Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JC8SzIjZ0S39mF7FMmBeWV *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *BOOK 1* *Wannan Labarin tundaga farkon sa har karshensa Tukwaici ne kuma Sadaukarwa ne zuwa ga HALIMA YUSUF GWARZO(Besty) Amincin Allah su tabbata a gareki Allahu ya iya miki Halima Allah ya jibanci Lamuranki Duniya da Lahira Ameen* _Da sunan Allah mai Rahma mai jinkai_ *Intelligent Writer's asso* *🅿️01* *GUMEL:Jigawa_Dutse* _Area:Zango Street_ Friday 5:30pm Ta jikin get din ta fara lekawa so take tagani ko da wani a Haraban gidan duk da tasan ba lalle ta samu gilmawar wani ba yau jumma"a kuma adaidai wannan Lokacin Duka mazan yara da manya suna masallaci inda Baba Mallam ke musu karatun yammah Matan kuma Kowacce tana cikin gida a irin wannan ranakun na Alhamis da jumma"a suke samun Damar Taimakama iyayen nasu Tunda Ranakun makaranta basa samun Lokaci da sun dawo makarantar Boko abinci kadai suke ci sai sallah da Haraman tafiya islamiya in suka dawo kuma Dare yayi sai Sallar mangariba sai zama yin karatun Tsakani mangariba da Isha"i,sannan in an gama sallar Isha"i kowa zai yi aikin makarantarsa,ko kuma wankin kayan makaranta ko Guga da Sauran aikin karfe 10na Dare kowa yake neman makwanci Saboda Kada a makara Sallar asuba da Shirin makaranta ba atashin mutum sau Biyu sau Daya na biyun kuma Da Duka ne zai sa ya tashi wannan Dokace ga Duk wanda yasan Daya Daga Cikin Dokokin gidan BABA MALLAM da BABA SA"IDU.! Hankalinta ta Dawo dashi tana kare ma anguwan nasu kallo Shuru ba wani Hayaniya ta Mutane yara duk suna gida Manya kuma suna wajen aikinsu Kofar wani masallaci take Hanga Daga inda take tsaye Fuska ta yamutsa ganin Takalma nan Birjit a kofar Hadadden masallacin mai kama da aljannar Duniya. Daman tasan yau Dole ne akwai karatun yammah shiyasa bata yarda ta Biyo ta gaban masallacin ba ta yanko Hanya duk da nisanta ta gwammace nisan da Haduwa da Zaluman dake cikin masallacin nan yau suyi bandashenta kamar yadda suka Saba.. Karamin tsuka taja tana gyara zaman Bakar Jakar bayan Dake makale a bayanta wacce ta Sagala Hannu Daya Hannun Daya kuma ta sakeshi. Yarinya ce wacce ashekaru akallah bazata gaza shekaru sha biyar aduniya ba Doguwace wankan Tarwada mai Dauke da wasu manyan Idanuwa da Doguwar Fuska,kallon Farko Zaka mata ayadda take Motsa baki zakasan tana da Surutu da Tsiwa Sanye take da kayan makaranta na Wando mai Ruwan kuka da Farar riga sai Farin Hijabi da Farin Dankwali kafarta Cikin Takalmin makaranta na Combas samfarin na mata da Safa. Akallon Farko in kayi mata zaka Fahimci yadda ta jigata,Tun daga yadda Fuskarta Duk ta Kode bakinta ya Bushe yadda kuma take tsaye bakin karamin get din gidansu mai kalan brown zakasan tana tantantaman Shiga gidan ne ko kuma tana Tsorom ta tarar da wani da bataso acikin gida. Ita Kadai taja tsaki kamar Tsaka afili ta Furta"Ni ba tsoron shiga gidan nake ba..Ni AMINA Aminene tsoron Uban wa zan ji..?kwakwazo ne bana so da Hayaniya uwa uba bana son Yaya ta fito ta ganni ita Kadai ce nake gujema Rigimata..! Tafada Lokaci Daya tana sosa giranta acikin Ranta tana Tunanin ko taje gidansu HANNE ne..? Da sauri tace"Kai bama zani ba..Saboda wannan uwar yar saka Idon Yaya Abida..! Tafada Lokaci daya tana Kallon Wani Makeken get din Daga gaba da Gidansu kadan wanda Jikin Gininsa Daya yake da wannan Kayattacen masallacin da na daga kaina naga ansakamai suna da wani Launin Fenti da larabci Cikin Sha"awa da Burgewa. *SHEIK YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA MOSQUE..* Sannan abun mamaki Gabadaya Daga gidan datake tsaye har wanda take kallo mai hade da masallacin Duka suna Layi dayane juna jikin juna Fenti Daya Komai iri haka get dim ma da kofofi kamar duka gidan gidan mutum Daya ne saboda babu abunda ya bambamtasu illah mai jikin masallaci yafi girma da kawatuwa Sabanin da wanda Amina ke Tsaye awajen yake karami sannan bai kai wanchan abubuwan More rayuwa Daga Ginin ba ammh bayanan komai da komai iri Dayane babu abunda ya bambamtasu. Tagama Tunanin bata da wata manufa yanzu banda tayi shahada ta kutsa kai cikin gida haka kuwa akayi Da karfin gwiwanta ta Tura kofar get din ta Shiga gidan maimakon na Hangi wanchan gidan sai na Fahimci Daga ciki katanga ta raba Tsakanin Gidajen. Mota Dayace aharaban gidan wata Siyana ce,Motar da ake kai su makaranta ce wani Lokacin in waccan babbar Macapoli din bata da lafiya ko kuma wani abu ya faru daman ko ABA bai cika Parking din motarsa anan ba yawanci yafi ijiyeta a haraban Gidan Baba mallam Saboda yawancin Saukarsa sai ya fara isa chan kafin ya iso anan Ko Yaya JA"AFAR bai cika ijiyar Mota anan ba Komai su sun saba gudanar dashi Bangaran Baba Malam din Daya zame musu tamkar wani bango abun Jigina da alhafarinsu. Wani kofa naga ta shiga mai Dauke da Dogon Koridin Dayaji Interlock ko"ina,Sannan yana Dauke da Dakuna Hudu ajere suna Kulle da Kofofi Daga gani Dakuna ne na mazan gidan ko baki indan hakan ta kama, Kafin inga ta kara ganin wata Kofa Da karfin gwiwanta ta Tura kofar ta shiga sallamar ma acikinta tayi ta Ba kowa a tsakar gidan nasu wanda ba mai Fadi bane Sosai Daga gefenta kuma Ta hangi HAMIDA tana Gaban Famfo botiki ne a Gabanta tana wanke Kayan makarantar. Dagachan yammh kuma Kitchen ne Babba Daga ganin yanayinsa zaka Fahimci haka sai daga chan Hannun Hagunta kuma Tiolet ne guda Hudu na Waje Biyu na Wanka Biyu na Lalura sannan Daga gabas dinta kuma Jerin Dakuna ne Guda Hudu,Daya yana nesa da ukun wanda ke Rufe Dakin Aba kenan mai Dauke da Ciki da Falo,Sai Dayan kuma Katon Dakin su ne mai Dauke da Falo kadai ammh babba ne Tun zamanin su Yaya Jalila adakin kowa ke cin yayinsa kafin Aure ya Dagasu har zuwa yanzu da suma suka taso suna cin nasu Lokaci. Sannan Daki na gaba kuma Dakin MAMANMU CE mai Dauke da Ciki da Falo da bayi sai Dakin kurya kuma Dakin YAYA ce shima kamar na Mamanmu haka yake Daga bakin Dakunan anyi Rumfa Babba wanda ya bada inuwa sosai Daga gaban Rufar kuma akwai katuwar Bishiyar Umbroller Ko"ina agidan yana Tsabtacene duk da Interlock ne aduka Tsakar gidan ammh bai hana ka gansa kal ba ta tabbata Hamida tayi aikinta kenan Saura ita Daga chan kuma wajen bayika igiyace Doguwa Cike da Shanyan irin kayan makarantar Dake Jikinta. Cikin Lokaci kadan tagama Nazarin Tsakar gidan ajiyar rai ta sauke Yaya bata Tsakar gida tana Dakinta bari ta Lallaba ta shige Dakinsu ta Sauke gajiyarta kafin ta fara amsan Korafin da kwakwason yan gidan nan akanta da Kullim baya karewa kara Hade ranta Tayi saboda bataso wani ya mata mgana ma ayanayin Datake ciki. Ita Zainab isa zata rainama Hankali..?tasan ta bata shiri da makaryaci mara Cika alkawarin Bata da Mutumcin in aka Shiga harkanta Tasan bata da kudi Ranar ita yau a makaranta ta ari kudin Break dinta..?ranar haka ta Dawo makaranta ko Biyar bata kashe ba Tana ganin Hamida na kashe kudinta itama ko oho haka take duk da karancin Shekarunta bataso ka Roketa abunda take dashi bata baka ba Zainab isa kudin Mashin dinsu na Ranar da zasu koma gida aka Sace acikin aji,ita da kannenta suke zuwa makarantar wata Unity school dake Cikin gari ne taji Tsausayinta yasa ta ara mata kudin Hannunta naira Hamsin ta Hada dana Hannunta da Niyyar Ranar jumma"a zata kawo mata kudinta,Amina tana girmama alkawari mai Saba shi kuma bata shiri dashi yau Zainab isa batazo makaranta ba ita kuma ana tashi Tana ganin Direban su Mallam Idi yazo Daukansu ta Boye tana ganinsu Hamida da jawaad suna ta Nemanta Ya Shamsu nata Muzarai ta Sulale tayi amfani da kudin Breakdinta da bata kashe ba ta hau mashin taje gidan su Zainab isa ai tasan gidan Saboda sun Taba zuwa gaisheta ida yan ajinsu Lokacin data kone da ruwan zafi. Sai dai kash tana zuwa ta iske gidansu a kulle wani yaro ta hadu dashi nan waje shi yake fadamata Zainab basa nan sun tafi garinsu Zaria yau da Safe. Ranta ya baci ta Cizi yatsa ta kudira aranta sai ta Gumdumama Zainab rashin Mutumci bata da ko asi ahannunta yasa ta tako a kafarta Tunda anguwan su Zainab Hadeja Road har anguwansu Zango Street. Ga yunwa ga kishi ga ba sallah ba Salati iya wannan kadai ya isheta batason kuma adameta da wata mgana. Ko barayin da Hamida take bata kallah ba Duk da tun shigowarta ta Saki abunda take yi ta mike tana kallonta Cikin mamakin karfin Halin Amina. Sai da taga ta wuceta zata shiga Dakinsu yasa tace"Ke kam Amina ina kikaje an tashi makaranta muna ta nemanki bamu ganki ba..?Anya Amina baki gudun mgana kullum Aba da Yaya mgana suke akanki naga hakan ma kara miki Dadi yake yi..? Amina tana jinta bataso ta waigo ba, Saboda bazata mata kyau ba Daga ita har Hamidan Tsakaninta da ita Wata Uku Cur..Kamar bata girmeta ba in Na samanta sun mata mgana ta Ragamusu Hamidan bata isa ba Ganin in ta tsaya tankata zata kara bata Lokaci yasa ta kara Sauri ta saka Hannu kenan ta Daga Labulen Dakinsu Taji Hamidan na Fadin"Tukunna ma ina kike je..? Ranta ya kara baci ga gajiya ga yunwa ga kuma wani banzan kallon da Ya Zulaihat da ya Zeenatu Dake Cikin Dakin kowacce kan gadonta na katako kamar na yan bording suke jifanta Dashi ta kasa gaba ta kasa baya. Kamar Daga sama taji Ya Zulaihat na Fadin"Shigo ki fadamana Gidan Uban wa kike je bayan an tashi makaranta..!? Bata gama Rufe baki ba Yaya Zeenatu ta Dauka da Fadin"Kema kinsan bazata taba fada ba wannan mai Taurin kan tsiya..Duka ne kadai yaran data sani kuma yau sai kin Daku..Domin ba Dadewa Ya Jafar yazo ya Tambaye ki muka Fadamai gaskiya shida Ya Nasir suka shigo kuma yadda suka Fita yau in s suka kama Dukanki sai na Lahira yafi ki jin Dadin Sakarya mara Tunani..! Ta karishe Fada tana Hararanta kafin ta saki tsaki ta Cigaba da Duba Littafin Turancin dake gabanta Fuskarta Kaf irin na Hamida ne sai dai Amina tafi su haske ammh har Zulaihat din suna kama ta jini ita Amina manyan Ido ta Fisu da rashin jiki. Har Duhu Amina take gani Saboda yunwa da gajiya ga bacin rai bataso ta shiga Cikin Dakin suna Cigaba da yaba mata mgana tasan sai ta tankasu kuma basu da imani Taruwa zasu yi suce zasu Daketa tasan bmai Centonta sai Mamanmu in ta Yaya ne su kasheta ita kuma bata iya Shuru da bakinta wanda ya fadamata goma sai ta Fadamai ashirin. Shawaran canza Daki tayi da Niyar Shigewa Dakin Mamanmu ta Saki Labulan Dakinsu tana Fadin"Duka ai baya kisa..Dayana kisa da ko Burbushin Amina ba"a samu ba..Kuma ni ba Sakarya bace Ehe..! Tafada tana kunkuni Zulaihat Dake Dakin tace"Eh me kike cewa ne..? Zeenatu Wlh Zaginki tayi..! Tafada Cikin takaichin yadda Amina take so ta zame musu ciwon kai acikin gidan ko Aba bata ce Amina na jin tsoronsa ba. Zenatu tayi Falati da Zanen datakeyi wanda Bilogy teacher dinsu ya basu Doguwar rigace ajikinta ta Fice tana Fadin"ki barta bakinta zan fasa wlh..Zatasan wa take ma rashin kunya..! Tana daga kwancen tace"Uhm..Ki Dirji bakin gudun Reni ammh nasan ko kin gama bakin Amina bazai taba mutuwa ba..! Tafada Lokaci daya tana girgiza kai aranta take fadin Allah ya shirya Amina Zeenatu ta fito Daga Dakin Daidai Lokacin da Hamida take fadin"Mgana fa nakeyi Amina..?gwara ki fara fadamin Inda kika Tsaya na samu yadda zan kare ki agaban Ya jafafar yau.! Azafafe Amina ta Dago Daga Nufar Dakin Mamanmu datayi niyya Jakarta ta Sauke Saboda Jidalin Dake kanta bazata iyasa da wannan nauyin ba,Manyan idanuwanta ta Sauke kan Hamida tana Fadin"Hamida...Hamida..Hamida Sau nawa na kiraki..? Hamida na yar dariya tace"Kamar sau uku..! Amina ta tareta da"ba kama bace..Sau uku na kiraki saboda ki gane girman Warning din da zan miki..Hamida ki Fita Daga Rayuwata Wlh..Ina ruwanki da inda naje inace ke bagaki kin Dawo gidan ba..!da kike fadin ki kareni gaban ya Jafar na sakaki ne..?ke kika saka kanki kina kokarin kare abunda bazai taba karuwa ba Hamida Ni Amina wake sona..?Aba kullum Amina mai Laifin ce awajensa Hakama Yaya kowa baya fadamin abun Alheri akaina Daga Mamanmu sai Baba Mallan ke sona..Sai Hajiya Baba da Hanneta bandasu fadamin me yabon Amina..?kinga kuwa ko Icce aka sakama baki haka Lalacewa yake yi ballatana Mutum kamar ni to bari kiji na Fadamiki ni AMINA SA"IDU GUSAU kainuwa ce dashen Allah baki ko Duka baisa yaga karshena ba, ballatana ganin baya na saboda haka ki adana kalaman bakin ki kuma Rufemin Dattin bakin ki in kuma ba Haka ba ki jirani na ci na koshi in Jidali kike nema na Rantse da wanda Raina ke hannunsa kin Tare ni kin sam.u..! Tafada Lokaci Daya tana Girgiza kugunta kamar wacce take Shirin Dambe,Zeenatu Data fito tsayawa tayi tana kallonta Hamida kuwa cigaba da wankinta tayi tana Fadin"Allah baki Hakuri..Kya yi bayani in kika shiga Hannun Ya Jafar..! Wani Tsaki taja kafin ta Duka tana Daukan Jakar makarantar tana Fadin"In yazo kada ya bar Amina da Rai..Yau aka saba ko yau za"a kareta Hamida..?da duka na kisa da yanzu Amina ta Dade a kushe..! Dauummmm...! Taji Saukar Dunkullen Dumdu abayanta kafin ta karisa mganarta Dumdum dayasa sai da ta Duke kasa kan Jakarta tana bankare baya saboda taji Saukan Dumdum a bazata. Zeenatu tace"Yauwa Yaya..Don Allah Daketa bari na karyo Iccen Bishiyar Nan ki Daketa da ita tunda tace Duka baya mata komai..! Tafada tana Nufar Bishiyan Dake Haraban wajen ai ko ba"a Fada ba,Tasan Hannu Dayake ke da wannan Dumdum ba tun yau ba Tun tasowarta bata iya Haddace dukan kowa ba, da an Dageta taji zafi ya Huce shikenan ta manta ammh Duka Daya Duka Daya daga Hannu Dayane bazata taba manta yanayin ba bata Cika Duka ba mai Hakuri ce sai dai In ta saka hannu ta Duma maka Dukanta Har Ka kwana bazaka manta dashi ba Hannu Dayane mai kama da goma YAYA CE..ita kadai ce Amina bata saba da Dukanta ba kuma Dukanta ne kadai ke saka Fitar Hawaye a Duka Idanuwanta Aba bai duka sai dai Fada Ko su Ya jafar sai dai su gaji su kyaleta zatayi ihu ammh in ka Duba ba Fitar Hawaye ko Daya Amina akwai Taurin rai da kafiya kamar kafuran Farko..! Dagowa tayi Idanuwanta na Cikowa da Hawaye ta Sauke kan Fuskar Yaya kamar an Tsaga kara yadda kukasan yan Biyu sai dai bambamcin Amina yarinya ce Yaya kuma Shekarun sunja akallah 49 aduniya ammh Hatta Shape din Fuskarsu iri Daya ne tafi Amina Haske sosai ita din Fara ce ammh ba Tar ba. Cikim bacin rai take kallon Amina rai Daya..Rai kwara Daya da Tunda ta Haifeta bata Huta ba Amina..Amina ta Addabi kowa acikin gida da waje ba inda ta bari ita kadai take so ta jazamusi hawan jini da Ciwon zuciya ita kadai TA FITA ZAKKA..cikin Ya"ya goma sha Biyu Dake gidan kowa ya gama lafiya banda Amina kowa Amina tagaji takai makura ga kauda kanta kan Lamarin Amina. Tana Kitchen Sanda Amina ta shigo Taje Duba Wani mganin Ciwon Ciki ne Ararrabi Data ijiye Cikinta ke Juyamata take so tasha..Tun Sanda yaran suka Dawo suna Fadin basu ga Amina ba takasa mgana to me zatace...?wannan ai ba karon Farko bane da Amina tataba batan Dabo a makaramta ba,akwai Lokacin da har an baza Cigiya agidan Radio sai gata ta Dawo wai taje Birthday din yar a Jinsu kaninta ake ma Birthday Bakimciki yasa Aba dinsu ya kamata yayi mata Duka ammh baisa ta Daina ba Amina kanta Tsaye take aikata Duk Abunda taga Dama,a kananun SheKarunta Duka ya Zame mata sabo eh mana Gaskiya ta fada Da Duka na Kisa da an kasheta ita kam Tin tana Daukan Amina aljanu gareta har ta yarda ma kanta Lafiyanta Kalau Amina Zakka take so ta zame musu Cikin gidan nan da Zuru"a gabadaya. Koda ta Haifesu kaf ya"yanta Ba ita take Renansu ba BALARABA ce Mammansu banda Jafar duka ya"yanta ita take Renonsu ta yayesu in ba Fadamaka akayi ba bazaka Taba Cewa Yaya ta Haihu ba Duka yaran Gidan komai nasu Mamanmu Mamanmu Kowa mamammu In kaji Yaya sai in Mamanmu ta sakota Cikin Shirginsu komai na Tarbiyan yaran da komai na Rayuwarsu na Hannunta ne sai In ma ta musu wani abun take sani Daga baya ba ita kadai kaf Dangin Sa"idu suna girmama Balaraba Kuma sun saka mata suna ita mai karamci ce Taci wannan sunan Domin ita Maman kowa ce. Bazata kyale Amina ta zautataba kullum Kokenta kan kare ma Amina ne,Mganar Rauninta kan Amina ne Koda yaushe Cikin nema mata Taimako take gani take Aminar ba ita kadai bace kullum kalamanta kenan "Yaya ku daina Ganin Laifin Amina..Adaina Dukar min Ya'a yaya ba Laifinta bane.. ku lura kamar Amina ba ita kadai bane ni dai ina Zargin Aljanu suka taba Amina Tun tana ciki..Yaya bazan taba barci ba sai naga Amina ta dawo kamar kowacce y'a acikin gidan da watarana Zaku yi alfahari da ita..! Lokacin datake Fadar haka kukane acikin Ranta da Zuciyarta tasha kuka Har da majina kan Amina in ana Dukanta haka zata zo ta tare har ana Samunta tana Fadin"Jafar ka bari..Kada ka sake taba ta nace..! "Mamanmu ki barni..Ki bari na Illata wannan rayuwar kafin ta kashe mana Uba da Bakaken Hallayarta..! Rike Amina take ajikinta ta Fashe da kuka tana Fadin"To in bazaka bari ba sai dai ka Hadamu duka ka Dakemu..Ammh bazan bari ku illatamin yata ba..! Ita ta Haifi Amina ammh wannan Raunin Maman Amina ke Daukansa bata Cika maida kai kan lamarin Amimar ba Tunda bata wata shakuwa Tsakaninsu,ammh yau taji tana so ta Nuna ma Amima ta bar wasu Zukata su Huta ta Duba Raunin Mamarta akanta ko Saboda ita ta sauya wannan Bakin Halin nata. Kallon Datake mata Da kuma Tuna wasu abubuwan yasa Hawaye suka Cika kwarmim idonta. Amina na Dafe da baya ta Bude tace"Yaya..ki ts Bata kai ayaba Yaya ta kaimata mari wannan karon ya Sameta da Karfi Har sai da ya fito da Zulaihat Daga Daki da Gudu Hamida ma ta bar wankin da Sauri ta karisa tana Fadin"Yaya kiyi hakuri..! Har Zeenatu Dataje Karyo Icce sai gata ta dawo Wlh bada gaske take ba Bata Dauka Yaya zatayi Duka ba,Duk da Rashin jin Amina yarinyace mai Shiga rai sannan Kaunar junansu ajininsu yake koyaya wni abu ya samu Daya Dukkansu sai sun ji wani iri. Amina na musu rashin kunya kunkuni da Sauransu suna zugawa in za"a Daketa ammh akazo ana Dukanta sun Rika bada Hakuri kenan Hamida mai Saurin kuka Harda kuka take sai an gama Dukan tazo tana Daga Aminan sai ta Kalleta tayi Dariyan dauriya da yaki da Abunda take ji tace"Wai Kuka kike Hamida..?kuka fa..Kima Daina kuka Amina ce Aminene ce badai mutum ba sai ta Allah..! Hamida na sharan kwallah takan Dungure mata kai tana Fadin"To kidaina wasu abubuwan don Allah Amina..Ba domin kowa ba domin Aba da kuma yadda muka zama Zuru"ar gidan bazanga..! Amina alokacin sai dai ta kalleta tana Fadin"A"ah fa..Ni bansan laifin da ake yawan Fadin Amina nayi ba. abunda dai nasani shine Amina..AMINA SA"IDU Haka Allah yayita..Ko ta Sauya shi Hali ai zanen Dutse komai zai Sauya da Mutum banda Halinsa..! Yaya ce ta katse ma Hamida Tunaninta Cikin Fitan Bacin rai da wani bakinciki Yaya ta Rufe Amina da Duka kota ko"ina tana Fadin AMINA Yanzu abunda kika Zabama rayuwarki kenan..?So kike kamar yadda kika saka ma ABA dinku Hawan jini nima ki sakamin ko..?Gidan Uban wa kika je bayan an tashi makaranta..?Duka Sauran yan"uwanki sun gaji da nemanki sun dawo..Saboda ke kin FITA ZAKKA agidan nan sai abunda kika dama kike yi ko Amina..?Bin Maza kika fara..?Nace bin Maza kika fara..?Wlh ina Tsausayinki Ranar da Bakinciki zai kai Alhaji kasa Nima kin Sakani kuka ba sau daya ba sau Biyu ba, Amina ki kashemu ki Huta nace ki kashe mu ki huta..! Amina bakinta bai yi Shuru ba Fadi take"Ni bana bin maza..Wlh Allah Amina bata bin maza ki yarda dani Yaya..! Take fada tana Tsiyayan Hawaye,Hawayen da Dukan Yaya ne kadai da kalamanta kan saka aga Fitarsu daga Idanuwan Amina. Bakinta ta Bike sai da ya fashe cikin Takaoci tace"Kina Kara batamin rai in ina mgana kina mgana..Amina Bakin ki na Daya Daga Cikin Nakasunki bakin ki baya iya mutuwa koda girman Laifinki yafi girman Duniya ne..! Amina ta sharce jinin bakinta tana Fadin"Yi hakuri Yaya..! Haka kawai take fada tana kuka sosai abu Daya yafi Tsaya mata arai Cewar da yaya tayi tana bin maza tasan Tana da kafar yawo da Bin Gidajen kawaye gayyar ko ba"a gayyaceta ba Amina sai taje tasan tana da rashin kunya da Kafiya da Taurin kai da Tsokana tasan bata da Kirki wani Lokaci ammh Wlh maza basa gabanta Tsakaninta dasu sai goge reni Domin har ayanzu Amina bata jin kunyar zagewa ta Chasa wanda yayi mata shiyasa kaf ajinsu na Boko da islamiya suke shakkarta bata Duba Jinsu ita wanda yace mata kole ne zatace mai cas ammh bata bin maza ita ba yar iska bace! Gabadaya jikinsu Hamida yayi sanyi Amina na kuka tana Fadin"Kiyi hakuri yaya..! Ita uwa Dabam take acikin Ranta tanajin kamar Amina ta koma Ruwan sanyi da Yaya zata Daina damuwa akanta Mamanmu zata Daina kuka akamta ammh ko ta Dauki alwashin abanza da ta gama Damuwarta za taji kamar kara mata wasu abubuwan akeyi wani Lokacin ita kanta Har mamakin irin Taurin zuciyarta take ko na wani kato albarka. Dukkansu Hakuri suke bama Yaya batace komai sai kwallah Data ke sharewa Zeenatu ne ta Ruga Dakin Mamanmu ta taso ta wacce take kurya tadan kwanta Sama Sama taji Zeenatu na Fadin"Mamanmu..Mamanmu..! Bude ido tayi tana Fadin"Zennatu meyasa kika tasheni..?nasan barcin yammah bai da dakyau..Kaina ke Saramin..! Da sauri Zeenatu tace"Daman nasan baki ji ba.Yaya yau ranta ya baci gashi chan tana kuka tana Dukan Amina..! Ai bata gama ba ta ingize Zeenatu ta Diro Daga kan gado Dankwali a Hannunta Zaninta na neman Faduwa ta Fice da gudu Zeenatu ta Bita da kallo ta Girgiza kai. Tana fitowa ta isa ga Amina ta Rumgumeta tana ganinta ta riketa tana kuka take fadin"Mamanmu don Allah ki fadama Yaya bana bin maza Wlh ban bi maza gidan su yar Ajinmu naje Zainab isa kudina naje amsowa na iske sun yi tafiya ba kudi a hannunsa saina tako akafa mamanmu ammh kiji fa abunda yaya ke..! Bata karisa ba ta Rufe mata baki Cikin Rauni tace"Basai kin fada ba..Nasanki Amineene..bazaki fara Halin da bana ki ba.. Share Hawayen Daina kuka matukar mamanki na Raye baki ba hawaye har Abada..! Tafada tana share mata kwallah Cikin kauna Yaya kada kai tayi ta bi hanyar Dakinta tana Fadin"ki Rika samun waje acikin ranki kina fadama Amina gaskiya..Ko tana so ko bata so Ta fita zakka acikin gidan nan..! Daga haka ta bankade labule ta shige Dakinta Mamanmu bata Damu ba mikewa tayi tana Dago Aminan Lokaci Daya tana Fadin"Hamida Dauki Jakar Amina ki kaimata Wajen Dirowarta..Ke Zeena zubo mata abincinta a filet ki hado mata da Ruwa da Zobo yanzu adakina..! Zulaihat dake gabanta ta kallah kafin tace"Matsa ki bani waje..! Zulaihat ta kalleta kafin tace"Mamanmu..! Rai bace ta balla mata Harara tana Fadin"Ki yi wanke wanke..Gobe Aminan tayi..ku kuma kuyi abunda na sakaku..! Daga haka ta shige Dakinta Dauke da Amina Dake kuka kamar ta maidata Ciki Hamida ta ja Jakar makarantar Amina zuwa Dakinsu Dirowansu kusa da juna ne Domin gadon su ma ahade yake ita tana Sama ne Amina na kasa saman gadonta ta ijiye mata ta Fice ta koma bakin Famfom ta Cigaba da wankinta ita kuma Zeenatu ta shiga Kitchen ta Bude Cooler ta Dibo Taliyar da Kifin Dake ciki ta Bude Fridge ta Dauko Ruwa da Zobo ta Fito zuwa Dakin Mamanmu. Ita kuma Zulaihat ranta bace ta Fara Fito da kwanukan da aka bata akichen Zuwa bakin Famfo. Hamida Dake Dauraye kayanta Tace"ki barshi Anty Zulaihat in na gama shanya zan wanke! Kai tsaye tace"Yauwa.Daman duk Ranar da Amina ta kwaso jidalinta yafi Shafarki..! Daga haka ta wuce Bata bi takan Hamidan Dake Dariya ba tana Fadin"Amina ce Anty Zulai..Wlh ko Aba baya iyawa da jidalinta ko Ya Jafar gajiya yake..! Take fada tana Dariya shanyan kayanta tayi tazo ta fara Jika kwanukan sai ga Amina ta fito Daga dakin mamanmu kallonta tayi itama ta kalleta kai tsaye tace"Gobe da Safe har zuwa rana zan yi wanke wanke..Zan rama miki kada kice kin Dauki Jidalin Amina..! Tafada tana Share bakinta Daya kumbura Hamida kai kawai ta kada Amina ce sai tayi mgana. Ta fara wanke wanke sai gata tafito jikinta Riga ce doguwa na Atamfa sai Hular Dake kanta Kayan makarantarta ne ke Hannun ta Zata wanke saboda gobe Asabar suna Hadda Tun Safe sai yammah,haddar tasu daya take da islamiyan shiyasa ana tashi Uku da Rabi ayi sallah aci abinci a shiga islamiya itama Madaratul Umar Bin kallab din mallakin Baba mallam ce snnan gabadaya malaman makarantar ya"yansa ne da Dalibansa har ya jafar yana koyawar ajin manya Wato Jss1 da ajin matan aure ya Nasir da ya Uzairu da ya Nazim Duka suna koyarwa anan,Sai dai yanzu Ya Nazim da ya Uzairu suna Makarantar jami"a sai sun dawo Hutu suke zuwa Yaya shamsu ne shima Dukka da kananun shekarunsu Kansa na ja yayi Sauka da Hadda ga Sauran Littafai kai duk ya"yan mallam haka suke akwai kwanya kuma ance duk Kwanyarsu basu kai Babban DA'N MALAM ba dake jami"ar madina yana koyawar chan yake zaune da iyalansa sai karshen shekara suke zuwa gida sai dai Sakonsa akai akai yana zuwa ga mahaifansa. Har ta fara wankinta ta gama bata cema Hamida komai ba itama batace mata ba Tana idar wa kenan tana Shanya Sallamarsu Ya Jafar da da Ya Nasir ta karade gidan da Sauri Amina ta juya tana kallonsu Fes suka Hada ido hudu da Ya Jafar wata uwar Harara ya Zuba mata yana fadin"Gama Shanya..Ki Tsaya a inda kike ki kama kunninki..! Nasir Dake gefensa yace"in kin gama kama kunnin ki hada da Tsallon Kwado..Yau zaki gane iskancinki kadan ne Amina..! Daga haka suka wuce lokacin suna amsa gaisuwan Hamida Jawaad dake bayansu ta kallah yana mata Gwalo yaro dan shekaru goma.! Amina Rai ta bata a fili ta Furta.."Azzalumai Biyu kenan..Allah ya Hadasu abota kamar yadda Muguntarsu tazo Daya..! Hamida ta kallah wacce ta zuba mata ido Hararanta tayi da karfi Tana Fadin"Bana son gulma Hamida..! Kanta ta kauda tana Dariya gama Shanyar tayi ta koma bakin kofar gida ta Coge taki yin abunda akace sai taji motsi sai ta yi kamar ta Duka ta kama kunni sai taga basu bane sai ta Mike Dakin yaya suka fara shiga. Tana chan tana Hararan Hamida suka Fito Da sauri ta Duka ta Daga hannunta Sama Jafar ya kalleta Cikin wani yanayi kafin yace"Kada kiyi..Kiga yadda zan yi dake agidan nan..! Nasir kuwa wayarsa yake latsawa hannanunsa Daya Dauke da Littafan Karatu na addini Dakin mamanmu sukayi sallama suka shige Amina ta bisu da Harara afili ta Furta"Duka ai baya kisa..! *Janafty* *15/07/2022* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *SADAUKARWA:ga Halima yusuf gwarzo (Besty) Alherin Allah ya kai miki a dukkan inda kike* _Wannan Labarin Jinjina ce gareki *SUMAIYYA ABDULKADIR TAKORI*(Takorinmu) Allah ya raya miki zuru"a ya tabbatar da aminci da zaman Lafiya agidan auranki_ *🅿️02* Hamida na wanke wankenta Ammh Rabin Hankalinta na kan Amina ganin yadda ta koma ta zauna Dirshan a kasa Tana wani cin mgani kamar babu abunda ma ya Dameta yadda take zaune kamar tana zaune acikin Daki ne cikin Natsuwarta. Abu daya ke bama Hamida mamaki bama ita ba kowa da kowa Dake gidan nan yana mamakin yadda Amina bata jin tsoron Ya Jafar da Ya Nasir wadanda kaf gidajen sune manya kuma su ke hukunci da kuma Daidatuwar Tarbiyansu bama su ba na Sama dasu su ya Zeena suna Tsoronsu da basu girmansu banda Amina Har yau har gobe bata taba ganin Wannan Tsoron da Shakkarta acikin Idanuwanta ba. Tagama wanke wanken kenan taji an fara kiran sallah Daga masallacin gidan Mallam Daidai da fitowar Zeena Daga Dakinsu kanta ba Dankwali sai akayi rashin Sa"a Lokacin Ya Jafar da Ya Nasir suka fito Daga Dakin Mamanmu tana Biye dasu abaya. Bata da yadda zatayi sun riga sun ganta Ya Jafar ya Duka yana Saka Takalminsa mai igiya Hamida Ta kalli Amina Dake zaunenta tace cikin Rada..'Ke Amina ga su nan fa sun fito..! Daga ido tayi ta kallesu kafin ta mike Tsugunne ta daga hannunta sama kamar gaske. Ya Nasir ne ya kalli Zeena Dake kokarin komawa Daki Cikin Muryansa mai Cike da Iko yace"Wacece nan take yawo ba Dankwali..? Ba yadda Zeena zatayi Dole ta juyo tana Fadin"Nice ina yini Ya Nasir..! Harara yayi mata kafin yace"Dillah wuce ki saka Dankwalin ki..Kuna manya kuda su Hamida zasu yi ku musu Fada..! Bata ko kara mgana ba ta shigo Dakinsu Daman Dakin Mamanmu zata shiga ta Dauko littafinta jiya ta manta Dashi,bata zata har alokacin basu tafi ba Shiyasa ta fito haka. Tana Shiga Dakin Zulaihat data mike Tana Tatattara Littafanta tace"Kema kin samu Rabonki kenan..! Zeena bata iya mgana ba Umh kawai tace ta Dauki Damkwalin Abaya ta saka lokaci Daya tana Tura kofar Bandakin Dake Daknsu ta shige Tare da Rufowa Zulaihat ta Bita da kallo Lokaci Daya. Achan waje kuma Nasir ne ya kalli Hamida yana Fadin"wai sau nawa zan ce kudaina zama bakin Famfo nan da mangariba..?baku gujema Lafiyarku ko .? Kanta na kasa tace"Ai nama gama yanzu zan tashi ina wanke wajen ne..! Mamanmu ta kalleta tana Fadin"Wato Zulaihat ke ta bar ma aikin kenan..?gobe kuwa sai tayi shi..! Tafada Daidai Lokacin Data hango Amina da Sauri tace"Amina wa ya sakaki kama kunni da mangariban nan...? Jafar kai tsaye yace"Nine mamanmu..Zata fadamin inda ta Biya bayan an tashe su daga makaranta..! Mamanmu ta Bude baki zatayi mgana ya Rigata da Fadin"Don Allah Mamanmu kada ki saka baki..Bazan Daketa ba in har ta bani amsar Tambayana..! Mamanmu tace"Kada ku maida Amina Jaka mana..Jikinta fa ya Saba Da dukanku..! Bai Saurareta ba ya Nufi Aminar Nasir ne ya tsaya yana Fadin"Wake ja Mamanmu..?yarinya Daya Tal zata zame ma kowa ciwon kai..! Mamanmu tace"Sai addu"a..nidai kada ku tabamin D'iya..Nasan ku da Duka kamar kun Hada kauna..! Yana jinta yar Dariya kawai yayi Hamida kam data gama kwashe komai ta maida Kitchen Dakin Yaya ta shige ta sameta Har ta Kabbarta Sallah Cikin kurya ta shige ta samu Jawaad na saka Jallabiya da Sauri yana Fadin"Ya Hamida Don Allah su Ya jafar na nan..? Hararansa tayi kafin tace"Bansani ba..Sai ka fita kagani..! Dariya yake yi kafin ya Fice ta bishi da kwafa tana Fadin"Zaka Dawo zakasan wanda kake ma Dariya..! Daga haka ta shige Tiolet din Dake Cikin kuryan Dakin na Yaya. Jafar gaban Amina ya Tsaya yana kallonta kamar yadda itama take kallonsa abun na bashi mamaki ba kowa ke iya Hada ido dashi ba Saboda kwarjininsa da yadda kannensa ke tsoronsa  ko Jadwa Datake Daga shi sai ita bai jin tana kallonso ido Cikin Ido. Kai Tsaye Cikin Kakkausar Muryansa yace"Da aka tashe ku makaranta ina kika Tsaya..?ko nace ina kikaje..? Amina kai tsaye tace"Gidan yar ajinmu Zainab isa..! Da mamaki yace"Yaya ta aikeki ko mamanmu..?ko Aba..? Itama Cikin dan mamakin ta Waro Idanuwanta kafin tace"Kudina naje amsowa..! Tafada tana Dan Tura baki Hannu yasa ba tsammani ya bige bakin yana Fadin"Watarana sai na rabaki da Hakoranki na gaba..! Nasir Dake bayansa yace"An fa Tada sallah Jafar..! Jin haka yasa ya ja kunnenta Har sai da tayi kara Cikin Fada yace"Kije kiyi sallah ki jirani kafin na wuce zan dawo ban yarda da mganarki ba..! Sannan ya saketa gefe ta koma tana Sosa kunnenta Nasir ma sai da ya bata Rankwashi mai Zafi sannan suka Fice Sai ga Jawaad ya Fito ya Bisu abaya da Gudu yana ma Amina gwalo,Tana Dafe da kanta Dataji zafin har Tsakar kanta tace"Yaro in na kama ka sai na Lahira yafi  ka jin Dadi..Na fika Jidali da Fitina..! Tafada kafin ta mike tana Kakkabe Jikinta nan bakin famfon ta karisa ta Bude ta fara alwala sai da ta gama kana ta shige Dakin Mamanmu ta isketa kan Darduma tana Lazimi..! Kai Tsaye Amina ta wuce uwar Dakinta tana Fadin"Mamanmu na Dauki Hijabinki Cikin Wardrope dinki..nawa suna Dakinmu kuma bana son shiga..! Tafada Muryanta Cikin yar shagwaba Tana Daga zaunen kan Darduma ta Daga mata kai Ciki ta shige ta Bude makeken Wardrope din ta Bude barayin Gogaggun Hijaban Mamanmu ta Dauko guda Daya ta fito tana zuwa Mamanmu ta matsa gefen Darduman Datayi sallar duk da Shinfidadden Cafet din italiyan din Daya malalen Falon Tana cikin Sallar mamanmu ta Fice kuma Tana da tabbacin Dakin Yaya zataje domin duk bayan mgariba da isha"i adakin take yinsa suna Hira da Tattauna wasu abubuwa Kamar ba Kishiyoyi ba.. Tana Idar da Sallar ko dan addu"a bata Tsaya yi ba ta mike Zaraf kamar an tsunguleta mganar Ya Jafar take Tunawa Dayace zai dawo duk da tasan da Wahala ya dawo yau sai gobe saboda akwai wa"azin da Baba mallam ke yi kowani bayan Sallar mangriba zuwa Isha"i sannan in an gama zasu Rufe da Sallar Isha"i kuma Tana da Tabbacin Aba ma ya dawo suna masallacin Tare in ma sun fito daga waje zasu gaisa ya wuce gidansa ina ma wannan mayyar matar tasa zata barsa ita Har mamakinta take yadda take mutuwar son Ya Jafar ko ina abun so a wajen wanda ya maida mugunta Dabi"arsa. Baki ta Tabe bata tsaya Cire Hijabin Jikinta ba ta Fice Takalmin mamanmu na Yawom Tsakar gida ta Zura ya ma mata yawa sosai karamar kafarta ta Zurma aciki batason shiga Dakin su ne Saboda hamida tasan su Ya zeenatu ba lalle su bi ta kanta ba ammu Hamida gani taake tafi kowa Shigar mata Hanci da Dunkunkune in ta koma Dakin Hamida tayi mgana sai ta tankata kuma Hakan kamar wani Lasisi ne ta siyo ma kanta Fada Wajen Aba Shiyasa ta zabi Tafiya gidansu Hanna tayi zamanta sai Dare yayi Lokacin Hamidan ta kwanta sai ta Dawo. Batare data Fadama kowa ba,kamar yadda ta Saba yin komai gaban kanta ta saka kai ta fice Daga gidan kuma Har ta fice bata Hadu da kowa ba,Awajen ma ba kowa Saboda an shiga masallaci Wajen yayi Haske Saboda an kunna Generator massllaci ba wuta suma ana Dawowa sallah su Ya shamsu zasu tada na cikin gidan Mallam babba ne mai bama Duka gidan da gidansu wuta taji dai ana ta Fada D'an malam Dake madina ya aiko da kudi aka siya har ma gyaran gidajen da aka sabunta musu wattanin baya duk shi yake turo ma dasu Ya Jafar kudi su kuma suna aiwatar da umarninsa. Tasamu nasaran shiga gidan kanta Tsaye saboda Buba megadi shima yana masallaci wannan Dokar Baba Malam ne,ba hujja kana jin ana Kiran Sallah ka fake da wani aiki ya zama Dole kowa ya bar komai ya tafi kiran Allah Gidan Baba Malam ya wuce yadda zan kwakwatanta muku Babban gida ne mai Dauke da Haraba mai girma Dauke da Motoci guda biyar hudu suna Bayyane Daya kuma an Lullubeta da Tamfol Tadade ahaka in ba mai mallakin Motan ya Diro garin ba bamai da ikon hawanta Duk da bai Saka Dokar haka ba,Sai Dayar bakar prado din ta mallam ce in fita ta kamasa Dayar 306 iri daya guda Biyu Daya ta Ya Jafar ce Daya ta Nasir,Sai wata benz baka ta Aba ce,Sai babbar Macapolo ta Jigilan makaranta ne. Haraban gidan na Zagaye da Fulawowi masu kyau da yarari. Daga Cikin gidan kuma Flat Biyar ne ajere na Farkon na Baba Malam ne grefensa akwai Dakuna kamar guda Biyar saboda mazan gidan Falt din Dake bayansa kuma Shashen Hajiya Babba ce Uwargidan Mallam sai shashen mai bi mata Hajiya uwa Daga nata sai na Anty Nasara na Anty Amarya shine na karshen wanda Daga gefensa kuma wani katon Kitchen ne da Store mai Dauke da Kimai na Bukatar mace na girki Kowacce tana da nata ashashenta ammh Gudun Fitina yasa aka Fitar da na waje inda duk wacce keda girki Zata Fita ita da yara da masu aiki suyi komai Tare Dokar gidan ce da Tsarin komai Bisa Tarbiya da Sunna Baba mallam Sharahararran malami ne Daba iya Nigeria ko Gumel ba Har Kasheshen Larabawa an san dashi. A Babban Falon Dake shashensa ake Taruwa Matan da yaran maza da mata aci abinci sannan Ashashen sa ne kadai akwai Talabijin shima kuma In suna wajen sai Tashar Karatu sai wa"azi in ba kaga an Sauya sai in Dare ya Tsala yana so ya kalli Labarai Sun saba ya Zame musu jiki Duk wanda ya kwana da tashi agidan Mallam ina ka Fito karatu ina zaka ne..Me kace Aya ce mai na maida maka Hadisine ba iya Iyalan gidan ba Har damu da muka Hade dasu muma Dokarsa muke bi Domin har yau har Gobe in ba"a Fada maka ba Mutanen gari Dauka Suke mu jikokin Mallam ne BABA SA"IDU ne babban yaron Malam..! Kai tsaye shashen Hajiya Babba ta wuce Domin nan ne Dakin su Hanne Auta take ga Hajiya,Bata Tsaya sallama ba ta Tura kofar shashen da Karfi Tana Kiran sunan Hannan. "Hanne...Hanne..Hanne..! Take Fada lokaci Daya tana Wulka manya Idanuwanta Cikin kayattacen Falon na Hajiya Dayaji komai na More Rayuwa. Sai dai mamaikon taga Hanne sai taci karo da Hararan Ya Aisha Dake Zaune kan Darduma tana karatun pass Q domin suna gabda fara WAEC da NECO, Bata katse Karatun nata ba ammh Amina tasan Hararan ko ta macece Yasa ta Daga Hannunta tana Fadin"Yi Hakutri Ya Aisha..sallamu Alaikum..! Tafada kai Tsaye tana kara Wurga ido wajen neman Hanne. Abida Dake zaune kan kujera Tana Karatun Qur'ani Wacce Tunda taji Bangazan kofa Da kira tasan sai Amina itace kadai bata da natsuwa Kaf acikin ya"yan gidansu da gidan Baba Sa"idun. Itama Hararan ta jefa mata kafin tace"A tsakiyar falon ake sallama Amina..? Sai alokacin Amina ta ganta aranta ta Furta"Uwar sa'ido..! Afili kuma sai ta Dan Rasauya ido kafin tace"Sallama fa sunanta sallama Ya Abida..! Abida daman ai tasan bazata koma ba Kafiya ce da ita kamar kafura. Bude mata ido tayi tana Fadin"Au bazaki koma bakin kofa ki sake wata ba kenan..? Amina ta Bude baki tace"Ah gaskiya..! Cikin kunkuni tace"Haka kurum..Tab... Abida tace"Me kikace..? Kallonta tayi da manya Idanuwanta kafin tace"Nifa ban ce komai ba..! Abida Kai ta Rausaya a cikin Idanuwan Amina akwai wani kaifin da indan ta kalleka sai kaji gwiwanka yayi sanyi..! Da hannu ta nuna mata tana Fadin"Hanne tana Dakinmu tana Guga..! Ai bata gama Rufe baki ba Amina ta Kwashi gudu tana kara kiran sunan Hanne Wacce sai Lokacin taji kiran da Sauri ta kashe Iron din Daman Hijabin haddarsu na gobe take gogewa ko mafarki take yi tasan Sautin Kiran Amina Dabam yake kuma akowa da Hannatu yake Kiranta Aminene ce kadai ke kiranta da Hanne. Akofar Dakin sukaci karo Dakin Dake kusa da Bedroom din Hajiya sai wani Wanda suke Saukar baki Dangin Hajiya in sun zo nesa dana Hajiya. Kusan karo sukayi da juna Wanda yasa Hanne tayi baya tana Fadin"AMINA gani nan fa..! Tsayawa sukayi suna kallon Juna kafin Amina Taja hannunta su koma Cikin Dakin Tana Fadin"Hajiya fa..!? Hanne tace"Tana Dakinta..! Amina tabi Dakin da kallo ta Sauke ganinta kan Hijabin da Hanne ke gogewa tace"Dadina Dake kina da Zafin Nama Hanne..ni fa ban ji ma Hijabin nawa awanke yake ballatana akai ga gugansa..! Hanne Dukawa tayi ta kunna Soket ta Cigaba da Guganta ita kuma Amina kan Karamin gadon Hanne ta Zauna Babban na Ya Abida da ya Aisha ne Hanne bata damu ba tace"ai ke babba ce..Amina kike ni kuma Hannatu..! Amina Tayi dariya tana Fadin"dillar Sarkin Tsoro..Ki Saki jiki ki amsa sunanki Hannatu Yusus Abdurraham Bazanga kowa shakkarki zai yi..! Hanne na Guganta bata Dago ba tace"Uhmm..Meya fito dake Daga gida da Daran nan..?nasan da Dalili..! Amina ta Tabe baki tana Kwabe Hijabin Jikinta Lokaci Daya tana Fadin'"Ke da kika sani..Yau fa Har Yaya sai da ta Dakeni Hanne su Ya Zeenatu suka min gami wajen su ya Jafar harda fadamin in ya Dawo sai na Sani..! Hanne na Duken ta Dago kanta tana kallon Amina Kafin tace"Kan Tafiyarki yawon da kika saba in an tashi makaranta ko..?nima fa ana tashi nazo ajinku bakya nan..! Gajiya akayi da jiranki Ya shamsu yace mu taho gida..! Amina ta Zabga mata Harara tana Fadin"Ni daman bance ku jirani ba..Nasan Hanya..! Hanne tace'Koma miye dai baki kyauta ba..Amina don Allah ki daina Wasu abubuwan kai tsaye ko ni in kika fadama zakije wani wajen.ko Hamida haka zata faru..? Amina ta Juya idanuwanta kafin tace"Hanne..Hanne..Ki kyaleni don Allah kada ki batamin rai bazaki iya da Jidali na ba..! Hanne bata Kara mgana ba itama Aminan haka Sai da ta juya taja Littafin Data gani kan gadon Hanne Ta Fara Budewa kafin ta Dago Tana Fadin"Hanne akwai Kwazo..Kin yi aikin Malamin Lissafin nan..! Hanne na Nimken karshe a Hijabinta tace"Ba Dole ba kada ma na manta kinsan mugu ne wlh ya Rantse Bulala goma ga duk wanda bai yi ba..! Amina ta tabe baki kafin tace"Kan bala"i..Wai haka yace..? Hanne ta kashe Soket din ta Mike Dauke da Hijabin tana Fadin"Ajinmu ba..Bansani ba ko ku bai Fada muku ba..Ammh nasan komai tare yake mana ba bambamci..! Amina tace"Oho ni fa sanda ya shigo ina chan ina Karatun littafin da Ziyada ta daukomim adakin Antyta Garin Kallon Ruwa kin ji Dadinsa Hanne..! Hanne ta tsaya kyam tana kallon Amina kafin tace"Amina Daman baki Daina wannan karance karancen nan ba..?kinsan fa in aka sani bazaki ji Dadi ba..! Amina tayi tsaki tana Fadin"To sai me..?ke zaki fada..?ke ni kyaleni Sai fa nayi kema zan koya miki Allah da dadi..! Hanne tace"Allah ya Tsareni..! Amina ta tsuntsire da Dariya tana ganin Hanne ta Bude babban Wadrope din Dake Dakin gefen inda kayanta yake ta sakashi Kana ta Rufo Tana kallon Amina kafin tace"ki Tafi da littafin gida ki kwafe kada muje Ranar Monday Uncle Gaddafi ya Dakeki kinsan Halinsa..! Amina tace"Dillah Rabu dashi..Duka na Kisa ne..?da yana Kisa da babu Burbushin Amina aduniya kuma ya Dade bai yi Dukan ba Alqur"an bazan yi ba..! Hanne ta kada kafin tace"Ammh in kika kiyye taba Lafiyarki fa Amina..? Amina tayi kamar bataji ta ba ganin Haka yasa Hanne ta karisa gabanta Tana Fadin"In ya jafar ya dawo fa..? Amina na Dariya tace"Ke bazai dawo ba kema kinsani..Yaushe mai wannan Dakalin bakin zata barsa..! Hanne na Rufe baki tana Fadin"Ke Amina Anty Shamsiyan ne mai Dakalin baki..? Amina na Dariya Harda Buga Kafa tace"Eh mana baki taba Lura ba..Sai ma in tana mgana..Sweetheart..! Amina ta fada tana kwaikwayonta Dayasa sai da Hanne ta Duka saboda Dariya Kafin ta Dago ji kake Tas sun Kashe da juna Cikin Nishadi Tare suke Zube kan gadon Amina nama Hanne Rada akunne dayasa ta kara Saka Dariya tana Tureta Lokaci Daya Tana Fadin"Ba ruwana..Ba ruwana Amina..Bazan iya Da jidalinki ba kinsani..! Amina bata Damu ba Chanza Fuska tayi tana Fadin"Kin Tuna sadda Muna aji uku a islamiya kullum Karatunta Dayane..Anjadada.Kalli Leben nata jadaddaad..! Dariya sai da tasaka Hanne Hawaye Saboda yadda Amina ke yi da baki kamar Tsohuwa zatace isuhu..! Cikinta ta Dafe tana Fadin"Ki barni haka Amina kada ki kullarmin da ciki da Dariya..! Dariyan suke gabadayansu Basu san da shigowar Hajiya ba sai dai sukaji mganarta Daga sama. "Dariyan me kukeyi haka ne..? Da Sauri suka jiyo suna kallonta Hajiya Babba tana sanye da Doguwar rigar Shadda ajikinta Mace ce Doguwa ga kiba,Akallah ta bama Shekaru hamsin baya sai dai Hutu sun Lullube shekarunta Da ka ganta Kaga su Hanne da Ya Aisha Saboda suna Kama da ita sosai. Amina ce ta mike zaune tana Fadin"Hajiya ina yini..? Hajiya na Daga kofar Dakin tace"Lafiya lau Mamah..Sai yau nake ganinki..? Amina na Dariya batace komai ba Bata iya maidama Hajiya mgana Saboda Kirkinta,Mamah take ce mata Saboda sunan Mahaifiyar Baba Malam Amina kec dashi basa Kiran Sunanta ita tace Mamah shi yace Mamana..! Hanne ce tayi zaraf tace"Yau ma Laifi Tayi Hajiya..! Hajiya ta kada kai tana Fadin"Ohh maamah duk baki ji nasihata ba ko..?Don Allah ki natau ki dinga jin mgana Bana son wannan Korafin Kowa yace ke Babanki Sa"idu kullum Mganarki yake yi hakama iyayenki mata Don Allah Mamah ki rika jin mgana ki zama kamar kowacce y"a acikin Gidanan..! Zaku Dauka yadda Amina tayi shuru Tana jin Fadan ne nan kuwa bata ma Fahimta Domin indai wannan Nasihan ne ta Haddacesu Daga bakin Hajiya da Baba Malam Ammh Cikin Dan kada ido tace"Shikenan Hajiya..! Kallon Hanne tayi kafin tace"Ku tashi kuyi sallar isha"i gashi chan ana Kira..Ku fito muje falon Malam mu ci Abinci..! Da Sauri Amina tace"Hajiya zamu ci namu anan..! Saboda in akwai abunda ta Tsana wannan al"adar ta gidan mallam Akwai Wadanda bata son Haduwa Dasu acikin gidan nan. Hajiya ta juyawa tana Ficewa Lokaci Daya tana Fadin"Ba ruwana ku da Babanku..! Sai da Hajiya ta fice ne Hanne tace"Meyasa indai kikazo gidanan bakya son zuwa Falon Baba cin Abinci..? Amina tace"Ba wani dalili..Kawai bana son ganin matar nan ne..! Hanne tace"Wai Anty Amarya..? Amina ta tabe baki kafin tace"Itafa Bata da Mutumci Ni tun Ranar da Fada ya hadani da Sa'adatu ta Shigar mata Har tana Fadin meyasa ta Hada kashi da irin Tsiya kamata..?na tsaneta Daga ita har ya"yanta kinsan ko a makaranta bana mgana Dasu..kuma ina jiran Watarana yarinya ta shigar min Harka na Sauke mata Hayakin kaina..! Hanne ta mike tana Fadin"Amina baki da mantuwa..! Amina tace"Bana manta wanda yayimin Alheri..Da wanda yayimin Sharri..Kina wani abu kamar kuma jin Dadin zama da ita kuke..Saboda Baba malan ne take Rage wasu abubuwan ammh da badomin haka ba Allah kadai yasan iskancin da zatayi..! Hanne tace"Ni ina ruwana da ita..Iyaka in mun hadu na gaisheta ko Shashenta bana zuwa sai ta kama..Sa"adatu ma ta Dade batamin mgana kinsani Saboda ke..! Amina tace"Share banza..Itace akasa mu muyin gaba badai ta Mutum ba sai Allah..! Hanne na Dariya tace"Kinsan fa Diyar yayarta Ya Dan mallam ke aure ko..? Amina