" "Alhaji Bala magana nake so muyi da kai." "To to Hajia, ai lokacina gaba d'ayansa naki ne, ina jinki." Ajiyar zuciya ta sauke tace "kullum kana fad'a min girma da matsayin da nake dashi a wajenka, wani aiki ne nake so kamin a matsayin alfarma idan zaka iya." "Hajia, aiba alfarma tsakaninmu, ki bada umarni kawai aikina cikawa ne." "Na gode, Bala kasan me nake so dakai?" "A'a Hajiata sai kin fad'a." Juyawa tayi ta kalli kanta a madubi tace masa " lokaci yayi da ya kamata ka waiwayi ajiyarka da kayi shekarun baya, ina so ka amshi 'yarka dake hannun Asma'u." Jim yayi kafin yace "Hajia hakan nada alaqa da alfarman da zan miki ne?" "Hakan da za kayi taimakone bawai alfarma ba, Bala yarka na takura min sosai ta hanyar aibata min mahaifina kullum, ba wai burina na muzguna mata ba, danni ina da tabbacin nafi soyuwar a zuciyar mijinmu , idan so samu nane ina so mu zauna lafiya da ita, amma ita kullum cin zarafin iyayena ne burinta, kuma abinda za kayi bawai zaisa tabar gidan nan bane, kawai ina so ne ka fito a matsayin mahaifinta na gaskiya." Shiru ya sake yi sannan yace "Hajia wannan ba matsala bane, a gaskiya bata kyauta ba kuma banji dad'i ba, kuma na tabbata hakan na faruwa ne ta sanadiyar mahaifiyarta, dan Asma'u ba mutumci ne da ita ba, amma karki damu Hajia zanyi abinda ki kace bawai a matsayin taimako ba, a'a sai dan na taimaki kaina da kuma ita yarinyar, lokaci ne yayi da zan tono shukar dana binne tsawan lokaci, kuma lokaci ne yayi da zan sadata da yan uwanta su san juna, kawai ki fad'i lokacin da kike so Hajiata." Da wani mugun murmushi a fuskarta tace "gobe nake so." "An gama Hajia, Allah ya kaimu goben." "Ameen, zan fad'a maka lokaci da kuma kwatancin gidan." Tana fad'a ta kashe wayar, dan ita dama bata bari ku dindige take kashe waya , yana daga cikin ikonta da take nunawa, wasu matasa ta kira su uku tace su sameta gida, suna zuwa ta basu wannan kudaden wanda Umar Faruk ya bata dana wajen Papa harda na Zubyn duk ta lissafa musu inda zasu kai, gida na farko data fad'a musu shine gidan Alhaji Bala, sannan sauran gidajen mutane, dama kuma yaran sune ke taimaka mata kowace shekara, suna girmamata ta yanda kiran Allah dana iyayensu ne kad'aizai hanasu amsa kiranta. Tunda Umar Faruk ya fita bai dawo ba kasancewar daren sallah ne kowa baiyi bacci ba, mutanen gidan nata hayaniya Khairat kuma na d'aki tana tunanin hanyar da zata tara yan uwan Zuby da mahaifiyarsu a gobe, yayin da Zuby ma ke nata d'akin tana tunanin abinda Khairat ta fad'a, ganin ta kasa fahimtar komai yasa ta kira Mama ta fad'a mata, Mama ma hankalinta ya tashi sosai dan tana tunanin abinda zatayi, da tsoro da fargaba bacci ya d'auketa. Khairat ma haka saida tayi bacci Umar Faruk ya shigo gidan, bai kuma tasheta ba sai sumbatarta da yayi ya kwanta gefenta badan yana jin bacci ba..... *Gobe sallah, kuma gobe tonon...*😜 23/08/2019 à 12:51 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ *Ina alfahari daku*💕💞 5⃣4⃣ Kiran sallah asuba ne yasa Khairat bud'a ido, dan yanzu tana jin kiran sallah take tashin kanta, sauke idonta tayi akan Umar Faruk dake zaune yana kallonta shima, zaune ta tashi tana murza ido tana masa murmushi, cikin muryar bacci tace " kai kuma haka ake saika kasa tashina?" A shagwab'e yace "kema kuma haka ake sai kiyi bacci ba tare da kin jira mijinki ba?" Dariya tayi wacce bata da sauti tace "ka gafarci wannan sakaryar matar taka, har yanzu quruciya na damunta ne." Dariya yayi yace "nadai fahimci yanzu babyna yasa kin rage bani kulawa, amma ba komai girmanshi ne ai." Kamar zata fashe da kuka tace "baby, na fad'a maka fa banda komai, me yasa kake son tsokanata ne? ina so ko zan fara haifa maka yara sai mun qarasa cinye amarcinmu." Yanda take maganar yasa ya janyota jikinshi ya rumgume yana fad'in "ina laifi wanda muka ci ma, ai kawai ki fara antayo minsu a shirye nake." D'agowa tayi ta kalleshi tace "ko 'yan uku uku ne ka shirya?" "Ai ko 'yan shida shida ne zan karb'a." Dariya tayi ta fara qoqarin sauka daga kan gadon, da sauri ya rik'ota yana fad'in "bara na cajeki na gani, dan naga baki yarda kina da ciki ba." Saida ta sauka da qafafunta qasa ta juyo saboda ya rik'e qugunta ita kuma ta zagaya hannayenshi a wuyanshi suna kallon juna, kallon qirjinta yake da yaga ya mishi wani b'ulb'ul ya cika sai walqiya yake kamar ta shafeshi da man gyad'a, bakinshi yasa ya janye rigarta ya cabko kan nononta ya fara tsutsa har yana lumshe ido, itama rufe idon tayi tana qara danna kanshi tana shafar kanshi, jin yana tutsa hannayenshi cikin rigar yasa ta janye tana fad'in "baby." Kallonta yayi yace "ki tsaya mana na nuna miki kina d'auke da cikina." "Um um." ta fad'a tana maqale kafad'a. Hararanta yayi yace "kinsan zan gano gaskiya kenan." "Indai ba coge kake son min ba kamar yanda ka fara min wayo a farkon zamanmu ta hanyar samun kusanci da jikina, to ka fad'a min baki da baki kawai." Hannu ya mik'a mata yace "naji to zo kiji." Matsowa tayi tace "ina jinka to." Cikin wani irin kallo ya fara da "da farko dai na lura da sabon canji daga jikinki, saboda wannan kayan sun qara fitowa suna cika min ido sosai yayin da kullum suke min qwalele, sun cika fiye da baya kuma sai sheqi suke." duk yayi maganar ne yana shafarsu. "Na biyu kuma yawan bacci da kike yanzu, ke baki fahimci hakan ba amma ni uban yaro tuni na fahimta, na uku kuma baki son cin abinci yanzu." Dangware masa kai tayi tace "hamagon uba kawai." Cikin dariya ya sake kamo hannunta yace "ya kuma had'u da hamagiyar uwa ba." Tashi sukayi dukansu suka fita, alwala sukayi shiya wuce masallaci ita kuma ta dawo d'aki..... ************** Gaba d'aya akayi girki a gidan, hakan yaba kowa damar samun shirin tafiya Eid da wuri, kowa fitowa yayi cikin shirinshi mai ban sha'awa, Umar Faruk kam cikin dogon d'inki yake na shadda kalar ruwan zuma, hula takalma agogo duk wanda suka dace da kayanshi, Zuby ma na cikin shaddar daya siya mata da d'inki kalar data dace da ita, Khairat ma fitowa tayi cikin shaddarta baqa wulik wacce aka d'inke ko ina da kwalliya, idonka kad'ai zasu nuna maka d'inkin yaji kud'i ba kad'an ba, hijabin dake jikinta baqi da takalma baqaqe kalar kwalliyar kayanta ne, tunda ta fito sanyayyen qamshin turarenta ya bige Umar Faruk da sauran mutanen wajen ma, Zuby kuma d'inki da shaddar take kallo tana tunanin ita Umar Faruk ya raina ya siyawa wannan shaddar da bata banzan kud'in d'inkin da basu kai na Khairat ba. A motarshi su Ruk'ayya da sauran yara da kula matanshi😂 suka tafi, banda tsaki da hararan mutane ba abinda Zuby keyi, Khairat kuma da angonta da sauran yara kowa zikiri ne a bakinshi kamar yanda sunna tazo dashi, a haka suka isa babban masallaci sukayi sallah, ana idawa kuma bayan taya juna murna suka d'auko hanyar dawowa gida, koda suka zo kowa ya samu waje ya zauna aka zubo abinci a manyan plate, gaba d'aya mutanen gidan ne aka taru maza daban mata daban aka ci abinci amma a waje d'aya. Khairat kuma da tsarin ya birgeta kallonsu take cike da birgewa, Umar Faruk ma da kallonshi ke kanta suna had'a ido ya da hannun ya tambayeta lafiya, murmushi tayi ba tare da b'oyewa ba tace " ina kallonku ne, ganin kun taru gaba d'ayanku kuna farin ciki, sai naji inama ina da yan uwa nima, da yau zan tarasu gaba d'aya mu mori farin cikin wannan ranar, amma ni kad'ai, sai kuma ku dana samu a matsayin sabbin ahlina." Mama ce ta dafa kafad'arta tace " 'yata, ki d'auka mu naki ne, dukanmu nan mun zama d'aya kinji ko." Dariya tayi ta shafi kumatun Mama tace "na sani Mamana, nima ina kallonku kamar ahalina." Suna haka dai aka gama cin abinci, a qa'ida mazan ma basa fita sai bayan sallah azahar, hakan yasa Umar Faruk da uwar gidansa Khairat suka shige d'aki suna lobayyarsu, saida akayi sallah azahar suka fita Khairat ta kira wayar Bala, yana d'auka tace " kana da lambar mahaifiyarta ne?" "A'a Hajia, amma dai ina da wanda nake da tabbacin yana da lambarta." "Ok to ka samu lambarta, idan ka kira ka fad'a mata zaka karb'i 'yarka ne." tana fad'a ta kashe wayar. Baisha wahalar samun lambar Ma'u ba dan haka ya danna mata kira, cike da shaqiyanci yace "nasan ba zaki manta da muryar nan ba, dan haka ba buqatar fad'a miki waye ni." A gigice Ma'u ta mik'e tsaye tace "Bala, kaine ka kirani, lafiya, me yasa ka kirani?" "Kwantar da hankalinki ba abun damuwa bane, kawai dai ajiyar dana baki ce nake so ki maido min da ita saboda nine ubanta." "Kai Bala ka kiyaye ni wallahi, kasan me kake fad'a kuwa? to kaji da kyau, wannan 'yar da kake magana akanta, itace 'yar daka kasa d'aukar nauyinta kuma ka manta da ita har wannan lokacin, shine yanzu dan rainin wayo zaka wani ce wai 'yarka kake so, to ka fita idona wallahi, dan dama a qufule nake da kai dan ba yanda zanyi ne na qyaleka , ka rasa wacce zaka fad'awa wannan sirrin sai kishiyar yata, wallahi ka cuceni ka cuci 'yarka mugu kawai." "Bana kira bane danki fad'a min wannan banzar maganar, na kira ne danna fad'a miki zanje har gidan auren nata danna fad'a mata nine ubanta, kuma karki sake kirana da macuci, dan in kin kirani da wannan sunan bansan wane sunan za'a kiraki dashi ba, kuma ai kema mai laifince tunda kika aurar da 'yata ina raye, kuma da sunan wani uban bani ba." Yana fad'a ya kashe wayar tunda umarnin da aka bashi kenan, Khairat ya kira ya fad'a mata yanda sukayi tace mishi kawai yazo gidan yanzu, kwatanta mishi tayi kafin tayi kwance akan gado tana jiran zuwan Mama. Ai kuwa baifi minti talatin ba saiga Bala ya paka yar motarshi data sha jiki, su Sa'ad na qofar gida yasa suka masa sallama da Baba, fitowa Baba yayi suka gaisa kafin Bala ya d'ora da " malam nasan baka sanni ba, to nidai sunana Alhaji Bala, kuma nazo ne ina son ganin sarakuwarka Zubeida." "To, Zubeida kuma, meye had'inka da ita?" "Eh to malam babbar magana ce ta kowani, kuma zanso kamin izinin shiga ciki danna ganta." "Amma daka fad'a min abinda ke tsakaninku ai zaifi, tunda kaga matar aurene a gidan." "To nidai mahaifin Zubeida, kuma mahaifiyarta tasan da zuwana." 😱😱😱😱😱😱 _Kuyi hak'uri da wannan._ 23/08/2019 à 12:51 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣5⃣ Kallon mahaukaci malam ya masa yace "uhum, malam ina jin dai kayi b'atan kaine ko? amma inba haka ba ya za kace haka." Cewar Bala "malam, maganar nanfa tafi k'arfin tunaninka , ba kuma zaka tab'a fahimtar komai ba inba dama ka bani na shiga ciki ba." Tsayar taxi a qofar gidan yasa suka kalli Ma'u dake fitowa a hargitse, duk da kayan sallah ne a jikinta shaddar da Umar Faruk ya bata amma yanda ta fito yasa ba zaka gane kan shirin nata ba, a harzuqe ta qaraso wajensu tana kallonsu, a d'arare tace "Bala, kenan saida kazo nan, wai me yasa kake haka, wannan wane irin tonon asiri ne dan Allah?" "Kinga mushiga ciki ki fad'awa 'yata koni waye, inba haka ba wallahi anan zan tara miki Jama'a." Bud'e baki tayi zatayi magana kuma sai tayi shiru, juyawa tayi ta kalli mutanen dake kai da kawowa sannan ta kalli malam daya kafesu da ido, saita nutsuwarta tayi tace "naji mu shiga ciki, amma dan Allah kamin alk'awarin ba zaka fad'a mata komai ba, zamu shiga ne kawai ka ganta." Wata shed'aniyar dariya yayi yace " idan ganinta nake so nayi ai abune mai sauk'i, kinga fa lokacina kike b'ata min." Malam ne ya kalleta yace "Asma'u, kiyi hak'uri da duk abinda zai faru ki d'auka yau itace ranar da dubunki ta cika, kaga malam mu shiga ciki dan ba zan yarda ku tara min jama'a ba anan." Ganin sun shiga yasa dole tabi bayansu itama, abin haushin kuma kowa na tsakar gidan harda Zuby da kuma Khairat da bata jima da fitowa ba, gaisawa yake da mutanen yayin da malam ya janyo mishi kujera ya zauna, Bala kam ko kallon Khairat baiyi ba sai Zuby da yake kallo, a hankali yace " xyata, zo mana." Wani kallo ta masa ta tab'e baki ta kawar da kai, murmushi yayi ya kalli Ma'u yace "ki fad'a mata nine babanta tazo wajena mana." Mamaki ne ya fito kan fuskar kowa harda ita kanta Zubyn, Khairat kuma da farin ciki ta kalleshi tace "lah, ashe babanmu ne." Da sauri ta taso daga inda take zaune tazo gabanshi ta mishi irin neman albarkar indiawa tana fad'in "Baba ka sama min albarka." Jin abun yayi banbaraqwai,amma dan karya kwafsa yasa ya d'an shafi kanta yace "Allah miki albarka." Tashi tayi zata koma wajenta ta zauna Umar Faruk da Abbakar sukayi sallama tare da Ishaq, gaishe da Bala sukayi harda Umar Faruk dake mamakin ganinshi, danya tuna shine suka had'u a shago ranar, Bala ne ya kalli Umar Faruk yace "wannan ne surukin nawa ko? masha Allah Allah yayi albarka." Da mamaki Umar Faruk ya kalleshi yace " suruki kuma,amma bakai muka had'u da kai a....." Khairat ce tayi saurin cewa "baby surukinka ne baka gane ba, baban Zuby ne fa?" Maida kallonsu sukayi gareta har saida Bala ya fahimci hakan sannan yayi gyaran murya yace "bai sani bane ai shi yasa, amma yanzu kowa zaisan komai." "Kai, wai baka da hankali ne, tashi ka fita daga gidan nan?" cewar Mama. Zuby ce ta mik'e tsaye tace "a'a Mama barshi, nasan turoshi akayi, kuma ba kowa bace sai wannan shegiyar matar marar mutunci." "Ke." Bala ne ya daka mata tsawa tare da tashi tsaye shima, a hassale yake kallonta idonshi har sunyi ja, ganin abin fa ba qarami bane yasa Mama tattara yaran dake wajen tace suje d'aki, Bala ne ya kalli Ma'u cikin b'acin rai yace "Asma'u, kina jin irin furucin dake fita daga bakin wannan yarinyar amma baki tab'a taka mata birki ba, yanzu wannan maganar ta dace aji ta fito daga bakinta? to kinga ni ba b'ata lokaci nazo yi ba, ki fad'a mata ko wanene ni a wajenta kawai." Hannu biyu Ma'u tasa ta dafe ciki saboda murd'awar da yake mata, kowa kuma qura mata ido yayi yana kallo, Mama ce cike da nutsuwa tace " yar uwata, kinsan mutumin nan ne, meya kawoshi me kuma yake fad'a ne haka?" Wasu yawu ta had'e masu nauyi da d'aci tana kallon Mama, Umar Faruk ne ya kalli Khairat yace "meye haka, waya gayyatoshi gidan nan?" Da mamaki tace "ni kuma taya za ayi na sani, gashi a gabanka mana ka tambayeshi." Tsaki yayi sannan ya kalli Bala yace "dan Allah malam inba wani abu mai mahammanci bane ya kawoka zaka iya tafiya." Saida Bala ya kalli Ma'u ya kalli Zuby da Umar Faruk yace "wannan yar tawa nazo karb'a, karb'a kuma ba ina nufin zan rabaka da matarka bane, ina so ne ka ara min ita muje tare taga yan uwanta kawai." Salati kowa ya fara dake wajen ana kallon kallo, Khairat ma bud'e baki tayi cike da irin tana mamakin nan, Zuby da gabanta ke dukan uku uku ne ta qurawa Mama ido ta kasa d'aukewa, da qyar ta d'aga qafafunta ta matso kusan Mama tana ci gaba da kallonta. Cikin wani irin gunjin murya tace "Mama, kina jin abinda mutumin nan ke fad'a, shin da gaske ne?" Kasa jurewa Mama tayi sai hawaye da suka taho mata, sake maimaitawa tayi tace "Mama tambayarki nake, da gaske ne abinda yake fad'a cewar ni 'yarsa ce?" Da k'arfi ta fashe da kuka ta durk'ushe gaban Zuby tayi zaune tana rera kuka, hakan kuma ya bawa kowa tabbacin abinda Bala yake fad'a gaskiya ne, duk'awa Zuby tayi ta dafa Mama tace "Mama ki fad'a min gaskiya dan Allah, zuciyata bugawa take karta fashe." Kai Mama ta girgiza mata cikin matsanancin kuka tace "kiyi hak'uri Zuby, wallahi ban tab'a tunanin wannan ranar zata zo ba shi yasa ban shirya mata ba, kiyi hak'uri dan Allah ki yafe min, haqiqa wannan shine mahaifinki, kuma hakan ya faru ne lokacin da nake kallon mahaifinsu Uwani ba'a bakin komai ba, amma wallahi nayi nadama Zuby na tuba." Hawaye ne ke fitowa daga idonta amma ta kasa ko qyabta ido, lokacin da kanta yayi wata sarawa ne yasa ta kwamtsa qara mai k'arfin gaske ta qarasa zubewa wajen somammiya, ganin haka yasa hankalin kowa ya sake tashi, da gudu Khairat ta qarasa wajenta dan gaba d'aya ta manta da abinda ke tsakaninta da Zuby, zubewa tayi ta fara girgiza Zuby cike da tsoro da tunanin halin da take ciki take fad'in, "Zubeida, Zubeida ki tashi dan Allah, ki tashi Zubeida karki mutu, dan Allah ki tashi Zubeida karki dora min laifin mutuwarki , wallahi ba nayi haka bane danna saki wani hali, kawai nayi tunanin zan kub'uta ne daga yawan aibata iyayena da kike, dan Allah Zubeida ki bud'a idonki wal....." Bata qarasa ba Umar Faruk ya suri Zuby ya rumgume ya fita da ita yasa mota, kai tsaye asibiti ya nufa da ita inda ta kwanta kwanan baya, Khairat bata tashi daga wajen ba hankalin kowa baya jikinshi Ma'u ta d'auko tab'arya, a lokacin da Mama Maimuna ta kula lokacin tana daf da kaiwa ga Khairat, ai kuwa saita sauke wa Khairat ita akai, qarar da tayi tare da zubewa wajen yasa kowa ya kallesu, da sauri kowa yayi kansu dan kai mata d'auki, ganin ko motsi ba tayi itama yasa matan suka kamata suka sa a motar Bala aka nufi asibiti da ita, Mama ce ta fad'a mishi asibitin da zai kaisu, acan suka samu Umar Faruk da aka shiga da Zuby urgency, ganin halin da suka shigo da Khairat sai hankalinshi ya kuma tashi, ana shiga da ita itama ya fad'i zaune a qasa ba tare daya ma san ya zauna ba, cire hular kanshi yayi ya dafe kai hawaye na zuraro mishi, a hankali yake furta "inna lillahi wa inna ilaihi raju'un." Haka yake maimatawa tsawon lokaci har aka d'auki minti talatin, babu wanda ya zauna sai Umar Faruk da baya hayyacinshi, tunaninshi matanshi da baisan halin da suke ciki, kuma babu wanda ke cikin nutsuwarshi daya damu ya rarrasheshi ma, ana haka kuma wata likita ta fito daga d'akin da Zuby take, zunbur ya mik'e yana fad'in "ya ake ciki dan Allah, tana raye?" Kallon mutanen da suka kewayeta tayi kafin ta kalli Umar Faruk daya kawota tace "tana nan lafiya, jininta ya hau sosai, kuma ba'a son haka na faruwa dan zai iya janyo mata matsala, musamman qaramin cikin dake jikinta, dan Allah a dinga kiyayewa." Da sauri yasa hannu ya rufe ido yana sauke numfashi, a hankali ya furta "alhamdulillah." Jin qarar bud'a d'akin da Khairat ce ciki yasa suka sake d'unguma suna tambayar Jamila data fito daga ciki, qura mata ido kawai sukayi babu mai magana saboda murmushin dake kan fuskarta, kallon Umar Faruk tayi tace "yallab'ai zan maka albishir amma saika ban goron tukuici na." Da mamaki yake kallonta cikin dakusashiyar muryarshi yace "matata kwance a asibiti kuma kina maganar na baki goron albishir?" "Eh mana, saboda na gano maka tana d'auke da d'an qaramin cikinka." Wani irin bayyanannen farin ciki ne ya bayyana a fuskarshi tare da cakumo hannun Jamila ya rik'e jim yana fad'in "ki fad'i abinda kike so zan bakishi , tabbas kin kawo min albishir mai dad'i, kuma dole na muku babbar kyauta, dan wannan daidai yake da albishir d'in haihuwar yan biyu." Kowa na wajen dariya yake da farin ciki fal a fuska, saida ya basu tukuici duka likitocin kafin suka d'aukosu suka tafi gida, suna shiga Mama ta taso ta tarbi Zuby, hannu ta d'aga mata tace "dan Allah ki tafi bana son ganinki yanzu.", zatayi magana Mama ta dafata tace "ki barta kawai, yanzu ranta a b'ace yake, muje d'akina.", wucewa sukayi itama ta shiga nata d'akin, sai lokacin Umar Faruk ya kirasu Mamie ya fad'a musu halin da ake ciki, amma babban abin birgewa shine yanda mahaifiyar Khairat ta nuna kamar ba komai a zahiri, koda dai bata ji dad'i ba amma dai bata nuna mishi ba, fad'a mishi tayi zasu zo anjima su ganta, saida akayi sallah magrib Baba ya buqaci ganin kowa a d'akinshi, a lokacin Zuby na kwance a d'aki ta dunqule tana hawaye Umar Faruk ya shigo, saida ya tayar da ita zaune ya rumguma a jikinshi yace, "Meye kuma na kuka yanzu, shin baki san abinda kike dauke dashi bane? yanzu fa damuwa da tunani ba naki bane, ina so ki d'auki hakan a matsayin qaddarar rayuwarki, tunda dai ya tabbata wannan ne mahaifinki to kiyi hak'uri ki d'aukeshi a matsayin mahaifinki, damuwarki kawai nake buqatar ki kawar da ita ki tayani rainon d'an gatan nan, kinji ko." Ya qarashe yana kallon fuskarta, wasu hawaye ne suka sake gangaro mata kanta qasa ta kasa kallonshi, share mata yayi yace "haba dai, ba nace bana so ba, kina so nima na shiga damuwa ne, ko kuma kina so ki b'ata min rai ne?" Kai ta girgiza cike da nadama da qunci tace "yah Umar taya zan daina damuwa, ai dole na damu kuma nayi kuka, wanda nake tunanin shine mahaifina yau ance bashi bane, wanda nake kallon yan uwana nasu uwa d'aya uba d'aya yau an raba alaqar zama uba d'aya dasu, yah Umar yau naji kunyar kaina dana mutane, abin baqin ciki bata hanyar aure aka sameni ba, da aure akayi zina aka samu cikina, yah Umar me mahaifiyata ta zama haka, me yasa zata lalata min rayuwa, me yasa zata cutar dani haka? yanzu shikenan ta rabani da kai." "Ke ke." yayi saurin katseta, d'orawa yayi da "waya fad'a miki zamu rabu, ina tare dake har abada Zubeida, wannan abun ba zai zama silar dagulewar alaqarmu ba, ke baki ga yanzu ma muka sake gyara sabon zama ba, domin kuwa akwai ajiyata anan." ya qarasa da zolaya. Murmushi tayi tace "ka tabbata ba zaka rabu dani ba?" Kai ya girgiza mata yace "hanyar da aka sameki Zubeida ba zai shafi aurena dake ba, kuma koda baki mazaunin matata haka ta faru ai akwai aure tsakaninmu kuma zan iya aurenki, bare kuma kina matsayin matata, dan haka dan Allah kar kisa damuwar da har zata haifar miki da wata matsalar, ba zanso hakan ba kuma zan iya yin hushi dake idan kika ja mana matsala." Murmushi ta sake yi tace "shikenan yah Umar, na daina insha Allah ba zan sake ba." "Yawwa yarinyar kirki, tashi muje to Baba nasan ganinmu." Hijabi tasa suka fito, a qofar d'akin yace "kije zan kira 'yar uwarki." Da kai ta masa alamar to ta wuce d'akin Baba, da sallama ya shiga d'akin Khairat dake kwance akan qafar Mammie da basu jima da zuwa ba tare da Mamie, kallonta yake harya zauna yana kallon bandejin dake kanta, gaishe dasu Mammie yayi ya d'ora da "ya mai jikin?" "Ah jiki da sauk'i." cewar Mamie. "Allah ya qara sauk'i, ya kiyaye gaba." Da "ameen." suka amsa. Kallonta yayi yace "Khairat, Baba kesan ganinmu a d'akinshi yanzu, zaki iya tafiya?" Ta d'an dafe kai ta tashi zaune tana kallonshi, saida ta daidaita zamanta tace "zan iya mana, muje kawai." Tsaye ya mik'e tare da mik'o mata hijabinta tasa, hannunta ya kama suka fara takawa a hankali, suna daf da fita daga d'akin ta kalleshi tace " kuyi hak'uri Faruk dan Allah karku d'ora min laifi, nima ba'a son raina bane." Murmushi ya mata yace "karki damu, muje." Yana rik'e da ita har sukayi sallama d'akin suka shiga, kusa dashi ya zaunar da ita kafin suka maida hankalinsu ga Baba, kallonshi Baba yayi yace "amma ba naga mahaifiyarta sunzo ba?" "Eh Baba suna ciki." "To ka musu magana mana." cewar malam. Tashi yayi ya koma d'akin ya kirasu suma dan ayi gabansu, zaune sukayi suma ana kallon kallo, Baba ne yace "to alhamdulillah kowa ya hallara, kuma ba komai yasa na taramu ba sai dan kawo qarshen matsalar data kunno mana kai, da farko ina so nasan musabbabin matsalar danta hakane zamu yaki matsalar dan gudun sake faruwar haka anan gaba." Khairat ya kalla yace "Khairat, kinyi wata magana a lokacin da Zuby ta some wacce nake tunanin kinsan komai, shin zaki iya fad'a mana meya faru?" Kallon Zuby tayi ta kalli Mama ta kuma kalli Umar Faruk kafin ta kalli malam ta fara magana cikin taushin murya da rawar murya tace "sanin kanku ne inhar cacar baki zai had'ani da Zubeida, to sai tasa iyayena musamman mahaifina, jiya ma hakane ya faru lokacin da Papa ya aiko mana da kud'i nida ita, bayan bata karba ba saida ta fad'a min baqar magana da banji dad'inta ba, kuma Ruk'ayya da aunty Saratu shaida ne dan suna wajen, shi yasa ni kuma naci alwashin kawo qarshen matsalar ta hanyar bayyana mata mahaifinta na gaskiya, dama kuma nasan Bala tunda jimawa, kuma shine ya fad'a min ita 'yarsa ce da suka haifa bata hanyar aure ba, shi yasa nace yazo ya karb'eta koba komai zata san mahaifinta na gaskiya." Ajiyar zuciya malam ya sauke yace "to Zubeida kinji dalilin da yasa tayi haka, kuma inhar za abi ta gaskiya to kece kika tunzurata har tayi haka, a zahirin gaskiya ba zamu ce tayi kuskure ba, koba kamai ta taimakeki wajen sanin mahaifinki na gaskiya wanda mahaifiyarki ke b'oye miki, laifinta kawai data tona abinda bai kamata ace ta tona ba, da tayi hak'uri wataqila lokaci ne zai bayyana hakan, dan haka ina rokonku da ku gafarci junanku ku kuma yafewa juna, rashin had'a kanku da ku kaki yine ya janyo hakan, yana da kyau kusan shifa aure ibada ne, kuma qarin aure ma Allah ne ya hallata mana shi, fad'a da kuke da junanku sam bai dace ba, idan kuka had'a kanku kuka zauna lafiya, shi kanshi mijinku zaifi samun nutsuwa da kwanciyar hankali, haka kuma Allah zai qara yalwata mishi arziqinshi, dan haka ina sake baku hak'uri tare da shawartarku daku yafewa junanku dan Allah dan soyayyarku da Allah." Kallon da yake musu yasa Khairat sauke ajiyar zuciya ta kalli Zuby tace "kiyi hak'uri Zubeida, ki yafe min? nima kuma na yafe miki abisa komai." A cije Zuby tace "na yafe miki, nima ki yafe min." "Ba komai 'yar uwa." cewar Khairat. "To masha Allah, sai kuma ke Zubeida, ina so kisan abinda ya faru qaddara ce kuma jarabawa, kiyi iya qoqarinki wajen cinye wannan jarabawar, hakan zai qara hauda imaninki a wani mizani da zai qara miki qarfin imani, kuma karki saki ki kalli mahaifiyarki da wani ido dama idon rahama ba, haka shima mahaifin naki ki girmamashi dan saikin kyautata musu ne duniya da lahirarki zasuyi kyau, kiyi koyi da sahhabai da tabi'ai wajen hak'uri nuna soyayya da kuma cinye jarabawa ko wace iri ce, ki zama jarumar gaske wajen shanye abinda ke zuciyarki, kuma karki tab'a kallon Khairat da abun, hakan zaisa shaid'an ya sake galaba a kanki, kuma ki sani iyaye nada girma da darajar da babu mai ita a duniya idan kika cire Allah da manzonsa Annabi Muhammad (S.A.W)." Sosai malam ya mata nasiha daga bisani kuma sauran iyayen suma suka tofa albarkacin bakinsu, a haka suka tashi daga zaman cike da fatan alkairi, amma fa duk abinda aka tattauna ta bayan kunnan Mama yabi ya wuce, dan tayi niyyar saita d'auki fansa akan Khairat dama shi kanshi Bala... *Wasa farin girki* _Ku biyoni dan jin me kuma zaici gaba da faruwa yanzun._ _Wannan sadaukarwa ne ga *Ummu Fawzan,* sama da tsawon lokaci har yau tana tambayata lafiyar mahaifiyata, wanda zaiso mahaifiyarka babban masoyine wallahi, ina sonki sister_ 29/08/2019 à 14:33 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 *MUJI TSORON ALLAH AKAN DUK ABINDA ZAMUYI* _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣6⃣ Kwance take akan qafafunshi suna hira yana shafar kanta, bacci ne ya fara d'ibarta yanata surutu amma yaji shiru, leqa fuskarta yayi yace "wai bacci ki kayi?" D'an bud'a ido tayi ta kalleshi lokaci d'aya kuma ta maidasu ta rufe, dariya yayi yace "lallai aiki fa ya samu." "To shikenan tunda dai bacci kike, kinga gobe kenan ba zuwa gida gaskiya, dan ba zan kaiki ba kije kina musu bacci ba a gida." Tunda yaji shiru ya tabbatar bacci take bilhaqqi, dan da idonta biyu da zata tashi ta fara mishi rigima, gyara mata kwanciyar yayi yana kallon fuskarta yana yawo da yatsunshi a tsakanin fuskarta da qirjinta, saida yaji bacci na shirin d'aukarshi shima sannan ya tofa musu addu'a ya kwanta yana qara matseta jikinshi kamar za'a rabashi da ita. ************* Da safe kuma fitowa sukayi cikin shiri ita da Zuby saboda zai kaisu gidajensu ne duka su wuni, tare suka fita bayan sunyi sallama da mutanen gidan, gidan baya Zuby ta bud'a ta shiga