ta yamutsa Fuska tace"Haka naji shiko Duk yanmatan Duniya sai ita .? Hanne tace"Kowa haka yake fadi..in kinga ya"yan masu Sarauta da masu kudi da malamai yadda suka rika kawo ya"yansu wajen Baba ammh Duk yaki sai kawai Rana Tsaka yace Anty Sakina yake so..Kinsan tare tatashi wajenta dasu ya Jidda ! Amina tace"Eh mana na Tuna lokacin duk da bamu da wayau tafi kowa iskanci kamar gidan Ubanta..Nifa inaga Tun da akayi auran ban kara ganinta ba Duk zuwan da sukeyi har su tafi bama Haduwa har shi Ya D'anmalam din bazan iya Tuna kamaninsa ba gaskiya..! Hanne tace"Kinsan bai cika yawan zuwa ba..?in yazo ma shi kadai kwana Biyu yake ya koma in kuma Zai zo da ita sai karshen shekara kuma suna Gidansu Dake nan Kano Road sai dai in sunzo gaida su Hajiya kuma Har gidanku yana shiga gaida Yaya Hajiya tace Dan Dakinta ne sosai..! Amina ta mike itama tana Fadin"Ke ni ban taba ganinsa ba..Kina da Hotonsa .? Hanne tayi Dariya tana Fadin"Sha Kurumimki naji Hajiya na Fadin nan da wata Daya suna na nan zuwa Saboda Mganar auran su ya Aisha..! Amina ta kwalalo ido kafin tace"Kice muna da shan Biki..! Hanne tace"Wlh kuma har dasu ya Sadiya ma za"a Hada fa...kilama Har dasu Ya Zeenatu..! Amina tayi wata Dariya kafin tace"Allah yasa hardasu..su tafi su barmana Gidan dagani sai Hamida muci uban juna..! Dariya suka saka Gabadaya Harta Tafawa suna cigaba da Hiransu Salla sukayi Tunda suna da alwala Sai da suka idar kana suka fita Falo ba kowa suna Falon Baba Malam Kichen din Hajiya Hanne ta shigo ta Dibo musu Doya da miyar Stew nan falo suka Fito suna ci suna Hira da Dariya Daga ganinsu kasan kaunar da suke ma juna Daga Allah ne. Sai wajen 9:30am na Dare su Ya Aisha da Ya Abida suka shigo Ya Aisha Daki ta wuce ita bata cika mgana ba Ya Abida ce ta kallesu tana Fadin"Meyasa baku je Dinner ba..! Amina ce tace"Mun yi namu mu kadai..! Kai ta kada kafin tace"Sannu Shafaffu da mai..To Baba na kiranku..! Amina Rada take ma Hanne tana Fadin"Mijin Ya Abida zai sha Gulma..! Hanne na Matse Dariyanta Ya Abida ta Zaro ido tana Fadin"Amina me kike cemata akunne gulmata ko..? Da Sauri Amina tace"Labarin wata yarinya mai Bala"in saka ido nake bata..yar ajinmu a islamiya..ko Hanne..? Hanne ta Daga kai da Sauri Abida Wucewa tayi tana Fadin"Sai na Daki bakin yarinya yanzu nan..! Amina ta Rakata da Daga Lefe tana Shigewa suka kyakyalce da Dariya Saida suka gama Hanne ta kwashe komai takai Kitchen Amina tace"Dauko Hijabina na tafi gida Hanne..! Hanne tace"Kiran baban fa..? Tace"In mun fito sai na shige gida..! Hanne tace"Nazata nan zaki kwana..! Kafada Amina ta Daga kafin tace"Anki din..Ina fa Kirge nice na kwana Na karshe..Malama kece fa da kwana..! Hanne tace"Dillah zan kwana nima gobe..! Amina tace"Yauwa sai na baki ma Labarin wannan litaffin..! Da Sauri Hanne ta Danne bakinta tana Nuna mata Dakin dasu Ya Abida suke Amina Tayi Dariya Kafin tace"Sai me..?Allah yasa ma suji..! Hanne dai wucewa tayi ta barta Tasan wacece Amina bata da tsoro komai zai Faru sai da ya faru ita zata saka a uku. Hijabinta ta Dauko mata itama ta Dauko nata tana Fadin"Muje na Rakaki..! Fita sukayi Daga Dakin suna Tafe suna Hira Amina na Zagin malamar hausansu har tana kwaikwayon mganarta Dukkansu Jss3 suke sai dai Amina Ita da Sa"adatu suna A ne yayinda Hamida da Hanne ke ajin B. Suna tafe har Shashen Baba Maallan Amina tasan inda suka zo yasa ta Bude baki Daga Kofar Falon ta kwarara Sallama. Hajiya Dake Cikin Falon gefen Baba Mallam Dake zaune kan kujera yana Duba wani Littafi tace"Ga Mamar taka nan ta iso..Kaji Doguwar sallama kamar ta Kirki..! Tafada Cikin Zolaya yana Duken yace"Ta kirkin ce mana Zainabu...Mamana Harda yarinta ajikinta da ta kara girma ta mallaki Hankalinta sai dai Labari..! Kai kawai ta Kada tana Hangen abunda ba Haka ba kan Aminar ita ta amsa Sallamar ta Amina Hanne na Shirin Shiga ta riketa tana Fadin"mu shigo baba cikin harshen larabci Shi kanshi sai da ya Murmusa ya Dago Fuskarsa Daya cika da Farin gemu Cikin Dattakonsa yace"Na"am...! Baisan meyasa ba Ko Muryan yarinya yaji sai yaji wani Dadi yana mata kauna wanda ko cikin ya"yansa sai an Tona Amina haka Allah yayi ta mai Farinjini ne Malam yana sonta Saboda Allah da kwazonta Duk da take bata maida hankali Kokari gareta yana ganin makamceceniyar kwakwalwarta Data D'an malam awajensa da itace kadai yake Dogon Mgana da Larabci bata kakare ba Tana Jin Labarci Fiye da yadda kowa ke Tunani kuma Bayan Baba Malam ko Baba Sa"idu baisan wannan baiwar nata ba.. Sannan ko makaranta sun sani tana da Jawo Jidali ammh itace Over roll acikin ajinsu har mamaki ake yi masu Hassada da ita na Fadin Cuta akeyi Amina jidalinta baya barinta gane Karatu shiyasa Sa"adatu ke Kishi da ita matuka basa Shiri ko a islamiya da hadda Itace Zakka kamar yadda ta Fita Zakka acikin gida Daga waje ba,sannan Amina Zakka ce sai kowa Tunani yake sa"a take ci Saboda ba"a Taba ganin tabama karatu Muhimmanci ba nan kuwa basu sani ba Tana da baiwa sau Daya zata ga Abu Ta kuma karantshi ta gane shi kuma ya Zauna Bisa kanta Har Abada. _Naji Dadin yadda kuka karbi Labarin nan kamar yadda kuka saba karban Duka Labaraina Naji dadi nagode matuka Allah ya bar zumunci nayi alkawarin bazan baku kunya ba_ *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo(Besty) Alherin Allah ya kai miki adukkan inda kike* _Intelligent writer's asso_ *🅿️03* Kai tsaye suka shiga Kayattacen Falon Dauke da wata sabuwar Sallama,Suna Shiga Kamshin Turaran da Duk wanda yasan Baba malam yasan wannan kamshinsa ne wani Turare ne mai kamshi mai Sanya natsuwa Turaren mai Tsada ne dan Kasar Saudi mai suna Arab Saboda yawan amfani da Turaran yasa Duk inda Malan ke yawan zama kamshin ya kama wajen,Kamar yadda Kamshin ya kama Falon Dayake ma mallakinsa. Kayattacen Falo ne wanda yaji kayan More Rayuwa na alatu Falon babba ne mai Dauke da Royal Chair da Tattausan Cafet na kamfanin Italiayan. Sannan Daga gefe chan wata Kofa ce data fita Haraban gidan akwai wani Falo shi na ganawa da bakin Baba Mallam ne,Sannan Daga cikin Falon akwai Kofifin Bedroom Guda Biyu sai Daga shashen Yammah akwai wani Cabet na glass mai girma da Fadi kafe ajikin Bango wanda yake Shake da Littafan addini Kala kala nau"i nau"i Dabam Dabam Sannan Daga gefensa wani katon Tebur ne mai Dauke shima Da Tarin Littafai ba masaka Tsinke,sai Kujera Guda Daya wajen zaman mallam ne in zai yi Nazarin wani Littafi kamar yadda ya saba koda yaushe. Sai katon Talabijin mai kama da Kamar Mutum yana waje ne saboda Girmansa,Sunna Tv ne ke tashi Acikinta Dauke da Muryan Sheik Haruna Kabir Gombe yana kwararo Wa"azi Cikin Barkwancinsa. Cikin Lokaci kadan Amina ta gama Nazarin Falon Kafin idanuwanta su sauka kan Mafi Daraja a wajenta,Wanda shi kadai ne bata iya kallonsa Kai Tsaye shi kadai take shakka Da bata iya Hada ido dashi shi kadai ne yasan Wasu abubuwa Game da ita Saboda yana janta ajiki Wanda ko Aba dinsu bai kaisa saninta ba. Cikin Farimciki gabadaya Fararan Hakoranta suna Waje ne ita ce kan Gaba Hanne na binta abaya zuwa Inda Baba malam ke zaune Saman Daya Daga Cikin Kujerun Falon Hajiya Babba na gefensa Zaune.. Kamar yadda take Farimciki da ganinsa haka shima ya Dago kyakyawan Farar Fuskarsa mai Dauke da Farin gashi Daya Lullube gemunsa Dattijo ne mai Kima mai Daraja mai Dattako masanin Addinin Musulunci Dana Zamani SHEIK YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA kenan Shehin Malami na bangaran Addinin Musulunci da na Sunna Gabadaya ba iya garin Gumel ba Kasa gabaki Daya susan da zamansa yana da kyakyawan alaqa wajen Sauran Malamai sannan kowa na girmamasa Malami ne mai Tsoron Allah da Sanin ya kamata ba Malamin Siyasa ba kuma ba mai ci da addini ba ba ga Jama"ar gari ba Hatta ga iyalan Dake Zagaye dasu sun san karamci da Dattakon Sheik Yunus bazanga. A kama baya kama da duka ya"yansa Domin shi Fari ne sannan yana da Cikar Fuska da zati Duka ya"yansa sun fi kama da matansa Daya Dayane Cikin Jerin ya"yansa ke kama dashi Shuiyasa har acikin Ransa UMAR NA dabam ne.. Akallah a shekaru bazai gaza 78 aduniya ko ya D'ara ma sai dai yanayin Hutu da jin dadi sun boye shekarunsa yana Sanye da Jallabiya Mai ruwan Madara ya Cire Rawanin kansa,Farin gashin kansa da Rabi da kwata ya koma Fari sai kyali kyalin baki,Wanda Saboda Cire Rawaninsa kansa ya bayyana Fuskarsa Sanye da wani Sirrin Farin Gilashi mai karamai karfin gani Jaridar Rariya ce ta Ranar a Hannunta yana karantawa sanda su Amina sukayi Sallama. Tun kafin ta karisa Tace Cikin Muryanta"Baba...! Yana kokarin gyara zaman Gilashinsa yacce"Mamana..Sai yau nake ganinki..? Yafada yana kallonta Cike da wata Kauna da Allah kadai yasan adadinta Daidai kafafunsa ta zauna tana Fadin"Baba nazo shekaran jiya kana da baki Hajiya bata fada maka ba..? Tafada tana kallon Hajiya datayi Saurin Cewa"Na fadamai fa Maamah..Mallam na Fadamaka zuwanta ko..? Yana Dariya ya dafa kanta yana Fadin"Tafadamin Tsokanarki nake Yanzu Sa"idu ya tashi nake Bidarki sai Hajiya tacemin kina ma Cikin gidan nan nace shikenan Tunda Wajen hannatu kikazo ba wajena ba .!. Yafada Cikin Mirmishinsa na koda yaushe,Amina ta rike baki Tana yar Dariya Hanne Dake gefenta ta Duka Tana gaida Baba mallam ya amsa yana kallonta kafin yace"Ke kika Rikemin Mamana ko Hannatu..? Hanne kanta na kasa tace"Baba nima yau ba zuwa na bane..Laifi tayi Ya Jafar yace zai daketa sai ta gudo wajena..! Baba Mallam yace"Laifi..?ba na Hana su Jafaru tabamin Uwata ba..?na fada musu komai zatayi duka baya gyara Tarbiya Nasiha ne kawai mafita ballatana Duka Duka Mamana nawa take..?nan gaba sai kun yi mamakinta..! Yafada yana kallon Amina da Ta dan Daga idanuwanta Sama kafin tace"Baba bafa Laifi nayi ba..Gidan kawata naje ta bani kudina..Baba Ranta fa tayi fa tace yau zata bani a makaranta kuma taki zuwa makaranta yau fa Baba ina Laifi Domin na Bita na amso kudina..! Baba Mallam na yar Dariya yace"Baki da Laifi Mamana..Daman ai kyan alkwari Cikawa..! Amina tace"Yauwa Baba..nasan Dama kai ne kadai zaka Fahimceni..! Hajiya na Dariya tace"Daman ai Mallam baya kware miki baya..! Malam yace"Wa kika Taba ganin ya kware ma Uwarsa baya Zainabu..?duk dan kwarai yana neman albarka ne..! Hajiya Dariya kadai tayi batayi mgana ba Amina ce ta Zunguri Hanne Tana Fadin"Tashi muje..! Tafada a Hankali Baba Malam Dake kallinsu tace"Ina zaku..? Hanne tace"Gida zataje Baba..Zan Rakata ne..! Agogon Dake manne adakin ya Daga ido ya kallah Goma Saura Kadan kafin ya Dawo da Kallonsa kan su yana Fadin"Dare yayi Mamana yau ba ki kwanciyarki wajen Hannatun taki..! Amina tace"Baba itafa ke da kwana agidanmu ni na kwana na karshe ko Hajiya..? Hajiya na Dariya tace"Kwarai kasan abun nasu Team team ne..! Baba maallam ya gyada kai yana Fadin"To..to hakane..To ke Hanne yanzu Zagayowarki ne kenan..? Hanne tace"Sai gobe in mun Dawo daga Hadda zan kwana Baba..! Hajiya ya kallah yana Fadin"Yayi kyau..Hajiya bani Wayar nan Dake kusa Dake..! Ba musu ta mikamai Wata Lafiyayyiyar waya Fara Samsumg ce,Ya karba yana fadin"ku zauna bari na Kira shamsu yazo ya rakaki Amina Dare yayi..! Alokacin da aka ambaci Shamsu sai da suka Kalli Juna ita da Hanne Amina ta Kada ido aranta tace"Mugu.com kenan..! Ammh Afili bazata iya mgana ba, bata ma Baba Malam gaddama Hanne kuwa ai tasan Halin ya Shamsu Duk gidanan yafi kowa mugunta Da Dukan Mutane ko bakamai komai ba. Baba Malam yana Kokarin Kiran Shamsu Kira ya shigo wayarsa Cikin Mamaki ya kalli Hajiya yana Fadin"Sa"idu ke kirana Hajiya..! Sunan da aka ambata yasa Amina ta Dago tana kallon Baba Malam Hajiya kuma cewa Tayi"Kila mamah ake Cigiya..! Ba musu ya Dauka da Cikakkiyar Sallamarsa kamar ko yaushe Sa"idu Daga chan bangaran yana Zaune afalonsa gefensa Mamammu ce Cikin Girmamawa yace"Allah yasa ban katse maka wani abu ba Baba..! Baba Malam yace"A"a Sa"idu ina fatan Dai Lafiya..?naga baka Dade da fita ba..! Aba ya Dukar dakai kamar yana Gaban Malam yace"Daman Maman yara nan ne tasa na kira wai ko Amina tazo nan gidan..! Mallam yayi Mirmishi Kafin yace"Gata ma kusa dani Sa"idu..Ammh yansu zan saka Shamsu zai Rakota..! Da Sauri yace"Tayi kwanciyarta nan mana Baba..! Baba Malam yace"Tace ba ita ke da kwana ba Hannatu ce..Kasan mamar tawa yar Ra"ayi ce..! Aba yar Dariya kawai yayi domin ya Daina mamakin Kaunar Dake Tsakanin Baba Malam da Amina abaya ya Dauka Domin tana da Sunan Mahafiyarsa ne sai Daga baya ya Gane Kaunace kawai Daga Allah.. Sallama sukayi da juna yana Datse Kiran ya Dago yana kallon Mamanmu Dake gefensa Cikin Basarwa yace"Kin ji tana chan yanzu..Shamsu zai Rakota..! Daga haka ya cigaba da cin Abincinsa Domin Alkawari yayi ya Daina bari Lamarin Amina na Tadamai Hankali yanzu ma Mamansu ce ta matsa sai ya Kira Malam din yaji ko ta na chan Tun bayan shigowarsa Duka yaran sun zo sun gaishesa banda Amina yasan bata gidan in tana nan itama Zatazo ta gaishesa. Mamanmu Tayi Mirmishi kafin tace"Daman Nasam ai bata wuce Gidan Malam din..Nace ka Kira ne Saboda na Kore Bacin ran Dake Kan Fuskarka kan Amina din..! Bai ce komai ba har ta Fidda rai da zai kara mgana sai chan taji yace"Uhm..Nifa ban Damu ba kawai dai naga ya kamata ko bata Fadama kowa zata fita ba..Ke mai karenta baki isa ta Fadamiki ga ta zuwa ba?..!ko don ita ta saba yin gaban kanta da yin abunda taga Dama..! Mamanmu ta Bude zatayi mgana ya Daga mata Hannu yana Fadin"Ki kyaleni don Allah..Yau na dawo agajiyae bana son sabon bacin rai..! Yadda ya fada din tasan Har ransa haka yake nufin yasa ta Hadiye mganarta ta koma gefe tana Sauke Numfashi. Shi kuma bai kara kallon Inda take ba ya Cigaba da cin Abincinsa Kamar acikin Ransa bai da Damuwa nan kuwa Tsoro ne da Fargaban wani abu kuma man Gaba Amina zata jawomai. Achan gidan Baba Malam kuwa Shamsu ya Kira yace yazo yana son ganinsa ba Dadewa sai ga Matashin Saurayin ya shigo,Dogo ne mai Kaurin Jiki Kadan yana da Haske ba sosai ba Yana Shigowa ya Duka ya gaida Malam da Hajiya Suka amsa mai Cikin Sakewa Hanne ta gaisheshi ya amsa yana Hararanta Tunda ya gansu yasan Su suka saka aka tadosa Amina kuwa kanta na gefe aranta tace"Yasin bazan gaishe shi ba..! Tafada Har tana Murguda baki Baba Mallam ya kalli Shamsu yana Fadin"Me kake yi sanda na Kira ka Alarammah..!? Daman haka yake kiransa Saboda Mahaddacin Qur"ani ne sosai. Kansa na kasa tace"Ina k'arama zubairu da Akilu karatu ne Baba..! Dan Mirmishi yayi kafin yace"Dakyau Alarammah..To kafin ka koma ka cigaba da Biya musu karatun Ina so ka Raka Mamana gida sai ka Tabbatar da ta shiga gida sannan ka dawo..! Kai ya gyada aransa yana fadin sai ya Daki bakin yarinyar nan ko gaisheshi batayi ba sannan ga Jiranta datasaka yau sukayi a makaranta tatafi gantalinta ga kuma Tasosa da ta sa akayi Duk sai ya famshe ajikinta. Baba Malam ganin yayi shuru bai ce komai ba yasa yace"Kana jina ko..? Kai ya jinjina yana Fadin"Naji Baba..! Amina ya kallah yana Fadin"Tashi kuje Mamana..Sai da safe kenan ko..? Mikewa tayi tana Gyara Hijabin Jikinta Tana Fadin"Baba sai da safe..Hajiya sai gobe..! Tare suka amsa mata da Fatan Allah ya kaimu Baba Malam ya kalli Hanne yana Fadin"Rakata mana Hannatu..! Tanajin Haka ta Mike suka Fice Shamsu ya Rigasu gaba suna Fitowa suka gansa yana Tsaye yana Jiransu Fuskarsa ta Hade kamar bai taba Dariya ba. Hanne ta makale bayan Amina tana Fadin"Ya shamsu..Wlh Fuskarsa ba Rahma..! Amina tace"Dillah sai me..?mala"ikan Mutuwa ne..! Kwas...! Bata sani ba kawai sai ji tayi wani Rankwashi ya Ratsa kanta Bata gama Dawo Hayyacinta ba taji an ja kunnenta an murde Cikin muryansa yace"Wato ba mala"ikan mutuwa bane ko..?zaki gane baki da wayau..! Yafada yana kara sakar mata rankwashi kanta da Dafe da hannu Daya tana Fadin"Occh..Ya shamsu kunni na..? Da bakinsa yace"Shiii..Yana kallon Falon Baba Malam,Hanne ta fara baya Baya tana Murza ido Amina ya Sakarma Kunni yana Fadin"Oya wuce muce..Wannan na Farkon na Jiran da kika sa mukayi yau a School ne..Akwai na Kin gaisheni da kuma Tasoni da kika Saka Baba Malam yayi..Wuce muje..! Yafada yana Tura kanta gaba Ta wuce tana Dafa kanta Cikin kunkuni take Fadin"Allah ya isa na mugu..! Shamsu da karfin ji kamar maciji Kallonta yayi yana Fadin"Me naji kince Allah ya isa Amina..? Da Sauri tace"A"ah fa..Cewa nayi Allah yayi maka albarka..! Mirmishi yayi yasan Allah ya isa tamai ammh Tunda ta nuna Tsoronsa yasa ya kyaleta Hanne ya kallah da Sauri ta Juya zata koma ya Kira ta ta dawo Kafin tayi mgana ya Tasa keyarta zuwa gaba yana Fadin"Ina zaki..?kema wuce muje..Duk tare kuke daman sai Hali yazo Daya ake aBota..! Har yana gwara kansu,Kafin yakai su kofar gidansu Amina sun Sha Rankwashi kamar kansu zai Cire Daman ai ya iya Rankwashi baya Dukan Bulala Murdan kunni Rankwashi da Iza keya a kofar Gidan ya Tsaya ya Tura get din yana Fadin"Oya to a shige..! Amina ta shige tana Hararansa ta kasan ido,Hanne tayi Saurin cewa"Ni gida zan koma..! Hararanta yayi yana Fadin"Ina..!nan zaki kwana tunda kika zo shiga.! Ya Tunkudata ya Rufe get din ya Juya yatafi Amina ta kalli Hanne tana Sosa kanta tace"Wlh Gidanku Duk mugaye ne Hanne..! Allah ya isa bamu yafe ba..! Hanne na Sosa kanta tace"Kaina Zafi yake ya iya rankwashi fa Amina..! Amina tace"Insha Allah sai ya samu mai mai mafinyinsa..! Hanne Dariya abun ya bata Amina Tayi gaba Tana Fadin"Alqur"an ban yafe ba Har kabarinsa na Balbali da Wuta..! Hanne sai kanne Dariyanta take har suka iso Tsakar gida ko"ina Shuru sai Hasken Inji Dayake an kunna Tun Dazu Hanne tace"Kowa yayi barci Amina..Da ma agida mukayo kwanciyarmu..! Amina ta balla mata Harara kafin tace"Bafa nayi niyyar kwanan bane..! Daga haka ta wuce Dakinsu Hanne tabiBayansu. Aba Dake bakin Kofarsa ya Sauke ajiyar rai kafin ya Fito Kai Tsaye Kofar Gidan yaje ya Rufe da Kwado kafin ya Dawo yana Dudduba Tsakar gidan,Shi ya Rufe Kofar Kitchen din kafin ya Shige Dakinsa ya Rufe Yau Mamanmu keda shi yasa Tun dazu Yaya ta shige Ciki ita da Jawaad. Hanne da Amina sukayi mukus da sukaji Motsi Amina na mata Rada akunne tace"Aba ne ya fito..! Hanne ta gyada kai basu wani motsi ba sai da sukaji Shigarsa Dakinsa Sannan Ya Zeena tayi barci ita da Hamida Ya Zulaihat ne batayi ba tana Karatu Saboda suna gabda fara Jarabawar Fita. Ta Dago ido ta kallesu Hanne tayi Saurin gaisheta ta amsa kafin ta maida kanta tana Cigaba da Karatunta Amina ta karisa wajen gadonta tana Fadim"Ji Hamida tayi barci..Hanne tasheta..Yasin da ita zamu Hirar nan..! Ba Musu Hanne ta Daketa sai gata tatashi Hanne tace"Tashi mu yi hira..! Hamida tayi Tsaki kafin tace"Uban Hiran gobe fa muna da Hadda kun sani..! Amina na Kwabe kayan ta tace"Hanne kizo ki Saka wannan Rigar..Ke Hamida Sarkin karatu Badai kin iya Haddar ba..?Hanna ma ta iya ba shikenan ba..! Hamida na Hamma tace"Ke fa Amina..? Amina na Dariya tace"bala"i ai ni na manta inda nike ma..Kamar Cikin Suratun Khafi ne ko..?nifa inaga Tun Sati Hudu daya wuce Malan Amadu bai karbi Haddata ba ni Tunda Ranar nan ban kara Bi ta kansa ba..! Hamida da hanne suka kalli Juna kafin Hamida tace"Kinsan Bulala goma ce..! Amina na Hawa kan gadonta tace"Shine me..?yayi ya gama na Kakkabe jikina..! Tafada tana Dariya Hanne Zatayi mgana Amina Taja Bargo Tana Fadin"Malama Hanne ki adana wannan wa"azin naki zuwa gaba wajen Amina bamai amfani bane..! Suna jin haka suka kyaleta Hanne ta Cire kayanta a Tiolet ta Sako Rigar Barci akwai Gado wanda ba kowa kai Saman na Ya Zeena Daman nan take kwana in tazo ta Haye tana Fadin"Uncle T ya baku Assigment Amina..! Amina tayi Tsaki kafin tace"Kila ya basu ni ina na sanin musu.! Au kice Uncle Gajere yana Tafiya kamar Dan kaciya..!. Sai Tasa Dariya Zulaihat ta Dago Dagachan kafin tace"Amina Dare ne fa..?sannan Tsakaninki ga Allah Uncle T din ne mai Tafiya kamar dan kaciya..? Da Sauri Hamida tace"Ya zulaihat kalli yadda Duk Unity ake Fadin kyansa da ajinsa..Ammh Amina Tsinarsa take..! Amina Dariyanta ta Rage tana Fadin"Ku Anty Sara mai Warin maza..! Don Allah kuna jin warin in tazo kusa da ku..? Hamida da Hanne suka kalli juna ya Zulaihat kuwa cewa tayi"Hamida Kashe mana Hasken Dakin nan nagama karatun..! To ai tasan Tunda Amina ta shigo to ta Daina Fahimtar komai kenan. Hamida ta mike ta Sauka tatafi Rage Hasken Dakin Hanne ce tace"Amina kiji Tsoron Allah duk Unity wa yakai Anty Sara gayu da kamshi..! Zulaihat ta tabe baki tana Fadin"To a ina ma tasan kalan warin maza Hannatu..! Amina tace"Tabdijam..To wlh warin kashi take duk wannan Uban Turaran datake sawa da kaje kusa da ita kake ji..Wai baku taba ji ba..?ku Tsaya Harda Warin bakin Sir Gumel ma baku Taba ji ba..? Gabadaya Salati suka saka Ba Hamida Data Kulle Kofarsu ba Hatta Zulaihat Datace"Amina Sharrin naki Harda Principal..! Bakinta ta Danne tana Dariya Hamida Da tadawo zata kwanta tace"Kibar mganar nan Amina kada kije ki Fadeta a makaranta ya koma kunnensu..! Amina tace"Sai me..?karshenta kenan Suppention Amina Saidu ta samu freedom ni daman suji Wlh a koreni Gabadaya..! Ba wanda ya kara tankata ita kadai ta Cigaba da mgana sanin Halinta Duk mganar data Fada har ranta take Nufin haka din. Zulaihait ne ta gaji tace"Ki kama mana Bakin ki anan wajen Amina ko in na taso kika ga yadda zan yi wurgi waje Haba..Muna so muyi barci kina Hanamu..! Tafada Cikin bacin rai Amina ta Tura baki cikin kunkuni tace"Mutum dai ya Kusa aure ya bar mu mu shakata..! Tana jinta batace mata koma ba Indai ta Biye ma Amina sai Su Aba sun fito sun jisu Domin bakinta bazai yi Shuru ba. Washegari tun Safe kamar abun arziki suna Idar da Sallar asuba Sukayi azkar Hamida da Hanne suka zauna Zulaihat na Biya musu karatu Ya Zeenatu na Kitchen tana Soya musu Dankali Amina ta Fita Tsakar gidan Dakin Mamanmu ta fara shiga bata Ciki Tana Dakin Aba sai ta wuce Dakin Yaya ta sameta kan Darduma tana Karatun Qur"ani yadda Amina Tayi sallama ta Shigo aranta Tana Fatan Daman Amina ta zauna haka sai dai ina tana Shigowa taci karo da Jawaad dake barci nan kusa da Yaya ta Daga hannu ta Dagamai Duka tana Fadin"Wana kama yanzu..? Ta Tashi yana Sosa inda ta Dakesa Wuyansa ta Chakuma kamar wani Babba tana Fadin"Wa kake ma Dariya Jiya..? Yasan Halinta yasa da Sauri yace"Bafa Dake nake ba..yi hakuri ya Amina..! Fayau Fayau ta Fallamai mari tana Fadin"Daman na Fada maka na fika jidali..Yanzu sai nayi wirgi dakai sai ka Bugu iya Buguwa! Dakatawa da Karatun tayi ta Dago Tana kallonta kafin tace"To sake sa kafin kiyi wurgi dashi..Fitarmin Daga Daki..! Ta Fada Cikin Bacin rai Amina ta kama Hanya tana kunkuni Lokaci Daya Tana Fadin"Yaro yayi ta iskaci ba"a gani..Sai ace baza"a Dakesa ba..Kwarankwatsa na gansa sai na bugesa..! Tana jinta tana Fada Har ta Fice Daga Dakin kai ta kada tana Kokarin Cigaba da Karatunta sai gashi ta Leko Tana Dagama Jawaad Hannu Tana Fadin"Zaka sani ne yaro bar ganin Yaya..! Ta dago Cikin Bacin rai tace"Amina..! Da Sauri tace"Ina kwana Yaya..Daman nazo gaisheki ne..! Ko Sake kallonta batayi ta kalli Jawaad tana Fadin"Wuce kaje ka Tube kaya na saka ruwa a Kittle a Tiolet kayi wanka dashi..lokaci na Tafiya..! Ba Musu ya wuce ita kuma Amina ta wuce aranta tace"Nidai na Fita Hakki na gaisheta..! Daganan Falon Aba ta je tana ta Sallama kafin taji ya amsa mata kamar ta Allah haka ta shiga kanta na kasa yana zaune kan kujera yana Duba Wasu Takardu ya Dago yana kallonta Da Sauri tace"Aba ina kwana..?mamanmu na ciki..? Yana Nazarinta yace"Ita kikazo nema..?tana ciki tana barci..! Da Sauri tace"A"a nazo gaishe ku ne Aba..Sannan na tambayeka..Wai ni na saka maka Hawan jini Aba..? Kai Tsayen yake kallonta kamar yadda Itama ta Sauke masa Dara Daran Idanuwanta wandanda yake kallonsu kamar na Hadiza Lokacin tana kamarta. Ita kadai ce acikin ya"yansa take iya Kalllnsa ido Cikin ido ta Fita zakka Tabbas ko acikin Ransa Amina Dabam take har Tunani yake daman Hausawa sunce Maraji aciki yayan Mutun sai kaga kafi sonsa To shima Hakanne sai dai yana kokarin Danne komai sannan yana ganin kamar Kaunar Dayake ma Amina tasamo Asali ne Tun Kaunar Daya ke ma Mahaifiyarta har yau gobe Hadiza In soyayyarta ta Motsamai sai yaji wani Abu acikin Kirjinsa mai Nauyi game da ita. Saurin Dauke kansa yayi daga kallonsa ita kuwa ganin haka yasa tace"Kayi Shuru Aba bakace komai ba..? Sai da ya Daidaita natsuwarsa kafin yace"Waye ya fadamiki haka..? Kai Taaye tace"Waye zai fada..Yaya ce Aba..! Kai ya dan jinjina kafin yace"A"a bake bace..Ciwo na Daga Allah ne da kuma Girma kinsan ai nafara Tsufa..! Yafada yana kallomta Itama kallonsa take Tana so taga tsufan Dayace ya Fara,Yana da Tarin Baiwa da Zati in ka kallesa shi ba Fari bane sai dai yana da Haske Daga Zaunen Dayake zaka gane yana da Tsawo da Dan Jiki Sannan akaron Farko zaka san a Tsaye yake Bakin Zamafare kodaga yanayin mganarsa da Zamfaranci. ALHAJI SA"IDU AMINU GUSAI kenan Ba Rago bane mutun ne Jajirtattace wanda ba abu kadan ke saka aga Rauninsa ba sannan mai Neman na kansa wanda baisan Lalaci ba mai Ra"ayi da Tsari da kuma tsauri kadan acikin Rayuwarsa. Ashekarunsa in ya wuce ne ya kai 59 zuwa da 60 yana da Tarin gemi baki Mai Kyali kyalin Furfura kadan Shi ai Dan Malam ne kuma Duk wanda yasansa Tun Farin yasan sa da Gemu ne shiyasa wasu Mutanen da suka sansa a baya suke mai lakabi da SA'IDU MAI GEMU..! cikin Lokaci ta kare mai kallo Kafin tace"Wlh Aba baka fara tsufa ba..Gemun ka fa baki ne bai yi fari ba irin na Baba malam..! Tafada Har Fararan Hakoranta suka Bayyana Kauda kai yayi yana Danne yanayinsa kafin yace"Tashi kije..Kuyi shirin makaranta kada,ku makara..! Da Sauri ta Mike tana Fadin"To Aba..! Daga haka ta fice ya Bita da kallo Acikin Ransa yana Fatan kada watarana Amina ta zame mai Zakka da gaskem da bazai iya Da Jidalinta ba. Ba wanda yamata mgana ta Dauki Tsintsiya ta Share gidan ta Fito da wanke wanke Lokacin da Hamida ta Fito ita da Hanne,bayan sun je sun gaida Aba da yaya suka zo suna Tayata Har suka gama suna gamawa Hamida ta Shiga Tiolet din Dakinsu sukayi wanka,Amina a Dakin Mamanmu tayi wanka ita da Hanne Yau Ya Zeenatu da Rigima tatashi Mgana Kdan sai ta fara Harara da Fada Amina tayi Dariya aranta tace"Su ya Zeena kwana nawa ne..! Domin adokar Malam in aka Aurar dasu ya Zulahat suma za"a bama Manemansu Daman neman su Domin Daman akwai su Baba Malam da Aba sun sansu kune bazaku sani ba sai Lokaci yayi. Su ya zulaihat wata Biyar da suka gabata aka bama Manemansu izinin fara ganawa dasu kuma Tunda Hanne tace mata taji ana mgana auran ya tashi..Ba adau Lokaci ba sukaji Baba Malam yace Rana kaza Daurin auran Da yinin Biki Daman komai na Bukata an Tanadar dashi Bikin Amare Hudu ne za"ayi Ya Zulaihat Daga gidan Ya Sadiya yar wajen Anty Amarya Ya Aishan Hajiya Babba Ikram din Anty Uwa sune za"a Aurar dasu wannan shekarar kuma Dukkansu suna matakin Shekarar karshe ne a makaranta Dama wannan kowa ya sani Tundaga kan Iyalan gidanmu har Gidan Malam maza ne ke Karatu mai zurfi mace kuwa iya Secondary sai Karatun addini har matakin Sauka da Hadda za"a Aurar Dake in mijinki ya amince adakin ki sai ki Cigaba ammh agidan Mallam da Gidan Baba Sa"idu ba wacce ta wuce wannan Matakin. Sama sama suka karya da Dankali da kwai da tea susan in suka bata Lokaci ya shamsu zai ce atafi a barsu makaranta bata da nisa dasu sosai ammh gabadaya yara da manya a School Bus ake kaisu. Amina ce karshen shigowa Motar Hijabinta yasha Tattara saboda Rashin Guga Daman a Kujerar tsakiya suke zama su uku ita da Hanne da Hamida Sanda ta Shigo sai da ya Shamsu dake Bakin Kofa ya rankwasheta yana Fadin"koda yaushe kece abaya..! Aranta sai da tayi Allah ya isa tana ganin Akilu da Zubairu na Dariya bama wani fa Girmansu sukayi ba Kwafa tayi aranta tana Fatan samun wata Dama. Tana ganin Sa"adatu na Hararanta itana ta maida mata kafin taje ta Zauna kusa da Hanne tana gyara zaman Jakarta wanda Qur"ani ke Ciki da Taujud sai Sauran Littafin Islamiya. sabeeha ce ta ga tana kallomta Lokacin da Motar ta Fita Daga Haraban gidan Baba Malam Hararanta tayi kafin tace"Qurwata Kur..Wlh Aniyar kowa sai ta bisa..Amina dai nan bari wh badai Mutum ba sai Allah..! Ya Zeenatu ce ta dago daga gaba Tana kallon Amina kafin tayi mgana Ya Umaimatu wacce bata da Cikakkiyar lafiya tana Fama da mtsalan junnu don ma ana Tsaye akanta saboda haka Tayi Deliying karatu Ashekaru ma ta Girme su ya Zeena kamata yayi tana Cikin su ya Aisha ammh Saboda Lalurarta yasa komai ya koma baya Bata zuwa makarantar Boko iyakarta jss3 Mallam yace ta daina zuwa. Cikin Sanyinta tace"Amina ki bar mgana haka kina cikamin kunni..! Tafada tana yamutsa Fuska Amina tamele baki tace ahankali.."Kaji Sauran Iska..! Hanne kadai ta jita Ya Abida Tsaki taja Zatayi mgana Shamsu ya Juyo Daga gidan Gaba yana Fadin"Kun Damemu da surutu..In bazaku Duba Littafanku ba kada na sake jin bakin kowa anan..! Duk da ya Aisha da ya Zulaihat suna gaba dashi ammh suna girmama juna..ya Ikram na gefe tana jinsuTak batace ba tana ta Duba Qur"aninta Ballatana ya Sadiya datayi kamar bata amotar....! ****** *A RANAR..!* 10:50am. Madina na gaji na Fara Sarewa acikin wannan Tafiyar tamu..Haba abu Daya yaki ci yaki cinyewa..Shekera wajen goma sha muna abu Daya babu Riba na kasa samun abunda nake so nake kowani Lokaci kina Fadamin wannan karon zamu dace To yaushe..?gobe ko jibi..?ba Rana Madina kowani Lokaci aikin baya Tafiya Daidai na Fara Tunanin ko dai bani da Sa"a ne. ?ko kuma ban zo Duniya da sa"a ba ko kuma kila bani da kashin arziki ne..! Bansan me ake cewa Dagachan bangaran ba Sannan ita kanta me wayar ba ganin Fuskarta nake yi ba ta riga ta juya ba waya ce rike a Hannunta tana mgana cikin Zafi da kuna..! "Kullum sai kice na kara Hakuri..?Har zuwa tsawon wani Lokaci zan cigaba da Dauriya da Nade wannan Bakinciki na shekara da shekaru dake Cikin Raina..?Nagaji fa Madina na Fada miki..nayi babbn aiki kan Na samu abunda nake muradi aka Kuskure a karon Farko Madina..JAFAR naso ya zama Haka JAFAR naso Madina..Ba AMINA ba..Meyasa shi aikin ya kuskure kansa sai ya koma kanta .?kinsani bata Cikin Lissafina Domin ita karamar alhaki ce..Sai gashi Sakacinki da yarda Dake da nayi yasa Aikina ya Lalace Komai ya kare ban samu komai ba sai Wahala da Bakinciki Madina to me yayi min Saura..!? Shuru ya kara Biyo baya kafin ta Daga hannu Cikin kaifin Murya tace"Kul..Dayyaba batasan Ja da baya ba..Madina yanzu aka fara wasan..Yadda nayi alwashin ta rasa komai sai ta rasa madina...Tun ashekarun baya nake fama da Kunar wannan Kaunar wannan Soyayyar dani ke gani acikin Idanuwana SA"IDU ji nake kamar na kashe shi na Wuta..Madina ki Dora aikinmu..Ba gudu ba ja da baya..! Mu keda Nasara....Nasara tamu ce.. Hahahaaa..!!!! Lokaci Daya tana Sakin Wata Dariya kafin Shuu kamar Walkiya tayi Saurin barin wajen batare datayi waige ba..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo(Besty)Alherin Allah yakai miki a dukkan inda kike* *Intelligent writer's asso* *🅿️04* Har cikin Haraban Makarantar Idi Direba ya kaisu,Mai Dauke da Babbar Haraba da jerin ginin Azuzuwa Sama da kasa makarantar bata fi shekara goma da samar da ita ba Sannan Filin na Baba Malam ne sannan Kungiyar izala reshen Jahar Gumel din suka bada kwangilan Ginata, Ta samu kafuwa sosai da Jajircewan Baba Malam yawancin Malaman makarantar Dalibansa ne sannan Ana Biyansu albashi da Kudin makarantar da yaran ke biya ammh ana karawa Tunda ba Duka bane zai isa abiya kowa da kowa Nauyin makarantar da komai yana Wuyan Baba Mallam ne..! Sannan akwai matakin Ajin yara akwai matakin Manya Tundaga aji Daya Har zuwa aji na Shidda Sannan akwai matakin Jss1 har zuwa 3 sannan akwai ajin Matan aure su kuma Daga 9am zuwa 12pm Na rana ajin da Su Ya Jafar suke koyawar shi da Ya Nasir in basu da wani aiki Alokacin. Tun zuwansu kowa ya Nufi ajinsa Hamida da Hanne da Amina da Sa"adatu suna aji Daya ne,Sannan Ya Aisha da ya Zulaihat da Ya Sadiya da Ya ikram da Ya Shamsu suna Matakin karshe ne Wato Jss3 yayinda Ya Zeenatu da Ya Umaimatu da ya Abida suna Jss2 ne Akilu da Zubairu ke Jss1 sai Jawaad Da Sabeeha Dake aji Hudu a matakin Shashen primary. Kamar yadda kowa ya sani ne Ranar asabar ake karban Haddan Qur"ani da Tajwid,Sai Washegari Ranar Lahadi ake karin karatu To aranar ma Amina bata kawo Hadda ba kame kame ta fara tama manta inda take. Malam Amadu Shine Malaminsu na Qur"ani Mahaddaci ne sannan ya Taba cin gasan Qur"ani na Duniya Gabadaya,Sosai yake da Ilimi da Sanin ya kamata Yana zaune Daga gaban ajin da basu wuce su Ashirin ba Mazan da matan Sanye yake da Jallabiya Fara da Hula tabani kaji Hadisi Jallabiyar da kadan ta wuce gwiwansa sannan Gemunsa zai kai kamu Biyu da Rabi baki Silif yasha gyara. Ya kalli Amina Dake gabansa kan wani Benci inda duk wani Malami kema indai zai bada Karatunsa. Cikin Tsausayinta Domin ta koma Abun Tsausayi yayi Dukan Har yagaji Amina bata Sauya ba. Cikin Natsuwarsa yace"Amina Sa"idu kinsan Satin ki nawa baki kawo Hadda ba..? Amina ta Dago Daradaran Idanuwansa ta kallesa Kafin tace"Kamar sati na Biyar kenan ko..? Tafada kai Tsaye mamaki Daya take basa Bata jin kunyar kallon Mutum Cikin Idonsa sannan abunda ke Daure ma kowa kai in akazo Jarabawa itace Take doke kowa acikin ajin,Abun mamaki kuma ko wajen Jarabawar Haddar baki itace Overoll acikin Ajinsu Tiryan tiryan zata yi karatunta Cikin kwarewa da Tajwid din Da sukansu Malamai suna mamaki yaushe ta koya yaushe ta iya..?Ahalin har aka gama Team bata Fahimci komai ba Kullun sai an Fito da ita bata bada Haddanta ba Wlh su kansu suna mamakin Amina sun kuma yardan ma kansu Kirarinta na badai Mutum ba sai ta Allah. Sauran Dalibai kuwa sai suyi ta cewa an yi Cucene ammh Amina me ta sani banda Rashin kunya da Rashin Muttumci. Kai kawai ya Kada Kafin yace"Fita kofar aji kisa gwiwanki a kasa..! Amina ta mike kai Tsaye ta Fice Tana Dariya Daman Wlh ta gaji da zaman Waje Daya tana Fita kamar abun arziki ta saka gwiwanta akasa agaban ajinsu sai Sauran azuzuwan Dake kusa dasu Hankalin Daliban ya Dawo kanta Kaf Daliban Makaranta Umar Ibn Khallad waye baisan Amina Sa"idu ba bama Dalibai ba,Hatta malamai Sun san dazamanta Musamman Malam Datti Wanda ke Rike da Mukamin Shugaban makarantar. Har Wajen karfe Daya Lokacin da za"a Tashi Sallah kana Malam Amadu ya Fito ya samu Rigima Amina ta Hada wata yar aji Biyar ta Leko to tana mata Dariya Amina ta nuna kanta tace"Ni kike ma Dariya..?lalle bakisan wacece Amina ba..Ammh yau zaki sani..! Dutse ta Dauka ta yi Saita sai a saman Goshinta ta window ajin sai kuwa goshin ya Fashe sai jini ta Fara kuka sai da Malam Lawali Dake ajinsu ya Fito yana ma Amina mgana ta Karkace baki tace"Dariya tamin..Ni kuma nayi mganinta..! Ransa ya baci yayi mata Bulala goma ta Kakkabe hijabinta irin ko ajikinta Din nan ga yarinyar nata kuka sai da aka kaita Chemis aka mata Dinki Domin wajen yayi zurfi mgana Har gaban Malam Datti Shugaba me zai ce.. ?Daman ai Amina ce kadai mganarta ke zuwa yana Dawowa Jikar Malam ce yana jin Nauyi ya Koreta ko kuma yace zai Dauki mataki Lokacin da aka kaita Office din Malam Lawali yana bayani yana nuna goshin Adawiya Daya sha Plasta yace"Shugaba kalli yadda ta ji mata Ciwo..?infa baka Dauki mataki ba yarinyar sai ta fara aikata wasu abubuwan da watarana zai zo yafi karfi mu..! Malam Datti na kallon Amina yana Nazarinta kwata kwata ba tsoro ko Karaya acikin Idanuwanta kyam Take kare ma kowa Dake Babban Ofishin Shugaban makarantar kallo. Sai da ya gama karantar ta kafin yace"Amina Sa"idu meyasa kika Fasama Adawiya Bala goshinta..? Sai da ta kallesa Ido na Cikin Ido kafin Tace"Yauwa Shugaba kai kadai kayi mgana mai kyau na Hankali..! Malam lawali ya Rankwasheta asaman kanta yana Fadin"Au ni na marasa Hankali nayi ko..! Tana sosa kanta tana kunkuni tace"Alqur"an ban yafe ba..Wuta balbal..! Yana kallon bakinta yace"Me kikace..?badai zagina kike yi ba ko..? Tana Juya Idanuwanta tace"Nifa cewa nayi kana da Hankali kama fi kowa ahankali a makarantar nan..! Ta Karishe fada tana Sauke ido Daga gani Ba har ranta ta Fada ba Malam Datti sai da ya Murmusa kafin ya kalli Malam Lawali yana Fadin"Mallan kyaleta tayi mgana..! Amina ina jinki..?kina sane da sai da Aka yima Adawiya Dinki a inda kika Buga mata Dutse..! Amina tace"Kai don Allah..?naji Dadin haka gobe ai bazata kara ma Amina Dariya ba..Shugaba Daga malan Amadu yace na fito kofar aji na saka Gwiwiyona a kasa ta Fara lekoni tana mim Dariya batan Uba ke ni zaki ma Dariya..Humm baki sanni bane ni ko Jawaad Yamin Dariya Barar dashi nake yi ballatan Ke da babu Dangin iya bare na Baba..Na Rantse da Sarkin dake Busamin Numfashi da awaje ne tamin Dariyan nan sai na mata Dukan Mutuwa sai na Lahira yafita jin Dadi Shugaba..! Ta Fada tana Hararan Adawiya dake kukan Wuya da Sauri tace"Karya take yi malam..! Amina ta Zaburo tana Fadin"Ke wake karya..!Alqur"an ki kiyayeni..Bar ganin gaban Shugaba bamai hanani Sama da Fadi dake na fiki Jidali wlh..! Shugaba ya Dakatar da ita yana Fadin"Ke Amina natsu..Ke Adawiya Fadi gaskiya kin mata Dariya ko A.a..? Adawiya kanta na kasa ta Daga kai alamun Hakane nan Shugaba ya fara mata Fada yace ta bama Amina Hakuri Data bata Hakurin Hanci ta Daga tana Fadin"Na Hakura Tunda ko banza za"a je gida da goshi Ham..! Tafada Tana Dariya sai da Shugaba ya Tsawarta mata sannan yasa itama ta bama Adawiya hakuri sannan ya Sallamesusu Suna Fitowa bakin Office din Amina ta Bangaje Adawiya tana Fadin"Ke karki Dauka har zuciyata na baki Hakuri ne..Amina bata Nadaman kan abunda ta aikata kuma bazan taba Nadama ba..! Tafada Tana Kada mata ido kafin ta wuce Damam an tashi Sallah zuwa inda suke sallah sannan tasan su Hanne nachan na Jiranta Adawiya dai bata tanka ba Daman ai tasan Amina tasu ne bata taba Hadosu ba sai yau. Wani kebabbam Waje ne aka Maida inda ake sallah na Maza na gaba barayin mata na Baya koda Amina taje su Hanne duk sun yi Sallah suna Wata Baranda inda ake cin Abinci kowani Dalibi ana kawo mai abinci Suma Daga gidan Baba Malan Idi ke kawo musu nasu Kula Uku Daya nasu Ya Aisha Daya nasu su da su ya Zeenatu sai Daya nasu ya Shamsu ne. Saida taje ta fara Sallar kana ta zo Inda suke cin Abincin Tana zuwa ba wanda ya Fara mata mgana sai itace ta Rike Haba tana Fadin"Naga yan Ubanci Hanne da Hamida ko ku Jirani nazo muci tare..! Ta Fada tana Leka Filet din gabansu Jallop din Shinkafa ce taji Kifi Sosai,Hanne ce tana kai Loma tace"Wazai tsaya miki .?jidalin ke sai ke Amina..! Su Ya Aisha suna chan gefe barayin manya su ya Zeena ne ke kusa dasu Tana Shirin zama Sa"adatu Dake gefe tama cin nata ita da Sabeeha tayi Tsaki kafin tace"Allah ya rabamu da Alfahari da jidali..! Amina tasan da ita take Ranta ya baci Hanne ta Rikota ganin tana Shirin Tace Cikin Lallashi tace"Ki kyaleta Neman Rigima take..! Amina ta Fizge Jikinta Tana Fadin"Neman Rigima..?to ai gidan Tatarar Dillah Sakeni naci Uban yarinyar nan..! Da Karfi ta kwace Hannunta ta Mike Sa"adatu bata sani ba sai gani Tayi Anina ta Chakumota ta Mikar da ita Lokaci Daya tayi Wurgi da Filet din Abincin ya bare a wajen Cikin Zare ido Tace"Maimaita abunda kikace in ba Tsoro ba..!.? Ayadda Aminan ke Huci Sa"adatu tasan bazata iya da ita ba Su Ya Zeenati Dake gefe ne suka taso dasu Hamida Cikin Fada ya Zeenatu tace"Miye haka Amina Sakar mata Hijabi..! Ya Abida tace'Ko sai an saka miki Duka ne..! Amina tace"Ta maimaita abunda ta Fada..In ba tsoro ba da yau Filin makarantar nan ta mana Kadan in na Fara Dukanki sai kinyi kanin Mutuwa..! Sa"adatu ganin maceta sun zagayesu yasa ta Kwace Hijabinta tana Huci tace"Wake tsoronki..?Allah ya kyauta..Kuma sai kin Biyani abincina..! Amina tace"In naki fa..? Kai Tsaye Sa"adatu tace"Sai me kuwa..?yar bakin ciki..Dadin abun dai arziki ake ci..Abincim ma badaga gidanku akazo dashi ba..Sannan makarantar ai bata gidan Uban Mutum bace duk Tsiya dai Ta Gidanmu ce Jinin Bazanga..! Tafada Cikin Isa da Gadara da kowa sai da ya tsaya yana kallonta Ya Abida ta Daka ma Sa"adatu Tsawa tana Fadin"bazaku bari ba ko..?bari na Kira shamsu shi ai kuna jin tsoronshi..! Amina bata ma jisu ba Kirjin Sa"adatu ta Daka kafin tace"Abincin banza..Kashi kema kinsan bamu Rasa Abun da zamu ci ba..Sannan da kike mganar ta gidanku ce karatun ma na Gidanku ne..?aida na Gidanku ne da baki zo nan ba sai ki zauna agida chan a Koya miki..Bari kiji na Fada miki ni bana Alfahari da Kowani Gida kada Kice da Gidanku nake alfahari Har yau har gobe bana jin kunyar Nuna BABA SA"IDU amatsayin Ubana kuma Har Gaban Abada Amina Sa"idu Gusai Dashi nake ado..! Sa"adatu tace"Hmmm..Naga dai ko shi Baban naku karkashin Baba Malan yake gidan Gonar da kike takama Dashi na Uba..! Bata karisa ba Amina ta kai mata Duka a kanta tana Fadin"Kada ki kuskura kice zaki zagi Ubana..Domin zan yi Kaca kaca Dake..Duk jidalina ina Martaba Aba..Ina Daraja Aba ina Mutumtatasa..Ni bazan zagi Baba Malam ba kuma bazan taba bari Azagesa ba..Bambamci na Dake kenan nasan Darajan Manyana..Sakaryawa kawai..! Tana gama Fadin haka ta Tureta sai da ta Fadi ta wuce Fuu sai hanyar ajinsu Su Hanne suka Bita da Kallo ya Abida tayi kafci kafin tace"Sa"adatu Duka abunda kika aikata....A kunnen Baba Malam..Kowa ya koma yaci abincinsa..! Abincin da Amina bataci ba kenan Har ajin Hanne ta koma tana Rokon Amina tazo taci abimci tace bataci Sai da Hamida ta saka baki ne Amina ta Kalleta tana Fadin"In Hanne bata Damu ba bazan yi mamaki ba..Ammh ke Hamida baki da zuciya..Ai ko abincin yakai Cikin ki kya amayosa Domin ki nuna mata ba yunwa ke Damun mu ba..Ammh sai gashi ko ajikinki..! Tunda ta Fadi haka susan ta Harzuka Shiyasa suka kyaleta har aka Dawo aji Malamin Tajwid ya shigo Malam ilaysu alokacin Amina tana Bencin su Zainab ce sai tatashi zata koma Wajen zamanta ita da Hanne da Hamida Inda Taga Mariya Muhammad ta zauna..! Tana zuwa kai Tsaye tace tatashi ita kuma ta balla mata Harara tana Fadin"Bazan tashi ba..ai bamai kujera Tunda bada gidanku kikazo dashi ba..! Amina tace"Haka kikace..? Ta Daga kai Batayi mgana ba Domin itama tana da Tsiwa Hanne ta Juya tana Fadin"Mariya ki tashi don Allah..Amina ta fara zama anan da Safe..Bana son jidalinta..! Mariya ta Bude baki Zatayi mgana kawai taji ta akasa Amina ta Zauna Daga chan Farko ta Dage iya karfinta ta Turo Kujeran sai da Mariya Dake Farko ta Fadi hannunta ya Bugu da kasan simintin ajin Dayasa ta saki Ihun zafi gabadaya Hankali ya koma kanta Harda Malam Iliyasu. Da Sauri ya mike ya kariso yana Fadin"Subhanallah me ya sameta..?ku kamata..! Su Hanne suka mike suka kama Mariya Dake kukan Hannunta zuwa Kujeran gabansu suka zaunar da ita Amina ko ajikinta Cikin Mamaki yace"Garin yaya ta fadi..? Da Sauri Sa'adatu tace"Amina Sa"idu ce ta Turota Daga kan kujera..! Tafada Tana Hararan Amina da ko kallo bata isheta ba. Mallam iliyasu ya kalli Amina a Harzuke yace"Ke zo ki fita. bana son Rigima kina jina ko..? Amina batayi gaddama ba ta mike Harda Daukan jakanta ta fice Tana wani Hura Hanci ya Bita da kallo kafin ya Kada kai afili ya Furta"Allah ya shirya. ! Da sauri Hamida da Hanne suka amsa da Ameen Domin su kadai ne In Amina ta Dibo Jidalinta yake karewa akansu Saboda sunfi kowa kusa da ita. Bata kuma koma ajin ba sai dai ta tari Islamiya kafin shima atashi sai da sukayi Tsiya da Samira tana Rubutu Daga ta mata mgana ta Dauki Littafin ta yaga suka Fara Fada da Chachar baki sai da aka kai su waje Dagachan da akaji abunda ya Faru Amina ce ba gaskiya aka sakata wankin Bayi batayi ba tadai je ta watsa ruwa ta kusa Rabin Bayin da Ruwa Dayake Inda Ruwan ke wucewa ya Lalace ya toshe Tana ganin haka ta Dinga kai ruwa sai da tayi Rabi Dashi ba Domim ma ta gaji ba ga yunwa taso ne ta Cika Tiolet din da Ruwa gobe ma su kara Sata aiki. Aranar da suka koma Gida Hamida ta bama Mamanmu Labarin Fadan Amina da Sa"adatu mamanmu ta rike baki Tana fadin"Lalle yarinyar nan bata da kunya..Kuma kalaman ba nata bane na Uwarta ne..Kin Burgeni Diyata gwara da kika fadamata haka..! Yaya na jinsu batace kala ba Tana Kofar Dakinta Lokacin bayan Sallar mangariba ne suna baranda Dukansu saboda Zafi ba wuta sannan kuma ba"a Riga an kunna inji ba. Ya Zulaihat nadaga gefe tace"Mamanmu kada fa kiga Laifin Sa"a..Amina ce mai laifi koma Meya faru ita tajawo..! Mamanmu ta Harareta Kafin tace"rufemana baki me kika Sani..?Uwar Sa"adatu yadda take kishi Damu ai bazai Fadu ba..Bata da yadda zatayi da Aba dinku ne Tare da Malam ammh