Khairat kuma gaba, saida ya fara aje Zuby a gida ya shiga tare da Khairat dansu gaisa, duk sallamar da sukayi Mama bata amsa ba, gaisheta sukayi shima shiru ko kallo, tausayinta ne ya kama Khairat dan haka ta d'an matsa da nufin ta mata magana, da hannu ta nunata tace "karki kuskura wallahi, kinga raunin kanki yanzu zan miki wanda ya fishi, wallahi na tsaneki bani bake har abada, kuma zaki gani a cikin qwaryar cin tuwanki , bake kad'ai ba harda shi banzan Balan daya taimaka miki, wallahi saikun gane kurenku, saina nuna muku nayi nisan da bana jin kira, kuma kamar yanda banji tsoron bakin iyayena ba wallahi ba zanji tsoron bakin wasu ba, dan saina nuna muku bakin mahaifiyata na yawo dani har yanzu, zan ajiye sauran imanin daya rage mini domin na tarwatsa ratuwarki, kuma abin kunya ba gareni farau ba bare ya qare kaina, dan haka ba zan sake jin kunyar wani ko wata ba akan abinda nayi, tunda wasu sunyi fiye da abinda na aikata, kuma ki zuba ido kiga abinda zai faru, ba dai kin tona min asiri ba, to kema zan tona miki naki asirin, wallahi sai kinji abinda nida 'yata mukaji, ku b'ace min daga gida, har kai bana son sake ganinka." Da qyar Khairat ta iya tashi ta kama hanya, Umar Faruk na bayanta shima yana tunanin abinda Mama ta fad'a, tunda suka shiga mota babu mai magana harya ajeta gida suka shiga, ba wani kuzari haka suka gaisa sannan ya barta, yana fita Khairat ba tayi nauyin baki ba wajen fad'awa su Mamie abinda Ma'u tace, Mammie ce tace ta Allah ba tata ba kuma babu abinda zata gani sai alkairi, haka dai tayi wurin ranar ba walwala ba kuzari, sai bayan sallah isha'i yazo ya d'auketa daga nan suka wuce suka d'auko Zuby, wacce itama tayi wunin ba dad'i ba walwala, gidan suka wuce suka zuwa kowace tayi d'akinta Umar Faruk kuma yabi bayan Zuby dan itace dashi, saida ya tabbatar da Zuby taci ta qoshi kafin ya nufi d'akin Khairat, duk da ba komai take son ci ba da qyar tasha yaghourt ta kwanta itama. *DAGA WANNAN RANA* komai ya sauya sosai da sosai, Zuby ta zab'i zaman d'aki indai tana gida, shi yasa take jin dad'in tafiya school dan tafi sakewa acan, gida kuma ta daina kula kowa sai kula da Umar Faruk ke bata, ko akasi yasa sun had'u da Khairat a tsakiyar gida bata kulata, hakan kuma yana wa Khairat dad'i dan kowa harkar gabansa yake yanzu, cikin Zuby cikin ne mai dad'in raino , danko ciwon kai ba tayi sai cin abinci kamar tashin hankali, komai so take taci komai sha'awa yake bata. Sab'anin na Khairat dake wahalar da ita, sam bata son cin abinci sai Umar Faruk da Mama sun matsa mata take ci, shima kuma tana cinshi zata amayar, ga yawan zazzab'i, wani lokacin kuma matsanancin ciwon ciki da kasala, idan ta fara haka zata dinga rusar kuka tana matsar ciki, hakan yasa kowa yafi tausayinta fiye da Zuby dake garas da ita, Khairat uwar kwalliya amma yanzu wanka ma sai Umar Faruk ya taimaka mata take yi , harta manta rabon data d'iga kwalli a fuskarta, daga kwanci sai kwanci bata iya zaune na tsawon lokaci, hakan kuma ya shafi har zuwa wajen aikinta, danta daina zuwa yanzu saboda larura, gashi kuma yanzu Papa ya bud'e mata tattalin arziqinta tunda ya gane duk abinda take akanshi ne take, sai dai babu wani anfani da hakan yayi saboda bata cikin qoshin lafiya bare ta mori kud'in, kuma yanzu Umar Faruk ne ke musu duk abinda suke so, saboda bud'i kullum Allah yake masa. Mama kuma ba zama, kullum a tafiye take tana shiga lungu da saqo na gari dan ganin ta tarwasta Khairat kamar yanda take, kamar yanda ta fad'a ta murje idonta ta nuna kamar ba komai daya faru ta qara shiga duniya, tayi sabbabin qawaye yan duniya wanda suka qara kaita suna shirin barota, a cikinsu ne wata ta kaita wajen wani babban malamin tsibbu suka kai kukansu akan Khairat da Bala, a take ya fad'a musu zai nakasasu suje gida kawai su kwanta aiki ya qare, cike da kwankwanto Mama taje gida tana tunanin aikin malam d'in. ************* Yau ma kamar kullum Khairat ce a d'akin Mama kwance akan gado da d'an dabino a bakinta tana tsutsa, Mama ce tayi sallama ta shigo ta zauna qasa tana fad'in "to taso ga abincinki kici." Juya baya tayi tace "wallahi Mama bana son ci, dana ci amai zanyi." Kallonta Mama tayi tace "Khairat, kin rainani ko? idan da mijinkine ya miki magana d'aya da kin taso." Juyowa tayi tana kallon Mama ta tashi zaune, gyara siket d'inta tayi daya tattare sannan ta sauko qasa, janyo kwanan tayi tasa hannu ta fara laquta, tun kafin takai baki take jin amai na taso mata amma saboda Mama sai tayi k'arfin halin kai lomar, bata kai ga had'eta ba amai ya taho mata da gudu ta tashi tayi qofar d'akin ta tsugunna ta fara qheqashi, saida tayi kamar zata amaye kayan cikinta sannan ta kurkure baki ta dawo d'akin, a galabaice ta kwanta qasa tana rufe ido, Mama dake jin kamar ta zubar mata da qwalla ne ta d'auki wayarta ta kira Umar Faruk, yana d'auka tace "dan Allah kazo gida, abin yarinyar nan ya fara bani tsoro wallahi, tun jiya har yau babu wani abinda ya shiga bakinta ya zauna bata amayeshi ba." Cike da tausayi yace "shikenan Mama ganin nan zuwa, tana kusanku ne?" "Eh gata." ta fad'a tana bawa Khairat wayar, tana d'orawa a kunne yace "baby, kina so kisa gwarzon mijinki kuka?" Murya qasa qasa tace "a'a bana so." "To indai hakane ki fad'a min abinda kike so na taho miki dashi yanzu?" Shiru tayi tana tunanin abinda zata fad'a, duk iya tunaninta bata tuna wani abinda take sha'awar ci ba, a hankali tace "baby ba komai, ni kawai kai nake so kazo nayi kwance saman jikinka." Dariya ce ta kubce mishi yace "shi kad'ai kike so?" "Eh." ta fada tana turo baki gaba, cewa yayi "to ki d'auka an gama saboda kai da kaya ai duk mallakar wuyane." Cikin shagwab'a tace "uhm uhum, wayo ko? to na yarda kai da komai naka duk mallakina ne." "Dama haka nake nufi nima, gani nan zuwa." "Sai kazo." tana fad'a ta kashe wayar, bawa Mama tayi tanata juyi a tsakiyar d'akin, Yusuf ne ya shigo ya nufi wajenta ya zauna yana cin gyad'a, juyowa tayita kalleshi tace "d'an tanti me ake ci ne haka?" "Guciya." a cewar yaron. Ruf da ciki tayi ta tokare hannayenta ta amshi ledar gyad'ar ta cika hannu ta fara b'arewa tana ci, ganin tana ci yasa yaron ya sake mik'a mata ledar gaba d'aya ya tashi ya fita, jim kad'an sai gashi ya shigo da wata a hannu, suna haka kuma Umar Faruk ya shigo, kusanta ya zauna yana aje ledar hannunshi yana fad'in "Ina kuma aka samu gyad'a?" Yusuf kawai ta kalla ba tayi magana ba, Mama kuma tuni ta tashi ta fita dan tasan sai sun saiyar da halinsu a gabanta ma, ganin Mama ta fita ta matsa ta d'ora kanta akan cinyarshi tana kallon fuskarshi, shafa fuskar yayi yace "tashi kiga abinda na kawo miki, kuma nasan zaki soshi sosai." Janyo ledar yayi ya fara fito da abin ciki ita kuma ta tashi zaunen, kifi ne soyayye ga bala'in zafi 😋 zaiyi dad'in ci, da sauri ta rufe hancinta tana fad'in "meye wannan kuma? ka rasa me zaka siyo min sai kifi." Kallonta kawai yake ya kasa magana, cike da b'ata rai tace "dan Allah baby ka fitar dashi wallahi amai zai sani." Shi kuma mamaki ma ya hanashi motsi gani yake kawai dagangan takeyi, bud'a baki tayi tace "bab......" da gudu ta qarasa fita daga d'akin sai kuwa amai, ganin haka yasa ya tashi yabi bayanta, kallonta yake tana yunqurin aman sosai daga ruwa sai gyad'ar da taci, d'akin ya koma ya d'auko kifin ya nufi d'akin Zuby dashi dan yasan ita tsaf zata handameshi, wucewa yayi yaji su Mama Sa'a na magana akan wahalar da Khairat kesha, da sallama ya shiga ya samu tana bacci, daddabata yayi ta tashi zaune da d'aurin qirji saboda zafin dake akwai, aje ledar yayi qasa yana fad'in "ga kifi nan." A yamutse ta kalleshi tace "wallahi yah Umar bana son turaren nan naka, tayar min da zuciya yake sosai da zaka daina anfani dashi da naji dad'i." Murmushi yayi yace "to nama fita daga d'akin gaba d'aya, kici dai kinji ko." Binshi tayi da kallo harya fita, qasa ta zauna ta samu kifin nan taci abinta sosai ta qoshi, saida ta gala ta fito ta wanke hannaye ta koma d'aki.... Kwance ya samu Khairat a tsananin galabaice abin tausayi, duk ta rame ta fita hayyacinta sai ido masha Allah, a lokacin Mama na d'akin ta kalleshi tace "Umar Faruk, ko dai zaka kaita gidansu ne ta wuni, wataqila idan taje ta d'an saki jikinta har taci wani abu, amma inba haka ba da matsala gaskiya, kuma idan zaku tafi ka biya asibiti adubata dan Allah." "To Mama." Kallon Khairat yayi yace "tashi mu tafi ko." Lokacin kuma wani bacci ne yazo mata, da qyar tayi tsaye tasa hijab dan yanzu zamanta d'akin Mama yafi yawa, slipas d'inta tasa tace "muje." "Haka zaki tafi?" cewar Umar Faruk, kallonshi tayi kafin tayi magana Mama tace "to danAllah wanda yake takanshi me kake tsammani dama." Haka suka wuce suka kama hanyar asibiti, kuma wannan fitar ita ta zama silar qara lalacewar komai, zaune suke gaban Sadiya bayan ta gama fad'a mata abinda ke damunta, had'e hannayenta tayi tace "cikin naki yakai wata nawa?" Kallon Umar Faruk tayi shima ita yake kallo kafin tace "uhum, wallahi ban sani ba." Dariya suka saka mata ita da Umar Faruk kafin tace "yanzu ciki a jikinki kice baki san watanshi nawa ba? kai Khairat Allah ya shiryeki wallahi." Umar Faruk ta kalla tace "yallabai, dole zamu mata éco (scanning) muga lafiyar cikin nata, dan ciwon cikin shi yafi zama matsala, zai iya yiwuwa cikin ne ya shiga cikin mara ko ya fita daga mahaifa, amma yanzu idan muka mata eco sai muga lafiyarshi." "Ba damuwa madam." Tsaye tayi tace ma Khairat ta taso, shamakin dake tsakanin gadon mai jiya suka shiga ta kwantar da ita, da mamaki take kallon Khairat dan a iya ganinta bata ga ciki a jikinta ba, photon ne ya fito suka fito daga wajen, zaune sukayi ana kallon juna sannan ta sauke numfashi tace , "Khairat kin tabbatar kina da ciki?" Da mamaki Khairat tace "alamu na nuna min haka, kuma a asibitin nan ne aka fara fad'a mana haka." "To a gaskiya ni dai banga wani ciki ba a jikinki Khairat." "Me?" cewar Umar Faruk, d'orawa yayi da "me kike nufi da da bata da ciki? dubi fa yanda ta koma saboda laulayi, kuma a hakan ne bata da ciki." Khairat ma kallonta tayi tace "Sadiya, kin tabbatar da abinda kike fad'a kuwa, ko dai cikin yabi wata hanyar ne daban kamar yanda kika fad'a d'azu, amma inba haka ba ina shan wahala fa sosai." "Wallahi na tabbatar da haka, idan kuma baku yarda ba kuje wani wurin a duba muku." Kallonta Umar Faruk yayi ya kama hannun Khairat suka fita, kai tsaye wata asibitin suka nufa, nanma dai abinda aka fad'a musu kenan, saida sukaje asibiti har hud'u duk sakamako d'aya ne, tashin hankalin da Khairat ta shiga yafi wanda Umar Faruk ke ciki, kuka ta dinga yi a cikin motar har suka isa gida, tare suka shiga kuma da kanshi ya fad'a musu halin da ake ciki, Mamie da Mammie dake shirye shiryen komawa india ma duk hakalinsu ne ya tashi suma, nan ya barta ya tafi da niyyar dawowa da dare ya d'auketa. ************** Tun tafiyar Umar Faruk Khairat ta rikice musu cikin gidan, wani zazzafan zazzab'i ne ya rufeta mai tsananin zafin gaske, har saida Mammie ta dinga sakawa hijabinta ruwa suna rufeta dashi, ba kuma zazzab'i kawai ba ciwon qafafu da hannaye kamar ba'a jikinta, zafi take ji mai rad'ad'in gaske wanda bata tab'a jinshi ba bare ta kwantata, hawaye kad'ai ke iya fita daga idonta ta kuma nemi addu'a a bakinta ta rasa sai a zuciyarta kad'ai take iya istigfari da tasbihi, Mamie ganin abin bana qarau bane yasa suka kira Umar Faruk yazo, har d'akinta da take kwance ya shiga, kallonta yake sosai har yana karkace kai, so yake ya fahimci abinda idonshi ke hango mishi a tare da ita d'in, wani murmushin takaici yayi ya cije gefen labb'anshi ya kalli Mamie yace "zamu tafi gida, komai zaiyi daidai." Da kanshi ya d'auketa ya kaita mota sannan suka wuce gida, da kanshi ya shiga da ita cikin gida kai tsaye d'akin Mama ya wuce da ita, duk uwayen gidan binshi sukayi suna tambayar lafiya, yana cikin fad'a musu Khairat ta bud'a ido, fashewa tayi da qara mai k'arfin gaske tana fad'in ya mayar da ita gida wajen Mamie, rik'eta ya fara yi yana so tayi shiru amma ina shure shure kawai take, zaune yayi kusanta cikin daka tsawa yace "kalleni nan." Bud'a ido tayi ta sauke a kanshi take ta kuma d'auke idonta, hakan ya tabbatar mishi da abinda yake zargi wato sharrin shed'anu ne, janyota yayi jikinshi ya rumgume yasa bakinshi a kunnenta yana mata karatu, fizge fizge ta fara sosai tana gunjin kuka tana so ta k'waci kanta, wani shegen rik'o yayi mata yasa ta kasa kubcewa, har saida ta fara rera kukan a hankali tana sauke ajiyar zuciya sannan ya kwantar da ita, a haka kuma bacci ya d'auketa, tashi Umar Faruk yayi ya fita yana ci gaba da fad'awa su Mamie abinda ya faru, a haka ya fita sallah magrib yana mamakin sabon al'amarin daya b'ullo musu. ************** Tana farkawa ta sauko daga kan gadon ta fito duk a yamutse da ita, Mama na k'ofar d'akin akan sallaya taga fitarta, bata mata magana ba saboda ganin yanayinta, Zuby ce ta fito daga d'aki suka kalli juna, wata shegiyar qwafa Khairat tayi ta wuce d'akinta, Zuby ma tab'e baki tayi ta wuce sabgar data fito da ita. Tana shiga d'akin taji ya mata zafi sam ba zata iya zama ciki ba, a turmuje ta ciro akwatinta ta fara had'a kaya, Umar Faruk na shigowa na nufi d'akin Mama, da hannu ta masa alama tana d'akinta, wucewa yayi kai tsaye yana shiga ya tsaya yana kallonta, qarasowa yayi ya zauna gefen gadon yana fad'in "yadai, tafiya zamuyi ne?" Ko kulashi ba tayi ba sai ci gaba da had'a kayan da tayi, tsaye yayi bayanta dan yaso ya fahimci halin da take ciki, cikin wata irin murya da baya yinta inba marar lafiya ya samu ba da zai taimakawa ba yace "ke." Cak ta tsaya amma bata juyo ba, sake maimaitawa yayi cikin amon murya yace "dake nake, kalloni nan." A hankali ta juyo ta sauke idonta a kan nashi, amma saboda bala'i da kwarjini da tsoro kawai saita zube qasa ta fashe da kuka cikin muryar da daga ji ba tata bace ta fara cewa ita kawai ya kaita gida bata san zama anan, banza yayi da ita ya d'auki cup ya zuba ruwa ciki ya fara yan karance karancenshi duk yana kallonta, koda ya gama tofawa a cikin ruwan ya taso yayo kanta, tana ganin haka ta zabura ta tashi tsaye tana ja da baya tana fad'in "a'a, a'a, karka matso kusa dani, kar kayi fa, wallahi zaka cutar da ita a banza, zafa ka iya kashe abinda ke cikinta, a'a zaka jamata fa." *Allah my sister na,😭 na tuna lokacin da kika sha wannan wahalar, a lokacin da naje gidanki da niyyar jinyarki, amma a qarshe sai tare muka dawo gida,😭 kai anga rayuwa fa, wallahi wannan ciwon na Khairat da nasa bawai qirqira bane, sak irin ciwon da sisterna tayi ne, Allah ka qara karemu daga sharri masharranta*👏 Saboda an saba gwagwarmaya irin haka yasa bai kula da abinda suke fad'a ba, hannu yasa ya d'ibi ruwan ya watsa mata ruwan, wata qara ta kwamtsa tana numfashi sama kamar zata d'auke rai, cikin gunjin kuka take fad'in "ka daina, ka daina haka." Fuskar nan a daure ya aje cup d'in ya zauna kan gadon yana fuskantarta yace "fad'a min, meya kawoku jikinta, meta muku da kuke neman cutar da ita, akan wani dalili kuka shiga jikinta? kuma idan kuka min qarya wallahi jikinku zai fad'a muku." Cikin wata irin tsawa yace "maza zauna nan." Zaune tayi inda ya nuna mata tana susar jiki saboda rad'ad'in ruwan daya zuba mata a jiki, cikin muryar daba tata ba ta fara magana.... _Ikon Allah, lallai ta bakin Mamien mu tace namijin duniya, yau kam na tabbatar, to amma kuna ganin zasu fad'i gaskiya ne?_ *WASA FARIN GIRKI.* 29/08/2019 à 14:33 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ 💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘 *TASKU* 💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘 _*My BK,* ina tayaki murnar fara wannan novel naki mai cike da abin al'ajabi, Allah ya baki ikon kammalashi cikin qoshin lafiya da hazaqa, fatan alkairi masoyiyar *Meerah.*_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Ohhh my sweet and lovely *Heenat*, kin tuna min da wannan had'uwar nima, ba zan tab'a manta ranar nan ba, soyayya hadin Allah ce kuma shi yake sakata a zuqatan bayinshi a sanda yaso, *My HEENAT* kin tambayi me nake so ko? to abinda *Meera* take so shine ganin kyakyawan murmushinki a koda yaushe, soyayya kuma *Meera* ta samu daga Heenat, dan haka kisha zamanki ki huta, Allahn daya had'a shine zai raba da izininshi._ 😘❤😘 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣7⃣ "Umar Faruk, mun maka farin sani shi yasa muka shirya da kyau kafin shiga jikin matarka." Suna fad'a da iya k'arfi aka fizgi Khairat aka bugata ga bango, take ta fad'i gurin kamar babu rai, da sauri Umar Faruk yayi kanta ya rik'eta, "Khairat, Khairat." D'aukarta yayi ya aje kan gadon ya d'auko cup d'in ruwa ya shafa mata, numfashi ta sauke da nauyi amma bata bud'a ido ba, ajiyar zuciya ya sauke saboda ganin tana sauke numfashi a hankali, a zuciyarshi kuma yana tunanin hanyar da zaibi wajen magance matsalar, danya lura suna son cutar da Khairat ne kawai da abinda ke cikinta, duk da ance babu shi amma bai yarda ba, yana shafar kanta yana kallon fuskarta data fita tayi fiyau da ita duk ta rame ta fice, qwaqwasa qofa yaji yasa ya tashi ya fita, Mama ce tsaye tace "Umar Faruk har yanzu jikin nata?" Saida ya juya ya kalleta daga qofar d'akin yace "har yanzu Mama,amma ta samu bacci yanzu." "To kazo mahaifinka nasan ganinka." "To Mama." ya fad'a yana saka takalmanshi. D'akin malam suka shiga da sallama suka zauna a tare, Baba ne yace "Umar Faruk mahaifiyarka ta fad'a min abinda ya faru yau d'in nan, nayi mamaki sosai tare da jimami, amma abinda nake so ka sani shine, babu abinda ya samu cikinta, kuma yana nan cikin qoshin lafiya kuma da yardar Allah za'a haifeshi/ta, dan haka ba sai na fad'a maka abinda za kayi ba, nasan kasan abinda ya dace da ita, amma idan kaga akwai cutarwa ga lafiyarta ko abinda ke cikinta saika sassauta kabi a hankali, kaji ko?" "Naji Baba, kuma nima abinda na fahimta kenan, kamar suna sob cutar da ita ne saboda yanda suka bar jikinta a yanzun, amma dai insha Allah basu fi k'arfin addu'a ba." "Allah ya kyauta." cewar Mama da Baba. Kallon Mama yayi kallo na tsanake yace "komai muqaddari ne daga Allah, ciwon Khairat kuma yana da sila kamar yanda ko mutuwa akance ga sila wani lokacin, zuciyar Khairat fara ce Mama bata qullatar kowa, amma tanti ta kasa fahimtar hakan har tana so taga ta cutar da ita, bai zama lallai na iya yin shiru ba Mama, amma dai zan qoqarta naga mun rabu da lafiya da shed'anun aljanu da kuma shad'anun mutanen, amma wallahi sukayi taurin kai, to Mama sai dai kiyi hak'uri, dan gaskiya zansa su koma kan wanda ya turosu, ba wai zargin tanti nake ba a'a tabbas ne nake da itace." duk da dai ranshi a b'ace yake, amma baya jin zai iya cutar da yayar mahaifiyarshi, kawai ya fad'i haka dan ya bada tsoro. Baba ne yace "Umar Faruk, ina kasan haka, me yasa kace itace?" Baba ya kalla yace "da bakinta kuma a gabana ta furta kalamai marasa dad'i akan Khairat, ban damu bane saboda nasan gidan nan na cikin kariyar ubangiji, kuma Khairat d'in yanzu bata da bace, kullumtana cikin karatu ne da kuma ibada, saboda ta gyara halayenta marasa kyau domin son rabauta, kuma tun ranar da tanti tayi wannan maganar ban tab'a kwanciya bacci ba ba tare dana tofa mata addu'ar bacci ba da kaina, koda kuwa ba'a d'akinta ba nake, hakan daya faru ya sake tabbatar min lallai sihiri gaskiya ne kuma zai iya shafar kowa idan Allah yaso hakan." Ajiyar zuciya Mama ta sauke wacce ke sairaranshi gabanta na fad'uwa, shirun da iyayen sukayi yasa ya tashi yana fad'in "saida safenku iyayena." D'akin Zuby ya fara shiga ya sameta kwance tun d'aurin qirjin daya sameta dashi da rana, tuhumammen kallon da yake mata yasa ta tashi zaune tana kallonshi itama, ita ba tace komai ba shima kuma baiyi magana har tsawon minti biyu, da qyar ya iya cewa "kin samu labarin abinda ke damun 'yar uwarki?" Cike da rashin kulawa tace " a'a, meya sameta?" Gyara tsayuwa yayi yace "da kyau tunda baki sani ba, na d'auka kina da labari ne danna miki hannunki mai sanda, amma duk da haka ina fad'a miki da kuji tsoron Allah Zubeida, kusan zaku koma gareshi kuma wallahi zai mumu hisabi, baya kuma yafe haqqin wani akan wani bare ka samu alfarma, lahirar nan da kika gani mai kad'aita Allah ne kad'ai ke shigarta ba wanda yake neman biyan buqata ga waninsa ba, kuma nine Umar Faruk kin samu, bai kamata a cutar da wani ba saboda kawai ana so a rabamu ko *d'aukar fansa* a kanshi." Matsawa yayi kusanta ya sunkuya yasa hannu ya shafi cikinta yana kallon idonta yace "ina fatan yana lafiya, kinci abinci?" Kai kawai ta d'aga masa, d'agawa yayi ya shafi kumatunta ya manna mata sumba a d'aya kumatun yace "ki kula da kanki, saida safe." Fita yayi kai tsaye ya nufi d'akin Khairat, yana so ko da Zuby nada laifi ya lallab'ata saboda cikin dake jikinta, kuma koba komai addini ya nuna ka rabu da mace da kyautatawa, tunda baya da hujja akan lallai da hannunta ba zai matsa mata ba, kayanshi ya cire yayi wanka yazo ya shirya duk Khairat na bacci, saida ya zauna ya d'auki littafi mai tsarki zai fara karatu kawai ta farka tana dafe qeyarta data bugu sosai, fashewa tayi da kuka tana shirin sauka daga kan gadon, tasowa yayi ya hau gadon yana so ya lallab'ata, kuka take sosai tana fad'in ya kaita gida ita ba zata zauna nan ba. Yayi rarrashin duniya amma tak'i shiru kuma gashi dare yayi, duk iyayen gidan babu wanda ya ritsa saboda rigamar da Khairat keyi, saida suka ga abin bana qarewa bane suka samu suka kwanta, amma babu inda suka kai aka kira sallah asuba, rana ta farko a tarihin rayuwar Umar Faruk da yayi sallah a gida, hakan yasa yaji abin ba kan gado saboda rashin sabo, yana gamawa yace mata ta tashi tayi sallah idan ta gama ta shirya ya kaita gidan, tashi tayi ta shiga douche ta kama ruwa ta d'auro alwala, fitowa tayi daf da zata shiga d'aki taji anyi sama da ita an buga qasa, qara ta saki wanda tasa Umar Faruk fitowa da gudu gudu, taimaka mata yayi suka shiga ciki, ganin yanda take dafe bayanta yasa yace "baki ji ciwo ba ko?" A marairaice ta kalleshi tace "akwai zafi mana, bafa santsi ne ya kayar dani ba, amma dai ina mamaki." "Karki damu kinji, je kiyi sallah ki shirya muje." Hijabi tasa a matuqar galabaice saboda babu komai a cikinta, da qyar ta gama sallah ta tashi zata shiga wanka, ganin yanda take yasa Umar Faruk zaunar da ita ya d'auko fresh milk ya bata, ji tayi har yawunta na tsinkewa tana so tasha, da azama ta daga ta fara sha ba qaqqautawa, saida ta gama ta tashi Umar Faruk yace "muje na miki wankan." Tare suka shiga ya fara mata wankan, suna cikin yi sai kuwa amai, saida ta amaye fresh milk d'in kad'ai aman ya sarara mata, haka suka fito kafin ya shiryata ya sake d'auko wata madarar da ayaba da kankana ya bata, da qyar taci ayaba guda biyu bata sake cin wani abu ba bayan ita. Fitowa sukayi ya shiga da ita d'akin Mama, da sallama ta shiga ta zauna tana d'ora kanta a qafar Mama tace "ina kwana Mama." "Lafiya lau Khairat, antashi lafiya?" "Lafiya lau Mama." "Ya jikin naki da dama?" Saida ta tashi zaune tace "da dama Mama." Ruk'ayya ce ta sallamo ta aje kwano gaban Mama tana fad'in "auntyna kin tashi lafiya?" "Lafiya lau Ruk'ayya." ta fad'a tana bud'a kwanon, ganin d'umamen tuwo sai qamshin man shanu ke tashi ya birgeta sosai, kallon Mama tayi tace "Mama ina so naci amma." "Indai kina so kici yata kici kawai, idan kina sawa ranki komai ki kaci zakiyi amai to da kinci kuwa sai kinyi." Kallon Umar Faruk tayi tace "baby bara na d'anci kad'an saimu tafi." Shi kam farin cikine ya kamashi tare da mamakin wacce ke kuka sai an kaita gida, hannu tasa tana d'an qwalbatar tuwon tana kaiwa baki, ji take kamar taci ta qoshi amma yanzu haka zuciyarta ce ke tashi, cire hannu tayi suna kallonta harta wanke ta dawo d'akin ta kalli Ruk'ayya tace "ki bani dabino dan Allah." Ledar dabino Ruk'ayya ta bud'e ta ciko hannu ta bata, karb'a tayi tana fad'in "ke qaro min malama." Da dariya Ruk'ayya ta qaro mata sannan sukawa Mama sallama suka tafi, tafiya suke a hanya tanata gwaigwayar dabinonta harta fara d'an b'ata rai saboda aman dake taso mata, hannunshi ta rik'e da yake tuqi ta kalleshi, alama kawai ta mishi ya tsaya, kai ya girgiza mata shima ba tare daya tsaya ba, tafiya suke ba mai magana har wayarshi tayi qara. D'agawa yayi suka gama hirarsu duk tana jinshi, saida ya gama ta kalleshi tace "akan me kake magana?" Ajiyar zuciya yayi ya kalleta yace "har yanzu muna kan magana ne bamu tsayar ba, dan haka ban fad'awa kowa ba." Kallon titi yayi yace "ina sone na tashi nawa compagnie nima." Murmushi tayi tace "naji dad'i kuma na maka murna, Allah ya sanya alkairi." "Ameen, yanzu ciniki ya fad'a, biya kawai zanyi kafin muje mataki na gaba." Da wannan tattaunawar suka isa gida, har ciki ya shiga suka gaisa sannan ya musu sallama ya tafi, kwance tayi akan kujera Mamie tayi saurin cewa "kije d'aki mana ki kwanta za kifi sakewa." Zaune ta tashi tana yamutsar fuska, Mammie ce tace "me kike so a dafa miki kafin ki tashi?" A yamutse tace "dambu zanci." "An gama shalelen Papa." cewar Mamie. Tashi tayi zata nufi d'akin Mamie kawai qafafunta suka kasa d'aukarta, zubewa tayi qasa kamar wasu kayan wanki, Mamie ce ta tashi ta kamata tana salati, zaunar da ita tayi tana kallonta da mamaki, matsa qafafunta tayi tace "Mamie, kamar ba qafafuna ba, wallahi ciwo suke min sosai." Kallon juna sukayi da Mammie, kafin kace kwabo kuma sai ciwon ciki mai tsananin gaske, Papa suka kira yazo gida yaga halin da take ciki, tausayi ta bashi sosai harya kira likita yace yazo ya sameshi gida, koda likita ma yazo shi cewa yayi baiga wani abu dake damunta ba, amma su kaita asibiti a duba lafiyar d'an cikin nata, Mamie ce tace ya tafi kawai sunji, yana tafiya ta kira Umar Faruk yazo, ruwa suka bashi a cup a mata addu'a, zai bata tasha tace ai ina bai isa ba, saida su Mamie suka kama mish suka d'ura mata ruwan tasha sannan taji sassaucin ciwon kamar an cire mata qaya, daga nan kuma bacci ya d'auketa. **************** Tunda Zuby taji fitarsu ta kira Mama duk da yanzu ba wani sosai suke waya ba, kira ta dinga yi amma ba'a d'agawa harta gaji ta daina, amma maganganun Umar Faruk na mata yawo har yanzu a qwaqwalwa, tana haka Ruk'ayya ta kawo mata nata abincin, gyara zama tayi ta handami abinta ta qoshi sannan ta d'auki kayan karatunta ta fara tilawa dan suna daf da fara jarabawa kwanaki suka rage musu. ****************** Koda yaje daukarta ma ya sameta kwance ranga ranga, Mammie na gefenta tana share qwalla, zaune yayi yana tambayar "Hajia lafiya kike kuka, meya faru ne?" Cikin kuka Mammie tace "wannan wane irin laulayi ne yarinyar nan take, tunda ka kawota gidan nan har yanzu wallahi ko ruwa tak'i sha idan ba ruwan addu'a daka bata ba, taya mutum zai rayu to a haka bare d'an cikinshi, gaskiya nidai abin ya fara bani tsoro." "Hajia dan Allah kuyi hak'uri ku daina kukan nan, insha Allah babu abinda zai faru sai alkairi, ku tayi mata addu'a kawai ita take buqata daga gareku." Ganin tana bacci yasa yace "ni zan tafi Hajia, tunda ta samu bacci ba sai an tasheta ba." "To shikenan, saida safe." A haka ya tafi gida rai ba dad'i ya fad'awa su Mama abinda ake ciki, d'akin Zuby dole ya kwanta amma baiyi bacci ba, yana cikin tsayuwar dare Papa ya kira wayarshi...... 