da Tuni ta rabasu..Bari Aba Dinku ya dawo zan Fadamai bazan Dauka ba..Bazan Dauki arika Cin Zarafin Diyata ba..In ta kama Malam Din yaji sai ayi mana iyaka da ita da ya"yanta Tunda bata da Mutumci..! Ba wanda ya kara mgana Sanin Halin Mamanmu in ta fara Fadan kan Amina bataji bata gani,Aminar batace komai ba abincinta take ci yunwa take ji Sosai,Jidalinta yafi Tashi ne inTaci ta koshi Hanne tatafi gida Domin Laifin Sa"adatu ya Shafeta Tana Ma Amina Mgana tayi kamar bata jita ba Abida ita ta Fadama Hajiya Abunda yafaru Ran Hajiya ya baci ana Falon Malam ana cin abinci Tace Abida ta maimaita abunda ya Faru yau a makaranta Ran Baba Malam ya baci matuka Anty Amarya ta Bude baki zatayi mgana ya Daka mata Tsawa. Nan take yasa Shamsu yayi ma Sa"adatu Bulala goma lafiyayyu da Jan kunnen in aka kara jin mgana makamancin wannan abakinta sai ta gane kuranta awajen Baba Malam ya kalli Matansa Cikin Kaushin Murya yace"In ma acikin ku akwai wacce take Kitsa ma ya"yanta Sa'idu bakomai bane a wajena Tayi kuskure..Sa"idu D"a na ne..Shine Babban yarona sai da na Sameshi na Samu UMAR..! Sannan nan gidan da Gidan Sa"idu Duka abu Dayane ya"yansa Jikokina ne..Har Abada..Kamar yadda ku da ya"yanku kuke da iko da Gidan nan da Dukiyata da ni kaina kuke alfahari dani Haka Sa"idu da yayansa zasu yi Na Rantse da Allah in na kara jin wata mgana mai kama da wannan Dukkanku Daga ku har ya"yanku sai naci Mutumcinku..! Ku tashi ku bani waje mutanen banza Ke Sa"adatu ban gama Dake ba..Ki Taka kije har gida ki bama Mamana Hakuri in ba Haka ba Wlh sai na maidake Kauye nayi miki aure kinji ma na Rantse tashi ki bani Waje..! Ya karishe Fada Ransa na kuna da wani kunya da Nadama yaya zai ji in Sa"idu yaji wannan mganar Tun bayan Haduwarsa da Sa"idu bai Taba ganin Daraja da kima kamar yadda Sa"idu ke ganin kimarsa ba ko Umar baya masa Biyayya irin yadda Sa"idu yamai dashi komai nashi ba..Shekaru nawa ya kwashe yana gina Iylansa Domin su zama abu Daya ammh ya Fahimci akwai babban baraka barakan in da ta barke baza tayi masa Dadi ba ya zama Dole yayima Abun Tufkar Hanci Ransa yayi Mummunar bacin da ko matansa sun Dade basu gansa Cikin wannan yanayin ba. Sa"adatu kuka ta saka ma Anty Amarya Tana Fadin"Anty ki bama Baba Hakuri kada yakaini Kauye..! Anty Amarya Farar mace alkyabban Mata itace kadai mai kananan Shekaru acikin Matan Baba Malam faman Zagaye take a Tsakiyar Falonta Ranta ya baci meyasa komai sai Sa"idu da Ahalinssa ta tabbata ko Yayan Daya Haifa da Cikinsa Mallam bai musu soyayya kwatankwancin yadda yake kaunar Sa'idu da Iyalansa .! SA'IDU....SA"IDU..SA"IDU..! Halitta kwara Daya da Tun Shigowarta Rayuwar Malam ya Hanata Rawan gaban Hantsi komai na Mallam din kafin ya"yansa suzo agaba Sa"idu ne kan gaba meyasa haka..?Tasan itama ta fito Daga gidan Manyan Mutane kakanta Shehin Malami ne kafin Rasuwarsa Malam kamar Dalibi yake garesa Duk garin Dutse ba wanda baisan Malam Armaya"u ba Shine ya Haifi Mahaifiyarta,sannan shi ya Daura mata Aure da Malam lokaci Rayuwarsa Duk da itama Tana ganin Baba Malam din a Talabijin yayi mata Duk da ya kasance ya Manyanta ammh bata Damu ba azatonta zatazo Tayi Mulki sai kuma taga akasin Haka Bamai iya Mulki agidan Baba Malam Suna Biyu ne ke yawo Daga na SA"IDU sai na HAJIYA BABBA..! Suna da matukar Tasiri a Rayuwar Baba Malam din.. Sa"adatu ce ta kara kallonta yadda tayi Zurfi wajen Tunani Kafarta ta taba Tana Fadin"Anty baki ce komai..? Dayake Tun zuwanta gidan Anty Amarya ake cema yasa bayan ta Haihu Sunan yabita har bakin ya"yanta. Anty Amarya ta Sauke ajiyar rai kafin ta koma kan Kujera ta zauna Kusa da Sadiya Dake kallonsu kala batace ba Daman ai bata da Hayaniya. Sabeeha na gefe itama ta Damu da ganin Sa"adatu na kuka. Kanta ta Dafe kafin ta Dago Tana Fadin"Mafita dayace..Kiyi abunda yace..! Sa"adatu tace"Naje na bama Amina Hakuri Anty..? Kai ta gyada mata kafin tace"Eh haka nce..Kinsan Waye babanku..Tunda ya Rantse bazai Sauya mgana ba..kuma bazai Fara kaffara Saboda ke ba Sa"adatu..! Sa"adatu zata sake mgana ta Daga mata Hannu lokaci Daya tana Fadin"Kiyi abunda yace..Koma meya Faru ke kikaja..?Amina..Amina wannan Shegiyar yarinya kinsan yadda Babanku ke Somta baya ganin Laifinta me yasa kika Biye mata..?kin ja An Tozartani gaban Kishiyoyi Kin jamin Kallo da Zubewar kimata a idanuwan Malam Kimar da nayi Shekaru ina Ginata Sa"adatu Kin jawomin Kafar Zargi da kallon Reni Daga ya"yan Cikin gidan nan Sa"adatu ki kyaleni da abunda kika jawo na raasa yau ki barni nayi Tunanin yadda Kimata zata dawo a Idanuwan Malam..Naki mai Sauki ne ki je ki bama Amina Hakuri Shikenan Mganar Zata kare..! Daga haka tana Huci Fuu ta shige Bedroom dinta ta bango Kofa Sadiya ma ta mike batace komai ba ta wuce Dakinsu aka bar Sa"adatu da Sabeeha. Gaskiya Anty ta Fada Mallam bazai Sauya mgana ba in tana son Tsira Daga Fushin Malan tayi yarda yace. Kwana Tayi kuka da Bakimciki Zata kaskantar da kanta gaban Amina sai dai bata da Mafita Baba mganarsa Dayace kuma ba Sauyi. Dole yasa da Safe tana Shiryawa na Tafiya makaranta,Tace Sabeeha ta rakata gidansu Amina Lokacin da taje gidan kowa yayi mamaki Saboda ya"yan Anty Amarya basa zuwa gidan Sai da wani Dalili mai karfi Sanda Take bama Amina hakuri ita tasani Aranta wani abu ya faru Sai da sukaje Makaranta Hanne take Fada musu yadda akayi Amina tayi Dariya ta Hura Hanci kafin tace"Amina Aminene..Wlh badai ta Mutum ba sai Allah..! Tundaga Lokacin Sa"adatu ta Fita Sabgan Amina bayan Baba Malam ya Kirasu ya musuvFada sosai atare sannan yasa suka yafi juna baisan na Ciki na Ciki ba ita kuwa Anty Amarya Sai da tasan yadda tayi mallam ya yarda ba wajenta Sa"adatu taji mganar ba Har Kara Dukanta tayi Saboda malam din ya yarda da ita kuma Hakanta ya Cimma Ruwa Saboda Har gidansu Aminan taje ta kara bata Hakuri ta yi mgana da Mamanmu wannan abun yayi ma Malam Dadi har ya yarda da Gasken Amarya bata da Masaniya kan abunda Sa"adatun ta aikata yarinta ke Damunta daganan aka bar mganar ammh Dai Sa"adatu da Amina sai dai kallo Daga nesa basa mgana ballatana wani abu ya kara Shiga Tsakaninsu. Amina bata Sauya ba Tana nan da Jidalinta a gida da makaranta,acikin Satin ma sai da aka bata Suspention na Sati Daya saboda ta fadama wata yar ajinsu Anty Sara Basic Teacher dinsu Tana warin maza ita kuma ta Fada har mgana takai kunnen Anty itakuma Anty Sara ta kai mgana Gaban Sir Gumel ya Rabbata mata Kora Daman ta Taba yima wani English Teacher dinsu Dariya dan Bautar kasa wai wuyansa kamar Lema Mgana Har sai da Ya Jafar yazo makaratar Duk da Dukan da Amina taci agida da makaranta baisa tayi Nadaman abunda ta aikata ba to wannan karon Allah ya Ceceta Mamanmu bata bari mgana takai kunnen Aba ba ta kai ma Baba Malam Waya kadai yayi mganar ta wuce ammh da Sharadin in ta kara cin Zarafin wani malami kora ce Baba Malam yace ya yarda Yayi ta ma Amina Fada da Nasiha wanda yasa Jidalinta yadan Ragu ammh Dalibai Kam bata Daina ba Kafin atashi an sha Fada in an tashi ma Amina yi take Wani Lokacin ya Shamsu ke taka mata Burki. Da gaske ne mganar Auransu Ya Zulaihat ya taso kamar yadda Hanne ta Tsegunta ma Amina,Ya Zulaihat wani Dan Sanda zata aura Dcp ne anan garin Jigawa kuma yana Daga Cikin Daliban Malan Duk Ranar jumma"a Wajensa yake zuwa Daukan karatu Daga Jigawa shi dan asalin kano ne aiki ne ya kawosa nan kuma Baba Malan yana da Hannu wajen zamowarsa a wannan matsayin. Ya Aisha kuma a kaduna zatayi aure Itama wani Soja zata aura sojan kasa ne mai Mukamin Captain,shi Mahaifinsa ne abokin Malam sai Ikram da anan garin Gumel zatayi auran kuma agidan Sarauta Domin Jikan Sarkin Gumel zata aura Sai Sadiya da zata Auri Yaron Yayan Anty Amarya yana America yana Karatunsa har yafara aiki achan kan abunda ya Shafi Dilar magunguna. Duka ya"yan Baba Malam auran gida ake yi musu yawanci ya"yan abokan Malam ne da kuma Dalibansa bashi yake Hadin ba Baya Tallar ya"yansa Sai dai akwai masu son Hada Zuru"a Dashi Sosai Da an zo Tambaya zai yi Bincike in yayaba da Hali da kuma abunda Annabi yace aduba shi zai ga wacce ta Dace da Mutum Wata Shida kafin mganar tataso sai ya bada Izinin ganawarsu da juna Sai dai Kiji ance ki Shirya yau kina da Bako Gabadaya yan"matan gidan haka yake Faruwa Dasu Mazan ne kai zaka nemi abunka da kanka ya aura maka sannan baya bambamci Da gidansa da Gidan Baba Sa'idu komai na auransu shi yake Gudanar dashi babu wani bambamci Shi kanshi Aba sai da yaji Baba Malaman yana Fadamai wane kaza yazo nema ma Dansa aure acikin Gida na yanke Hukunci cikin ya"yanka zai zoya gana da Daya daga Cikinsu nashi Shima Bin Umarni ne Domin Malam ya wuce komai awajensa. Mganar auran tatashi Sannan kowa yasan Hajiya Babba itace ke Rufe Amaran da komai itace Malam ke sawa agaba Kayan Daki kuwa da komai da komai Daga Dubai ake Oda sai dai akawo kayan abinci kuwa Store ne guda basu da mtsalansu Domin ashekara ba wanda yasan adadin abunda Baba Malam ke Nomawa. Duka duka nan da Wata Biyu Baba Malam yace za"ayi Bikin Tunda su Ya Zulaihat sun gama WAEC har sun Fara Neco dinsu sannan za"ayimusu Walimar Sauka ana gobe Daurin auransu ne,Shiyasa Duka bangarorin ke ta shiri Amina ba Haka taso ba taso harda ya Zeenatu Daki ya zama Daga ita sai Hamida ammh itama ai wata Shekara ne zasu bugar dasu kamar yadda kowa ya sani. Bikin yana Saura Wata Daya Dan Malam Dake Madina yayo ma Malam Waya yace cikin Satin nan suna Tafe Shida iyalansa Hutun karshen Shekara da kuma Bikin Sannan yace Jirgin yawo zai Fara yo gaba da kayansu su sai daga baya zasu iso. Sai Shagalin ya ninka na Baya Ga yadda aketa Murna ma zakasan ko waye wannan ana Matukar ji dashi agidan Anty Amarya sai Shiri take Saboda Zuwan SAKINA nageria Mganar Shirin Biki kuma yana Hannun Hajiya Babba ne da Hajiya Uwa Ita da Hajiya Nasara yan Shawara ne da kallo kawai..,! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo(Besty)Alherin Allah yakai miki aduk inda kike* *🅿️05* *SHEIK YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA* Haifaffan garin Bazanga ne Dake Yankaji B karamin gari ne cikin karamar Hukumar D'anja ta Jahar katsina,Mahaifinsa Maigarin Bazanga Abdurrahaman da mahaifiyarsa Aminatu auran zumunci ne a Tsakaninsu Domin suna matsayin abokan wasan juna ne. sakamakon Bazanga karamin gari ne yasa Gabadaya Rabin garin Dangin Abdurrahaman ne da Aminatu wanda suka fito daga Tsatson mai Maigarin na Bazanga Tun Tale tale Duniya tana kwance. Kowa yasan garin bazanga gari ne mai yalwar amfani gona da kuma Kyautata Kiwo,Dukiya da arzikin Baba Malam ba Haye yayi ba Gadonta yayi Tun asali Mahaifinsa ya Rasu yana da Shekara goma aduniya ya barsa Da Mahaifiyarsa da Tarin Dukiya na gadon gonaki da kuma Dabbobi. Abu Daya Yususa ya rike dayasa ya Fara Fafutukar nemam Ilimi shine Kafin Mahaifinsa ya rasu ya Fadamai Yunusa kada ka zauna ka fita ka nemi Ilimi Domin Watarana kazo ka iya rike Dukiyar da nabar maka sannan komai sai da ilimi Yunusa da wannan kalmar yasa ya matsa sai da aka kaisa Makarantar allo acikin garin Bichi Dake kano yana da shekara goma sha Daya alokacin Aminatu taki yarda sai dai kuma Hujjar da aka bata na Neman Ilimi yasa ta amince Sannan kuma abaya babu Macuta masu hawa kan Dukiyar maraya,Yunusa bai Samu matsalam Komai ba Saboda wan Mahaifiyarsa shi ya Dinga Noma Gonakin Daya gada da kuma Kula da Dabbobinsa. Yunusa wannan Nasihan ta Mahaifinsa ita ke rike dashi yasa Duk inda yaje ya zama mai kwazo sannan Yana da baiwar Dauke abu akansa Lokaci Daya shiyasa kafin ya Rufe Shekara Uku ya Sauke aqur"ani Cur asaman kansa Daganan ya Dawo gida ya Fara Cucukin yadda zai Fara Karatun boko Domin ya Fahimci ko na addinin gareka in baka da na Boko baya Tafiya Daidai. Lokacin yana da Shekara sha uku A Danja ya fara primary dinsa Tunda alokacin Yara da girmansu suke shiga Karatunta,Saboda Ilimin bai yawaita kamar yanzu ba yana Gabda gama Primary Aminatu ta rasu sakamakon Saran Maciji abunda yasa Yunusa ya bar Bazanga kenan kwata kwata ya nausa neman Ilimi Duk da kananun Shekarunsa sai dai ya bar Kula da Dukiyansa Hannun wan Mahaifiyarsa Bala. A makarantar kwana yayi Duka Secondary School dinsa sannan bai Zauna ba yana neman Sani a Duk inda ya Samu kafin ya gama yayi suna Ba wanda baisan sa ba wajen Kokari da Kuma Sanin ya kamata ta Fanni Addini da kuma Bokon Ba inda akayi masa Zarra yana zuwa gida Lokaci Bayan Likaci in Bukatar kudi ya taso mai yakan je wajen Kawu Bala ya basa Kudi Domin yayi amfani Dashi Wajen Karatunsa. In suka samu Hutu baya zama Waje Daya yakan shiga Har kano wajen Malaminsu bai yadashi ba yana Daukan Karatun Sauran Littafi a wajensa Shiyasa Lokaci Daya Ilimin Yunusa ya shahara batare da an Farga ba. Bayan ya gama Secondary Diploma yayi kafin ya bar karatun ya koma Zurfafa a neman ilimin addini Duk inda ya san akwai wani Malami mai karantar da Al"umma Yunusa baya zama Waje Daya yana zuwa ya zauna aduk inda yasan zai karu zai kuma Samu ilimi bai koma makaranta ba Sai da yasan abubuwa da yawa ya Sauke wasu Littafan addini da Hadisai bisa kansa sannan ya koma makaranta yayi Degree dinsa akan Islamis Studies anan Abu Zaria. Kafin ya gama yayi suna ya Rike Shugaban Dalibai na Bangaran addini musulunci MSS, Sannan Kafin Gamawarsa har Limanci yayi zaman yi a masallacin Cikn makaranta sannan bashi da girman kai ko ka girmesa indai kafisa Sani zai Duka ya nemi Sani a wajenka Sannan shine Overoll student a site dinsu sannan bayan ya gama ya Zama Shine First class alokacin Babu wanda alokacin baisan Yunus Abdurrahaman Bazanga ba Ana ganinsa wani Dan kauye alokacin sai dai mai Tarin hazaka da Ilimi wanda da Fara raina masa wayau akeyi sai Daga baya aka Fahimci iliminsa da Baiwarsa. Ya samu Shedar kwalin Degree sannan kuma ya kara Sanin addininsa Sosai,Tun yana da Kananun Shekaru ake mai Lakabi da Malam sannan alokacin ba kasafai akesamun yan Baiwa kamarsa ba yasa Takardarsa ta bama Department dinsa mamaki da Taimakon Shashen addinin Musulunci na Jami"ar Ahmadu Bello Yunusa ya samu Scholorship na Tafiya Jami"ar Madina yayi master dinsa kan Islamis Studies Daukakarsa ta Farko da bai Taba Tsamani ba Domin alokacin har ya koma Gida yana Taya Kawu Bala Kula da wasu abubuwan kafin ya kuma yasan inda Zai Lula sai ga Takarda ta Fito Dauke da Sunansa sannan Ita Jami"ar ita tayi komai Har kudin Jirgin Tafiyarsu. Shiyasa Har gobe bazai manta da Malamnsa na Abu Zaria ba Domin sune matakin Zamowarsa koma meya Zama arayuwa. Acham Madina wata irin Rayuwa Yayi Domin waje ne garin Manzon Allah sannan Zaka ga abububuwa kala kala da bakayi Tsamami ba bai da matsalan Wajen kwana da abinci Sannan Har kudi suna samu bai zauna ba,yana Fita yayi aiki ana Biyansa Sannan Nemam ilimi yunusa bai gaji ba Larabawan Malaman nan nasu Haka yake binsu Daya bayan Daya yana kara Fahintar abunda bai Sani ba Yunusa shine Yazo Daga Jahar Katsina Sannan akwai Sauran bakaken Fata irinsa Da kuma Labarawa mazauna chan din sai dai Duk da Haka Yunusa ya Dokesu Duk da ya Sauya Karatun nasa wannan Karon yama Karantar Hadith and Islamis Studies ne a islamic University of Madina. Ko Larabawan wucesu yake yi basa iya Ja da Yunusa shiyasa tun kafin ya gama kowa yasan Ustaz Yunusa Abdurrahaman bazanga Daga Nigeria Ita Nasara Daman ta Allah ce sannan kuma da Dagewa anan din ma Shine ya Fito da Firstclass kaf a Site dinsu ba ga yan Madinan ba Har ga Bakaken Fata yan Nigeria Jami"ar ta karramasa Sannan ta roki data rikesa yayi mata Koyarwa Duk da alokacin Shine mafi karancin Shekaru acikin Malaman wannan itama wata nasara ce yana da Shekaru Ashirin da takwas a Duniya ya samu wannan Daukakar Daga Ubangiji Duk da yana son ya koma gida kasarsa ta amfana da iliminsa Da kuma Shima yana ganin ilimin bai isheshi ba yana Bukatar kara Sanin Wasu abubuwan. Ya zauna Amadina Tsawon Shekaru Biyar ya samu Cigaban Rayuwa sosai ya Samu Daukaka da kuma arziki Ta Dalilin iliminsa sai dai bai manta da gida ba yana Turo ma kawu Bala Kudi Daga chan shi kuma batare Daya Fadamai sai ya rika siyan Dabbobi yana karamai Cikin Garkensa. Alokacin Yunusa yaji gida yake son Dawowa ba yadda Jami"ar madina batayi dashi ba yaki Tsayawa Dole ta Rabu Dashi ya Tattaro ya Dawo Mahaifansa da kowa yake mamakin Yunusa ne ya koma haka..?bakinsa ya Hade da Labarci Da Turanci Hausa ma Kadan kadan ne yake ji yayi matukar mamaki yadda yaga Dabobinsa sun kara yawa sai da Kawu Bala yayi mai bayani Sannan ga amfani Gonar nan da ake Fitarwa Duk Shekara bayan ana Fitar da Zakka Daman Tun a shekarun baya ya hana Kawu bala Noma Sai dai biya suke ana Noma Gonakin Duk Shekara shiyasa yana da kananun Shekaru yana da Dukiyar da baisan iyakarta ba. Da Farko anan bazanga ya fara zama Yana koyama matasa masu tasowa Cikin Abunda ya Sani Rasuwar Kawu Bala yasa Yaji garin ya fita kansa,Dabbobinsa ya saida wasu wasu kuma yayi kyauta dasu sannan amfanin gonarsa ya Raba ma yan garin Gonakin ne kawai bai saida ba ya barsu Domin Watarana ya Kalla ya Tuna da Mahaifansa. Daga garin bazanga Yunusa Maidurguri ya zauna yayi Shekaru uku achan yana neman ilimi kuma Shima yana karantarwa sannan yana Noma yana kiwo Domin shine gadonsa Tun kaka da kakkanni Duk inda yaji wani Babban Malami mai Karantar da addini Yunusa sai ya taka baida Girman kai sam shiyasa yake Samun Nasaran Rayuwa Daki Daki. Hajiya Babba mai suna Zainabu yar Garin Bama ne alokacin yan Boko Haram basu Rikita garin ba Sannan a wajen Mahaifinta ya zauna Mallan Zanna yayi shekaru ukun nan yana neman ilimi Da zai tashi Tafiya ya Dauki Zainabu ya bashi auranta Saboda ya yarda dashi. Hajiya Babba ba yar kowa bane Mahaifinta Malan zanna malamin Zaure ne bai da komai sai Rufin asiri Duk garin da Yunusa ya zauna zai yi Noma da kiwo in kuma ya tashi Tafiya zai sai Raba biyu ya Dauki Rabi sannan ya bar ma Inda ya Zauna Rabi haka ta Faru da Malan Zanna Da karamcin da yayimai Duk da ya Fadamai Asalinsa da kuma Burinsa na neman ilimi Har ya koma ga Allah. Malam yunusa ya zauna agaruruwan Nageria baisan iyaka ba Duk inda yaji Labarim Malami sai yaje ya nemi Ilimi Shima ya Bayar Daga Cikin abunda ya sani Sannan Dukiyarsa ya zama kamar Rabata yake duk inda ya Zauna ya sami Riba sai ya bar Abunda yazo Dashi ya tafi da Ribansa Shiyasa Acikin matansa ba kamar Hajiya Babba ita tasan shi tun yana matsayin Malam Yunusa ta kuma yi kokari da Jeka kadawon da suke yi shi da ita har Kuma alokacin ko Fegin Fili bai dashi na kansa Duk inda yaje za"a basa Gida ya Zauna har sai ya gaji ya tashi Tunda alokacin Duniya na kwance Malamai Darajasu akeyi sannan ana Kimantasu da musu kallon su din magada Annabawa ne ba kuma kamar yanzu da suka yawaita ba Alokacin basu da yawa. Agarin da Malam Yunusa ya fara Zama agarin Gusai ne anan ya siya Gida mai suna gida Suka zauna Domin su samu natsuwar zuciya Shida Zainabu Tunda Tana da karancin Shekaru malan zanna ya aura masa ita kimamin Shekaru goma Sha Biyar alokacin. Yayi Shekaru akallah zasu kai goma agarin na Gusai Anan ya bar Zainabu sai dai yana yin Tafiye Tafiye ballatana alokacin Malamai sun Fitar da da"awan da suke zuwa gari gari suna yi Domin Sanar da addinin Allah kuma Malam Yunusa yana Daga Ciki bayan Haka a Inda yake yana karantar da Kimamin Dalibai da baisan adadinsu ba Sannan itama Zainaba Daga Cikin Gida Tana karantar da mata kafin kace me Sunan Malam Yunusa yayi Tambari a garin Gusai da kewanta ballatana kowa da arzikinsa ya gansa Yana da katon Fili kusa dashi nan yake kiyonsa da masu kula dasu samnan yana da gonakinsa na garin bazanga da ake Nomamai Duk Shekara sannan Duk garin daya zauna yana samun kyautatawa da kyautar gonaki da Dukiya tunda bai Taba amsar ko Naira Biyar Domin wani ya amfana da Saninsa ba. Shikenan Kafar Nasararsa sai ta bude alokacin yan Siyasa sukayi Tunanin irin nasu ne, suka fara zuwa mai da Bukata sai dai yana kokarin Sanar dasu shi baya Shirka baya Duba ammh in kace ya tayaka Rikon Allah Domin Biyan wata Bukata naka zai Tayaka wannan Dattakomsa nasa da Wadatar zucci da ko Duniya zaka basa bazai karba ba,Yaje Saudiya Da kudinsa Har Sau biyu ballatana Lokacin yana Madina Duk Umura da Hajji Dashi akeyinta. Shikenan kimarsa ta Karu aka Fara Gayyatansa Taron karama juna Sani na Malamai sannan Har ana gayyatansa Gidajen Radio da Gidajen Talabijin Abunda ya karamai Daukaka yana Daraja na sama Dashi Malamai haka yake Daukan su Tamkar Madubinsa komai girmamsa haka zai Duka gabanka yana neman Sani wannan Dabi"a ta Siyamai Soyayya da Daukaka da Nasara Lokaci Daya da ba"a taba Tsammani ba. Har kuma zuwa Lokacin da Daukakar nasa ta fara ko bari Zainabu bata tabayi ba Duk da yana Fatan Samun magaji bai Taba Korafi ko nina wani abu da Zainabu zata Fahimci ya Damu ba Mutum ne mai Tsantsani da Tsoron Allah da Wadatar zucci. Ana cikin Hakame kwatsam Allah ya Hadasa da Shaharran Dan Siyasa nan wanda ke rike da Mukamin Kakin Majalisar Ta Jahar zamfara. *AMINU GUSAI* basu hada komai ba sai da sun Taba Hada yin Makarantar allo anan garin na Bichi kano A talabijin yaga Malam yunusa yana ganinsa ya ganesa Domin alokacin ba wanda baisan Yunusa bazanga ba, Yayi Tattaki har gida yaje ya samesa sukayi Zumunci da Tambayan bayan Rabuwa,Aminu ya sanar dashi bayan Sun yi Sauka yayi karatu shima Har matakin Masters sannan kuma sai ya Fada Siyasa Daman gidansu gidan yan Boko ne da kuma Tsofaffin masu Kudi Dayake awanchan zamani Karatun allo yana da Daraja ba kamar yanzu Domin yawancin manyan mu na yanzu in da zasu baka Tarihinsi zaka Ji cewa sai da suka fara da Karatun allo kafin su dawo su Dora na bokon Aminu yaji mamakin ganin yadda Malam Yunusa ya koma sannan ya kara yarda ma kamsa yana na nan bai Sauya ba Tunda Har ya iya bari Garin Madina yazo kasarsa yana Wahala. Daganan Zumunci ya fara Har Ya kawo Iyalinsa Hadiza da Dansa Daya mai Suna SA"IDU mai kimamin Shekaru goma sha biyar alokacin tun gaanin Farko da Yunusa da Zainabu sukayi ma Sa"idu ya shiga ransu Matuka suna son yara suna kewarsu sai dai Allah bai basu ba,Sannan ga Hadiza mai kunya da karamci Sa"idu shima yana son zuwa gidan Malam Yunusa kodomin yaga Dabbobi kaunarsu acikin Ransa yake Ranar har cema Malam Yunusa yayi Baba ina son ka bani Rago in na kara girma na kula Dashi alokacin gaban Dukkan ne ya Fadi mganar Malam Yunusa ya Dafa kansa Cikin Kauna yace"Insha Allahu Watarana kai zaka kula dssu Sa"idu..Fatana ka Dake da Karatu..! Wannan mgana ta saka Sa"idu Farinciki kuma abunga ga yaro ya rike mganar acikin kansa. Tundaga Ranar yake murna yana Fadin in ya girma zai zama mai kula da Raguna kowa yana ganin Shirme ne da yarinta. Duk da alokacin Zainabu zata girmema Hadiza ita Allah ya bata Haihuwan da Wuri tana da kananun Shekarunta Ammh sun zama kawaye tunda Zainabu batasan kowa agarin ba sai suka zama kamar yan"'uwa koda yaushe suna ziyatar juna Sannan Sa"idu duk karshen Sati wajensu yake yi kaunar yaron ta fara ne tun Tuni Sannan Shi kauna Allah ke hadashi ma Mutum ba. Akwai Ranar da Malam Yunusa suna mgana da Aminu ya kallesa yana Fadin"Aminu ina kaunar Sa"idu ina jinsa kamar dan cikina..Ina ji kamar ya zauna Dani har Abada..! Alokacin Aminu Dariya yayi ya Dafa Kafadar Malam Yunusa yana Fadin"Haba yunusa ai ni da kai mun Zama Daya..Wlh har araina na yarda da wannan kaunar Dake Tsakaninka da Sa'idu Dama Hadiza nada juna Biyu sai ta Haifa mana wani kai kuma ku rike Sa"idu kai da Zainabu har abada na tabbata ko bayan Raina Sa"idu zai fi Alheri Dakai Fiye Dani..! Wata mganace da Malam Yunusa ya Dauketa kamar Fadice sai dai ba Haka bane Har azuciyan Aminu haka take Malam Yunusa bai Tabbatar ba sai da Aminu ya Tara Duka yan"uwansa ya Fadamusu ba wanda yayi gaddama Sanin Waye Malam Yunusa Shiyasa kowa yayi Na"am da Batun Hadiza ma bata kawo Damuwa ba macece mai kunya da kawaici Duk da kasancewarta Bazanfara gaba da baya. Malam Yunusa yayi kukan Murna Aranar da Aminu da Hadiza suka Dauko Sa"idu da duka kayansa suka kawo musu shi Har abada shi da ZAINABU sun kasa Daina kuka suna ganin kamar mafarki ne sai dai Zahiri ne,Sa"idu bai damu ba ya Saki Jikinsa Sosai Saboda Dabbobi daman yafi son gidan Baba Malam kamar yadda Sa'idu shine Mutum na Farko Daya Fara Radamai wannan suna kuma yake binsa yana alfahari dashi. Abu kamar wasa karamar mgana ta zama ba Sa"idu ya dawo hanun Malam Yunusa da matarsa zainabu abun Tsusayi Cikin Da Hadiza ta Samu ta Haifeshi ba rai ammh duk da Haka basu Damu Sa"idu ya cigaba da zuwa makarantar Boko sannan kuma Malam da Zainabu suna Karantar dashi karantun addini acikin Gida sannan suna iya bakin kokarinsu wajen Tarbiyansa da Rike Amanar da aka basu Wajen sau uku Hadiza na Haihuwa ba rai sai ana Hudu ta Tsaya macece mai Suna Hafsah sunan Mahaifiyar Aminu ce suna cemata Husai sai kowa ya samu nashi Sa"idu na zuwa ganinsu Lokaci bayan Lokaci kamar yadda suma basa gajiya da Ziyartan Juna. Tun alokacin ana ta yima Malam yunusa Tayin ya"ya Domin ya kara aure ko zai Samu Haihuwa sai yace A"a Domin Zainabu nada kima awajensa,Sannan koda an mai mganar Haihuwa sai yace Sa"idu ya isheni Rayuwar Duniya da Lahira Saboda irin kauna da Shakuwar Dake Tsakaninsu suna bashi Dukkan wani Gatan Duniya sai dai suna kokari wajen Kula da Tarbiyansa. Cikin Ikon Allah kamar yadda Malan Yunusa yace Haihuwa ta Allah ce Hakan ce ta kasance Domin Sa"idu ko Shekara uku bai yi da Dawowa Hannunsu ba Zainabu ta samu Ciki kuma Haihuwarta na Farko Ta Haifi Namiji Malam Yunisa ya saka masa Suna UMAR IBN YUNUS..! Koda zainabu ta Haihu mganarsa Dayane Sa"idu ne babban yaro na Domin kafin na Samu Umar Sa"idu na Haifa,Duk da Mutane sunsan ba Dansa bane ammh suna Girmama Kaunar dake Tsakaninsu kuma koda suka samu nasu babu abunda ya Sauya Daga soyayyar da sukemai. Yayinda Aminu Daga Husai Hadiza bata kara ko barin wata ba kuma basu Damu ba Tunda Da ga Allah ne sun Tabbatar Sa"idu yayi Dace da iyaye nagari kuma ko bayan ransu Watarana sai yayi alfahari da hakan Tundaga lokacin Haihuwa ta Budema Hajiya Babba Daga Umar tazo tayi Nazir wanda Tsakaninsu ba Nisa alokacin kuma Malam Yunusa ya kara aure Shima Bashi matar akayi sun je Da"awa garin Tsafe na Jahar Zamfara gidan Malamin da suka sauka Malam Hamza ya Dauki Yarsa Kwara Daya cikin jerin ya"yansa Uwani ya bama Yunusa shi kuma bazai iya Bijiremasa ba ya karba Hannu Bibbiyu achan aka Daura aure sai dai ya Dawo da mata kawai Sannan bai samu matsala da Zainabu ba ta karbi Uwani Hannu Bibbiyi suka cigaba da zaman Amana ko ita sai Daga baya tasan ba Malam ya Haifi Sa"idu ba shima sai da ya Fadamata ta yarda ammh tana Girmama wannan kaunar Daga Malam din har Zainabun da ya"yanta basu da Mganata sai ta Sa"idu ko"ina kaje agidan nan Sa"idu ne wannan kaunar Daga Allah ne. Haka Rayuwa ta cigaba da gangarawa da Dadi ba Dadi Malam na Cigaba da nenan sani da Da"awa sannan Lokaci Daya yana karantar matasa Abunda ya sani na Addini Alokacin Aminu gusai akayi Chanjin gwannati bai samu Kakin majalisa ba sai aka Nada wani Daga Shekarar kuma Jinya ta kamasa na Ciwon kafa Daga Sama Sama sai abu ya Zarce baya iya tashi Sai dai a kwantar atayar Jinya tayi Jinya anyi mganin Asibiti anyi na gargajiyam Duka ba"a Dace ba Sai da Duka Abunda Alhaji Aminu ya Tara ya kare Malam ma bai zauna ba Shima Duk in da yaji wani mgani zai amsomai Sai dai ita Kaddaran Allah Daman Dayace komai Tsalle Tsallen bawa bai isa ya Gujemata ba, Aminu gusai ya Rasu Lokacin da Jinyarsa ta karar da komai ya Rasu ya bar Matarsa Hajiya Hadiza da Yarsa Husai da Sa'idu ko kafin Rasuwarsa ya kara Jadaddama Malam Sa'idu nasa ne har Abada wannan karamcin na Aminu Malam har ya koma ga Allah bazai manta ba. Yaso ya Dauko Husai da Hajiya Hadiza ya Rikesu sai yan"uwan Aminu suke roko alfarman ya bar musu Rikonsu sai ya kyale musu Tunda karamcimsu garesa mai girma ne Gidan yayan Aminu Hajiya Hadizan ta koma da zama ita da Husai ba kyashi ba Hasaada riko na Tsakani ga Allah Sa"idu Lokacin yana makarantar kwana ta Hassan gwarzo Dake kano Aminu ya rasu sai da ya Dawo yaje yayima iyayensa gaisuwa Kowa bashi yake tsausayi ba Domim cewa ake Aminu yayi ma Sa"idu gata Domin Uba irin Malam abun Alfaharin kowani Cikakken D'a ne. Tun Rasuwar Aminu Garin Gusai ya Fita kan Malam Yunusa batare da Shawara da kowa ba ya Fara Binciken yadda zai tashi Daga garin Dayake Tunamai da adalin Amini kamar Aminu,Ba Dadewa ya samu Cikakken bayani kan garin Gumel da yadda Suke da amfanin gona da Sauran Cigaba ba Dadewa ya mallaki Fili a wannan anguwan ta Zango ya Fara Gina iya adadin ida zasu zauna. Sannan ya samar da Katon Fili Domim Kiwo yayi alkawarin Sa"idu sai ya zama wani abu sannan yana da Burin Cikamai wannan Burin nasa. Dawowar Malam Yunusa garin Gumel baima Hajiya Hadiza Dadi ba Saboda ta Saba da Hajiya Babba sosai sannan Husai ta Saba da su Umar ammh bata da yarda zatayi tun anan din ma ba Wahala take ciki Yan"uwan Aminu ba suna Rike dasu tsakani ga Allah Duk da itama Duka na gida ne Shekarun da suka Shude masu yawa ne sannan sun zo da Nasarori da Dadama da kuma akasinsu Sa"idu ya gama Secondary ya Fada Jami"ar garin Dutse yana karantar agric abunda ya Shafi noma da kiwo Ko alokacin Gidan gonar Baba Mallam Dake kusa dasu Sa"idu ke da Ahakin kula dasu Haka Allah ya yisa Zama Cikin Dabbobi sune ke sakashi Nishadi sannam Agarin ba wanda yasan Sa"idu ba yaron Malam bane Sannan kowa Dauka yake Shine Babba sannan su Umar Duka kannensa ne,Malam bai yi kasa a gwiwa ba anan din ma ya Cigaba da Karantar wa Ya Hakura da neman ilimi ya Zauma yana karantar da Duka Dalibin Dayazo wajensa neman ilimi Sannan bai da ina zuwa Da"awa ba duk inda za"a je dashi ake zuwa. Zuwa Lokacin Malam ya Kara auran yar nan garin Jigawa ce Hajiya Nasara ita yar Masu kudi ce sannan zuwa Lokacin Gidan Malam ya fara Cika da Ya"ya kamar yadda yake fata sannan bai manta da Hajiya Hadiza da Husai ba da Lokaci bayan Lokaci suna zuwa suma suna zuwa sannan babu abunda suka nema suka rasa na bangaran Rayuwa. ******* *Bayan shekaru Talatin..* Cigaba da Nasaran Rayuwa da Rashi da Samu ba wanda Baba Malam bai gani ba ya Samu Nasara ya Daukaka bama Nageria ba Duniya gabadaya ta Shaida Iliminsa da Sadaukarwansa kan kasarsa zuwa Lokacin hatta Kasar Saudiya tasan da zamamsa yasan Manyan Mutane masu Saurata da masu Dukiya yasan manya malamai kala kala ta Dalili Jajircewansa da kuma Dattakonsa zuwa Lokacin baisan adadin Daliban Daya rike ya karantar ba kuma ya Taimaka musu suka zama wani abu baisani ba Sai Dai Burinsa ya Cika ya amfanar da iliminsa ga al"umar kasarsa kamar yadda yake Fata. Yayi rashin Amini kamar Alhaji Aminu sannan kuma sunyi Rashin Hajiya Hadiza Cancer ce ta kasheta sannan sun aurar da Husai Tana Jordan da zama ita da Mijinta da iyalanta wanda ya kasance amsader ne mai Wakiltan Nageria Akasar sannan kuma Burinsa ya Cika Sa'idu ya zama wani Jigo..Jigon Dayake alfahari dashi har yau har gobe Sa"idu yayi karatu har matakin Master akan abunda ya Shafi sanin Noma da kiwo sannan baisan adadin Kwasakwasan Daya Hallata kan Abunda ya shafi abunda yake so ba Sannan Bayan haka shi ya bama Baba Malam Shawaran Siyan wani Katon Fili a Farkon gari Dake Hadeja Road Inda suka Samar da Katuwar Gidan Gona babu abunda babu,na kiwo awajen katon Fili ne mai kama da alkarya Guda Abaya iya Dabbobi ne yanzu kuwa da aka Cigaba Har da Kaji da Talo Talo komai fa babu abunda babu Sannan kuma an Fadada abun har da Offices acikin wajen sannan akwai ma"aikata masu kula da wajen da masu Dawainiyar Kwashe kwaiyayan in Kaji sun saka sannan Baban Gidan Gona ne da kaf garin Gumel ba Kamarsa da kewaye. *GIDAN GONAR BAZANGA..! babu wanda baisan da zamansa ba Sannan Sa"idu shi ke da alhakin Kula da komai na Dukiyar Baba Malam,Sannan bangaran Gonakinsa Sa"idu ke da Ahalin kula da komai Daga Daukan masu Noma biyan su Cire amfani gona Fitar da zakka Komai na Hannunsa ne Baba Malam abu Dayane ke gabansa yakan Koyar da Dalibai Kadan Daga abunda ya Sani ammh Gabadaya alhakin Kula da Dukiyarsa da Komai yana Wuyan Sa"idu ne,Tare suka wahala sannan Kusan kula da komai dukiyar ta habaka Jajircewan Sa"idu ne. sannan har zuwa wannan Lokacin Sunan Sa"idu ne gaba abakin Malam kafin ya"yansa Baba Mallam yayi ma Sa"idu Auren Farko da Hadiza Haifaffiyar garin nan Gumel ce sai dai marainiya ce bata uwa bata da Uba ba wani Cikakken Dangi Labarinta yaji ya Tsausayamata Tana daga Cikin marayun da suke samun Tallafi Daga Kungiyarsu na Ahalus sunna Sa"idu tunda yake bai Taba Saba mganar Mallam ba Gabadaya Rayuwarsa ta kare ne a Yimasa Biyayya Da Hannu Bibbiyu ya Karbi Hadiza,Bayan Baba Malam ya gina mai Filin Dake kusa Dashi Daman Tunda ya siyeshi da Sunan Sa"idun ya siya Halak malak. Shekararsu Biyar da aure Har sun samu karuwar ya"ya Biyu Jafar ne Babba ne sai Jadwa sai kuma tazo tayi Jaleela daganan ne ya kara aure da Balaraba yar"uwansa ce Daga Gusai Daga Dangin Babansa suka auramai ita tazo suka Hade kai da mamanmu suma zaman Lafiya da juna. Sannan Daga gefe Dayama Malam ya kara aure da Marliya Itace yarinya Cikin matansa ita yar Garin Dutse ce sannan itama kakanta Malami ne sun gaji arziki da malamanta itama yazo ya Hadata Cikin matansa ta shiga Zazzaga ya"ya Kamar yadda gidan Baba Malam ya Cika da Wadatar ya"ya Haka Gidan Baba Sa"idu Wanda suna ne da su Umar suka sakamai kuma ya bisa,Shi Allah ya basa Haihuwar akai akai ba kamar Mahaifinsa ba da su Biyu kadai ya Haifa ba, Sannan sunan Sa"idu ba arayuwar Malam ba kaf a Duka ahali da Zuru"arsa wannan Kauna Tsakanin BABA MALAM da BABA SA"IDU daga allah ne Kaunace da Duk hassada da Kyashinka sai kabarsu sun Hade sun zama abu Daya da har har gobe Baba Mallam Sa"idu ne agabansa Duk kuwa  ya"yansa sun Girma ammh bakin sai sai ya ambaci Sa"idu kafin su kamar yadda shima Baba Sa"idun duka Rayuwarsa baida wani abin Dubawa Wanda ya zamemai Madubi Wanda shi yake kallo amtsayin komai Daya Taka na Rayuwa sannan yana Mai kauna Kaunar dako Mahaifinsa Daya kawosa Duniya baya masa kwantankwancin kaunar Dayake ma Baba Mallam..Ita Kaunar junansu Daga Indallahine. *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️06* Ayanzu kimanin Matan Auren Baba Malam Hudu Cif ya riga ya Rufe kofar Sannan da albarkan Ya"ya Guda Ashirin Daga duka jerin Dakunan matan nasa. Hajiya Babba keda shida Daga bangaranta Bayan Umar da Nazir sai da aka Auro Hajiya Uwa kafin ta sake Haihuwan Nasir,Daga sai Aisha sai Abida sai karamarsu ta baya baya ce Ta karshe kuma Auta Hannatu. Sai Hajiya Uwa Dake da guda Biyar itama Babban shine Nazeem,Su.Nasir sun Girmemasa saboda sai da suka Dawo Gumel ta dan Dadewa ta Haifeshi,Sai Uzairu,Nazifa da Umaimatu sai Shamsu Ta aurar da Nazifa wacce ke garin Abuja ita da ya"yanta Umaimatu ma Saboda bata da Lafiya ne ammh a ka"idan Gidan Mallam bakya wuce sha takwas yake aurar Dake mazan yaransa ne ke Karatu mai Zurfi. Sai Anty Nasara itama ya"yanta Biyar Fatima ce babba sai Akila sai Ikram,Akilu da Zubairu sune yaran Matasa Sai Anty Amarya ita kuma Tana da yara Hudu Jidda ce Babba saimai bi mata Sadiya sai Sa"adatu karamarsu kuma Sabeehatu. Hajiya Babba ta gama aurar da Duka Mazan ya"yanta Umar Shine Babba yana Madina,Shi Tun farko bai yi Rayuwarsa anan ba Yana gama Secondary Shcool Dinsa Baba Malam ya Turasa Madina Wajen Abokinsa da Sukayi Karatu Tare A madina Kattab,Wanda yanzu yake kasuwancinsa achan Madina Balarabe ne Asalin Haifaffan Garin Ma"aiki wato Madina achan yayi Degree dinsa na Farko kan Islamis Studies sannan yayi maaster dinsa kan Qur"an and Islamic Studies Domin Shi Umar irin Mahaifinsa ne Tarin Baiwa da kuma Daukan karatu ko wani iri ne shima achan haka ya Fita Zakka cikin Sa"aninsa,Shima kamar Mahaifinsa ne sun rike sa achan yana Musu koyarwa Sannan Tuni ya Samu Lasisin zama achan kasar Madina yayi aure Da Sakina Diyar yayar Anty Amarya Data riketa a Hannunta Bayan Mahaifinta ya rasu Shekaru Biyar kenan ammh bata taba ko bari ba sannan da Farko anan Gumel din ta fara zama Sai da ya Samar mata Lasisin zama achan kasar kana yazo ya Dauketa. Umar shima mai arziki ne sai dai komai ya samu na Iyayansa ne da yan"uwansa sannan da yima Addinin Allah Hidima,Shi ya rika aiko da kudi aka Gina wannan Masallacin sannan aka Sabunta gidansu da kuma Gidan Baba Sa"idu. Sannan ginin gidansa kuma baya nan aka Fara har aka gama Duka Alhakin Kula da komai Baba Sa"idu ne Dayazame musu wani jigo kuma babban yaya shi yake Turomawa Shi kuma sai ya Wakilta Jafar da Nasir Saboda shima akwai wasu ayuukan agabansa,Umar bai cika zuwa ba sai dai Waya in ma yazo ya Dade karshen Shekara ne in kuma ta kama yazo din yakan zo yayi kwana uku hudu ya koma Gabadaya Rayuwarsa a Madina ce achan ya Farota kuma achan zai karisa Domin har gidan zama ya mallaka anan kusa da Jami"ar Musulunci na Madina afarko acikin Jerin Gidajen Malamai na Cikin makarantar ya fara zama sai dai Umar mai Kokari ne Tuni yayi Fafutuka ya mallaki nasshi Da Taimakon Uban Dayake Dashi achan Wato AbuKattab. Sai Nazir wanda shine Dan Boko ne Yayi Duka Karatunsa Har matakin Master yanzu yana Lagos yana aiki da Hukumar Tattara Haraji na Kasa Wato (FIRS) Federal inland Revenue Service,Yana da Matar aure Daya mai Suna Hedaya da ya"yansu Biyu Matarsa itama yar Boko ce yar gidan masu kudi ce Babanta ya rike Alkalin alkalai na kasa gabadaya Shiyasa Rayuwarsa kamar ba D'an Malam ba Cikin Boko da wayewa shi da ya"yansa Yana zuwa gaida iyayansa ammh matarsa bata cika zuwa Gumel ba sai ya zama Dole. Sai Nazir Da ke matsayin Likitan yara yana aiki a anan asibitin gwannati na Garin Gumel bai jima da Aure ba Lokaci Daya sukayi Aure da Jafar din Baba Sa"idu shima yayi karatu Abunda ya shafi harkan Tattalin arzikin kasa ya karanta sannan yazo yana aiki da Wani kamfani na Sarrafa Takin zamani gefe Daya yana Taimakama Baba Sa"idu kan Harkan gidan gona. Aisha da Abida basu yi aure ba sai Hannatu,Aisha tana daga cikin wadanda za"a aurar dasu wannan Shekarar sai Dakin Hajiya Uwa Nazem yana Abu zaria inda yake Masters dinsa Shi da Uzairu dake matakin Degree dinsa Nazifa tayi aure Umaimatu na nan sai Shamsu dake Gabda kamallah Secondary School alokacin.. Sai Dakin Anty Nasara Fatima Tayi aure ta nan a garin Dutse sai Akila Dake aure a Katsina cikin Masaurata,sai Ikram wacce itama Tana cikin amaran da za"a aurar dasu alokacin Sai Akilu da Zubairu dake matakin SS1 amakaranta Dayake basu da nisa Haihuwan nasu kusa kusa ne.. Sai Anty Amarya,itama Jidda na gidan Auranta anan Kano,sai Sadiya da itama tana cikin Amaran wannan Lokacin Sai Sa"adatu Sa'ar Hannatu ne Sai Sabeehatu yar kimanin Shekaru goma da wani abu. Bazan ce gidan Baba Malam ba"a zaman Kishi ba A"a ana kishi sosai da Takun Saka ammh cikin Ilimi da Hikima Baba Malam Tsaye yake kan gidansa da tarbiyan ya"yansa sannan Hajiya Babba ta Dauki wannan Girman Daya bata Duk matar da zai aura sai ya sanar da ita ta bi shi tayi mai Biyayya kamar yadda zatayi ma Hajiya Babba. Tsakanin Hajiya Babba da Hajiya Uwani sun fi Shiri hatta ya"yansu ma sun fi Jituwa Duk da ya"yan gidan Gabadaya ahade suke basu da Rabuwan kai sannan Anty Nasara ta Ware kanta Daga ita Sai ya"yanta yayinda itama Anty Amarya ta ware kanta duk da Anty Nasara taso su Hada kansu kamar yadda su Hajiya sukayi sai Anty Amarya taki bada Dama ta Nuna kowa nashi ta Fisheshi. In ma akwai wacce Kishinta ke Bayyana afili Anty Amarya ce tana Takama ita Amarya ce sannan haka Allah yayo ta in bata yinka bata iya Boye maka don kaji Dadi ko acikin ya"yan gidan ba da kowa take yi ba,Shiyasa kowa yasan inda ya Ijiyeta Duk da Aurattaya ya shiga Tsakaninta da Hajiya Babba basa Shiga Harkan Juna Hajiya ta kama kanta Ta ja Girmanta Dole Anty Amarya take bata wannam Girman a matsayinta na Uwargidan Malam kuma uwa ga Mamyan ya"yansa. Auran Umar da Sakina Rana Tsakane Domin ba wanda yayi Zato ko Tsammani Sai dai kuma Daya Furta ko Hajiya Babba bata kushe Zabinsa ba ammh Ranta taso ya nemi Daga waje ne,ita kuma Har acikin Ranta taso Cikin Manyan ya"yan Baba Sa"idu ne sai kuma hakan ta Faru ko Mallam bata Furtamai ba batasan Shima aransa yaso hakan ba Har yau har gobe auratayya Tsakanin ya"yansa da na Baba Sa"idu bai Shiga ba Duk da yana da Burin haka sai dai bai yima ya"yansa Maza Auran Dole Samin Halin Rayuwa kada azo a Samu matsala Sai dai shi yake kokarin Zabama Matan Inda ya Dace dasu Tunda su tundaga matakin Haihuwansu har girmansu suna Under Contorl ne kuma Har yau har gobe ya"yansa suna Alhafari da Zabinsa sannan inda yakai suna Alfahari dasu Saboda sun Samu Wadattacen ilimi da Tarbiya. A Gidan Baba Sa"idu ma akwai Mata guda Biyu Hadiza da yara ke Kiranta Yaya sai Baralaba da yaran ke kiranta Mamanmu Saboda Gabadaya yaran danatan da ba natan ba Duka Dayane a wajenta itace komai nasu ita Yaya kamar yar kallo ce acikin Gidan Yaya nada ya"ya bakwai ne Jafar ne Babba sai Jadwa sai Jaleela sai Jamela sai Jawahir sannan Amina sai Jawaad Dakin Mamanmu kuma ya"yanta biyar Zulfa ce Babba sai Fatima Zahra sai Zulahait sai Zeenatu sai karamarsu Hamida. jadwa tana auran Yaron Goggo Husai kanwar Baba Sa"idu Dake chan Jordan tana chan itama sai  Jaleela Dake auran Abokin aikin Ya Nazir wanda Sun zo Tare ne ya ganta yayi ma Malam mgana Akayi Bincike aka gano na gari ne aka bashi Tana chan Lagos din da zama Duk da shi ma Dan Jahar kano ne. Sai jamila Dake  Gombe Tana auran wani Contoroller ne ma"aikacin Costume ne,Sai Jawahir Data Tafi Gusai Tana auran yaron wan Baban Baba Sa"idu ita auran gida tayi tana chan gusai ba kasafai suke zuwa gida ba Malam ya hana sai da wani Dalili mai karfi. Sai Zulfa itama tana Zaria Tana auren wani Lecture ne Awajenta ma su Nazeem suke zaune Tunda suna Cikin Jerin Gidajen malama ne na Abu zaria,sai Zahra Dake parthorcourt Tana auran wani Mai kwangilan Titin Sama ne sai Zulahait da wannan Lokacin ne za"a aurar da ita sai Zeena mai bi mata sai Hamida wanda Tsakaninta da Amina Wata Uku ne Amina ce aka fara Haihuwa sannan Hamida,Rayuwar Gidan Baba Sa"idu Kamar Rayuwar gidan Baba Malam ce Domin komai Tare suke Gudanarwa sannan Gabadaya Doka da Tarbiyan Lokaci Daya take aiki bama Haka ba Baba Sa"idu Tarbiyan Malam ne ko shi baya Tsallake mganarsa Ballatana Iyalansa. baza'ace Duka gidajen yaran basa Samun Sakewa ba A"a sai dai ba irin Sakewar nan ta ya"yan da suka Samu gata mai yawa ba suna cikim jerin ya"ya masu samun komai na Rayuwa cima mai kyau Sutura mai kyau komai Tare Baba Malam ke gudanarwa ba Nuna bambamci Gabadaya makaranta Daya suke yi manyansu da yaransu in Sallah Tayi kaya iri Dayame kuma Duka Mallam zai bada Umarnin Asiya Baka Taba Nuna wani bambamci Tsakanin ya"yan Gidansa dana Baba Sa"idu. Suna Samun ilimi sosai Da Tarbiya Mata basa Rike waya sai agidan mijinki Wani Daga cikin su tun kan su Jadwa ba wacce tataba Tsayawa da wani Namiji a waje Da sunan Zence sai wanda zaki aura zaku gana afalon Baba Malam ko Falon Baba Sa"idu ba inda suke zuwa Daga makaranta Sai gida shima mota ce kai kaisu ta Dawo dasu basa ma Fita Ballatana Har wani ya Taresu su Rayuwarsu tana cikin Gida ne sannan Gidan Baba Malam da Baba Sa"idu ba"a Kallo basu ma da kayan kallo Saboda gidan Mahaddata ne ba"a Saka Musu abunda Zai Dauke musu Hankali. Sannan akwai girmamana na gaba Dakai ba Rashin kunya Yaro ko kwana Daya ya baka Dole ka Kirasa Yaya kuma ka Girmamasa Dole kuma in yayi maka Hukunci ka karbeshi Haka suka Taso Tundaga Tushen manyansu har kawo yanzu suna girmama juna da ganin Darajan juna. Ba"a taba Haihuwar Mara kunya Mara jin mgana irin Amina ba,Tunda aka Haifeta tazo Duniya ba wanda ya Huta da Fitinarta da Jidalinta ita Kadai ta Fara Rashin kunya da kin girmama na gaba da ita tun Tana karama sannan ita kadai ta fara yin abu gaban Kanta Amina ba irin Sauran yara bane Duk wannan Hallayar nata yarinya ce mai Shiga Rai Aba yana Matukar Kaunarta Ballatana Datake bala'in kama da Yaya Hadiza sanda sukayi aure ba sonta yake yi ba ammh Hakurinta Sadaukarwanta Nasabanta Kirkinta yasa Ta samu Matsayi mai girma acikin Ransa tana da Kimar da Har Abada wata mace bazata kamota aransa ba. Ba shi kadai ba ya zamo Hatta Baba Malam yana Kaunar Amina Saboda Baba Sa"idu yayi mai kara ya saka sunan Mahaifiyarsa yasa tun Amina na karamarta ta fara Bude ido da Kaunar Baba Malam gareta Har girmanta kuma wannan Kaunar shi yajamata Bakin jini wajen Ya"yan Anty Amarya da suke ganin Baba Malam na