😭😭😭😭 Yana d'auka Papa yace "Umar Faruk jikin yarinyar nan fa yayi tsanani, koda wani abinda da kuke bata ne?" "Subhanallah, Papa ku d'ora mata wayar a kunne." D'ora mata yayi shi kuma cikin taushin murya yace " Khairat, me yake damunki?" Cikin matsannancin kuka tace "Faruk mutuwa zanyi, mutuwa zanyi Faruk, ciwo nake ji tako ina a jikina, ba zan iya cewa ga abinda yake damuna ba, amma dai bana jin dad'i ko kad'an, Faruk ka taimaka min dan Allah bana son cikin nan wallahi, dan Allah ka taimaka ka cire minshi kafin na mutu." Saida taji numfashinshi cikin kunnenta, a hankali ya lumshe idonshi daga inda yake tsaye, wasu hawaye ne masu zafi suka zubo mishi, tsantsar tausayinta ne ya lullub'eshi, saida ya saita nutsuwarshi yace "haba baby, ya kike fad'an haka? komai yayi farko yana da qarshe, kowace uwa da kika gani a duniya da kalar nata wahalar da tasha kafin ta haifi abinda ke cikinta, kema kamar hakane Khairat, ki sani wannan d'anki ne ko 'yarki kike d'auke dashi, ki daina cewa ba kya sonshi hakan zai iya tasiri akan abinda ke cikinki koda yazo duniya ne, yanzu kinsan me nake so dake?" "Ina jinki Faruk." ta fad'a cikin kuka da sake kama cikinta sosai tana matsewa. "Ina so ki sake neman gafarar iyayenki, wala'Allah ki samu sassauci, wataqila mahaifiyarki tasha fiye da wahalar da yanzu kike sha, sannan karki bari anbaton ubangiji ya fita daga bakinki inba bacci kike ba, kinji ko baby?" Sassauta kukanta kawai tayi ba tare da tace komai ba, d'orawa yayi da "kinsan me?" "A'a." ta fad'a cikin muryar kuka. Saida ya kalli Zuby dake bacci hankali kwance yace "duk abinda kika haifa na bakishi kyauta, kisa a ranki d'anki ne ba nawa ba, kece zaki zab'ar mishi sunan da kike so, ni nawa kawai hidima ne gareshi da kuma ke." Duk da bala'in ciwon da take ji bai hanata jin dad'i ba har cikin zuciyarta, su Papa dake tsaye mamaki ne ya mamayesu ganin murmushin da tayi, cikin ikon Allah sauqi saiya samu hakan yasa da Umar Faruk yaji bacci na shirin d'aukarta sai yace ta rufe ido zai mata addu'a, tun tana jin sautin muryarshi yana mata addu'a har bacci ya d'auketa ba tare daya daina ba, ganin bacci ya d'auketa yasa Papa d'auke wayar a kunnenta ya mayar a nashi, Papa ne yace "Ikon Allah Umar Faruk, kaga yarinyar nan tayi bacci, meka mata ne haka?" Murmushi yayi yace "ba komai Papa, sai dai Papa dan Allah kar kuyi sake da addu'a musamman idan tana irin haka, sannan na fad'a mata ta sake jaddada neman afuwarku, hakan nada anfani musamman ma Mama, dan zai iya yiwuwa tasha wahala fiye da wacce take sha yanzu." Papa kam kallon Mamie yayi yace "bansan komai ba game da wannan lokacin Umar Faruk, dan haka ba zan iya cewa komai ba, kuma insha Allah zamuta yi mata addu'a." "Shikenan Papa saida safenku." "Allah sadamu da alkairinsa." *Asuba ta gari* Ko abinci bai tsaya ci ba suka fita tare da Zuby ya ajeta makaranta, daga nan kuma wucewa yayi wajen da zasu had'u da mutanen da zabawa kudin tsohon store d'in daya siya danya tayar dashi, suna gamawa ya wuce gidansu Khairat, zazzab'in data tashi dashi shi kanshi saida ya bashi tsoro saboda zafin jikinta, amma saboda dauriya data ganshi haka ta tashi zaune tana gaisheshi, ya jima gidan yana hira da ita harya tashi tafiya, koda ya mata maganar yaushe zaizo ya d'auketa su koma gida, take yanayinta ya canza dan haka kawai ya rabu da ita...... Daga nan kuma yaje wata harkar, koda lokacin tashinsu Zuby yayi ya wuce ya d'aukota, suna isa gida koda suka shiga suka samu tanti zaune da alama zuwan Zuby take jira, kallonta Umar Faruk keyi saboda ganin wata sabuwar shiga ga tantin , duk da dama ba ma'abociyar saka hijabi bace, amma kuma siket d'in daya gani a jikinta da kwalliya a fuskarta ne yafi d'aga mishi hankali, kamar yanda ya samu suma mutanen gidan mamakin da sukeyi kenan, d'aki Zuby ta bud'a tanti tabi bayanta suka shiga ko magana, shi kuma juyawa ma yayi ya bar gidan saboda b'acin rai..... 29/08/2019 à 14:33 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 5⃣8⃣ Tana kallon Zuby harta cire kayan jikinta ta d'auka za tayi wanka ne sai taga tasa wasu kayan, tab'e baki tayi ta kawar da kanta tana kallon d'akin, saida ta gama ta zauna kusan Mama, Ruk'ayya ce ta sallamo ta shigo ta aje mata abincinta dan yanzu sun daina saboda rainon ciki, saida ta fita Mama tace "naga kiranki jiya, meya faru?" Kallon Mama tayi da kyau kafin tace "Mama wannan sabuwar shigar fa, da quruciya ba kiyi ba sai yanzu kawai saboda ki zubar mana da mutunci, waime kike so ki zamane Mama?" "Ke, karki fad'a min maganar banza, ki fad'a min abinda kika kirani jiya kawai na tambaya, kece zaki fad'a min abinda ya dace." Kallon qofar d'akin tayi sannan ta kalli Mama tace "Mama, me ki kawa Khairat?" "Mtssss, dama akan haka kika kirani, to me tace miki na mata?" "Ba ita tace min kin mata wani abu ba, amma dai naga kwanan nan tana wahala sosai bata da lafiya, nasan kuma ba zai wuce da hannunki ba." Gyara zama Mama tayi tace "aina fad'a musu ba zan bari haka ba saina d'auki fansa, kuma yanzu ma ta fara gani, dan yanzu haka nima inada mutane kamar yanda take taqama tana dasu, kuma yanzu haka daga nan zan wuce wajen wata matace da akace tsohuwar karuwar ubanta ce, zanje mu cika aikinmu na gaba." "Mama, Mama, wallahi babu ruwana idan ki kayi abinda za'a qara d'aureki, nidai in dan saboda ni kike haka to na yafe bana so, ki barni zan zauna da ita a haka, kawai ki cire hannu a al'amuran gidan nan dan Allah Mama." Kallonta tayi tace "tun kafin ki mallaki hankalinki nake shiga na fita akan lamarin aurenki da Umar Faruk, daf da kaiwa ga gaci wallahi ba zan zubar da makamaina ba, dole na d'auki fansa tare da mallaka miki Umar Faruk a hannunki." Kafin tayi magana ta d'auki jakarta ta bud'a ta fito da qullin magani ta bata tace "karb'i nan, a abinci zaki zuba mishi yaci, wannan kuma kije qofar d'akin waccen hatsabibiyar ki zuba mata, ba zata sake sha'awar qara koda minti d'aya ba a gidan nan." Rumgume hannaye tayi tace "bana so Mama ki koma da kayanki, kuma meya rage a yanzun tunda gida ta kwana jiya." Wata yar dariya tayi tace "da kyau, hakan ya tabbatar min aikin malamin nan yanayi fiye da waccen na baya." "Mama sabon malami kika samu kuma?" "Eh yarinya, ai ban fad'a miki ba sabon malami ne wannan, kuma kinga shekaranjiya ne kad'ai na fara zuwa wajenshi, amma gashi aiki yayi." Da kyau ta kalli Mamanta tace "wallahi Mama yah Umar ya fara zargina akan haka, dan Allah ki daina duk abinda kike ki tuba ga Allah Mama, niko a haka ma zan zauna dashi tunda ina sonshi, ina jiye miki tsoron ranar da zaki sake jin kunya akan abinda kike aikatawa Mama." Tab'e baki tayi tace "humm, shi yasa ma na taho miki da maganin matsalar nan, idan ki kayi anfani da wannan maganin na hannunki komai zai yaye." Ta fad'a tana bata d'aya qullin maganin, ganin tana hararanta yasa ta karb'a tana turo baki, d'ora mata tayi da " ki tabbatar kinyi aiki dasu kamar yanda na fad'a miki, idan ba haka ba ki sani, wallahi wata rana saikin zubar da hawaye, dan ina tabbatar miki hankalinshi zai koma kan wacce bata da lafiya ne, in ba kiyi sa'a bama ya tare da zama acan gidan sai dai kawai yazo ya ganki ya koma, ni kinga tafiyata ina da abinyi." Bata jira komai ba ta wuce gyalenta najan qasa sai yan mazaunanta dake motsawa, da takaici ta bita da kallo tana jin kamar ba tayi sa'ar uwa ba, qarqashin gado ta jefa maganin ta d'auki abincinta ta fara ci. *************** Fitarta daga nan gidan wata qawarta ta wuce, koda taje kuma suka wuce kamar yanda ta mata alk'awari, wani matsakaicin gidane sai dai yana da kyaun gaske da kuma tsari, bayan sun gaisa hamshaqiyar matar tasa aka kawo musu ruwa, qawar ta Mama wacce ake kira da *'yar fara* ce wannan hamagiyar matar ta kalleta tace " xyar fara ina jinki." Nuna tanti tayi tace "kamar yanda na fad'a miki a waya tun kafin muzo, wannan itace matar da take neman taimakonki." Murmushi tayi da bakinta kad'ai ya motsa kafin tace "ta fad'a min komai a waya duk abinda ya shiga tsakaninki da 'yarsa, na yarda zan taimakeki ne a zahiri saboda kin samemu tsakiya da shirye shiryen zab'e, kuma akwai wani aiki da mai neman kujerar Mani Bukar ya biyani kud'ad'e danna kai Mani Bukar qasa kamar yanda ina d'aya daga cikin wanda suka sakashi yayi sama, dan haka karki damu zuwa gobe zan gama shirya komai, kuma zakisha mamakin abinda na shirya, tabbas Khairat zata ji ba dad'i itama." Da farin ciki tanti tace "na gode sosai Hajia da wannan taimakon, kuma insha Allah Hajia za kiji babban biya." D'an b'ata rai matar tayi ta kalli yar fara tace "yar fara ina fatan kin fad'a mata ba'a min wasa da maganar data shafi kud'i ko?" "Ai karki damu Hajia, na fad'a mata komai a game dake, ba za'a tab'a samun matsala ba." cewar 'yar fara. "To yayi kyau, zaku iya tafiya." tana fad'a ta tashita shiga wani d'aki ta barsu nan, tashi sukayi Mama na yaba matar tana ji inama ta zama ita, har saida 'yar fara tace "to ai matsalar kin tsufa ne, amma badan haka ba ai zaki iya hawa network kema." Hararanta tayi tace "karki cimin mutunci mana, me kika d'aukeni?" "Ba komai." cewar 'yar fara. *Mamienmu amin afuwa*👏🙇‍♀ **************** Umar Faruk na zaune daf da Khairat yana bata magani zazzab'i tana sha, Mammie na gefen Khairat sai Mamie da Papa dake d'aya kujerar suna kallonsu, duk da dare yayi yana so yaje gida amma ganin jikin nata ba sauqi yasa ya kasa tafiya, tana shan maganin ta koma ta kwanta tana sake dunqulewa cikin bargon da Mamie ta d'auko mata, a hankali take lumshe ido alamar tana so tayi bacci, a haka har baccin yayi gaba da ita, tashi Umar Faruk yayi ya musu sallama zai fita, da k'arfi sukaga Khairat ta fad'o daga kan kujerar, a zabure ta farka itama tana kallon mutanen wajen, da sauri Umar Faruk ya qarasa wajenta ya kamata ta tashi ta koma ta zauna, fuska ba annuri yace "kalleni nan." Kallonshi tayi ya sake had'e rai yace "wallahi ku daina wahalar da ita haka in kuna son zaman lafiya, kunga ina binku a hankaline saboda ina so mu rabu lafiya daku, tab'ata da kuke shine kuskuren da kukeyi." Qwafa yayi ya mik'e zai nufi hanyar fita Papa yace "Umar Faruk, me yake damunta ne?" Juyowa yayi yace "karku damu Papa, komai zaiyi daidai na baku tabbacin hakan." Yana fad'a ya juya ya kalli Khairat, hararan sama da qasa ta masa taja dogon tsaki, fita ranshi a b'ace ba tare daya damu da abinda tayi ba, sam yau ma basuyi bacci ba ko kad'an, daga wannan ciwo sai waccen a haka suka kwana. ************** Tunda Zuby taga shiru bai dawo ba sai ranta ya fara b'aci ta fara tunanin abinda Mama ta fad'a mata, ta kuma yarda tabbas wata rana zaice zai tare can tare da Khairat indai har ana haka tun yanzu, ganin Ruk'ayya ta kawo abincinshi ta aje kawai saita tashi ta d'auko maganin data jefa qasan gado ta duba wanda zata saka a abinci ta mayar da sauran, tsautsayi ya kawo Umar Faruk a lokacin da take zuba maganin a abinci, komawa yayi da baya ya saita kansa tare da had'e b'acin ranshi sannan yayi sallama ya shiga, ko kad'an bai nuna mata wani abu ba ya share kawai, wanka yayi sannan ya zauna cin abinci, bismillah yayi yana shu'umin murmushi ya kai lomar bakinshi, saida ya cinye wanda ta zuba mishi duka saboda yunwar da yake ji, dan duk lokacin da zai kai abu bakinshi saiya tuna Khairat, hakan yasa shima bai cika ci yana qoshi ba kwanan nan, da farin ciki Zuby ta kwana sab'anin Umar Faruk daya kwana yana kallon fuskarta, tsanarta na sake mamayeshi, daga qarshe kuma tunanin Khairat ya maye gurbin tunaninta dashi har gari ya waye. Tana zaune harya gama shirinshi zai fita, juyowa yayi ya kalleta yace "ni zan wuce, babu komai?" "Ba komai." Hannu ya mik'a mata cike da qoqarin taushe qiyayyar da take mata yace "ina so zan gaisa da yarona." Hannun ta mik' masa ta taso shi kuma ya bi cikinta da kallo wanda ya turo riga ya fito, shafar cikin yayi yace "nasan ka tashi lafiya, haka Papanka da mamanka, kuma nasan zaka kula min da kanka, ni zan tafi." Sunkuyawa yayi ya sumbaci cikin sannan ya fice, saida ya gaishe da iyayensu sannan ya wuce gidansu Khairat, da shigarshi sallama kad'ai yayi ya samu duka mutan gidan tsaye akan Khairat dake ta birgima a qasa tana kuka tana cewar zuciyarta zata fashe zafi take mata, qarasowa yayi dan babu ma wanda ya amsa sallamar tashi, tsaye yayi shima yana kallonta idonta rufe sai hawaye dake fitowa, matsowa yayi da nufin zama kusa da ita kawai saita d'ago ta bulalo amai, duk da ta b'ata mishi jiki bai damu ba saida ya zauna ya fara taimaka mata da addu'a, a hankali a hankali ta fara samun nutsuwa da sauqi, bayan wani lokaci kuma sai bacci yayi gaba da ita, Mamie ce tace "Allah ka dubi yarinyar nan ka sassauta mata abinda yake damunta, Allah ka yafe mata kurakurenta badan mu ba." ta qarashe da fashewa da kuka. Kallonta Umar Faruk yayi yace "dan Allah kuyi hak'uri ku daina kukan nan, insha Allah zata samu lafiya." Cikin kuka Mamie tace "wallahi tausayi take bani, kwananta biyu yau a gidan nan amma har yanzu baccin da tayi baifi na awa biyu ba idan aka had'a, ace daga wannan ciwo sai waccen, da anji sauqin wannan kuma sai wani da danno kai, wallahi nidai ban tab'a ganin laulayi irin nata ba." Gyara mata kwanciya yayi ya mik'e yace "ku kula da ita zanje na samo ganyen magarya, insha Allah zata samu lafiya da yardar Allah." Yana fad'a ya fice daga gidan, zaune sukayi suna kallonta kafin ta farka kuma, ba dadewa kuwa ta farka tana dafe kai, Mamie ce ta kawo mata abinci taci amma sam tak'i ci, saida Papa ya lallab'ata ya rarrasheta kad'ai ta samu taci kad'an, tana gama ci ta tashi da gudu taje k'ofar shigowa falon ta fara amaye abinda taci, tana haka Umar Faruk ya shigo gidan, tsaye yayi yana kallonta da tausayawa saida ta gama ya rik'ota suka shigo, kallonta yake sosai duk da cikinta ya girmema na Zuby amma ko alamun fitowa baiyi ba, zaunar da ita yayi sannan ya bawa Mamie ledar hannunshi yace "ku jiqa wannan ku ajeshi a wuri mai kyau, zan nemeshi nan da kwana bakwai insha Allah." "To shikenan." cewar Mamie tana karb'a. **************** Misalin *09:30* na dare duk suna zaune a falon, Khairat na kwance akan cinyar Umar Faruk da yake so ya tashi ya tafi ta rik'eshi, hira suke sama sama wani jami'i ya shigo ba tare da sallama ba ya sarawa Papa alamar girmamawa yana fad'in, "Yallab'ai, wata mata ce a qofar gida tace tana son ganinka, na tambayeta abinda ya kawota amma tace ita kai take son gani." Shiru Papa ya d'anyi kafin yace "ok ba damuwa, kace ta shigo." Juyawa jami'in yayi bayan ya amsa da "an gama yallab'ai." Harsun fara tab'a hira sukaji ance "salam." Kowa kallon qofar yayi dan ganin mai sallamar, zunbur Papa ya mik'e da tsananin mamaki yace " *Odette*, kece gidana, meya kawoki nan, kin manta rabuwarmu ne?" Kowa dai da mamaki yake kallonsu harda Khairat da jikinta ya d'anyi dama, juyawa matar tayi ta kalli qofa tace " *Salim*, shigo mana." Wani matashin saurayine da bazai wuce shekara sha shida ba zuwa sha bakwai fari sol dashi kamar matar, d'an gaye ne sosai irin matasa ne masu aji, turo yaron tayi gaba ya nufi Papa tace "kaje, yau dai na sauke wannan nauyi, kuma na huta da qorafinka kullum, kuma yanzu asirinmu zai rufu." Daf da Papa yaron ya tsaya yana murmushi ba b'ata lokaci ya rumgume Papa yana fad'in "oh Babana, naji dad'in had'uwa da kai." Papa daya kusa mtuwar tsaye da qyar ya raba jikinshi dana yaron yace "kai wace maganar banza ce wannan, waye uban naka?" Hamshaqiyar matar ce tace "kunga na barku lafiya, saida safenku." "Ke, wai miye haka, wanene wannan yaron?" cewar Papa. Cike da yabqi da yanga tace "oh yi hak'uri fa, wannan ai shine *Salim* danka dana jima ina boye maka, amma kwanakin nan yana addabata waishi dole na had'ashi da mahaifinshi danya gaji da ganinka a tv kullum, nace yayi hak'uri amma sai yace zai fad'a a gidan jaridu da tv cewar shi d'in danka ne, shi yasa naga zaifi ayi komai asiri rufe ba tare da anyi tone tone ba, kasan zab'e ke tafe." "Wannan ai maganar banza ce ma, kin sani na sani lafiya lau muka rabu dake, karki yarda kice zaki b'ullomin ta wannan hanyar, dan wallahi ba zakiji dad'i ba, kuma ki gaggauta fita min da wannan d'an iskan yaron kafin nasa a fitar min dashi." Rai b'ace tace "a'a Mani, karka sake zagar min yaro wallahi, kuma idan kace baka yarda ba kai ka sani bana abu babu hujja, kamar yanda kasan bana qarya ko kuma cuta." Jakarta ta bud'a ta ciro da takardu ta jefa mishi a qirji tace "wannan suna dauke da duk wasu bayanai tun daga lokacin dana d'auki cikin Salim har haihuwarshi, sannan akwai gwajin da asibiti sukayi na qwayoyin hallitunshi iri d'aya ne da naka, idan kuma baka yarda ba zaka iya sakawa a maka sabon gwaji." Tana fad'a ta juya ta fita daga gidan, yaron kuma zaune yayi kusa da Mamie yana kallonta yace "bonsoir (ina wuni)." Da sauri Mamie ta shige d'akinta tana hawaye, maida kallonshi yayi ga Khairat data tashi zaune tana kallon ikon Allah, da azama yaje wajenta ya zauna yana kallonta yace "wannan itace auntyna ko?" Kafin ayi magana kuma ya kamo hannun Khairat yana maqalewa da nashi, badan rashin lafiya da matar nan ta gane kurenta cewar Khairat a zuciyarta, amma duk da haka cikin zafin rai ta d'aga hannu ta wanke yaron da mari ta nunashi tace "karka sake tab'ani dan kai ba d'an uwana bane." Dafe kunci yayi yana murmushi yace "ke kuma haka kike tarban bak'inku, ba komai ke yayata ce zaki iya yimin komai." Tashi tayi danta bar wajen amma saita zube saboda qafafunta da suka rik'e, Umar Faruk ne ya tashi ya d'auketa ya kaita d'akinta ya kwantar da ita, addu'a ya mata ya rufeta sannan ya fito ya bar d'akin dan tak'i kallonshi ma, yasan badan rashin lafiya ba da gidan nan ya hargitse yau. Papa ya samu tsaye yana duba takardun nan har yanzu, indai har zaiyi anfani da abinda ya gani a takardun to tabbas Salim d'ansa ne, amma ba zai yarda ba dan haka Umar Faruk na musu sallama ya fita ya kira docteur d'inshi yace gobe zaizo, d'akin Mamie ya shiga ya samu tana kuka, zaune yayi ya fara magana da "Na'ima, dan Allah..." D'aga mishi hannu tayi ta tashi tana share hawayenta tace "kar kaba kanka wahala wajen rarrashina, nima ba hushi nayi da kai ba, kawai dai banji dad'i bane saboda ban tab'a tunanin ka haihu a waje ba, amma inhar ina da hankali aibai kamata nayi hushi da haka ba saboda nasan komai a game da rayuwarka ta baya." "Na gode da kika fahimceni Na'ima, amma wallahi nima ban tab'a sanin inada wannan yaron ba, kuma har yanzu ma ban yarda d'ana bane harsai Allah ya tashemu gobe munje asibiti an sake mishi wani gwajin." *Wata sabuwa* *Barka da Ranar Hausa ta duniya, Allah ya d'aukaka matan hausawa.* 29/08/2019 à 14:33 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Haka kawai sai kaga Allah ya had'a zuqatan bayinsa, ba gari d'aya ba bare unguwa, amma haka Allah ya had'amu har muke qaunar junanmu, Allah ubangiji ya baki lafiya my Meerahgee *(Maryam Gital)*, Allah yasa zakkar jikina kuma sanadin yake zunubanki, your Meerahgee again._💕💞 _Dan Allah ki daina wahalar da zuciyata ki fito ki naganki ko naji sanyi, Allah ya qara miki lafiya dawamammiya, *My BK* i love you_. _Bismmilahir-rahman-rahim_ *Idan nayi magana dubannin rayuka zasu b'ace, dan haka nayi shiru.*😎 5⃣9⃣ Ba'a b'ata lokaci ba Papa ya d'auki Salim suka je aka sake mishi gwaji, ba yanda ya iya tunda gwajin ya bayyana d'anshi ne na cikinshi, daga nan kuma sai yaji yaron ya shiga ranshi, ashe shima Allah ya bashi namiji. *Hummmmmmmm* Koda suka zo gida Papa yasa aka gyara mishi d'aya daga cikin d'akuna, ana cikin haka ya had'a yaron tare da masu gadinshi suka je babban boutique aka siyo mishi kaya masu kyau da tsada, sabuwar rayuwa kenan wa Salim. *Wacece Odette???* Odette shahararriya kuma 'yar duniya ta gidan gaba, sun jima tare da Mani Bukar saboda gogewarta da kuma iya bariki da soyayya, tun kafin ya fara siyasa suke tare da ita, kuma tana d'aya daga cikin wanda suka bashi gudummuwa sosai harya hau kujerar da yake yanzun, a waccen lokacin zai iya cewa bayan mahaifiyar Khairat ita macen da yake so, amma a lokacin da shiriya tazo mishi saiya fad'a mata ya shiryu kuma itama ta tuba ga Allah, sam tace shi dai yaje amma ita tana nan har yanzu, saida mata babbar sallama sannan suka rabu cikin mutunci, amma shine yau tazo mishi da maganar yaro d'an shekara sha bakwai, wanda baisan dashi ba sai yanzu. **************** Kamar yanda Umar Faruk ya kai Zuby école, haka ma yanzu duk da abinda ke gabanshi ajeshi yayi saboda lokacin tashinsu yayi, koda yaje ta taso daga inda take zaune harta shigo ta zauna yana kallon cikin dake maqale jikinta, saida ta rufe motar sannan ta kalleshi tace "sannu." Bata jira amsarshi ba ta bud'a jakarta ta fiddo ledar awarar data siya ta bud'e, ba tare da kama hannun yaro ba ta fara gaigayar awarar ko kallonshi ba tayi, shi kuma kallonta yake da gani kasan yunwa take ji sosai, yanda take cin awarar sai yaji ta birgeshi yana ji kuma inama Khairat itama haka take cin komai, murmushi kawai yake mata har suka d'auki wata hanyar ta daban, sai lokacin ta kalleshi tace "yah ina zamu je kuma nan?" Ba tare daya kalleta ba yace "zanje na siyar daku ne, ko baki san mace mai ciki tsadane da ita ba?" "Hum, aiba zaka fara ba, dan nasan ko ka siyar dani ba zaka yarda ka siyar da magajinka ba." Dariya yayi yace "gaskiyarki kam, amma taya zan siyar da uwar bayan itace mai haifawar? abune da ba zai yiwu ba ai a wajen Umar Faruk." Kallonshi tayi ta cika baki da awara tace "kana sona ne har yanzu?" Kallon qwayar idonta yayi amma ya kasa cewa komai, maida kallonshi yayi ga tuqinsa ita kuma tace "basai ka fad'a ba nasan baka sona." Kallonta yayi yace "Zuby, kina so na b'ata lokacina wajen fad'a miki abinda kika sani, ko kuma kina sone dole saina ce miki ina qaunarki fiye da tunaninki, nasan kema kinsan da haka." Ganin dai suna shiga wani wajen yasa tace "wai ina zamu ne?" Kashe mata ido yayi hankali nutsu yace "ki yarda dani mana, ba zan cutar dake ba." K'ofar wani matashin gida suka paka, shine ya fara fita kafin ta fito itama, goge maiqon dake hannunta tayi a hijabinta sannan tabi bayanshi suka shiga ciki, babu hayaniya gidan sosai hakan yasa sai wata dattijuwar mata ta musu iso ciki, suna shiga falon Zuby ta tsaya cak saboda ganin babanta Bala zaune da alama bashi da lafiya, saida Umar Faruk ya d'an ja hijabinta sannan suka samu wuri suka zauna, gaisawa sosai Umar Faruk yayi da mutanen Zuby na kallonshi dan yanda taji suna gaisawa alama ce ta yana zuwa gidan, kallon da Umar Faruk ya mata yasa ta kalli Bala tace "ina kwana?" "Ina kwana yanzu?" cewar Umar Faruk. "Ina wuni?" ta fad'a tana cika baki. "Lafiya lau Zubeida, ya makarantar?" "Lafiya lau." D'aya daga cikin matance tace "wannan matarka ce?" "Eh, amaryar ba." cewar Umar Faruk cike da kunya. Bala ne ya d'ora da "kuma 'yata ba." Da mamaki matan suka kalleshi yayin da Zuby ta kalleshi, babbarce tace " 'yarka kuma Alhaji, taya ta zama 'yarka kuma?" "Eh, haka nace, 'yata ce kuma ta cikina, zaku iya bamu wuri." ya fad'a a kausashe. Tashi sukayi suna kallon Zuby, Bala kuma kallon Umar Faruk yayi yace "ya jikin Hajia Khairat?" Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace "jiki da dama." "Allah ya qara sauqi, insha Allah zata samu sauqi, dan bata da haqqin kowa a kanta, hasali ma zuciyarta fara ce, taimakon mutane shine aikinta, kuma Allah yayi alk'awarin ba zai kunyartar da mai irin wannan hali ba." Yatsa yasa ya share qwallar dake idonshi yana ci gaba da cewa "baiwar Allah, wallahi da inada maganin cutarta dana batashi, da ace kuma nasan inda zan samo mata maganin da zanje na samo mata koda kuwa zansha wahala ne, sai kash muna ji muna gani yarinyar kirki tana wahala babu yanda muka iya, alhalin ita bata jurar ganin talaka a cikin wani hali." Cikin sanyin jiki Umar Faruk yace " sai dai muyi hak'uri kawai, Allahn daya d'ora mata shi zai yaye mata insha Allah." Kallon Umar Faruk Bala yayi yace "shin kasan wacece Hajia Khairat a wajena, shin kasan taimakon da tayi mana a rayuwa? nasan zaka sani tunda matarka ce." Katseshi Umar Faruk yayi da "a'a wallahi Baba, ko sau d'aya Khairat bata tab'a fad'a min wani abu daya danganceta ba." Murmushi Bala yayi yace "kaji yar arzik'i, to Hajia Khairat da kake gani a yanzu haka nida iyalina muna rayuwa ne da taimakon da tayi mana, *wasu shekaru da suka gabata* na kasance mai munanan halaye, ta sanadiyar haka na rasa komai nawa saboda almubazzaranci, a lokacin da muka fara rasa abinda zamu ci nida iyalina sai hankalina ya sake tashi, a hankali sai rayuwa taci gaba da garani yanda ya kamata, nasan kuma hakan nada alaqa da cin amanar da nayiwa abokina wato Hamza, wata rana mun tashi gidan nan babu yara ma zasu saka a bakinsu bare manya, na fita da tunani samo musu duk abinda ya sawaqa , amma amma ina babu abinda na samo sai dawowa nayi, a ranar kuma akayi sa'a ana bikin wata yarinya anan, babbar sa'a da mukayi shine kasancewar Khairat a cikin qawayen amaryar, koda na dawo kasa shiga cikin gidan nayi saboda ba zan juri kallon yaran ba a wannan halin, hakan yasa na zauna a qofar gida na zabga tagumi, a lokacin Khairat ta fito daga gidan dake kallon nan gidan ta ganni a wannan hali, saboda kyakyawar zuciya yasa tazo inda nake ta tambayeni me yake faruwa, nan na fad'a mata halin da nake ciki, gani nayi ta zubar da hawaye da bansan kona miye ba,tambayarta nayi me yasa take kuka sai tace karna damu , komawa tayi gidan data fito ta jima kafin ta fito, abin mamaki da al'ajabi sai Hajia Khairat ta cire hauran makka dake haqoranta da k'arfi har suna mata jini ta bani tace naje na siyar, kuma ta bani hak'uri tace babu kud'i ne a jikinta kuma gashi wayarta ta d'auke bare ta kira, amma ta gargad'eni na gaggauta siyar da hauran guda biyu na siyawa yara abinci, duk da naso mata godiya bata bani damar hakan ba saboda tafiyarta da tayi, nan na tafi na siyar da hauran biyu kuma sunyi daraja sosai sannan na siyowa yara kayan abinci na kawo gida, kasan meya faru Umar Faruk?" Kai kawai Umar Faruk ya girgiza yana kallonshi, d'orawa yayi da "wallahi yara na cikin cin abincin Hajia Khairat ta shigo gidan tare da wasu matasa da wasu kayan abincin, bata bar gidan ba saida ta tambayi duk yaran matsalolinsu na makaranta ta biya musu, wani babban alherin data sake yi mana da yasa na kusa mutuwa saboda farin ciki shine, kyautar *million d'aya* data bani tace naja jari, tofa tun daga wannan rana na d'auki girma da matsayi na bata kamar na mahaifiyata saboda mahaifiyata bata raye, kuma wallahi wallahi Umar Faruk, zan iya fansan ran Hajia Khairat da rayuwar d'an daya fito daga cikina, domin kuwa da gaba d'aya rayuwarmu tata ce, ina fatan Allah ubangiji ya dauke duk wani ciwo da radadi dake jikin Hajia Khairat ya dawo dashi kaina koda zai zama ajalina ne, wallahi a shirye nake dana bada rayuwata dominta." Kallon Zuby yayi yace "shine yasa a lokacin data nemi taimakona ban kasa yi mata ba saboda ta wuce hakan a gurina, kuma banji dad'i ba sam dana samu labarin rashin kunyar da kike mata, kinga mijinki gashi nan?" ya fad'a yana nuna Umar Faruk. Da qyar Zuby ta d'aga kai dan ita kanta jikinta yayi sanyi saboda girman al'amarin Khairat, ci gaba yayi da "to wallahi zan iya sashi ya sakeki inhar zaki din cin zarafin yarinyar nan, idan ma bai sakeki ta dad'i ba zan iya yin shari'a dashi danya sakeki, dan haka ki kiyaye in kina son zaman lafiya da albarka, kuma bawai na fad'a miki haka bane dan bana sonki ko kuma ina son aurenki ya mutu, a'a ina sone na nuna miki girmanta a gareni, ina fatan kin fahimta? Allah ya muku albarka ya baku zaman lafiya da hak'uri da juna." Umar Faruk kad'ai ya amsa da "ameen Baba." Haka suka dawo gida Zuby na sake jin kunyar Khairat da kanta, Umar Faruk kuma na sake jinjina al'amarin Khairat, dan inbai manta ba ta fad'a mishi ta manta sunan wanda tabawa hauran makkanta, ashe bata manta ba kawai dai bata son fad'a ne saboda kawai tayi dan Allah, a lokacin daya shiga wanka doushe ya lumshe ido ya furta a hankali cewa " *Allah ka azurtani da zuciya irinta bauwarkan nan, Allah ka cire min son abin duniya, Allah ka bani ikon yin komai dan kai, matata kuma Allah ka dubi kyakyawar zuciyarta ta son taimako ka cireta a halin da take ciki.*" Nidai nace "Ameen." _Haka ma team d'in Khairat da *"ameeeen."* suka amsa._ *Bayan sati d'aya*, ranar litinin su Zuby suku fara shiga jarabawa, Umar Faruk ya kaita dan zana jarabawa, sunyi sai dai Zuby saida tayi qwalla saboda sarewa da tayi, a lokacin da suka tashi Umar Faruk ya zo d'aukarta tare da Khairat daya d'aukota daga wajen awo, suna jirar fitowarta wata mota ta fito daga cikin makarantar, babban mutum ne amma yana ganin Khairat zaune a motar ya fito daga tashi yazo inda take, tana ganinshi ta sauke glass d'in motar suka gaisa, mutumin ne yace "Hajia Khairat na ganki anan, lafiya daiko?" "Lafiya lau wallahi, munzo d'aukar qanwata ne." "Allah sarki, anan take jarabawar itama?" "Eh, anan take." "Masha Allah, to Hajia meye sunanta?" "Me yasa kake tambaya?" cewar Khairat. "Hajia aimu qasa muke dake, bamu cika samun irin wannan damar ba, ba kuma zanyi wasa da ita wajen kyautata miki kema." "Zubeida..." kallon Umar Faruk tayi tace "sunan babanta?" "Hamza, amma ai kinsan ba shine originale d'in ba." cewar Umar Faruk. Murmushi tayi ta kalli dattijon tace "Zubeida Hamza." "Shikenan Hajia, ki d'auka qanwarki taci." Cewar Khairat "amma dai a dinga duba cancanta , idan za'a dinga bawa mutane irinmu saboda wani abu, to wanda basu da alfarma fa?" "Hajia aike ba kamar kowa bace, amma insha Allah za'a kiyaye." Lokacin Zuby ta fito, gaishe da dattijon tayi sai taga yana washe mata baki ba kamar idan suna cikin makaranta ba, baya ta shiga tana fad'in "sannu." Khairat ce ta fara amsawa da "sannu." Saida ya aje Khairat gida sannan ya wuce da Zuby gida.... *Bayan gama jarabawa*, da daddare Umar Faruk ya dubowa Zuby sakamakonta, tun a hanya ya kira ya fad'a mata taci écris, zo kaga murna da farin ciki, cikin qanqanin lokaci fad'awa kowa, Umar Faruk dai kallonta yake yana ganin kawai ta samune a sanadiyar Khairat. *A gurguje* Umar Faruk dai ya zage damtse sosai wajen yiwa Khairat magani da addu'a, kuma cikin ikon ubangiji komai yayi sauqi yanzu, sai ciwon qafafu da yan abinda ba'a rasa ba, sai dai bai d'auki kowane mataki ba ga tanti ko Zuby, idan har lokacin arziqinka yayi to ba fashi , duk da hankalinshi ba'a kwance yake ba amma ubangiji na bud'a mishi tako wace hanya, yanzu haka da taimakon Allah har an fara aiki a compganinshi daya siya, ga kuma shaguna da yanzun suma suke shigo mishi da kud'i, yanzu haka baya qarqashin kowa zaman kanshi yake shima yana cin gumin kanshi, yanzu haka yana nan ya siyi wani babban fili daf da gidansu har an fara gini dansu koma gaba d'aya ahalinshi, kuma duka 'yan uwanshi maza suna tare dashi suma suna cin arzik'i, sai dai kawai ace alhamdulillah, a wajen Zuby kuma baqin cikine ya isheta saboda rashin nasara akan maganin data saka mishi, shi kuma dama ya dogara ga Allah ne yasan babu abinda zai faru dashi dama, kuma har yau bai nuna mata komai ba, idan ka ganta kace cikin yan uku ne da ita, shi yasa ma uwarta ke kiranta da uwar uku wani lokacin. Duk da lokacin da Khairat ta d'auka a gida bata son komawa gidanta, kuma kullum Umar Faruk sintirin zuwa gidan yake, yanzu haka *cikinta na wata na biyar*, amma idan ka ganshi za kace cikin wata hud'u ne, sai dai yanzu da dama ciwo yayi sauqi, musamman amai da rashin son cin abinci, yanzu duka tana ci kuma tana sha, sai dai matsalar Salim a yawon sakata damuwa, dan yaron yazo da raini sosai da rashin kunya, Mamie kullum cikin baqin ciki take akan yaron, sai tsirfa iri iri kamar mai ciki, zuciya kuma bata da qashi sai Allah yasawa Papa son yaron saboda yana ganinshi namiji ne, da wannan taskun kullum basa farin ciki, ga kuma karb'ar kud'i da yaron ke yawan yi, amma duk abinda ya nema Papa yi mishi yake. Wani bala'i daya taso musu shine yad'uwar maganar Salim a kafafen sada zumunta da gidajen tv da redio, wannan abu sosai ya tab'a mutuncin Papa har saida ya kai ya daina fita waje, ga kuma kira daya sameshi daga jam'iyarsu wai an cireshi daga partie d'insu, bai damu da wannan ba ko kad'an tunda dama tunaninshi barin siyasa, maganganu marasa dad'i kawai ake a social media da gidajen radio, sai dai masoyanshi na alaqanta hakan da yarfe na siyasa, hakan ya sake tadowa Khairat tsohon ciwonta na qirji da ciwon kai, hakan kuma ya d'aga hankalin iyayen nata da mijinta, hakan yasa Umar Faruk d'amarar binciko gaskiyar alamarin, dan yanzu suma iyayenshi ne ba ita kad'ai ba. *Yau* ma kamar kullum zaune suke a falon ana hira sama sama, hankalinsu ne ya koma kan tv saboda wani shiri da ake tattaunawa akan manyan mutane har aka d'auko misali da Papa, mai gabatar da shirinne yakewa d'aya tambaya da "to yallab'ai me zaka iya cewa akan wannan magana, ace shuwagabanni daya kamata ace muna koyi dasu kuma sune suke aikata bad'ala a doron qasa?" Mutumin da aka tambaya ne ya gyara zama zai bada amsa Mamie ta kashe tv, Papa kuma qasa yayi da kanshi cike da takaici da kunyar iyalinshi, shiru da falon ya d'auka yasa Papa cewa cikin muryar nadama yace " kuyi hak'uri ku yafeni, ni naja muku wannan abun kunyar, haqiqa na bar muku abinda har jikokinku zasu ji kunya, yanzu ne nake qara tir da rayuwata, ku yafe min dan Allah, nasan na cutar daku." Babu wanda yayi magana sai Umar Faruk yace "kuyi hak'uri Papa, wannan itace jarabawarku, kuyi qoqari ku cinyeta, insha Allah Allah ba zai kunyatar daku ba kuma zaku samu sakamako koda ranar gobe ce." Salim ne ya shigo yana wasa da makullin tsandareriyar motar da zab'inshi ce wato *Prado*, kai tsaye dinning ya nufa yana bud'a kwanukan abinci, tsaki yaja ya juyo yana kallon Mamie yace "wai me yasa ne ni ake nuna min wariyar launin fata a gidan nan ne? nasha fad'a bana cin macca amma dole sai an dafa, to yanzu me zanci kenan?" "Uwarka, nace uwarka kaji, marar kunya d'an rainin hankali." cewar Khairat dake b'antarar d'anyan mangaro. Yunqurawa tayi ta tashi tsaye da nufin taje wajenshi, da k'arfi ta koma ta zauna kamar an jefata saboda ciwon da qafafunta keyi, rik'e hannunta Umar Faruk yayi yana kallon fuskarta yayi ganin yanda take hararan Salim yasa ya kamata suka tashi ya kaita d'akinta, duk da abinda Salim ke fad'a tana so ta tsaya Umar Faruk ya hanata, saida suka shiga ya kwantar da ita ya rufeta sannan ya kalli fuskarta yace "qaninki ne fa, ki kama girmanki mana karya rainaki." "Wallahi ba d'an uwana bane waccen banzan yaron, rainin wayonshi yayi yawa, kullum da kalar iskancin da yake zuwa." Wani mayan kallo ya mata ya kwantar da kanshi a qirjinta yana sauke numfashi, shafa kanshi tayi tace "ya dai baby?" D'ago kai yayi yana kallonta a marairaice yace "Khairat nayi kewarki sosai wallahi, dan Allah ki daure mu koma gida Khairat kona d'an rage zafi, wallahi na kusa kaiwa matakin qarshe." "Karka damu zan koma." ta fad'a a tak'aice. "Yaushe?" ya tambaya. Kallonshi tayi tace "nan da sati d'aya, lokacin na qara warwarewa." Rumgumeta yayi yace "Allah ya yarda baby, zanyi farin ciki da wannan ranar fiye da farin cikin da nayi a lokacin da aka kawo minke gidana." Ya jima suna hira saida yaga bacci ya fara dibarta sannan ya shafeta da addu'a ya rufe mata d'akin ya fita, Salim ya samu gaban Papa yana fad'in "Allah idan ba tayi hankali ba zanyi maganinta a gidan nan, yanzu kawai ka bani wani abu nan zanje na samu wani abu naci, tunda a gabanka ake nuna min bana da mahimmanci kuma ka kasa d'aukar mataki, dan anga uwata bata cikin gidan." Kallonshi kawai Papa yayi yace "yanzu kace baka da kud'in cin abinci a wajenka?" "Eh, bana da." ya fad'a yana hararan Mamie. D'auke idonshi yayi daga kan Mamie cikin akasi suka had'a ido da Umar Faruk, wata arniyar harara daya gabza masa yasa yaji gabanshi ya fad'i, kallonsu Papa yayi yace "saida safenku." Tunda Umar Faruk ya sanar a gida da Khairat zata dawo hankalin Zuby ya tashi, dan gani take yanzu zai rage nuna mata kulawa, duk yanda zaiyi dare a gidansu Khairat baya wuce k'arfe 10:00, kuma bata gansu ba bare taga me sukayi, dan haka hankalinta ke kwance, nan ta fad'awa Mama abinda ke faruwa, ita kuma fad'a ta mata tace da tayi aiki da maganin data bata da ba za taji sha'awar dawowa ba. ************** Tunda sukayi maganar dawowarta sai kuma ciwo suka dawo, ya kuma fahimci gidan ne bata san zama yanzu, dan haka yayi shirin d'aukar mataki akan hakan. Da sallama ya shigo gidan ya samesu falo tare da likitan Papa dake dubata, ko gaisawa basuyi ba ya zuba ido yana kallonsu shima, likitan ne ya d'ago ya kalli Papa yace "a gaskiya bansan dalilin da yasa cikin ke haka ba, amma dai abinda zan iya fad'a muku anan shine, da zaran ta fara naquda ku gaggauta kaita asibiti dan a mata tiyata." A duburburce Umar Faruk yace "me, tiyata, akan me?" Kallonshi likitan yayi yace "eh tiyata, saboda ba zata iya haihuwa da kanta ba." "Akan me, kaine keda iko akan haka da zaka fad'i haka? babu wanda ya isa ya fasa min mata wallahi, zata haihu da kanta." Likitan Papa ya kalla yace "kafi kowa sanin wacece 'yarka, dan haka nidai na fad'a muku abinda ya dace, idan baku ji ba zaku wahalar da itane da d'an cikinta a banza." Ficewa yayi su kuma suka zauna Mammie ce ta kalli Umar Faruk tace "duba kaga abinda cikinta keyi fa." Da sauri ya sunkuya gaban Khairat ya janye rigarta yana kallon cikinta, waro ido yayi cike da tsoro saboda ganin yanda dan cikinta ke motsi, bawai motsi bane kamar kowane, wannan kamar yana neman hanyar fitowa ne ta hanyar parka cikin nata ya fito, yawo kawai yake mata ko ina, ita kuma harta darrahe ta barwa Allah sai ruwa kawai dake fita a idonta, kallonta yayi yace "kiyi hak'uri Khairat, nasan zaki sha wahala, amma dole ayita ta qare." Wasu hawayen ne suka sake bulbulo mata ta qara qamqame hannunshi, girgiza mata kai yayi alamar ta daina kuka, cikin muryar kuka cike da tausayin kanta tace " *Umar Faruk*." Kallonta yayi sosai dan shine na farko tunda sukayi aure da yaji sunan Umar Faruk a bakinta, ci gaba tayi da cewa "ni kad'ai nasan me nake ji a jikina, na wahala iya wahala, nasan jarabawa ce daga Allah, wataqila had'e da hukuntani akan kurakuraina na baya, Umar Faruk bana jin zan rayu saboda azabar nake sha, amma ina so kamin alk'awarin zaka kula min da abinda zan haifa idan Allah yasa ya fito duniya, ina so ka bawa abinda zan haifa tarbiyar da ban samu ba, ka yafe min Faruk akan komai dana maka." Hannayenta tasa ta janyo kanshi ta had'a goshinsu waje d'aya tana kallonshi tace "ina sonka Umar Faruk, ina qaunarka fiye da abinda yake cikin nan nawa." Rintse ido Umar Faruk yayi hawaye suka zubo mishi ya d'an kawar da kanshi gefe kafin ya kalleta cikin kukan da bai tab'a irinshi ba yace "me yasa Khairat, me yasa zaki soni fiye da yanda kike son abinda yake cikinki? me yasa ba zaki kalleni a matsayin wanda yayi sanadiyar shigarki wannan halin, Khairat ban cancanci wannan soyayyar ba, ko kad'an ban cancanci wannan soyayyar ba Khairat." Ya qarashe da sake fashewa da kuka, Mamie Mammie Papa duka babu wanda bai zubar musu da hawaye ba, saida suka ci kukansu babu mai rarrashi kafin Umar Faruk ya goge nashi hawayen ya tashi tsaye, kamata yayi suka nufi d'akinta ya kalli Mamie yace "dan Allah kuzo." Bayanshi Mamie tabi saisu Mammie da yace ma "ku tayamu da addu'a." Suna shiga d'akin ya zaunar da ita qasa ya sata tsakiyar qafafunshi, janyota yayi jikinshi sosai yasa bakinshi a kunnanta ya fara sambad'a mata karatu, tun yana karatun tana d'an motsi a hankali harta fara turmushe turmushe, Mamie ya kalla yace "ku kawo ruwan nan dana kawo tana sha." D'aukowa Mamie tayi ta bashi ta koma gefe sai addu'a take duk wacce tazo bakinta, koda ya watsa mata ta kwamtsa qara tare da qoqarin fincikewa daga jikinshi, wani d'an banzan rik'o da yayi mata saida ya rufe idonshi saboda yasan zata wahala haka ma d'an cikinta, ko kad'an bai saurara mata ba haka ya dinga karatu da watsa mata ruwan nan, kuka take cikin gumjin murya ana fad'in yayi hak'uri zamu fita amma bai saurara ba, saima cewa da yayi "aina fad'a muku ku fita a jikinta lafiya kafin aji kanmu amma baku ji ba." Turmuje turmuje take sosai tana kokawa dashi amma ina, har saida takai kayan jikinta sun fita saboda bala'i shima kuma ta yaga mishi riga, idonta ne sukayi jawur dasu kamar wuta, cikin muryar shan wahala akace "zamu fita, wallahi zamu fita har abada, ka fad'a mana ta ina kake so mu fita?" Cikin d'aga murya yace "ta hancinta, kuma bana so ku cutar da ita, sannan kumin alk'awarin ba zaku sake dawowa gareta ba." "Munyi, munyi wallahi, amma fa zamu...." Shurin da sukayi yasa yace "amma me, me zakuyi?" "Gaskiya zamu koma kan masu hannu a turo mu, saboda munsha wahala." "Karku fara wallahi, ku barni dasu kosu waye ni zanyi maganinsu, in kuma baku ji ba to zaku mutu wallahi, kunji na rantse." Wata irin bille bille Khairat ta fara ga wata irin majina dake fita ta hancinta kamar an kunna panpo, a cikin haka kuma take had'awa da atshawa kuma idonta rufe, saida tayi atshawa ba adadi kafin ta fad'i kwance amma kuma majinar nan naci gaba da fita daga hancinta ba qaqqautawa, gyara mata kwanciya yayi ya kalli Mamie yace "Alhamdulillah, yanzu sun fita, kuma insha Allah ba zasu sake dawowa ba da yardar Allah, yanzu ku canza mata kaya saiku barta ta samu bacci." Yana fad'a ya d'auketa ya mayar kan gado sannan ya fita, su Papa ya samu har yanzu suna tsaye cirko cirko, kallonsu yayi yace "karku damu, ta samu lafiya da izinin Allah." Yana fad'a ya fita su kuma suka shiga d'akin Khairat dan ganin halin da take ciki, saida ya shiga mota ya kula da rigarshi, a haka yaje gida yana fita ya fad'a cikin gidan yana d'an kare rigarshi, kai tsaye d'akin Zuby ya shiga bai kula kowa dake zaune ba, zaune ya sameta tana shan exotic d'in daya wadatata dashi, rigarshi ya cire yana shirin cire wandon Zuby tace..... _To Hajia Zuby Allah yasa karki sake b'ata ran mazaje._ 29/08/2019 à 14:33 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _Bismmilahir-rahman-rahim_ 6⃣0⃣ "Halan yau mahaukaciyar ta keta maka kaya, dan nasan dai ba fyad'e zaka mata ba, kuma ma ko hakane ai ba kaine farau ba bare ta tashi hankalinta, hasali ma kai *jihadi* kayi." Da wani irin matsanancin yanayin dashi kanshi baisan ya shiga ba yake kallonta, kasa cire belt d'in yayi ya matso kusanta yace "Zubeida, anya kina da hankali kuwa, kinsan me kika fad'a, Khairat d'ince kike kira da mahaukaciya? to bata haukace ba kamar yanda kuka shirya, kuma da yardar Allah duk abinda kuka shirya kanku zai dinga komawa, tunda har yanzu kun kasa gane itace gaba daku kuma ta muku nisan daba zaku tab'a kamata ba, to bara yau na fad'a miki abinda kullum nake dannar zuciyata da karta fad'a miki haka." Sake matsowa yayi kusanta yace "kina cewa nayi jihadi ne na auri Khairat, to ki sani Zubeida kema a halin yanzu *jihadi* nake naci gaba da zama dake, kiyi tunani akan abinda na fad'a miki dan babu qarya a maganata, kuma ki sani akwai abubuwa da dama dana sani a game daku Zubeida amma na shanye, badan komai ba sai dan nasan Allah ma baya kama bayinsa da laifi d'aya tak, zaki ga bawa na laifi iya laifi amma sai Allah ya d'aga masa qafa, wala'Allah ya gyara a gaba ko kuma a mishi kamun kazar kuku, to akan me ni ba zan iya yi muku uzuri ba, amma kwata kwata kun kasa gane haka, to wallahi ba zan qara shiru ba, *Khairat ta fiki komai Zubeida, ta fiki zuciya mai kyau, ta fiki halaye masu kyau, ta fiki girma da matsayi ba'a wajena ba har a wajen mutane, kuma da yardar Allah babu abinda zai sake samunta ta sanadiyar jahilai irinku.*" "Zubeida, ina son Khairat, ina mata son da ban tab'a ma kowa irinshi ba, kuma wallahi zamu zauna da ita muyi rayuwa a tare, ki sani wannan ne na qarshe da zan sake miki uzuri akan banzan quruciya da tab'argazarki, nasan dole zaki ji zafin kalamaina, amma Allah ma yaga zuciyata na kasa jura ne, kuma nayi iya qoqarina na b'oye duk abinda yake damuna." A fusace ya fice daga d'akin ya nufi d'akin Khairat kamar yanda yake yi duk lokacin da ranshi ya b'ace, saida ya kai tsakiyar gidan ya tuna ko riga babu a jikinshi, bai damu ba haka ya ciro makullanshi ya bud'e d'akin ya shiga ciki, kwance yayi akan gado ya rufe ido yana tuno 'yar rayuwar da sukayi da Khairat da farin cikin daya samu a tare da ita, ya jima d'akin kafin ya shiga douche yayi wanka ya fito ya shirya, fita yayi baibi takan kowa ba bare wata Zuby. Yana kan hanyarshi ta zuwa ma'aikatarshi yaga motar Salim a gabanshi, wani banzan kallo yama mota kafin ya fara binshi a baya zuciyarshi na raya mishi abubuwa da dama, yana binshi har saida ya shiga wata unguwa da babu mutane sosai, qofar gidan da yayi parking yasa Umar Faruk fitowa shima daga mota, yana kallo ya shiga cikin gidan sai dai bai iya binshi ba saboda yaga irin gidan nanne da an bud'e qofa za'a san wanda ya shigo, yana nan tsaye harya fito tare da mahaifiyarshi Odette, tare suka shiga mota suka d'auki hanya kuma, binsu yayi har suka sauka unguwarsu Khairat amma nesa da gidansu a gidan wani d'an siyasar mai neman kujerar Papa, murmushi yayi ya d'auki glass d'inshi mai baqaqen ido yasa, sake kallon qofar gidan yayi yace, "Yanzu ainihin maganar zata fito fili, yanzu ne zanyi *jihadin* gaskiya, dan dole saina dawo da farin cikin masoyiyata da iyayenta." Wani murmushin ya sakeyi saboda ganin Salim ya fito ya shiga mota yayi gaba, cewa yayi "da sannu kai zaka warware min komai." Binshi yayi ya kira wayar Aliyu, yana d'auka ya fad'a mishi inda yake yace ya sameshi, ba b'ata lokaci Aliyu ya sameshi saboda yana da abin hawa, sauka yayi daga motanshi ya shiga motar Umar Faruk, kallonshi yayi yace "yah Umar lafiya kace na sameka nan?" Nuna mishi motar Salim yayi yace "kaga wannan motar?" "Eh na gani." Nuna mishi Salim yayi dake cin abinci a restaurant d'in yace "kaga mai ita can, ina so ne daga yanzu ka fara bibiyarshi, kuma ina so na dinga sanin duk inda ya kasance." "Shikenan yah Umar, insha Allah zanyi yanda kace." Nan ya bar Aliyu shi kuma ya koma unguwar da Odette take, kasancewar yana da kati hakan yasa ya wanke mutanen unguwar ta hanyar tambayarsu wacece Odette, cikin tsoro suke fad'a mishi duk abinda suka sani a kanta, daga nan ma komawa yayi gidan *Alhaji Sani Saley* ya kasa ya tsare har saida yaga fitowar Odette. Ganin a qasa take tafiya yasa ya d'an jira yaga inda zatayi, yana kallonta kuma sai yaga mota biyu sun fito daga cikin gidan, mai gadi ya gani ya rufe qofar ya zauna qofar gidan akan kujera, saida yaga b'acewarsu sannan ya fita daga motar ya nufi wajen mai gadin, sallama ya mishi suka gaisa kafin ya kalli hanyar da Odette tabi yace, "Abokina dan Allah tambaya nake, wannan matar data fita ba Odette bace kuwa?" Ya rik'e sunan ne tun ranar da Papa ya fad'a, kasancewar mai gadin mai hankaline yasa yace "itace, lafiya, ka santa ne?" Ganin bazai bada matsala ba yasa Umar Faruk gyara tsayuwa yace "sosai ma na santa, tana zuwa harnan kenan?" "Eh, tana zuwa nan, ai mutuniyar mai gida ce sosai." "Ok na gane, na gode sosai, amma naga mai gidan ya fita, shin kasan inda yayi?" "A'a, ban sani ba gaskiya." "Shikenan na gode." Hannu ya bashi kafin ya wuce, wani abokinshi ya kira mai sunan *RB* ya nemi sani akan *SS* wato Sani Saley....... *Yanzu fa Umar Faruk zai fara nashi wasan* Kwana ma wuya yakewa Umar Faruk yanzu sobada binciken da yasa gaba, kuma cikin ikon ubangiji ya tara hujjoji masu yawan gaske akan Sani Saley da Odette, dan ko rintsawa bayayi sai bincike da tambaya, ya samu masaniya tun daga yanda Odette ta fara harkarta har zuwa yanzu, kuma komai rubutashi yake yana copie d'inshi a wayarshi. *Yau* ma kamar kullum tafe yake cikin sabuwar motar daya siya izuwa wani gida da wajen bincikenshi a fad'a mishi zai samu masaniya akan duk abinda suke shiryawa game da maganar Salim, yana zuwa daidai kwatancen ya fito daga mota ya nufi gidan, a hankali ya tura qofar sai yajita a rufe, tsaye yayi yana d'an kalle kalle ya hango wani yaro, qarasawa yayi yana fad'in "sannu yan samari, dan Allah masu gidan nan basa nan ne?" Kallonshi yaron yayi yace "ai duka mazane ba mata." Da mamaki ya kalli yaron amma saiya share, shafa kan yaron yayi ba tare da yayi magana ba ya koma qofar gidan, d'aga kai yayi ya kalli katangar yaga bata da tsayi sosai, yar dariya yayi a ranshi ya tuna ranar daya ma su Musa kutse a cikin gidansu, kallon unguwar yayi yaga ba hayaniya sosai, tsalle yayi ya rik'e katangar ya haura ciki, yana direwa ya tsaya yana kallon gidan, idonshi ne ya sauka kan takalmin dake qofar d'akin, da sauri ya qarasa jikin bishiya ya b'uya yana jiyo tashin muryoyi, cikin sand'a da dubara ya dinga takawa har ya kai bakin window ya leqa, abinda ya gani shi yasa shi saurin yin qasa yana waro ido waje da tsananin mamaki..... Da d'an k'arfi ya furta "su Musa, taya hakan zata faru, mutane dake kurkuku me zai kawosu nan, ko dai anyi bellynsu ne?" Sake leqawa yayi ya tabbatar sune dan haka kawai ya qarasa qofar ya bud'e sakatar qofar a hankali ya fita, da hanzari ya bar unguwar yana tunanin abinda ya gani, Khairat ya kira wacce ke zaune gaban Mamie ta aje mata farfesun kaji tana ci😭(ina ci my Hajiata), koda ta d'auka yace ta taimaka mishi da lambar wannan gendarme d'in daya qwamushe su Mama, yarda da kanta yasa ba tayi tunanin komai ba ta aika mishi da lambar. Cikin sa'a ya samu lambar Abdul waid, koda ya fad'a mishi wanene shi ya samu tarba ta musamman, tambayarshi ya fara yi ko yasan wanda sukawa Khairat fyad'e? amsar dai itace "eh, lokacin dana dawo nan da aiki ake nuna min su." nan ya tambaye ko zai iya sanin shekara nawa aka yankewa su Musa, nanma fad'a mishi yayi yaji ko shekara basuyi ba a cikin shekarun da aka d'iba musu, d'orawa yayi da "amma kuma taya za'a sakesu bayan basu cika wa'adinsu ba, taya za ayi irin haka?" Nan Abdul waid ya fad'a mishi basu da laifi a ciki daga samane aka yanke hukuncin a sakesu saboda wani babbane yazo bellynsu, tambayarshi yayi "wa yayi bellynsu?" "Sani Saley ne." cewar Abdul waid. Suna gama waya yana ci gaba da tafiya kuma Aliyu ya kirashi, yana dauka nanma ya fad'a mishi yau ma gasu a gidan nan dake unguwar *Lazare*, da mamakin abinda ke kai Salim gidan Umar Faruk yace " kaci gaba da saka masa ido, an jima zaka kawoni gidan." **************** Tafe suke a mota shi da Aliyu suna yar hira har suka isa wannan gidan, saida suka fito Aliyu ya nuna mishi sannan ya shiga gidan cikin baqaqen kaya, sallama yayi matar dake zaune ita kad'ai ta amsa mishi, sai dai a tsorace take sosai musamman da Umar Faruk yace "sannu Mama, sunana Faruk, kuma ni jami'in bincikene na farin kaya, nazo ne zan miki wasu tambayoyi, fatan zaki bani hadin kai ba saita kaimu ga tafiya dake ba offishinmu." Cikin saurin kuka matar ta fashe da kuka tace "na shiga uku ni *Salmu*, dama nasan wata rana sai Salim ya jawo min magana, yallab'ai wallahi zan fad'a maka gaskiya, ba saika tafi dani ba." Kujera Umar Faruk ya janyo ya zauna tare da fad'in "bismillah." a zuciyarshi kuma istigfari yake akan qaryar da yayi yanzun... _Hummmm, ranar fa ta kusa zuwa._ 29/08/2019 à 14:33 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *JIHADI* _Umar faruk_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _NA_ _SAMIRA HAROUNA_ _DEDICATED TO_ *MA FAMILLE* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 _My sweet and lovely Dotana *(Khadija Journaliste)*, ina tayaki murnar fara wannan novel mai sunan *Rayuwata ce*, a gaskiya na jinjina miki sosai musamman yanda kika d'auko yanda ya kamata iyaye su tarbiyanci yaransu, Allah ya baki ladar fad'akarwar daki kayi niyya._ _Bismmilahir-rahman-rahim_ 6⃣1⃣ "Ina jinki Mama." ya fad'a yana fito da qaramin littafin ajiye muhimman bayanai a aljihunshi da alqalami. "Ina so nasan meye tsakaninki da yaron nan Salim da yake yawan zuwa gidan nan?" Cikin muryar kuka tace "Salim, Salim dai d'ana ne, ni na haifeshi, kuma maraya ne mahaifinshi ya rasu, matsalar Salim rashin jin maganata, a lokacin da yazo min da maganar zaije a matsayin d'an wani babban mutum saida na hanashi, amma sam yaron nan yak'i jin maganata, amma bansan komai ba wallahi." Shiru tayi haka ma Umar Faruk yana rubutun basaja kamar gaske, jin shiru yasa ta marairaice tace "dan Allah yallabai ka taimakeni kamar yanda Allah ya taimakeka, ka rufa min asiri karka kama yaron nan dan Allah, wallahi shi kad'ai gareni kuma shima ni kad'ai gareshi, idan ka taimaka mana wallahi zanja mishi kunne, kai har garin ma zamu bari na mayar dashi wajen dangin mahaifinshi, dan Allah ka taimaka." Kallonta Umar Faruk yayi yace "Mama, kinsan girman laifin da d'anki ya aikata kuwa? ya yarda ya zama d'an wanda baiji ba bai gani ba, hakan ya ruguza rayuwar wannan bawan Allah, ya kuma dagula farin cikinshi dana iyalinshi, taya kike tunanin zai samu sassauci?" "Dan Allah ka taimaka ka min rai, wallahi ba zai sake ba, kuma talauci na daga cikin abinda yasashi aika hakan." Saboda yanda take kuka yasa yace "shikenan Mama daina kukan, insha Allah zamu duba al'amarin muga yanda za ayi." "Na gode yaro, na gode sosai, Allah ya saka maka da alkairinsa." Kiran daya shigo wayarshi ne yasa yaja "ameennn." d'in, fito da wayar yayi ganin lambar babanshi na uku ne ya kira (Bala) yasa ya tashi tsaye tare da d'aukar kiran, abun mamaki muryar macece tace "Hello Umar Faruk ne?" "Eh nine." "Dan Allah kayi sauri kazo, Alhaji ne yace a kiraka kazo." "Ince dai lafiya ko?" "Ba lafiya, jikinshi ne yayi qamari, kuma ruwan addu'a daka bayar ma ana bashi sam yau yak'i ya karb'a." "To shikenan, gani nan zuwa." Yana fad'a ya kashe wayar ya fita ya manta ma da inda yake, da azama ya shiga motar yaja suka d'auki hanya, Khairat ya kira tana d'auka yace "baby, Salim yana gidane?" "Salim kuma, lafiya?" ta tambaya da mamaki. "Lafiya lau, ki duba min dan Allah. Mamie ta kalla dake gefenta ta tambayeta, "yana d'akinshi har yanzu." cewar Mamie. Maida mishi tayi da "yana d'akinshi bai fita ba, lafiya dai ko?" "Lafiya lau, dan Allah zaki iya samo min lambarshi?" "Baby, lafiya, me yake faruwa ne?" "Babyyyy, kiyi abinda nake fad'a miki mana." "To naji." Mamie ta sake kalla tace "kina da lambarshi wai?" "A'a, me zanyi da lambarshi ni kam, sai dai ki tambayi mahaifinki." "Babu mai lambarshi a gidan nan sai wada yake zaune dominshi, bara na tambayar maka." "Yawwa 'yar aljannata, ina jiranki." Cikin mintuna qalilan ta tura mishi lambar bayan ta karb'a daga wajen Papa, yana ganin lambar yasa Aliyu ya d'auketa a wayarshi sannan yace "kasan dubara da za kayi mishi irin taku ta matasa da za tasa ya kai kanshi wannan sabon filin dana siya wanda ke *Yantala*." Akan titi ya tsaya ya saukeshi Aliyu na mamaki da tunanin yanda zaiyi ya kaishi wajen, da qyar ya samu dubara ya kira lambar, ba jimawa ya d'aga Aliyu ne yace "yane Baabaa, ka fita ko kana gida?" Fad'uwa kawai gabanshi keyi, cike da qasaita Salim yace "waye kai kuma?" Cikin murd'awar 'yan ciki Aliyu ya dake yace "kana nufin baka d'auki muryata ba kome?" Cikin d'an sakin fuska Salim yace " *Rabilou* kaine?" Cike da dakiya Aliyu ya nuna mishi shima matashin zamani ne yace "shege baabaa, nine mana, dan Allah kazo ka d'aukeni ina nan yantala." Cike da isa Salim yace "kai ina motar taka take, mema ya kaika can unguwar?" "Motarce ta bani matsala, yanzu haka ma da wayar makaniken ne na kiraka tawa ba caji, abinda ya kawoni kuma idan kazo na fad'a maka." A gadarance yace "Ina kan hanyar kita daga gida, ka jirani kawai." "Sai kazo." ya fad'a ya kashe wayar, wata ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, dan ba qaramin sauqi bane cika aikin Umar Faruk, da azama ya tari taxi ta kaishi can kafin shi ya isa wajen. *************** Umar Faruk na barin nan gida ya wuce dan amsar wasu ruwan addu'a a wajen Baba, da karsashi ya shiga gidan da fad'in "assssss..." Sallamar tashi ce ta maqale a maqoshi saboda ganin hasken fila a kewayen Khairat alamar akwai mutum a wajen, a hankali ya sulala yana takawa danshi gani yake Khairat ce zata masa bazata, leqawa yayi ta katanga sai yaga Zuby ce ke barbad'e a qofar d'akin, mamakinshi bai yawaita ba saboda ba yaune farkon ganinshi ba, dan haka ya qura mata ido yana kallo harta gama zata juyo yayi saurin cewa, "Sannu da aiki 'yar gidan d'an me ganye." 