Fifita Amina akan Ya"yansa Tun Tasowarta tare sukayi wasan kasa da Hanne da Hamida da kuma Sa"adatu daman Tun alokacin ba",a Shiri kafin agama wasa ayi Dambe fin sau Biyar wannan Kiyayyar tasu ba ta yau bane Ta Dade a zukatan junansu Sannan Kaunar Junansu Tsakanin Hamida da Hanne Daga Allah ne Duk kuwa da Amina ta fisu Baudewar Hali Ammh suna Tare da ita kowani Jidali ta Debe suna Daukansa ya koma kansa.. In nace Amina ta gagari kowa Zaku yarda..?duka ko Fada baya mata komai Domin in duka nasa yaro ya Natsu da ba haka ba sai dai bata Jin ko Daya ba wanda ya isa ya hanata abunda tayi niyya Duka baya Damunta Domin ya Zame mata Jiki Aba tun baya Damuwa da Lamarinta Har ya fara yana Tunanin kada watarana Ta fita zakkan da zata sakamai wani Cutar da zai kaisa kasa ganin Tun tana da kananun Shekarun Idanuwanta a Tsaye suke basu da Ladabi ballatana su Rankwafa. Goggo Husai taso ya bata Amina Tatafi Da ita Saboda Duka ya"yanta Manya maza ne macenta Dayane kuma Tayi aure Baba Sa"idu ya Hanata Saboda yana Tunanin anan ma Amina ya aka kaya ballatana taje Cikin Jajayen Fata hakanan yaji gwara Tana gabansu da wata uwa Duniya Malam ma bai amince ba yace Amina zata Sauya Har yau har gobe yana ganin yarinta ne ke Damunta. Baba Malam bai manta da gida ba Yana Zuwa bazanga kaima yan"uwansa da suke Rage ziyara suma suna zuwa sannan Duk Shekara achan yake Fidda Zakka Sannan Har alokacin ana Nomamai Gonakinsa Daya gada wajen Mahaifinaa sannan bai daina yawon Da"awa ba yana cikin Malaman Kungiyar Sunna alokacin ba garin da basa zuwa Da"awa ko kuma wani Taimako in wani abu ya taso bai da matsala Baba Sa"idu na kan komai zai kuma Kula da komai kamar yadda ya Sani. Hajiya Babba itace Uwa bada Mama ga Baba Sa"idu ko ya"yanta sun sani in Abu ya Shafi. Baba Sa"idu Hajiya bata Zaune bata Tsaye gabadaya ya"yansa matsayin kaka suke kallonta Tasha Fadi Sa'idu babban yaro na ne Balle da bata Kiran sunan Umar sai dai tacemai D'an mallan sunan Daya bisa Har yau bamai kiran sunansa sai Yaya D'an Malam in ya nuna jin Haushinsa sai tayi Dariya Har ce mata ya Taba yi Hajiya meyasa ni bakya Kiran sunana..?ammh kuma kina Kiran sunan Baba Sa"idu..! Dariya take alokacin sai tace"Sa"idu babban yaro na ne..Dashi na Fara sanin Soyayya ya"ya Shiyasa bana masa alkunya..! Tabbas bata masa alkunya Wani mtsalan nasa Baba Mallam saidai yaji sa bakin Hajiya akwai Fahimtar juna da Shakuwa Tsakaninsu hakama Hajiyar ko wani abu ne saita Dauki Waya ta Kirasa Sa"idu in ka dawo kazo ina nemanka..Ko ya"yanta basu isa su san Tsakanin Hajiya da Baba Sa"idu ba,ita din Uwace garesa bada Mama ko Baba Mallam wani Lokacin sai yace suna mai Wariya da yan Ubanci fa Shi Kanshi yasani Haihuwan Sa"idu ne kadai basu yi ba ammh Suna mai kauna irin wacce ko ya"yan Cikinsu basu yimawa. Shi kanshi Baba Sa"idu haka yake jinsu Ammh Duk da Haka baai yada Danginsa na Gusai ba suna zuwa shima yana zuwa ballatana Har gaban Abada bazasu Daina Labarin kima da Dattakon Baba Malam ba..! Koda Yaushe suka zo ko Sa"idu yazo Sai sun Fadamai ya yi ma Baba Malam Biyayyah Shi din Uba ne Cikin Dubu sai antona Gaskiya suka Fada In yana Kallon Alkhairan Baba Mallam zuwa garesa sai yaga yafi kowani Da Sa"an Uba awannan Duniya Soyayyar da ko su Umar basu Sameta ba Sa"idu Shi kadai ne Mallam bai Taba Hadasa da wani ba kowa ya san da wannan ba ga ya"yan nasa ba har ga Matan nashi. Wannan kenan ..! ****** Tare suka Fito Daga massalaci Dayake bayan an idar da Sallar Isha"i Baba Malam yakan dan yi jan Hankali kan masu wasa da Sallah na Tsawon Mintina Ashirin kafin su tashi Sun Dade acikin masallacin shi da Baba Sa"idu kafin su fito Daga Masallacin Kai tsaye Falon Baba Mallam suka shiga Baba Malam na zama Saman Daya Daga Cikin kujerun Falon lokaci Daya yana gyara zaman alkyyaban Jikinsa Cikin Nazarin Baba Sa"idu Daya Duka gabansa kamar me neman gafara yace"Sa"idu da wata mtsala ce..! Baba Sa"idu ya Dago yana kallon Baba Mallam kafin ya maida kansa kasa yana Fadin"Eh Malam...Kun yi mgana da D'an Malam cikin kwanakin nan kuwa..? Baba Malam na Cire gilashin Dake Idanuwansa yace"Eh mun yi mgana Dashi yace suna tafe cikin Satinan..Sai dai bamu yi wata mgana ba..Ammh in ban Manta ba har alokacin yace min Baba Malam Baba Sa'idu bai ce maka komai ba..?Tun da naji haka nasan Yan"uwan juna sun yi abun da suka saba..Nasan da wani abu Saboda haka ina jinka wani Laifi ya aikata yau kuma ya Labe abayanka..! Ya fada yana Kayattacen Mirmishi Baba Sa"idu na sosa kansa shima yana Dariya Baba Malam yana da Saurin gano Mutun yasan indai aka Fara wannan Zagayen Zagayen wani abu ne ya Faru asan Sa"idu Dabam ne a wajensa Dashi yaran suke kamun kafa in suka aikata wani abun ko kuma suna son suyi wani abun da  suna Tsoron yima Mallam mgana Kai Tsaye. Baba Mallam ya kara Muskutawa yana Fadin"Uhm ina jinka...Meya faru ko ya fasa zuwa Bikin kennan nasa ne..? Da Sauri Baba Sa"idu yace"A"a yana nan tafe..yau ma yace ma Jirgin kayansu ya taso zuwa gobe zai kariso nan..! Baba Malam ya gyada kai yana kallon Baba Sa"idu wanda kansa ke kasa Kafin yace"Dama..Dama yace na Fada maka ne..Abukattab ya basa auran yarsa Sarood shi kuma bazai iya masa Musu ba ya karba..! Baba Mallam bai Sauya Fuska illah Cewa da yayi"Ina ce ba an Daura auran Jiya ba..,? Da mamaki Baba Sa"idu ke kallonsa kafin ya jinjina kai bai basa Zarafin mgana yace"Abokina bai Rufeni ba kamar yadda kuka Rufeni..Bai Fadamai bane ammh bai Daura masa aure Yarsa ba sai da Izinina..! Baba Sa"idu ya washe baki yana Fadin"Allah kara girma Baba..! Dariya yayi kafin yace"In kunyi waya ka Fadamai nasan komai..Kuma har munyi mgana da Kattab da ita zai zo Gida Taga Dangi..Wannan Abu ne mai kyau kuma Sunnar ma"aiki ne Sallalahu alaihi wasallam,Sannan kuma Kattab ya wuce wannan a wajena ballatana Wajen Umar..Ina Farincikin Shigowar Zuru"arsa Cikin Zuru"ata Allah ya Zaunar dasu Lafiya..! Baba Sa"idu nata amsawa da Ameen Baba Mallam ya cigaba da Fadin"Ya mganar Katin gayyata Sa"idu ina Fatan ka Tura inda ya Dace..? Baba Sa"idu yace"Insha Allahu Mallam..Jafar da Nasir suna ta aiki sosai su sukace na basu bangaran Baba mallam..Sannan Mutanen bazanga fa ko Mutum zamu tada zuwa chan..? Baba Mallam yace"Ba Bukata..Zan kira mai gari Ashiru na Sanar dashi..Ina so kasa agyara bangaran Baki na gidan gona Ba lalle bane gidajenmu na nan ya wadata in bai isa sai ku rage wasu zuwa chan..! Baba Sa"idu yace"Insha Allahi zan yi ma su Mamuda mgana zasu gyara komai...Sannan Husai tayo waya fa..Tace tana nan zuwa sannan tace zata Kiraka kan tana Rokon alfarma abar Jadwa tazogida Don Allah..! Baba Malan na Mirmishi yace"Husai Diyata..Ta Kirani Dazu da yammah..Munyi mgana nace Tazo ammh naso sai ta kara shekara Uku bata zo gida ba..Hajiya tasa baki nace tazo Tunda suma Sauran yan"uwan nata suna ta kama kafa wajen Iyayensu mata suna son zuwa Bikin nan. ! Baba sa"idu yace"Ai yana da kyau Mallam..zumunci sai ya kara karfi Tunda in ba irin wannan ba sai adade ba"a ga juna ba..! Baba Mallam yace"Ai bana son Bidia ni ba Taron mata zan yi ba..Ana Daura auree kamar yadda aka Saba Kowacce Mijinta zai Dauketa ba Shikenan ba..! Baba Sa"idu na Dariya yace"Adai yi hakuri Baba Malam..! Shima Dariyan yayi kafin yace"Naganeku..Kai da Hajiya bakin ku Daya..asan duk abunda kuka Saka baki bana iya Ture wannan mganar ko..!Shikenan Allah ya nuna mana Allah yasa kowa yazo Lafiya ya koma Lafiya..! Baba Sa"idu ya amsa da Ameen kafin su Cigaba da Tattaunawa sai wajen 9 na Dare yayi mai sallama ya tafi Gida sannnan sai alokacin Anty Nasara ita ke da Mallam a wannan Daran kuma ita keda Alhakin Shigo da Abinci anan Falon taci Kwalliya tana tashin Kamshin Tana jifan Malam da Sanyayyar Mirmishinta yana Girmama Nasara saboda Kaifin Tunaninta da kuma Sanyinta. *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo(Besty) Alherin Allah yakai miki aduk inda kike* *🅿️07* A kimanin Lissafi Saura Sati Hudu Bikin su Ya Zulaihat,Ta kowani bangare ana Cigaba da Shirye Shirye daga Duka gidajen guda Biyu duk da ba wani Sha"ani ake yi sosai ba Baba Malam ya hana anayin gayya dai makota da abokan arziki su zo su tayasu Murna,Walima kadai Baba Malam ya yarda ayi ana yima Amaran ne ana Gobe Daurin aure Ranar Daurin aure kuma ayi Taron mata na Cikin Gida da Safe zuwa yammah Sannan a Dokarsa Daga manya har yara Bamai Raka Amare Dakinsu Haka Tsarinsa yake ko su Ya Jadwa ba wacce aka Raka da an Daura aure zai Damkaki Hannun Mijinki bayan yayi muku Nasiha,ku tafi kin Riga kin zama nasu Jere ne dai ake zuwa ayi kafin Biki aga inda zaki Zauna kuma ko bayan Biki irin kannen Amarya suje wajenta Baya cikin Tsarin Gidan nan da kin tafi shikenan sai kuma Waya zuwa ma sai da Dalili mai karfi. Gidan Baba Malam ba"a kai Amarya bai yarda ba baya cikin Tsarinsa ba"a Taba ba kuma baza"a Fara ba kuma Daga Washegari Taro zai tashi Baki Duk zasu koma Gidansu komai nashi Cikin Taka Tsantsan ne baya yarda yayi abunda zai kaucema Tsarin Addini da Sallah. ****** *Monday..* 10:20am Gidan Baba Sa"idu..! Mamanmu Dake kofar Kitchen Tana Gyaran Zogale Awani Faranti mai kyau tana Zaune kan karamar Kujera yar Tsugunno,Yaya kuma na Daga Kofar Dakinta Tana zaune kan Wata Darduma Data shimfada Farcenta Datake yankewa da abun Yanke Kumba,Hira suke da Mamanmu Sama Sama yayinda Amina ke daga Cikin dakin Mamanmu Saman Daya daga cikin kujerun da sukayi ma falon kwanya tana kwance ne tayi kwanciyar Ruf da ciki tana Sanye da riga da sikat na kanti kanta sanye cikin Hula baka Wayar mamanmu ce a hannunta Kirar Nokia tana game din Maciji Cikin kwarewa Amina ce kadai keda wannan Damar bayan ita Mamanmu bata yarda wani ya taba mata yawa suma banda ita bawanda ma ya damu da wayar tunda ba sabawa da ita sukayi ba. Hamida ce ta fito Daga Cikin Dakinsu Dauke da wani Sikat na Leshi a Hannunta duk ya yamutse tana nuna ma Mamanmu itama Riga da Sikat din ne ajikinta sai dai nata Ja da Baki ne Cikin Mamaki tace"Mamanmu kalli wannan Sikat din..!na Amina ne fa ko gegesu batayi ba duk sun yamutse.. Mamanmu Dake duke ta Dago tana Fadin"Shine me...?tunda bata gyara ba ki gyara mata mana..?kema kinsan Amina bata da kokarin nan ke tunda kina da Himma sai ki gyara mata amfanin Yan"uwan kenan..! Hamida ta tura baki Tana Fadin"Allah Mamanmu ki daina cewa haka..Tafa iya Tsabar Wulakanci ne irin na Amina ai naga kayan da zata saka Ranar Bikin su ya Zulaihat.! Mamanmu tace"Eh ko bama haka ba ta isa ta sakaki ai tana gaba Dake..Oya kije ki gyara mata kayan Dirowanta in kuma sun kawo wuta ki goge mata ki adana mata kinji ko Hamida..? Ta Karishe da Sigar Lallashi Baki tadan Tura kafin tayi mgana Mamanmu ta Katseta da Fadin"Ban sanki da gaddama ba Hamida..Mganar kaya kuma Hajiya Babba tayi muku kayan Fitar Biki Ranar dana shiga na gansu Tace Shamsu zai kai Dinki..! Jin haka Hamida ta washe baki Tana Murna Amina nadaga Ciki ta Daga Murya tana Dariya Hamida ta Daga Labulen ta Leka Amina na ganinta tayi mata gwalo Lokaci Daya tana Fadin"Kinci Darajan Mamanmu ne yarinya..! Amina na Dariya tace"Yarinya na bayan Uwarta..Mganin masu sa ido kenan ina Ruwanki da kayana..!Ni inaga naga Lokacin gyara wasu kaya..! Hamida tace"Kiji Tsoron Allah..Tun yaushe muke gida..?tun gama Jssce din mu bama zuwa makarantar Boko Sai dai Hadda Karshen Sati..! Amina tayi Tsaki kafin tace"Kinga bana son Hayaniya..ki kyaleni kawai..! Hamida ta saki Labulen bata kara mgana ba Amina fa yar Ganin damace ko kayanta bata gyarawa sai ta ga Dama Kuma fa suna gida Tun sati Biyu da gama Jssce dinsu su ya Zulahait ne ke zuwa tunda basu gama Neco ba kwafa tayi ta koma Dakinsu ta cigaba da gyaran Dirowarta dana Amina da Mamanmu tace sai ta gyara mata. Yaya na zaune har suka gama mganarsu bata Daga kai ba Daman Tana da kawaici bata cika mgana kan wasu abubuwan ba Musammab kan ya"yanta Tana yi ma mamanmu kara gwarama kan su Ya Zeena zakaji muryanta ammh baida kan Amina ba sai Ta cikata sannan take mganinta. Sai da ta gama yanke Farcen nata ta kankare Lokacin Mamanmu ta gama gyaran Zogalen ta shiga kitchen ta Jikata da Ruwa,ta fito kenan Yaya ta kalleta Tana Fadin"Ni ko Mamansu kinsan D'an Malam ko zai dawo Cikin Satin nan..? Mamanmu ta Tsaya rike da Kugu kafin Tace"Eh naji su Babansu na mganar sannan naji bakin Hajiya dana Shiga wajenta Ranar..,! Yaya na Fadada Mirmishinta Tace"Yau da asuba ya Kirani mun gaisa ya Fadamin gobe jirgin Asuba zasu taso...Daga Jidda zuwa gata suna gida..! Mamanmu ta washe baki Tana Fadin"Masha Allah Allah ya kawo su Lafiya naji jiya Babansu na Fadin kayan su har ya iso tun jiya Shi Kadai zai zo ko Harda ita Sakinar..? Yaya tace"Yace min Har da ita Sakina sannan yace min zai zo da Bakuwa ma..! Mamanmu ta tsaya rike da Haba tana Fadin"Bakuwa kuma yaya..! Yaya bata samu Zarafin mgana ba Hanne tayi sallama Lokaci Daya tana Bayyana atsakar gidan. Mamanmu da Yaya suka juya kanta Cikin Kulawa sai da ta karisa kan Darduman Yaya ta zauna tana Fadin"Mamanmu yaya sannanku da gida..! Mamanmu tace"Maraba da Hannatu..Hannatun Aminata..! Take Fada tana Dariya Hanne ma Dariyan take kanta na kasa ta shiga gaishesu suka amsa mata Yaya ta kalleta Cikin Dogon Hijabinta tana Fadin"Hannatu ya wajen su Hajiya..! Hanne tace"Kowa lafiya..Tace a gaishemku..! Suka amsa mata kafin ta mike tana Fadin"Mamanmu su Amina fa..?Daman Hajiya ne tace nazo na Kirasu zamu je chan gidan Ya Dan mallam ne mu yi musu yan gyare gyare kafin su iso..! Mamanmu tace"Amina na cikin Dakina..Hamida na Dakinsu tama gyara kaya..Amina..Hamida..! Baku ji Zuwan Hanne bane..? Ta fada tadan Daga Murya Hamida ce ta Fara fitowa tana Fadin"Naji zuwanta Mamanmu ina so na karisane Dirowar Amina kamar Dirowar mara rai mamanmu kaya duk sun Yamutse Wlh Amina kin bani da kazanta..! Hanne tace"Amina jidalinta bazai barta ma tayi abu mai kyau ba Kina ina ne..? Amina na jinsu sai da taga Dama ta Fito tana Wani Kallonsu Daya bayan Daya Kafin tace"ina jinku...kawai bana son mgana ne..Ya akayi ne..? Tafada tana Dafa bangon Dakin Mamanmu. Hanne tace"ai kinji..Hajiya tace nazo na gayamuku ku shirya muje gidan Ya Dan Malam mu yi musu yan gyare gyare kafin su iso..! Da Sauri Hamida tace"Kai don Allah..?Bari na gama Yanzu na shirya mu tafi Daman nayi wanka..Amina ce batayi ba..! Amina ta juya Idanuwanta kafin Tace"Ai ba zuwa ma Zan yi ba..Bar Fadin ma ban yi wanka ba..! Ba su kadai ba Hatta Yaya sai da ta Dago Tana kallonta Mamanmu bata a wajen tana Kitchen bata jisu ba. Hanne Tace"Saboda mene...?Hajiya ce fa tace nazo na gaya muku..! Amina ta mele baki tace"Daman bansan Kakam banki bane hanne Hajiyar ai batace Dole sai munje ba..Ke ni fa nagaji ba wani aikin da zan yi ina kannen Matarsa..?su je mana..! Hanne tace"Wai su Sa"adatu..?to tare zamu tafi da ita fa..! Amina tace"Ai kaji..Shiyasa ma bazani ba kinsam na Tsani Hada waje da yarinyar nan.balle tana ganin gidan Yayarsu akaje sai ta nemi Budan Hanci ni kuma kinsan Halin Jidalina Kamar Zawo nake bani da Hakuri..! Hanne tace"ba abunda zai faru..ai ta Daima Shiga shirginki Tun Sanda Baba mallam ya mata mgana..! Hamida ta Kada kai kafin tace"Kyaleta Hanne in bazataje ba ni zani..Daman in jin Labarin Haduwar gidan nan banta zuwa ba..! Hanne tace"Nima ban taba zuwa ba..Kinsan Wanchan Dawowar nasu su ya Abida aka tura shima Dakyar..Yau din ma Baba Sa"idu Hajiya tasa ya Kira Baba Malam ya tambayeshi Da yace baxamu je ba sai dai su Ya Shamsu suje su gyara! Kinsan Baba Mallam baya son muna Fita ko fa gidansu ya Jafar sau daya muka taba zuwa Inajin Hamida..! Hamida tace"Wlh kuwa shima Lokacin da Anty Shamsiya ke wannan Laulayin ne muka bi su Hajiya Dakyar Shima Daga Cikin gida sai mota Daga Fitowa sai Mota ko dan gari bamu gani ba..! Sai Lokacin Yaya ta saka baki Ta mike tana Nannade Dardumanta tana Fadi "Sai abarku kuna mata kuma Yawo agari..?ai ina godema Baba Mallam Har gobe ina jinjina ma Hikimarsa..! Hamida kiyi ki shirya ku tafi..Ku kyale wacce tace bazata je ba..Rashin zuwanta bazai saka afasa komai ba..! Tafada Ko kallon Barayin Aminan batayi ba Amina da tasan da ita akeyi ta Tura baki kafin tace"Ai bance ba zani ba..Yasin sai naje nima naga abunda za"ayi Ehe..! Tafada lokaci Daya tana Juya ido Yaya dai bata ko bi ta kanta ba ta Shige Dakinta Idanuwanta sun kawo kwallah ai akwai wanda Hallayar Amina ke sukan zuciyarta Bayan itace ko Sa"idu bai kaita jin wannan Dacin ba itafa uwace wacce tasan Ciwon abunda ta Haifa Sannan Ita ta kadai tasan aibun mgana da Kullum ake yi akan Amina ita Kadai tasan Ciwon Haifar Zakka cikin Tarin ya"yanka sai dai tana amfani da Nasihar Baba Malam da kullum yake Fada mata Ta rika ma Amina Addu"an Shiriya kada ta sake ta bari ranta ya baci akanta Ballatana watarana ta aibatata Duka basa gyara Tarbiya Sai ma kara Fandarewa Addu"a da Nasiha sune Jagora. Hawayenta ta Share kafin ta Daga Hannu Sama tana Fadin"Allah ga baiwarka nan Amina kai ka Halliceta kuma Kaddaranka ne kayi ta yadda take..ya Allah ka shiryar da ita..Ka Natsar da ita..ya Allah kada ta zame mana Zakka watarana..Allah ka Bata wani bawanka da zai shigo Rayuwarta da Alheri ya SauyataWatarana..! Tafada Lokaci daya tana kallon Sama alokacin Bata sani ba Kaddaran Amina Rubutattace ne sannan addu"arta an dade da amsarta bata sani ba. Amina bata bi ta kan Hamida da Hanne dake mata Dariya ba Har suna Tafawa tayi kwafa batayi mgana ba ganin ta isa Gaban Famfo tana wanke Kafa yasa Hanne tace"Amina wai nufinki bazaki wanka ba..? Cikin Masifa Amina ta Juyo tana Fadin"Eh din bazan yi ba jikin ki ko nawa..Ban son munafunci Hanne ki Kyaleni..! Hanne tace"Daga mgana..?Tsiya na Dake bakisan gaskiya..! Hamida ta leko Daga Cikin Dakimsu tana Fadin"Kice dai batasan abun arziki ba..! Amina Ta Hura hanci kafin tace"Ba"asani ba din..Hamida da Hanne bana som munafunci kowa yayi harkarsa Fakat..! Basu kara ma tanka ta ba,Hanne Dakinsy ta shige suna mgana da Hamida tana Fadamata Malam yau baya nan yaje Jigawa Saukar Al"qur'ani da wata Makaranta ta gayyaceshi sai ga Amina ta shigo Tana Hura Hanci jira take amata mgana ta Fara jidalisai ta ga Tataga sun yi banzada ita suna Cigaba da Hirarsu. Tsab Hamida ta Shirya ta saka Hijabinta da Safa Amina ce ta Tsaya sai bata Musu Lokaci take Hanne tace"Amina don Allah kiyi sauri..Dakyar fa Baba ya barmu..Kuma kinsan in muka Dade hukuncinmu..! Amina ta cika Bakinta da iska kafin tace"kunga nifa bana son ana Damuna..In kunga bazaku iya jira ba Kuyi gaba ban ce Dole wata Cikin ku ta Jirani ba Atoh..! Tafada Lokaci Daya tana Bude Dirowarta ta kaya Baki ta Washe ganin Hamida ta gyara mata Cikin Shakiyanci tace"Hamidas..Kai mijinki Wlh ya More da gyara baki da kiwuya..wlh irinku ne masu yima Kishiya wanki da guga harda Uwar miji..! Ta karishe Fada tana Tsintsira Dariya Hamida tayi tsaki kafin tace"Kina da mtsala Amina..! Amina tace"Nafi gidan Haya..Tsohowar Mota ma nan taganni ta barni don kwal ubanta..! Amina ce fa sai ta gama bata musu Lokaci kuma amata mgana tace an Dameta in baza"a jirata ba ayi gaba.. Saida ta gajida mgana kana ta shirya sai da taga Hanne ta kusa kuka sannan ta Sauya kaya zuwa Doguwar riga tama mata kadan Gwiwan kafarta a waje ta kuma Sanya Hijabi ko kasa bai kaimata ba. Hamida ta kalleta Kafin tace"Amina kalli kaurinki a waje..Ki saka Safa mana..! Amina tace"Wlh bazan saka ba..Ke haka Kurum ana Fama da Zafin nan..Nifa bana son Zuhudu bazan kashe kaina ba. ke dai bakin saka ba. to miye na Damuwa sai na saka..? Hamida tace"Kafarki fa awaje..Kinsan fa bai kamata ba..! Amina ta Tsaya Lokaci Daya tana Fadi "Kafata a waje take..A"a kice Tsirara nayi ba kafata a waje ba..Hamida kin fara isata acikin gidan nan in ban kwabe ba nace na fasa zuwa kuce ba sunana Amina ba..! Da Sauri Hanne tace"Yi hakuri..Don Muje.Wlh in muka bata Lokaci Hajiya zatace mu barshi su Ya shamsu suje.! Tsaki Amina Taja tayi gaba tana Fadin"Dilla yo Laifina ne..?baga wacce ta wani Dameni da mganar banza ba nan..Ni wlh na tsani iyayi hamida kuma Halinta kenan Shigen Neman suna da son Nuna tafi kowa son Allah..! Hamida ta kalli Hanne zatayi mgana ta Rufe mata baki tana Fadin"Don Allah ki kyaleta..Kinsan Halin Jidalin Amina bataki a fasa tafiyar na ba ta Zauna tana sauke mana Rashin Mutumta..! Dole Hamida tayi shuru suka Fice Kitchen suka fara shiga suka ma Mamanmu Sallama Amina ta Bude Tukwinyar girkin tana Fadin"La Mamanmu Zogale kike Dafawa..! Tana Dariya tace"Zulaihat na Rage ma aiki..Dambun Zogale zatayi inta Dawo Saboda Aba dinku..! Amina tace"Wayyo Mamanmu..A ijiyemin mai yawa don Allah..! Hanne ta Harareta tana Fadin"Ke kadai.?kina da son kai mu fa ba mutane bane ko..,? Amina ta juya ido tana Rumgume Mamanmu ta baya tana Fadin"Saboda ni kadai ce Diyar Mamanmu ko Mamanmu..? Mamanmu na Dariya tace"Kwarai kuma baki da na biyu a wajena..Kuje zan Dibar muku da yawa saboda Diyata..! Fita sukayi Amina nayi musu gwalo Dakin Yaya suka shiga suka mata sallama Amina kin shiga tayi Daga waje ta tsaya suka fito Kafin su Rankaya zuwa gidansu Hanne din Shashen Hajiya suka shiga sai Fada take musu rana tayi. Hanne tace"hajiya Amina fa ta bata mana Lokaci..! Hajiya tace"ku kuka sani..In Malam dai ya Dawo bazaku je ba..Tun Dazu Na kira Idi na jiranku zai kai ku kuma zai Tsaya ya Dauko ku..Kuna da yawa..Kagaki ga Mamah ga Hamida da Sa"a kuyi hanzari share share ne da goge kunji ko..?bana son Malam ya Dawo baku dawo ba Dagani har ku ranmu sai ya baci..! Hanne tace"To Ina key din gidam Hajiya..! Hajiya tace"Na duba na wajena ban gani ba..Kuje shashen Amarya ku amsa wajenta tana dashi..! Amina saita koma ta Zauna tana Fadin"in kun amso ku gayamin..! Hajiya tace"In baki je ba..Tafi Haraba wajen Mota Idi na nan na jiranku..! Ba Musu ta mike suka fice Tare su suka Wuce Shashen Anty Amarya ita kuma ta koma Haraban gidan Inda Idi ke Cikin mota kirar Siana yana Jiransu. Tafi minti goma da Fitowa sai gasu sun Fito Sa"adatu ce abaya tana wani Bude Hanci Hannunta Leda ne babba komiye aciki oho..?Sai key din gidan tana wani Kadawa Amina Kallo Daya ta mata ta Kauda kai itama Shiga Motar sukayi bayan sun gaisar Idi kamar yadda Tarbiyansu take.. Kai Tsaye daganan bai Diresu ko"ina ba Sai Kofar Arewa,inda gidan Ya Dan Mallam yake. Tundaga Wajen gidan suka saki baki suna kallon Wannan Tsaruwa kamar a Turai akwai megadin Dake Tsaran Gidan wani Buzu ne,bai ko jin Hausa sosai,Idi megadi yayi Hon ya Bude musu suka Sulala Ciki tun da suka Fito sukayi ta kallon gidan ba wani Babba bane sai dai ya Tsaru matuka Gashi gabadaya Haraban gidan yana Shimdide da Marbels mai Santsi Kalan Ruwan kasa mai Duhun Get din Gidan Fari ne Fentin gidan kuma Ciki da wajensa Mai ruwan pich ne mai kyau da kyalli. Sa"adatu ce agaba ita adole masu gida Amina ta tabe baki ita Sakarcin Hanne ta gani ita wazai je gidan Ya Jafar yamata wannan Ikon bata ci uban Mutum ba. Sai da suka Shiga Falon suka san Waje basu ga komai ba Duk da gidan ya Dade a Rufe ammh kuma babu abunda ya Sauya wani Sanyin Dadi ne ya Daki Hancinsu sai da Amina ta Lumshe Manyan Idanuwamta tana kare ma Falon kallo. Komai Baki da Fari ne duk yadda akayi Mai gidan yana son Kalan sosai. Sannan Duka kujerun da Dining an Rufesu da Fararan kyallle,Sai Cafet duk an Nadesu waje Daya Komai dai yana Muhallinsa ammh an Killacesa Daman gidan bayan wani Lokaci su Ya Shamsi na zuwa suna gyarawa sannan Sai Karshen Shekara yake zuwa da ita iyalin nasa,ammh yakan zo a shekara su Uku zuwa Hudu kuma agidansa yake sauka. Falo ne Babba sai Bedroom guda uku sai Kitchen guda Biyu Sa"adatu ita ta Bude bedroom din guda Biyu Bata Bude Dayan ba ta Dago tana kallon Su Hanne Lokaci Daya tana Fadin"Bari na Bude muku kitchen ku fara da Chan kafin mu zo Falo..Ni zan gyara Bedrooms din Anty Sakina..! Bawai neman Shawaransu take ba Umarni ne take basu Hanne ko ajikinta ta taka ta mika hannu Tana Fadin"Bani key din na Bude Kitchen din..ki gyara chan din Saboda aikin yayi mana Sauri.Ko kuma Hamida ta shiga Dayam ta gyara ni da Amina mu gyaro Kitchen din ko ya kika gani..? Da Sauri Sa"adatu tace"A"a ku gyara chan gabadaya in kun gama ga Falo.ni zan gyara Duka bedrooms din ai guda Biyu ne Dayan na Yaya D'an Malam ne kuma Key na wajen su ya Jafar..! Hanne bata kara mgana ba ta karbi key din ta Bude kitchen din ta Juya tana cema su Amina"Bismillah..! Hamida tabi bayanta Amina kuwa sai da ta gama Tabe baki kana ta Bisu Ciki Sa"adatu kuma ta shige Ciki abunta. Amina baki ta saki da Hanci tana kallon Tsaruwa da Haduwar Kitchen din Shima Fari ne da baki gabadaya Cabinet din kitchen din Fari da Baki ne Hatta marbels din Dake Kitchen din ma Fari ne yana kyali Kamar ana Gyarssa ba wani Datti sai ku ran da baza"a rasa ba tunda komai na amfanin Girki suna cikin Kwalayensu ne Fridge ma ba komai aciki sai ruwa da Lemo,Hamida na Duba Kitchen din tace"Gidan ma ba wani Datti..! Hanne na Kokarin Bude Store tace"Ai Dayake su ya shamsu na zuwa suna gyarawa..Sannan Anty Sakina gaskiya akwai Tsabta kafin su tafi sai ta Hada komai nata ta adana..! Ba wanda yace wani abu har ta Bude Store din Gabadaya kayan abinci ne Dankam aciki Hamida ta Leka tana Fadin"Hanne kayan abincin su basa Lalacewa ne..? Hanne tace"Suna Lalacewa mana..kamar fa wannan kwananan aka Zubasu ai kafin su koma suna Kyautar da komai kafin su koma..! Hamida ta gyada kai tana Fadin"Hum..! Amina dai na gefe batace komai ba sai Kalle kalle takeyi basu bi ta kanta ba suka Fara goge gpge Da kakkabe kakkabe tunda sun ga tsintsiya da Moper anan Kitchen din da Towel din gogen Kitchen Amina na gefe ko Hannu bata saka ba Domin Taga abun akwai rainin Wayau aciki. Hamida ne ta juya tana kallonta kafin tace"To ke Amina tunda mun kama nan ko zaki je ji kama Gyaran Falon ne..? Amina ta tabe baki kafin tace"Ni daman nace muku zan yi wani aiki ne..?ke hanne wai nan ba gidan yayanki bane..? Hanne bata gane Tambayan ba tace"Bangane ba..? Amina tace"to gani nayi ta zabi Aiki mai Sauki ku ta hadoki da gyaran Kura..ji yadda take bada Umarni kamar gidansu..In tana takama matar gidan yayartace..Ai kema mai gidan ne Yayanki kin fita iko dashi..! Hanne tace"Sai me..?ni ina komai ne Saboda Allah da Ya Dan Malam ba Saboda wata Sa"adatu ba..Kema don Allah kidaina mgana in baki yi ba ki koma Falo ki zauna nidai muyi mu gama Lafiya mu tafi gida..! Hamida tace"Ni ban ma ga abun mgana ba Wlh..! Amina ta ballara mata Harara tana Fadin"Ai bazaki gani ba..! Daganan ta yi ficewarta Falo ta koma ta Haye gan Dining ta zauna tana Kada kafa Domin daman chan batayi yi niyyar ko Taba wani abu ba Sa"adatun tazo tayi duka mana. Tana nan zaune Sa"adatu ta fito Daga Dayan Bedroom din suka kalli juna kafin kowa ya Kauda kansa Dayan ta shiga shima ta gyara kafin nan su Hanne sun gama da kitchen din suka Dawo gabadayansu suna gyaran Falon Sai alokacin Amina ta saka Hannu ta yaye abunda aka Lulluben Dining din ta Goge suma Kujerun sun yaye komai sun goge Dayake Sa"adatu tazo da Klin da Turaran Wuta mai kanshi na Tsinke da na Bunner Dayake akwai Wuta suka jona suka Turara gidan. Ba inda basu share sun goge shi ba Ko"ina yayi tas yana tashin Kamshi Cikin Awa Biyu suka Idar da komai Sai da sukayi salla suka yi shirin Tafiya Alwarma a Sink din Kitchen sukayi ga yunwa sai dai suka sha Ruwa da Lemo Amina ko Ruwa bata sha ba Sallah kadai ta yarda tayi. Karfe 2:30pm na rana suka Dawo Daganan Amina da Hamida gida suka wuce basu koma gidan Baba Malam ba. Koda suka koma su ya Zulahait sun Dawo daga makaranta sun gama Jarabawa Ya Jafar tayi ma waya yaje ya Daukosu Tunda Idi baya nan Daman kuma Dokar Malam ce ya Hana su Hawa adaidaita,Ita da Ya Sadiya da Ya Aisha da ya Ikram da Ya Shamsu sune suke Jarabawar Neco su Ya Zeenatu sai da ya maida su Amina yaje ya Daukosu. Amina tunda suka Dawo ba wanda yaji wata mgana Daga bakinta Da Daddare bayan sun gama Karatu tana jin Hamida nata bama su ya Zeenatu da su Mamanmu Labarin gidan Suna Zaune abaranda suna shan iska ba Wuta kuma Gen yaki tashi sai mai gyara yazo. Amina na daga Cikin Dakinsu kwance taji Sanda Hamida ke fadin Tsarin gidan Mamanmu na gefe tana Fadin"Ai bama Sakinar ba shi kanshi Dan Malam din dan gayu ne na karshe..Mun je gidan ai tun sanda aka gama ginashi sannan mun ga Hoton ginin a waya Daya Turo ma Aba dinku..! Kowa saiTofa albarkacin bakinsa yake yi har Yaya ma tana Saka baki Amina na jinsu aranta tana mamakin yadda Yaya take Ji da Dawowar Dan Malan koda yake taji fa ance Dan Dakinta ne har waya suna yi da ita. Aba yau ya Dade wajen Baba Malan Amina ta fara barci Sama sama taji Shigowarsa kuma tana ji yana tambayanta yaga kowa bai ganta ba Mamanmu ke fadamai inda mukaje Tunda muka Dawo nake kwance nagaji. Bai ce komai ba,ya wuce Dakinsa Yaya ke da Aba Aranar ita take ta kai da kawon kai mai abinci da abubuwan Dayake so su kuma su Mamanmu na Tsakar gida suna cigaba da Hirar gidan Ya Danmalam sannan suka koma Hirar Biki da kuma Labarin Sati na sama Baba Malam yace za"a jere kamar yadda aka saba daman ba"a kawo Lefe sai dai kayi shi ka sakashi Cikin Dakin Amarya intazo tagani kayan Fitar Biki Daga na Amaran har na Sauran yan gida Baba Mallam ke yin komai Hajiya babba ita keda jagaba kan Komai Tare da Shalelen baba mallam Baba Sa"idu. Kuyi hakuri nayi baki ne..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo (Besty) Alherin Allah ya kai miki har inda kike Ameen* *🅿️08* Ko daga yanayin yadda ake Murna da Shiryen Shirye zakasan D'anmalam na musamman ne,Amina batasan haka yake da Tasiri har agidansu ba sai Ranar da Daddare gabadaya wuni akayi mganarsa,Tana jin sanda Aba suka shigo da Ya Jafar da Ya Nasir,suna mganar gobe da zafe zasu sauka a Kano tun dazu da Rana suka Taso Daga Filin Sauka da Hawan Jirage na Jidda. Bata kara jinjina Lamarin ba sai da taji da zasu tafi Ya Jafar na Fadin su Anty Shamsiya zasu zo su wuni Zasu zo kawo su yima Ya D'anmalam barka da Dawowa bazata iya Tuna Rabonsu da gidan ba Mallam baya barinsu suna Barin matansu suna zuwa sai da wani Dalili mai karfi ammh sai gashi yanzu zasu zo Anty Shamsiyan Tsohon ciki gareta Haihuwa ko yau ko Gobe,Anty Fadilan ne keda karamin Ciki Sannan gidansu Daya Tare sukayi Gininsu. Amina na zaune a wajen anata Hira tayi kamar bata awajen Tsaki take ja acikin Ranta Har ga Allah tana so taga wannan Ya D'anmalam din nan Duk da Tasanshi ammh ayanzu bazata iya Nuna sa ba ko ta Tuna da Kamaninsa ba. Sanin da tayimai Tana yarinya ne Lokacin Jidalinta ne agabanta da kuma ta fara girma in yazo har ya koma basa Haduwa sai dai tana jin Labarin zuwan nasa,Wannan karon Taji tana son ta gansa wanda har Aba a Fuskarsa yana Nuna Farincikinsa. Ba gidansu kadai ba Har chan gidan Baba Mallam,Dazu da Rana hanne tazo ta jata sujeta tayasu aikin Sinasir da Waina,Saboda Ya Danmallam yana so Amina tayi kwanciyarta taki zuwa Hanne Tagaji tatafiyarta ko ajikinta Tasan zuwa gobe zasu koma Daidai. Washegari da Safe Amina ke da Sharan Tsakar gida Hamida kuma Wanke wanke tana fa Sane tana Idar da Sallar asuba ta koma barci ba wanda ya Damu sanin ita ba Karatun asuba take yi ba,Su Ya Zeenatu suna Idar da karatunsu suka fara shirin makaranta Ya Zulaiha ke kitchen tana Hada abun kari,Yau basu da Jarabawa suna gida. Hamida tana gama karantunta ta fita Waje ta fara Hada kayan wanke wanke zuwa wajen Famfo Mamanmu ta Fito Daga Dakin Aba da Hijabi da Carbi a Hannunta Da Sauri Hamida ta gaisheta ta amsa tana Fadin"Bake keda Shara ba Daman..? Hamida tace"Amina ce ke da Wanke wanke..Jiya tace nayi wanke wanken Ita zatayi Sharan..! Mamanmu kai kawai ta kada ta wuce Kitchen wajen Zulaiha. Ya Zeenatu ta fito Cikin Shirin makaranta tsakar gidan ta kallah tana Fadin"Wake da shara ne..?hala Amina ce..? Hamida na Duke tace"Eh itace..! Karamin Tsaki taja tana Fadin"Indai Amina ce..Ba"ajin kowa Ranar aikinsa sai ita..! Tafada Lokaci daya tana komawa Cikin Dakin Amina tayi Daidai tana barci taji An Daga mata Duka abaya Da Sauri ta Zabura tana Fadin"Kan Uba..Wani dan...! Ta kasa karisawa ganin ya Zeenatu tsaye tana kallonta Lokaci Daya da Hararanta Baki ta Tura kafin ta wani Juya ido cikin kunkuni tace"To wai don Allah me nayi..? Ya Zeenatu tace"Bansani ba..Nasha Zaki karisa Ashariyan da kika fara ne..! Amina tawani Tona baki tana kunkuni Tana Fadin"To haka kurum..Ni..! Zeenatu ta Make bakin Amina da yasa tayi Shuru cikin Bacin rai tace"Kinsan Allah? Da Safan nan zan Dirji bakin ki bana son Rashin kunya..! Amina Bakinta ta Dafe tana Dubawa taga Danshi Cikin Zare ido tace"Jar uba..Kan bala balagagge..! Ya Zeenatu tace"Ko kan uban Balan ne...Malama ki tashi kije kiyi mana Sharan Tsarkan gida waje duk datti kin zo kin kwanta kina barci kuma kinsan aikin ki ne..! Amina kamar tayi kuka bakinta na mata Zugi tace"To ni nace bazan yi bane..! Ya Zeenatu da har ta juya ta dawo tana Fadin"Me kika ce..? Amina tace"Toh..nace..! Ya Zeenatu ta juya tana Kyafci Lokaci Daya tana Fadin"Da kin maimaita da kin sani..! Wajen gadonta taje ta Zauna tana kokarin saka Safa,Amina na zaune sai Hararanta Take tana kunkuni Lokaci Daya tana Fadin"Haka kurum..Allah ya isa na..ban yi miki komai ba..Allah ya sakamin Wuta balbal Yasin..! Ya zeenatu na jinta bata yi mgana ba Sanun Halin Amina ko za"a Mutu bakinta bazai mutu ba. Amina kin fitowa tayi sai da Ya zeenatu ta kara mata mgana ta Zare mata ido tana Fadin"To wai bana ce toh ba..ba cewa fa nayi bazam yi ba..! Tana jin haka taje ta Fadama Aba yana Zaune ne yana Duba Tarkadun Lissafin kwan kajin da aka Fita dashi Daga gidan gona ya Dago kai yana kallon Zeenatu kafin yace"Kiramin Aminar..! Tana daga kwancen Zeenatu ta Dago Labule tana Fadin"Ki tashi kije Aba na kiranki..in kin rainamu shi ai bazaki Rainasa ba..! Amina ta rike baki afili ta Furta"Munafuki dai bai ji Dadi ba..! Kara Dago Labule ya Zeenatu tayi tana Kallon Amina da Sauri ta mike tana Neman Hijabinta Lokaci Daya tana yar waka"Kan munafiki dai baya gashi..ko yayi sai ya sauke..! Ya zeenatu tace"Dani kike Amina..? Sai data saka Hijabinta Na Hadda kana tace"Nifa badake nake ba..Wakata kawai nake ba"aji na ambaci Suna ba Atoh..! Tafada tana wucewa tana ta kunkuni Ya Zeenatu ta bita da Harara Domin in ta tsaya Biyema Amina sai ta makara. Fuu kamar kububuwa ta fito sai Dakin Aba da sallama kamar Mutuniyar arziki ya amsa mata kafin ya bata izinin Shigowa. Kanta na kasa ta shiga chan gefe ta Zauna Sannan ta dago kanta tana Fadin"Ina kwana Aba..! Bai kalleta yana Rubutu Bisa Takarda yace"Lafiya..Ya akayi akace an saki aiki kikace bazaki yi ba..? Amina ta yamutsa Fuska kafin tace"Nifa karya takemin Aba..nace zan yi fa..! Sai Lokacin ya dago yana kallonta Cikin wani yanayi itama kallonsa take yi Cikin Daure Fuska yace"Zeenatun ke miki karya..?Sa"arki ce..? Amina ta Tura baki kafin tace"Aba har fa Baki ta fasamin..Wannan ai Zalunci ne..! Aba ya karkace kai yana Kallonta,Yana kara nazarinta Har yau bata Chanza ba Ganin zata ma batamai Lokaci yasa yace"Tashi kije kiyi aikin da aka saki. daga yau in na nakarajin ana Fada Dake kan aikin da kika san naki ne..sai naci Mutumcinki Sannan Gargadi na Karshe kada na kara jin kin kara kiran wani Dan"uwanki Azzalumi kina jina ko..! Amina tayi kasake tana kallon Aba aranta tana ayyana yadda ba"a taba goyon bayanta Kullum itace bata da gaskiya ganin tayi shuru yasa yadan daga Murya yana Fadin"Kin ji ko baki ji ba. ? Amina ta Tura baki kafin tace"Naji Aba..Ammh..! Hannu ya Daga mata bai kalleta ba yace"Tashi ki bani waje....! Dole ta mike sanin Halin Aba Tunda yace haka bai Bukatar kara jin mganarta kamar Amina ta Buga ita kadai haka ta fito kamar kububuwa Taje ta Dauki Tsitsiya ko Hijabin Jikinta bata Cire ba ta Fara waka da Karfi tana Fadin"Munafuki dai baya gashi..Ko yayi sai ya Sauke.! Ba wanda bai jita ba Har Yaya Dake Daki Tana Shirya Jawaad kai kawai ta Kada aranta tana ma Amina Fatan Shiriya. Ya Zeenatun ma tana jinta tayi mata Banza Mamanmu ce ta fito tana Fadin"Amina ki bar wakar nan..Ko kin manta Aba din ku na gida..?kina so yaji ya fito ya saba miki ne..,? Amina ta Dago tana Fadin"Mamanmu bana son munafunci ne..Cewa nayi bazan yi sharan ba..?an wani je an Hadani da Aba yamin Fada..! Mamanmu tace"Yi hakuri yi shararki..Kada ki kara tanka kowa zan ma Zeenatun mgana..! Saboda Mamanmu yasa ta kama Bakunta ta Cigaba da Sharan,Har tazo wajen da Hamida ke tsunggune tana wanke wanke tayi ta yarfo mata Shara da Datti Hamida ranta ya baci ta Dago Tana kallonta Lokaci daya tana Fadin"Bana son Rashin mutumci Amina baki ganni bane..?ai sai kice na tashi ki share ko..! Amina ta balla mata Harara kafin tace"Dayake baki da ido ne..Kada Allah yasa ki tashi ta kanki zan bi na wuce..! Tasan zata aikata kuma abokin Jidali take nema yasa Ta tashi Tsam ta bata waje ta Share ammh duk da haka sai da bata mata wasu kwanukan sai da ta kara Dauraye Amina tana gama Sharan ta koma Daki tayi kwanciyarta tana ta kunkunin mgana Har su ya Zeena suka karya ita da Jawaad suka fita Idi na Jiransu da su Abida.. Hamida data ga Amina bata tashi ta yi Breakfast ba,i ta tayi mata mgana sai ta mata Banza ganin haka yasa ta karisa kusa da ita tana Fadin"Amina ki tashi ki karya..Mutuninki aka Soya Dankali da kwai..! Amina ta Tsaki tana Fadin"Baza aci ba din..Ina ma Ruwanki dani Cikin ki ko Cikina..? Hamida ta rike baki tana Fadin"Allah ya baki Hakuri..! Amina tace"Ameen in da gaske kike..! Ita dai Hamida ta fice zuwa Dakin Yaya ta bar ma Amina Dakin Mamanmu kuma tana Dakin Aba ta kaimai abun karyawa ya Zulaihat kuma ta shiga wanka adakin Mamanmu. Amina tun tana kunkuni har barci ya Dauketa bata sani ba Bata Farka ba sai da taji Ihun Hanne asaman kanta Lokaci Daya tana Kiran sunanta"Amina..Amina tsshi..! Amina ta Bude ido ta ga Hanne Saman kanta bakinta Har kunne Cikin Dariya ta rike Hannunta tana Fadin"Ki tashi Ya Danmallan sun dawo..Yanzu su ya Jafar da ya shamsu suka je Airport zasu Dauko su..! Amina wani Kololon Takaichi ya zo mata wuya batasan Sadda ta Fizge hannunta ba tana fadin"Shine zaki zo ki tasheni ina barcina..?tsakanina Dake Hanne wlh sai Allah yamana Hisabi..! Ta karishe Fada tana Sakin Tsaki kafin ta juya tana fadin"Ni ina ruwana da wani Dawowarsa..! Hanne Jikinta yayi sanyi ta kalli Hamida Dake Tsaye da Sauri Hamidan tace"Kiyi Hakuri Hanne..! Hanne ta mike batace komai tayi yake kawai kafin tace"Na tafi Hamida..Sai kin shigo..?ai zak zo musu sannu dazuwa ko..? Hamida tace"Sosai ma zan shigo insha Allahu..! Daga haka ta fice Amina na jinta tana Fadama su Mamanmu a waje tana jin Sanda Yaya ke fadin"maraba..Maraba..! Tsaki ta kara ja aranta tace"Kamar wani Gold..?ita zata so taga wannan Mutumin nan..da harda Yaya da bata wani Shiga Sabgan mutane tana ji dashi..! Bayan tafiyan Hanne Hamida ta kalli Amina Dake ta Zakuda Kafada Daga kwancen tana Fadin"Amina ammh kinsan baki kyauta ba ko..?Hanne fa kika ma haka..! Amina na Daga kwancen ta Dago kanta kafin tace"To uwata..Hadiza ina jinki..?gayamin abunda nayi wanda ban kyauta ba..! Tafada Lokaci Daya tana Mikewa Zaune kamar abun arziki. Hamidatace"Koma me zaki ce..Gaskiya ne sai na Fadamiki baki da wacce tafini Amina..bai kamata kima Hanne haka ba kada ki mamta Hanne yadda take awajenki..Ko ni da muke gida Daya ban kai Hanne Daukan Jidalinki ba Amina Tana ta Murna tazo fadamiki Dan"uwanta ya Dawo kalli yadda kika gwasaleta alhalin batayi Fushi da abunda kika mata Jiya ba yau kuma ta dawo..Wlh ban taba ganin Hanne ta Damu da Halinki ba sau yau..kwallah sai da taru acikin Idonta..! Amina tayi kasake tana jin Hamida ko ajikinta Ganin haka yasa Hamida ta Cigaba da Fadin"Kuma kada ki manta Ya D'anmallan d'an Hajiya da Baba Mallam ne ko domin yadda suke Kaunarki bazaki musu kara ba..? Amina ta yamutsa Fuska kafin ta mike tana Fadin"Ke kikasan wannan..Sannan wai da gaske kike Hanne Fushi tayi..! Hamida ta kalleta Cikin jin Haushi kafin tace"Watarana Amina.Zaki Tuna Damu har kinemu mu bamu kusa Dake ballatana mu gayamiki gaskiyan..! Amina tayi tsaki ta wuce tana Fadin"Ai da nasan Fushi tayi..Da nasani na Dago na kalli Fuskar ta..Tabdijam waya ga kunu In hanne tayi Fushi..! Ta Karishe Fada tana Dariya Hamida ta Bita da kallon Yaushe Amina zata Damu da wadanda suka Damu da ita ne..? Abunda bata sani ba Bawai bata Damu bane A"a ita tana da Saurin Shanye abu,Tana ganin ai ba wani abu bane..Zasu shirya da Hanne tasu bata Baci Shiyasa bata Cika Damuwa ba don sun yi irin wannan ba Ta tabbata ko Kowa ya kyaleta Hamida da Hanne suna gefenta Har acikin Ranta ta basu matsayin dasu basu sani ba. Kitchen taje ta karya abunta Sannan ta Fito ta isa Dakin Mamanmu bata Ciki tana Dakin Aba Amina ta rike Baki ganin Har 10 ta wuce ammh Aba bai Fita Lalle Ya Dan Malan na zuciyar kowa ta tabbata Saboda Dawowarsa ne Aba bai fita ba Dakin Yaya ta Leka ta iske ya Zulahait na karatun textbook din Biology Lekawa tayi domin ita bata fiya shiga Dakin batace"Ya Zulahat yaya fa..? Kanta na Duke bata Dago ba tace"Gata na goyata abaya na..! Amina ta karkace baki tana Hararanta kafin ta yi kasa da Murya tana Fadin"Ta kusa aure..Ta kusa aure an kusa a bar mana gida..! Tajita tana mgana yasa ta Dago suna Hada ido ta washe baki kafin tace"Ina kwana Yaya. ! Da karfi Saboda Yaya taji kuma tajin tana gyara kayanta ne Ta girgiza kai kawai chan kuma sai ta dan Murmusa Amina tayi wucewarta aranta tace nasan taji ita yayan nan kowa tana mai Dariya bandani Saboda ta Tsaneni..! Afili ta Furta"Da ace Aba bai auro Mamanmu ba Al"quran wajen Hajiya zan koma ina zan iya..! Zulaihat kam sai da ta Toshe kunnenta Amina Mtsalace wlh yarinyar nan kamar mai Almatsutsai Dakinsu ta koma ta iske Hamida ta Shiga wanka gadonta ta Haye harda jan Zani tana wani Lumshe ido Hutu Dadi ita bataki ma akyaleta kada ta koma makarantar ba ina Laifi takai har Jss3 tafi wasu ma kuma ai ta samu na yaki da jahilci. ******* Ya Shamsu ne ya fara shigowa Shashen Hajiya babba da wata Jaka ta matafiya irin ta yan Saudiya haka,Hajiya na cikin Dakinta Hanne da Ya Aisha afalon suna ganinsa suka Mike gabadayansu Cikin Murna Ya Aisha tace"Shamsu har sun iso..? Yana ijiye Jakar nan Tsakiyar Falon yace"Eh suna Haraban gida..Ina Hajiya..,? Hanne tace"Tana Dakinta..! Juyawa yayi yana Fadin"Ya D'anmalam yace ku gyara Dakin ku akwai bakuwar da zaku sauke..! Daga haka ya fice Hanne bata Tsaya ba ta Ruga Dakin Hajiya tana Kiran sunanta sun kusa cin karo Cikin Fada tace"Miye haka ke kullum baki abu Cikin Hankali..? Tana Dariya ta makaleta tana Fadin"Hajiya su yaya sun iso..! Kwace jikinta tayi tana Fadin"Shi ne me..?kika rikeni kamar zaki gadani..! Ta fada tana kariso cikin Falon kafin ma tace wani abu Shamsu ya Sake shigowa da irin Jakar Dazu Ko kafin Hajiya ta samu bakin mgana taga ya Bada Hanya yana Fadin"Bismillah..! Gabadaya Kofar suka Zubama Ido Hajiya tasan ba D'anmallam bane Domin shashen Malam yake fara isa in ya Dawo kasar kafin ya shigo wajenta sannan in Sakina ne kuma Shashen Uwarta take sauka sai Daga baya take zuwa ta gaisheta. Bata gama wannan mamakin ba wata Farar balarabiya Jajir da ita kamar ka Taba jini ya fito ta bayyana agaban Shamsu Cikin Shigar Doguwar Abaya baka tayi Rolling din gyale asaman kanta irin yadda matan Larabawa sukeyi,kyakyawace sosai ko gasan kyau zata iya shiga kuma taci sannan Doguwa ce mai Jiki kadam Hannunta Dauke da wata karamar Jaka ta mata Hannanyenta sunsha Jan kunshi kwanin Sha"awa da Burgewa Tunda ta shigo Ta saki Fararan Hakoranta da suka kara Fito da kyanta Tana kallonsu Hajiya. Suma ita suke kallo Cikin mamaki harta Hanne data saki baki da Hanci tana kallon Tsabar kyau yau datake jin Labari yau gashi ta ganin ma Idonta. Ya shamsu ne ya Katsesu da Fara gaida Hajiya ta amsa tana Dan Boye mamakinta. Da Sauri yace"Hajiya bakuwa ce..Ya D'anmallam yace na kawota Shashenki kafin ya shigo..,! Hajiya bata nuna wani Damuwa ba ta Washe baki tana Fadin"Toto..Nifa nace bakin labarawa da Safen nan..Maraba maraba Sannu da zuwa..! Tafada Cikin Sakewa Duk da batasan me Hajiyar ke fadaba Tunda batajin Hausa sai larabci ance Tabarman Fuska tafi tabarman zama yadda take ta mata Dariya yasa ta gane tana mata Lale ne. Shamsu ta kalla daya ijiye jakar hannunsa inda ya Sauke Dayan Dazu tace"Shukran..! Mirmishi yayi mata shima aransa yana Fadin ina Yaya Danmallan ya Samo Balarabiya mai kyau haka sai da bai tanka ba ya Fice Daga Falon. Hajiya ta kalli SAROOD tana