😂😂😂😂😂😂 Wani irin fad'uwa ne gabanta yayi had'e da kad'awar 'yan cikinta, tsabar tsoro ne yasa ta jefar da ledar maganin da wayar hannunta, kasa kallonshi tayi tunda tasan ko waye, a hankali ya zagayo yana kallonta harya sunkuya ya d'auki kayan data zubar, janyo hannunta yayi ya bata kayan yana ci gaba da kallon fuskarta, ganin dai ta kasa cewa komai yasa yace, "Wannan itace damarki ta qarshe Zubeida, da ace a abinci nane na samu kina zubawa kamar yanda na tab'a gani, to da zan iya yafe miki kuma na zuba miki ido, danni yanzu ban damu da rayuwata ba kamar yanda na damu data wasu, wasun kuma ba kowa bane face iyalina, ba zan iya miki uzuri ba Zubeida dan kina qoqarin cutar da wacce tafi rayuwata mahimmanci ce, akanta kuma sai inda k'arfina ya qare, Zubeida ki gafarceni, amma dole zan d'auki matakin da nasan ba zai miki dad'i ba, na d'aga miki na miki uzuri duk saboda tunanin zaki shiryu wata rana, amma matsalar tana ga mahaifiyarki ne, ni kuma ban isa na rabaki da ita ba, saboda uwa uwa ce, dan haka zan saukewa kaina nauyin nan, kije *na sakeki saki d'aya*, ban sakeki saboda Khairat ba sai dan na fahimci babu Allah a tare dake, kuma ina neman alfarma da karki fad'awa kowa dalilin rabuwarmu, dan ke zaki fi cutuwa da hakan, Allah ya sadamu da alkairinsa, ki kula min da yarona ko yarinyata." Juyawa yayi zai fita tayi saurin rik'e qafarshi ta zube qasa tana kuka tana fad'in "yah Umar kamin rai, dan Allah kar kamin haka, wallahi na tuba ba zan sake ba, wal....." Rufe mata baki yayi ya sunkuya yace "zaifi miki kiyi shiru kar mutane suji, zaifi kyautuwa ki bar gidan nan ba tare da kowa yaji ba." Fit ya fice ya koma d'akin Baba, sallama yayi shiru dan haka ya tura qofar, jin ta bud'e yasa ya leqa amma Baba baya ciki, da hanzari ya shiga ya nufi wajen ruwan addu'a da yake da tabbacin sune, dauka yayi ya fito ya rufe d'akin, motarshi ya hau kai tsaye ya nufi gidan Bala. *************** Koda yaje ya samu jikin ya tsananta sosai, tallabo kanshi yayi da niyyar bashi ruwan, yana zuba mishi a baki ruwa suka dinga gangarowa suna fita daga bakinshi, aman da Bala ya fara tare da jini ne yasa Umar Faruk saduda ya kalleshi a matsayin gawa, danya tabbatar wannan karan aljanu sun raina masa hankali, dan lokacin farko daya fara taimakawa Bala sai suka nuna sun tafi, amma ganin hakan a yanzu ya nuna mishi suna cikin jikinshi kuma sun mishi raunin da harya tab'a zuciyarshi, da qyar Bala ya rik'e hannun Umar Faruk ya fara magana cikin rawar jiki yana fad'in "ka ka....ya femin.....ka roqar min..." Bai qarasa ba ya fara da "Ashhadu an la'ilaha illalah.....tare da taimakon Umar Faruk ya qarasa karlmar shahada. Koke koke iyalinshi suka fara amma dole dai ayi hak'uri. 😭😭😭😭😭😭 *Zuby anyi rashin uba* Dare ne dan haka suka d'aukeshi izuwa asibiti dan a ajeshi wajen ajiyar gawa, tun a hanya Aliyu ya kira ya fad'a masa Salim na kan hanyar zuwa wajen, dan haka koda ya ajesu ya taka mota da k'arfi ya isa wajen, kuma zuwanshi yayi daidai da isar Salim wajen yana kiran lamba da Aliyu ya kirashi, Aliyu na ganin motar Umar Faruk ya fito daga wajen daya b'uya danya kalli drama, fitowa yayi daga mota ya tunkari motar Salim, shima yana ganinshi fitowa yayi da niyyar yi mishi magana, da fara'a Umar Faruk ya bashi hannu suka gaisa yana fad'in, "Petit frère (qanena), yana ganka nan?" Jin Umar Faruk bai saki hannunshi ba kuma yana nufa dashi wani kango yasa yace "ina jiran wani ne anan." A lokacin har sun shiga ciki, sakin hannunshi yayi ya tsaya bayanshi, juyowar da zaiyi ya d'aukeshi da mahaukacin marin da yasa ya fad'i kwance kamar sumamme.... _Hhhhhhhhhhh, akwaita fa_ A firgice Salim ya tashi zaune yana dafe da kunci yana ja da baya yana kallon Umar Faruk dake matsowa kusanshi, "kai, meye haka, kana da hankali kuwa, kasan me kayi, ni ka mara? wallahi zaka....." bai qarasa ba Umar Faruk ya matso kanshi ya shaqo wuyan rigashi, jayoshi yayi qiiiii a qasa har saida ya kaishi gaban wani dakali sannan ya zauna ya sashi gaba yana qara had'e rai, kukan da Salim keyi ne yasa daka mishi tsawa yana fad'in "yimin shiru." Tsaf Salim yayi shirun yana kama baki, a kausashe yace "tambayarka zanyi, kuma ina buqata sanin gaskiyar al'amarin, idan kuma kamin qarya, wallahi saika gwamaci kid'a da karatu." Kai kawai Salim ke d'agawa alamar toh, cikin daga murya yace "kana jina?" "Eh, ina jinka, wallahi ba zan maka qarya ba." "Da kyau." Umar Faruk ya fad'a yana shafar fuskarshi da hannu d'aya, d'aya hannun kuma ya ciro wayarshi ya dannan wajen records d'in murya kafin ya d'ora da "naje har gidanku, kuma na gana da mahaifiyarka ta fad'a min komai, dan haka abinda nake son sani daga gareka shine, ya akayi ka shirya duk abinda aka shirya, sannan su waye masu hannu a ciki?" Gyara zama yayi yana shafar kuncinshi dake mishi zugin zafin masifa ya fara da "wallahi son kud'ina ne ya jamin nayi duk abinda nayi, mun fara had'uwa da Odette ne a unguwarmu taje gidan wata qawarta 'yar fara, itace ta fara min magana tace wankana ya birgeta, na nuna mata jin dad'ina saita d'auki kud'i ta bani, daga nan duk lokacin da tazo saita nemeni mun gaisa, shine wata biyu daya wuce tazo min da maganar tana so ta sani wani aiki, nan ta fad'a min zanje gidan Mani Bukar a matsayin d'an da suka haifa bata hanyar aure ba, amincewar da nayi yasa ta fara kaini asibiti aka min gwajin da ake so yazo d'aya dana Mani Bukar, cikin ikon Allah sai jininmu yazo d'aya amma sauran qwayoyin hallitarmu sunsha banban, nan ta sanya likitan ya rubuta duk wani gwaji ya zama iri d'aya tsakaninmu ta yanda zan zama kamar d'an cikinshi, kuma bata tsaya nan ba saida ta ziyarci asibiti har hud'u wanda tasan Mani Bukar zai iya tuntub'a idan har bai yarda da abinda muka zo mishi dashi ba, daga cikin likitocin da Papa ke huld'a dasu harda likitanshi na gida daya yarda dashi fiye da kima, hakan yasa ta had'a takardu na qarya da zasu nuna ni d'anta ne kuma jinin Mani Bukar, kuma koda aka kawoni ma muka je asibiti wannan sakamakon qaryar aka fad'a mishi da yasa na zama d'anshi." Shiru yayi yana zare ido yana kallon Umar Faruk, ganin yana kallonshi yasa yace "ina jinka, baka fad'a min masu hannu a ciki ba." "Odette, itace alhakin shirya komai, amma dai nasan tana aiki da Sani Saley." "Bayansu baka san wasu da take mu'amula dasu ba?" "Gaskiya ban sani ba, amma dai akwai wata mata da suke zuwa tare da 'yar fara, ranar ma dana kai Odette gidan Sani Saley na tarar da wannan matar tare da 'yar fara, sai kuma wasu samari guda hud'u, naji da kunnuwana suna magana akan wani shiri da zasuyi akan Mani Bukar, amma bansan ko menene ba." "Kenan baka san waya tura maganar kai d'an Mani Bukar bane a social media?" cewar Umar Faruk. "Na sani, wannan samarin ne, kuma naji suna cewa zasu tattaro sauran matan da Mani Bukar yayi alaqa dasu." Hararanshi Umar Faruk yayi yace "kar kamin qarya fa." "Wallahi ba qarya bace, basa doguwar magana idan ina wurin." "Kenan su sukace ka dingawa iyalenshi iskanci da shaqiyanci?" "Eh, saboda suna so na baqantawa matarshi rai da Khairat, kuma wannan matarce tace na dinga yin haka, amma duk kud'ad'en da nake amsa nine keyin gaban kaina saboda na samu na fitar da kaina kafin ta kwab'eme mumu." "Wacece matar?" ya tambaya a daqile. Shiru yayi alamar tunani kamar kuma an tsokaleshi sai yace "yawwa na tuna, sunan *Asma'u*." Wani bazawarin murmushi yayi na gefen labb'a, tsayar da d'aukar yayi a wayarshi sannan ya tashi tsaye yana fad'in "bansan ko zan iya taimakonka ba idon doka tazo hawa kanka, dan haka kayi ta kanka." Ficewa yayi ya samu Aliyu suka d'auki hanyar gida, kiran Khairat ne ya shigo wayarshi ya d'auka, "Ka kyauta baby, wuni d'aya har ana shirin kwanciya bacci amma ka kasa zuwa gaka matarka da yaronka." Cike da kasala yace "ayyah baby, kiyi hak'uri ki yafe wa wannan hamagon mijin naki, yanzu haka a hanya nake zanje gida, abubuwa sun faru da dama yau d'in nan, amma dai zuwa gobe da safe nasan zakiji wasu labarai marasa dad'i." "Subhanallah, meye faru baby?" "Um um, ba yau ba, saida safe zan fad'a miki insha Allah." Cikin kukan shagwab'a tace "yanzu kenan ba zaka zo ka ganni ba, nifa ina son ganinka." Cikin rikitaciyar murya yace "na fiki son na ganki, kin manta yaushe rabon damu had'u ne? aiki shirya kawai, amma idan na kamaki wallahi dole yarona ya samu ingantanccen abincinshi yaci koya samu kuzari." "Kai baby , wane irin abinci kuma?" Saida ya d'an cije lips kamar yana gabanta yace "wannan sirri ne, amma idan na daukoki kika dawo gidana, to zaki sani." Cikin wani kukan shagwab'ar tace "hum hum, wallahi ni har kasa na fara jin tsoron had'uwarmu, dan kasan fa ba 'yar qaramar jarumta nake yi ba wajen d'aukarka, amma yanzu nasan zaka sausauta min saboda abinda ke cikina." Darayi yayi yace "ashe ana jin maza dauriya kawai akeyi, to karki damu, jarumin mijinki zai dinga sassauta miki, kiji dad'i abinki *maini*." "Yawwa yaron kirki, ina sonka." "Nima ina sonki alkairina, saida safe." Yana kashe wayar ya kalli Aliyun da yake kallonshi kamar wani gunki, maida hankalinshi yayi ga tuqi yana fad'in "yadai Aliyu, da matsala ne?" Ajiyar zuciya ya sauke yace "gaskiya da matsala." "Tame?" ya fad'a yana kallonshi. Gyara zama yayi yace "yanda naji kuna farin ciki kai da aunty Khairat, saiya qara min son aure a zuciyata wallahi." Murmushi kawai yayi suka ci gaba da tafiya, saida suka kusan kaiwa gida sannan yace "kana son aure kenan?" "Ina so, amma kasan ba lallai malam yamin ba." "Me yasa?" "Saboda nayi qarami." Daga gira yayi sama yace "a hakan, kana shakara ashirin da d'aya ne za ace kayi qarami, gashi kuma soyayyar wasu ma na birgeka, kaga indai kana so ni zanyiwa malam magana, kuma kaima kasan zai fahimta, fatana kawai Allah ya had'a da mace ta gari mai tsoron Allah, faqat." "Ameen yah Umar, ai yama had'a insha Allah." "Toh , wacece wannan?" ya tambaya cikin 'yar dariya. Shima cikin dariyar yace "wannan yarinyar mana, qanwar aunty Saratu, *Firdaussi*, gaskiya ina sonta, kuma tana da hankali sosai." Shiru Umar Faruk yayi yana tuna kullum tazo gidan nan to ranar gidansu saiya shaida tazo saboda hidimar da take mishi, bugu da qari inhar zata gaishe dana sama da ita to zata sunkuya har qasa, da haka suka isa gida Aliyu ya nufi makwancinshi sai Umar Faruk daya shiga d'akin Baba ya fad'a mishi rasuwar Bala, fitowa yayi ya baroshi yana jimamin abin, d'akin Zuby ya kalla yaga amma yaga alamun tana ciki, tab'e baki yayi ya wuce d'akin Khairat, dan iba tilastashi za ayi ba ba zai tab'a maido da ita ba cikin sauk'i haka. *Washe gari* da safe duka mazan gidan malam ya had'a kansu suka tafi wajen jana'izar Bala, Zubeida na d'aki bata san wainar da ake toyawa ba tanata had'a kaya, su kuma basu fad'a mata ba saboda ganin halin da take ciki, sun jima zaune acan kafin suka taso suka dawo gida, sai lokacin Zuby tayi niyyar barin gidan saboda tunanin malam ba zai bari ba, Umar Faruk na shirin shiga d'akin Mama Zubyta fito da kaya da ciki, Mama ce tayi saurin cewa "Ina zuwa haka Zubeida?" Tana kallon Mama saita fashe da kuka, hankali tashe Mama tayi kanta da sauran matan gidan suna tambayar lafiya, durqushewa tayi a wajen tana ci gaba da kuka, haushi ne yasa Umar Faruk qarasa shiga d'akin ya zauna yasa kwanan abinci gaba yana jiran a kirashi, cikin kuka tace "sakina yayi." "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." shine abinda uwayen suka fad'a a tare. Baba ne yace "saki fa, Umar Faruk d'in?" "Kai Umar." cewar Baba cikin d'aga murya. Da "na'am" ya amsa yana fitowa daga d'akin, yana zuwa gabansu ya durqusa yana sauraronsu, "me yarinyar nan ta maka da zaka saketa a wannan halin, me yake damunka ne?" Ba tare daya kalli Baban ba yace "Baba ku gafarceni, nasan hakan ba zai muku dad'i ba dama, amma nasan kunsan haka kawai ba zan d'auki wannan matakin ba ba tare da wani dalili ba, a gaskiya zamana da Zubeida ba zaici gaba da yiwuwa ba a haka, shi yasa na kawo qarshen abin." "Meta maka, wane irin laifi ta maka da zaka yanke wannan hukuncin a kanta, kasan abinda zai iya biyo baya a dalilin abinda kayi?" cewar Mama cikin hushi. "Babu abinda zai faru Mama, kuma fa Allah ne ya hallata aure ya kuma hallata saki, amma gata nan ku tambayeta idan nayi mata rashin adalci a wannan lamarin." Maida kallonsu sukayi gareta Mama tace "me kika mishi ke kuma?" Shiru tayi sai goge hawaye take, Baba ne ya qara "me kika mishi Zubeida?" Kallon Umar Faruk tayi da tace bata mishi komai ba, amma ganin shima ita yake kallo, dan haka tayi shiru daga abinda taso fad'a, ganin ta kasa magana yasa ya mike yana fad'in "bance ki fita daga d'akinki ba ai, ki zauna anan harki haihu." yana fad'a ya fita daga gidan, hanya ta kama zata fita Mama tace "a'a babu inda zaki je, ki zauna kiyi iddarki kamar yanda yace." Duk da cikin kuka take saida tace "Allah ya sawaqe, kenan ni gani marar zuciya, ya sakeni kuma yace na zauna nayi idda anan, to ba zai yiwu ba wallahi, ai nima da gidanmu, kuma kunfi kowa sanin inda ya d'aukoni, dan haka banga wanda ya isa ya rik'eni ba wallahi." Zata wuce Baba yace "kash Zubeida, banji dad'in fitar wannan kalma daga bakinki ba, abinda muka fad'a miki yanzu ba fad'armu bane, wannan fad'ar ubangijinmu ne wanda shi yafi sanin daidai yake kuma tsara mana rayuwarmu, karki bijerewa umarnin Allah da manzonsa, hakan zai iya jefaki cikin hushin ubangiji, amma in kinga hakan bai miki ba to ga hanya nan ki wuce." Suna kallo itama ta sulalata fita daga gidan tana kuka, Mama kuma haushin Zubeida ne ya kamata sosai, sai taji koba komai d'anta zai iya tsira daga sharrin 'yar uwarta. *************** Koda taje gida ta fad'awa tanti tashin hankali da masifa kam ta shasu, zagi kuma ba Umar Faruk ba har malam ya samu rabonshi, haka dai ta gaji da masifa Zuby na sauraranta harta d'auki gyalenta ta fita daga gidan. _Hmmm, yanzu ma kika fara gani._ ***************** Shima koda ya fita daga gidan gidansu habibiyarshi ya nufa, da sallamarshi kuwa suka amsa mishi suna zaune falo, kamar yanda yanzun ya fara zama jiki a wajen Papa zaman gida, zaune yayi suna gaisa har Salim ya fito daga d'aki, kallonshi kawai Umar Faruk keyi wanda Salim kad'ai yasan ma'anarhi, saida ya zo tsakiyar falon ya sunkuya yana kallon Umar Faruk yace "Ina kwananku." Papa da Mamie basu amsa ba saboda mamaki, sake fad'in "ya tashin asuba?" "La...fi.....ya lau." cewar Papa yana mamaki. Murmushi Umar Faruk ya kalli Mammie yace "Hajiata ina d'aya Hajiar tawa?" Turo baki tayi da kawar da kai tana fad'in "ban sani ba." Mikewa yayi tsaye ya matsa kusanta yace "ran gimbiya ya huce, kinsan bana son hushinki, fad'a min inda zan ganta ko hankalina ya kwanta?" D'an dukan damtsenshi tayi tana fad'in "hankalin sarki ya kwanta, sarauniyar tana d'aki." Da dariya ya nufi d'akin ya bar Salim durqushe anan, yana ganin Umar Faruk ya shige d'akin Khairat ya mik'e tsaye da sauri ya bar gidan gabanshi na fad'uwa yana tunanin ta yanda zai bar gidan nan cikin sauqi, bai zame ko ina ba sai gidansu wajen mahaifiyarshi, da shigarshi ya fad'a d'akin nasu daba kayan kirki, tana kwance ya fara kiran sunan "Ma, Ma, tashi dan Allah zama bai kamamu ba." Tashi tayi zaune tana kallonshi, "Maa , ki tashi fa." "Meya faru, ka sake jangwalo wata tsiyar ko? anya Salim kana tuna waye kai?" duk tayi maganar ne tana tashi tsaye. Kallonta yayi yace "Maa, ba lokacin wannan nasihar taki , yanzu ki had'a mana kayanmu gaba d'aya ki kimtsasu, daga yanzu zuwa ko wane lokaci zanzo mu wuce *Maradi*, tunda can danginmu suke." Yana fad'a bai tsaya jin ta bakinta ba ya fita a guje, ita kuma da kallo ta bishi har saida ya fita, fashewa tayi da kuka tana fad'in "Salim wace irin rayuwa ka jefa kanka cikinta ka jefani , me zan fad'awa dangin mahaifinka yanzu idan wani abu ya sameka?" Ganin bata da wani zab'i yasa ta fara had'a musu kayansu, dan ita kanta tayi farin ciki da hakan idan suka bar garin. ************** Yana shiga ya sameta kwance tana bacci, zaune yayi kusanta yana kallon fuskarta ganin kyawunta harya fara dawowa, ya jima yana kallonta kafin ya tasheta, da taimakonshi ya cire mata kaya ya kaita bayi dan wanka, harya ajeta a cikin bahon wanka yana kallon tanqamemiyar douche d'in, a zuciyarshi kuma yana sake jinjina hak'uri da sadaukarwar da Khairat tayi domin aurenshi, kallon ko ina yake yana ganin tsabagen tsagwaron kud'in da aka narka wa bayan gida kad'ai, wannan idan ka shigo ai awa d'aya ba zata saka ka fita ba *(inaga fa wannan shine dalilin da yakesa Khairat bata fitowa da wuri)*, ganin yanda yake kallon wurin yasa tace "baby ya dai?" Nunfasawa tayi yace "Ina kallon ikon Allah ne, ashe haka douche d'inki take da kyau da girma, shi yasa ranarki ta farko a gidana kika kasa shiga tawa douche d'in, gaskiya bayan ganin wannan kyakyawar douche d'in taki sai naji kunyar kaina." Ruwan cikin bahon ta d'iba ta watsa mishi tana fad'in "ka ganka ko, ni kuma yanzu nafi jin dad'in wacce qaramar." "Hum, wasu shashashu na cewa wai *jihadi* nayi na aureki, amma basu san cewa Khairat ce tayi *jihadi* ba data zauna da Umar Faruk." Hannu yasa cikin bahon ya fara zuba mata ruwa a jikinta, da kanshi ya mata wanka ta fito daga bahon ya b'oyeta cikin towel sannan ya kaita d'aki, kafin ya gama shiryata ya jima sosai da saida ya rage zafi sannan, a lokacin kuma suka fito falo tare ya fad'a musu rasuwar Baban Zuby, sunyi jimami sosai musamman Khairat sai taji kamar wani babanta ne ya rasu, shiryawa sukayi suma suka tafi wajen rasuwar. **************** Sai yamma tanti taji rasuwar nan sannan Zubyma taji, uba ubane, saida Zuby tayi kuka sosai tayi jimamin mutuwarshi, tanti ce tace ta shirya taje amma ita ba zata je ba, dan haka Zuby ta nemi rankiyar Zabba'u kuma ta samu. *Da safe* Zabba'u tazo suka wuce, Zuby taji inama bata je ba, dan matanshi ne suka dinga fad'in ita d'in yarshi ce amma basu san taya ta zama ba, nan aka fara tsurfa iri iri har zuwa ake ganin Zuby, wasu na tambayar wacece mahaifiyarta wasu na tambayar taya ta zama yarshi, saida ta gaji Zabba'u ta janyota suka koma gida. ************** *Kwana biyu* Umar Faruk ya qarasa had'a duk wasu hojjoji da suke nuna Salim ba dansa bane, kuma shirene na yan adawa tare da hadin gwiwar wasu tsofaffin masu laifi, abinda ya mishi dad'i sosai shine sake binciko mishi wani laifin Musa da Abdul Waid yayi, an sake kama shi da laifin yiwa wata budurwar fyade a wani qauyen *Agadez* da ake kira *Adarbisa* , babban abin farin cikin shine saida Abdul waid yasa wani jami'i dake can garin ya samo mishi cikakkiyar hujja a kan hakan, kuma anyi nasarar samun abinda ake nema, dan haka yau koda ya tashi da kanshi ya ziyarci offishin lawyer Papa. Bayan gaisuwa ya fad'a mishi abinda ya kawoshi, nan ya nuna mishi jin dad'inshi kuma ya mishi alk'awarin za'a shigar da qara nan bada jimawa ba, amma zaije a nemi amincewar Papa dasa hannunshi, alfarma Umar Faruk ya nema kan baya so asan da hannunshi a ciki, kuma ya amince da duk abinda ya fad'a, a haka suka rabu shi kuma ya kama hanyar auwa gidan Papa. *************** Koda yaje da maganar ta girgiza Papa sosai, Khairat kuma tace "ai dama na fad'a muku, wannan yaron ba zai tab'a zama danka ba kawai raina maka hankali sukayi." Da mamaki cikin rud'ewa Papa yace "taya haka zata kasance, docteur *Shehu* fa da kanshi ya mana gwaji kuma ya tabbatar." Lawyer ne yace "ka kwantar da hankalinka Alhaji, muna da duk wasu hujjoji a hanunmu , koma miye dai zaka ji." Umarni Papa ya bayar aka shigar da qarar, take aka kai magnar babbar kotu, kamar yanda aka sallama gidan Sani Saley aka bashi takardar sammaci, haka su Musa da sukaga takardar sukayi mamaki, dan a ganinsu babu wanda yasan da fitowasu bare mafakarsu, Odette ma na tsaka da jin dad'in rayuwarta aka kawo mata wannan takarda da tasata gudawa tsawon wannan yinin , tanti na d'aki aka sallama dan haka Zuby ta fita ta karb'o saqon , Zuby ta shiga d'akin ta samu tanti na waya, wayar da tasa cikin Zuby barazanar zubewa..... _Me kuma taji???_ **Muje zuwa*😘 *Kuyi hak'uri da rashin jina , qanwar mijina ce tayi saukan Qur'ani yau.* _Wanda suka kira ban d'auka ba kuyi hak'uri, duk kun kirane a lokacin da banawa ba, nasan dai kun fahimta saboda maganar ta manya ce, my Belle *(momyn khadija)*, naga kiranki kema, sorry, i love you all._ *************** 6📓2📓 Cike da kwankwanto tanti tace "Malam anya kuwa baka ka kashe Bala ba? danni nasan dai mun baka aiki akanshi." Jim tayi alamar tana sauraro, ta jima kafin tace "a'a wallahi babu ruwana ni, kai ka kasheshi, nidai kawai nace kasa su gane kurensu amma babu wanda nace ka kashe a ciki." Nanma shiru tayi alamar tana sauraro sannan tace "yanzu ya kake so nayi in aka ganewa hnnuna a cikin kisanshi? nifa na fad'a maka babu ruwana wallahi." tana fad'a ta kashe wayar ta jefa kan gado, juyowa tayi da nufin fitowa sukayi karo da Zuby dake sauraronta. Hawaye na zuba a idonta tace "Mama, dama ke kika kashe min mahaifi? lallai Mama kin wuce tunanina, wallahi ke shed'aniya ce ta qarshe, a gaskiya ba zan iya ci gaba da zama dake ba, wallahi gwara na fita ko akan titi ne na dinga kwanciya akan na zauna waje d'aya dake." "Kinga Zuby ba abinda kike tunani bane, bab.." "Ya isa haka." ta d'aga mata hannu, takardar sammacin ta jefa mata tana fad'in "ga wannan kad'an daga abinda kika shukane zaki fara girba." Tana gama fad'a ta shige d'akinta dama kuma bata gama barbaza kayanta ba, dan haka ta tattara ta fito duk da maganar da da Mama ke mata bata saurara ba saida ta fita daga gidan, tunani take inda zata nufa, gidan Uwani ta nufa, amma ina ta samu itama da matsalar data sha mata kai, dan dole ta barnan ta nufi gidan Zulfa'u, itama dai ta samu yanzu ba kamar da ba, dan tana fuskarntar tsangwama ta miji, dan haka bata tafi gidan Zabba'u ba kawai ta wuce gidan mahaifinta kamar yanda Uwani ta bata shawara tun farko, kasancewar anyi sadakar uku hakan yasa bata samu mutane sosai ba, koda ta fad'a musu ta dawo gidan mahaifinta ne tijara wasu suka fara mata, yayin da wasu ke cewa gadone ya kawota, saida ta nuna musu ba shine a gabanta ba kuma ai bata cikin magada kad'ai ta samu lafiyarsu, babbar matar Bala ce tace su barta ta zauna koba komai zasu moreta. ********** Hankalin SS ya tashi sosai, hakan yasa ya fita ya je ya samu malaminshi amma saiya fad'a mishi sune da nasara, badan komai ba saidan ya samu wani abu a wajenshi, bayan fitarshi kuma lawyern Papa yazo gidan SS amma bai sameshi ba, haka ya koma ba tare daya ganshi ba, yaso dawowa da dare amma bai samu dama ba, hakan yasa washe gari ya dawo ya sameshi, mai gadi ne ya mishi iso har cikin falon SS, kasancewar b'angarenshi daban ne yasa har mata na shigowa wajenshi ba tare da sanin iyalinshi ba, idan ma sun gani babu yanda sukeyi sai dai suyi shiru. Su Musa ya samu wajen suna tattaunawa, kasancewar su Musa sun sankomai sa game da Papa yasa yanzu haka suke shiri akan yanda zasu had'o duka karuwan da Papa yayi mu'amula dasu dan gabatar dasu a gaban kotu, gaisawa sukayi nan ya fito da duka hujjojin da Umar Faruk ya bashi, da mamaki yasa hannu zai karb'a kawai ya janye takardun da qaramar recorder da aka d'auki muryar Salim, murmushi ya masa yace "yana da daraja, dan haka zaka biya farashinshi." "Meye wannan d'in?" "Duk wasu hujjoji da zasu ruguza rayuwar siyasarka, dan da zaran wannan sunje gaban alqali, to babu tamtama cewar za'a yanke maka hukunci ba tare da ansha wahala ba, ni kuma bana son haka ta faru, shi yasa na kawo makasu danka biyani." Fizge takardun yayi yana fad'in "ka fad'i farashinka ni kuma zan biya." Yana fad'a mishi kud'in yace ya amince, kallonshi yayi yace "taya ka samu wannan hujjojin?" Nunfasawa yayi yace "surukinshi mana." "Wa kenan?" "Umar Faruk, wanda ke auren Khairat." Musa ne yace "zaka iya nuna mana shi?" "Eh to, yanzu bansan ina zan sameshi ba, amma ai gobe zaku had'u dashi a kotu, dan dole zaije duk da ya buqaci karna fad'i shiya samo hujjojin nan." "Allah ya kaimu goben." cewar Musa yana wata zazzafar qwafa. ************** Umar Faruk ne ya shigo gidan da sallama, Mama dake bakin panpo ta amsa mishi da fad'in "sannu da zuwa." "Sannu Mama, ya gida?" ya fad'a yana kallon d'akin Zuby, kallon Mama yayi yace "wai Mama badai yarinyar nan tafiya tayi ba?" "Um, ta tafi." Tsaki yayi ya wuce d'akin Khairat ya shirya sannan ya fito, kai tsaye gidansu Khairat d'in ya nufa, falo ya sameta zaune da doguwar riga mai siraran hannaye ta girke plate d'in wainar qwai gabanta da fritte sai yaji da take dangwalawa tana ci, da sauri ya zauna gabanta tare da d'auke robar yajin yana fad'in "kaji min yarinyar nan, yaji ne kike hambad'a haka? gaskiya bana so." Marairaicewa tayi tace "dan Allah baby ka bani, yafi dad'i da yajin mana." "Ki shiga hankalinki fa." ya fad'a yana rufe robar yajin. Turo baki tayi gaba taci gaba da ci tana kallonshi, shima kallonta yake yanda take cin abincin da matuqar birgewa, ganin yana kallonta yasa ta fara saka mishi a baki shima, Mammie ce ta fito cikin shiri zata fita, gaisawa sukayi Mammie tace "ni zan wuce saina dawo." "Sai kin dawo." cewar Umar Faruk. Khairat ce ta qara da "qawata ki siyo min abu mai dad'i dan Allah." "Kamar me?" cewar Mammie. "Abu mai dad'i fa nace." "To angama." Tana fita Khairat ta kalli Umar Faruk tace "baby, docteur fa yace da zaran na fara naquda muje asibiti." Sanin waye docteur d'in yasa yace "kinga ki rabu da wannan likitan, insha