Fadin"Maraba lale..Kariso mana..! Hanne ta saka Dariya tana Fadin"Hajiya wayace miki tana jin Hausa..? Hajiya tace"Oh to..To ku da kuke yara yanzu kwakwalwar ku take ku mata mgana da labarci kuce tazo ta zauna ai batayi ta tsayuwa ba..! Aisha ce taje ta kamo hannunta tana mata Sannu da zuwa Cikin Harshen Larabci batayi mamaki ba Sanin Daman Umar ya fada mata zataji dadin zama a Nigeria Domin agidansu akwai masu jin yarenta Har kan Daya Daga Cikin kujerin Falon ta zaunar da ita sai dai bata Zauna ba ta Zame ta Zauna akasa Cafet kanta na kasa Umar ya fadamata Shashen Mahaifiyarsa za"a kaita Shiyasa kanta na kasa ta shiga gaida Hajiya da Harshenta Hajiya na jin Larabci tun abaya don ma Shekaru da kuma Rashin yinsa Lokaci zuwa Lokaci. Cikin jin Dadi ta amsa mata da Tambayan Hanyan ta amsa da Alhamdulillah kanta na kasa Muryanta Dadi Cikin Harshenta. Hajiya ta kalli su Aisha tana Fadin"Aisha ce mata ta tsshi a kasa..Ta zauna kan kujera..ke kuma Hanne kwashe kayan nan kikai Dakin ku..Ki kuma Shiga Kitchen ki Hado mata Ruwa da Lemo..! Daga haka ta wuce zuwa Dakinta Aranta tana Tunanin to wacece wannan yarinyar da D'anmallam ya Taho da ita kuma kai Tsaye a bata Masauki a shashenta da wannan Tunanin ta karisa Dakinta bazatayi gaggawa ba koma me ke ciki tasan Malam ya sani Tunda tasan yaronta bazai Taba zuwa da wata garin nan batare da Izinin Malam din ba..! Kowacce tayi abunda Hajiyar ta sakata Hanne ta kwashi kayan zuwa Ciki Aisha kuma tace mata ta Hau kujera sai taki Mirmishi Kawai tayi. Kafin Lokaci an cika gabanta da Ruwa da kunun ayan da sukayi Jiya da Daddare. Bata taba ko Daya ba tana gefe kanta na kasa tana wasa da adon Kwalliyar Dake Cikin Jakarta Hanne da Ya Aisha suna gefe suna kallonta kowacce aranta tana ayyana kyau kamar ita tayi kanta wannan Balarabiyar da Tambayan Ina Ya Danmlam ya samota..? Hajiya tana Shiga Bedroom dinta Wayarta Dake kan gado na neman Dauki tana Dubawa taga D'anmalam ne,Da Sauri ta Dauka Tana Fadin"Danmallam kun iso Lafiya..!? Dagachan Falon Baba Malam Baba Sa"idu na zaune akasa kusa da Baba Malam Dake kan kujera Cikin Farin Raawani suna mgana shi kuma yana Daga chan gefe kamar zai bar Falon kansa na kasa yana Shafa Sumar kansa da bata da yawa. Cikin Tattausan Muryan da ban taba jiba wacce ta Chakule da Labarci Yasa bata fita saosai kamar yana Koyonta yace"Mun sauka lafiya Hajiya..!ya muka Sameku..? Hajiya tace"Duka muna Lafiya..! Sai kuma Shuru ya biyo baya Hajiya Bata Damu ba Sanin Halinsa ko Waya ya Kirata sai ya bata Lokaci kafin ya ce wani abu bayan sun gaisa. Kamar ana Fizgan mganar Daga bakinsa yace"Hajiya kinga Bakuwa ko..? Hajiya tace"Eh fa..Yanzu na Dawo Ciki Shamsu yace kai kace ya Kawota Shashena..! Karkaace kai yayi kamar mace kafin yace"Eh Hajiya..Aisha na kusa ko Hannatu..!? Hajiya tayi mirmishi tace"Suna Falo Tare da Bakuwar D'anmallam ko na fita na kirasu ne..? Sai da yayi shuru jin bai yi mgana ba yasa tasan yana jin nauyin yace ta kai musu wayar ne yasa ta Nufi kofa tana Fadin"Kada ka damu..bari na fita na kai musu wayar..! Da kamar yace ta barshi bari ya Kira Sarood din ammh Hajiya Har takai Falon ji kawai yayi tana Fadin"Lafiyanku kuka zauna kuka tasa Bakuwa agaba kuna kallo..?bana son Shanshanci..Ke Aisha karbi Waya yayanku na son mgana Dake..! Tafada tana mika musu wayar ganin yadda suka wani tasa Bakuwa gaba suna kallon Dariya sukayi harda Hanne yana ji sanda tace"Wlh Hajiya tana da kyau baki gani ba..? Hajiya ta tsaki kafin tace"Bangani ba..! Daidao Sanda Aisha tamai Sallama Cikin Girmamawa ta gaisheshi ya amsa Lokaci Daya yana Fadin"Ke da Hannatu meyasa bakuje makaranta ba..? Da Sauri tace"Yaya ai muna Jarabawa ne.kuma yau bamu dashi ni da Sadiya da Ikram duk muna gida Hanne kuma sun gama Jssce suna gida suma sai an koma Firstime..! Kansa ya kara shafawa ya manta fa ko Dazu Shamsu ya fadamai haka da sukaje Dutse suka Daukosu Daga Filin Jirgi,Dayake ta Kano suka Sauka Daganan suka Hawo Jirgin Daya kawosu Dutse. Cikin Muryansa mai Cike da Zati yace"Kunga bakuwa ko..? Tace"Eh yaya..Mai kyau da ita wlh ya sunanta..!? Dan Bakinsa ne ya Motsa kafin yace"Sarood..sunanta batajin Hausa ki rika mata Labarci yanzu dai me kuka bata..? Kai Tsaye tace"Ruwa da abun sha..Muka fara bata yaya..,! Kamar bazai yi mgana ba sai chan yace"Aisha ki kaita Dakin ku kice mata tayi wanka..Ta huta tukunnah kina jina..? Da Sauri tace"To yaya..! Kai Tsaye yace"Mika mata wayar na Fadamata..! Ba musu ta mikamata tana Kallomta Tace"Yaya..! Karba kwwai tayi ba Domin ta gane ba tana kara a kunne taji muryansa Nan da nan ta washe baki basu san me ya Fadamata ba suka ga ta mike Lokaci daya tana mika Aisha wayar Ita kuma tayi gaba sai gata tana Binta abaya Har Dakinsu Hanne ta Bisu da kallo kawai Har Toilet din sai da Aisha ta nuna mata sannan ta Fice ta barta bayan ta ja mata Kofar Dakin Hajiya ta shiga ta Isketa tana Duba wani Turaran wuta da aka aiko mata Daga garinsu Maiduguri duk da yanzu Saboda Rashin Zaman lafiya Danginta duk sun Dawo Cikin maiduguri wandanda suka Rage Mahaifinsu ya Dade da Rasuwa. Mikama ta wayar Tayi Hajiya ta karba  batayi mgana ba ita bata wannan Shisshigi sai Aishan ne tace"Hajiya Dakin mu yace na Kaita tayi wanka ta Huta..! Kai kawai hajiya ta gyadamata bata ce komai ba ba irin su daya da Aisha ba Abida ba mai Shigen Surutu ba da hannatu,yasa bata Dameta ba ta fice ta barta sai Faman Raba Turarenta take zata Bama abokan zamanta Sauran ta aika ma su mamanmu Dashi haka Hajiya take Ko sun san da abu ko basu sani ba Sai ta Dibar musu wannan Kirkin nata kowa yana Girmamata Saboda shi. Sanda ya gama wayar ajiyar Zuciya ya Sauke lokaci Daya yana Sauke wayar Daga kunnensa,kusurwan Falon Mallam yake kallo inda Cabet din Jerin Littafansa suke,Tunani yake yi yazai yi ya Sanar da Hajiya ya kara aure..?ga Halin da Sakina take Ciki Tunda ya Fadamata an Daura musu aure da Sarood take kuka taki cin abinci ta Daina mai mgana Har yau da suka so gida Allah ya gani bai taba son Sarood ba ammh Tana da kimar da bai isa ya Wulakantata ba. Daga Bayansa yaji Baba Sa"idu na Fadin"UMAR Baba mallam na mgana..?yace ko baka gama wayar bane..? Jin Haka yasa Lokaci Daya ya Dago kansa Tare da Juyowa Ya fara Tako Doguwar Kafarsa Zarara saman Tattausan Cafet din Dake Falon Malam din Tsarki ya Tabbata ga Shugaban Hallitun Duniya..Domin Tsabar kyau da Zati da kwarjini wajen bawan Allah nan,Shi ba Fari bane kuma ba Baki ba Fatarsa wani irin Fatace mai kalan Haske kamar na yan Moroci Tattausa Saboda jin Dadi da Hutu tana Sheki Dogon Namiji ne wanda ake Kira Ingarma yana da Fadin Kirji Daga Kafadunsa zuwa cikinsa ya Bude,FUSKARSA doguwa ce Sambal masu Dauke da matsaikatan Idanuwansa da Gashin gira dana Ido..Hancinsa Dogo ne ammh ba Sosai ba wanda ya karamai kyau da Zatinsa Sannan Bakinsa Zagaye da Saje baki wanda ke karamai kwarjini Daga kasa kuma gemunsa wanda yabar gemu kadan wanda bau wuce kamu Daya ba. Wanda ya Dace da Zagayyen Bakinsa mai dan Fadi kadan da Tudu,yana Sanye Cikin Pakistan Riga da Wando na yan Saudiya Rigar Tawuce gwiwansa Sannan wandon bai rufe kwarin Kafansa ba Kansa Sanye Cikin Hula irin ta Larabawa karamar nan wacce iyakarta rabin kansa mai Kulin Gashin Sakan Hulan Daga sama Wanda ya ba Sumar kansa Daga kasa zuwa sama sama Bayayyana Duk da ya Asketa ammh gatanan tayi kwance gwanin Burgewa sannan Goshinsa ga Bakin Tabon sallah nan wanda ke karamai kwarjini da Haiba. UMAR YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA kenan Namiji kwara Daya Tal da Bayan Sa"idu Mallam ke matukar kauna acikin Ransa a Cikin Jerin ya"ya ashirin din da Allah ya basa mai tarin baiwa da Allah kadai Daya Hallicesa ya sani mai kimanin Shekaru Talatin da Takwas zuwa da Tara aduniya. Har ya kariso ya zauna Kusa da Baba Sa"idu Baba Malam da Baba Sa"idu basu daina kallonsa ba. Suna kara yaba kyan zatinsa ko su kansu kwarjini yake musu Tabbas Qur"ani ba karya bane kana ganin Mahaddacinta kake ganewa Saboda Natsuwar dabam take. Kansa na kasa Cikin Muryansa mai Zaki yace"Afuwan Baba..na kira Hajiya ne..! Baba Malam ya gyada kai kafin yace"Kace Shashenta ka Sauki bakuwar taka ko..!? Kansa na kasa ya gyada kai Baba malam ya cigaba da Fadin"Hajiya ko bata san mutum ba ita din mai karamci ne..Zata karramata matuka..! Baba Sa"idu yace"Sosai shiyasa nace a kaita chan kaawai..! Baba Malam yace"Da kaji an ambaci Hajiya Jikin ka na rawa ka yabeta..Ina mamakin yadda ZAINABU ta kwacemin SA"IDU NA..! ya karishe Fada Cikin Zolaya. Baba Sa"idu na Dariya Danmalam kuma Mirmishi kawai yayi. Kafin Baba Sa"idu yace"Haba dai..Ai Tsakanin Uwa da d'a akace sai Allah baba..Kuma haka Tsakanin Uba da Dansa sai Allah har Abada Sa"idu na Baba Malam ne ba shi ba duk wadanda ke karkashin sa naka ne Baba..! Baba Mallam Zuciyarsa kamar Farar takarda ya gyada kai kafin yace"Allah ya albarci Rayuwarka Kai da iyalanka Sa"idu..! Suka amsa shi da Umar atare,Kafin Baba Malam yace"Ni na hana Sa"idu ya Fadama Hajiya komai..na bari sai ka zo..Ko sauran abokam zaman nata ban Sanar da kowa ba..Ina Fatan ka Fadama ita Dayar iyalin naka ko..? Kansa na kasa yace"Eh na sanar da ita tun muna chan..! Mallam yace"Dakyau haka ake so..Allah ya zaunar daku lafiya..Sai ka zama jajirtattacen adalin zama da macen Fiye da Daya sai Adali Umar..Bana jinka nasan bazaka taba aikata wani abu mara kyau ba..Sannan itama Diyar Kattab din indai Halin Mahaifinta ta Biyo Har Abada bazakayi nadama ba..! Baba Sa"idu yace"Allah ya sa...! Kansa na kasa shidai bai ce komai ba basu Damu ba Sanin Halinsa Shuru Shuru bai da Hayaniya. Baba Malam ne ya kalli Baba Sa"idu yana Fadin"Sa"idu ka tafi wajen aika..Nima anjuma kadan zani Gidan Sarki Tun jiya Sakon sa ya isoni yana son ganina..Umar kuma ya shiga Cikin Gida ya gaida iyayensa zuwa anjuma sai mu zauna gabadaya domin a gabatar da Bakuwar data shigo Cikinmu Gabadaya..! Baba Sa'idu ya jinjina kai yana ma Malam Allah ya kiyaye Hanya. Tare sukayi mai Sallama suka Fice shida Baba Sa"idu sun Dade aharaban gidan suna jingine jikin Motar Baba Sa"idun suna mgana kafada na gugan kafada Malam na daga cikin Falonsa yana Hangesu ta Wandow Falon Lokaci Daya ya saki kayattacen Mirmishi. In ka gansu kamar wasu yaya da kaninsa uwa daya uba Daya ya Tabbata abunda bazai iya Fadamai bane yake Sanar da Sa"idu Akwai Shakuwa da Fahimta a Tsakaninsu Yana Daukansa kamar kaninsa Shima yana Daukansa kamar yaya kuma Uba agaresa Sun dan jima suna mgana kan yana Fadamai bai Tsara Karin aure yanzu ba, sai dai kana naka Allah na nashi ne Baba Sa"idu na ta bashi Wasu Shawarwarin kafin suyi sallama ya Shiga Mota ya wuce Gidan gona yayinda Shi kuma ya Fara takawa yabar Filin Haraban gidan zuwa Shashen Hajiya ammh Kuma Ransa da da Kallonsa na Shashen Anty Amarya yana Tunanin ko Sakina ta Daina kukan..?ya manta Rabonsa Daya ga taci wani abu sai ruwa kawai..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima Yusuf gwarzo (Besty) Alherin Allah ya kai miki a dukkan inda kike* *🅿️09* Cikin Tafiyarsa ta natsuwa ya karisa Shashen Hajiya babba kamar yadda yake a ka"idarsa sai ya fara isa shashen Mallam sun gaisa sannan sai ya shiga cikin gidan Daya bayan Daya ya Bisu ya gaishesu. Hajiya na cikin Dakinta har alokacin Daya shigo Aisha ce da Hanne har Lokacin afalon yana Shigowa Cikin Sallamarsa da Muryansa mai Zaki da Sanyi a koyaushe,Lokaci daya da kamshin Turaransa na Arab yayi musu Sallama..! Gabadayansu suka mike Cikin Fara"a da Murnan ganinsa domin sun Dade basu gansa ba Tun Karshen wanchan Shekara sanda yazo Lokacin Duba Hajiya ce Datayi ta Fama da Kafa suna makaramta basu gansa ba kuma Kwana Biyu yayi ya koma. Hannayensa duka Sanye Cikin Aljihun wandonsa ya Kariso Tsakiyar Falon gabadayansu har suna Hada baki wajen gaisheshi da yanayin Natsuwarsa ya kallesu yana amsa gaisuwarsu yana kara ganin girmansu acikin Idanuwansa. Kai Tsaye yace"Hannatu Aisha meyasa baku je makaranta ba..? Da Sauri Aisha tace"La yaya bana Fada maka ba..! Sai Alokacin ya tuna da Sauri yace"ohm.Sorry na manta..Allah ya bada sa"a..! Suka amsa da Ameen gabadayansu sai kuma yayi shuru yana kara nazarin Falon kamar me neman wani abu basu Damu ba Sanin Halinsa Sannan babu wani Shakuwa sosai a Tsakaninsu Tunda shi Babba ne sannan Lokacin da suka taso baya kasar yana Madina so zamansa Dasu bashi da yawa ammh duk da Haka yana da Kwarjini da baiwar da kowa ke girmamasa,ba Duka yake yi ba ba kuma Fada ba,Shi ina ma ya zauna ballatana yayi Hukuncin ..?in yazo kuma bai wani Dadewa yake komawa sai dai AllAh ya riga ya bashi wannan girman kuma ya Dauka kamar yadda In mallam yayi mgana bamai Musamai haka shima mgana Daya zai yi Cikin kwanciyar Hankali da Salama kowa zai shiga Taitayinsa bawai bashi da Sakewa bane, bai da yawan wasa da Dariya sannan bai da mgana ballatana Hayaniya yana da Matukar Sanyi Sosai a lamuransa. Kamar ma ya manta daasu acikin Falon Saboda yadda yayi Shuru bai kara mgana ba sai chan ya kalli Aisha kafin yace"Ina bakuwar ku.? Da Sauri tace"Na kaita Dakinmu na nuna mata Tiolet tana ciki na barta Tun dazu..! Kai ya gyada kadan kafin yace"Ina Hajiya..? Wannan karon Hanne ce ta nuna mai Dakinta tana Fadin"Tana ciki Yaya..! Bai tsaya kara mgana ba ya Kama Hanyar zuwa Dakin Hajiya Cikin Natsuwarsa kannensa suka Bisa da kallon Sha"awa Duk cikin gidan nan ba kamarsa Sai dai abiyo bayansa. Sai da suka Tabbatar da ya shiga Dakin Hajiya sannan Hanne ta Juyo Tana Fadin"Ya Aisha kinga yadda Ya D'anmalam ya kara kyau kuwa..?Wlh nima ina son naje Madinar nan Watarana..! Aisha tana jinta batace mata komai ba illah ta Cigaba da Duba Littafin Dake Hannunta Hanne bata Damu ba Sanin Halin Aishan itama din mai Sanyi ce. Hajiya na Tsaka da kasafin Turaranta Taji Sallamarsa Cikin Sanyi da Haiba Lokaci daya da Kamshin Turaransa mai Sanyaya Zuciya batasan Lokacin data saki Mirmishi ba Cikin Farinciki ta amsa sallamar tasa tana jaye kayan gabanta Lokaci Daya tana mai maraba. "Maraba..Maraba..Maraba da Danmallam maraba da bakin madina Bakin Larabawa..! Sai alokacin hakoransa kadan suka Fito yana Mirmishi gaban Hajiya ya Duka kansa na kasa yace"D'anmallam dai Hajiya..?Har yaushe ne zaki Fara Kirana da Umar ne..?Alhalin Baba Sa"idu Sa"idun sa kike kiransa Hajiya..! Hajiya na Dariyan Farincikin ganin Yaronta ta kauda mganar da cewa"Masha Allah..Danmallan me kuke ci a Madinar ne.?gabadaya ka Sauya ka koma kamar Balaraben chan..! Kai kawai ya gyada yana Shafa Gemunsa kafin yace"Hajiya bakomai..Sai nasaran addu"an ku gareni..! Hajiya tace"Hakane..Allah ya kara Tsareka Allah ya Dafa maka Allah ya albarkaci Rayuwarka..! Ya amsa da Ameen kafin ya Dago yana Fadin"Hajiya baki ce Allah ya bani Zuru"a ta gari ba..! Hararansa tayi kafin tace"Ko ban Fada ba..Ina maka wannan addu"ar D'anmallam..! Daman yasan haka zatace yadda Hajiya ke kunyarsa ko Ita Bafullatanane sai haka Tambayan kowa da kowa yayi tace duk suna Lafiya,Shuru ya biyo baya shi bai ce mata ba itama yasan bazatace ba Hajiya nada wannan Halin bata matsa ma Mutum akan abunda tasan Dole zata saani Shiyasa bata ce masa komai kan Sarood ba shima bai ce mata ba. Kansa na kasa yana Duke ita kuma tana Cigaba da Zuba Turaranta Ganin Yaki zama kuma yaki tashi yasa ta kallesa tana Fadin'Ka zauna mana..Kada Tsugunnen ya gajiyar Dakai..! Kai ya girgiza kafin yace"Hajiya Ina da gajiya ajikina..So nake na shiga na gaisa da su Hajiya uwa..Kafin naje nayi wanka na Huta..! Kai ta gyada kafin tace"Hakan ma ya kamata..Mallam ya fitan ne..? Kansa na kasa yace"Bai riga ya fitan ba ammhh yace yanzu zai fitan..Muna ma nan Haraba ni da Baba Sa"idu yanzu ya wuce gidan gona..! Hajiya tace"Sa'idun Zainabu da Malam..ya shigo mun gaisa tun zuwansa..! Bai yi mgana ba ita kuma ta kallesa tana Fadin"Dame zaka Karya..?nasa dai yaran sun yi maka Sinasir da waina..Bansan kuma me zamu ba wannan bakuwar ba kasan ku achan ba irin Cimar mu bane naku..! Sai alokacin ya Dago kafin yace"Da kuli Hajiya..? Kai ta gyadamai tana yar Dariya shima Mirmishin yayi yana Fadin"Yaushe Rabona da waina da kuli Hajiya..?Naji dadi sosai su dafamin ruwan Tea da na"a na"a,su hadomin da waina din ita kuma Sarood su hada mata Tea su soya mata Kwai is ok..! Hajiya bata wani Damu ba tace"Shikenan.Ammh a Shashen mallam zaka Huta..?ko yanzu zaku isa gidan naku..? Da Sauri yace"Sai Dare hajiya..Dakin su Shamsu zan yi wanka na Huta zuwa an juma..! Hajiya tace"Na manta ne da na saka su Akilu sun gyara maka Dakinsu Nazem ka Zauna aciki..! Kai ya kada kafin yace"Bakomai Hajiya nan din ma ya isa..! Hajiya tace"Ai shikenan..! Yana kallonta Kafin yace"Hajiya Turare kika fara saidawa..? Hajiya tace"A"a Goggonku Yakura ta aikomin dashi shine nake rabawa zan aikama sauran iyayanka Sauran kuma na matan Sa"idu ne..! Danmallam ya Murmusa kafin yace"Su yaya suna Lafiya..! Hajiya tace"Duka suna Lafiya..! Daganan sukayi shuru hirar ta kare ya Dade kafin ya tashi ya mata sallama ya Fice,Bayan ya fito su Hanne sun zata zai nemi Sarood sai dai bai ce musu komai ba ya Fice bayan Fitarsa Hajiya ta leko tace Hanne ta Dafa Ruwan Tea ta soya kwai ita kuma Aisha taje wajen Shamsu ta karbi key din Dakin Su Nazem ta dan gyarama Danmallam ya samu wajen da zai karya ya Huta. Dukkansu da toh suka amsa Aisha tatashi ta saka Hijabi ta Fice,Hanne kuma ta shiga Kitchen. Daga Dakin Hajiya Shashen Hajiya Uwa ya isa Tana ganinsa Cikin Fara'arta ta fara mai maraba itama Dukawa yayi yana gaisheta ta amsa tana Fadin"Umaru basai ka jira mu zo sannu da zuwa ba..! Kansa na kasa bai ce komai ba tayi Dariya ya tambayeta yaran tace kowa Lafiya sai ga Umaima ta fito ta gaisheshi ya amsa yana kallon Hajiya uwa kafin yace"jikinta ya daina tashi ko..? Hajiya Uwa tace"To ya dai yi Sauki Umaru..! Kai ya jinjina kafin yace"Allah ya kara afuwa..Nazo mata da wasu manganuna in na Huta zan kawo mata ta fara amfani dashi mu gani..! Hajiya Uwa ta fara mai godiya yana amsawa Har ya fice tana Rakasa da addu"an haka take ita tana da Kirki kamar Hajiya take. Daganan sai bangaran Haj.Nasara itama ta karbesa sosai suka gaisa da Tambayan bayan Rabuwa Ikram ya gani tazo ta gaisheshi ya amsa yana kallonta ganin ta girma har zai tambayeta meyasa bataje makaranta ba sai ya tuna da mganar Aisha sai ya Fasa Yana Shirin Fita ne Take tambayansa ko da ba Sakinar suka zo bane..? Cikin Haibarsa yace"Tare muke da ita..Tana bangaran Anty Amarya..! Baki ta tabe batace komai ba yayi mata Sallama ya fice yana fita tace Ikram ta shiga Kitchen ta Dafamai Tea da soya kwai,Saboda Umar Domin in yazo garin ba wacce bata kokarin kyautatamai kamar yadda zata kyautatama Malam. Kai Tsaye Daganan sai Shashen Anty Amarya ita kam koda ya Shiga bata Falon Sa"adatu kadai ya gani Tana Kwance saman kujera ko Sallamarsa ma bataji ba sai dai ta gansa saman kanta Cikin Muryansa yana Fadin"Ke baki jin sallama ne..? Kamar ta kifa haka ta sauko daga kan Kujeran tana Raba ido Cikin Kifta ido Tace"Sannu da zuwa ya D'anmallam..! Bai amsa mata illah Falon Dayake bi da kallo kafin yace"Ina Anty..? Da Sauri ta mike tana Fadin"Tana Dakinta ita da Ya Sakina..! Baima ce ta Kirata ba yaga ta wuce sai bai kirata ba Hannayensa Cikin Aljihun wandonsa ya kurama waje Daya ido kamar mai nazari. Sa"adatu sai da tayi knooking Domin Tun isowar Sakinar tana kuka suka Kule Cikin Daki ita da Anty basu Fito ba,Kuma sun kulle kofar Daga ciki Anty Amarya da Ranta ke bace domin ta gaji da Lallashi da Tambayan Sakina meke Damunta taki gayamata gabadaya Tunda suka iso take kuka taki mgana ballatana tasan meke Faruwa.. Dagachan tace"Waye..? Da Sauri Sa"adatu tace"Nice Anty..! Tashi tayi taje ta Bude Kofar da Sauri Sa"adatu tace"Anty Ya D'anmallam yazo yana Falo..! Da sauri tace"Yazo .? Ta daga kanta Sakina ta juya tana kallo wacce ta Dunkule kan gado tana kuka kafin ta Dawo da kallonta kan Sa"adatu tana fadin"Kice mai gani nan zuwa..! Daganan Sa'adatu ta juya ita koma ta maida kofar ta Rufe ta Dawo bakin makeken gadon Dake Bedroom din inda Sakina ke Dunkule ta Dade tana kallonta kaf ta gama Hasashenta bata hango abunda zai sa Tunda suka iso Sakina ke wannan kukan ba ta kuma yi Tambayar Duniyar nan Sakina taki Mgana. Kai ta kada Kafin tace"Ai shikenan Tunda bazaki mgana ba..ga Umar din chan yazo..Bari naje na tambayesa kila shi ya fadamin abunda ke faruwa..! Har ta bar Dakin bata Dago Daga kukan datake yi ba ballatana tasaka ran zata kalleta Ta iskeshi Tsaye bai ko zauna ba Sadiya ta fito sun gaisa Sa"adatu ta shiga Dakinsu ta Fadamata zuwanshi. Yana ganin Fitowarta ya Rage tsawonsa ya Durkusa kan kafafunsa yana gaisheta ta amsa Lokaci Daya Tana zama kan Daya daga cikin kujerun Dake Falon. Daga gaisuwan ne bai kara cewa komai ba kansa na kasa yana kallon adon Zanen jikin Tattausan Cafet din Dake Falon. Anty ta kalli su Sadiya kafin tace"Ku tashi ku shiga ciki..! Ba musu suka mike zuwa Dakinsu sai da taga Shigewarsu kana ta maida Hankalinta kansa kafin Tace"Umar meke Faruwa ne..?ko kun samu Sabani da Sakina ne .?Tunda kuka iso take kuka gatachan kwance kuma nayi Tambayan Duniyan nan tayi banza dani har yanzu taki cemin komai..Shine nace bari kai na Tambayeka meke faruwa ne .? Kansa na kasa bai Dago ba abu Dayane ya kara bashi mamaki me Sakina ta Dauki kanta ne..?tana Tunanin kukanta da Rigimanta zai sa afasa komai..?ai ta makaro Domin bakin Alkalami ya riga ya Bushe..Sannan bata isa yasa ya Sauya abunda Allah ya Tsaramai ba Duk da karin aure bai Cikin Tsarinsa. Yasan yana da Sanyin Hali baya son Damuwa da Hayaniya ammh tasanshi Yana da zuciya mai karfi wanda in yagaji da baka baki bazai biyema iskancinka ba zai Fita batunka ne kamar ita yadda tayi mai tun suna Madina yake bata baki ganin yadda Hankalinta ya tashi bayan ya gayamata bayan an Daura auran Abunda yasa ya Biyemata yana ganin ya bata mata Tunda shima abun Daga sama yazo mai ammh akallah ba Dadi Kaji Mijinka yayi aure Lokaci Daya sai dai ya gaji da Lallashinta zai kyaleta In ta gama kukan don kanta ta Hakura shi bai kuma san da wani Kalma zai kara lallashinta ba. Anty Amarya ta gaji da jiran amsar sa bai ce mata komai ba gabanta nata Faduwa kada matsalan yazama babbace Fiye da Tsammaninta. Yasa ta gyara zama tana Fadin"Kayi Shuru..!?Ina fatan Allah yasa abun bai kai ku ga Saki ba..? Sai alokacin ya Dago yana kallonta bata ga wani abu a Fuskarsa ba Illah Haibarsa da Zatinsa Cikin kakkausan Muryansa mai Cike da Sanyi yace"Babu ma mgana makamancin wannan Anty..! Ajiyar rai ta sauke na samun natsuwa kafin tace"To me ke faruwa..? Nan ma Shuru yayi mata ta kara kallonsa tana nazarinta har ta Fidda rai da zai yi mgana sai chan taji yace"Tunda bata gayamiki ba..Bakomai kenan..! Kai Tsaye ya fada batare da Tunanin wani abu ba ya mike yamata Sallama ya Fice Daga Dakin tana Binsa da kallon mamaki. Aranta tana ayyana wani abun Meke Faruwa..?meyasa Sakina taki mgana..?tana ji ajikinta koma miye babban al"amari ne sannan ta godema Allah daya kasance ba Zencen Saki bane Komai miye ai zai zo da Sauki. Tashi tayi ta koma Dakin ga mamakinta sai ta iske Sakina ta shiga wanka sai taji Dadi,Yasa ta fita da Sauri zuwa Dakin su Sadiya tace su tafi Kitchen su sama ma Sakina abunda Zata karya dashi Dakin ta koma ta iske Sakina ta fito Fuskarta Duk ta kumbura idanuwanta duk sun shige Saboda kuka. Anty Amarya ta kalleta tana Fadin"Ko kefa Sakina..? Dagowa tayi ta kalleta Fara ce kyakyawa Daidai Misali sannan ita din mai matsakaicin Tsawo ce Tana da Jiki kadan da Jikin mata. Kai Tsaye tace"Ya gayamiki wani abu..? Anty tace"Kema kinsan bazai yi mgana ba..Umar yafi Ubansa Miskilanci da kyaluwa..! Dan Mirmishin Fatan baki tayi Lokaci Daya tana Cije bakinta Towel ne Babba ajikinta taja Kujeran gaban madubi ta zauna ta Fara Shafa mai,Acikin Ranta tana jin kanta yayi mata Girma kamar zai Rabe Biyu Saboda Tsananin Kunar da zuciyarta ke mata. Tana gama Shafaa mai ta Sauya kaya Cikin Wata Riga da wando Saukakku,Lokacin Sadiya ta shigo mata da Faranti shake da kayan karyawa Tea kadai ta sha bata iya cin komai ba,Bakinta ba Dadi Saboda yanayin Datake ciki. Tagama kenan sai ga Anty Amarya ta shigo Dakin tana kallon Farantin Dake gabanta take fadin"Ya haka..?naga baki ci komai ba..? Sakina na Sake komawa kan gadon tace"bakina ba Dadi Anty..! Anty ta waro ido kafin ta karisa gefen gadon ta zauna tana Dafata Lokaci Daya tana Fadin"Ke na tabaki da Alheri Sakina..Allah yasa abunda muka Dade muna jira ne..? Cikin Mamaki take kallonta kafin tace"Me kenan..? Kai Tsaye tace"Ciki mana Sakina..Naji kince bakin ki baya Dadi..shine nake Tunanin kodai kodai..! Da Sauri ta katseta ta fadin"Ba ciki bane Anty..Wannan al'amarin yafi gaban na..Rufo kofa kizo kiji..! Da Sauri tatashi ta Rufo kofar ta Dawo ta Zauna kusa da ita kamar wata kawarta. Sakina ta Fara matsan kwallah kafin tace"Anty Umar fa aure ya kara..! Anty tayi wani Sansarai rai kafin tace"Aure wani irin aure kuma..? Sakina ta ballo Hawaye saman kumatunta kafin tace"Aure da kika Sani Anty..Abun bakin cikin ma bai Fadamin ba sai da aka Daura auran. ! Anty Amarya ta Dafe Kirjinta kafin tace"Daman da gaske kike yi Sakina..!Wani irin aure kuma ana Zaune kalau..! Sakina tace"Uhm yadda kikaji haka naji Anty..Ni ba komai yafi Tadamin Hankali ba..Irin matar daya aura..Anty Balarabiya ina ni ina kishi da Balarabiya..? Ta karishe fada tana Kuka Wiwi Anty Amarya ta Dora Hannu akanta tana Fadin"Na shiga tara ni Marliya..?wannan wani irin kaddara ne..? Sakina ta kwanto da kanta Saman Cinyar Anty Amarya kafin tace"Kaddara mai muni ma Anty..Kinga kyan yarinyar..?wlh ko gasar kyau ta Shiga sai taci..Tafini komai da komai ta bangaran kyau da Zati da nasaba da asali Wlh Anty wannan suka fara zama da Umar ni Bora zan zama..! Ta karishe Cikin gunjin kuka Anty Amarya gabadaya jikinta rawa yake yi Cikin Tashin Hankali tace"Wai garin Yaya haka ta faru...?Diyar wacece ya auran..? Sakina tace"Diyar abokin Baba Mallam ne..! Anty Amarya tace"Kattab..? Da Sauri ta Daga kai kafin ta cigaba da Fadin"Ita..Diyar su din nan kwara Daya Sarood..yadda Umar din yace min shi Abu kattab din ne ya bashi Auran kuma bazai iya kin karba ba..Ni ban sani ba saida aka Daura auran a Satin da zamu taho..! Anty Amarya gabadaya Hankalinta baya Jikinta Har Sakina ta cigaba da Fadin"Tashin Hankalina Daya Anty..In tazo ta Haihu fa..?wlh Bora zan zama a idon Umar da Danginsa na zama bani da wani amfani..! Da Sauri Anty Amarya tace"Ina.karya ne..Ba wanda ya isa wlh..! Ta fada Lokaci Daya tana Ture kan Sakina Daga Jikinta ta mike tana Mazari Cikin bacin rai tace"ba wanda ya isa ya maidake baya Sakina..Kamar yadda ban zama baya ba..Wani Cikin ya"yana bazai taba zama baya ba..! Take Fada tana Huci Sakina ta Mike Zaune tana Sharan kwallah kafin tace"Nama zama..Domin da ita muka zo kasar nan..! Da Sauri ta zaro ido tana Fadin"Eyee...! Sakina ta Daga kai tana Fadin"Eh tana ma Cikin gidan nan..Inaga Shashen Hajiyarsa yace shamsu yakaita..! Anty Amarya ta rike Haba Kafin tace"Kenan iyayen nasa sun san da Labarin auran shine mu bamu ji ba..? Sakina tace"Ni bansani ba..Ammh dai Malam ya sani Da Baban su Jafar tunda naji suna mgana tun muma chan..! Anty Amarya ta Lailayo Ashar ta Dankara kafin tace"Sa"idu...Sa"idu..Ko bai kira Malam ba..Ina mai Tabbatar miki Sa"idu zai fara kira..Sa"idu ne ja gaba kan komai..Ko Malam da Hajiya basa tsallaken Shawaran Sa"idu abunda yace shi akeyi acikin Gidanan Sakina..! Sakina ta Sharce majina tana Fadin"Anty ya zamu yi..?wlh karki so ki ganta Kinga kyanta..? Anty Amarya Haushi ya kamata ta Ballama Sakina Harara tana Fadin"Kyan me..?kyanta na banza..Takai ki wayau ne..?Kyan ne kawai ammh batakai Budewar ido ba ..ina taje ina ta taka..?Irin wadanan kyan ne kawai da zaman waje Daya na Tabbata bata samu wata Sakewa ba..! Sakina tayi shuru tana kallonta kafin tace'"Eh kam..kamar sakara haka take..Sai dai namiji ba ruwansa da wannan..! Anty Amarya tayi Mirmishi kafin tace"Kada ki damu kanki..Ki Share Hawayenki kada ki kara kuka..Waannan auran wani matakin Nasarmu ce Sakina..! Sakina tace"Taya ya..? Anty Amarya ta kama Hanyar fita tana Fadin"kidai ki saka ido kawai..Mu zuba mu gani..! Shege ka fasa..! Daga haka ta Bude Kofar ta Fice tana Tafe tana Mirmishi ita kadai kamar an ce mata an biya mata aikin Hajji. Falo ta koma ta Zauna ta Dora Kafa Daya kan Daya tana Kadawa kamar wata yar yarinya yar shekara Goma sha. Sakina kuma tana Fita ta koma ta kwanta Damuwarta ya ragu,Saboda tasan duk abunda Anty tace kada ta Damu to tasan cewa kada ta Damun komai zai zama Daidai,Daman ga Rashin barci ga Damuwa yasa batasan Lokacin da barci ya kwasheta ba Cike da Mafarkin yadda makomarta zai kasance Tsakaninta da Umar da Sarood. ****** Amina sai gabda Azahar tatashi Daga barci tana mika Hamida bata Dakin yasa bata damu ba tatashi ta shiga waanka Lokaci daya ta Dauro alwala sai da tazo tayi Salla kana ta Sauya kaya ta saka Riga da Sikat na wani leshi da Mamanmu ta Dinka musu ita da Hamida. Sannan ta fita Tsakar gida ba kowa ko'ina tsit,Kitchen ta Zarce ta iske ya Zulahait ta gama abinci Kuskus da Miya da nama Amina tayi Dariya kafin tace"Mijin ya Zulaiha zai ja kaya Wlh...! Haka take fada tana Dariya kafin ta Diba iya sonta ta cika nama ta koma gefe taci tayi kat ta koshi,sannan ta fito taje bakin Famfo ta wanke hannu Dakin Mamanmu ta leka ta isketa tana Sallah Tana jin Hayaniyar Hamida a dakin Yaya taki Shiga Daki ta koma ta Sake kwanciya taci ta koshi Takaichinta Daya bata zuwa da Littafin hausa agida iya makaranta take karatunta ko boko ko Islamiya. Ammh bata zuwa dashi gida ba Domin tana jin Tsoro ba ko wani abu ba, Aron daman iya makaranta ne ana tashi zainab take karba Saboda na mamanta ne take aro mata itama ba"a Sani ba agida. Yasa barci ya kara Daukanta bata Sani ba sai Bayan azahar ta tashi Shima Mamanmu ce tatasheta tana Fadan ta Daina barcin yammah ba kyau. Lokacin datasahi  ta ga mamanmu Sanye da Hijabi tana Mitsike ido ta Sauko Daga kan gadonta tana Fadin"Mamanmu ina zaki na ganki da Hijabi..? Mamanmu tace"Gidan Mallam zamu shiga ni da yaya..Danmallam sun iso tun Safe..! Zamu je maraba da barka da zuwa..! Amina ta tabe baki kafin tace"Mamanmu sai ku bisa..?bashi zai zo ba..? Mamanmu na Dariya tace"Basai kin Fada ba zai zo..ammh yana da kyau mu bara zuwa din..! Ta fada tana Ficewa Lokaci Daya tana Fadin"Ki tashi kiyi sallah tunda ke bazaki shiga ba..Tun dazu hamida tatafi..! Mamanmu bata tsaya ba ta fice Amina tana so ta tambayeta chan gidan nasa Hamida tatafi ko gidan Baba Malam..? Bata samu mai bata amsa ba yasa ta Tabe baki ta fito Bakin famfo tayi alwala tazo tayi sallar Ta gaji da kwaciya bayanta har ya gaji yasa ta zauna tana Tunane tunane Zulaihat na Dakin Yaya tun Safe batama zauna adakin ba Tana jin tashin mganar Ya Zeena na tashi,Yau Alhamis ba islamiya Shiyasa suke gida. Bata fita ba Sanin Yau jidalinta na Saman kanta in taje Bakinta bazai yi Shuru ba kuma baza"a samu Zaman lafiya ba. Yasa ta Cigaba da zama inda tayi Sallar har ya Zeenatu ta Shigo ganin yadda Amina ke zaune da Hijabi yasa abun ya bata mamaki yasa ta kalleta kafin tace"Amina yau kuma Lazimin yammah aka fara..? Amina ta kalleta shekesheke kafin tace"Uhmm..! Daga haka bata kara mgana ba Ya Zeena tayi Dariya tana fadin"Gwara dai kiyi shuru..yau gidan ya Sarara..! Amina batace komai ba Tunani take taje gidansu Hanne ko A"a tana Shawara da zuciyarta ne Har ya zeena ta Dauki abunda zata Dauka ta Fice ta bar Amina nan zaune tana cigaba da Shawara tasan Hanne Sarai in taje sai ta basar da ita Kafin su shirya. Tana nan zaune har su Mammanmu suka Dawo bata tashi ba har Lokacin kuma Hamida bata Dawo ba Amina ta Mike tana Fadin"Alqur"an sai naje naga ni..Hamida iyayan gulma ba"a Dawo ba..! Ko Hijabin jikinta bata Cire ba,Ta fice batare da tace ma kowa gata zuwa ba. Mazan duk basa nan suna msallaci wajen karatun yammah Da Baba Mallam ke yi,yasa kai Tsaye ta Nufi Shashen Hajiya Babba. Daga Kofar ta fara kiran sunan Hanne kafin ta shigo tana Fadin"Hanne ni zaki Wulakanta ina ta Kiranki kinyi banza dani..! Tafada Lokaci Daya tana Shigowa Falon batare data Tsaya Lura da kowa ba,Idanuwanta suka fada kan Hanne da Hamida dake gefe sun hada kai suna mgana Amina ta rike baki Tana Fadin"Hamida an ci amanata..Shine ko ki tasheni sanda zaki taho..! Tafada Lokaci Daya tana karisawa gabansu Hannu tasa tana jan hannun Hanne Lokaci Daya tana Fadin"Hanne taso kiji..! Hanne taki tashi lokaci Daya tana Fadin"Ba inda zani..Lokacin da naje ina miki mgana kin manta me kikacemi ..? Amina tace"Hamida ce zata Hadamu Hanne..?Haba hannenta Hannen Aminene..! Tafada tana Dariya har tana Jan kumatun Hanne da Duk Dauriyanta sai da tayi Dariya. Hamida tace"Amina kinzama abun kallo kin shigo baki gaida kowa ba..! Sai alokacin ta juya tana bin wadanda ke falon Idonta ya Sauka kan Sa"adatu lokaci Daya ta balla mata Harara,Sai kuma wacce ke kusa da ita Tana Sanye da Babban lullube asamaa kanta Sakina ce Anty Amarya ta saka Sa"adatu ta rakota tazo ta gaida Hajiya bayan sun gaisa Hajiya ta shige ta barsu da yara. Sakina taki tafiya ne tana so taga ta inda Sarood zata fito Saboda ta tabbatar tana Shashen Hajiya,Shi kanshi Umar din bata kara jin motsinsa ba ance yana Masallaci Wajen karatun mallam Sai ga Amina ta shigo Tunda ta shigo Kowa ya koma kallonta Saboda yadda ta Fado falon kamar Daga sama. Amina ta Dawo da kallonta kan Hamida kafin tace"Su waye..? Ta fada tana yamutsa baki Da Sauri Hanne tace"Matar ya D'anmallan ce Anty Sakina..ki gaisheta..! Amina taja Tsaki da karfi kafin tayi mgana Hamida tace"Amina don Allah...! Yasa bakinta ya mutu,Ranta bace ta Juya tana Fadin"Ina yini..! Sakina sai da ta kare ma Amina kallo sama da kasa kafin ta tabe baki tace"Lafiya..! Lokaci daya tana kallon Sa"adatu kafin ma tayi mgana tace"Amina ce..Ta gidan Baba Sa"idu..! Sakina ta Tabe baki ta kauda kai ita bata gabanta abunda ke gabanta ya Isheta tana so ta Sako mganar Sarood wajen Aisha sai dai bata so ta Fahimceta sannan Aishar ma Azkar ne a Hannunta tana karantawa bata bi ta kan abubuwan dake Faruwa acikin Falon ba. Amina ranta yakai kololuwa abaci da karfi tace"Jaruba..Kayyasa..! Hanne bata bari ta karisa ba ta Tashi Tsaye ta Toshe mata baki lokaci Daya ta jata suka zauna kan kujera tana Mata rada a kunni. "ke ya D'anmallan yazo da bakuwa wata balarabiya mai kyau baki ganta ba..? Amina jin gulma yasa ta saki baki tana Fadin"Kice Wlh..?wacece tana ina..!? Hanne tace"Tana Dakinmu..Bamu san ko wacece ba..Hajiya ma bata ce mana komai ba..! Amina ta mike tana jan hannu tana Fadin""muje naganta..! Hanne ta mike tana Fadin"Ke banza batajin Hausa sai labarci..! Amina tace"Muma mun iya..Kaifa antum ne sai mu sakar mata..! Sai da Hanne da Hamida sukayi Dariya dukkansu suka Dumguma zuwa Dakin Sa"adatu da Sakina suka Bisu da kallo banza. *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️10* Koda suka shiga Dakin sun iske Sarood na zaune gefen gado tana Danna wata karamar farar wayar Dake hannunta ta sauya kaya zuwa Saukakkan riga ta larabawa Sannan mayafin kanta ya zame kadan wanda ya bama Gashinta Daman bayyana har gadon bayanta. Amina Sakin baki tayi tana ganin Tsabar kyau da zati ita kuma Sarood tana ganinsu ta washe bakinta Hakoranta Farare suka bayanna Ta gane Hanne Hamida da Amina ne bata gane ba ammh ai tasan Kannen Umar ne,Hannu ta mika musu alaman su matso kusa da ita Lokaci Daya tana Sauko da Tattausasun Fararan Kafafunta a saman Cafet din Dakin kafarta kamar ta jaririn da aka Haifa yau bai taba taka kasa ba. Kamar masu neman gafara haka suka buga Layi agabanta bayan ta saka Hannunta Zara zara da yaji Jan kinshin Larabawa ta matsar da Farantin da Hanne ta kawo mata Fankwasau kuma tacida yawa Saboda mai gishiri akayi. Daya bayan Daya ta fara tambayansu Sunayensu cikin Harshen labarci wanda sai ma sun Dage suke iya gane abunda take fadi,Amina ce karshen Fadamata Sunanta Lokaci Daya tana mika mata Hannunta alamun musabaha. Sarood bata da bakunta gata da Sakewa nan da nan ta karbe hannun Amina Cikin Fara"arta,Amina taji hannu kamar auduga batasan sanda tace"Jar uba..Kun ji hannunta kamar Auduga .?ina ga tunda aka Haifeta bata taba wani aiki ba..?kayya sannan Hanne kunga gashinta mai kyau ce Wlh ta Burgeni..! Har acikin Ranta ta kejin Sarood din ta kwanta mata Har tana Ji dama ace itace matar Ya D'anmalam din da wannan Banzar Sakinar. Jin abunda Amina tace ne yasa suka rika bata Hannu Daya bayan Daya alamun musabaha su ba gane ma mganar suke ba in tayi musu mgana sai dai su daga kai Amina ce take ji kuma bazata taba nuna tasan ma tana ji ba Amina bayan Baba Mallam ba wanda yasan Wacece Amina A zahirinta. Tasata sukayi kamar sun samu Tibi suna kallon Duka motsinta Sai dai ta kallesu ta Murmusa Amina ta Raba gefen kunnen Hanne tana Fadin"Hala Budurwansa ne..? Hanne tace"Kai..Bana Tunani ko kila Diyar abokin Baba mallam ne Dake chan Madina .! Hamida tace"Zata iya yiyuwa haka din ne..Kila tana so tazo taga kasarmu shiyasa ta biyosu..! Da haka suka bar mganar Musun ammh acikin ran Amina Tana Tunanin haka kurum sai yazo da ita..?da wata akasa. Basu da Niyyar Fita sai Hirarsu sukeyi sai dai ta kallesu tunda baji take yi ba, basai ga ya Abida tashigo ba, Amina na ganinta ta kyabe baki a hankali Tace"Ga uwar iyayi ta shigo..Uwar sa ido..! Ai bata gama mgana ba ta Rike kugunta Tana Fadin"Ji yaran nan..Uban me kuke yi..?kun wani zo kun zauna kun sakata gaba sai kace kuna jin abunda take cewa..? Hanne ce tace"Mu fa ba Damunta muke yi ba..Muna Hirarmu ne muna kallonta..! Abida ta saki Tsaki kafin tace"To ku tashi ku fita ku barta ta Sake..Kauyawa kawai..! Dole suka tashi Amina ta Zumbura baki tana kunkuni fadi take"Mu ba kauyawa bane..Kema ai ita kika zo kallon..! Tana ganinta sanda take mganganun Yasa tace"Ke Amina da wa kike..? Amina tace"Ni nayi mgana ne..? Hanne don Allah me nace..? Tafada tana gwalo idonta dukkansu suka Hada baki wajen Fadin"Bafa tace komai ba ya Abida..! Kwafa tayi kafin tatasasu suka bar Dakin ita kuma Sarood sai kallonsu take tana Mirmishi.. Koda suka fito falo ba su Sakina sun koma Shashen Anty Amarya Amina tayi Tsalle ta Dire kan kujera ya Aisha Dake gefe ta kalleta da Sauri tace"yi hakuri ya Aisha..! Tana kunshe bakinta ganin yadda take Hararanta Fitowar Hajiya yasa Amina ta Mike Zaune tana Fadin"Hajiya ina yini..! Hajiya tace"Mamah..yaushe kika zo..? Amina tace"Ban dade da zuwa ba..!. Hajiya tace"naga zuwan Hamida tun dazu nace kina ina tace kina gida..Sanda su yaya suka zo ma na Tambayeki..! Amina kanta na kasa tace"Gani nazo Hajiya Lokacin kina Daki ne..! Hajiya tace"Barka da zuwa Mamah..! Kafin ta juya tana Kallon Abida Lokaci Daya tana Fadin"Sakina ta koma wajen Amarya ne..? Ta daga mata kai tana fadin"Sun tafi tace wai in kin fito ace ta wuce kanta ke ciwo zataje ta kwanta..! Hajiya bata Damu ba ta juya tana Fadi "Hanne ku zo ku karbi Sako ku kaima su Hajiya uwa..! Daga haka ta shige Ciki Hanne Tajeta karbo Sakon Turaran wutan Har ta juya ta Dawo tana Fadin"Hajiya ina nasu mamanmu..? Hajiya tace"Yanzu na basu da suka shigo yi ma D'anmallam barka da zuwa. ! Jin haka yasa ta fita zuwa falon tace ma su Amina su taso suje Amina Kirkiri tace ba inda zataje Dole Hanne da Hamida suka fita Shashen Hajiya uwa suka fara zuwa suka kaimata Tana ta godiya sai wajen Haj.Nasara itama tana godiya tana cewa ace ma Hajiya sai ta shigo Shashen Anty Amarya kuwa tana ciki ita da Sakina Ya Sadiya suka bama Sakon sukayi Fitowarsu suka koma Shashen Hajiya suna Hiransu Abida ta shiga Kitchen tana soya kaza Ya Aisha kuma ta koma Dakin Hajiya tana gyara mata sai su kadai afalon suna ta Hayaniya. Amina ce ta kalli Hanne kafin tace"Wai ni banga ya D'anmalam din ba..?ko yana gidansa ne chan kofar arewa..? Hanne tace"A"a yana nan gidan..Tun Safe Dakin su ya Nazem aka gyaramai ya yi wanka ya huta..yanzu haka yana masallaci tare da mallam sai Dare zasu wuce gidansu in ji Hajiya..! Amina ta gyada kai kafin tace"Shi nazo gani gashi ban ganshi ba..! Hanne tace"Zai shigo ki tsaya don Allah..! Hamida tace"Nima ina so na gansa..Na dade ban gansa ba wlh Amina mu kara jira mu gani..! Amina batace komai ba sai chan ta rage murya tana Fadin"Ku jinin al"adarku sau nawa kuka gani..? Hanne ta kalli Hamida itama ta kalleta kafin tace"Ni tun na Farkon nan ban kara gani ba..! Hamida tace"Ni ya kara zuwar min Sau Daya wanchan watan..! Amina tayi tagumi tace"Hanne bamu da lafiya ne..?nima fa daga sau dayan nan fa ban kara gani ba..! Na tambayi mamanmu tace kada mu damu zai zo haka yake yi..! Hanne tace"Eh mana kin manta ya Sayyadi yayi mana a islamiya yace in yazo na farko kafin ya kara zuwa ana Daukan Lokaci..! Amina ta kalli Kirjin Hanne ta kalli nata ta kalli na Hamida kafin ta Bushe Da Dariya Hanne ta Daga mata Duka tana Fadin"Kefa baki jin mgana..! Amina na nuna kirjin Hamida tana Fadin"Hamida zan siya miki Breziya in muka gani a hanyar makaranta..! Tafada tana Dariya Hamida ta ji kunya ta juya Baya Saboda ita Nonuwanta sunfara girma har ana gani A hijabi Saboda yanayin Jikinta..sabanin Amina da kirgan Dangi makale a kirji har gwara Hanne ma sun Fara bayyana. Hanne tace"to ai sa"adatu ma tana Saka abunta..! Amina tace"ita wannan ai ko uwarta ta siya mata mara kunya ce..! Na taba gani a Littafin Haussa fa ance maza na son Nono shine in nayi sallah nake Rokon Allah ya bani kada yazo banidashi nayi aure mijina ya karomin Kishiya..! Gabadayansu baki suka rike suna kallonta kafin su fara kallon kofar Dakin Hajiya ganin ba kowa yasa suka Fixgeta sai Chan lungun Falon atare suka Hada baki wajen fadin"Amina daman baki daina karatun Littafan Hausanan ba ko..? In akaji labari fa..? Amina na Dariya tace"Dilla kun cika Tsoro..! Hanne tace"Na Dauka da ya Sayyadi ya kamaki a makaranta ya Dakeki kin daina..! Amina ta yi wata Dariya kafin tace"Aminene ikon Allah..Ni duka ai baya sani na fasa abunda nayi niyya..In ma zaku daina wannan Tsoron ku daina ku zo kuma ku fara Wlh Dadi kunga Love..?nace ni ko su ya Zulahait da zasu aure basa wannan Love din da mazajensu koda yake ko waya fa basu da ita ta ina zasu ma kirasu" ta karishe fada tana yar Dariya Hanne tace"Allah ya shiryeki Amina..' Tace Ameen Hamida kuma ta kasa mgana Domin ta gama Sarewa da Lamarin Amina girma kawai yake karawa. Suna nan har shidda na yammah Amina ta gaji ta mike tana cema Hamida"Kinga tafiyata in ke baki tashi ba..! Hamida ta mike tana Fadin"Mu bari bayan mangariba mu tafi kinga yanzu kila su ya jafar suna waje zai mana Fada..! Amina tace"Allah yasa yankamuzai yi ba Fada ba sai na tafi..! Hanne tasan bazata tsaya ba yasa taje ta Dauko hijabinta Dakin Hajiya suka je suka mata sallama tana bakin gadonta waya na Hannunta tace"Mamah ku bari Abida ta gama Pepe Chicken din nan mana ta Dibar muku..! Amina na jin haka tace"Hajiya ko Tafashasshe ne abamu hakanan..! Dariya suka mata Har da Hajiya kafin tace"Kuje Abida ta baku..! Amina tace"Ya Abida taf..Hajiya sai dai in kizo da kanki dama yar aljannah ce ya Aisha ..! Ya Aisha na Gaban wardrope din Hajiya tana gyara mata tana jinta batace komai ba Amina fa yanzu zata yabeka anjuma ta zageka tas. Hanne tace"Allah yasa ya Abida ta jiki..! Amina ta Zunguri kafadarta tana Fadin"Ke in ta ma taji fa..?sai nayi abunda na saba nace bada ita nake yi ba..! Hajiya na jinsu tayi Dariya Amina manya Kafin tace"Kuje dai ku ce mata ni nace..! Dole suka wuce Kitchen din suna Shiga tana ganinsu ta Fara masifa"me aka zo min Ehe..?ba kwa son aiki sai Ci ko..?ku fita ku bani waje bana son Iskanci..! Amina ta kalli Hanne itama ta kalleta Hararansu tayi kafin tace"Bana son munafunci lafiya..? Hanne tace"Hajiya ce tace ki bama su Amina nama wanda baki soya ba zasu tafi ne..! Abida tace"Bazan bayar ba..Kada Allah yasa su tsaya din..Ke Hamida ki bari na gama in Amina zata tafi ki barta tatafi din.. Sai na gama Duka sannan Wlh zan baku. ! Kyam suka tsaya suna kallonta ta juya baya ta cigaba da aikinta ganin sunki Tafiya yasa ta Juyo tana Fadin"Kuka tsayamin aka..?zaku wuce ko kuwa..? Amina ta fara juyawa Hanne zatayi mgana ta rike hannunta kofar Kichen din suka Labe Amina na fadin"Wlh sai na Sata tunda taki bani da lalama..! Basu ma yi mamaki ba Domin Amina bata Fadar abunda bazata iya shi ba. Hijabinta ta Tattare sai da ta bari hankalin ya Abida na wajen juya Naman dake cikin kasko ta fara Sanda ta shiga kitchen din sai ji tayi kawai an Dumbuzu Naman Daya Rage bata soya ba har Garin Sauri tana Zubar da wani a kasa Abida ta Juyo taga sanda Amina ta Ruga Su Hanne suka mara mata baya suna Dariya fitowa tayi da Gudu da Abun suya a hannunta yana Digan mai tana Fadin"Kai kai..Ni yaranan zaku raina ko..?wlh na kama yarinya sai na Lahira yafi ta jin Dadi barin ma Amina zaki gane dani kike..!.abun ya bata mata rai kamar ita yaran nan suka ma haka su ko juyowa ma basuyi ba Hanyar Fita Amina ta kama Tana Fadin"Ku ka tsaya wlh ta Sauke Haushina Akan ku..! Ta kawo bakin kofar kenan tana juya baya bata ma kallon gabanta Daidai Lokacin aka Bude kofar Shashen na Hajiya Lokaci Daya da shigowa Amina bata sani ba da karfinta ta juyo Hannunta Damke da naman data Diba sai Gaf taji tayi karo da Mutum ammh kamar Da Icce taci karo Saboda ko gizau na Tsayen bai yi ba sai ma itace ta koma da baya Kamar zata Kifa da Azama da wani Zafin Nama ya ciro Hannunsa guda Daya daga Cikin Aljihun bakin wandon Dake Jikinsa ya Rike hannunta Cikin Tsausatsayi wanda Naman ke Ciki gabadaya maikon da ruwan Tafashen ya gama Mamaye hannunsa.. Ammh duk da haka bai saketa ba sai da ya Dagota da hannu Dayan nan ta Tsaya da Kafafunta Idanuwanta na Runtse domin ta gama Sadakarwa ta Fadi Numfashi take saukewa shima da azama ya saki hannunta yana Bin Hannunsa da kallo ransa nan take ya baci kyamyami garesa Har tsikar Jikinsa na tashi. Cikin Tatattausan Muryansa ammah Cikin Fada yake fadin"Ke wata irin mara Hankali ce..?kina tafiya ba natsuwa kamar wata namiji..? Muryan daga sama ta jita sannan kafin ta gama Daidaita Natsuwarta ta Bude Dara daran idanuwanta Daga baya taji Hanne na Fadin"Sannu da zuwa Ya D'anmalam..! D'ANMALAM..! DAM gabanta ya fadi kenan da Ya D'anmallam ta ci karo bata sani ba.. Da sauri ta Bude idonta ta Sauke akansa alokacin bama ita yake kallo ba Hannunsa na Sama kamar wanda kashi ya taba yana kallon Hanne yace"Hannatu meke damun ku..?wani irin wasan banza ne wannan..? Yafada har Giransa na sama yana Hadewa waje Daya ya Abida Daga Kofar Kicthen ranta fes tasan sai ya D'anmallam ya chasa mata su sosai. Amina batasan ta saki baki tana kallonsa ba Domin kamar mayen karfe na janta haka taji ta kasa Daina kallonsa Duk da bai juyo ma gareta ba Kyau da zati kawai da wani Haiba take gani da Hange da kuma wani Dattako da wajen Baba Mallan kadai tasan dashi. Hamida jin Hanne tace ya D'anmallan yasa ta gaisheshi ya amsa bai Damu Daya kalleta ba Yasan dai Cikin yaran gidan ne saboda ai ba Duka suka taso agabansa ba. Hannunsa ya kallah kafin ya Yamutsa Fuska yace"Miye wanna..?wacece ta shafamin wannan kazantar a Hannuna..? Yafada yana kara kyamatar hannunsa nasa Amina Girman idonta ta Bude tana kara kallonsa Daga sama har ksa Yana Sanye da Jallabiya mai Ruwan Madara,Da bakin wando sai kansa Sanye da Hula irin ta yan Saudiya karama iyakarta rabin kan nasa Fuskarsa tayi wani Haske mai Annuri sosai da Zati Lokaci Daya. Abida na jin abunda yace ta kariso Tana Fadin"Ya D'anmallan gwara da Allah ya kawoka..Nama suka zo suka Satarmin Hajiya ta sakani suya..! Cikin mamaki yace"Nama..? Da sauri tace"Eh ga shugabarsu na..Amina wlh yaya har tana Zubarda Naman a kitchen bata da natsuwa kamar yadda ka Fada kazamar ce..! Tafada tana nuna Amina wacce ke Tsaye tana kallonsa ga Hannunta Dunkule da Naman data Sato din Shi ko da suka ci karo ya Rikota bai Tsayama kallonta ba Duk azatonsa Sa"adatu ne ko cikin yaran gidan sai yana kallonta yaci gabansa yayi wani Dif saboda yadda Fuskarta ta Tsaya aransa yana so ya Tuna mai irinta Saboda Tsabar kwarjinsa akaron Farko Amina taji ta kasa Jurre kallon Cikin Idanuwansa Sai da ta sadda kanta gabanta na Fadi haka kurum taji Wani tsaro karon Farko da kunyar da Amina bata taba jin irinta ba. Ganin yadda ya Dawo da kallonsa kan Abida ne Cikin Alamun Tambaya. "Amina...? Da sauri tace"Amina..Diyar Baba Sa"idu ne..Yar wajen yaya ce fa..! Ga Hamida ma itama duka na gidan Baba Sa"idu ne..! Sai alokacin ya kara kallonta yasan wannan Fuskar matar dayake ganin kimarta bayan Hajiya babba ne wato yaya. Shi bai ma san tana da Wata karamar yarinya ba ya Dauka Jawaad ne Autanta Saboda in yazo yana ganinsa Tare da Baba Sa"idu shi bayansu Jadwa sai su Jaleela yaran nan duk ba Saninsu yayi ba. Hayaniya ce bai so sannan hannunsa kyamkyami ya ishesa yasa yace"Nama kuke sata agidan Baba Mallan..? Yafada Cikin Sanyinsa a karon Farko Hamida da Hanne basu Dauki Jidalin Amina ba suka Hada baki Wajen fadin"Bamu bane..Wlh Amina ce ta Shiga ta Dauko..! Suka fada suna Nunata Amina taji kamar kasa ta Bude ta shige saboda kunya tana jin idanuwansa akanta Ga hannunta Dauke da Nama Ruwan maiko na Diga da Sauri ya kauda kai ya wuce da Hanzarinsa cikin Natsuwa "Ita mace da natsuwa aka santa..Hakane ke bambamta ta da Namiji..Sannan kazanta ko a addini bashi da kyau Hadisi ne guda Ko Sallah bata cika sai da Tsabta..! Bai ko kara kallonsu ba ya shiga Kitchen din ya tara hannunsa a sink ya wanke har da saka Omo yana jin karnin Naman a Hannunsa karamin Tsaki yaja kafin yace"Kazamar yarinya kawai..! Suna nan Tsaye kamar an Dasasu ya Fito Abida ssa Dariya take musu suna ganin ya fito Hanne taja hannu Hamida suka fice da Sauri ammh Amina ta kasa gaba ta kasa baya. Kunya da wani abu data kasa sanin Dalili taji wani abu sunan yau an kunyatata Duk da gaban Hanne da Hamida ne an kirata mai Satar nama kuma kazama kuma mara natsuwa har ana Dangantata da Namiji wadandan kalmomin sun taimaka wajen sata ta cigaba da Tsayuwa a wajen Saboda ji tayi kafafuwanta sun kasa Daukanta. Tana tsaye a wajen taji yana Tambayan Abida Hajiya tace tana ciki Tana kuma jin Sanda ya fara taku zuwa Dakin Hajiya yana Shigewa Abida ta saka Dariya tana Fadin"Bera mai satan Nama..!. Sai ga Idanuwam Amina sun ciko da kwallah suna Shirin zubowa. Su hamida sun fara gaba suna juyowa suka ga ba Amina Hanne tace"Amina bata taho ba..? Da sauri suka juya suka koma suna Shigowa falon daidai Yana fitowa Daga Dakin Hajiya shi da Aisha yana mata mgana ganin haka yasa suka kasa ma Amina mgana shi kan yama manta dasu sam Aisha Dakin da Sarood take ta shiga ba jimawa sai gata ta dawo tare da ita tana ganinsa ta Nufesa kamar zata Rumgumesa sai ya rike hannuwanta Hanne nata Zungurin Amina duk son gulmarta wannan karom bata Dago ba Domin har alokacin bata gama Dawowa daidai ba. Mgana suke da harshen Larabci Cikin kwarewar da in ba ka iya Sosai ba bazaka gane komai ba, ba Dadewa ya Dauko waya daga gaban Aljihun jallabiyansa ya bata Sannan ya Saki hannunta Tana Sakin mai kayattacen Mirmishi yana Shirin juyowa Hanne ta Fizgo hannun Amina suka jata suka fita da sauri har suna Bugo kofar Falon da sai ya da maida Hankalinsa wajen. Ganin bai ga kowa ba yasa ya barsa shima Ficewar yayi suna ganinsa labewa sukayi a wajen Bayan Shashen Hajiya,sai da ya wuce suka Fito Hanne ta kalli yadda Amina tayi zata Rantse da Allah bata taba ganinta Cikin wannan Halin ba Da Sauri tace"Amina lafiya..?ko wai Fadar sunanki da mukayi..? Da Sauri Hamida tace"Wlh shi ba irin ya jafar bane..Kinga idonsa kana mai karya sai ya ganeka..! Amina bata ma Tsaya bi ta kansu ba Naman Dake hannunta ta saki ya Zube a kasa,kawai ta kada kai ta wuce Suka Bita da kallon mamaki suna kwala mata Kira bata amasasu ba. Suka fita har suna Hadawa da gudu ganin ana ta Haraman Alwala Domin lokacin Sallah ya kusa. Amina bata tsaya musu ba Har suka iso gidan Ya Zeena na bakin Famfo tana wanki mamanmu na Shimfida Darduma kofar Dakinta Amina ta shigo ba sallama Ya Zeenatu ta dago tana Fadin"In kika gyara Halinki ai ke baki cika Amina ba..ki rika shigowa gida kamar Kafira..! Mara natsuwa kawai..! Amina ta jita ta kuma ji sanda Mamanmu kr fadin"Zeenatu bana son haka..?ban ce ki daina shiga Harkan Amina ba..,!? Ita dai sai da ta danganta da kan gadonta taci kukan data ke rikewa ya zo mata Kamar wacce aka Daketa ta Fara kuka tana jin Hanne da Hamida akanta suna tambayanta tayi kamar bata jisu ba. Kuma taji sanda ya Zulaiha ta shigo ita da ya Zeena ganin Amina na kuka yasa suka tambayesu sanin halinta ba kasafai take da Saurin kuka ba. Hamida ta fara maida yar da akayi tazo wajen bayanin abunda Danmalan yace Amina ta Dago afusace tana Fadin"Eh yace min Kazama mara natsuwa ko..?haka kika so kice munafuka..! Tafada tana Sakarmata Jajayen idanuwanta da sai da ya basu Tsoro. Sai a ka rasa mai mata mgana har ta Fice Fuu Daga Dakin Zeenatu ta kwashe Dadariya tana Fadin"Ba Duka ba Zagi ashe mgana na Ladabtar da Amina bansani ba..? Hamida dai da Hanne sun kasa mgana ajikinsu yayi sanyi. Yasa suka fita suka fara shirin yin alwala Jam'i suka bi Amina na Dakin Mamanmu ta Dunkule kan kujera ko Sallar batayi ba tana jinsu a Tsakar gida suna Fadin yau Yaya Danmalan ya bada Sallar Itama ai taji Sanyayyar Muryansa yana Karatu Karatun da Har ita tayi karya tace bai natsar da zuciyarta ba tana jin Yaya na Fadin"Allah Sarki mun yi kewar karatun D'anmallam..! Daman in yana nan shike bada Salla har ya koma..! Amina aranta tana ayyana yadda yau yaci Zarafinta sai taji gabadaya Duhu ya mamaye saninta dashi an sha ce mata mara natsuwa da kazanta ammh yau sai abunda ya Zafeta fiye da koyaushe. Tana jin sanda Hanne ta ke ma su Mamanmu sallama tatafi gida sai Alokacin Amina tatashi tayi sallar Tana Tura baki. Ganin yan jidalin na kusa yasa bama wanda ya sake bi ta kanta. Sai dai tun Safe Hanne ta Dawo Lokacin Amina ta dan Huce Tana zaune bisa gadonta ita da Hamida alokacin Ya Zulaihat bata Dakin ya Zeena na makaranta. Hanne tace"kunsan wani abu..? Hamida ce ta girgiza kai Amina kuwa Yamutsa Fuska tayi kawai duk da Hannen na kusa da ita ne. Hanne tace"Ashe balarabiyar nan mai kyau dinan da ya D'anmallan yazo da ita matarsa ce..!? Amina ta Zaro ido kafin ta mike tana Fadin"ki bari don Allah Hanne..? Hamida tace"Nima naji Mamanmu da yaya suna mgana da safe..Wai Aba ya Fada musu jiya da Daddare..! Hanne tace"Kwarai muma jiya Mallam ya taramu har da ita ya fada mana aka gabatar da ita acikin mu Ashe Diyar dai abokin Baba mallam ne na Madina ya aura ma Ya D'anmallan diyar tasa achan Madinan.! Amina tace"Ya su Sa"adatu sukayi..?Ina Anty Sakinar..! Hanne tace"Abun mamaki basu nuna komai ba Anty Amarya tafi kowa ma karban Abun tatashi ta Rumgume Anty Sarood din agaban kowa tana mata maraba..! Amina tace"Jar uba..Wlh na karya ne..Wannan matar din..? Hanne tace"Bakisan wani abu bama..Ta kwace ta Daga Shashenmu tace ma Hajiya ita ke Saukan Anty Sakina to yanzu bata Sauya ba ita zata Sauki Anty Sarood jiya ai shashenta ta kwana..Sai da Safen nan suka wuce gidansu kuma Anty Amaryan ta rakasu Mallan yace taje..! Amina sam Labarin bai kwanta mata Baki ta Tabe kafin tace"Uhmm! Daganan bata kara mgana ba aranta bata yarda don Allah tayi ba Matar da ko su Mamanmu suna Fadin Rashin Kirkinta sun ce ko Aba bata cika mgana Dashi ba tana jin Haushinsa Sabida Hajiya da Baba Malam. Tundaga Ranar Amina bata kara yarda ta koma gidansu Hanne ba Duk kuwa da Tasan ya Danmallan yana gidansa ammh ai kusan nan anguwan yake zama Saboda bada sallah haka kurum taji batason su kara Haduwa Ya riga ya gama da ita tunda ya ce mata kazama kuma mara natsuwa bawai ta tsaneshi bane sai dai Acikin Ranta bai burgeta ba,duk da baya Duka ammh kuma yana mganar da zai saka ka kwana kana kuka aran Amina tasa masu sanyin Halin nan ba masu Kirki bane to Danmalam yana Daga cikinsu. ****** Shiryen shiryen Biki ya cigaba da Gudana ta kowani bangare kamar yadda Al"adar gidan mallam take ana Saura kwana Goma sha Hudu Biki Aka je akayi jerin Dakunan Amarya Tunda kayan suna isowa kowacce inda zata Zauna aka Sauke nata,Ikram aka fara ma nata Jerin nan Kusa da gidan Sarki Inda Dan Sarki Mahaifin Sultan din ya gina mai wani Dankarern gida su Mamansu suke je jeren su da su Hajiya,Sai Ya Zulaihat da ita agarim jigawa aka mata nata jeren agidan mijin nata Daya gina duk da kano zasu koma da zama inda yake aiki itama su yaya suka je dasu Hajiya uwa. Sai Ya Sadiya itama Garin Dutse aka mata Jerin duk da itama bayan Bikin America zata bi mijin nata. Ya Aisha sune yan kaduna Anty Amarya ce kan gaba ita da Hajiya Nasara da Mamanmu suke je suka mata Jerenta suka Dawo.. Daganan shiri ya cigaba da kamkama ta kowani bangare.. Tun ana Saura Sati Daya Biki baki suka Fara zuwa goggo Husai ita da Jadwa suka ssauka Daga Jordan gidan Dan"uwanta ta sauka Baba Sa"idu. Asatin Shiri Daya akeyi na Walimar su ya Zulahait da za"a hada da Saukasu a Haraban makarantar Islamiyarmu za"ayi Taron,Gida ko"ina ya cika ba matsaka Tsinke duk da Baba Mallam baya son taro ammh ai bai isa ya Hana Dangi zuwa ba,Mutanen gusai ma sun iso,sannan ga su Ya Nazifa tazo jidda ma tazo ya Akila ma haka ya Fatima tazo gidan Baba Sa"idu ma ya cika su Jaleela yan lagos sun sauka jamila ce bata zo ba uwar mijinta ba Lafiya sai Jawahir itama ta iso. Ana jibi Daurin aure Hidaya matar ya Nazir ta iso Daga Lagos ashashen Hajiya uwa take Sauka Daman in tazo,Ya Nazir sai jibi zai iso tace. Amaran kuma Kaf dinsu suna Gidan su Ya Jafar chan Hajiya ta roki Baba Mallam ya bari suka tafi Danginta yan Maiduguru sun zo suna chan suna gyaran Amaran sannan Bakin bazanga ma mata sun zo mazan sai Ranar Daurin aure. Kowa yazo yaga Balarabiya sai yace Daga ina sai ace Amaryan D'anmallan ne Abunda ke bama kowa mamaki yadda Sakina tajata ajiki Ko'ina suna Tare kamar kawaye,Sarood bata da Zabin kanta sai abunda Sakina tace kamar itace jagoranta. Da su ake ta Hidima gidansu suke kwana ammh kullum suna nan anguwan Danmallam shi kanshi yayi mamakin yadda Sakima ta Saki Lokaci Daya sai da yafi kowa Murna da hakan ganin yadda ta karbi Sarod Hannu Bibbiyu Hajiya bata ce komai ba Domim ita a kan Hurumim D'anmallam Mallam yafi ta karfi ta wannan bangaran. Amina Bakinciki take in za"ayi taro Saboda yadda kowa ke mai dasu jakai yayi ta sakasu aiki. Kusan ita da Hamida da Hanne gidansu suke kwana Saboda su ya Zeenatu suma chan suka tare da Amaran yau aka kawo musu Sabbin kayansu da Hijabai Dukansu iri Daya na Amaran ne kadai ya bambamta sai na iyayensu mata. Yau kwata kwata basu zauna ba sai saasu aiki akeyi,aikin ma na Wahalan Cirema yara pampers ko Ronensu su kuma suna ta aikin yi Cake da Donut da meatpie,suna ta sakawa cikin Takeway wanda za"a raba gobe wajen Walima ga Drinks nan da Ruwa cikin Falon Aba na Hidima da Rabo banda wanda ke chan Gidan Baba Mallam rabawa akayi nan ana Snaks gidan Baba Mallan suna gyaran kayan Miya na abincin da zasu yi su ya Jaleela kuma ana fama da suyan kaji da Nama. Sakina dai bamai ganinta tana Shashen Anty Amarya ita da Sarood ko aiki batayi ba kuma wanda ya Damu duk da itama chan gidansu akwai Biki Tunda yayanta da suke Uba Daya Sadiyan zata aura. *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo (Besty) Alherin Allah ya kai miki har inda kike* _Ya Allah ina rokon ka da ka Saukar da Farinciki,salama da kwanciyar hankali Da Aminci, zaman lafiya Da kaunar juna,sadaukarwa da yarda da,kima da mutumtawa, martabawa agidan auranki *AISHA ALTO* (Sisina) Allah yasa,kin shiga a sa"a Allah yasa gidan zamanki ne na har Abadan Da"iman Ameen_ *🅿️11* Amina ta gaji da sakasu Reno ya"yan da ake yi ko kuma dawainiyar Cire pampers duk wanda Yarta ko D'anta yayi kuka su ake kwalama Kira su zo suyi Dawaniya Hamida da Hanne basu nuna gajiyawarsu ba sai Amina Domin ta tsani in ana sha"ani a Rika nuna su yara ne basu isa komai. Dalilin haka yasa taja su hanne suka koma Chan koridon gidan wajen Dakunan da su ya Jafar sukayi zama Tun suna matasa sai ya zamana nan Aba ke sauke yan"uwansa maza in sun zo Daga gusai ko wasu baki dai Dakunan duka akwai Cafet da katifu aciki Wannan karon ma nan yan gusai suka sauka matan mazan sai Ranar Daurin aure zasu taho. Cikin guda Daya su Amina ke kwana Tunda Dakinsu su ya Jaleela sun zo sun koresu chan gidan baba Mallam ma ko"ina ya cika Tunda kowani Shashe cike da yake da baki Daga Duka bangaran matan kowacce Danginta sunzo Shashen Hajiya ba matsaka Tsinke cike Taf da Danginta na Maiduguri. Nan Amina ta jasu suna Fira Yawancin Firan Labarin Littafan Hausa ne da Amina ta smu yar"uwan yi suna ta Hiran Zafira D'iya take wajen Aba tunda Babbar diyar goggonsa ce Sa"aninsu Amina ce koma nace kawarsu ce suna Dasawa da ita Saboda indai Mamata mamanta zata zo da ita take zuwa itama ta fara karance karancen Littafansa Hausa shine suka Hade da Amina suna ta Labarinsu Hanne da Hamida Tagumi kawai sukayi suna kallonsu suna mamakinsu. Amina ce ta kalli Zafira tana Fadin"Kin karanta garin kallon Ruwa...?Labarin Faruq da khaleesat..? Hannu Zafira ta bata suka Tafa Lokaci Daya tana Fadin"Kai kai..Na karanta wannan Littafin yayi Amina..Salon soyayyar Faruq dabam ce..! Tare suka saka Dariya Hamida ta tabe baki tana Fadin"Ke Zafira a ina kike samun Littafan nan kina karantawa..?ammh Mamata bata sani ba ko..? Zafira tace"Anty Aina take dasu..In ta ijiye sai na sata na karanta kuma ina aron wasu a makarantar mu..! Amina ce tace"Hamida munafuncinki ya baci..To bata Sani ba ko zaki je ki Fadamata ne..? Hamida tace"Ina Ruwana..?ammh aikwai ranar da Dubu zata cika..Nama fi Tsausayamiki yadda su ya Jafar zasu Bandashenki Domin sai kin Daku Abunda ko Lokacin su ya Jadwa basu yi wannan karance karancen ba Sai ke..! Amina ta daka wani Tsaki kafin ta Tabe baki tace"In sun kamani kada su bar ni da Rai kin ji Hamida..? Ni fa bana son munafunci malama in kina son Fada musu ai ba sai kin zo kina wani Yadamin mgana ba ke bazan Fasa Karatun ba yanzu na Fara in ma baki je kin Fada ba sunanki ba Hamida .! Tafada tana kumfar baki ganin Abun na neman zama fada Hamida na Fadin"Da ina son na Fada da Tuni an wuce wajen kema kin sani..! Kawai gaskiya nake Fada miki..! Amina tace"Munafunci ba..Kin Saba..Hamida ki kyeleni ko?ance ba"a son gaskiyan ko Dole ne..? Ni bana son sa"ido kowa yaji da kansa mana .! Hamida zatayi mgana Hanne ta Tareta da Fadin"Kyaleta Hamida..! Hamida itama ta fara harzuka cikin Daga Murya ta fara fadin"Saboda me .?Saboda ita tafi kowa sai ta rika yadda taga dama ana kyaleta..?ai ba wani abu nace ba Fadan taso kanta nayi mata ina amfanin karatun Littafan da takeyi..!alhalin bata maida hankali a duka karatunta da zai amfaneta watarana..Ammh da anyi mgana sai ace a kyaleta to bazan yi Shuru ba nima yau ina daidai da Jidalinta Wlh..! Ta karishe Fada tana Hararan Aminar Dake kallonta kamar taga Kashi. Kafin ta yi Dariyan gefen baki tace"ban fi kowa ba Hamida..Ammh ni Dake ba Daya bane .ke sunanki Hamida ni kuma Amina nake..Ance ba"ason gaskiyan ko ana Dole ne..?ke wai ina ma Ruwanki da Rayuwata ne. ? anki a Tsaya ayi karatun sai me..?har kina Fadin zaki iya da Jidalina na Rantse da Allah baki da wannan Juriyan da zaki iya dani in kuma zaki iya Bismillah..! Ta Fada Lokaci Daya tana Chakumo Wuyan Hijabin Hamida suka Mike Atare Hamida ta Zuciya zata rikota Hanne da Zafira suka Tareta suna Fadin"Amina saketa..! Amina na Hararanta tace"Ku gayamaya ta daina Shiga harkata..ana Dole ne nace ta kyaleni ko..? Hanne tace"taji..Saketa..dafa mutane acikin gida in akaji fa kina ta Daga Murya. Amina ta Saki Hamida tana Fadin"Aji mana..Sai mene..? Daga bayansu sukaji ance"Meza"aji din..? Gabadayansu suka juya suna kallon mai mgana Anty Shamsiya ce matar ya Jafar Tsaye daga Bakin koridon Daga alamu bayi zata shiga Domin ga Buta nan a Hannunta da Katon cikinta agaba tayi wata katuwa ba kyan gani. Amina Tayi kamar bata ganta ba ta Juyar Dakai Hanne ce tayi saurin cewa"Bafa komai Anty Shamsiya..! Tana kara nazarinsu tace"Fadan da kuka saba kuke yi ko..? Da sauri Zafira tace"Wlh ba Fada bane..! Kai Tsaye tace"To tunda ba Fada bane ku zo ga aiki..Daman tun dazu Jaleela ke nemanku zaku Daukar mata Walid ya hanata aiki Zahra ma sai Cigiyarki take ashe ku gaku anan wajen..! Amina Sai hararanta take ta kasan ido ita ko Fadi take"oya ku zo ku wuce..Zahra ai ga su Hannatun nan fa...?ana ta nemansu..! Ta juyatana fada daga Cikin Gida su Hamida sun tafi Amina na wajen taki Tafiya Shamsiya ta kalleta tana Fadin"Ke da kike Tsaye fa? Amina ta Tura baki cikin kunkuni tace"Kiji da kanki dai da wani katon bakin ki..! Tana kallonta yasa tace"Badai zagina kike yi ba ko Amina..? Da Sauri Amina tace"ni..?cewa fa nayi gani nan zuwa..! Kwafa tayi kafin ta juya tana Fadin"Kada ma kizo..Jaleela gafa Aminar nan taki zuwa kinsan ta batasan aiki..! Amina ta Mele baki tana Fadin"Ai ni ba Jaka bace..! Su hamida sun shiga cikin gida yasa ta bisu jin Ya Jaleela sai kwala mata kira take yi tana shiga taga an saka su Hanne Wanke wanke mai uban yawa Daga nan ta Tsaya afili ta Furta"Jaruba..Kamar wasu jakai..! Bata gama Rufe baki ba aka Rankwasheta asaman kanta Dafe kan tayi tana kallon Ya Jaleela Dake Tsaye kanta Da yaronta Walid a hannunta. Mika mata shi tayi tana Fadin"Ke da ba Jakar ba..Karbesa ki cire mai pampers ki wanke mai ina ga ya batashi ne kije Dakin mamanmu wajen kayana ki Bude karamin akwati zaki ga kaya da pampers ki Sakamai ki goyasa sai rigima yake min..! Amina bakinta kamar zai Fado Saboda Takaichi hakanan ta mika hannu ta karbesa yadda take yi ne yasa Jaleelan kallonta tana Fadin"Kada ki kadamin da yaro..Nasan Zafinsa ko bazaki yi bane..? Amina Dakyar tace"ni fa ban ce bazan yi ba..! Jaleela tace"Au naga kina neman min kuka ne..?daman baki iya komai ba Mamanmu ta gama bataki..! Ya Jawahir Dake kusa dasu tana Bare leda tace"Kamar kin sani Allah yasa ta iya ma saka pampers din..?Dama Hamida kika saka ko hannatu.Amina kiyuwarta da son jikinta bai barta ta iya komai ba..! Jaleela ta kara Dungurinta tana Fadin"Sai kazanta..da Rashin kunya zaki wuce kiyi abunda na sakaki ko sai na mareki..!? Acikin kunkuninta tace"Ni ba kazama bace.Haka kurum ko da haihuwa ni nayi ta wahala da yara..! Suna ganin tana mgana Jaleela tace"Me kike cewa ne..!? Wucewa tayi tana Fadin"Ni ban yi mgana ba..! Hanne da Hamida suna Duke suna Dariya kwafa tayi ta wuce wajen Bayin waje ta dukar da yaron da bai wuce shekara Daya da rabi ba ta Zare mai ido ganin zai fara kuka tace"Kai kama bakinka..bar ganin idon uwarka Wlh kana min kuka sai na Dirkeka..! Tafada tana Zaremai ido kamar yasani sai yayi Shuru kwafa tayi tana Fadin"Shegen yaro mai kama da Ubansa..! Tana Ciremai pampers din tana Ta Mai masifa ubansa ya sha Zagi harda uwar ma,Amina Fadi take""Kun iya haihuwa..ammh bakusan yadda zaku reni ya"yanku ba Amina ai ba Jaka bace..! Inda Allah ya taimaka Fitsari kadai yayi aciki a Bola ta watsashi Tana Fadin"Allah yaso ka..Da kayi kashi Wlh bazan wanke maka ba..Sai da na Sake nadeka dashi..! Ko Tsarki batamai ba Ta Daukeshi Fuu Sai Dakin mamanmu Dayake suna ta aiki ba wanda ya Lura da ita Tana shiga ta Dungurar dashi a kasan Cafet ba kowa afalon Yasa ta Zare mai ido tana Fadin"Kai zauna anan..In ka sake ka tashi sai nayi wuji wuji Dakai..! Gwanin Tsausayi haka ya koma ya Zauna yana so yayi kuka Lekowa tayi taga hankalin kowa baya kanta ta bar Walid chan ta sababo wajensu Hamida Daidai kunnenta tace"Ku taso mu gudu..! Hamida ta kalleta dasu Hanne da Sauri tace"Wannan uban wanke wanke yaushe zaku gama..?ai biki suka zo su yi aikinsu ne nidai kunga tafiyata in kuna son kuyi ta aiki ku zauna..! Tafada tana wucewa ba wanda ya Lura dasu domin yammah ta Farayi suna ta aikinsu. Zafira ce ta fara tashi tana Sake Hijabinta Data Daure Lokaci Daya tana Fadin"Amina jirani muje..! Daman ita ke wankewa Hanne da Hamida na Daurayewa ganin sun wuce yasa Hanne ta kalli Hamida tana Fadin'"Mu bisu Hamida in muka Tsaya Laifin duka zai shafemu..! Ba musu suka Tsame hannunsu Daman da Hijabansu ajikinsu,Su Amina sun riga sun fita daga Tsakar gidan su Hanne Jawahir ta Hanga da Sauri ta fara kiransu"Kai ina zaku kuma..?kun gama aikin ne..? Ai ina kafa mai naci ban baki ba su Amina Dake jiransu ganin suda gudu yasa suma suka Ruga Jaawahir ta saka Salati tana Fadin"Yaran nan basu da mutumci sunbar aikin sun gudu..! Zahra ce ta jita tace"Amina ce zata ce su gudu..ammh Hamida da Hanne basu da kiyuya.! Jawahir tace"Amina na Dakin Mamanmu tare da Walid..! Bata rufe baki ba Mamanmu ta Fito da Walid a hannunta tana Fadin"Jaleela garin yaya ki bar walid a daki shi kadai sai faman yanka ihu yake..? Zahra suka kalli juna da Jawahir kafin Tace"Daman na Fadamiki..! Jaleela nachan suna aiki Saka Abu a Takeaway aka mika mata Walid ta karba Tana Fadin"Sai naci uban Amina Wlh..! Zahra tace"Inda kika ganta ba..ai sai ma kin ganta sannan kici uban nata..! Gabadaya Dariya aka saka ana Fadin Halin Amina sai Allah ya Shirya. Su basu tsaya ba sai da suka fita Daga gidan sannan suka Tsaya suna Haki Hanne tace"Ya Jawahir ta kamamu tana ta kiranmu muka gudu..! Amina tayi Dariya tace"da kun tsaya..! Tafada daidai Lokacin da sukaji Hayaniya suna juyawa suka ga ashe Karatun Baba Mallan ne aka tashi Maza sun fara fitowa daga masallaci. Hamida ta zaro ido tana Fadin"Mu shige gidan Baba malman gasu ya Jafar nan sun fito masallaci kunsan in ya gammu a waje sai yayi mana mgana..! Amina tace"mu tafi gidan su ya jafar inda su ya zulaiha suke muga abunda suke achan..! Dukkamsu sukayi Shiru suna kallon Amina kafin tace"Dilla mu bi ta nan baya bamai ganinmu..!. Jin haka yasa suka yarda nan da nan suka Zagaya suka bi ta baya suka fara Tafiya akuyan Daure ta samu Sake sun san gidan Dayake ba wani Nisa Sosai a kasa sukaje sai gasu abakin get din gidan Amina ta fara buga get din gam gam..gam gam.kamar zata Fasa kofar Daga chan sukaji Muryan Abida tana Fadin"Waye haka..?ana zuwa kada ya balla get din..! Ido suka gwalo sun san Halinta kafin suyi mgana ta Bude get din Tana kallonsu tasha kunshi ja hannu da Kafa Hararansu ta farayi Daya bayan Daya kafin tace"Daman Araina sai da naji kune..To kuma uban me kuka zo yi..?ko nan da sa"anninku ne..? Amina tayi Saurin cewa"Mufa mun zo muga amare ne..! Abida ta ballaa mata Harara kafin tace"ku musu mene..?kaji min yara da iyayi to bAzaku shiga ba ku juya ku koma..nasan ba wanda yasan kun fito Daga gida..! Hanne tace"Muna ganinsu zamu tafi ko Amina..? Da Sauri Amina tace"Eh Wlh..muma kinga basai amana irin kunshinki ba..ko Hamida..! Gabadayan su suka amsa Domin su ba wanda yabi ta kansu ma mganar kunshi gwara Hanne da Hamida suna ma kansu Amina kuwa sai dai in Mamanmu ce ta kamata ta kunsa mata. Abida ta Daure Fuska Kafin tace"To wlh bazaki shiga ba irin lalle na ko..?ni sa"arku ce..?kuna yara da ku sai son shiga cikin manya dillah ku wuce ku bama mutane waje..! Amina ta tura baki kafin tace"To mu leka..!? Abida tace"To leka..!. Da Sauri Amina ta Zura kai ta wajen Hannun Abida Data Bake get din zata Leka taji ta Daketa abaya Dayasa ta Dawo da kanta da Sauri Abida tace"Matsa ku bani waje..Marasa kunya kawai ba sa"anku anan..! Tana gama Fadin haka ta fara kokarin maida get din Amina ta kalleta tana sosa inda ta Daketa da karfi tace"Dadin abun ai ke ba Amaryan bace Ehe..! Tana gama Fadin haka ta Zura da gudu su Hanne suka mara mata baya Abida ta saki baki tana kallonsu afili ta Furta"Yaran nan sun bala"in Raina ni..! Kan bala"i zamu hadu ne duk sai kun ci ubanku..! Tafada kafin ta maida get din ta Rufe suna Shashen ya jafar ne suna ta Hayaniya amaran Dayake Duka yan"uwan Hajiya daga Maiguduru ne sukayi musu Lalle da Kitso da kuma gyaran jiki nan suke kwana Anty Shamsiya yau chan gida zasu kwana ita da Fadila. Daganan da suka fito sai da suka kusa gida suka Daina gudu suka Duka suna Hutawa Amina ta Dago tana Haki tace"Ya Abidar nan muguwar yar bakin ciki ce..! Ta hanamu shiga mu gani ance ana ta mu su gyaran Amare..! Hanne tace"Eh su yakura ne fa suma tun ranar da sukazo hajiya ta turosu nan..! Amina tace"Ai dai zamu gansu gobe duk Tsiyanta nifa daman tunda naji muryanta nasan sai ta bamu mtsala..! Zafira tace"bata da kirki ne..? Amina ce"Ko kadan..Bata da mutumci ya Abida kina ganinta haka..! Gabadayansu dariya suka saka Amina ta Cigaba da Fadin"Ke kinga gidansu Hanne..?Kaf ba mai mutumci yasin..! Hamida tace"Kai Amina ga ya D'anmalam ai bai taba Dukanmu ba..! Amina tayi jim kafin tace"Shi kuma wannan dama dukan yake yi da Mganarsa..! Hanne da Hamida suka Kalli juna suna Danne Dariya Amina ta gansu ta Hararesu tana Fadin"Munafukai..! Zafira tace"Me ya faru ki bani labari..? Da Sauri Amina tace"Wlh kuka Fada mata sai nayi muku Rashin Mutumci..! Dariya suka kara saka mata ta kwalo musu ido Zafira na magiyan su Fada mata Amina ta Faki idonsu tace"Wayyo bayanku maciji..! Ai bata gama Rufe baki ba suka Zura aguje tabi bayansu tana Dariya. Allah ya taimakesu sanda suka Dawo an shiga Sallar mangariba sai suka Lallaba suka Shige gidan Baba Malam. Shashen Hajiya ba waje duk ya cika duk da wasu suna Kitchen din gidan suna ta soyan kaji su da su Baba Lami yan aikin gidan. Karsahenta dai Shashen Hajiya uwa suka Shige sukayi salla adakinta ita bata ma nan tana Shashen Hajiya taje suna mgana.. Sallar kadai sukayi suka Fito su leka chan su leka chan har shashen Anty Amarya sai da Amina tace suje saboda tana son ta kara ganin gulma Akwai suna shiga suka iske Sakina da Sarood zaune kugu Daya Jidda na Kan Cafet tana ta Hada Turaran wuta da Sabulun Salo cikin wasu kananun Robobi ita da wasu Daga cikin Dangin Anty Amarya..basu ga Sa"adatu ba bata nan tatafi kunshi an samu Sake. Hanne ne kadai da Hamida suka gaida su Sakina banda Amina Data yi keme keme Anty Amaryan bata Falon. Anty Sarood ta ganesu tana ta yi musu Mirmishi. Sakina taga Amina na wani kallonsu Daya Daya yasa tace"Ke..Baki da kunya ko..? Baki iya gaisuwa bane..? Amina ta yamutsa Fuska kafin tace"Na gaisheku..! Sakina tace"Karya kike..Hanne kadai da Hamida suka gaishemu da wannan yarinyar..! Ta fada tana nuna Zafira. Amina ta Tura baki batayi mgana ba Jidda ta dago tana kallonta Kafin tace"Wai Amina daman baki daina wannan Rashin ta idon ba ko..?ko ni ai baki gaisheni ba..? Amina ta yi wani jim kafin tace"Ina yininku..! Daga haka ta juya tana Jan hannun ZAafira Dake kusa da ita. Sakina ta rike baki kafin tace"'Yarinyar nan bata da kunya..! Amina na kunkuni tace"Eh din ai na gaisheki tunda kuma ba Duka miki zan yi ba..! Da karfi tayi suna ji ta fice Jidda ta girgiza kai tana Fadin"Kamar ba yar gidan Baba Sa"iduba kaf ya"yan gidanan ta fita zakka..Allah ya shirya..! Sakina batayi mgana ba baki kawai ta Tabe ta juya tana ma Sarood mgana Wacce ta maida hankalinta Sakina na jin Labaraci tun anan balle kuma Da suka koma chan Zama da Larabawan yasa yaran ya zauna mata sosai. Kitchen suka shiga suna neman abinci sun samu Jallop din shibkafa da aka Dafa da Rana. Amina idonta na kan manya manyan Baho cike da Naman kaza da Naman rago duk am soya Amina da nama Tuni Ranta ya biya. Akitchen din sukaci abinci suna cikin ci Amina tayi ma Hanne Rada"Yasin sai na saci naman chan..! Hanne tace"In aka kamamu fa..! Amina tace"Dillah bamai ganinmu..! Har suka gama cin abinci Amina na Tunanim mafita Su baba Lami na Kitchen da sauran mutane suna ta aiki kowa Hankalinsu baya kansu Anty Nasara ce ta shigo ta gansu yasa tace"Me kukeyi a kitchen..? Kuje waje mana ku sha iska..! Dole suka fice Hanne nama Amina Dariya ita kuma tayi Fuska Shashen Hajiya suka koma suka samu chan gefe suka zauna bama wanda ya Lura dasu Amina aranta tana Takaichun yadda in ana sha"ani bamai bi ta kansu aranta tace ai suma sun girma sun wuce yara yanzu. Suna nan har akayi sallar Isha"i suka tashi sukayi salla. Sai alokacim Hajiya ta gansu tace"kuna nan ashe..?na zata kuna gidan Sa"idu ne..! Hanne tace"Tun dazu muna nan..! Tana Sauri ne ana mata mgana yasa ta wucesu Amina tace"Kowa baya bi ta kanmu..! Hamida tace"Wlh fa kallemu kamar wasu almajirai..! Amina tayi dariya kafin tace"Almajiran ne mana duk inda mukaje ana koranmu..! Hanne ce ta ma Amina Rada a kunne tana Fadin"Kin fasa satan naman ne..? Amina tace"A"a Ku tashi muje..! Haka suka sake ficewa Kitchen din Amina ta leka taga ba kowa sai su Baba lami su kuma suna ta Hidiman yanka Albasa suna Hira Amina ta yafito hanne tana Fadin"Ku tafi daga chan..Ni zan shiga na Debo mana zan taho..! Hanne ta mika mata wata bakar Leda Data Dauko daga Dakin Hajiya tace"Zubo mana anan..! Zafira ce tazo zatayi mgana Amina ta mata alaman tayi shuru Hanne ta mata rada tana fadin"Ke nama Amina zata sato mana..! Zafira tace"Yauwa daman wlh tun dazu miyauna ya tsinke..! Amina ta Sadada ta shiga kitchen din ta Duka ta Bude ledan ne ta rika Zuba Nama Har sai da ta Kusa Cika Hanne da Zafira suna daga bakin kitchen din suka hango Anty Amarya zuwa da Sauri Hanne tace"Amina Ga Anty Amarya nan ki taso..! Jin haka yasa ta taso da gudu su kuma sun riga sun ruga har tana bangaje Anty Amarya,Da tayi baya tana Fadin"Ke ke..Waye anan..! Ina Amina bata tsaya ba sai Aharaban gidan inda su Hanne ke jiransu Anty Amarya bata ga Fuskar Amina ba. Ta shiga kitchen tana yi ma su Lami Fadan suna barin yara na Shigowa. Haraban gidan akwai haske tunda an kunna Gen yasa Amina ta jasu suka shige wani dan lungu Dake Wajen kofar Shiga Shashen mallan da dan Duhu kadan suka ZAuna Amina ta Fito da Naman Hamida ta zaro ido tace"Amina kin Debo da yawa in aka gane fa..? Amina ta tura wani nama bakinta Tunda naman sa ta Debo na kajin suna kusa da Baba lami yau gidan Gonar Baba malam yasha Diban kaji da Shanaye. Sai da ta cika bakinta sannan tace"Dillah kefa kin cika tsoro..Abu da yawa wazai gane..? Zafira ta mika hannu zata Diba Amina ta make hannunta tana Fadin"Kada ki samin hannu ko na Hanaki wlh..! Jin haka yasa ta Dakata Amina ta Dauki Tsoka Hudu hudu ta basu Ta bama Hanne Biyar ta Dauki Sauran tana Fadin"Mai sata ke da wannan..! Hamida tace"Kai Amina naki yafi yawa.. Amina ta balla mata Harara tana Fadin"To Sarkin korafi..Dayake ke kika je kika Debo naman..! To wannan ma in baki so bani kayana..! Tafada tana mika mata hannu Hanne tayi Saurin cewa"Hamida karbi abunki..Mun ji Amina tunda ke kika Debo Dauki wannan..!. Amina ta murguda baki kafin tace"ko baku yarda bama..In mutum yaji Haushi yaje ya Debo nasa. ! Hamida tasan da ita take yi ammh bata tankata ba suna cin namansu Zafira ke fadin"Wai shanaye nawa aka yanka da kaji..! Duk gidajen nan fa akwai Nama ko"ina ka shiga. !. Amina tace"Waya sani Zafira..?kila sun kai dubu kajin Shanayen kuma kila goma..! Tafada tana Tura naman bakinta Hamida tace"Haba inaga ma sun fi..Kinsan in ana Biki haka ake ta Yankosu ana shigowa dasu..! Zafira tace'Cab...ai gidan Gonar ta kare..! Amina tace"Ke..kina da Hankali kuwa..?Kinsan adadin Dabbobin Dake gidan gonar nan ta baba malam..? Ke babban waje ne fa na taba gani a Wayar Ya jafar da yazo yana nuna ma su Mamanmu na rantse da wanda Raina ke hannunsa gari guda ne..! Hanne ta karbe da cewa"To yaushe zamu je mu gani..?bamu taba zuwa ba..? Amina tace"Kuma fa hakane..?to ammh Aba chan yake zama fa..?ya zamu yi mu je chan Hadeja Road ne fa..? Hamida tace"Nidai ba ruwana..! Amina tace"Sai me..?ke dai kin cika Tsoro..Hanne bari nayi shawara na Rantse koda bala'i sai mun je mun gani ko da zamu dawo a yankamu ne..! Hanne tace"A"a fa ni wasa nakeyi..! Amina tace"Ke fa sai an je..Inaga ma gobe saboda bama wanda ya Damu damu..! Hanne zatayi mgana kenan sukaji mgana a kofar Falon Baba maallam gabadayansu suka Leka suna ganin Ya Uzairu ne ya fito Daga Falon mallam din Bayansa ya Shamsu ne sun saka Takalmansu sun nufi barayin da Dakumansu suke Amina ta juyo tana Fadin"Jaruba..Daman ya Uzairu ya Dawo ne..? Hanne tace"Eh mana tare suka zo da Ya Zulfa..! Amina tace"Harda Ya Nazem..? Wannan karon Hamida ce tace"A"a shi naji Ya Zahra na fadin sai gobe yace zai taho yana da Karatu gobe..! Amina tace"Mugayen gidan.com zasu Taru Lokaci Daya bala"i..! Hanne tana Danne Dariyanta take Fadin"Har na tuna ya Nazeem sanda ya miki Dukan Tsiya Lokacin muna aji hudu kin Tuna. ? Amina tace"Kan bala"i ina zan mata..Ranar ai mariya na Tsungula ya kamani Shine ya fitar dani gaban aji kusan awa daya nasha ya manta dani ne na Daga Murya nace Tattasan da ka shanya ya isa Bushewa sai kazo ka kwashe..! Gabadayansu suka saka Dariya Hamida tace"Kin ga kwashewa kuwa..Amina kin Daku fa hannu. Ya Nazeem..! Amina ta Ciji yatsa Kafin tace"Kuma Wlh har yanzu ban yafe ba Wuta bal bal har kabarinsa..! "kai su waye anan..? Mganarta ta Katse ne sanda aka Dallaresu da Filita Lokaci Daya da mgana suka Tsorata gabadayansu sukayi Tsumu Tsumi. Ya Uzairu ne zai fita shago ya Siyo katu yaji mgana daga bayan shine ya Haskasu da wayarsa. Karisawa yayi gabansu yana kallonsu Daya bayan Daya ya ganesu mamaki ya kamashi me suke anan..? Cikin Tsawa yace"Su waye anan..? Hanne ce baki na rawa tace"Mune ya Uzairu..! Amina kuma namanta take kullewa a leda yace"Ke miye wannan..? Daidai Lokacin da su ya jafar suka fito daga Falon Baba Malam daman tun Fitowarsu masallacin Sallar isha"i suka Dumgumo suka shigo. Bayansa Ya Nasir ne sai ya Da'nmalam Daya fito Daga karshe. Jin mganar ya uzairu yasa Ya jafar Daya sanya Takalminsa yake fadin"Kai Uzairu lafiya..?kai da su waye..? Juyowa yayi yana fadin"Wlh yaya zan wuce naje siyan kati naji mgana ta nan ina Haskawa naga yaranan bansan Uban da sukeyi anan lungun ba Cikin Duhu..! Dukkansu matsowa sukayi shi da Ya Nasir banda Ya Danmallan Dake gefe yana Danna Wayarsa. Gabadayansu suka Haskesu da Fitulan wayarsu Ya Nasir yace"Lalle nema yaranan to ku fito don kaniyanku..! Ba musu suka mike suka firfito Amina ce ta karshe tana Boye abunda ke hannunta ya Uzairu ya jawota yana Fadin"Bani abunda kike Boyewa..? Baki ta Tura kafin tace"Bafa kom..! Bata karisa ba ya make bakinta yana Fadin"Bani kafin nayi kasa kasa Dake mara kunya..! Hannunta Dafe da baki da mikamai ya karba Daidai sanda Ya Jafar ke fadin"Me kuke yi anan da Daddaran nan..? Gabadayansu sun kasa mgana Ya Nassir ya fara Duba bayansa yana Fadin"Inaga sai sun ji ajikinsu..Kai shamsu Dubamin Sanda don Allah..! Ya karishe Fada da karfin daya Janyo Hankalin D'anmallan kansu ya Zura wayarsa gaban Aljihun farin yadin dake jikinsa Riga da wando. Shamsu Daman tun farko ya fito jin haka yasa ya shiga Dakinsu ya Fito da wata Bulala mai kyau katuwa da ita ta duka yaran mutane A islamiya Ai Hanne da Hamida na ganin ya mikoma ya Nasir har ya Fara Nade Hannun riga suka Duka harda Zafira Data fara fadin"Wlh ba komai..! Sai kuka ya Uzairu ya Bude ledan sai ga Nama da Sauri yace"Ya jafar nama ne aledan nan..? Gabadayansu suka ce Nama..? Cikin mamaki Har da ya D'anmallan Daya kariso wajen basu sani ba. Da Sauri zafira tace"Eh nama ne..Dama Dama..Amina ce ta sato a Kitchen shime muka zo nan ta san mana muna ci ammh Wlh bamu yi komai ba..Amina ce ko Hamida..? Hamida da Hanne sun kasa mgana Amina na Tsaye ko gizau. Ya Jafar yace"ai ta saba indai Satan Nama ce..Amina ta saba..! Ya D'anmallan sai Lokacin ya Fahimci mganar ya kuma kare ma su Amina Dake wajen kallon idonsa ya Fada kanta yadda take wani Juya ido. Aransa yace"Again..?satan nama..? Meke damun yarinyar nan..? Ya Nasir ya kalli Amina yana Fadin"Anan gidan ne kike mana Satan nama..?kin ce abaki an hanaki ne..? Ya karishe fada cikin Tsawar dayasa Baba Mallam da Aba Dake cikin Falon zaune suna mgana sai da sukaji. Amina kuwa baki ta Murguda kafin tace"Ni ba barauniya bace..Ba sata nayi ba..! Ya Nasir yaga sanda ta mai haka yasa ya Daga Bulalar ya Shimfida mata yana Fadin"Karya zan miki..?kuma ni kike juyama baki zaki gane yarinya kwana Biyu jikinki na kaikayi..! Ya Jafar yace"Dake ta shegiya bakinta baya mutuwa..! Amina ko ko gizau ya kara Lafta mata wannan karan da karfi tace"Ai ba Sata nayi ba..ni ba barauniya bace..! Dukanta yake tana mgana su Hanne sun koma gefe har sun fara Hawaye.. Ya Danmallam mamakin Taurin ran yarinyar yake ganin da Har yanzu ko Dukawa batayi ba kuma bakinta bai Daina mgana ba Su ya shamsu na gefe suna Dariya. Ya Danmallam yaga dukan yayi yawa yasa yace"Kai Nazir bar dukanta hakanan mana..! Ya Jafar yace"Ka bari ya Daketa baka ga bata da kunya ba ai tare sukayi Laifin da yan"uwanta meya su ba"a Dake su ba..! Sai ya kasa mgana Idanuwanta yake kallo ko kwallah basu Tara ba kuma bata tare dukan ba,Idonta kyam ba ko alamin nadama ballatana ta bada Hakuri. Yana auna Shekarunta ne har ya isa ta Zama kangararriya irin haka..? Yana cikin wannan Tunanin yaji mganar Baba Malam a sama yana Fadin"Kai kai Nasiru..Kaga naka nan..?ka samu jaka ne dake dukanta kamar ka samu namiji Dan"uwanka..? Sai Lokacin suka Lura dasu shi da Aba suna Tsaye ran Malam ya baci da azama ya kariso wajen Har Alkyabban Dake jikinsa na neman Rinjayansa. Gaban Nasir ya tsaya ya Fizge Bulalar yana Fadin"Sau nawa zan gaya muku ba kyau Horo da duka..?Wlh banta Hora ku da duka ba sai Nasiha mai yasa kuma bazaku yi haka ba..? Ya nasir kansa na kasa yace"Baba ra..! Hannu ya Dagamai Lokaci daya yana Fadin"Bana son jin komai..Bana son Sarkaci kai Umar agabanka suka Tasa yarinya karama da duka baka Tsawatar musu ba..! Danmallam ma ya kasa mgana Dakyar yace"Kayi hakuri Baba..! Aba Dake gefe yace"Baba da barsu sun mata Hukunci Amina ce..Amina ai bata jin mganar kowa..! Aran Danmallam yace"Kenan ta gagara..! Baba Mallam ya Dagamai hannu yana Fadin"Kaima ka fita idona Sa"idu..! Jin haka yasa suka fara basa Hakuri ko kallonsu bai yi ba ya Juya ga Amina Data ga Baba mallan ta fashe da kuka Tana Fadin"Ce min fa yayi barauniya Baba..Ni kuma bana sata Daga na Diba naama shikenan..! Baba malam ya rikota yana Fadin"Bai kyauta ba..Mamata ai ba ta sata..Kuma naman da kika Diba ai na Gidanku ne ba wanda ya isa ya hanaki daina kuka Share hawayenki kinji..! Yana Fada yana goge mata Hawaye Ya Danmalam mamaki ya cikasa ya Tabbata ko cikin kannensa bai taba ganin Baba mallan yayi ma wata haka ba..Kenan ita wannan Dabam take.? Su ya jafar ko basu yi mamaki ba sunsaba ganin haka. Har su hannen haka ya taso su ya Damka musu Amina yana Fadin ku shiga Cikin gida..! Amina tace"Gidanmu muke kwana nan ya cika..! Baba mallam ya kalli su shamsu kafin yace"Ku rakasu sai kun tabbatar da sun shiga gida kana ku dawo..! Hakanan basu so ba suka tasa su Amina suka rakasu gida ya shamsu kam harda Tsaraban rankwashi. Baba malam bai Tsaya Sauraran ban Hakurin su ya jafar ba ya koma Falobsa Ransa bace. Aba ya Sauke Numfashi yana Fadin"Ku tafi gidajenku..Yau baba malam ransa ya baci..An taba Amina..! Ba wanda yayi musu suka juya wajen Motocinsu ya Danmallam dai na tsaye aransa yana ayyana wasu abubuwa kafin ya Tabe baki kawai. Don Allah mu ding yi ma junanmu Uzuri kusan hakan nan ba zan ki Typing ba sai da wani Dalili Biki naje bani agida sai jiya da yammah na Dawo bana cikin Natsuwar da zan iya Rubuta wani abu shiyasa aka samu Tsaiko..