Allah da kanki zaki haihu, karma ki d'aga hankalinki kinji." "Amma fa baby...." "Amma me?" ya katseta. "Na fad'a miki karki damu, da kanki zaki haihu." Kallonshi tayi tace "a gaskiya ba zan bari nasha wahala ba, tunda yace ga yanda za ayi to kawai ayi yanda yace." A zafafe ya daka mata tsawa yace "na fad'a miki zaki haihu da kanki, karki qara min maganar banzan likitan nan." Kallonshi take kamar zata fashe da kuka, d'aga muryar da yayi ne yasa Mamie fitowa daga d'aki, Khairat na ganin Mamie ta tashi da qyar ta juya ta nufi d'akinta yana binta da kallo ganin yanda cikin ya fito sosai har yana mamakin girmanshi, zaune Mamie tayi saman kujera tana kallonshi tace "Umar Faruk, lafiya nake jiyo muryarka haka?" D'an sosa kai yayi yace "Mama akan maganar da likitan nan ne yayi duk tabi tasa a ranta ta yarda da abinda ya fad'a." D'an murmushi tayi itama tace "ayya, Umar Faruk ai dole ta yarda, gaskiya fa Shehu ya fad'a maka, dole a gaggauta kaita asibiti data fara naquda." A sauqaqe yace "Mama, karmu cire rai da rahamar ubangiji, idan muka kai kukanmu ga Allah zata haihu da kanta kuma lafiya qalau." Ajiyar zuciya Mamie ta sauke tace "abinda baka fahimta ba shine, Khairat na d'aya daga cikin irin matan nan masu matsatsen gaba, kuma nasan kasan haka a matsayinka na mijinta, ba zata iya ba da kanta wahala kawai zata sha in ba'a kaita da wuri ba." Shiru yayi yana tunani, ashe dama wannan ne dalilin da yasa take matse, ashe halitattar tace haka shi yasa kullum take shan wahala idan zan shigeta, lallai in haka ne kam ba lallai ta iya haihuwa da kanta ba, take ya fahimta ya kuma shiga d'akinta ya bata hak'uri akan tsawar daya mata. *Washe gari* an shiga kotu, a zaman farko lawyern Papa ya bada wannan qaramin recorder a matsayin hujjar data rage musu ita kad'ai yana fad'in "ya mai girma mai shara wannan itace hujjarmu ta farko kuma ta qarshe da muke da a hannu, da wannan d'aukar ne mai girma mai shari'a zamu samu adalci." Mik'awa magatakarda yayi, abin mamaki koda aka danna d'aukar sai akaji babu komai a ciki, dan haka lawyern SS ya mik'e ya fad'i ra'ayinshi akan ana so a b'ata sunan SS ne kawai, saida suka gama jawabansu tsaf alqali ya fara magana Umar Faruk ya d'aga hannu ya nemi izinin magana, umarni alqali ya bashi dan haka ya mik'e tsaye ya kalli tanti Odette dasu Musa sannan yace, "Ya mai girma mai shari'a, ina neman alfarmar kotu data sake bamu wata damar danmu sake kawo wasu hujjojin?" Saida alqalin yayi yan rubuce rubuce sannan ya kalli Umar Faruk ya kalli lawyensu yace "lawyen mai qara, mai zaka ce akan wannan qorafin?" Tsaye lawyer ya mik'e yana zufa da in ina yace "muna neman alfarma ya mai girma mai shari'a." Nanma saida yayi rubutu kafin yace "bayan neman alfarmar kotu da lawyen mai qara yayi, kotu ta karb'i qorafinsu ta basu nan da gobe su kawo hujojjinsu, idan ba haka ba za ayi watsi da wannan qarar, dan ba za'a b'ata lokacin kotu ba, zama ya qare." Juyawa yayi ya kalli lawyen yana mishi wani banzan kallo, maida kallonshi yayi ga tanti Ma'u, a haka zama ya qare abu ba dad'i. ************** Da kanshi yaje gidan tanti Ma'u neman Zuby dan yaga lafiyarta data abinda ke cikinta, habaice da zagi da baqar magana ya jisu, amma haka ya toshe kunnenshi har saida ta gama sannan ta fad'a mishi Zuby bata nan, tambaya yayi tana ina amma taqi fad'a dan itama bata san ina take ba, haka ya baro gidan yana kiran wayar Zuby, k'in d'auka tayi dan rayuwarta harta canza cikin qanqanin lokaci. ************** Bayan yaje gida Khairat ta tambayeshi ina zai samu wasu hujjojin? amma yace ta kwantar da hankalinta ba komai, a raunane ta kalleshi tace "baby, ina jin tsoro fa, dan Allah karka saka mana kanka a matsala, idan wani abu ya ta faru da kai wallahi nima zan shiga wani hali, dan Allah ka fitar da kanka a maganar nan." Shafa kumatunta yayi yace "karki damu kanki, insha Allah za muyi nasara, kuma mun riga mun fara, kinga bai kamata na cire hannuna ba." A shagwab'e tace " kenan ba zaka cire hannunka ba?" Da kai ya ta mata alamar eh, tureshi tayi daga kan gadon ta fashe da kuka tace "shikenan kaje, tunda kana sha'awar ganina ina takaba, mutanen nan ba imani ne dasu ba, kaje kayi abinda kake so." Juya masa baya tayi yayi rarrashi harya gaji, sai lokacin zai tafi ya ya fad'a mata fa sun rabu da Zuby, ta girgiza sosai ta kuma tambayi laifin me ta mishi, 'kin fad'a mata yayi dan haka ta sake yin wani hushi tace ya tafi itama babu ruwanta dashi, haka ya baro gidan sai dai yasan dole zasu shirya, amma girmanta ya qaru a idonshi. A hanyarshi ta zuwa gida su Musa suka tareshi, yana ganinsu ya fito yana murmushi yana kallonsu, gaban motar yaja ya tsaya ya rumgume hannaye yana kallonsu suna takowa wajenshi, suna zuwa gabanshi suka tsaya kafin suyi magana yace "Ya dai matasa, kunzo ku gaisheni ne?" Cikin takaici Bello yace "kai, mune zamu zo gaisheka d'in, kama rainamu wallahi." Cike da dariyar mugunta da raini Umar Faruk yace "to kenan meya kawoku nan, ko kunzo karbar hujjoji ne?" "Yawwa d'an gari, abinda ya kawomu kenan, idan ka bamu saimu tafiyarmu salin alin, amma idan ka k'i kuma sai kaji a jikinka." cewar Musa. Murmushin gefen labb'a yayi yace "da ganina nasan kunsan ni ba matsoraci bane, kamar yanda ni ba ragon namiji bane, dan haka kuyi duk abinda kuke ganin zakuyi, amma fa ba zan baku ba." "Haka kace?" cewar Musa. Gira kawai ya d'aga mishi alamar eh, ganin suna tunkarowa wajenshi yasa ya gyara tsayuwarshi yana tattare hannayen rigarshi, Musa ne yasa hannu aljihu ya ciro wata qaramar wuqa yana fad'in "da alama kai jarumi ne, amma fa karka manta mu sojoji ne, kaga kuwa dole ka shafa mana lafiya." Dariya Umar Faruk yayi yana fad'in "kaji sakarai, jarumi kake so a kiraka kenan? ai jarumta irin taka ba'a fatanta, ka rasa inda zaka nuna jarumtarka sai akan mata wajen yi musu fyad'e, ai jarumta yana nufin shanye duk wani d'aci da qunci harka riski farin ciki." Dariya Musa yayi yace "to ai ba ragwayen maza ke iya yiwa mace fyad'e ba, musamman ma masu taurin kai da tirjiya irin matarka Khairat." Yana fad'a suka bushe da dariya dukansu har suna tab'a hannu, lumshe ido yayi dan zafin da zuviyarshi keyi, ji yake kamar ya ciccira namansu a wajen, muryar Bello ce ta dawo dashi yana fad'in "a kan matarka na fara sanin 'ya mace, amma har yanzu ban had'u da wacce ta kaita ba, gaskiya da naji ance tayi aure saida naji ina kishi da wanda ta aura, kullum kowane dare kasa bacci nake saboda tunanin yanzu yana can yana shan romon da muka sha." Aminou ne ya bashi hannu suka tapa yana fad'in "wallahi kuwa, nima fa har mafarkin wannan ranar nake, gaskiya yarinyar ta had'u." Cewar Musa "ai zazzafa ce ta qarshe, waiku dan ma baku ne farko ba, aini zan fad'a muku gaskiyar magana nida na fara, a lokacin dana shiga wannan duniyar kai kace a aljanna aka tsundu....." Bugun daya sauka akan bakinshi ne yasa ya fad'i qasa kwance yana dafe da wuri, kallon Umar Faruk suke da idonshi suka canza kamar ba mutum ba, kafin su ankara ya sake shaqo wuyan rigar Musa ya d'agoshi tsaye yana fad'in " kamar me kake so kace, kamar an tsundumaka a aljanna? banza mahaukaci, kai kana tunanin zaka shiga aljanna bayan ketawa mata haddinsu da kake, aiko a wuta ma zaiyi wuya ka samu mazauni." Yana fad'a ya sake kai mishi bugu, da azama sukayo kansu suka fara qoqarin rabasu, sosai ya shaqi Musa yake dukanshi, suma dai ganin ya kasa sakinshi yasa suka rufeshi da duka toko ina, amma duk da haka baya jin dukansu dan hango Musa yake akan gado yana kokawa da Khairat har yayi nasarar shiga gonarshi, dan haka yake jin kamar ya cinyeshi d'anye, suna ta dakuwa da bawa hammata iska kawai Umar Faruk yaji wani abu ya sokeshi a ciki, kallon wajen yayi yaga ashe Musa ne yayi nasarar soka mishi wannan qaramar wuqar da wahala ta kai mishi. A hankali ya fara sakinshi harya sulale qasa, basu barshi haka ba saida suka sake binshi da duka hakan yasa suka canza mishi kamaninshi, duk jini ne ta ko ina, saida suka ga baya motsi sannan suka nufi motarshi suka bincike, ganin basu samu komai ba yasa suka lalaba har jikinshi, nan ma babu komai haka suka tafi babu nasara. Umar Faruk na kwance baisan inda kanshi yake ba, ya jima a wajen kwance yana zubar da jini, wata mota ce ta nufo wajen da yake, mutanen dake motar ne suka ganshi kwance suka fito, da ikon Allah suka taimaka mishi suka d'aukeshi sukayi asibiti dashi, ta hanyar wayarshi suka kira lambar daya kira qarshe lambar Abbakar, cikin tashin hankali Abbakar ya sanar a gida suka nufi asibiti, ganin halin da yake ciki ga jini ana qara mishi yasa basu kira d'aya daga cikin matanshi ba. Saida safe ya farfad'o, lokacin Khairat na kiranshi dan tuni sun hallara a kotu rashin ganinshi yasa take kiranshi, Abbakar ne ya d'auki kiran saida suka gaisa take tambayar "yah Abbakar ina Umariri ya shiga ne?" Sunan data kira saida yasa ya d'an murmusa, dakewa yayi yace "baya kusa, ina asibiti ne." "Asibiti kuma, meya faru, waye bashi da lafiya?" Ajiyar zuciya ya sauke yace "ki kwantar da hankalinki Khairat, idan zaki iya zaki iya samunmu a babban asibiti." Rintse ido tayi saboda fad'uwar da gabanta yayi, a kaurare tace "inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." Shiru ne ya ratsa kafin ta sake cewa "yah Abbakar sun mishi wani abu ko? ni nasan dama yasa kanshi a had'ari." "Karki damu Khairat, jikinshi da sauqi sosai." "Shikenan yah Abbakar, gani nan zuwa." Papa ta fad'a ma suka nufi asibitin su Mamie suka jirasu. ************** Koda ya farka ya tashi zaune ya Fara qoqarin cire qarin ruwan da aka maka mishi, Abbakar ne ya aje wayar ya fara rik'eshi, tureshi yayi da qarfi ya fizge sirinjin hakan yayi sanadiyar fitowar jini daga hannunshi, a tsawace Abbakar yace "wai meye haka, me kake yi ne haka?" Kallon Abbakar yayi yace "tafiya zanyi, ba zan zauna ba, dole saina qarasa abinda na fara." Qafafunshi ya zuro da niyyar saukowa, da sauri ya dafe cikinshi inda aka soka mishi wuqar tare da cije lips ya rufe ido, Abbakar ne yace "uhum, ga irinta ai, ina zaka je a wannan halin?" Bud'e ido yayi ya sauko daga kan gado cike da jarumta da dauriya, rigarshi ya kalla da duk taji jiki itama, Abbakar ya kalla yace "taimakon da zaka min shine, ka kaini gida." "Umar, baka da lafiya fa, yanzu haka Khairat nakan hanyar zuwanta nan." Cikin fitar hayyaci ya shaqo wuyan rigar Abbakar cikin d'aga murya yace "me, kana nufin ka fad'a mata, me yasa to zaka fad'a mata? Khairat nada rauni sosai, komai zai iya faruwa da ita idan taga halin da nake ciki." Shigowar Baba dasu Mama ne yasa saki wuyan rigarshi yana kallon Baba, "lafiya, meya faru?" cewar Baba. "Ba komai Baba, wai gida yake so ya tafi a wannan halin da yake ciki." "Gida kuma, me zakayi a gidan?" A marariraice yace "dan Allah Baba ku barni na tafi, wallahi akwai mahimmanci zuwana yanzun." Kallonshi Baba yayi sosai kafin yace "shikenan, bara muga ko mun samo maka takardar sallama." "A'a Baba, ku barsu kawai, ba lallai bane su sallameni." Haka dai shida Abbakar suka sulale suka bar asibitin, kai tsaye gida suka nufa yana shiga ya canza riga sannan ya had'a sauran hujjojin da suka rage mishi sannan suka tafi kotu. *************** Koda su Khairat suka zo asibiti su Baba ma na shirin tafiya kotu, da qyar suka fad'a mata jikinshi da sauqi suka lallab'ata suka bar wajen, kai tsaye kotu suka hallara suma, tana ganinshi ta ruga a guje ta rumgumeshi tana kuka, sosai ya rintse ido saboda wani bala'in zafi dake ratsashi saboda dafe wani ciwo da tayi amma ya kasa fad'a mata, yanda take qara cukwikwiyeshi yasa ya saki qara bai shirya ba, da sauri ta d'ago tana kallonshi da mamaki, turo baki yayi gaba tare da dafe wajen data rik'e yana fad'in "kin min famin ciwona." B'ata rai tayi ta kai mishi duka a wajen tana fad'in "na fama d'in, aiga irinta nan, jiya mena fad'a maka akan maganar nan? amma baka saurareni ba kai mai taurin kai, saina shek'eka da hannuna, hamago kawai kana so mu rasaka gaba d'aya, ya kake so muyi to, me zamu gayama yaranka idan sun tambayemu." Duk maganar da take tana zubar da hawaye ne, shi kuma hawayen nata yake kallo yanda suke zuba da k'arfi, hannu ya mik'a mata da nufin ta taho, buge hannun tayi da k'arfi tana fad'in "Bana so, bana sonka mugu kawai, saina kasheka da hannuna." Sake bata hannun yayi ya marairaice kamar zai fashe da kuka yace "dan Allah baby, kizo mana ko naji sauqin ciwon dake damuna, nayi kuskure amma ki yafe min." Ganin qwalla sun taru a idonshi ne yasa ta fad'a jikinshi da k'arfi har yana shirin fad'uwa tana tsananta kukanta tana fad'in "me yasa Faruk, me yasa zaka sa mana kanka a had'ari, kasan fa muna buqatarka musamman a wannan yanayin." A hankali ya kai hannunshi kan cikinta ya shafa yana fad'in "ki gafarceni, ina hakane saboda farin cikinki da iyayenki, Khairat na kasa samun sukuni ganin halin da iyayenki ke ciki, dolena ne nayi saboda farin cikinku ya d'ore." Goge hawayenta tayi tace "Amma ai ina farin cikin kasancewata da kai, kuma su Mamie ma suna farin cikin samun suruki kamarka, farin cikinmu zai gushene idan kasa kanka a had'ari, dan Allah karka sake irin haka, Faruk ba zan juri rasaka ba wallahi, nasan mutuwa zanyi nima idan na rasaka, dan Allah ka zauna tare dani." Abbakar ne yace "to Roméo da Juliette ku wuce mu shiga ciki kowa ya shiga." Dariya sukayi suka wuce ciki suka zazzauna, su Musa kam idone ya sake raina fata musamman abubuwan da suke gani a hannun Umar Faruk, lawyer ne ya matso kusan Umar Faruk ya sunkuya yace "kawo hujjojin na fara dubawa kafin alqali ya shigo." A wulaqance ya kalleshi yace "barshi kawai, aida hannayena nima Allah ya horemin, idan alqalin ya shigo na bayar a bashi." Yana gama fad'a kuma alqali ya shigo, tsaye suka mi'ke harya zauna, bayan maganganun da alqali yayi ne ya tambayi ko hujjojin sun bayyana gaban kotu kamar yanda Umar Faruk ya nemi alfarma aka mishi, Umar Faruk ne ya mik'e yayi daidai da mik'ewar lawyensu, hararanshi yayi ya rab'ashi ya bawa maga takarda duka hujjojin, saida alqali ya gama dubawa duka sannan ya nisa ya gama ruubuce rubutunshi kafin ya fara magana, "Bayan hujjojin da aka gabatar a gaban kotu, kotu ta samu Sani Saley Odette Asma'u dasu Musa da laifi dumu dumu, sai dai kuma babu matashi Salim a kotun nan, dan haka kotu ta bada umarnin da a gaggauta gurfanar da Salim a gabanta, dan shima mai laifine, sannan kotu na buqatar a gabatar mata da docteur Shehu, dan shima da nashi laifin abisa cin hanci dan gurb'ata sunan wani." Tsaye Umar Faruk ya mik'e dan girmamawa yace " ya mai girma mai shari'a, ina so kotu ta sani cewa wad'annan matasan samarin dama fil'azal masu laifi ne, laifinsu kuwa shine fyad'e wa mata, muna da shaida akan hakan idan kotu na buqatara gabatar dasu a gabanta zamu iya, bayan fyad'e kuma ni kaina sun so su kasheni badan komai ba sai dan su karb'i hujjojin dana gabatar, amma da ikon ubangiji kuma Allah bai basu sa'a ba, da wannan nake roqon kotu mai alfarma data yanke ma wad'annan hukunci mai tsaurin gaske wanda ba zai bayar da damar da za'a sake fito dasu ba daga gidan yari, dan a cikin hujjojin dana gabatarwa da kotu akwai bellynsu da akayi ba tare da sun cika wa'adin da aka dib'ar musu ba, abin takaicin ace anci zarafin yar babban mutum kuma shugaba, amma su kasa samun adalci, wannan ne yasa wata matashiyar budurwa da Musa yaci zarafinta yasa iyayenta suka barshi da Allah, dan sun san ba zasu samu adalci ba, na gode ya mai shari'a." Tsawon lokaci alqali na nazartar lamarin kafin ya fara da "bayan hujjojin da aka gabatarwa da kotu tare da dogon nazari da tayi, kotu ta samu wannan mutane da laifi dumu dumu, dan haka wannan kotu mai alfarma ta yanke wa su Musa hukunci kamar haka, dukansu zasuyi shekara.....a gidan yari, haka ma Odette da Asma'u da Sani Saley da kuma yaro Salim an yanke musu hukuncin d'aurin wata uku uku a gidan yari tare da horo mai tsanani saboda magud'i a cikin siyasa da b'ata sunan wani, sannan kotu na umartar su Musa da subiya tara ta 150 0000cfa ga Umar Faruk saboda rayuwarshi da suka nema, kuma zasuyi hakan ne a cikin sati d'aya tak, sannan kotu ta wanke Mani Bukar cike da girmamawa da mutuntawa, sauran a gurfanar da likita da Salim a gaban kotu, da wannan zaman kotu ya qare." (Ba lallai hukuncin dana yanke yama kowa dad'i ba, bana da ilimin shari'a, kuma wanda zai bani bayanin haka na rasa lambarshi a d'aya layin da aka min asararshi.) Kallon tanti yayi yace "kiyi hak'uri tanti, banso haka ta faru ba kuma banji dad'in faruwar hakan ba, amma nasan zaki fahimceni." Yana fad'a yayi gaba abinshi Odette ta bishi da mugayen ashar, tanti kam bakinta ma ya mutu murus bata san me zata ce ba. A wajen su Bello suka fara tuhumar Musa akan shiya lalata musu rayuwa, gashi yaja musu zasu qarar da rayuwar da basu da tabbacin zasu kaita a gidan yari, suna cike da wannan jimami da zulumi da kuka Umar Faruk dake rik'e da hannun Khairat ya tsaya gabansu yana murmushi, gemunshi ya shafo yana kallonsu yace "gashi a karo na biyu na sake antayaku gidan da kuka fito, amma wannan karan zanyi iya bakin qoqarina naga baku fito ba, kuma na muku alk'awarin ziyartarku kowane qarshen sati dan yin wa'azi wa yan gidan, aci gabza lafiya yan samari." Wucewa sukayi Musa yayi saurin cewa "dama kai ka tona mana asiri a farko ma?" Da wani shegen murmushi ya d'aga masa gira kawai suka wuce har saida suka shiga mota Khairat ta kalleshi tace "dama kai ka bayyana masu laifin a waccen lokacin?" Shiru yayi sai Mamie dake baya ce tace "shine 'yata, haqiqa Umar Faruk ya mana taimakon da ba zamu iya biyanshi ba, sai dai kawai mu bishi da addu'a." "Ita nafi buqata a wajenku Mama." ya fad'a yana kallon Mamie. D'ora kanta tayi akan kafad'arshi ta rumgume hannunshi tana fad'in "ashe kaine ka taimakeni a waccen lokacin ma, na gode maka sosai baby, gaskiya kai na daban ne, kuma kasa naji kunya akan abinda na dinga yi maka a baya, da nasan kaine wanda ya taimakeni da banyi abinda nayi ba." Shafa fuskarta yayi yace "karki damu, komai ai ya wuce, ba gashi kin zama tawa ba." "Kuma nima ka zama nawa ba." ta fad'a tana qara qamqameshi. 6📓3📓 *A gurguje* Saida Umar Faruk yayi jinya sosai kafin ya samu sauqi, a lokacin kuma cikin Zuby yana wata takwas, a lokacin kuma Allah ne yayi ikonsa, yayin da Zuby ke fuskantar rayuwar qansqanci a gidan mahaifinta da wulaqanci iri iri, kyara da zagi ga aiki babu tausayi haka suke sakata duk da tsohon cikinta, amma da zaran Umar Faruk ya shigo gidan da sunan yazo ganinta zasu dinga sakar mata fuska, amma kasancewar shi ba yaro bane yasa ya fahimci canji daga wajen Zuby a take ya fahimci halin da take ciki, amma abin takaici daya umarceta su koma gida sam sai tace gidan ubanta itama zata zauna, dole ya rabu da ita a haka yake d'awainiya da ita da abinda yake cikinta. Khairat kuma yanzu lafiya ta samu, sam bata cika cin abinci ba sai kayan qwalam da maqulashe, Umar Faruk kuma kullum cikin kashe mata kud'i yake da faranta ranta, yayin da kullum suke maqale da juna bacci kad'ai ke rabasu, tayi nauyi sosai saboda cikinta na watan haihuwa ne, kunburin qafafu kuma shi yafi takurata sosai, sai nauyin jikin da tayi ko qwaqwaran motsi bata iya yi da kyau, hakan yasa har Papa yake tunanin ko za'a fitar da ita ne waje ta haihu a can, amma tace bata so. Salim kam anyi nema amma shiru babu labarinshi, dama kuma tunda Umar Faruk ya qwamusheshi ya tsorata yasa suka bar garin shi da mahaifiyarshi, basu tsaya ko ina ba sai Maradi, anan suka fara wata sabuwar rayuwar a wani qauyen da ake kira *Madarunfa*. ************** Wani bala'in ciwo ne ya addabi tanti a gidan yarin da suka rasa gane gabansa, da farko sun d'auka hawan jini ne amma sai suka fahimci abin ya wuce nan, gashi idan aka ce dare yayi to babu mai bacci saboda bala'in haukan da take tsurawa a wajen da hayaniya, a hankali kuma wani qurji ya fito mata a qafa, da sannu sannu saiya dinga girma har yakai matakin da yayi ruwa ya fashe ya fara wari, da qyar aka samu aka canza mata waje ita d'aya. ************ Koda Zuby ta wayi gari ta tashi bata jin dad'i sai rik'ewar da bayanta keyi, sai dai babu wanda zata fad'a ma ya kalleta ma bare ya tausaya mata, tana cikin yanayin nan Hajia babba ta gidan ta fito mata da kayan wanki, duk qoqarin Zuby nasan ta fahimceta amma ina saida ta fara wankin tana kuka, tana gamawa ta d'ora girkin rana, tana idawa ne ta fara qoqarin shara ,amma ina bata kai ko ina ba ta fad'i wajen tana neman taimako, da taimakonsu suka d'auketa suka kaita asibiti sannan suka kira Umar Faruk dan yasan halin da ake ciki. A lokacin Umar Faruk na zaune bakin gado d'akin Khairat yana kallonta tana kai da kawowa sai sharar gumi take, qafafunta yake kallo da sukayi sumtum dasu kamar zasu fashe, wata qaramar riga ce gareta mai siraren hannuwa, tsaye yayi ya nufi wajenta ya rik'o hannunta yana fad'in "zo ki zauna dan Allah ki huta, yawon ya isa haka." Fincike hannunta tayi za tayi magana kuma tayi saurin dafe cikinta da qugu tace "washhh, wayyo Allah na, dan Allah ka kira min Mamie, wallahi bana jin dad'i." Qara rik'eta yayi yace " jikin ne, bara na kirasu To." Zai fita kenan ta fizgo rigarshi cike da azaba ta durqushe qasa tana kuka tana fad'in "wayyo Allah, Faruk da ciwo wallahi, dan Allah ka min addu'a, wallahi ji nake kamar zan mutu, wayyo Allah na Allah ka taimakeni." Durqushewa yayi shima yana rik'e da hannunta yana kallon idonta dake rufe sai hawaye ke fitowa, janyo kanta yayi ya manna a qirjinshi ya kara bakinshi a kunnenta yace "kiyi hak'uri Khairat d'ina, ki yawaita anbaton sunan Allah a bakinki, a yanzun kina cikin wani hali ne da babu abinda zan iya yi miki sai dai addu'a, amma mahaliccinki shine ke tare dake a wannan halin, da ace idan nace ciwon nan ya dawo kaina zai dawo, haqiqa da zanyi addu'a a yanzun nan dan na d'auke miki wannan shan wahalar, amma kiyi hak'uri kinji ina tare dake insha Allah." Sake qamqameshi tayita fashe da kuka, rarrashinta yake yana tofa mata addu'a yana so ya tashi ya kira Mamie amma ina, suna haka ta sake kwamtsa wata qara tare da cakumo rigarshi, a gigice ya d'auketa ya sauko da ita falo inda Mamie suke zauna, nan dai suka nufi asibiti, a hanyar zuwa ne kuma kiran Zuby ya shigo, koda ya d'auka Hajia babba ce, koda ta fad'a mishi sake rud'ewa yayi musamman daya tuna cikin Zuby ba watan haihuwarshi bane yanzun. D'an magori ya kai Khairat, Zuby kuma asibitin da aka kaita daban itama, koda sukaje aka yi shirin yiwa Khairat aiki dan fito da abinda ke cikinta, cikin nasara kuma akayi sa'ar fito da kyakyawar yarinya sak mahaifiyarta bata bar komai ba dan gane da ita, a lokacin kuma Umar Faruk na wajen Zuby tare da Mama, tasha wahala sosai kafin ta haiho abin cikinta, namiji ne amma sai yazo babu rai saboda yana wata takwas ne, suna cikin wannan jimamin suka tafi ganin Khairat da yarta, nan kuma farin ciki sukayi sosai yayin da asibiti ya cika da mutane ana ta murna. A hankali Khairat ta bud'a idonta daga baccin da take na hutu, wani irin ciwo taji yana taso mata da ba zata iya misaltashi ba, da qyar ta hango Umar Faruk rik'e da yarinyar yana kallonta sai wasar baki yake, jin abin na qara taso mata yasa ta tara mishi alamar yazo, duk mutanen dake d'akin kallonta suke suna tambayar ya jikinta, bawa Mama yarinyar yayi ya qaraso wajenta, sunkuyawa yayi tare da rik'e hannun nata, bud'a baki tayi tana magana amma baya jin me take fad'a dan haka ya kara kunnanshi wajen bakinta. Murmushi ta masa tace "baby, ni kad'ai nasan me nake ji, bansan ko zan rayu ba, amma dai saida na tabbatar na baka wata babyn kafin zan barka, ka kula min da ita sannan ka tabbatar ta samu tarbiya wacce ban samu ba a lokacin yarintata, nasan kamin kyautar yarinyar nan tun tana ciki, amma yanzu ta zama taka, dan bata da wani gata daya fika a duniyar nan, alfarma d'aya nake nema a wajenka?" Kallonta yayi yace "alkairina bana son irin maganganun nan fa, me yasa zaki fad'i haka a irin wannan lokacin, yanzu fad'a min wace alfarma kike nema a wajena?" Murmushi ta masa tace "ina so ka sawa yarinyar nan suna Islam, ina so ta zama mai tsantsar addini da fahimtar sunna." Qara matse hannunta yayi yace "zanyi Khairat, dan Allah kiyi shiru kinji." "Ina....." shiru tayi ta kasa fad'a ta rik'e cikinta, rik'e hannunta yayi yana fad'in "lafiya, me kike jine?" Numfashi ta fara ja amma ta kasa mayar dashi, ga maganar da take so ta fad'a amma ta maqale mata, nan dai aka kira lokitoci aka koma da ita wani d'akin aka fara dubata, da qyar da sud'in goshi aka ceto Khairat, Umar Faruk yayi farin ciki sosai a lokacin kuma koda akayi sallah la'asar aka kauda yaron da Zuby ta haifa, Zuby tayi kuka sosai gashi yan uwanta ne kad'ai tare da ita babu mahaifiya babu wani babba sai Mama kawai. 