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️12* Lallabawa sukayi suka shige Dakin da suke kwana suna jin Hayaniyar su ya Jaleela a chan Tsakar gida,da kuma Hayaniyar Mutane,Har alokacin suna Tsakar gidan suna kamallah aikin su. Suna shiga Dakin Zafira ta yaye Hijabin Jikinta ta zauna Dabas kan Cafet din Dake Dakin ta Dago tana kallon Amina Dake Tsaye kyam takaicinta Daya yadda Ya Uzairu ya karbi Namanta bai bata ba Shi yafi kona mata zuciya ba Dukan Ya Nasir ba. Zafira tace"Amina ke kam baki jin Duka ne..? Amina ta wani kalleta a kaikace kafin tace"Me kika gani..? Zafira tace"Gani nayi kina Tsaye sai Dukanki ake yi ko kiyi Tunanin Guduwa ma ballatana ki bada Hakuri..! Hameda da gajiya yasa har ta kishingida tace"Tab Aminan ne zata bada Hakuri..!ai mutun Daya Amina na taba ganin ta bama Hakuri..! Hanne na gefen ta ta karbe da Fadim"Yaya..Yaya ce kadai Amina ke bama Hakuri bayan ita ko Aba Tsayen nan take mai .Zuciyarta kamar ta Kafuran Farko..! Zafira ta jinjina kai kafin tace"Tabdijam Haka kurum na zauna ayi ta Jifgana kamar wata Jaka..! Amina ta Daga idonta Sama kafin tace"Duka ai baya kisa..Daya na kisa da Tuni ba Sauran Amina Zafira..Sannan mganar na bada Hakuri ma bai taso ba..Me nayi..?Amina bata bada Hakuri matukar tasan ita keda gaskiya..! Zafira tace"Uhmm..Ko dai aljanu gareki. ?su suke saka ki wannan Taurin kan Amina..? Amina ta mata kallon Tara sau ra kwata kafin tace"Sai dai in naki ne suka Dawo kaina yanzu .! Da Sauri Zafira tace"Ni bani da Aljanu..! Amina ta tari numfashinta tana Fadin"Nima haka..! Daga haka ta samu chan Lungu Bayan ta Nanannde Hijabin jikinta tayi matashi Dakin ba Katifa Cafet ne kawai sai tarkacen kayansu da suka Kwaso zuwa nan baya ta juya musu aranta Allah ya isa kawai take antayama Ya Nasir da ya uzairu kafin ta Muskuta tana Fadin"Ai shima ba Zubar da naman zai yi ba ci zai yi..Wlh In na yafe Allah Tsinan..! Suna jinta ba wanda ya tanka mata suna Hiransu sama sama Tsakaninsu Amina ko kala bata kara cewa ba tun tana jinsu sama sama,Har sanda Hanne tace"Naga fa ga Ya D'anmalam Dazu da su ya Nasir suka Turkemu..! Hamida tace"Nima na gansa ammh bai yi mgana ba..! Hanne tace"Baida Hayaniya ne..duk acikin Yan gidanmu yafi burgeni..! Hamida tace"Gaskiya..! Amina na jinsu batace komai ba Domin kwarjinsa ma ya isa yasa kakasa mai gaddama Dole ace baida Hayanjiya. Har barci ya kwasheta ba ita ta farka ba sai da taji an Fara sallah Cikin Wata Zakin murya cikin Sanyi da Haiba Muryan Ya D'anmallam ne tunda ya Dawo Duka Khamsin Salawatun shi ke badawa ko da tatashi ta iske Hamida da Hanne na Sallah har da wasu ma yan gusai adakin suna Bin Jam'i. Tashi tayi ta fice Suka kusa cin karo da Zafira ta Dauro alwala Daga cikin Gida. Kallonta Amina tayi kafin tace"Meyasa baku tasheni ba..? Zafira tace"Hamida ta gaji da tadake kin ki tashi..! Wucewa tayi tana Fadin"Bansan munafunci barcin mutuwa nayi da har aka ta she ni naki tashi..!? Zafira dai bata tankata ba ta shige Dakin ta tada Sallar Amina Raka"a daya ta Samu Allah yasa ma a Rak"ar farko Suratul Muhammad ya karanta ita kanta yana karatun acikin Zuciyarta wani natsuwa take samu wanda ta rasa Dalili ammh aranta take fadin Muryansa nada Dadi in yana karatu. Suna Idar da Salla Mamanmu ta shigo Dakinsu suka Taru wajen gaisheta Hamida ta kallah tana Fadin"Hamida ku tsefe kanku na Roki Wasila zata yi muku Kitso da kunshi kafin Lokacin Walima..! Hannatu kema ki tsefe Tunda nasan kema baki Kitson ba..! Cikin Fara"a suka amsa mata Hanne ke fadin"Mamanmu irin kunshin Zafira za"amin..! Tafada tana nuna mata Kunshi naSalatif ne mai gidan siga Mamanmu tace"Ba matsala sai tayi miki..Jiya Da Daddare ya kamata ayi muku..Nayi ta Cigiyarku baku dawo ba kuna gidan Baba Mallam..! Amina taso na Tsefe miki kan na wanke da ke Wasila zata fara ta yar fa miki iri iri mai kyau..! Ba musu Amina ta Mike tana Sosa kanta kafin tace"Mamanmu da kin barni..Ban yi niyyar kitson nan ba .! Mamanmu tace"A"a Amina kan ya Dade ba..yafi wata biyu tun Wanda nayi miki din nan ne fa..?ki bari a Tsefe a sake wani..! Amina ta make kafada kafin tace"Ammh bazan yi Kunshi ba..Bana son zama Mamanmu..! Kallonta tayi ta Tube Dankwalin Dake kan Amina tana Fadin"Bakomai kiyi kitson kawai..! Mamata Mahaifiyar Zafira Dake Dakin Tace"Balaraba gaskiyan Ya Sa"idu ne dayace kike kara bata Amina..Ammh wannan Katuwar Budurwan da yau ko gobe Gidan miji ne kike lallabata Ta gyara kanta..?bayan ke zaki mata Tsifan ki kuma wanke mata..?Anya Balaraba..! Mamanmu tace"Amina fa yarinya ce..?nawa take..?in Lokacin ta fara gyara kanta yayi zata gyara Mamata..! Mamata ta tabe baki kafin tace"Ai shikenan..adai taimaka ayi kunshi ta Rufe wannan Farar kafar kamar ta kato..! Amina ta Tura baki hararan Mamata kawai take ta gefen ido Tana ganinta tace"Hararata kike ko..?na tashi na Gafjeki Wlh..,! Amina ta kauda kai tana kunkuni Mamanmu taja hannunta suka Fice tana fadin"Don Allah ku kyalemin Diyata hakanan kada kambun baka ya kamamin ita..! Da kallo suka bita har ta Fice Da Amina wacce ta Juyo tana musu gwalo.. Zafira tace"Wai Amina sai an mata Tsifa an wanke mata kai..? Hamida tace"Ko kayanta bata wankewa sai Uniform Duka mamanmu ke mata ko ta sakani..In ba ita ta mata tsifa ta mata Kitso ba sai Kanta ya shekara bata Damu ba..! Mamata tace"Kuma wamman ba so bane..Watarana ake ji ranar da zata gidan kanta sai ta gane bata da wayau..Irun su Amina kazaman mata za"ayi in an hadu da kishiya kuma ta ran mata ta zama Bora..! Hanne tayi dariya kafin tace"Waya ga Amina tayi aure..!ina so naga mijinta yadda zasu zauna ballatana Har da Kishiya..!tabdijam..! Hamida tace"Zasu ga Tijara ne da Jidali ganin idonsu..! Mamata tace"Ubanta zata ci..Daman na Fadama Ya Sa"idu ya mata aure. tsab zata Saitu don Ubanta ai chan ba Balarabar da zata kare mata..! Dariya suka saka Zafira na Fadin"Nima ina son ganin zaman auran Amina akwai Comdy..! Dariya suka kara sawa har da Tafawa chan ma Tsakar gidan haka mutanen Gusai suka taso ma Mamanmu ganin ta Tasa Amina tana Tsefe mata kai. Fadi suke"Balaraba kina sangarta Amina..?Tsifan ma sai anyi mata..? Ita dai Fadi take"Eh mana..Nawa Aminar take?Sai fa wannan shekaran ne zasu shiga Sha shidda ita da Hamida..? Yaya na jinsu ko tankasu batayi ba suna chan suna Hidiman yin waina da Za"a raba wajen Walima su ya Jawahir kuma suna Daki suna Tsara Memo da Turaran wutan tsinken da Zulaihat zata raba wajen Walima. Ya Jaleela dai sai ta fito tayi mgana bayan ta kalli kan Aminar tace"Amina wlh ba karamar kazama za"ayi ba Watarana..kanta har Tsagan kitso ya bace..?in taje gidan auran naga Uban da zai rika zama yana mata Tsifan..! Ya zulfa tace"Kila mijin zai rika zama yana Tsefe mata..! Wata daga cikin kannen Aba Daga Gusai Talatu tace"Sai dai taci Ubanta..aai nan ba gida bane..!na jaki zata ci barin ma mazan wannan zamanin..! Dariya suka saka Amina ta tura baki Tana Fadin"Kina jinsu ko mamanmu..? Wai har fata suke nayi aure mijina ya Dake ne..! Mamanmu tace"Kyalesu..Zulfa Jaleela zan saba muku..Ba ruwanku da Diyata..! Basu kara mgana ba ganin Mamanmu ta Hade rai ba wanda ya kara tankawa har ta gama mata Tsifan wajen taje kan Amina sai Wash Wash take Ya Jadwa ta fito Daga Daki tana kallonta kafin tace"Kai Amina kin ji Haushi Wlh..! Mamanmu tace"Jadwa..Zan saba miki Wlh..! Jadwa ta juya tana Fadin"Nayi shuru mamanmu..! Amina aranta fadi take"Bana ga jin haushi ba Ehe..! Dakyar ta bari aka gama Taje kan mamanmu ta Debo ruwan zafi ta fara wanke mata kan wajen Famfo Amina Har da Hawayenta Wai Zafi take ji mamanmu na Faman Lallashinta Su Jaleela na kallonsu Tsausayama Aminan sukeyi ko domin gaba Watarana ba Mamanmu a kusa da ita. Tana gama wanke mata yasha Iska ta Shafa mata mailn kitso ta kara Sharce mata taja hannunta suka koma Dakin da Wasila ke ma su Hamida kitson. Har ta kusa gama ma Hanne daman kanta a Tsefe yake Mamanmu ta kalli Wasila tana Fadin"Da kin gama ma Hanne ki fara ma Amina Wasila..! Wasila tace"Dole zan yi ma Amina kitsin nan..Kada ki kullaceni Balaraba..! Mamanmu ta fice tana Fadin"Tunda bata som kunshi a kyaleta..! To daman wacZai matsa mata Ana gamama Hanne aka fara ma Amina Wasila tace"Wani iri zan miki..! Amina tace"shiku..Guda goma..! Wasila tace"Daman bai wuce haka ba..In akayi miki mai yawa ina zaki iya Tsefesa bakar kazama..! Amina ta Juya idanuwanta kafin tace"Nifa ba kazama bace..! Wasila ta Dungure mata kai Tana Fadin"Rashin kunya Kadai kika iya ni gyara kafin na fasa yi miki kitson wlh..! Amina bata kara mgana ba tana kallon su Hamida na kuskus Amina ta Daga baki Tana Fadin"In aan ci namata Allah ya isa Wuta bal bal..! Suka kwashe mata Dariya Amina tayi kyafci Tana Fadin"Munafunci dai Dodo ne..! Suka kara saka mata Dariya Sai suka kara kunnata ta rika Hararansu Wasila ta gaji da motsinta tace"Zaki Taaya ko kuwa na saki kan naki ne na kama na Hamida..! Amina batace komai ba aranta Fadi take"Yadda kike baka a fuska har aranki ma haka mata sai Masifar Tsiya..! Dakyar aka samu aka gama ma Amina Kitso kafin Lokacin Zafira da Hanne sunyi wanka har zafira taje raka Hanne gida ta Dauko kaya Hamida aka Fara mawa itama ita kuma Amina taje tayi wanka duk wanda yayi mata mgana sai ta Turamai baki tana kunkuni ta Zagesa shiyasa ma su Ya Jaleela suka yi kamar basu ganta ba Mamanmu ce sai yaba Kitson take tana Faman fadin sai tayi ma Wasila kyauta. Amina koda ta fito wanka ta Iske Sabbin kaya Atamfa Hajiya Babba ta Dinka musu su uku ita da Hanne da Hamida da Dogayen Hijaban ankon Walima da su ya Zulaihat sukayi. Amina ta Daka tsalle Saboda Murna Tana Fadin"Jar uba..Yau din nan ba wanda zai fimu na Rantse..! Hanne tace"iri daya da nasu ya Abida Hajiya ta mana fa..? Amina ta sha Dariya kafin tace"Su ya Abida yau kuma za"a sa anko da yara..! Dariya suka dinga yi sai da suka jira an gama ma Hamida kitso kana suka karya da kunu da kosai da waina basu saka kayan ba Saboda su Hanne zasu yi kunshi Amina ta zauna ta jirasu aka Jera musu Salatif aka sanya musu Lalle Hamida tana ta lallaban Amina Tayi kunshi tace bazatayi ba da ta gaji ta Daga mata Murya tana Fadin"Don Allah ki kyaleni Hamida. haba kin cika kwazzaba..Nace miki bazan yi ba ko Dole ne..! Wasila tace"Ke so ake a Rufa miki asiri ki Rufe farar kafar nan taki kamar ta maza..! Amina ta Daga idonta sama Tana Fadin"Ni kafata bata maza bace..Kuma ai Farar kafar ta Allah ce ba wanda yace saka Lalle Dole ce..! Wasila tace"Duk wanda ya auri Amina ya auri kazanta da rashin kunya..! Amina tayi mata banza aranta tana Fadin"Tunda mijinki ya aureki nima zan auru..! Lokaci daya tana kallon Wasila tana yar Dariya Domin Wasila baka ce Dulum sannan ga muni ba Laifi Basu je ko"ina ba Saboda kunshin su Hamida sai Gabda La"asar suka Wanke kunshi suna ta Sauri Domin Tuni wajen Walima ya cika tun dazu su ya Abida suna chan suna ta Gyare gyare Tuni masu Kanofi sun isa da kujeru sun kafa komai mata ma sun Fara Tafiya da wasu kayan Rabo da kuma abinci. Domin karfe Shida na yammah Za"a tashi Daga Walimar,Lokacin da suke Shiryawa ne Anty Hidiya ta shigo gidam Cikin gayunta Sanye da Wata Farin Leshi ta Nannade Jikinta da Lifaya ta saka Takalmi mai Tsini Da ya"yanta Yunus da Zainab suna Kiranta Zeeta. Yaran basa jin Hausa sai Turanci Amina ta kyabe baki tace"munga Magofork karewar Turanci don Uban mutum..! Tazo gaida Yaya ne Amina na mamakin kaf ya"yan Baba Mallam sun fi Ji da yaya kan Mamanmu komai suka samu sai kin ji Yaya Amina abun na bata Haushi Afili ta kan ce"Ai Mamanmu tafi ma yaya som mutane..! Sun gama Shiryawa Cikin kayansu sun saka Hijabasu Takalman sallansu suka sanya,Duk yadda suka so su Zille Basu samu Dama ba sai da su Ya Jaleela suka tasa su suka Dora musu manyan Kololin waina almajirai kuma suka Dauki Buhunhunnan Take away sauran kayan kuma Ya Nazem da yazo dasu yayi ta Jigilan Daukansu zuwa Chan haraban makarantar Data Fara cika da Mutane kaf Daliban Isalamiya da Hadda Tare da malamai da kuma Duka bangarorin gidajen biyu sun Hallata. Su Jadwa suka je suka zo da Amare da Amotar ya Nazeem,sun sha Fararan Hijabai Har kasa da Abaya bakake kamar Larabawa Hatta Kafarsu bakin Takalmi ne sun sha kunshi ja da baki Suna kyalin gyaran yan Maiduguri. Daga chan gidan wajen Walima aka Zarto da su ko gida basu je ba. Kowani Daki sun yi nasu ankon Banda anare da Baba Mallan yayi musu komai iri Daya su Ya Abida da nasu ankon tare dasu Amina data gansu dashi baki ta rike tana Fadin"Hajiya bata kyautamin ba..Sai fa da nace kada tayi ma yaran nan irin namu..! Suna ta kunshe mata Dariya tana Hararansu. Hajiya uwa ma da Danginta irin nasu Amina sukayi da Fararan Hijabai sai Dakin Haj.Nasara ma ita da ya"yanta da Tawagarta sai Dakin Anty Amarya itama da nata ita da ya"yanta da Danginta Less sukayi Sa"adatu sai uban iyayi take Amina ta tabe baki tana Hura hanci da karfi tace"Ba"adai Fimu ba Ehe..! Sa"adatu tasan da ita take ta kalleta suka Harari juna kafin kowacce ta kauda kanta. Duka gidajen ba wanda bai zo ba sai wadanda aka bari su Zauna agida Dokar Baba Mallam ne har Hajiya Babba ya bada Izinin taje Wajen Walimar Ya Nazir ya kawo su Duka iyayen nasu Anty Hidaya kuma da su Anty Shamsiya Amotar ya Nasir suka Taho. Ya Jafar kuma ya Dauko su Mamanmu Sauran mutane kuma da kafa suka taho Tunda ba Nisa Anty Sakina da Anty Sarood kuma ya Uzairu Ya kawo su a Motar ya Danmalam,shi yana chan gida yana Hutawa baya son Hayaniya. Wajen ya cika da Mutane,Walimar ta mata ne za"ayi wa"azin aure bayan an bama Amare kyautuka,Suma din sai sunyi karatu. Shugaba ya fara Jawabi mallam Datti ya yi bayanin Yadda su ya Zulahait suka zama Zakwakurai a cikin makarantar ya fada cewa suna da Haddar Qur"ani da kuma Sauran Littafai a kansu makaranta suna alfahari dasu matuka. Daganan aka fara gayyatosu Daya bayan Daya suma karatu suna kuka ana Kabbara bayan nan aka basu Kyatttuka,kowacce adarasin data fi kwarewa ya Zulahat taci kyautan Iya Tajhud da kuma Muryan karatu sannan ta ci kyauta kan Haddace Buhari da Muslim. Su Ya Sadiya ma haka gabadaya gidanmu kowa mai kokari ne bamu da Malalaci ta bangaram karatu. Daganan sai aka fara Rabon Waina da su Donut abunda aka sanya a Takeway. Amina suna Daga chan baya ba wanda ya Nemesu su ya Abida ne da yan ajinsu ke ta raban har da su Mariya yan ajinsu Amina da Sa"adatu abun Rabon na abinci Gabadaya akayi ba bambamci Amina ta tabe baki Tana Fadin"Mu fa na lura a bikin nan kamar bamu da wani gata..Ji fa wai Rabon takeway din ma ba wanda ya Neme mu..! Hanne ma taji zafi tace"Uhm..Wai har da su Mariya..! Amina tace"ji sa"adatu dame tafimu..?Ai ba kowa bane yayi mana bakinciki sai ya Abida..! Yanzu bamu da bakin mgana in an koma Hadda kowa yaga yadda aka yarsar damu kamar wasu bare..! Zafira tace"Mu tashi muje muma ayi Damu mana..! Amina tace"Sai kin dawo ban tashi Wulakanta ba..! Wlh ya Abida sai ta tsinka ki a gaban Dubban Mutanen nan kawai mu Tsaya muga ikon Allah..! Suna nan zaune suna kallon kowa Amina ta karkata kunnen Hanne tana Fadin"kalli Yan"uwan Anty Amarya..Sun fi kowa zagewa. wai suma chan gidansu ba"ana Bikin ba..?sun wani zosun cikamana gida..! Hanne tace"Sai an sun tafi da Amarya zasu je chan suyi Bikin su..! Amina tace"Gulma dai..Gani suke sun fi kowa ji yadda Sa"adatu take..! Hanne tace"Kalli ma yadda take shigema Anty Sarood .Gabadaya sun kwaceta ni ko ganinta banayi..! Amina ta Kurama Inda Anty Sakina da Anty Sarood ido da ke zaune Dukkansu Cikin Shigar Jallabiya baka Sakina ta saka farin hijabi bai kai kasa ba ammh Sarood bata saka ba Bakin Gyalen Jallabiyan ta nada akanta baka ganin komai sai Walwalin Fararan Hakoranta. Sakina na mata mgana tana Dariya wasu Dangin Anty Amarya suna kusa dasu suna ta Hira kamar Sakina na Fassara mata abunda suke cewa ne.. Amina tace"Wlh ba don Allah suka jata ajiki ba..! Hanne tace"Baba Mallam nata yabon Anty Amarya da Sakina..! Amina ta tabe baki batace komai ba. Suna nan zaune ana Rabo yan ajin su ya Abida nata Fama da jama"a kada su mike su Yamutsa wajen. Mariya tazo gabansu da buhun Take away din tana Fadin"An baku..? Amina ta ballata mata Harara kafin tace"Mu bama yunwarsa mun cisa agida har mun gaji..Wannan sai ke in an gama Rabon har sata sai ayi aje gida aci a kora da ruwan lemo an Dade ba"a Hadu ba gida babu makota sai D'ai d'ai..! Mariya ta kallesu Tana mamaki Hamida tace"Bamu mariya ba"a bamu ba..! Tayi yar Dariya ta Dauko musu leda uku .mai Ruwa da lemo ta miko kenan Amina ta kabar dashi ya zube akasa Mariya ta Dago tana kallonta Lokaci Daya tana Fadin"Miye haka Amina..? Amina tace"Bansani ba..Mun ce bamu bukata ko..? Ke kuma Hamida wlh ki fita Daga idona..Kina sawa wadanda basu kai ba suna raina mu..! Mariya kwashe ki hada da wanda kika Sata..! Mariya ta Duka tana kwashewa Cikin yar Dariya tace"Ko ba ku yi haka ba..Kowa ai yasan ku ba wata Tsiya bace Haushi dai kukeji an bani Rabo ku ba"a Kiraku ba..! Amina ranta ya baci tana Kokarin mikewa Hanne ta rike ta tana Fadin"Kyaleta..ana jin kunyi fada kinsan ce za"a ce baki da gaskiya..! Amina ta koma ta zauna tana Fadin"Bari mu koma Hadda wlh sai na Watsa ma Mariya mari in ban Daki bakinta ba Ranar asabar Allah ya Tsinan..! Cikin su ba wanda ya kara mgana suna nan zaune ba wanda yabi ta kansu Zafira tace"Amina kin hanamu karba..gashi yana neman karewa bami samu ba..! Amina tayi shuru kafin tace"Ku tashi muje..Koda bala"i sai mun Diba..! Binta sukayi har zuwa aji Biyu inda aka Sauke duka kayan Rabon su ya Abida ne ke ciki suka Labe awaje suka Fito bata gansu ba suna ganin haka suka shiga ciki ya Umaima ce aciki sai wasu Daga cikin yan ajinsu sai ya Zeenatu suna mgana da wata. Umaima ce ta gansu batayi musu mgana ba tana zaune tana Duba Wani abu a Littafin Azkar din dake hannunta. Ganin haka yasa Amina ta kallesu a Hankali tace"Duka..D'auka..zura da gudu..! Sun san yaran yasa suka Bita tana Dukawa suma suka Duka suka Dumbuza Ledojon suka Zura aguje Sai alokacin su ya Zeenatu suka juyo suna kiransu Zeenatu ta rike baki tana Fadin"Ya Umaima su Amina ne ko..? Kai ta gyada batayi mgana bata son Hayaniya saboda ciwonta. Badiya yar ajinsu ya Abida tace"Aminar gidanku ko"ina sai ta nuna Hali..! Sai ga Abida ta shigo tana Fadin"in na rike su Amina sai nayi musu dukan Tsiya..! Ya Zeenatu tace"Ki hadasu da ya Nazeem ne yaci ubansu..! Kyafci tayi tana Fadin"Ku bar badawa hakanan..bari agama Walima sai mu fara Shirya na malaman mu ki hada musu da abun Rabon duka Zeenatu..! Suka amsa mata kafin ta fice Chan ta hango su Amina akarshe suma cin abunsu hankali kwance suna Dariya kai kawai ta girgiza domin tasan in tayi mgama zasu Raba Hali ne gaban Mutane. Mariya ce tazo gabansu tana Fadin"Kunci kun barsa ne naga har da Sata..?ana ci hannu baka Hannu kwarya..! Amina ta balla mata Harara tana Fadin"Mariya in baki bar nan ba na Rantse na mike bazaki ji da Dadi ba..! Mariya ta saka musi Dariya tana Fadin"Kudai ku ci kawai..! Harda gwalo Amina tace"in ban dagi bakin yarinyar chan ba ba sunana Amina ba..! Zafira na Tura Donut bakinta tace"Daga gani irin yan Shisshigin nan ne..! Amina tace"Kamar kin sani..Tusa kai ba kwarjini..kamar mayya..! Har Malaman da zatayi Wa"azin tazo suna chan baya suna Ciye ciye,Daya Daga Cikin matar wani abokin Baba Malam ne Sheik Ahmad Hadeja Ta iya Wa"azi sosai kawar Hajiya Babba ce ta na hallarta Dukkan wani Mahadara na mata sannan Har programme tana yi agidan Radio da Tv akan mata ta kuma yin Wa"azin aure irin wannan in gayyaceta Motace ta Lalace musu ahanya Anan garin Gumel din suke zaune. Nan ta fara Lacra kan hakkokim mata akan Mijinta kafin ta gangaro kam Hakokin miji kan matarsa sannan ta bada Shawarwari sosai da kuma Mgugunar karin Ni"ima bangaran isalama domin Taimakom mata Hamida ta taba Amina tana Fadin"Ku Tsaya ku Saurara Wlh mgangunta akwai amfani aciki..! Amina ta saki Tsaki kafin tace"Dilla mu kyalemu ta ina zai amfane mu..?ko kina cikin Amaran ne Hamida? Hamida tace"A"a abun ba bakar mgana..Ko don gaba nake nufi..! Zafira tace"Gaskiyan Hamida mu ma nan da Shekara Biyu muma amaran ne..! Amina ta saki Tsaki kafin tace"Sai ku jira Lokacin..Me kuke ci na baka na zuba..? Ba wanda ya tankata ita kanta Hanne ta maida Hankalinta kan malamar ganin haka yasa Amina ta maida Hanlinta itama Sai tabe baki take yi Domin ita bama wani fahimta take yi ba. Shida saura Mintuna aka gama Wa"azin bayan an gama su ya Abida suka fara rabon su Jakunkuna da Karamin Frame na Ayatul kursiyi da su ya Aisha zata raba Daga bangaransu. Sai ya Zeenatu da ita da kawayenta suna ta Rabonsu Turaran tsinke da Memo na ya Zulaihat su Sa"adatu kuma suna ta Rabon Turaran Wuta na Rushi,da su Sabulun Salo harda Fallen Atamfa,acikin Wata Katuwar Leda da mafitai na zamani. Bangaran Haj.Nasara ma su na ta Raba Kananun Kofuna da Kuma Mug na shan Tea abun sai wanda ya gani. Kowanne sai da su Amina suka Dauka ba"a sani ba Har da su Sa"adatu Amina tace"Da kudin Baba Mallam akayi sai mun dauka..! Hamida na Dariya tace"Amina kina da Karfin Hali..! Amina ta balla mata Harara,sukayi Dariya kafin ma atashi suka Gudu gida Saboda kada asasu wani aiki kamar kuwa sun sani ana ta Cigiyansu su taimaka a kimtsa wajen aka nemesu aka rasa sai su Ya Abida suka Bige da aiki chan aka barsu a makaranta bayan sun gama Sallaman malamansu maza Hajiya kuma ta Sallami Malama Hafsah da tazo tayi Wa"azin mata. Duk a kasa suka koma gida su Ya Nazeem suna masallaci wajen Karatun Baba Malam. Sai Bayan mangariba su ya Abida suka Dawo amaran kaf suna Shashen Hajiya Babba nan Zasu kwana Har sai gobe bayan Daurin auran za"a kai kowacce shashen Mahaifiyarta na karshe,Shine Falon Baba Mallam inda shi da Aba da kuma su ya Danmalam manya inda za'ayi musu Nasiha Tare da mazajen nasu sannan kowacce a Damkata Hannun mijinta. Su Amina ko Abincin Dare basu ci ba suna ta cin kayan Fulawa Hamida tace"Kada ya danne mana zuciya mu kasa tashi..! Amina tace"Dillah zuwa gobe da Safe ya Sabbabe..! Sai da suka cinye kusan duka Sauran suka bama yara har suka koma suka kwanta suna Hira Daganan sai barci. ****** Anty Amarya na Falon Shashenta Cike da baki,Wayarta Dake hannunta ta Fara kuka tana Dubawa sai da gabanta ya Fadi agogon bangon Dake Dakinta ta Duba 12am na dare ta wuce Acikin Dakin akwai wadanda sukayi barci akwai wadanda basuyi ba. Sulalewa tayi ta nufi Bedroom dinta nan ma cike da Mutane Dayan Dakin ta Nufa taga Sakina na ciki ita Sarood sai kawai ta Juya ta Fice Daga Shashen Har wata yayar Anty Amarya tana Fadin"Marliya ina zaki da wannan Tsohon Daran. ?Sha biyu fa ta gota..! Ta fice tana Fadin"Yanzu zan dawo Ya Salamatu..! Kitchen dinsu tana jin hayaniya su Lami suna aikin Miya zasu soya da Daran nan na abinci gobe nan zasu kwana ganin haka yasa tayi kamar zata je shashen Baba Mallan sai ta Shige lungun Dake tsakanin Shashen nasa da Bangaran Dakunan mazan gidan. Jikinta na Rawa ta Daga kiran har ta katse sake kira akayi Cikin Makale murya tace"Miye haka DAYYABA..? Kinsan fa gidan cike yake da Mutane..! Shuru tayi na dan Lokaci da alamun Tana Sauraran mai mganar ne Daga Chan bangaran Kafin na ga ta saki wata Kayattaciyar Dariya kafin tace"Daman nace sai an gama wannan Hatsaniyar zan kiraki muyi mgana..Balarabiyar banza..?tasha gabana har ta sakani Fargaba..Tuni nayi mganinta Daman na Fadamiki bayan Sakina ba macen da zata Kafu a gidan Umar bayan ita. wannan Burina ne in ban samu mallaka Malam ba..Zan samu Damar mallakan abunda yake Takama Dashi Dagashi har Hajiya Babban atafin hannuna suke Dayyaba..! Shuru ya sake biyo baya kafin chan kuma ta kara Sakin Dariya tana Fadin"Kema saura kiris...Ki kara Hakuri kawai..SA"IDU ma matsalata ce Dayyaba..Shiyasa na Hada hannu Dake ni Burina bazai cika ba sai Sa"idu ya bar mallan..Kema naki Burin bazai cika ba MAtukar HADIZA na Numfashi acikin gidan Sa"idu zamu yi mgana..Hanya Dayace...Kawai da zai sa komai ya Dawo hannunmu. Zamu yi mgana in Hankula suka kwanta..! Kamar Motsi taji abayanta da Sauri ta katse wayar ta leka Shamsu ne ya Fito yayi alwala ya koma Dakinsu sai da ya Dade da shiga sannan ta fito inda Allah ya Taimaketa An kashe gen Duhu yayi sosai yasa ta Lallaba tana Waige waige ta shige shashenta Lokaci Daya tana Sauke Numfashi. Sako ta Turama Lambar data kirata. *Kada ki sake kirana..Sai ni na Kiraki da kaina..* *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* _Ina matukar godiya ga Tarin masoyan labarin Aminene ikon Allah..Nagode matuka Baiwar ba tawa bace ta Allah ce godiyar kuma zuwa garesa ne Allah ya bar zumunci nagode matuka da Alherinku gareni musamman Halima yusuf Besty Alherin Allah ya cigaba da Bibiyanki har gaban Abada_ *🅿️13* Karfe Daya da Rabi na Ranar jumma"a 1:30pm aka Daura auran su ya Zulaihat a babban masallacin Gidan Baba Mallam bayan an idar da Sallar jumma"a masallacin Daman Kaf anguwan da Zagayenta shine babban masallaci,Shiyasa bayan karattukan Addini da akeyi da kuma Duka Sallolin khamsin Salawatu ana Sallar Jumma"a acikinsa. Kamar yadda kowa ya sani ne al"adan gidan Baba Mallam Ranar jumma"a yake Daura auran ya"yansa To hakan ce ta kasance ayau din ma ana idar da Sallar jumma"a Daman kowa yasan da Daurin auran anguwan ta cika ta batse da manyan mutane kama Daga manya malamai Daliban Baba mallam,Angaye da duka Tawagan abokansu, abokansu ya Jafar da Sauran Mutanen anguwa da kuma Jama"a da basa Wuce sha"anin Babban malami irin Baba Mallam. Bayan an gama Daura auran Gabadaya Tawagan angayen da abokansu da su ya jafar da su ya Danmalam dashi da abokinsa kwara Daya Tal Daya gayatta wanda ko bai gayyaceshi ba zai zo tunda sun zama Daya tare sukayi makaranta Tundaga matakin primary anan Gumel kafin aiki ya maida mahaifinsa Dutse,suka koma chan cikin ikon Allah kuma sai suka Sake hadewa a Dutse a Wata Bording school ta maza Inda suka Dora matakin Secondary Dinsu. Aliyu Ahmad Gumel yanzu haka Lacture ne a School of Nursing Dutse acikin makarantar ma yake zaune da Matarsa mai suna Aliya da ya"yansu Hudu sai mahaifiyarsa dake tare da Iyalinsa mahaifinsa ya Dade da Rasuwa shine kadai amini kuma aboki ga D'anmalam wanda Tare ma suka zo da Iyalin nasa tana cikin gida wajensu Sakina,Kawaye ne ita da Sakina Tunda in dai suka zo garin suna zuwa Dutse wajensu sannan Aliyun yaje Madina shi da Aliya ashekarar da suka je Hajji sai suka Rankaya gabadaya suka isa makka suka Sauke Farali. Gabadayansu cikin gari suka tafi wani kayattacen Waje inda sukayi Reception wanda Danmallam ya Dauki nauyin komai ya hana su Hajiya yin wani abincin Daurin auran Mallam ne kadai da Aba basu awajen,Suna chan gida sallaman baki mutanen bazanga da kuma yan gusai da ana gama Daurin auran suka juya Ammh Tundaga kan su Zubairu har ma da Mutanen gari da abokan arzuka suna wajen Sun ci abinci sannan sai aka gaggaisa aka Dauki Hotuna Saboda Tarihi. Gabadaya Iyalan Baba Mallam Fararan Shadda suka Sanya Sai illah D'anmallam da ya Nazir ne suka saka Shadda mai Ruwan kasa Babban Riga da Hula Aikin hannu kuma iri Daya wannan aikin Baba Sa"idu ne shi ya Dimka musu su Hudu Cikon su Baba Mallan ne wanda ya Dora Rawaninsa kan Hularsa mai sakar yan Maiduguri wato Zanna Bukar. Angwayen kuma kowani Tawaga da nasu irin Tsarin Shigar Cikin Burgewa basu wani Dauki Lokaci ba Misalin Biyu da Rabi na Rana Motocinsu suka Fara Dawowa Kofar gidan Baba Mallam,Saboda Daukan Amran kamar yadda ka"idan take mata na cikin gida Ana ta Haraman Hada abubuwan Daya Dace kada a manta da wani abun Amaren Shashen Hajiya Babba suka kwana kuma ba"a fito dasu ba sai da aka Daura aure dukkansu sun saka Shadda Fara mai aikin Gold sannan hijabinsu har kasa mai Ruwam Gold ne da Takalmansu,ayayinda su Hajiya kuma Shaddar su mai Ruwan kasa ce suma Dukkansu har da su Mamanmu Da yaya a ka"idan Biki su kayansu iri Dayane Baba Mallam ya hana Sauya kala sannan Tundaga kan su Amina har kan su Abida shaddarsu Kalan Sararin Samaniya ce Kuma Dinkin su Duka iri Dayane da kalan aikin zaren mai ruwan zuma suma Duka Hijabinsu mai ruwan zuma Tunda saka gyale sai da su gani wajen wasu Tundaga kan na gaba dasu har iyanzu ba wani wanda har ya gama zamansa yayi aure yasan yadda ake saka Mayafi wannan Tarbiyan Baba Mallam ce Hijabinki har kasa da Safa Nikab ne bai saka musu Dole ba wacce tayi Ra"ayi ta saka abunta Hatta masu auran suma sun yi shaddarsu sai dai kowacce kalan ta ta Dinka. Sai bayan an gama Daura auran Angwayen sun tafi cin abinci mallam da Aba sun gama sallaman baki wajen yadan Ragu da maza kana Hajiya Babba da Hajiya uwa suka taso Amaran zuwa gidan Baba Sa"idu domin suyi sallama kowace na Lullube Cikin Hijabi tana kuka yara irinsu Amina da basa jin mgana suna Bin bayansu rii,su ya Abida kuma suna Shashen Haj.Nasara nan suka Sauke kawayen Amaran in sun zo Duk su ba wani gayya suke yi ba yawanci Duk yan islamiyan su ne sai yan Hadda ko yan makarantar Bokonsu sai Daidai kowa ya sani su kansu sun isa gayya a sha"aninsu. Dakin Mamanmu aka fara kai su bata wani Tsaya ba suma Dayake gidan yana Cike ne,addu"a kadai ta yi musu da Nasihan Hakuri kafin tace a kai su Dakin Yaya. Hajiya Babba tace"zamu bar miki Zulaihat ku kebe a matsayinki na Uwa gareta..! Mamanmu Dariya tayi kafin tace"A"a Hajiya..Ni Uwar Amina ce inda yau auranta akeyi bama sai kin ce mu kebe ba..Ammh Ai Zulaihat Diyar yaya ce ku mika mata ita Dakinta ta kara mata Fada ita da Sauran yan"uwanta..! Ana ta Dariya Kowa wannan karamcin na Mamanmu yasa take da kima a idon kowa Musamman Mutanen Gusai Dangin Aba,ba musu aka Kwashesu sai Dakin Yaya tayi musu Nasiha matuka tare da Fatan Alheri Suna ta kuka banda Sadiya kanta dai na kasa. Amina da Hanne da Zafira da Hamida suna Dakin Domin duk inda aka saka Kafa nan suke saukewa sai ana Tafiya su rika jama su ya Aisha Hijabi suna leken Fuskarsu ba wanda ma yake Lura dasu. Zafira tayi ma Amina Rada tana Fadin"Wanchan fa naga bata kukan Rabuwa da gida ne..? Amina ta kalli Sadiya kafin tace"Diyar Anty Amarya ce..Yayar Sa"adatu..Ai bazatayi kuka ba yar na gada ce..! Zafira tace"Tab wai ina ma Sa"adatun ne yau duk ban ganta ba..? Amina tace"Tana Shashensu mana .Ki bari zamu ganta ai duka za"a kaisu..! Zafira tace"Yauwa sai na kara ganin Balarabiyar nan..! Amina tayi Dariya tana Fadin"Basabam ba..bakauyiya..! Ita dai Dariya tayi Hamida da Hanne suna gefe suna jin duk nasihan da ake mu su ya Zulaihat Banda Amina da Hankalinta ba bashi a wajen. Basu wani jima ba Saboda Baba Mallan yace karfe uku kowacce zata mika Gidan Mijinta Gabadaya Har dasu Mamanmu da Yaya da su ya Jalela da Mutanen gusai aka Dumguma gidan Baba Mallam Dakin Hajiya Nasara suka yada Amaran itama Amtsayinta na uwa zatayi musu Fada da Nasiha,alokacin ne ya Zulfa ta hango su Amina Cikin mamaki ta tabo Jawahir tana Fadin"Jawa kalli yaran nan..? Ta kallesu kafin tace"Baki gansu ba..?ai tun dazu suna kugu da manya ko su Abida basa wajen nan sai su nayi mgana Hajiya tace a rabu dasu..! Zulfa tace"Amina ta na wani juya ido..Kamar wata babba..! Jawahir tace"Ko an koresu sai Amina ta Rika Labe kamar baki santa ba..? Zulfa tace"Allah ya shirya..! Jawahir tace"Ameen. ! Su bama su san suna yi ba suna chan suna ta Gulmar wata Kanwar Haj.Nasara da take da kiba katuwa ce Amina na Danne Dariyanta kasa kasa tace"Chabdijam..Wayaga Him..Buhun Masara..! Tana kallonsu suna Dariya kasa kasa Sai ta kallesu sai su kauda kai ganin hakane yasa suka koma Daga kofar Shigowa suna Dariya nan ma basu Dade ba suka fita zuwa bangaran Anty Amarya,chan suka iske Danginta Na Duste har da yayin angon Sadiya wadanda zasu tafi da Amarya sun zo su Sakina an ci wani Leshi mai Tsada an kashe Dauri Sarood ma ta saka Leshi iri Daya dana Sakina mai Ruwan Maroon da Kwalliyar blue gabadaya Cikin Dakin nan sai da ta Haskawa kowa yadda tayi wani kyau kamar ka ijiyeta kayi ta kallonta Masha Allah. Zafira tace"Tsarki ya Tabbata ga Allah..Amina kinga kyau..! Amina tace"Gaskiya kayan sun mata kyau..Ji Anty Sakina da ta saka Wlh kamar akuya..! Tafada tana Dariya Hamida ta Zungureta tana Fadin"Kiyi a hankali Tana kallonmu kada ta gane..! Amina na Danne Dariyanta tace"Kalleta..Sai kiba take karawa ga Gajarta kamar akifeta da kwarya..! Hamida tace"Amina ki bari..ba kyau kushe Hallitar Allah fa..! Amina ta balla mata Harara Tana Fadin"Anki a barin kabarinki Daya Dani ne..?nifa Hamida kin isheni Wlh badama ayi abu sai ki ce Amina kamar Ni kadai ce uwar Laifi..! Hanne tace"Mu dai don Allah kada ku fara wannan Fadan..! Amina tace"Gayamata ta Daina ambaton sunana..In ba Haka ba taga Tijara ganin idonta Wlh..! Hamida ta tabe baki kafin tace"Daga Fadin gaskiya..? Kuma da kike mganar Tijara.?har akwai Sauran Tijaranki da ban gani bane Amina..! Amina ta Hura Hanci kafin tace"Tab..ai baki ga komai ba Hamida..! Hanne ta raba Fadan da Fadin"Ku ga Sa"adatu chan..! Jin haka suka koma inda ta Nuna musu Daga bakin Kitchen din Anty Amarya suna ta Fito da kwalaye suna Tarawa anan Tsakiyar Falon itama Less ne ajikinta,mai Ruwan kasa Iri Daya dana Jikin Sabeeha ta gansu yasa ta zo ta wuce ta gabansu Amina ta kalleta kamar taga kashi kafin ta Mele baki tace" Aikin mur in ji tusa..! Zafira tace"Ita bata saka irin kayan ku ba..! Hanne tace"Ko Anty Amarya ai bata saka irin nasu Hajiya ba..Itafa komai nata Dabam take yi ita da ya"yanta Baki ga yawancin Danginsu da less ba kila su nasu ankon kenan..! Zafira tace"Hala Baba Malam bazai yi Fada bane..? Hanne tace"Ina ma zai Lura yana Fama da Jama"a..Kuma kinsan Hajiya ba ruwamta da wannan..Daman Anty Amaryan ne akwai kai kara da ance kace..! Amina na jinsu kafin tace"Ko Uban me zasu saka Wlh basu fimu ba..! Hamida tace"Infa..Bama zasu Fimu ba Wlh..! Anty Amarya suke kallo da take ta Dafa Duka kawunan Amaran tana ta musu Nasiha da saka albarka. Basu jima ba suka fito bayan sun bar Sadiya anan Shashen itama Ikram shashen Haj.Nasara aka maidata Su ya Abida basa nan wai sun tafi gidan ya Jafar Ya Uzairu ya tuka su zasu Dauko wasu kayan Amaran Dake chan gidan Ya Aisha da ya Zulaihat Shashen Hajiya Babba aka maidasu,Sannan Hajiya ta fice zuwa Babban Store din gidan Inda su ya jafar da ya Nasir ke jiranta aka Bude aka Fara Fito da Buhun hunan Shinkafa taci da na Tuwo sai garan kayan abinci bangaran su Taliya da Sauransu sai manyan Bombi na su kayan fulawa da Akayi ma kowaccensu. Harda da manshanu sai da aka saka ma kowacce Dukkansu garansu kowacce abu Biyu ne wani uku,Harda da su kuka Kubewa yaji,Fulawa da Sauransu kayan Kamshi Hajiya Babba ta saka su Baba Lami sun Dakasu kowacce an Dibar mata har da kayan Miya Tattasai Bushashe Tumatiri na angwangwani aka Siyan musu. Sun Raba kayan gida Hudu kowacce aka kwashe mata Daya su ya Shamsu ke Fita dasu suna Lodawa a Motocin angwayen. Hajiya Babba ta koma Shashenta ta Fito da wasu kayan Kitchen da zannuwan gado masu kyau na Saudiya,guda Biyu Daya na Aisha Daya na Zulaihat kayan Kitchen dim Biyu aka Raba duk da an siya musu wasu wannan karin ne saboda kayan aiki basa kadan,Bangaran Anty Amarya ma suna ta fito da kwalaye ita harda Nakiya suka kara ma Sadiya sai bangaran Haj.Nasara itama Danginta suna ta fitowa da wasu kayan Sai ga su ya Abida daman Tururuka suka Dauko na Ruwa da na Turaran Daki,Na Aisha da Zulaihat ne ta riga ta bama nasu sadiya ta bama iyayensu mata. Kowacce Angwayen sun zo da Danginsu guda Biyu da zasu tafi da Amarya Ya Aisha Mata uku suka zo Daga barayin mijinta Daga kaduna ya Zulaihat kuma mace Daya,Sai ya Sadiya ita gasunan da yawa tunda Abun gidane Ya ikram kuma algaita Tuni ya Cika kunnin Mutane Tawagayan ya"yan Sarki manyan uku suka zo tafiya da ita. Anriga an gama Loda Duka kayan Daga bangaran Duka Motocin guda Daya,Daya Kaduna Daya Jigawa Daya Dutse Daya kuma nan Gumel Cikin gida ma duk an gama Shiryawa Ya Rage saura Falon Malam Dashi da Aba sai Sauran manya yayyi irin su ya Danmallam da su ya Jafar Daga Falon Baba Mallam shi zai fito da kansa ya Mika kowacce Motar da zata sadata da gidan Mijinta bayan ya mata Fatan Alheri. Su Amina sun kasa sun Tsare a Kofar Shashen Anty Amarya suna Hiransu Sama sama,Jidda ce ta fito ta gansu Cikin mamaki tace"Ku kuma lafiyanku kuke tsaye anan..? Hanne ce tace"Bakomai muna son ganim Tafiyar Amare ne..! Jidda Tayi Dariya kafin tace"Ai Daga kan su Abida sai ku Duka Mallam ya Hadeku mu aurar daku rana Daya..Wannan fa ban gane ta ba..? Ta fada tana nuna Zafira Wannan karon Hamida ce tace"Daga Gusai take Diyar kanwar Aba ce..! Jidda tace"Goggo Husai..? Hamida tace"A"a Mamata..! Jidda ta gyada kai kafin tace"Allah Sarki naji ma ance goggon na kwance Zazzabi ya Rufeta ko..! Hamida tace"Eh Tun jiya da yammah Shiyasa ma baki ganta tare da su Yaya ba..! Jidda tace"Allah ya sauwake in an wuce da Amaran zan shiga na gaisheta..! Daga haka ta koma ciki,Hanne ta Tabo Amina tana Fadin"Baki ce komai ba..! Amina tace"Yan mganar basa kusa..ai duk cikin ya"yan Anty Amarya ina girmama ya Jidda ba ruwanta..Mara kirkin sai Sa"adatu itama ya Sadiya ba baya ba akwai gulma..! Dariya suka saka Zafira tace"Wai ni ban gane wacece matar Ya Danmallam din ba..! Hanne tace"Anty Sakina..?gatanan mai Less iri Daya dana Anty Sarood..Gajera..! Zafira tace"Naga wata Doguwa Fara kusa da ita..! Hanne tace"Ba ita ba wannan Anty Aliya ce matar abokin Ya D'anmallan ne ya Aliyu..! Amina tace"Ke don Allah..?oh na tuna ko wanman abokin nasa mai zuwa gaida su Hajiya wani Dogo baki haka..! Hanne tace"Shifa matarsa ce Dazu suka zo da safe ai kinsa kawar Anty Sakinan ne. ! Amina tace"Ke kam matar abokai..! Dole su zama kawaye kuma Halinsu yazo Daya itama sai kiga tana maka kallon kashi kashi..! Hamida zatayi mgana kenan sai ga Kanwar Haj.Nasara ta fito mai kiban nan tana Tafe jikinta na rawa waya ce a kunnenta ta fito tana mgana sai Goran Ruwa Dake hannunta. Mai su Amina zasu ba Dariya ba gwara su Hamida suna Rufe bakinsu kada taji ammh Amina Da karfi take Hamida ta Daketa tana Fadin"Dillah Amina kiyi a hankali kada taji..! Amina na Dariya tace"Jar uba kalli Wuyanta..Timama kenan..?Wlh ko Buhun Dawa albarka Markadi..! Daidai sanda Matar ta Juyo tana kallonsu daman tun dazu da suka shigo taga suma mata Dariya yanzu ta fito tana waya tana jin Dariyansu. Tana juyowa suka shanye Dariyansu ta Harari Amina kafin tace"ke wa kike cema buhun dawa..? Amina ta zaro ido ta kasa mgana Tana Danne Dariyanta. Hamida tayi Saurin cewa"Ba Dake muke ba..! Da Sauri Amina tace"Ai buhun dawar ce.!naga kin ma fi buhun masara ..Dankari..! Matar ta Zaro ido kafin tace"Ni..? Amina na Dariya tace"Ku kalli Duwawunta asama Hanne..! Matar ta nufosu gadangadan tana Fadin"Kaga min yan iskan yara marasa Tarbiya..! Kafin kace me sun Zura a Sittin Amina ce kan gaba sai hanyar waje suka Nufa suna Dariya Ta riga ta saki jikinta Tana kuma Gudu tana waigen su Hanne Dake bayanta sai ji tayi Ta buge Mutum agabanta Da kuma karar Faduwar wani abu wanda ya bada Sauti Tus...chas..! Baya tayi da Sauri bayanta ya Bugu da Goshin Hanne Dake bayanta Sauran Kadan su Fadi Hamida ta Rikesu tana Fadin"Zaku fadi fa..! Sai alokacin Hamida ta ga wanda Amina taci karo dashi ta kuma Lura da yadda Haraban Gidan ya Cika da maza bayansu ya Jafar har da wasu bakin Fuska ma. Salati ta saka ranta Jikinta ba inda bai Rawa hanne kuwa datagama Fahimta baya ta koma tana Kifta ido kamar wacce tayi karya Amina kuwa Tsoro ne ya kamata sanda ta Dago ido ta ga Ya D'anmallan agabanta Fuskar nan tasa ba Annuri ko Kadan Cikin Shigarsa wacce ta kara Fitomai da kyansa da Zatinsa Lokaci Daya da kwarjinsa. Shikadai ne bata iya Hada ido dashi bazata iya jure kallonsa ba Tunda suka Hada ido taji gabadaya bakinta ya Mutu gabbanta sun saki ta yi Saurin Sadda kanta kasa tana Bin waayarsa Tadata watse akasa kenan lokacin data ci karo dashi Tayi sanadiyar Faduwar wayar. Kamar wacce aka kai kasa haka ta durkushe ta fara Tattara wayar tana Fadin"Bansani bane..Kayi hakuri..! Su Hanne suka saki baki suna kallonta Hankulan mutanen Dake wajen ya Dawo kansu har su ya Shamsu sun matso da ya Nazeem kallonta yake tana Tatarra wayar tayi Daidai yace"Amina ce ko..? Wlh Yaya kaci Ubanta yarinyar nan sam bata da Hankali..! Bata kara mgana ba sai da ta Tattaro wayar ta Mike bata yarda ta Kallesa ba ta mika mai wayar kanta na kasa. D'anmallam Cikin Takaici yake kallonta ya kasa karban Wayar wai meyasa yarinyar nan bata da natsuwa ne..?ji yadda ta kwaso gudu kamar wata ballagaza kamar wata Namiji..? Ganin yaki karba yasa Abokinsa Aliyu Dake Gefensa ya saka Hannu ya karbi Watsatsiyar Wayar yana Fadin"Ba kyau gudu acikin gida..! Yafada yana kallon Amina acikin Ransa yana Tunamin ko kanwar Danmallan ne to bai santa ba. Sai da yayi mgana ne Amina ta Dago suka Hada ido da Aliyu sai alokacin tasan ba Ya Da'nmallam ya karbi Wayar tasa ba. Gabadaya taji ta muzanta ne ganin da Maza awajen yasa ta Ja kafafunta zata wuce su hanne kuwa suna gefe sun Rakube kamar wasu marayu. Ba zato kawai taji wani Dogon Hannu mai Laushi ya Riko Duka Kafadunta da karfi ya Dawo da ita gabansa Cikin Mutuwar jiki ta Dago manyan Idanuwanta ta Sauke a nasa da suka Fara Sauya Launi saboda bacin rai. Ya Jafar suna chan nesa suna Hira da wasu abokansu su ya Nazeem ne ke kusa ya Nazir kuma yana chan gefe saman manyan Darduman da suka shimfida a Haraban gidan yana kallon meke Faruwa ammh bai maida Hankali ba Chart suke da Hidaya matarsa Tana Fadamai Hayaniya ya Isheta sai yake tambayanta tana ina..?tace tana Bedroom din Hajiya inda ta Sauka shi bai ma tsaya lura da abunda ke Faruwa ba. Kamar mayen karfe haka suka Tsaya suna kallon Juna shi yana mata kallon Haushi da Takaichi ne ita kuma ta kasa Sauke idanuwanta ji take kowani gabobinta suna yin Sanyi kamar yana Hukuntasu duk Rashin kunyarta yau sai da aka ga Tsoro a cikin Idonta Lokaci Daya kuma Jikinta ya fara rawa. Ya Shamsu ne ke fadin"Yaya ka bari ni na Chasa su basu jin mgana Daman Abida ta kawo min karan su jiya Wajen Walima suna ta Satan Takeway kamar baza"a abasu ba kuma Shugabar su Amina ce gatanan batajin mgana ta Raina kowa..! Awannan karon a Saman Labbansa ya Furta"Sata again..? Meke damun yarinyar nan ne..?tana so ta zama Wata gangarriya..! Sai alokacin ta iya Sadda kanta tana jin kamar kafafunta bazasu iya Daukanta ba. Cikin Muryansa mai Sanyi Da Zaki yace'"Meyasa kowani abu sai ace ke..?kece Satan nama..?abinci..?rashin kunya Kazanta sannan Main din shine Rashin Natsuwa..?ke kadai ce agidan..? Ina ce su Hannatu age Mate dinki ne..? Why..? Ya fada yana Jijjiga Kafadanta kafin ya Saketa da karfi yana Fadin"Abunda ke Raba Mace da Namiji shine Natsuwa da kamewa..Duk macen da bata da Natsuwa sannan kazama ce ita..Sunanta ba Mace. sunanta ballagaza..! Yafada yana jin Bacin Ransa na Sauka da Hannu ya nuna su Hanne yana Fadin"Daga ina kuke..?ina zaku cikin maza awaje..? Hanne kamar tayi kuka tace"Ba..ba ko"ina..! Hannu ya daga ya nuna su dashi yana Fadin"Duk yaran Dake cikin gidan nan ko yara kanana iyayensu basu bar su sun zo suna guje guje ba sai ku..?Ku yara ne..?wato duk iskancin ku da ake Fada akanku gaskiya ne ko..? Hanne ta kwaso Rantsuwa tana Fadib"Wlh Yaya..! Shutt up..! Ya katseta da Karfi Cikin Bacin rai yace"In kun raina su Jafar ni sai na Ladabbar daku kafin na koma ku bar ganin bana Duka inna na Fara Dukan yarinya sai na Fasa mata jiki..Comom Ku wuce ko ku koma cikin gida Wlh ko da Wasa na ga Fuskar Daya Daga Cikin ku bama awaje ba anan Haraban sai na Karya mata kafa Daya..! Ku wuce ku bama Mutane Waje..Wawayai kawai kun girma bakusan kun girma ba..! Ai kafin ya Rufe baki su Hanne sun juya Sumai sumai sun wuce Amina ce kanta na kassa da idon kowa ke kanta ta kasa gaba ballatana baya Sau Biyu kenan ya Taba Tozartata na Farko Ba Mutane ya Abida ce kadai sai su Hanne yau kuma bayan su Ya Nazeem har da Bakib ido.. ya sake kiranta Barauniya,Sannan yasake ce mata kazama kuma yau harda ballagaza Gabadaya sai taji Ruwan Hawaye sun cika idonta aranta Fadi take"Ni ba barauniya bace..kuma ni ba ballagaza bace..! Ammh ta kasa Furta haka afili Tama kasa wani motsi. Aliyu ne ya Dafasa yana Fadin"Cool down Shehi..Bana som Fushin nan naka mara kyau..! Ya Nazeem ne ganin Amina taki tafiya yace"Au ke bazaki wuce bane..? Ya uzairu yace"Duka fa take so ya Nazeem ba"a shiga Jikinta bane..! Mamakin Tsayuwarta yake Cikin Daga Harshensa yace"Bazaki wuce ba..? Yafada kuma yana Daidaita Fushinsa Da Sauri Aliyu yace"Amina wuce ki koma Cikin gida kin ji ko..? Ya fadi sunanta kamar yadda yaji an Fada Bata Dago ba kamar wacce muryansa ta bata gwarin gwiwa maimakon ta Juya sai ta fara Tafiya kawai da Sauri ya Shamsu yace"Ke ina zaki..? Daman wanda zata Huce akansa take nema wanda yayi mata yafi karfin ta Ja dashi yasa jin muryan Shamsu ta waigo cikin Fada tace"To gida zani..! Tafada Lokaci Daya tana Sakarmai Idanuwanta tana kuma Murgudamai baki harda Harara sai kuma Hawaye dukkansu sun gani Shamsu ya Zaburo yana Fadin"Ke ni kike juyama baki..?zan karyaki in na rike ki..! Amina ta Tsaya kyam tana Fadin"gani..Kada kabarni da rai ya shamsu don Allah..! Tafada tana kallonsa da Jajayen Idanuwanta.. D'anmallam yakalleta ta fa Daina bashi mamaki Aliyu yace"Kai shamsu kyaleta..baka ga yanayinta ba inajin ba ita kadai bace..! Ya Nazeem yayi Dariya bai ce komai ba acikin Salo Salon iskancin Amina wannene basu gani ba Ya shamsu yace"Wlh lafiyarta Kalau..Duk Salon rashin kunyarta ne Daman bata tsoron kowa ta bari nazo ta gani..! Ya fada zai nufeta yaji D'anmallam ya Dakamai Tsawa yana Fadin"Shamsu kyaleta... Ke bar nan wurin..! Ba musu ta juya bayan ta kara juyama Shamsu baki tana kunkuni ta wuce tana Sharan kwallah D'anmallam ya Saki Siririn Tsaki yana Fadin"Kazama kaawai..! Ya Uzairu yace"Yaya da ka bari Shamsu yaci Ubanta..Ko"ina ta Addabi mutane chan ma bata bari Baba Sa"idu ya Huta koda yaushe Fitinarta..! Hannu ya Dagamai yana Fadin"Nace ku bar mganar ko..? Dole suka koma suka zazzauna shi kuma sai Sakin Huci yake Kafadarsa Aliyu ya Dafa yana Fadin"Allah huci Zuciyar Shehi..Ungo