6📓4📓 Dukansu sun koma gida, Zuby ta koma gidan mahaifinta Khairat kuma dasu Mama da sauran yan gidan sun tare a sabon gidansu, a ranar Khairat tayi kuka sosai tare da qara godewa Allah da kuma Umar Faruk, dan sak sashin daya mata irin sashinta ne na gida, musamman d'akinta da toilet d'inta, haka ma kayan daya zuba mata irin na d'akinta ne duka, lallai dukiya ta kwanta sosai sai dai ace alhamdulillah, babban abin farin ciki shine, islamiyya daya bud'e dake liqe a gidan, wacce malaman ciki suka kasance, shi, Ruk'ayya, Usman, Aliyu da kuma babban yaya Abbakar, kuma tuni suka fara koyarwa a ciki, mutane na zarya zuwa gidan kuma suna samun kulawa sosai, kasancewar su Uwani na wuni gidan kullum yasa Zuby ke farin ciki dan babu wannan aikin da muzgunawar mutan gidan, bayan kwana biyu sunje su fad'awa Mama Zuby ta haihu, amma sai hankalinsu ya tashi saboda ganin yanda Mama ta koma, a mutanen dake kusa da ita suka samu labarin cewa ko bacci ba tayi yanzu sai surutai da sambatu, sun tsorata sosai musammanma da tayi kamar bata sansu ba, haka suka dawo Zulfa'u dake da tsoro cewa tayi ba zata sake komawa ba sai an sallameta. Ranar suna anyi bidiri da shagalin da babu wanda yayi tsammanin za ayi, dan Umar Faruk cewa yake walima kawai zaiyi, amma saiya shammaci Khairat ya mata duk abinda tayi burin yi, yarinya kuma taci sunan Islam, sai dai abin mamaki shine Umar Faruk yana kiranta da qaramar Khairat, kullum ya kira sunan sai Khairat ta kalleshi tayi murmushi, a haka aka gama sabga suka fara jego cikin kulawar Mammie da Mama dasu Mama Sa'a, ga kuma tururuwar da har yanzu mutane keyi a gidan, kuma a wannan lokacin ne Khairat ta fahimci kyautatawa nada anfani sosai, a haka suka yi Arba'in cike da qoshin lafiya, sai dai Khairat naci gaba da samun kulawa saboda ita aikine aka mata, kuma jikinta da sauqi sosai. *BAYAN WATA BIYAR* A lokacin Khairat ta tayar da rigima sai dai Umar Faruk ya dawo da Zuby, da farko bai amince ba, amma data saka mishi kuka tace zata fad'awa malam dole ya yarda, da kanshi yaje danya dawo da ita, amma saboda tasan ba sonta yake ba yasa tak'i amincewa, ganin irin rayuwar da take yasa yace to su koma can gidansu ta zauna, shima da qyar ta yarda ta bishi suka koma gidan ta fara rayuwar 'yanci. Sai dai sauyawar rayuwa yasa Zuby yin biyayya wa Khairat tunda itace shugabar gidan, wani abun al'ajabi shine soyayyar Islam da Allah ya sawa Zuby a zuciyarta, kullum ta kalli yarinyar sai taga da yaronta na rayé da yanzu yana kamarta shima, hakan yasa Zuby rainon Islam kullum tana tare da yarinyar, tun tana aika yara su d'aukota mata ita har wani lokacin ta kanje da kanta ta d'aukota musamman in yara na school ko islamiyyar dare, yarinya ce mai shiga rai saboda yar qibartada kyawunta ga kuma gashinta da kullum Zuby ke kan mata gyaranshi duk da uwarta na mata. Hakan nawa Khairat dad'i sosai danta samu damar zuwa islamiyya hankali kwance ba tare da damuwa ba, kuma kullum cikin kyautatawa Zuby take ko abinci ita ke fidda mata sutura kam ba'a magana, karatu kuma sosai ta mayar da hankalinta kanshi, a islamiyya Umar Faruk malamine, a gida kuma miji, wani lokacin yakan takurata sosai, hakan yasa har bata fata ranar shigarshi ajinsu yayi, tafi son Ruk'ayya kullum dake musu Bulugul Maram. *********** Tunda al'amarin Mama ya girmama bayan ta fito malam ya duqufa wajen gane meye matsalarta, amma duk qoqarinshi bai gane komai ba, hakan yasa ya tuntub'i malaman da yake ganin sune manyanshi, amma a cewar wasu matsalarta kawai sai dai a tayata da addu'a, amma abun kam ba'a magana kamar wacce bakin uwa ya tab'a, haka itama Umar Faruk ya ware mata d'aki a gidan ta fara rayuwa amma kullum cikin matsalarta suke, qoqarin fita daga gida sambatu iri iri, babu sambatun da suka fi daga hankalinsu kamar idan tana fad'in "eh wallahi, nice nan da kaina nayi sanadiyar mutuwar mijina, domin kuwa baqin cikina ne ya kasheshi saboda ya ganni da cikin Zubeida, uwata kuma, ihihi, ai da hushina ta mutu, wallahi na rantse muku da b'acin raina ta mutu, Bala kuma, hum wai wai wai, ai nice nan nasa aka tura mishi aljanu sukak kasheshi, wannan yarinyar kuma, matarka ba, matar Umar Faruk, ai tunda ta samu ciki muka bayar da cikin ga aljanu, kuma suka zuba mata cutar da zata kasheta, amma wannan tsinannen yaron ya taimaketa." Wannan maganganu ne da kullum saita fad'esu, shi yasa Zuby bata zuwa inda take, su Uwani ma basa zuwa gidan, ana haka tsawon wata takwas a gidan wata rana ta fita basu sani ba, ashe kiran ubangijinta ne ta amsa, a titi mota ta kad'eta sai labari mutanen gidan suka samu, sam yayanta babu wacce tayi jimamin hakan, wannan dalilin ne yasa malam ya tarasu ya musu nasiha sosai ya fad'a musu mahimmanci uwa, duk da dai yasan alhakine ke binta, duk da sun bita da addu'a amma dai Zuby kam ita dai ta riga data tsani mahaifiyarta kawai. Ganin ta daina walwala a gidan yasa Umar Faruk ya tilasta mata komawa islamiyya itama, daga ranar suka fara zuwa tare da Khairat da sauran yara, bayan wani lokaci kuma Umar Faruk da kanshi ya nemawa Ishaq auren Ruk'ayya danshi kunya ta hanashi fad'a, a take malam yasa musu ranar tunda sun amince da junansu dukansu, daga ranar aka fara gudanar da shirye shirye, Khairat kam kai kace itace uwar amarya saboda hidimar da take yi. Kwanahud'u ya rage bikin Ruk'ayya, yara da Khairat dukansu sunyi roqo akan Umar Faruk ya basu hutu a makaranta amma yace sam bai amince ba, hutun rana d'aya kawai ya basu shima dan a ranar ake biki, Khairat ce ta had'a yaran ta kaisu wajen lalle da kitso duk qoqarinta saida karatun yamma ya sub'uce musu, tana sallah magrib ya shigo bedroom d'in nata, amma tana hangen fuskarshi taga ba annuri sai tak'i sallame sallar ta sake tashi tsaye, gabanta faduwa yake dan sam baya wasa indai b'angaren addini ne, a hankali ta saci kallonshi sai kawai suka had'a ido, da sauri ta liqe idonta take maganganunshi suka dawo kunnenta a lokacin da zasu fita tunda sanyin safiya. "Alkairina, kinga na lamunce muku kuje yanzu ba tare da kunyi darasin safe ba, amma ina sake jaddada miki, wallahi kiyi iya qoqarinki kiga kun dawo kafin a shiga ajin yamma, idan ba haka ba fa rai zai b'ace, ba kuma na yaran ba kad'ai, harda naki tunda ke kike daurin musu gindi, kin yarda?" "Na yarda baby, insha Allah ma zamu dawo akan lokaci." "Hum, Allah yasa." "Ameen." ta fad'a tana manna mishi sumba a kumatu, shima sumbatarta yayi dan hakan harya zama jikinsu. A hankali ta aje ajiyar zuciya dan tasan dole sai ranta ya b'ace, zata sake satar kallonshi muryarshi ta daki kunnuwanta "idan kin gama qaryar sallah kije ki had'o min kan yaran ku sameni d'akin karatu." "Bab...." dole tayi shiru saboda harya fice daga d'akin. Wani zazzafan iska ta furzar cikin sanyin jiki ta sulala ta nufi b'angarensu Mama, zaune ta samu yaran suna cin abinci Islam na ganinta ta sauko daga qafafun Zuby tana cin abinci ta rarrafo, d'aukarta tayi tana fad'in "yahhh, sarauniyar Papa, ya kike, abinci ake ci?" Nufa tayi da ita wajen Zuby ta aje mata ita akan qafafu tace "rik'eta ina zuwa, zamuje wajen Papa musha bulala ne." Mama ce tace "wai badai bai hak'ura ba?" Cikin sanyin jiki tace "Mama ai kinsan ba zai hak'ura ba dama." "To kinga tafi da Islam d'in wajenshi." Da mamaki ta kalli Mama tace "me yasa Mama?" "Ki tafi da ita kedai." "To Mama." ta fad'a ta d'auki Islam da rigarta ta fara b'acewa da miya bakinta ma haka. Had'a yaran tayi suka tafi d'akin karatun, da sallama dukansu suka shiga kuma yana amsa musu, dukansu zaune sukayi akan lumtsumemen carpet d'in dake shinfid'e a wajen, wani littafi ne yake karantawa dan haka yayi banza dasu, aje Islam tayi ta rarrafa wajenshi ta rik'e qafarshi, da murmushi ya d'auketa ya aza saman cinyarshi yana mata wasa, saida ya gama sannan ya kallesu duk kowa jikinshi sai 'bari yake, a kausashe yace "meya hanaku zuwa islamiyya da maraice?" Duka yaran mayar da kallonsu sukayi ga Khairat, itama kallonsu tayi tace "ya kuma zaku kalleni?" Kallon Umar Faruk tayi tace "baby wallahi....." "Waye baby?" Yanda yayi maganar yasa ta kama jikinta, had'e yawu tayi ta sake cewa "wallahi malam nay...." A tsawace yace "wai magabar ba zata yiwu ba sai anyi rantsuwa, alamar qarya zaki fad'a kenan." "A'a malam, dama dan ince ne nayi iya qoqarina naga mun dawo da wuri, amma abin yaci tura, gashi ni kaina ban samu lallan qafafu ba, dole sai dai gobe na koma ayi min." Wani kallon kin rainani ya bita dashi, wani coffre ya bud'a ya d'auko wata zungureriyar bulala ya taso yayo kansu da ita, ai da sauri kowa ya fara qoqarin gyara zama, cikin muryar kuka suka fara bashi hak'uri, aje Islam yayi akan qatuwar kujerar dake d'akin yace "kiyi kallon yanda mamanki zata sha bulala, bata jin magana." Daga kan Fateema ya faro yace ta bashi hannunta, tuni Fateema ta b'arke da kuka tana bashi hak'uri, ganin yanda take kuka yasa Khairat cewa "malam, nice babba kuma ni na tafi dasu, dan haka amin bulalarsu na d'auka." Tabe baki yayi yana kallonta kafin ya kalli yaran yace "to an d'auki kaifinku, amma ku sani idan kuka sake ku zan daka ba wani ba." Cikin tsawa yace "ku b'ace min da gani." Duk a sanyaye suka tashi suna kallon Khairat, suna fita ya dawo kanta yace "bani hannunki, kuma kiji da kyau, wallahi idan kika sosa hannunki ko kika janye hannun, to duk sun zube koda kuwa na miki bulala ta kusa data qarshe ne." Bud'e baki tayi tana kallonshi tana tunanin yanda haka zai yiwu, zaro mata ido yayi yace "kinji dai na rantse miki ko, wallahi nace miki." "Hannunki." ya sake fad'a. Had'e wani irin abu tayi mai nauyin gaske daya tokare mata maqoshi, rintse ido tayi ta fara zuro hannun dama a hankali kuma tana d'an janshi da baya, tsawar daya sake mata ce yana fad'in "kefa nake jira." yasa ta zabura ta mik'o hannun. D'aga bulalar yayi ya sauke mata ita ira a hannu, qara ta saki tare da mayar da hannun cikin hijabi, a kaurare yace mata "kinsan dai ba zaki sani kaffara akan wannan abunba ko, dan haka ki d'auka ban fara ba har yanzu." Kallonshi tayi sai dai tsagwaron gaskiya kawai ta gani a idonshi, dan haka ta yanke shawarar tsayawa maimakon ta wahalar da kanta a banza, fito da hannayen tayi duka ta mik'a mishi amma idonta rufe, ai kuwa tsuga mata ya dinga yi kai kace qiyayyace tsakaninsu, kamar wasa saida ya mata bulala goma sha biyar ta mutum uku, dan duk d'aya yana da biyar ne, zai zuba mata ta sha shida tayi saurin bud'e idonta ta sauke akanshi, saida gabanshi ya fad'i saboda ganin yanda idonta sukayi jawur dasu, hawayene suka gangaro mata langab'e kai tayi ta marairaice cikin muryar kuka tace "baban Islam, dan Allah." Shiru tayi daga nan, da sauri ya kawar da kanshi yayi qoqarin mayar da qwallan da yaji na barazanar taho mishi, juyawa yayi ya kalli Islam dake son saukowa daga kan kujerar, maida kallonshi yayi ga Khairat d'in data kasa janye hannayenta, dakewa yayi yace "meye?" Lumshe ido tayi yayin da gashin idonta yayi sharkaf da hawaye, kasa rik'e kanshi yayi baisan sanda ya jefar da bulalar ba ya durqushe gabanta ya rumgumota a jikinshi, cikin kunne ya rad'a mata "ki gafarceni alkairina." Kafin tayi magana ya d'agota ya kamo hannayen nata ya rik'e yana kallo, sunyi jawur duk shatin bulala ya fito, sumbatar hannayen yayi ya had'esu wuri d'aya yana kallon fuskarta cike da nadama, a hankali ya sake furta "kiyi hak'uri kinji baby." Fizge hannayenta tayi ta mik'e tsaye tace " naki nayi hak'urin, kullum nayi laifi baka tab'a min uzuriba saika dakeni, kuma kafin ka dakeni saina baka hak'uri amma baka hak'ura, shine yanzu ni zaka bani danka rainani." Fita tayi daga d'akin ta koma b'angarenta, bin bayanta yayi da Islam a hannunshi, hak'uri ya fara bata da rarrashinta amma tak'i sauraronsu, saida taga ya damu sosai kad'ai tace "na yarda zan hak'ura, amma da sharad'i?" "Meye sharad'in to." "Sai inka amince zaka dawo da Zubeida d'akinta." Wani tar yayi da ido tare da jan tsaki, shiru ya mata dan haka tace "yanzu baby wannan alfarmar ce ba zaka iya yi min ba? alhalin kana fad'a min zaka iya yin komai saboda ni, kana cewa ranka fansane ga nawa ran, amma ace wannan alfarmar na gagara samunta a wajenka, bafa sab'on Allah nace kayi ba, hasali ma wata sunna ce zaka qara dabb'aqawa mai k'arfin gaske, amma shikenan tunda ba zan samu ba, kaga yanzu saina dinga rik'e kaina wajen tambayarka alfarma dan nasan ba zan samu ba." Harta juya zata koma d'akinta ya rik'e hannunta, zaunar da ita yayi akan cinyarshi yace " indai wannan ne zaisa kiji a ranki kin wuce komai a wurina, to na amince, ki fad'i ranar da kike so ta dawo gidanta." Da farin ciki a ranta tace "kawai a sake d'aura muku aure ranar d'aurin aurensu Ruk'ayya." "An gama alkairina." Sumbatar kumatunshi tayi sannan ta mik'e ta shiga d'akinta, shi kuma Islam ya d'auka yana fad'in "qaramar alkairina, ina fatan zakiyi koyi da hallayen mahaifiyarki, ita rayuwata ce, ita aljannata ce, ita komai tawa ce, ita dabance a gareni, ba ayi ba kuma ba za'a tab'a yin wacce Umar Faruk zaiso ba kamar mahaifiyarki, ita alkairi ce a wajen Papanki, ina sonta ina qaunarta fiye da komai." ya qarashe da sumbatar bakin yarinyar. ************** Lokacin da Umar Faruk yaje wa da Zuby da maganar bata amince ba yanzu ma, amma da Mama tasa baki saita amince a sake d'aura musu aure a karo na biyu, nanfa hidima ta qaru yayin da Khairat tayi farin ciki da hakan, washe gari ganin babu wani shiri da Zuby keyi yasa Khairat had'a wani sirri daga cikin sirrin da Mamie ta bata ta aika aka kai mata, da farko taji d'ar a ranta amma data tuna Khairat ba kamar ita bace mai barbad'e saita daure tasha, daga ranar har zuwa kwana ukun daya rage musu ita ta dinga musu gyara, dama kuma ita kema Ruk'ayya d'an abinda zata iya. Gobe d'aurin aure, anyi sallah magrib gidan ya qara kaurewa da hayaniya, yayin da su Khairat suka kama aiki gadan gadan, duk wanda yasan Khairat ya ganta tana qoqarin d'ora babbar tukunya da ita kanta zata iya shiga ciki a rufeta sai yayi mamaki, tana tsakiyar mutane ta d'ora tukunya Umar Faruk ya shigo da Islam a hannunshi tana kuka, kamar daga sama taji muryarshi yace "alkairina." Juyowa tayi tana goge zufa da zaninta, takowa tayi ta nufo wajenshi, kallonta yake harta tsaya gabanshi yace "me ki keyi hakane? yaushe kika fara aikin da har zaki fara gwagwarmaya da waccen manyan tukunyan?" Shagwab'ewa tayi tace "baby, me yake damuna to? yanzu fa Islam watanta tara da haihuwa, kana gani yarinyar dake qoqarin tafiya ma." "Sai akayi me?" Shiru tayi tana kallon Islam dake kuka har yanzu tana qpqarin zuwa wajenta, hannu tasa zata karb'eta yace "dan Allah ki daina sakarwa yaran nan ita suna fita da ita waje ana magrib." Karb'arta tayi tana fad'in "kayi hak'uri ba za'a sake ba, bansan sun fita da ita Ba." Saida ya d'an saci kallon mutanen dake wajen sannan ya aika mata da sumba, itama mayar masa tayi ba tare da sun tab'a juna ba, juyawa yayi zai fita tace "ango ango, ango Zubeida." Juyowa yayi yace "ango Khairat da Zubeida dai." "Kuma baban Islam ba." cewar wata abokiyar wasanshi Chapa'atou. Hararanta yayi yace "ke kuma wa yasa bakinki?" Dariya Khairat tayi taja kujera ta zauna zata bawa Islam nono tana fad'in "dama baban qaramar Khairat ki kace da baice miki haka ba." "Fad'a mata dai, ai kune ke kiranta da Islam, amma ni inkiyar da nake mata itace alkairi." Kallon Khairat yayi yace "na manta ban fad'a miki ba, Papa yazo fa suna tare da malam." "Da gaske, amma shine basu fad'a min ba? koda yake ma yanzu sun daina sona sunfi son Islam, amma zasu shigo hannuna, nasan ba zasu bar nan ba dole zasu nemi Islam." "To ai shi yasa na kawo miki ita danki bata nono tasha, dan da ita zasu tafi gida ta kwana acan." Waro ido tayi tace "wa, autar tawa zan bayar ta kwana ba kusa dani ba? a'a ma karku fara." Duk da mutanen dake wajen bai hanashi yowa kanta ba yana fad'in "ina autar take?" Tashi tayi daga kujerar ta nufi wajen Mama Sa'a ta zauna akan tabarmar tana dariyar mugunta, wani shegen kurmanci ne sukayi daga nan dani kaina ban fahimta ba, naga dai ya kashe mata ido tare da cije lips d'inshi, itama idon ta kanne mishi ta d'aga gira sama ta lashe baki, juyawa yayi zai fita ya nuna mata yatsa yace "zan kamaki." Gwalo ta bishi dashi harya fita mutanen wajen suna mamakin yanda Umar Faruk ya canza sosai, a da idan ana taro irin haka idan har kayi sa'ar samun ganinshi to da qyar zai tsaya ku gaisa saboda miskilanci da rashin san magana irin nashi, amma yanzu gashi a arha, Chapa'atou dake tare da wata yar uwarsu dattijuwa ce tace "gaskiya idan nice yah Umar, wallahi babu abinda zai sani na maido da Zubeida bayan nasan komai game da ita." Dattijuwar tace " to ai bashi bane zai maidota gaban kanshi, nida na kwana biyu gidan ai naji meya faru, Khairat ce da kanta tace ya maidota, amma fa harda wani cijewa ita ba zata koma ba, saida Maryam d'in tasa bakinta kad'ai." "Jar uba, lallai ma ta raina mutane, ita yanzu duk abinda tayi amma har za'a nemi ta dawo tayi tirjiya, wallahi Khairat ta zama yar halak, ta bamu mamaki sosai, farkon zuwanta gidan nan da nazo ganin amarya ko kallon tsiya bata min ba, amma yanzu kaga kamar ba ita ba." Dariya tsohuwar tayi tace "aike kad'an kika gani, kwana bakwai da nayi a gidan nan naga abubuwa da dama, kinga hidimar da take, yaran nan kowa nata ne kamar yayan cikinta, uwayen kuma kamar su suka haifeta, kai gaskiya yarinyar tayi sai dai fatan Allah ya tsare." Haka suka dinga tattaunawa akan Khairat harta wuce ta gabansu ta nufi b'angarenta tana amsa wayar Umar Faruk, sake jaddada mata yayi ta shirya Islam yama Papa alk'awarin zasu tafi da ita, cike da jin za'a rabata da yarta tace "amma me yasa babu, yarinyar nan nono take sha, ya zasuyi idan ta hanasu bacci tana buqatar mahaifiyarta?" "Ba zatayi ba, ni na fad'a miki haka." "To amma baby..." "Amma me kuma yar aljanna, kiyi abinda hamagon mijinki yace miki mana." Murmushi tayi tace "shikenan to zanyi, ka gafarci bahamagiyar matarka da bata jin maganarka sau d'aya." Dariya yayi da saida taji sautinta yace "aike yar aljanna ce ba kwankwanto, buri da fatana d'aya a duniya shine, Allah yasa nima na shiga aljanna danna rayu dake." Ajiyar zuciya ta sauke cikin jin dad'in maganganun mijinta tace "idan har na bud'a idona a aljanna ban ganka ba, to na tabbata qamshi da hazon gidanne ya b'oye min mijina." "Ko kuma matan aljanna sun rik'eni ba." yayi maganar yana qyaqyata dariya. "Tabdjim, aiba zata sab'ub'a, Allah ko a aljanna dani kad'ai zaka kasance." Dariya yake kamar yana gabanta kafin yace "kina kishina har haka amma kika sani dole saina raba miki kaina biyu?" "To ai baka sani ba, zan iya kishi da mata indai ta gidan duniya ce, amma ina jin tsoron kishi da matan aljanna, saboda nasan sunfini da komai, sannan matane da suke burin mazan duniya su riskesu idan sunga basuyi dacen mata ba a duniya." "Amma ai ban dake, Khairat ke ba kya ciki, wallahi ke yar aljanna ce, na tabbata matan aljanna ma zasu zama hadimankine kawai, amma ba matan mijinki ba." "Zaka fasa min kai Umariri." "Toya na iya Khairiri, ke d'ince ta musamman a wajena, idan kika cire farin cikin da nake idan ina cikin masallaci, to nafi farin ciki idan ina tare dake." Ajiyar zuciya ta sauke tace "idan na biye maka zan kwana a haka, bara na saka mata kaya su tafi, amma ka sani yaufa zan gurzaka sosai." "A ina?" ya ya fad'a yana d'aga murya. Kwantar da murya tayi tace "a kan gado mana, tunda yau babu Islam a b'angaren namu, dan haka yau sai kowa na gidan nan yaji ihunka." "Na shiga tara, dan Allah ki rufa min asiri, wallahi nasan zaki iya, kar kisa mijinki ya haukace mana ko ya zama sakarai a idon Jama'a, ki taimaki wannan bawan Allah mana, kinji babyta." ya qarashe da sigar rarrashi. "Naqi d'in, saika gane ka shigo hannun mata." Tana fad'a ta kashe wayar ta aje ta fara sauya mata kayan jikinta, tsaf ta shiryata cikin kyakyawan shiri sai qamshi take kafin ta fito da ita....... Koda Papa yazo suka shiga falonshi suka gaisa sosai, sun fara tab'a hira kuma Papa yace "malam akwai wani muhimmin abu daya kawoni wajenka." Gyara zama malam yayi yace "to Alhaji ina sauraranki, Allah yasa muji alkairi." Murmushi kawai yayi kafin ya fito da wata enveloppe daga aljihunshi ya bawa malam d'in, amsa yayi ya kalli envellope d'in da kyau sannan ya kalli Papa yace "wannan fa." "Malam a karatun daka mana jiya ka nuna mana mahimmancin yin wasiyya, wannan ne yasa koda naje gida na rubuta kuma na kawo maka, dan kai kad'ai ne kafi cancanta daka adanata wajenka." "Idan ka duba zaka gani a ciki, na raba dukiyata gida biyar, uku daga ciki, ayi hidimar addini da ita, biyu a kuma a rabawa magada." Da farin ciki malam yace "a gaskiya naji dad'i sosai da faruwar hakan, ina fatan ubangiji ya saka maka da mafificin alkairinsa, Allah kuma yasa hakan ya zama sanadiyar shigarka aljanna." "Ameen ameen malam, dama wannan ne ya kawoni, ni zan tafi." Tare suka fito yayi daidai da fitowar Umar Faruk d'auke da Islam, Papa na ganinta ya saki murmushi tun basu qaraso ba ya tara hannu dan karb'arta, da yake yarinyar ma ta gane Papa sai kawai ta tafi wajenshi tana bud'e baki alamar dariya, amsarta Papa yayi saida ya danna mata sumba kusan guda goma duk suna kallonshi kafin ya rumgumeta yana shaqar qamshin jikinta, ya jima a haka kafin ya dago fuskarta ya kalla, d'an qaramin hijabin da aka saka mata ne yasa Papa ya ganta sak Khairat da tana qarama, murmushi Papa yayi yace "lallai qaramar Khairat." Umar Faruk dake kallon tsantsar soyayyar da Papa kewa yarinyar ne yayi dariya yace "kuma haka kuke kiranta ne?" Kallonshi Papa yayi yace "ba kaga tana kama da mahaifiyarta ba?" "Eh to, da yake ban ganta ba tana qarama." cewar Umar Faruk. "Hakane kam, bara ka gani." ya fad'a yana fito da wayarshi a aljihu, saida ya nemo photon Khairat sannan ya bashi wayar yace "ka ganta nan tana qarama." Amsa yayi ya d'ora idonshi akan photon, baisan dariya ta bayyana a fuskarshi ba sanda ya kalli photon Khairat bata wuce shekara d'aya zuwa da wasu watanni, tsaye take da kayanta riga da wando masu kyau farare qal, masha Allah an gyara mata gashinta amma harga wuya, sai chocolate d'in dake hannunta ta turo baki gaba kamar zata fashe da kuka, maida kallonshi yayi ga Islam dake hannun Papa, dan badan yaga Khairat a tsaye ba da sai yace Islam ce kawai saboda matuqar kamar da suke, kallon Papa yayi yace "Papa ko zan iya turawa?" "Ba komai, amma karka tsokaneta dashi, bata so ana ganin photonta tana yarinya, a qalla akwai photunanta a d'akina sunfi guda d'ari, amma ko d'aya bata da wai bata so." Turawa yayi a wayarshi harya matsu ya shiga gida ya ganta, Papa ne ya miqo mishi Islam da cewa "gata ko, ni zan tafi, ka gaishe da shalelena ba zan samu damar ganinta ba." Kafin yasa hannu ya karb'eta saida Papa ya sake sumbatarta kamar karya rabu da ita, murmushi yayi yace "Papa ai kawai ku tafi da ita, idan ma tayi kuka ku bata madara tasha." Da farin ciki yace "anyi haka Umar Faruk, mahaifiyarta ta sani?" "Ta sani Papa, kuje Da ita kawai." "Kai amma gaskiya naji dad'i sosai, saida safe." Da haka sukayi sallama Papa ya wuce shima ya shiga ciki, amma daya samu Khairat harta koma ga aiki dan haka ya qyaleta kawai ya shiga wani sha'anin shima. A lokacin daya shigo gidan kuma dare yayi sosai saboda gidan har yanzu akwai wanda basu kwanta ba, ya sameta har tayi bacci ita kuma dan haka yayi wanka shima ya kwanta ba tare daya tasheta ba dan yasan tana tare da gajiya sosai. *************** Misalin k'arfe 09:00 daidai aka d'aura auren Ruk'ayya da Ishaq, Umar Faruk da kuma Zuby a karo na biyu, hidima ake sosai tare da walima, yayin da Khairat ke juyawa yanda take so saboda babu Islam a gabanta, a haka akayi shagali sai yamma Mamie tazo tare da Islam, koda dare yayi duk kowa ya watse aka tafi rakiyar Ruk'ayya gidanta, Zuby kuma dama daga wani d'akin ne aka wuce da ita wani d'akin. 10:30 na dare Umar Faruk ya sallamo cikin falon, Khairat ya samu zaune da Islam har tayi bacci, aje Islam tayi ta tareshi tare da mishi sannu da zuwa, zai sumbaceta tayi saurin gocewa tana fad'in "a'a, ba yanzu ba baby." "Me yasa?" ya fad'a yana gyara zaman babbar rigarshi. Wasa ta d'anyi da idonta kawai taja hannunshi suka nufi d'akin Zuby tana fad'in "muje na rakaka d'akin amaryarka." Binta kawai yayi saida suka kai qofar d'akin Khairat taja ta tsaya, kallonta yayi kawai tace "kaje kawai, saida safe." Da saurin ta juya ta dawo ta d'auki Islam ta shiga d'akinta, k'in kallonshi da tayi ya fahimtar dashi tana so ta b'oye yanayinta ne ko kuma hawayeb fuskarta, da sallama ya shiga d'akin Zuby dake kwance ta amsa tare da tashi zaune, sannu da zuwa ta masa ya amsa tare da aje ledojin hannunshi, babbar rigarshi ya cire ya aje sannan ya d'auki d'aya ledar ya fito da ita yace "ina zuwa." Bud'a d'akin yayi ya shiga ba tare da yayi sallama ba, zaune ya sameta taba Islam baya ta fashe da kuka, tana ganinshi tayi saurin mik'ewa tsaye tana share hawayen, cike da qarfin hali da son nuna ba komai tayi murmushi tace "baby, me kake yi nan kuma?" Saida ya tsaya gabanta sannan yace "abunfa bashi da sauqi, amma kin kasa gane haka, na fahimci kina son b'oyewa ne kuma na jinjina miki akan hakan, amma karki bari hakan ya cutar dake." Rufe bakinta tayi ta fashe da kuka ta fad'a jikinshi tace "ina so na taushi zuciyata amma na kasa, kukan nan ne kad'ai zaisa naji sauqi a raina, amma kayi hak'uri banyi dan na b'ata ranka ba." Shafa bayanta ya dinga yi yana rarrashinta har saida tayi shiru, toilet yajata ya cire mata kaya da kanshi ya mata wanka ya saka mata kayan bacci ya bata maganinta na ciwon kai tasha, dan tana tsoron kanta ya fara ciwo baya kusanta, sannan ya kwantar da ita ya musu addu'a tare da Islam sannan ya fice daga d'akin, yana fita ta sake fashewa da kuka tana jin kamar tayi ihu, ta koma tana kuka amma babu sauqi a al'amarin, dan haka kawai ta d'oro alwala ta kabbara sallah, ba ita ta kwanta ba saida tayi sallah asuba, a lokacin Islam ta farka ta bata nono bacci ya d'auketa, koda ta farka sai taji wani shaqat a zuciyarta ba wata damuwa, hakan ya mata dad'i sosai da farin ciki tayi duk wani abinda ya zame mata jiki tasan tana yi a wannan lokacin. Tana gamawa ta shiga cuisine (kitchen) tare da abin sauraronta ta maqala a kunne ta fara aikin hankali kwance, saboda Islam tasha wanka ta koma bacci, aikinta take tana rausayawa ita kad'ai tare da bin waqoqin da take sauraro, tana cikin aikin taji kamar motsi a bayanta, da sauri ta jiyo dan ganin waye, tana ganin Umar Faruk tayi saurin cire abin sauraron ta rik'e a hannu tana zazzare ido, danya hanata sauraron waqoqi barkatai musamman idan tana cikin nishad'i, takowa yayi har gabanta ya tsaya ya janyo kunne d'aya yasa a kunnenshi, cirewa yayi yana kallonta yace "yanzu bana hana ba?" Kamar zatayi kuka tace "kayi hak'uri baby." "Shikenan na hak'ura, ina Khairat?" Sakin jikinta tayi tace "ta koma bacci." Hannu yasa ya bud'e tukunyar data rufe yana fad'in "shalelen Papa kenan, hutu kawai." "To ai mamanta tabiyo." cewar Khairat. "Na sani mana, tunda kamarta d'aya ma da mahaifiyarta kamar an tsaga kara." Kallonshi tayi ta d'auki albasarta taci gaba da yankawa tace "a ina kaga mamanta? da ace ka tsere min da shekaru masu yawa ne sai nace ko ka tab'a ganina." Kallonta yayi kafin ya d'auki cokali yana juya mata sauce d'in yana fad'in "aiba zaki qara min wayo ba, nasan komai a game dake, kullum na kalli qaramar Khairat saina dinga tunanin ina ta samu wannan tsalelen kyawun na yarinyata, ashe dai mahaifiyarta tayo." "Wai da gaske ka ganni?" Kafin ya bata amsa tace "nasan ma aikin Papa ne, dansu keda photona bila adadin." Rufe tukunyar yayi ya aje cokali ya rumgumeta ta baya yana shaqar qamshinta tare da fad'in "na ganki alkairina, saina kasa banbance a wane matakine ki kafi kyawu, yanzu ko kuma a matakin yarinyata." "Ai yanzu nafi kyau, kaima ka sani." "Na gani to." ya fad'a yana juyo da ita gabanshi. Qura mata ido yayi yana kallon fuskarta a hankali ya kai bakinshi a nata ya fara tsotsa, sunyi nisa a duniyarsu suka ji wani qauri qauri, da sauri suka raba jikinsu suna kallon tukunyar bisa wuta, Umar Faruk ne ya kai hannunshi ya bud'e hayaqi yayi sama, kallon juna sukayi Khairat ce ta turo baki gaba kamar zata fashe da kuka, shima turo bakin yayi yana kallonta ya kama kunnuwanshi alamar ban hak'uri, kawai sai suka tuntsire da dariya kuma har suna rumgume juna, kashe gas d'in tayi tace "tunda wannan ya qone, sai kuyi hak'uri kuci qwai da dankali." "Ni dama shi nake sha'awar naci." ya fad'a yana satar kallonta. Qwai ta d'auka yayin da ta had'ashi da dankalin turawa ya ta fara ferewa, zata buga qwan taji yace "ki dai buga a hankali, karki ruguzashi kamar yanda ki kayi a waccen ranar." Da dariya tasa qugu ta tureshi tana fad'in "ai dane wannan ba yanzu ba, kaima kasan haka yanzu matarka gogaggiyace." "Uhum, zan gani dai." Kallonshi tayi tace "baby, amma dai ba zaka fara fara fita aiki da wuri ba ko?" Hararanta yayi yace "me yasa, yau ma akwai islamiyya, amma kafin na shiga ajin farko zan fita na dawo." Cikin shagwab'a tace "haba baby, dan Allah ka taimaka ka bamu hutu, ka ganni nan wallahi a matuqar gajiye nake, kawai saboda bana so kaci abinci a wani wurine ba nan ba yasa nake had'a abin karin nan, idan kace mu shiga aji a haka Allah bacci zanyi maka." "Kiyi baccin mana, ai tsumagiyata nanan." Aje wuqar hannunta tayi ta matso daf dashi ta rik'e qugu tace "me zakayi, nace me zakayi, dukana wai? to gwada ka gani, wallahi da kayi nadamar da har iya tsawon rayuwarka ba zaka manta da wacece Hajia Khairat ba." Gimtse dariyarshi yayi shima yace "to ki jaraba ki gani mana, ba Hajia ba ko hajijiya ce Allah zaneki zanyi, kaji min marar kunya kai." Shaqo wuyan rigarshi tayi ta kara bakinta a hancinshi tace "wacece marar kunya, Ni? yanzu baka ji kunyar fad'a min haka ba, lallai ma yaron nan." Da sari ya fizge rigarshi ya shaqi kwalar rigarta yana fad'in "waye yaron, Ni, ni kike kira da yaro? karki sake, wallahi kika sake qalubalantar mazantakata zaki gane kurenki." Itama dai fizge rigarta tayi ta d'auki wuqar dake gefenta ta d'ora mishi a wuya a wajen da babu kaifin tana fad'in "zan zubar da jininka." Shiru tayi tare da kallon qasan cikinta, da mamaki ta d'ago ta kalleshi dan bataga lokacin daya d'auki cokali mai yatsun daya d'ora mata a ciki ba, aje wuqar tayi tace "hamago, kullum kai ke nasara a kaina, wai me yasa ne haka?" Aje cokalin yayi shima ya rumgumeta jikinshi yace "ban sani ba nima Khairiri, haka kawai gudanar jinina ke nunkuwa a duk sanda nake kusa dake, kuzarina kuma yana rub'ayya fiye da yanda zan kasance a wani wajen daba kusanki ba, amma duk da haka kuma Khairat ce nasarar Umar Faruk." D'ago kanta tayi ta kalleshi tace "haka nima, Umar Faruk kaine silar duk wata nasarata da kuma kasantuwata akan hanya madaidaiciya, wannan yasa nake qara sonka a kullum a kowane fitar numfashi." Laqace mata hanci yayi yana fad'in "ban tab'a tunanin zan mallakeki ba, musamman a lokacin da kike ji da kanki da kuma izza da iko." Turo baki tayi tace "bana son tuna bayan nan fa, nima ai ban tab'a tunanin zan mallakeka saboda marin daka tab'a kwad'amin, a gaskiya a ranar na tsorata da kai, kuma raina ya b'aci sosai saboda ganin wani ya d'aga min ysata, abinda ba'a tab'a yi ba." Dariya yayi yace "ashe kinji ba dad'i, amma kuma ba kiyi tunanin ni me zanji ba? aiko yanzu kika qara marina, to zan sambad'eki da marine." A raunane ta kalleshi tace "kasan kuwa a waccen ranar marin daka min ne yaja na kwanta asibiti saboda b'acin rai." Ajiyar zuciya ya sauke yace "kiyi hak'uri to." Maqale kafad'a tayi irin na yara tace "um um." Dariya yayi ya durqusa gwiwoyinshi biyu ya kalleta yace "ki rama to, idan hakanne zaisa ki hak'ura, ni Umar Faruk zan tsayar da kumatuna har lokacin da kika gaji dan kanki kika dakata." Maqale mishi tayi a wuya ta sakar mishi nauyinta hakan yasa suka fad'i kwance a tsakiyar cuisine tana fad'in "wace ni na mari mijina, waccen ma ai dan tabbatar da soyayya ne a tsakaninmu." Da dariya ya kalleta yace "uhum, ashe dai tun a waccen lokacin ma kika kware min, yarinya taga dogon saurayi mai dogon hanci." Da dariya ta laqace hancinshi tana fad'in "inji wa? ba wani nan malam, kai dama maman Dady tace tsawonka yayi yawa." Ciccib'awa yayi Da ita sukayi zaune yana rumgume da ita yace "ita maman Dadyn ce tace haka?" Gira ta d'aga masa shi kuma yace "barni da ita, bansan bata cikin masoyana ba sai yanzu, amma insha Allah d'an da zata haifa zata haifi jarumi ne kamar ni kuma harda tsayin ma da komai." "Ameen." cewar Khairat. Da irin wannan shirmen suka qarasa wannan girki da rabinshi surutu ne, saida suka fito falo jera kwanukan abincin suka tuna akwai Zuby fa a b'angaren nasu, tana zaune tana jin hayaniyarsu ita dai tayi shiru tana kallon tv. ************ Haka rayuwar taci gaba da kasance musu cikin farin ciki da jin dad'i da kuma soyayya, har yanzu qalubale na rayuwar aure Khairat bata fara fuskantarshi ba dangane da mijinta, wanda Umar Faruk na ganin Khairat d'in ce silar faruwar hakan, dan duk yanda ranshi zai b'ace ko kuma ta b'ata mishi rai, to a take a wajen take bashi hak'uri tare da rarrashi, dole yake saukowa ko baiyi niyya ba, Zuby kuma yanzu ta kwantar da kai, zaman lafiya da mutunta juna kai kace yan uwane a yanzun, sosai suke zaman lafiya hakan kuma nawa Umar Faruk dad'i sosai. Yanzu Khairat ta aje fita aiki a ma'aikata yayin da ta damqa ragamar kula da komai a hannun manager, amma daga gefe saita bud'a wani qaton boutique data cikashi da kayan mata komai da komai, shima kuma yana qarqashin kulawar wata mata ce sai dai taje ta dubo ta dawo gida, karatu da kuka da mijinta ne kawai a gabanta da kuma yayanta, arziqi na hab'aka sosai musamman na Umar Faruk kamar yanda wuta kecin busashen ice, ta ko ina bud'i yake gani hakan yasa ya dage sosai wajen taimakawa addininshi da k'arfinshi da kuma dukiyarshi, yayin da ya kwashi suka iyalinshi suka koma sa'udiya yana sake d'aukar karatu. *SHEKARA TAKWAS* suka d'auka basa qasar, a lokacin idan ka gansu sai kace haihuwar can ne dama, musamman Khairat da Islam da kuma yaran da aka haifa acan, yanzu haka Zuby nada yara hud'u, Imane ce farko sai Ihsan, Kaussar da kuma qaraminsu Marwane, Khairat kuma tana da uku, Islam, Ammar da kuma Usseimine, kuma dukansu saida aka m Khairat aiki ta haifesu, shi yasa ma likitocin garin suka bata shawara akan a juyar da mahaifarta domin lafiya idan tayi haihuwa ta hud'u, Umar Faruk kuma ta amince da hakan, dan haka yanzu take cike da tsoro bata fatan d'aukan wani cikin dan karsu juyar mata da mahaifa, koba komai tana so ta cikawa Umar Faruk gida da yaran da suka fito daga tsatsonta, yaran na d'aukar karatu a masallacin madina kuma hadda kawai ake, hakan yasa iyayen da yaran duka ke jin dad'in zaman acan, amma haka suka dawo suka ci gaba da rayuwarsu da kuma ci gaba da harkokin da suka bari a hannun mutane. Bayan dawowarsu sun tarar da abubuwa sun faru, a ciki akwai qara aure har biyu da Abbakar yayi, da kuma auren Usman da Aliyu, islamiyya kuma nanan yanda take, amma yanzu daga cikin malamai masu koyar da tahfizin Qur'ani harda Islam da qaninta Ammar, rayuwar Alhamdulillah Zuby da Khairat kai kace ba kishiyoyi bane, zaman lafiya kawai suke, yayin da Umar Faruk ya bawa Zuby jari itama ta fara siye da siyarwa a cikin gida. *************** Mammie ta dawo gaban yarta da zama saboda tsufa daya kamata tana buqatar mai tamaka mata a yanzun, yayin da Mamie da Papa suka k'i tsufa da soyayya, dan yanzu ne Papa ke nunawa Mamie soyayyar da bai nuna mata ita ba a baya, suma dai suna zaune lafiya cikin farin ciki, Papa ne yama Mamie wata kyauta mai girman gaske data kusan fitar da ita a hayyacinta, kuma ya batane saboda hak'uri da tayi dashi a lokacin da ba kowace mace bace zata iya zama dashi, dan haka Mamie da taji Khairat ta dawo gari tace tana son ganinta idan ta huta, ta fad'awa Umar Faruk kuma yace ta shirya da kanshi zai kaita tare dasu Islam. *********** Khairat ce zaune akan sallaya ta mik'e qafafu tana azkar na sabah, da sallama Islam ta shigo d'akin tare da zaunawa tana fuskantar mahaifiyarta, amsawa Khairat tayi Islam ta d'ora da "Ina kwana Mamie, antashi lafiya?" "Lafiya qalau yarinyar da babu kamarta, kin tashi lafiya kema?" Da murmushi Islam ta amsa da "lafiya lau cher mère (uwa mai tsada), ya gajiya ya kuma hak'uri damu?" Dariya Khairat tayi tace "ai yara irinku iyayensu basa hak'uri dasu, hasalima kune zakuyi hak'uri da rigimar iyayenku." Hannayenta tasa ta fara latsawa Khairat qafafunta Khairat d'in ce tace "kamar kinsan kuwa qaramin qannanku yana saka min ciwon qafafu." Cike da nutsuwa ta kalli mamanta tace "Mamie, zaki sake haifa mana qane ne?" Kai ta d'aga mata kafin tace "insha Allah ba." Walwalar fuskarta ce ta d'auke tace "Amma Mamie me yasa ba zaki huta haka ba? kinfi son kullum a dinga fed'eki wajen fito damu duniya." Dariya Khairat tayi tace "Islam, duk wahalar da nake sha daga d'aukar cikinku har zuwa haihuwarku, ina d'ora idona a kanku saina ji na manta da wahalar dana sha, ina sonku kuma ina sonku fiye da kaina, dole zan juri kowace irin wahala wajen ganin kunsha iskan duniya kuma, bugu da qari bana takaicin haifawa mahaifinku 'ya'ya, da ina da iko Islam saina haifawa mahaifinku yara goma sha biyu, sai dai bansan ko zan iya ba dan ana barazanar rabani da mahaifar gaba d'aya, amma a gaskiya a yanzun haifawa mahaifinku yara ne kad'ai abinda nake ganin zan iya yi na biyashi alkairanshi gareni." Islam kam da ido kawai ta kafe mamanta tana saqe saqe a ranta, jin shirun yasa Khairat qyasta mata hannu, a d'an zabure ta kalli mahaifiyarta tace "Mamie, ina jin dad'in yanda kike zaunar dani kina fad'a min abinda ya shafi rayuwarki, duk da shekaruna sun kasa amma bakya gudun zaunawa dani kiyi hira, a gaskiya ina jin dad'in hakan." Da murmushi a fuskarta tace "kefa 'ya macece, dolena na n'a a matsayina na uwa na jaki a jiki, inhar ina so kema idan kin girma karki b'oye min komai daya shafi rayuwarki." Murmushi kawai Islam tayi yayin da Khairat tace "an jima zamu tafi gida wajensu Mamie saiku shirya da wuri keda qannanki." "To Mamie, yau zanga mai gidana da 'yar tsohuwa." Duka Khairat ta kai mata ta goce tana fad'in "uwaki tsohuwar ai." Sallamar Umar Faruk tare dasu Ammar da Useimine ne yasa suka nutsu suka amsa, qara yaran suka zube suka gaishe da mamansu ta amsa tare da shafa kawunansu tana fad'in "har an dawo daga masallaci kenan?" "Eh Mamie." cewar Ammar. "Da fatan dai kun min addu'a ko?" "Eh Mamie, mun miki." "To na gode sosai, Allah ya albarkaceku yaran kirki." "Ameen." duka yaran suka amsa. Kallon Umar Faruk tayi dake zaune bakin gado yana kallonsu cike da qauna tace "baby ina kwana." "Lafiya qalau, kin tashi lafiya?" "Lafiya lau, ya gajiya?" Islam ce ta kalli babanta tace "ina kwana Papa." Saida ya shafa kanta yace "Lafiya lau alkairina, kin tashi lafiya?" Kallonshi tayi tana murmushi shi kuma yace "kullum kina mamakin wannan sunan ko?" "Eh Papa, ni dai nasan Mamie keda sunan, amma kuma sai kuka kirana dashi." Kamo hannunta yayi yace "kina ji ko? karki damu kanki da wannan sunan, ina jin dad'in sunan ne saboda soyayyar da nakewa mai sunan, zan iya kira kowace mace da sunan amma kuma mahimmancinshi yasa ke kad'ai nake fad'awa shi saboda girmanki a zuciyar Papanki, sannan a ranar da aka fito dake daga cikin mahaifiyarki, a lokacin mamanki tayi barazanar barina a doron duniya, amma da izinin ubangiji sai Allah yasa kwananta basu qare ba, hakan ma ya qarfafa min gwiwa wajen kiranki da alkairi." Wata ajiyar zuciya Islam ta sauke tace "Papa, Allah ya bar manaku, Allah ya qara muku lafiya mai anfani, a gaskiya ina alfaharin kasancewa yarku, nasan da za ace iyaye d'aya ne da suka rage a duniya mutanen kirki, to zan iya cewa kune kuma Allah ya mallamaka minku, kunga kenan nafi kowa sa'a." Rumgumeta Umar Faruk yayi dan sak tana magana kamar mahaifiyarta, Khairat ce tace "ina magana ka min shiru saboda kana magana da 'yarka." Shiru yayi yana kallon yaran da suka mik'e suna fita daga d'akin, yana ganin ficewarsu ya janyo hannun Khairat ta taso ta fad'a saman qafafunshi yana fad'in "ashe 'yarki ta fini muhimmanci yanzu?" Da mamaki tace "ban gane ba, meya faru?" "Tunda har zaki fad'a mata kina da ciki alhalin ni ban sani ba." Dariya tayi cike da kunya tayi qasa da kanta, binta yayi da kallo yana murmushi, d'agowa tayi tace "kenan lab'e kake mana idan muna sirri nida yarinyata?" "Eh mana, kuma daga yau zan fara, danna fahimci abinda kike fad'a mata ma ba kya fad'a min." Kallonshi tayi tace "wai kishi kake da hakan?" Turo baki yayi gaba yace "eh mana, naga yarinya na neman rabani da babyta ba dole ba." Danna kanshi tayi tsakiyar qirjinta tana fad'in "babyna sarkin rigima, in banda abin baby ai Islam daban, kuma baban Islam daban." "Taya zan tabbatar da haka?" cewar Umar Faruk. Saida tayi wasa da idonta kafin tayi murmushi tace "bara ka gani." Hijabinta ta bud'a ta zura kanshi a ciki ta fito da nononta tasa mishi a baki tace "har yanzu baban Islam nasha nono, amma Islam ko a mafarki ba zata sha ba saboda ta wuce nan." Yana jin bakinshi a qamamin nonuwanta kawai saiya narke ya rufe ido ya fara tsotsa yana sauke numfashi da k'arfi, da qyar ya rabu da ita ya ta samu ya kashe wuta ya rufe d'akin, dawowa yayi a hankali ya kwantar da ita kan gado ya ta fara kulawa da ita wata duniyar, da qyar ta samu ta kalleshi tace "baby, ka sarara min mana, jiya fa baka bari nayi bacci ba, gashi ina buqatar nasa wani abu a cikina, idan ka qara yanzu fa zan iya mutuwar maka." Dariya yayi yace "ba laifina bane baby, laifinki ne da kika zama mafi zak'in zuma da kuma gamsar dani, idan a ra'ayina ne saina shekara tare dake ina abu d'aya, domin kuwa bana gajiya dake ko kad'an, kuma da kike cewa kina buqatar zaki ci wani abu ai wani abun zan baki kici, dan haka ki daina maganar mutuwa ma dan tare zamu mutu." Yana fad'a ya sake wata addu'ar cike da son kaiwa a bakin gab'a ya zura kanshi, wata irin ajiyar zuciya ya sauke mai kama da kuka, qamqameta yayi yana fafutar sauke numfashi, itama yar siririyar qara ta saki saboda ratsata da yayi, wanda hakan harya zamar mata jiki indai zai shigeta, ya jima a haka kafin ya fara rad'a mata a kunne cikin muryar kuka "Khairat kin had'u, wata rana zaki kasheni da wannan d'and'anon naki, wallahi bana gajiya dake ko kad'an, dan Allah ki taimaka ki rage wahalar dani haka, Khairat na baki kaina da komai dana mallaka, na baki kyautar yayana duka dama gidan nan, Khairat, yawwo Allahna...." Danna kam kamar karatu ne da kullum saiya biyashi, dan haka ta rufe mishi baki da bata bakin dan karya tona mata asiri yara duk sun farka.... Bayan awa uku suka fito cikin shirin tafiya gidansu Mamie, yaran suka samu zaune sunata hayaniya sai Zuby zaune a kujera tana kallonsu, kallonsu Zuby tayi har cikin zuciyarta taji sun birgeta saboda qyalin da suke fuskokinsu d'auke da tsantsar farin ciki, harga Allah ta sani sarai Khairat ta mata nisan da ba zata iya kamata ba, ta sani ta fita kula da mijinsu yanda ya kamata, da murmushi a fuskarta tace "auntyna barka da fitowa." Kunyace ta lullub'e Khairat, cike da basarwa tace "barka yer uwa, kina zaune." "Barka oga." ta fad'a tana kallonshi. Da murmushi shima yace "barka amaryata, ya yaran?" Tsaye ta mik'e tace "bismillah ko, abincinku na jiranku." Dinning suka nufa Khairat na fad'i "yara sun karya?" "Ai harni na karya, dan naga idan mun tsaya jiranku sai olcer ta kamamu." Yanda Zuby tayi maganar yasa suka kwashe da dariya suna zaunawa, da kanta ta zuba musu sannan ta zauna suna ci ita kuma tana kallonsu suna hira gaba d'ayansa, saida suka gama Khairat tace "yer uwa zanje gidana amsa kiran Mamie, amma da yaran zamu tafi." "Dukansu?" cewar Zuby. "Eh to, ki zab'i wanda kike so na bar miki, saina tafi da wanda suka rage." Turo baki tayi gaba tace "auntyna ba wayo zaki min ba kuwa, kinsan ba zan kasa cewa ki bar min Islam da Ammar ba, kuma nasan dole kina so ki tafi dasu saboda su Mamie nasan ganinsu." Cije baki Khairat tayi tace "umm gaskiya kam, to kinga na bar miki Ihsan saboda ta kama miki wasu aiyuka, koya ki kace?" "Eh to, hakan ma yayi." ta fad'a da fara'a. D'ora hannayenta tayi akan tebur d'in ta matso da kanta kusan fuskar Zuby tace "toya maganar girki? kinsan fa mijinki acici ne." Dariya Zuby tayi kafin tace wani abu Umar Faruk ya gimtse hak'ora yana d'aukar makullinshi da waya yana fad'in "idan akayi gulmata Allah yana sama yana kallo, kuma ba zan yafe ba." Kamar had'in bakin Khairat da Zuby suka kalleshi suna fad'in "zaka yafe ne ai." Kallon juna sukayi saboda had'a bakin da sukayi, Khairat ce ta d'ora da "zaka yafe idan kaji matsa." Qasa da sama ya hararesu yace "to saina gani ai idan dole za'a sani." Zunbur suka mik'e sukayi kanshi da sauri ya bar wajen yana fad'in "kuyi hak'uri dan Allah, wallahi ban shirya canza wannan kayan ba." Dariya suka saka mishi kafin yace "uwar gida sarautar mata, ke kawai nake jira ki wuce muje idan kun gama kacaccana min yara kamar naman miya, dan ba zan barki kiyi tuqi da kanki ba." kallon Zuby Khairat tayi ita kuma ta rik'e hannun Khairat tace "baki da matsala auntyna, kije gida kisha zamanki ki huta, girkin rana dana dare yana kaina insha Allah, zan kula da komai kamar kina nan." Dafa hannunta tayi tace "na gode sosai yer uwa, sai mun dawo." "Ku tashi mu wuce, Iman kiyi hak'uri ke zaki zauna gida tare da Mamie kinji." Tashi yarinyar tayi ta rik'e hannun Khairat tace "Mamie ina so naje tare daku nima." Shafa fuskarta tayi tace "karki damu kinji yata, kiyi hak'uri ki zauna, na miki alk'awari fita ta gaba da zanyi dake kad'ai zan tafi." "Da gaske Mamie?" ta fad'a da murmushi. Da ido kawai ta mata alama dan haka ta musu addu'a sai sun dawo suka fice Umar Faruk na fad'in "harda wani fita ta gaba, to waya fad'a miki zaki fita? aike da fita saikin haife abin cikinki insha Allah." "Ko kuma idan ka haife ba, dan wannan karan kai zaka haihu kaji me muke ji, duk da dai ana cewa waini kamar kyauta nake samun yaran, saboda fasani kawai ake ana fitowa dasu, bansan zafin da ake ji ba n'a a lokacin da yaro yake son fitowa ta gaba ba." Hakan yayi daidai da zuwansu b'angarensu Mama, da sallama suka shiga nanma sun jima suna gaisawa da tsokanar da yaran ke musu, kafin nan suka fito suka wuce, sai lokacin ya jefeta da tambayar maganar da tayi lokacin da zasu shiga da fad'in, "Inji wa? ai kinfi kowa wahala." ya fad'a lokacin da yake zaunawa mazauninshi. Kallonta yayi yace "ai insha Allah kema zaki haihu da kanki, da yardar Allah zaki ji me ake ji kema." Dukanshi tayi a kafad'a tana fad'in "baby, wacce nake yi ma fa akwai zafi sosai." "Na sani, amma ina so ya tsaga ya fito ta gaba." yayi maganar qasa qasa yanda yaran ba zasu ji ba. "Ashe baka sona, amma karka damu zan baka mamaki, wannan karan da kaina zan haihu in Allah yaso ya yarda." "Haka nake so." ya fad'a da kanne mata ido. Gida ma koda suka isa gaba d'aya suka shiga ciki, sun samu Papa dan haka suka jima suna tab'a hira kafin Umar Faruk ya barsu a zuwan saiya dawo da dare, duk da Marwane Iman da Kaussar ba daga cikin Khairat suka fito ba, amma sun sake sosai a gidan kuma su Mamie babu wani banbanci da suke nuna musu, haka yaran keta wasarsu har suka fita harabar gidan lokacin ne kad'ai Mamie ta samu ta keb'e da Khairat, anan ta fito da takardu da makullai da kuma check na kud'i ta bata tana fad'in "wannan sune abubuwan da mahaifinki ya bani a matsayin godiyar zama da nayi dashi, takardun gida ne dana compagninshi dake sarrafa kayan roba, sai kuma makullan gidan dana mota, da kuma check ta kud'i har million goma sha biyar." Da farin ciki Khairat ta rik'e kayan tace "wow Mamie, a gaskiya na tayaki murna, Allah ya qara danqon qauna, ya albarkaci zuri'arku." "Ameen, amma Khairat ba zan iya rik'e abubuwan nan ba, sunyi yawa, gashi kuma girma yana zuwa mana, ke kad'ai gareni a fad'in duniya, dan haka nima na mallaka mikisu halak malak." Biro ta fito dashi tayi rubutu akan wata takarda sannan tace "zanyi magana da lawyer, komai zai koma naki." "A'a Mamie, nima ban amsa ba gaskiya, idan kuma ba kyaso to kawai zai a miki kyauta dashi." "Na riga da na saka hannu, kiyi abinda ya dace kawai mallakinki ne yanzu." Ba yanda Khairat ta iya haka ta rik'e wannan kayan, suna nan har zuwa karfe 09:15 na dare sannan Umar Faruk ya iso, saida ya jira ita da yara suka gama harhad'a komantsansu kafin suka wuce, koda suka isa gida kowa wanka yayi babu wanda ya kula ta abinci sai Umar Faruk kad'ai, amma su sun qoshi tun daga can dan haka kowa yabi lafiyar katifa suka kwanta, dare yayi Umar Faruk da Zuby suka tashi daga kallon tarihin annabi Yusuf kowa ya nufi makwancinshi, zai shiga d'akin Khairat yaga haske a d'akin Islam, d'akin ya nufa a hankali ya tura qofar d'akin, zaune take akan sallaya ta d'aga hannaye sama sai kwararo addu'a take a harshen labarci tana kuka sosai, kallon Iman da Ihsan yayi dake kwace akan gadajensu suna bacci, qarasawa yayi wajenta ya sunkuya yana kallonta, tana kallon mahaifinta ta goge hawayen tace "Papa, baka kwanta ba?" Cike da qaunar yarinyar yace "Qaramar Khairat ya zan kwanta alhalin baki kwanta ba." D'an murmushi tayi tace "yanzu zan kwanta Papa." "Amma me yasaki kuka haka?" Yana tambayarta saita sake fashewa da kuka zuciya a wuya, fad'awa tayi jikinshi tana kuka sosai, da qyar ya rarrasheta yace ta fad'a mishi meya faru, cikin muryar kuka sosai tace "Papa, Mamiena nake wa addu'a, ina tausayinta sosai Papa, d'azu Mamie ta fad'a min bata damu ba dan an fasata an fito damu, ita kawai burinta ta ganmu a raye, Papa Mamie tace zata iya haifa maka yara goma sha biyu kuma duk a fasata amma ba zata damu ba, Papa naji girman mahaifiyata ya qaru a idona kuma ina sonta fiye da yanda nake son kaina, Papa bansan me zamu sakawa mahaifiyarmu dashi ba, Papa shi yasa nake kuka saboda rashin sanin sakamakon da zanyiwa Mamiena." Shafa bayanta ya dinga yi cikin taushin murya yace "Islam." Da sauri ta kalli Umar Faruk saboda tunda take bata tab'a jin sunanta daga bakinshi ba, kafeshi tayi da ido tana sauraronme zaice, cikin nutsuwa yace "mahaifiyarki macece da babu irinta nidai a wurina, zuciyar Mamienki zuciya ce da koni dana zama malaminta wallahi bana da irinta, Islam mahaifiyarki tamin alkairi da dama kuma ta nuna min soyayya tare da kulawar da banyi tunanin zan samu ba a rayuwata, ku 'ya'yanta ne dole ta soku fiye da komai, kuma ina fad'a miki da babbar murya kiji da kyau Islam, son da mamanki take miki bana miki ko d'aya daga cikin uku, domin kuwa ni ubane mahaifi, a lokacin data d'auki cikinki an cutar da ita sosai ba ba tare da haqqinta ba, saida takai lokacin da ko ruwa tasha saita amayesu, amma bayan ta samu lafiya ta kuma san ba zata iya haihuwa da kanta ba, wallahi Islam ko sau d'aya bata tab'a nuna min damuwa akan hakan ba, saiya zamana kullum tuna min take akan idan ta fara naquda a kaita asibiti da gaggawa, amma kasancewata ina namiji sai nake ganin kawai zata iya haihuwa da kanta, saina dinga fad'a duk lokacin da tace haka, amma ita burinta kar abinda ke cikinta yasha wahala ba zata so hakan ba, a ranar da aka fito dake daga cikinta sai tayi qoqarin barina a cikin wannan duniyar, bansan tsoroba, amma a ranar na tsorata a lokacin da naga ana fafutukar ceto rayuwarta, maganar Islam a wannan lokacin na fidda da matata, a take a wajen na qudurawa raina zan rad'a miki sunan Islam kamar yanda ta buqata, amma ni zan dinga kiranki da Khairat, amma sai ubangiji yayi ikonshi ta hanyar maido min da farin cikina, wannan yasa kullum nake cikin godewa Allah, maganar da ki kayi kuma ta rashin sanin me zaki sakawa mahaifiyarki dashi, kinsan me zaki yi?" Kai ta girgiza tana share hawaye, d'orawa yayi da "ki daina kuka idan kina wa mahaifiyarki addu'a, abu d'aya da zakiyi shine, ki dage kullum wajen sakata addu'arki, na biyu kuma shine ki tsaya tsayin daka wajen kyautata mata da kuma yi mata biyayya, na uku kuma ki guji duk wani abu da zai b'ata ran mahaifiyarki, kin fahimta?" Da murmushi a fuskarta tace "na fahimta Papa, kuma zanyi yanda kace insha Allah." B'ata rai tayi ta kalleshi sosai tace "amma Papa, waya cutar min da uwa da ina cikinta?" Kallonta yayi yace "me zakiyi, me yasa kike so ki sani?" Fuskarta ba alamar wasa ko kad'an tace "zan tsani wanda ya cutar min da uwa, zan sakashi addu'ata Allah ya sakawa mahaifiyata." Hannunta ya rik'e yace "a'a Islam, wannan ba halin mahaifiyarki bane, burina shine duk wani yaro daya fito ta tsatsona koda ba ita ta haifeshi ba to yayi halinta, tana da yafiya da mantuwa ga alkairin da tayi, ba zan fad'a miki ba dan bana son haddasa gaba a cikin gidana, amma ina umartarki daki yafewa wanda yayi kamar yanda mahaifiyarki ta yafe itama." "Papa, Mamie ta yafewa mai laifin?" ta fad'a da mamaki. Murmushi ya mata yace "sosai, aina fad'a miki ita ta dabance, shi yasa nake qara qaunarta kullum." Itama murmushi tayi tace "shi yasa Mamie bata tab'a yin hushi da kai ba Papa, sai taje islamiyya ka daketa a hannayenta amma ba zata nuna ba a gida." "Wannan shine karamcin Khairat." D'aukarta yayi ya dire akan gado ya rufeta da zani yace " kiyi bacci lafiya gimbiyata." Da murmushi tace "ka kula min da mamana." Kumatunta yaja yace "wato ni kin wareni ko?" Da dariya tace "uhhibuka ya Abhi." Shafa kanta yayi yace "uhhibuki kasiran." Da haka ya kashe wutar d'akin ya koma d'akin Khairat, tsaye ya sameta tana sallah, amma tana ganinshi saita fara gaggawa dan karta shiga haqqinshi, da hannu yace "kici gaba kawai." Dan haka bata tsaya ba taci gaba, zaune yayi a tsakiyar gado yana kallonta yayin da yake fad'a a zuciyarshi "haqiqa kyawun zuciyarki ne ya mallamaka miki yarinya kamar Islam, dama Allah yayi alk'awari yana tare da masu hak'uri, kinyi hak'uri kuma gashi kina tare da ubangijinki, da idona ina ganin suffofin yan aljanna a tare dake, kamar yanda nake ganin wacce Allah yake so, a Qur'ani Allah ya fad'a mana wad'anda yake so, kuma kusan duka kin had'a wannan suffofin, Allah yace yana son masu hak'uri, kina da hak'uri alkairina, Allah yace yana son masu tuba da tsarkakewa, kina tuba daga kurarenki na baya da kuma tsarkake zuciyarki a kullum, Allah yace yana son masu tawakkali dashi, kin dogara ga ubangijinki, da kuma sauran suffofi da dama, ina fatan Allah ya qara miki imani da tausayi a zuciyarki, Allah ya baki yaran da zasu ji tausayinki kema." *************** Kasancewar yau safiyar Alhamis ce yace duka gidan suka tashi da azumi, Khairat kuma ta bawa Umar Faruk wannan kud'in da Mamie ta bata, tambayarta yayi "na miye kuma?" Cikin fara'a tace "Mamie ta rasa yanda zatayi dasu, shi yasa na baka a matsayinka na mai da'awa, kuyi anfani dasu wajen d'aukaka kalmar Allah, ina so sakamakon ya samu mahaifiyata a duk inda take." "Khairat, yanzu gaba d'aya kud'ad'en nan kin bayar ayi hidimar addini da ita? Allah kad'ai zai biyaki, kuma insha Allah zanyi iya qoqarina wajen ganin anyi abinda ya dace." "Haka nake son ji, Allah ya taimaka." A wunin ranar Ruk'ayya tazo gidan tare da yaranta uku saina biyar dake ciki wanda ba zai wuce wata shida ba, dukansu zaune suke a falonsu Mama, yayin da Aunty Saratu ke d'auke da tsohon ciki matar Usman ma da Aliyu ga kuma Ruk'ayya, hira ake sosai cike da farin ciki da nishad'i, Saratu ce ta kalli Aliyu tace "qaramin miji dan Allah ka taimaka ka siyo mana alala muci." "Ke fita idona in rufe, da wane kike so naji to, siyan alala ko siyan rago, dubeku fa ku uku zan siyawa ragon suna, wataqila ma cikinku wata ta haifi yan biyu." Umar Faruk ne ya kalleshi yace "uku kuma, biyar dai ko." Kallonshi Aliyu yayi ya kalli Khairat da Zuby yace "oho, amma shine baku fad'awa mai siyan ragon ba, to shikenan banda ku a ciki." Hararanshi Khairat tayi tace "to miye namu a ciki, d'anka za'a goranta ma ace baka siya mishi ragon suna ba." Zuby kam cewa tayi "nidai ka cireni ma a lissafi, idan akace dukanmu muna d'auke dashi ai sai abun yayi yawa." "Inji wa, ba wani yawa, suka zamu iya ji daku." "To nidai ban dani gaskiya." cewar Zubyn. Umar Faruk ne ya bita da wani kallo yace "in tona?" "Ka tona mi?" ta fad'a tana kau da kanta. "Kice eh kawai kiga aiki da cikawa, saina tona tun daga farko." Da sauri tace "dan Allah rufa min asiri nidai, kar kamin tonon silili." Dariya aka saka Khairat tace "yer uwa ashe dai gaskiya ya fad'a, to Allah ya raba lafiya baki d'ayanmu." * To nima nace ameen my lovely and lovely Khairiri* Allah ya saukeku lafiya Family Ahmad. Anan nazo qarshe yan uwa, duk da banso abin yazo a haka ba, amma dai nayi qoqari na qarasa muku shi, bansan ko zaku sake jina ba, amma dai ina muku fatan alkairi masoya. *Mamien Bk* *Momyn Sultan* *Momyn Khadija* *Auntyna Aisha* *Sis Alawiyya* *Yar mulki* *Bilqies* *KawaTa Hussy* *Munirah* *Wassia* *Ummu Faruk* *Aisha mahamane* Da sauransu ina miqa godiyta a gareku, ina alfahari daku. BISSALAM😘 Sameera Harouna.