wayarka kila sai ta Hau kan Teburim mai gyara..! Karba yayi Lokaci Daya yana ganin yadda Sreen din wayar ya tashi aiki. Karamin Tsaki yaja kafin yace"Yarinyar nan bata jin mgana..kamar ballagaza bata da natsuwa ji asaran da ta jamim Wayar nan fa sai dai na Sauyata ta gama aiki..! Aliyu yace"Is ok..Kayi Hakuri muna da kudin Siyan wata kannen namu ne sai Hakuri..naji Uzairu na Fadin Baba Sa"idu Hala Diyarsa ce..? D'anmaallam ya gyada kai bayason mgana ba Domin Kada mallam yayi Fada da Tuni yana gida ya kwanta ya Huta. Aliyu yace"haba na kamar su da Yaya..Hala Diyarta ne..? Nan ma kai ya gyadamai Aliyu ya Kalli Umar yana shafa gemunsa yace"Irin su ne Sweet Sisty Shehi..Anya bazan kama Daya Cikin kannen nan namu ba..?tunda kai ka yi auranka da balarabiya..! Danmallam ya kallesa a adage kafin yace"Wadanan yaran zaka kwasa..? Aliyu yace"ofcourse sun fi Dadin harka ne..! Danmallan yayi Tsaki kafin yace"Wlh baka da Hankali..kai yanzu Gemi gemai dakai AA kace wadanan yaran kake so ka aura..?Ya"yan Cikinka..? Aliyu yace"Bangane ya"yan Cikina ba..?nifa ba Tsoho bane mallam Shekara Talatin da taran ma ban cika ba..Sai watan jibi..! Wani Tsakin ya kara ja kafin yace"Me yayi Saura a arba"in AA..?Wlh da auran Fari mukayi dukkanmu da muna da kamarsu ko basu kai su ba suna Tsaransu..! Aiyu na Dariya yace"Kai nifa ba Tsoho bane..Ko yanzu naso zan auri yar 12 ma ballatana yaran nan sun Haura 15..! Dan mallam ya Dafe kansa kafin yace"Plz ka kyaleni da wannan Shirmen naka am not in d Mood..! Aliyu na Dariya yace"Kai Shehi..Kaifa nasan sai ka cike kofa Danmallan fa kake..!sunnar nan sai ka ciketa..Ina baka Shawara in zaka kara ka karo irin yan yaran nan sun fi Dadin Sha"ani nidai kar ka manta ina kamun Daya Daga Cikinsu duk wanda ka bani am Greetfull..! Danmallam ya fara ma Aliyu kallon ya Tabu ganin haka yasa ya Buga Kafadarsa yana Fadin"Am Serouis fa Shehi..! Danmallam ya Kauda Fuska yana Fadin"Plx ka cireni cikin Shirmen naka..Kuma wlh in kace zaka auri irin yaran nan sunanka Sorry ka kai Jidali Gidanka da kanka am Telling u..! Aliyu yace"Eh bakomai..Tanque for ur Advice..! Ko kara kallonsa bai yi ba shi kuma Aliyu na Dariya yace"Tunda ka gaji dani..Bari na kira Aliya nace ta fito ita da yaran mu kama Hanya..! Kamar bai son mgana yace"Ka bari yaran chan su tafi mana..! Aliyu yace"Wasu yaran..? Yamutsa Fuska yayi kafin yace"Amaran mana..! Aliyu yayi Dariya yana Fadin"Shehi Umar..Mijin Sakina ango Saratu..! Hararansa yayi kafin yace"Sarood na ce maka..! Aliyu yace"oh..Sarood kasan bakin ya saba da Hausa ba irin ku da bakin ya Juye da Laranci ba..Angon Balarabiya..! Yake fada yana Dariya Danmallam Mirmishi kawai yayi kafin yace"kana da matsala AA..! Sa da aka fara Haraman fita da Amare su Hanne suka Tabbatar da Amiba bata gidan sun Duba ko"ina basu ganta ba. Zafira tace"To ina taje..? Hamida tace"Gida ta koma fa..! Zafira tace"Muje to..! Hanne ta harareta kafin tace"Jeki a karya miki kafa.. Zafira ta kama bakinta kafin tace"Au na manta ne kai ban kara zuwa Bikin Gidan nan Wlh..mu achan gusai in ana Biki ba inda bama zuwa bamai Takura mana..! Hamida da Hanne suka ce Hamm atare sun kasa mgana. Suna gani aka fita da Amaran suna kuka ammh ba Halin su bi Tawagan masu Rakiya. Falon Baba Maallam aka shiga Dasu Hajiya Babba,Sai Hajiya uwa sai Yaya kadai suka shiga dasu. Baba Maallam da Aba sai su ya Danmaallam da Su ya jafar ya Nazeem ya Nasir ya Nazir dukkansu dai mazan suna ciki hatta su ya shamsu Sauran matan kuma suna Waje suna Jiransu Ciki harda Sakina da su Sarood da Aliya sakina taso ta bi Sadiya zuwa Dutse Umar ya hanata yace ta bari Daga baya. Nasiha ne maallam yayi musu,Kadan Ba da yawa ba Domin yace duk abunda zai Fada musu an sanar dasu sai Aba shima yayi nashi sai Ya Danmaallam sannan ya Nazir sai su ya Jafar hatta su shamsu sun musu sallama. Daganan Baba Mallam ya ba kowacce Qur"ani Izu Sittin da azkar da Casbaha yace in suka rike kyautarsa sun gama Lafiya.. Daganan ya mike suka fito shi da Aba da Hannayensu suka saka kowacce a Motar da za"a kaita gidan Mijinta suna kuka suna Daga ma iyayensu Hannu. Su ya jaleela da su ya Nazifa da su ya Fatima duk suna Kofar gida bakin Motocin suna sallama dasu sauran matan suna daga cikin gida. Daya Bayan Daya Motocin Amaran suka tashi sai fatan Allah yakai Lafiya sannan mata suka koma cikin gida. Alokacin ne Danmallam suka shiga cikin gida shida Aliyu suka gaisa dasu Hajiya sannan yace Aliya ta fito su tafi sai da taje ta ma Hajiya sallama ta bata kayan Cincin na biki tana ta Godiya. Kafin La"asar suka wuce Bayan sun Rabu kan suma suna nan zuwa. Sallar la"asar kadai yayi a anguwan ya Shiga Mota ya koma gidansa ya kwanta Saboda Hayaniya. Zuwa Dare gabadaya Amaren Dake nesa sun isa Mazajensu sun kira Baba Maallam suka shaidamai sai Hamdala gidan kuma sai aka Fara Hada hadan kayan Tafiya zuwa gobe hatta su Ya Jaleela ma Baba Mallan yace kada wacce ta kai mai jibi agida ya Jadwa ne kadai zai Dagama Kafa sai visan su ya fito. Ya Akila da ya Fatima gobe zasu bi mazajensu su koma su jidda ne jibi zasu koma ammh gobe Dutse zata sauka bayan tagama ganin Dakin kanwarta ta wuce kano..! Su hanne sai Dare suka ga Amina adakin Mamanmu taci kukanta ta Share hawayenta duk yadda suka so su Zolayata yau Amina bakinta ya Mutu kazil batace ba haka suka kwana gari na wayewa sun sani suka Fara shirin tafiya Hadda harta su ya Abida kuwa. Kafin su tafi sukayi sallama da Zafira aranar zasu tafi Allah Sarki Sabo kamar kada su rabu,ko kafin su Dawo makaranta da yammah yan gusai sun koma,gida ba kowa sai goggo Husai da Ya Jadwa da Ya Jaleela da gobe jirgi zatabi zuwa Lagos ya Jawahir ta bi yan Gusai sun koma. Ya Zahra ma jirgin yammah tabi ita da Mijinta Daman yazo Daurin auran sai ya Zulfa da gobe zasu koma ita dasu Ya Uzairu su ya Nazir da Matarsa tun safe suka hau jirgi suka koma Lagos. Chan gidan Baba mallam ma kowace Danginta sun tafi yan maiduguri kadai suka Rage sai gobe zasu wuce Ya Jidda ta Sakina da Sarood sun tafi Dutse tun Safe,Danmallam yaso ya hanasu Tafiya Hajiya tace ya barsu su tafi sai gobe zasu dawo. Ta bangaran kowacce Danginta sun Tafi Sai daidai su Baba Lami nata Faman gyaran gidan. Koda sukaje Hadda Amina bata manta ba sai da Taja Mariya da fada aka Fitar dasu Waje Mariya ta rika yima Amina Allah ya isa. Ta kalleta tana Dariya kafin tace"Allah ya isa taki ce awajen Amina kin ga kaina tafi Dubu.. Take fada tana ma Mariya gwalo sai Da aka tashi Hadda aka Sallamesu da aka shiga islamiya ba haka ta Dinga Tsungulinta sai da aka kara Kadata waje. *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️14* Kimanin Sati Biyu kenan da Watsewar Bikin su ya Zulaihat baki na nesa da na kusa duk sun koma Gidajensu Goggo Husai ce mutanen Jordan da ya Jadwa basu Tafi da wuri ba saboda Mtsalan Visa sai cikin Satin nan suka samu tafiya. Amaran suna gidajensu cikin Koshin Lafiya sai Fatan Allah ya Zaunar dasu Lafiya Bakin Madina ne kadai ya Rage basu koma ba suma suna ta Shirin Tafiya cikin karshen watan da muke ciki Zasu fara sabuwar shekarar Musulunci achan Madina din. Yau ta kama Laraba ce Tun Safe Amina ke kwance kanta na ciwo Daga Dakinsu sai ta koma Dakin Mamanmu saboda Hamida ta isheta ta Mitar ta tashi ta gyara Kayanta data Zube kan gado wajen nemam Hula ta saka ma kanta ita kuma ta mata banza Tun bayan kallon Hamidan da tayi tana Fadin"Don Allah Hamida ki gyaramin kin ga fa ban da Lafiya..! Hararanta Hamida tayi Kafin tace"Kin ma isa..?Wlh bazan gyara ba Daga neman Hula sai ki baro da Duka kayanki a kasa ai da gangan kikayi Tunda kinsan kina da mai gyara miki yau kam bazan yi ba ki tashi ki gyara da kanki ko kuma ki bar Kayan naki su Rube anan wajen..! Amina kallon Hamida ta Rikayi acikin Ranta Tana Tunanin Hamidan ta Rage Mutumci yanzu ganin dagasken bazata gyara ba kuma tana ta Damunta yasa ta mike ta Bar mata Dakin Tana Fadin"Kici kanki ke Kadai..! Allah yasa ya Zeenatu bata nan Tana makaranta Sai su agida tunda basu fara zuwa makaranta ba tukunnah. Dakin Mamanmu ta shige ta Kwanta Chan saman gadonta Batama san tana ciki ba sai Daga baya ta shigo ta ganta Tashinta tayi tace ta tashi taci wani abu tasha Ko panadol sai da mamanmu tayi da gaske sannan Amina ta tashi tasha Tea ta Hada da Panadol ta koma ta kwanta Sai barci kuma barcin mai Nauyi ne ya Dauketa Ta Dadebatayi irinsa ba Tunda ba barcin Rana Amina keyi wani Lokaci ba. Ba ita ta farka ba sai Wajen uku Saura na Rana taji kan nata ya Sauka sai kuma Kasala ya kamata ta kasa tashi ta koma ta kwanta Sama sama tana jin kamar tashin mganar mutane Daga Falon Mamanmu sai dai bazata iya tantance ko su waye ba Ita duk a zatonta su ya Zeenatu ne da Hamida yasa ta gyara Kwanciyarta sai Bayan La"asar taji mamanmu na Kiran sunanta Idanuwanta Cikin yanayin Barci da Nauyi ta Bude manyan Idanuwanta ta Sauke kan Mamanmu wacce ke Tsaye kanta tana Fadin"Amina ki tashi hakanan kiyi sallah kici abinci in kan bai Daina ba In Aba din ku ya shigo na Fadamai ko Asibiti sai akai ki..! Amina na shirin komawa barcin Mamanmu tace"Tashi mana Amina...Kada ki koma barcin nan .! Dole yasa ta mike tana Mika Lokaci Daya tana Fadin"Wash...! Mamanmu na Shirin Fita Daga Dakin tace"Ki rika Salati mana Amina.! Daga haka ta fice Daga Dakin Dakyar Amina ta zuro da Kafarta Ta Sauka Daga kan gadon tana gyara Zaman Doguwar rigar Dake jikinta na Wata jar Atamfa Sai ta Dauki Hulanta ta Rufe kanta sannan ta fito Daga Cikin Uwar Dakin kanta tsaye ta fito Falon Sai dai Fuskokin data gani ne yasa ta Dan Tsaya tana binsu da kallo kamar yadda suma suke kallonta. SArood ne ta washe mata Fararan Hakoranta daya sa itama ta Sakar mata Dariya. Sakina kuma Kanta na kasa tana Danna wayarta Sai da taji mamanmu na Fadin"Kin taso..?ki farayin Sallah sai kici abincin ina Fatan kan ya Sauka..? Da kai ta mata mgama ganin yadda Sakina ta Dago tana mata kallon Sama da kasa,Mamanmu ta cigaba da Fadin"Matan D'ammallam ne suka zo mana Sallama jibi zasu koma tun Dazu suka zo Lokacin kina ciki kwance..! Amina ko Tsayama bin mganar mamanmu batayi ba har takai Kofar Dakin Sanda Taji Sakina na Fadin"Yarinyar nan bata da kunya Bata iya gaisuwa bane..?yar wajenki Hamida ta fita hankali da natsuwa..! Sanda Amina takai Tsakar gidan Sai data juyo ta Harari Dakin na mamanmu kafin ta Murguda baki afili tace"Eh din baza"a gaishekin ba..Mutum sai gajarta kamar an kife kwarya..! Tana jin Sanda mamanmu ke Dariya tana Fadin"Amina ta dai fi Hamida baki ne ita kuma Hamida ta fita Hakuri..! Tabe baki Amina tayi kafin ta karisa Cikin Kitchen Babban Cooler da suke zuba abinci ta Bude Farar shinkafa Akayi miyar kifi bata wani Dameta ba,Kadan ta Diba ta saka Miyar nan Kitchen din ta zauna taci ta Bude babban Fridge din Dake Kitchen din ta Dauki Ruwa tasha Tana cikin shan ruwan sai ga yaya ta shigo Kitchen din,Kallonta tayi batayi mata mgana ba ta wuce tana Bude Dirowar saman Kitchen din Ko kallon inda Aminar take batayi ba sai da Aminar tace"Yaya duk yau ban ganki ba..! Bata kalleta ba tace"ina zaki ganni tunda baki je inda nake ba..? Meyasa baki je makaranta ba..? Amina tace"Ban fa da Lafiya ne Tun Safe..! Yaya ta Dauki kulin Ararrabinta Data ijiye ta fice Daga Kitchen din tana Fadin"Allah ya sauwake..Tunda kin ji Sauki ki kwashe kwanuka nan ki wanke yau hamida da Zeematu sukayi ta aiki acikin gidan nan..! Baki Amina ta Tura afili ta Furta"Hamida bata da mutumci yanzu..Shine ko tamin ko..? Kyafci tayi domin ta Tsani wanke wanke gwara tayi shara Daman Hamidan take tusama wanke wanken Sau tari ita kuma sai tayi shara to kwanakin nan taga Hamidan ta waye ne sai tace kowa yayi aikinsa. Batasan komawa Dakin mamanmu Tanayin alwalanta ta shige Dakimsu kayanta kan gadonta Hamida ta Tula mata su baki ta karkace batayi mgana ba bayan ta idar da sallar kan gadon Hamida ta koma ta kwanta tana jin bayanta ya gaji Tunanin yadda zata fita tayi wanke wanken kadai take yi kara narkewa tayi In mamanmu tazo sai tace ciwon kam ya Dawo Dole Dai yaya ta kyaleta Domin mamanmu bazata barta ta fito bata da Lafiya tayi wani aiki ba. Sai dai addu"arta bata ci ba Domin tana jin an Daga Labulen Dakin ta kara Lafewa har tana wani Nishi Sama Sama Yaya ta kalleta kamar tayi Dariya ammh sai ta kanne Cikin Kaushinta tace"Zaki taso zuwa aikin ki ko kuwa sai na shigo na iskoki kan gadon nan..? Amina ta tura baki jin Muryan Yaya Kafim ta Mike Zaune tana Fadin"Kai Yaya ciwon kan fa bai daina ba..! Labulem ta saki Tana Fadin"Ki gama aikin ki in bai Daina ba In Jafaru ya shigo sai ya kaiki Chemist ayi miki Allura..! Ido Amina ta zaro Kafin ta Diro Daga kan gado afili ta Furta"Na yarda yaya bata Kaunata..! Yadda ta Tsani Allura kuma sannan ma a rasa wanda zai kaita sai ya Jafar ai data Kade har gayenta an samu mugayen duk sum koma inda suka fito ya shamsu ne sai a islamiya suke Haduwa su ya Jafar kuma sai dai taji muryansu in sum shigo gaida su yaya bataama yarda su hadu tun bayan Watsewar sha"anin suna gida Tunda ba makaranta suke zuwa ba ko Hanne ta rage shiga wajenta itama Ganin haka yasa sai ta kwana Biyu bata shigo ba sai dai su hadu a islamiya da yammah. Hakanan tana Tura baki tana kunkuni ta fito da kwamukan wanke wanke zuwa Bakin Famfo Dakin mamanmu ta leke bakowa ita ta shiga wanka su Sakina kuma suna Dakin Yaya Daga Tsakar gidan ma tana jiyo Tashin Hirar Sakina da yaya Sarai Sarai ta kwashi kwanukan da suka bata nan Falon mamanmu tana kunkuni ita Kadai. "Sun wani zo sun bata mana kwanukan sun karamim aiki..Mtsewww..! Nuku nuku ta dinga yi Saboda Mamanmu ta fito ta hanata sai dai Addu"arta bata amsu ba Mamanmu bata Leko ba sai ma yaya ce ta Leko raka su Sakina suka leka Dakin mamanmu suka mata sallama sai gasu sun fito Tare tana gyara Daurin Dankwalinta Lokaci Daya tana Fadin"Ke Sakina yar"uwar taki bata jin Hausar tamu sai labarcimu kuma bamu kware ba..! Tafada tana Dariya Sakina ke Fadin"Mamanmu wanda aka Haifa achan yayi Rayuwarsa achan ina zai ji Hausa..?Sai dai hankali zata iya Tunda yanzu ta shigo Cikin mu..! Yaya tace"Kwarai tunda ta auri Bahauahe ba..koda yake shima ai Danmallam din Harshensa ya Karye kamar Balaraban chan..! Mamanmu tace"Ai ya Dade fa achan yaya..Ina jin yafi shekara goma ko..? Sakina tace"Yana cikin shekarata ta ashirin ne fa naji yana Fadi..! Mamanmu tace"Koda naji..! Yaya tace"Zai yi fa Tun su Zahra na kanana fa alokacin..! Ita dai Sarood sai dai tayi ta washe baki in ta tambayi Sakina me akace ne sai Sakina ta gayamata da Larabci Duk da itama ba wani kwarewa tayi ba Harda iyayi ita Adole tana jin Labarcin. Amina na Tsugunne tana wanke wanke ta tabe baki aranta tace"Allah yasa ma tasanme take fadi..! Mamanmu ce ta ganta cikin jin Dadi tace"A"ah jiki yayi kyau Amina..! Dole ta Dago tana yake tace"Eh Mamanmu kam ya daina ciwo..! Da sauri tace"Masha Allah..To kiyi Sauri ki gama kada mangariba ta Sauko baki gama ba! Da toh ta amsa batare data kara mgana ba,har suka wuce har korido suka Raka su Sakina suna kara musu sallama da alkawarin agoben kafin su tafi zasu shigo gidan su kara yin sallama. Tana jin har sanda su mamanmu suka Dawo tana mata Fadan tayi ta gama Ko mgana ma batayi ba da kai ta kara amsaa mata,nuku nuku ta Dinga yi sai tafi minti Biyar bata wanke Kwano Daya,Har Su hamida suka shigo sun Dawo Daga islamiya Ya Zeenatu ne ta kalleta tana Fadin"Har duhu ya shiga Amina kina zaune bakin Famfo alhalin kinsam har Aba yayi Fadan hakan.!? Amina taso ta dago tace"Ina Ruwanki ne..? Sai kuma ta fasa ta Tura baki ta Kauda kanta Ya Zeenatu ta wuce tana Fadim"Ke kika sani..! Hamida ne ma tace"Kin warke kenan..! Daman jiranta take sai ta mike ta Rike kugu tana Fadin"Ina Ruwanki..Im ma na warke in ma ban warke ba..Duk ba Damuwarki bane..Kada kuma ki Dameni Mutum ba Taimakaa maka zai yi ba sai ya isheka da mita akyaleni ko sai gobe ne in gama ina Ruwan wani..! Hamida bata tanka ta ta wuce Daki abunta ta ijiye jakarta,Duk tana wajen suka fito sukayi alwala ba wanda ya tankata ta juye Jidalinta akansa itama sai Harare harare take yi karshenta dai kan Jawad ta Sauke Haushinta wai ya Watsaa mata Ruwa haka ta mike ta Rikeshi ta Falfalmai mari har sai da yayi kuka da kuka ya fita masallaci Lokacin Yaya tana Sallah Hamida ce awajen kuma batace komai Domin tasam ba karamin aikin Amina bane ta Dawo da duka jidalin kanta Shiyasa bakinta kanin kafarta ta koma Daki. Amina har aka Idar da salla tana bakin Famfo bata gama wanke wankenta ba,Yau din ma Ya Danmalam ya bada Sallah Ita Rabonta da gansa tun Ranar Daurin aure da yayi mata wannan Tijaran ta gujema haduwa dashi Shine mutuum na Farko Daya taba Cin Zarafimta bata samu ko Baki ta Turamai ba yana da ta wata baiwar da komai Rashin kunyarka sai kaji Shakkarsa. Afili ta Furta"a Muryansa kamar mai kirki nan kuwa cikinsa fal Tozarta Mutane..! Bazata ce taji Sallamamsa ba Daga sama kamar acikin kanta taji Sansanyayyar Muryansa cikin Zatinsa yana Fadin"Waye anan..? Ya ke fada domin Lokaci akwai Duhu kuma ba"a riga a kunna injin ba. Kyam Amina ta kame Daga inda take Sai kuma jikinta ya fara rawa da taji Muryansa batasan Dalili ba Bata son Haduwa dashi bata son jin muryansa Domin Fadar mata da gaba Muryansa yake yi sannan Uwa uba ganinsa ba Alheri bane sai ya Tozartata. Kokarin Fito da wayarsa yake ya Haskata sai Haske ya gauraye Tsakar gidam,Nepa sun kawo Wuta Daidai Lokacin da Idanuwan Amina suka shiga Cikin na Umar Dake Tsaye Gabda da ita yana kallonta kamar yadda itama take kallonsa. Sanye yake da Jallabiya mai Ruwan kasa da Hula a saman kansa sai Bakin Wandon Dake jikinsa Tunda Jallabiyar bata kaai mai Kasa ba. Fuskarsa ta kara kyau ya Kara Haske har wani Kiba taga ya karaa mata. Cikin mamakin ganinta acikin wannan yanayin yake Fadin"Ke me kike yi anan da Mangriban nan..? Yake Fada yana kara Nazarinta da Sauri ta Sadda kanta kasa ta kasa mgana,Jikinta ba inda baya rawa,Lebenta Kamar ya Nane haka taji ta Kasa mgana shi kuma Ransa ya fara baci yarinyar nan bata da kunya Rainin Da take yi ma su Jafar shi take so tayi mai yasa ya Dakaa mata Tsawa Cikin Bacin Rai yace"Bada ke nake mgana ba..?Kika bari na nazo wajen nan sai na Lahira yafi ki jin Dadi..! Ki bari na taso ki gani..! Tsawamsa shi ya fito da su Hamida Harda Mamanmu da Yaya sai suka ga Danmallamm Mamanmu ce ta washe baki tana Fadin",A"a Umaru barka da zuwa! Kallonta yayi kafin yace"Mamanmu me yarinyar nan take yi anan wajen nan har yanzu..? Mamanmu tace"Amina ce wanke wanke take.! Katseta yayi da fadin"Haba Mamanmu tana mace? Da mangariban nan ita Kadai acikin Duhu bata tsoron lafiyarta.? Mamanmu ta kalli Amina da Kanta ke Kasa tana ta fiki fiki da ido tace"Wlh Danmallam sai da nayi mta magana Tayi ta gama Kafin Dare yayi..Dayake ba Lafiya ne da ita ba..! Amina taso daga wajen nan Hamida da Zeenatu ku taaimaka ku karisa don Allah ina ga Kan ne ya Dawo mata! Zeenatu tace"Mamanmu Wlh lafiyarta kalau Aminar ce baki sani ba! Hararanta tayi Kafim tace"Bazaki yi ba kenan? Dole tayi shuru bata kara mgana ba Amina kuma kamar mumafuka kanta na Kasa ta taso tsomai Tsomai kamar Wata kazar da aka Cirota Daga Ruwan Zafi Danmallam ya bita da kallo Cikin kyama aransa yana Tunanin yarinyar nan ta wuce Tunaninsa Yaya ce ta faraa mai maraba tana Fadin"Maraba da zuwan Dan mallam Ga bakin Larabawa..Lale..! Jin Muryan yaya yasa ya kariso Cikin Fara"a nan Tsakar gidan ta Shimfida mai Darduma ya zauma suka Fara gaisawa Zeematu da Hamida suka gaisheshi ya amsa kafin mamanmu tazo ta zauna su gaisa Daganan ta koma Daki ta bar su shi da Yaya suna ta Fira Amina dai tunda ta samu ta shigo Daki bata kara fitowa ba Hamida da Zeenatu suka karisa aikin suka maida komai Kitchen suka share wajem abayin Dakin tayi alwala tayi sallah Ta Haye kan gadonta bata Damu da Kwashe kayanta akansu ta kwanta bata Damu ba Ya zeenatu ne ta shigo tana ta Fada Fadi take"Wlh Amina ki rika Karisa aikinki..Domin nan gidam ba bawanki..Ni ba Hamida bace Darajan Mamanmu kikaci Wlh..! Amina na jinta tana Danne Dariyanta Daga kwamcen Tana kallonta kai ta kada kafin tace"Ba Laifinki bane..Mamanmu ce take Daure miki gindin Iskanci Watarana ai ba Maman ko..? Naga uban da zai zauna kina wannan iskancin bai ci ubanki ba..! Ita dai bata tanka ba har ta gajii da Mitan ta fice bayan Fitar Danmallam Daman Sallama yazo yi ma su Yaya Gobe Jirginsu na dare me zai tashi zuwa Jidda a Filin Sauka da Hawa na Aminu kano. Sai da ta ficen ne Amina ta fito da Dariyanta tana Fadin"Allah Sarki..Ya Zenatu kawar ya Abida...! Hamida ta kalleta kafin tace"Ke kam ki tashi ki gyara kayanki Amina Harda fa Sabbi ciki..! Amina ta kyabe baki kafin tace"In kin Damu ki gyaramin Hamida! Hamida tace"Na rantse kuma bazan yi Kaffara ba..! Tsaki Amina taja Kafin tace"To sai ki kyaleni malama! Hamida tace"Yau anyi Fada da Mariya da Sa"adatu..Har da Dambe sai da mallam Auwal ya Zanesu..! Da Sauri Amina ta Mike tana Fadim"Don Girman Allah..? Hamida tace"Wlh suna Zage Zage..Kinsan Hanne da tsoro sai kuka take yi..! Amina ta Daka Tsalle har da shewa kafin tace"Ahyayyeee...Yau naji Dadi karshen alewa kasa. daman ai xaman munafunci baya karko..Tacizi yatsa Kafin ta cigaba da Fadin"Naso yau naje..Da sai na kara Yamutsa wajen munafukai..! Hamida tace"Gwara dai da baki je ba..! Amina ta balla mata kafin tace"Ga Shedan ko..? Hamida kina shigarmin hanci fa ki kyaleni.!. Hamida tace "Daga Fadin gaskiya..?ai ba karya nayi ba Da kina nan wajen Allah kadai yasan iya inda abun zai kai..! Amina ta karkace baki kafin tace"Hanne wai me aka mata take kuka..? Hamida tace"Me kuwa..?tsoro gareta Taga suna Ta kwasan Dambe..! Amina tace"Aikin banza Hanne banza ce..Meye abun kuka..? Allah ya Tsareni..! Hamida dai bata kara mgana ba Domin Har ga Allah taji Dadin da Amina bata zo ba Domin Allah kadai yasan Iya inda Fadan nan xai kai Amina sai ta hau Fadan ta siyeshi ta kara Maggi da gishiri. Waashegari Da Safe ta shiga wajen Hanne ta iske Su Sakina suna gidan suna ta shirin Tafiya Ya Jafar zai kai su kano Ya Nasir yana da aiki a asibiti. Amina ta kalli Hanne tana Fadin"Wai ganin ana Fada da Sa"adatun ne kike kuka..? Hanne tace"Ni bana son ganin ana Dambe ne..Ko ke kike Fada ai ina kuka..! Amina tace"Wlh karya kike yi..Natan Dai kike kuka ke mai yar"uwa Ki kama Kanki Hanne Domin in kece Dariyama zata yi kina abu kamar wata sakarya..! Hanne tace"Bakomai naji..! Kinsan yau su ya Danmallam zasu koma..? Amina ta tabe baki kafin tace"Jiya sun zo gidanmu naji Mamanmu na Fadin yau zasu koma Dukkansu zasu koma..? Hanne tace"eh mana..! Amina tace"To in suka tafi sai yaushe..? Hanne tace"Yace ma Hajiya sai wani abu ya taso..Im bai taso ba sai nan da wata Shidda zai zo..! Amina tace"Allah ya tsare..! Aranta kuma Fadi take"Allah ya raka taki gona..! Lallabawa tayi ta gudu gida abunta batama san Tafiyarsu ba su yaya dai da mamanmu sun je sun karayin musu sallama sai yamma suka Dawo suna Fadin wai har ya Jafar ya Kira suna kano basu dai tashi ba sai Dare. Sai washegari wajen chan Rana taji ana Fadin sun sauka a jidda Daganan zasu hau Mota zuwa Madina ko ajikinta Sai taji kamar wani Nauyi ya tafi Bata ko kaunar ganinsa ma ballatana jin muryansa. ******* Bayan wata Daya..! Amina na kwance da Safe tana barci Taji ihun Hamida asaman kanta tana Dukanta Lokaci Daya tana Fadin"Amina tashi..Tashi.! Next week zamu fara zuwa makaranta an gama mana komai..! Amina da sauri ta Bude idanuwanta cike da barci tace"ke a ina kika ji..? Hamida tace"Yanzu naji Ya Jafar yana Fadama Mamanmu..! Amina tace"Ina zamu koma..? Hamida tace"Ina kuwa..?Unity...? karamin tsaki taja kafin ta gyara kwanciyarta Tana Fadin"Yanzu dai chan zamu koma..?nifa na Tsani Unity din nam..Allah yasa banda munafukar nan Sa"adatu..! Hamida tace"Kema kin sani..Gabadayanmu ne..! Amina ta Yamutsa Fuska kafin tace"Ban so ba..! Naso kowa ya kama gabansa..Ke ni fa Wlh nafi son zaman gidan nan akan komawa Shegiyar Unity din nan..! Hamida tace"Ke yanzu zaman bai isheki ba..?Tab ni Wlh na gaji..! Amina tace"Da an bari Second Term sai mu fara zuwa..! Hamida bata bi ta kanta ba ta Fice tana Murna Amina ta Bita da kallon Na Tsausaya. Da yammah ma sai ga Hanne tazo suna Murna ita da Hamida Amina tun Tana Daukan mganar wasa sai gashi ta Tabbata an kawo musu sabbin kayan makaranta na Senior da Jaka da takalma Da Safa da Sabbin Littafai ya Shamsu yakawo musu nasu Ranar Monday zasu fara zuwa. Kowa na Murna banda Amina Tsakani ga Allah Hutun bai isheta ba ta so sai Second Time su koma makaranta ammh Ina ba wanda zai bar su su zauna agida ana kallonsu Takaicinta Daya Sa"adatu bata kaunar su na Hada Hanya don bata da yarda zatayi ne kawai. Har ya Zeenatu sai da ta mata mgana Tana Fadin"Ke Amina Hanne da Hamida na Murnan Jjc yan SS1 KE banga kina yi ba..! Amina tace"Murnan me..?Unity ce fa..?Daman wata kayan gabas ne ba nan ba..Ni gabadaya makarantar ta isheni..! Ya zeenatu tace"Kina da aiki..Tun Zamamin su ya Nasir Unity ta kyankyshesu ballatana ke Zuwan yau yau..Yarinya Unity Dolen kowa ne indai D'an nan gidan ne ko dan Gidan Baba Mallam ne..! Amina baki ta Tura bata kara mgana ba Ganin yadda ya Zeenatu ta zakal kale,Tana ta bayani Hamida na Tayata su adole suna kara yabon Unity a wajenta Tabe baki tayi aranta tace ko Ta Tsani makarantar nan ba Sauyi kowa ban yayi ya gama suma kuma nan din zasu gama..! Kullum ba cigaba haba don Allah. *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️15* *Jumma"a* 9:00am Labulen Dakinmu Mamanmu ta daga tana kallon Amina Dake zaune Saman gadonta ta tasa kayan da mamanmu ta gama wanke mata jiya ko fara ninkesu batayi ba. Hamida na Gefenta itama wajen Dirowarta tana shirya Littafanta Cikin Sabuwar Jakar makarantarta Mamanmu ta kalli Amina Data Zabga Tagumi kamar wacce akace mata nata ya rasu Cikin Lallami tace"Amina baki Fara Ninke kayan nan naki ba ko..?yi hakuri ki adanasu ina aiki ne da na Gyara miki..Kwashesu ki saka cikin Dirowarki in anjuma in nepa sun kawo Wuta Zan saka Hamida ta goge miki sai ki adana Kayanki..! Hamida na jin haka ta Dago tana kallon Mamanmu kafin tace"Ni kuma Mamanmu..? Tafada Tana Bata Fuska Mamanmu tace"Eh ke..Ko bazaki yi bane..? Tunda ita haka Allah yayi ta bata da Zafin nama ku kuma yan"uwanta ne kun fita karsashi ba sai ku taimaka mata ba..? Hamida bata iya mgana ba ta maida kanta Gefe Amina kuma sai Danne Dariyanta take yi kafin tace"Dama ta barshi mamanmu..! Bata bi ta kansu ba ta saki Labulan ta koma tana Fita Amina ta Fara Dariya Har tana ma Hamida gwalo kallonta Tayi kafin ta girgiza kai tana Fadin"Kiyi Dariya son ranki..Lokacin ki ne ammh ki sani akwai watan watarana..Da babu mamanmu ba Hamida wlh sai kin raina kanki..! Kamar ba mace ba komai sai dai ki zauna komai Mamanmu tayi miki ko kuma ta sa muyi miki..! Tafada Cikin jin haushi Amina ta kara saka Dariya kafin tace"ko ba mamanmu ba gaki ba..? Hamida ta Harareta kafin tace"Ni kuma sai bazan yi aure ba sai na koma kula Dake..?Sannu Amina yar gata..! Amina tace"To miye..?Sai ki auri kanin Mijina..! Karamin Tsaki Hamida taja Amina ta kara saka Dariya tana Fadin"Hamdiya..Hamdiya..Hamdiya..! Take Fada cikin Sigar waka Da sai da Hamida tayi Dariya tana Fadin"Ke kika sani..Allah yasa ki shiga gidan mai mata Biyu kece na uku..Ya"ya kadai sun isheki Amina..! Amina tace"jar uba..ya auran ma kansa dai..Mai mata Biyun daya kwashi Amina ai mai Budurwan Zuciya ne..Sai yayi Nadama Tijara ne da Jidali ne zai gani harda na Siyarwa..! Take Fada tana Dariya Hamida na Tayata Daganan suka shiga Hirarsu Amina na tusa kaya cikin Dirowanta batare data Tsaya Ninkewa ba Hamida tace"Kai Amina mugunta ma harda karan kanki kike yi mawa..? Amina ta tsaki kafin tace"Ki kyaleni Hamida ni nagaji..! Hamida ta mike tana Fadin"Zaki ma mike ne yarinya yau ke kike da gyara mana Daki..! Amina tace"Kan bala balagagge..Ranar fa ni na gyara..? Hamida tace"Ai ba sau Daya ake gyaran Daki asati ba malama..! Amina ta Tura baki kafin tace"To nidai na gaji bazam iya ba..! Hamida ta bita da kallo batayi mgana ba Amina ta cigaba da Fadin"Mutum kamar jaki aiki aiki..Ni wlh nagaji..! Hamida baki ta rike ta kasa mgana wai Amina na Mganar aiki me takeyi..? Aiki sai ya zama Dole Amina ke yi in ba zama ba zamanta take Mamanmu na Daure mata wajen iskanci sanin da tayi bafa zata gyara Dakin ba yasa tamike ta fara gyarawa Amina na Mata Dariya sama sama tana jinta tayi mata banza kamar bata jita ba. Har ta gama gyara Dakin bata gyara wajem kayan Amina ba ganin haka yasa tace"Hamida Kashi nayi miki akan gado da baki gyara barayina ba..? Hamida tace"Bansani ba.! Amina ta tabe baki kafin tace"Allah ya baki Hakuri Anty Hamidaaa..! Ta karishe Fada tana mata gwalo karaf suka Hada ido Hamida tace"Don Allah nake yin komai ni..! Amina tace"Allahu akbar..Allah ya Biya malama Hamdiya..! Danne Dariyanta take yi kada Hamidan ta gani ta fasa gyara mata Sauran kayan ma Hamida ta gyara mata ta Ninke mata da kyau ta saka Cikin Wardrope din Amina ta kuma gyara mata gadon ita Amina Tuni ta shiga Tiolet din Dake Dakin zatayi wanka. Koda ta fito har Hamida ta gama gyaran Dakin ta share ta goge ta saka Turaran Wuta Amina ta Hura hanci tana Fadin"Kai Allah yayi ma Hamida albarka..! Komai yana son gyara ko"ina yayi kyau tas dashi,Zama tayi ta shafa mai ta saka wata Doguwar rigar Material tana cikin Daura bakin Dankwalin abaya ne Mamanmu ta kara Daga Labulan Dakin ta leko tana Fadin"Hamida zo don Allah..! Gishiri ya yankemin ina girki..! Amina ta Dago tana Fadin"Bata anan fa Mamanmu tana waje..! Mamanmu tace"Ai ban ganta bane..? Ta juya tana kiran"Hamida Hamida...hamida..! Yaya Dake Kofar Kitchen tana Taya Mamanmu gyaran wake tace"Hamida fa ta shiga makewayi..! Mamanmu tace"Gishirin nan fa ya kare Yaya..Bansani ba ina Dago Buhu sai bakomai aciki..! Yaya tace"Yafa Dade ya kusa shekara Tun Gishirin nan da Jafar ya hado cikin Wani siyayyan kayan abinci ne fa..! Mamanmu tace"Gaskiya ya jima..Gashi Babansu ya fita ba kowa agidan..! Yaya tace"Sai dai ki kirasa a waya,ki Fadamai ko kuma ki bada asiyo in ya Dawo sai ki samar dashi..in za"ayi Siyayyan kayan abincin wannan Watan kada a manta da gishirin..! Mamanmu tace"Nayi tunanin haka bari Hamida ta fito ta leka shagon baya ta siyomin ta dawo da wuri kafin cikin yayinsu su ganta nasha Surutu..! Yayaa tayi Dariya kafin tace"Aifa kinsan su masu yayyi ne..! Mamanmu tace"Nasani ne Yaya..Yaran da ba"ason ko nan da chan sufita..! Hamida wai ina ta shige ne..? Yaya tace"Ki aika Amina mana..Tunda Hamidan bata fito ba..! Mamanmu tace"Yauwa..Amina..Amina..! Ta tafi tana kwala ma Amina Kira sai gashi sun hadu a bakin kofar Dakinsu Tana Fadin"Gani Mamanmu..! Mamanmu ta kwanto kudi a Haban Zaninta ta mika ma Amina Dari Biyar Sabuwa tana Fadin"Maza sa Hijabin ki kije Shagon nan na baya ki amso min gishiri na Dora sanwa kuma na Duba ashe Gihirin ya kare yi maza Amina don Allah..! Amina ta karbi kudin ta koma Daki ta Dauko Hijabin Hamida Data gani Saman gadonta ta fito flat din Takalminta ta saka baki tazo tana Fadin"Gishirin nawa Mamanmu..? Tana gaban Famfo tace"Ki siyomin babban Jakan nan..Ki hadomin da Amo Amina wannan naga bazai kai an juma ba kuma shima shikenan jiya Zeenatu tace ta Dauko acikin Kwalin..! Da Toh Amina ta amsa zata fice Yaya na Zaune kan kujeran yar Tsugunno ta Dago kanta tana Fadin"Saura kuma ki Dade..! Juyowa tayi tana kallonta kafin tace"Ina zani to..! Ta fada tana Tura baki Hararanta Yaya tayi kafin tace"Daman baki bace..Inda aka ijiyeki ba nan kike Tsayawa ba..! Mamanmu tace"Amina kyale Yaya..Yi maza ki dwo yar albarka. Da haka ta fice tana kunkuni afili tace"Yaya bata taba Fadin Alheri akaina..Yoni ina zani..! Sai kuma Tayi Dariya sanin Halinta sai ta iya juya alaqanta zuwa gidansu Hanne ta ma manta da aiken Mamanmu karamin aikin Amina kenan. Sakamakon Safe ne anguwan tayi shuru ba kowa maza sun tafi wajen aiki yara kuma duk suna makaramta Shagon yana ta bayansu kadam ne ba zuwa shago suke yi ba komai na Bukatar gida a kasuwa ake siyo shi,sai dai in wani abu ya yanke kamar irin rana mai kama ta yau Bazata kirga Sau nawa tataba zuwa shagon ba kamar bai fi sau Biyu ba,Shagon babban Shago ne babu abunda baya saidawa mai shagon ba Dan garin bane bakano neyazo ya samu waje sai Allah ya saka ma kasuwancin nashi Albarka. Samda ta shiga shagon akwai Layin mutum uku agabanta sai ta koma gefe sai da aka sallamesu sannan ta matsa kusa da katan Shagon ta mikamai kudin Hannunta Lokaci Daya tana Fadin"Bani gishiri babbar jaka da omo..! Karban kudin yayi yana kallonta Ganin bai taba ganinta ba yasa yace"Wani irin Omo..? Amina ta yamutsa fuska kafin tace"Kowani iri..! Dauko mata yayi duka yana nemam ya Hadasu a leda Daya da Sauri tace"Tsaya tsaya..Mallama a ina kataba ganin an Hada gishiri da Omo waje Daya..? Yana yar Dariya yace"Au na manta ne..Yi hakuri don Allah..! Hararansa Amina tayi batayi mgana ba ya Raba kowannen Ledansa Dabam yana Fadin"Nace ba..A ina kike ne..? Naga bantaba ganinki ba..! Amina ta Tsaya tana kallonsa kafin ta saka Hannu ta warce ledan hannunsa tana Fadin"Ina ruwanka..?malam bani Chanjina na tafi..Tunda ba Sana"ar kake yi ba tambayan inda mutanen da suka zo siyayya shagonka suke kake yi..! Tsiwanta ke bashi Dariya yanzu ma Dariya yayi kafin ya Hado mata Chanjinta ya bata Kamar zata Dakesa haka ta Fizge chanji kadan ya Rage ta Hada da hannunsa baki ya rike yana Fadin"Kai..Allah ya baki hakuri..! Ko jinsa batayi ba tayi wucewarta Hankalinta na kan chanjin hannunta Tana Kirgawa shi kuma ya Sawo kansa Shagon Kansa na kasa yana Danna Wayarsa Daga bayansa kuma wani ne kebinsa yana Fadin"Oga da ka bari na amso maka..! "Bazan iya da shiriritarka ba Nura..Na ri..! Mganarsa ta makale ne sanda suka ci karoda juna kusan Tsawonsu Daya In maya fita da kadan ne yasa suka Daki Goshin juna Dayasa kudin hannunta da Ledan duka suka zube a kasa shidai Allah ya taimakesa wayarsa bata Fadi baya riketa Dakyau. Amina ta saki karamin Tsaki ta Duka tana kwashe chanjinta da omon Daya Fado a leda Daga saman kanta taji anaa Fadin"Baiwar Allah ki rika Tafiya kina kallon gabanki ok..? Sai da ta gama kwashe komai kana ta Dago suka Hada ido Hudu dashi Kallonta yake yi da Fararan Idanuwansa kamar yadda ta sakarmai nataa manyan Idanuwan Cikin kallon kama Raina ni tace"Dakata mallam..Ni dakai waye baya kallon gabansa..? Ni fita zan yi kai kuma zaka shigo acikin ni dakai wazai kalli gabansa..? Ta karishe Fada tana Hararansa Harda Murguda baki kafin ta Raba ta gefensa zata wuce. Cikin Wata sanyayyar Murya mai Cike da yanga taji tace"Ya zaki tafi..?,Alhalin baki bani hakurin Laifin da kikamin ba..? Juyowa Amina tayi tana kara kallonsa kafin ta Nuna kanta tana Fadin"Ni..? Kai ya gyada mata cikin yanga Lokaci Daya yana Jaye Hulan kansa Facing cap Kyakyawan Farar Fuskarsa ta bayyana. Amina tace"ai ban yi maka wani Laifi ba ballatana na baka Hakuri..Kumani Amina ban cika bada Hakuri a laifin da ban aikata ba wani Lokacin ma ko nice bani da gaskiya bana Laushi da wuri..! Ta saman Lebenshi yace"AMINA...! Nice name..! Kin fada min sunanki batare da na sha Wahala ba..! Amina ta Tsaya sake da baki tana kallonsa Wabda ke gefensa ne yace"Oga..! Bai bari ya karisa ba ya Laluba aljihunsa ya Dauko Walet dinsa ya Mikamai yana Fadin"Kayi abunda ya kamata Nura...! Karba yayi yana kallon Ogan nasa Daya Fara susucewa ganin wannan Kwailar yarinya to kwaila mana wannan ta wuce sha Biyar tsawon kafa ne kawai Kafada ya Daga kafin ya Nufi Cikin shagon Dutse zasu koma yanzu nan Kati ya yanke ma Ogansa acikin waya suka Tsaya su siya to lokacin ankirasa a waya ya Dauka sai Ya kasa jira ya fito da kansa zuwa Cikin Shagon..! Amina bata kara mgana ba ta fara tafiya da Hamzari ya sha gabanta yana gyara zaman Jaket din Dake Jikinsa Cikin Mamaki da Budewar ido Amina tace"Malam lafiya?Mtsamin Daga Hanya tunda bata gidan ku bace..! Mirmishi yayi har sai da Fararam Hakoransa suka bayyana Cikin Muryansa yace"Wani ya taba Fada miki kina Burgesa..? Yafada yana kallonta Cikin wani Salo Sai kuma taji mganar ta shigeta Cikin Sausasauta Murya tace"Ni AMINA ba wanda ya taba cewa ina Burgesa..Ni ai bana Burgewa kowa.! Wayarsa ya saka Cikim Aljihun Jaket dinsa Lokaci Daya yana Fadin"To yau Ni AMINU BUBA nace kina Burgeni...! Ido Amina ta zaro tana kallonsa mganar ta shigeta kanta ta kara nunawa kafim tace"Da gaske ina Burgeka..? Kai ya gyada mata Sai ta washe bakinta kafin tace"Nagode..yau na fara ganinka ammh naji Dadin Haduwa Dakai domin kai ne Mutum na Farko Daya fara cewa Amina Aminene na Burgesa bazan manta da wannan ba..Thank you..! Tafada tana Juya idanuwanta cikin bayanna Farimcikinta Shagala da kallonta yayi baisan ya Furta"She is Beautifull...! Bai an kara ba yaga tana Shirin Tafiya da Sauri yace"Ya zaki tafi kuma ki barni..? Da mamaki Amina tace"Bangane ba..? Mirmishi yayi kafin yace"Ke yar nan garin ce..? Da kai ta amsa mai cikin mamakinta da kuma kara ganin yarintarta yace"Ammh baki sanni ba..? Amina tajuya ido kafin tace"To a ina zan san ka bawan Allah..? Da sauri yace"Sunana Aminu..Aminu Buba..! Nayi matukar mamaki da baki sanni ba Shekararki nawa ne..? Amina tace"Shekarata goma sha Biyar da Wata Goma saura wata biyu na cika Sha shidda..! Tafada tana Kirgamau da hannu Dariya ta kamasa har sai da Wushiryansa ta bayyana. Tsayawa tayi tana kallonsa yadda yake Dariya abun sha"awa. Cikin Matse Dariyansa yace"Amina..Amina kina Burgeni..! Zan so na rika ganinki koda yaushe ko domin ki rika sakani Nishadi Aji nawa kike a makaranta..? Kunya Amina taji yasa ta sunkuyar Dakai kafin tace"SS1 sai monday ammh zamu fara zuwa..! Yana mata Dariya yace"Kice Jjc ne...! Amina yan matan SS1..! YAadda yake Dariyan ne ya fara Kular da ita yasa ta Hade ranta Nura Daya Fito Daga shagon tun dazu ya gaji da ganin wannan Drmar yayi gyaran Murya yana Fadin"Oga lokaci fa na Tafiya....! Hannu ya Dagamai kafin ya fiddo da wayarsa yana mikama Amina Lokaci Daya yace"Sakamin Lambarki..Amina ai daman Amina kawar Aminu ce ko..? Yafada yana Dariya itama Dariyan Tayi Domin Farat Daya taji ya burgeta kamar yadda yace itama ta Burgesa. Noke Hannu tayi kafin tace"Ni ai bani da waya..! Ido ya zaro kafin yace"Duk girmanki Amina saura fa wata Biyu ki kai shekara goma sha Shidda! Ya karishe Fada Cikin Zolaya Da sauri Ta kauda kai tana Mirmishi Kara Tura mata wayar yayi yana Fadin"Ko lambar Antynmu Babu Amina..? Amina tace"Tab..Bafa mai waya agidanmu Daga yaya sai mamanmu to ta yaya ma Jawaad ya jefata ruwa Ta mamanmu ce kadai ta rage sai kuma ta Aba..! Da sauri yace"To sakamin ta mamanmu ko ta Aba din..! Ido ta zaro kafin tace"Tabdijam..Rufamin asiri ba ruwana kaga mallam bansan ka ba sai anjuma..! Kafin yayi mgana ta wuce da Sauri harda gudu Kiran sunanta yake yana Amina..Amina ita ko Waige batayi ba sai dai ta kule ya Daina ganinta sannan ya Dafe kansa. Nura ya kariso yana Fadin"Oga Oscar na Kira na fa kuma nasan kai yake nema..Sannan ka koma mota kafin mutane su farga Dakai..! Lokaci Daya yana mikamai katin Daya siyo Airtel na 1k Mtn ma haka bai tsayama karba ba ya wuce Ya bude gaban wata Farar Bugatti ya shiga yana Fadin"Nura bana son mita..Kyale Oscar tukani muje kawai..! Kai ya girgiza yana mamakin Yar yarinya karama Oga ya zauna yana bata Lokaci a kanta kafin ya Zagaya ya shiga Mazaunin Direba ya Tada Motar sukar bar Layin da gudu kamar zasu tashi Sama. Koda Amina ta koma gida sai da Mamanmu tace"Amina ina kika Tsaya..? Amina tace"Mamanmu chanji ne Babu..! Da wannan karyan ta Kashe mganar Duk Surutunta ta kasa bama ko Hamida Labarin Haduwarta da Aminu buba kamar yadda yace sunansa Ranar duk in ta Tuna sai tayi Mirmishi ita kadai a kallah yau ita Amina ta samu wanda yace komai nata na Burgesa ashe itama Macece kamar kowa wannan yabon ya xauna aranta da Har Abada bazai fita ba. Ko washegari a hadda bata yarda ta Fadama ko Hanne da bata boye mata komai ta kasa bata Labarin Haduwarta da Farin mutanin da ya kasa barin Ranta Ko yaya ta Tuna dashi sai ta murmursa acikin Ranta. Da suka tashi Sallah ne Amina ta kalli Hanne suna wajen alwala Tace"Hanne ashe nima ina Burge mutane..? Hanne na kuskure baki sai da ta Furzan da ruwan bakinta kafin su hada ido da Hamida suka kwashe mata da Dariya Duka Amina ta Dirkama Hanne a baya tana Fadin"Bana son iskanci ban tambayi Hamida ba sanin Halinta yar bakin ciki ce.! Hanne na Dafe inda ta Daketa tana Fadin"Muguwa..Uban wa zaki Burge..? Hamida ta Karbe da cewa"Sai dai ki Gunduri mutane Jidalinki Amina wlh bamai iya Daukansa sai mu da muka Saba..! Hanne tace"Wlh wani waje duka zataci in taje tayi..! Dariya suke ta mata ita kuma bata su take ba Hankalinta ya tafi Tana Jin Muryan Aminu sanda yake Fadamata Tana Burgesa ita din abar Burgewa..! Daga Ranar bata kara musu mganar ba sai dai yana Ranta Lokaci bayan Lokaci yana Fado mata acikin Ranta. Har tazo Ranar Monday suka fara zuwa makaranta Sun samu Dalibai irin su da suka Cigaba da Unity sannan akwai Sabbin Dauka kamar yadda aka saba Amina ta cigaba da abunda ta saba sai ma abunda yayi gaba ta addabi Dalibai da malamai Sai kuma akayi Rashin Sa"a aka hadasu aji Daya da Sa"adatu Hanne da Hamida Ajinsu Daya. Amina kamar ta mutu saboda Bakimciki tace ma Hanne"Naso aji Daya aka hadamu hanne..Sai dai ban da Sa"a anhadani da Shegiyar Sa"adatun nan..! Hanne tace"Ina Ruwanki da ita..? Amina tace"Ta shiga Harkata Dakuwa zatayi..! Sa"adatun bata shiga Harkan Amina Saboda Anty Amarya taja kunnenta Sosai kan Amina shiyasa ko Aminar Zata takaleta bata bi ta kanta. An hadasu Aji Daya da Zainab Isa Kawar Amina sai suka Kulle atare Sit dinsu Daya Dalili kuma tana Aro mata Littafan Hausa na kishiyar mamanta take Sato musu ta kawo makaranta su karanta ita Zainab Amina take kawo mawa,ita sai agida ta ke shigewa Dakinsu ta Boye ta karanta sannan bayan su Hanne Zainab isa ta jure Gwagwarmayan Amina da Jidalinta. Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah su Amina sun mika cikin Zangon karatunsu na Farko a SS1 dinsu cikin salama da kwamciyar Hankali kamar Amina tayi sanyi Saboda ta Rage Tonon Fada sai dai jidalinta da Masifarta sai abunda yayi gaba Dakyar Hajiya ta rokar musu Baba Mallam ya bari Idi Direba yakai su gidan ya Ikram Dukkansu har da su ya Abida su Amina an sha Murna har Fada sai da taja su hanne suka shiga da karambaninta. Abida tace"Kai amina bala"i wlh watarana sai takai kanta inda zata mutu..! Ya Ikram tace ko ita sai da mijinta take shiga Gidan Sarki batama san Hanya ba sai ga Amina tana kutsa kanta Kusfa kusfa,Chan suka mata wuni sai yammah suka dawo suna Santin Haduwar gidan kamar aturai Amina tace"gaskiya gida biyu suka tabamin kyau..Daga gidan ya Danmallam sai gidan ya ikram..! Hamida tace"Gaskiya gidansa shima ya Hadu tsarin daidai kamar aturai..! Haka dai sukayi ta santin gidan Har Mamanmu na saka baki tana basu Labarin Tsaruwan gidan Sadiya Dake Dutse Amina tabe baki tayi batayi mgana ba sai da Hamida tace"Kai zan so naje ngani mamanmu..! Yaya na gefe tace"Naji kamar ance cikin watan man zata bi mijin chan kasar Dayake aiki..! Mamanmu tace"Nima haka naji Haj.Nasara na tadin ita da Haj.Uwa..! Amina tace"Ni kam ban sha"awar zuwa..Nasan bazai kai yadda nake Hasaahe tsaruwa ba..Shiyasa naga yau Sa"adatu nata wani yamutsa Fuska araina nace an ga inda aka fi su..! Hamida tace"Kai Amina baki son zaman lafiya..? Balla mata Harara tayi kafin tace"Eh din ke kuma an tabo masoyiyarki..! Ganin zasu fara fadan nasu ne mamanmu ta Tsawarta Ya Zeenatu na Gefen Yaya tace"ZAman lafiya ko na Minti Daya ne Amina bata kaunarsa..! Amina na jinta ta Daga kanta sama aranta tana Fadin"Eh din..! Nan dai mganar tatashi ta koma Tsakanin su Mamammu da su Hamida Amina bata kara saka baki ba Kada tata ta karayin zafi. Ana cikin haka acikin Satin Matar ya Jafar ta Haihu Anty Shamsiya. Su Amina Sai ana gobe suna suka samu zuwa barka shima din su Yaya da su Hajiya sukabi da zasu barka mamanmu ita ke zuwa tana Ma jariri wanka wanda yaci sunan Baba Mallam Suna zaune Jaririn na Hannun Hanne Amina ta karkato tana Fadin"Wlh bakinsa Sak na uwar ne..! Hanne ta Zunkuleta tana Fadin"Ba Ruwana Amina..kada taji.! Amina na Danne Dariyanta ta Dago tana Fadin"Mamanmu kalli jaririn nan yana karami bakinsa babba..! Hamida da Hanne da suka san mganar suka yi tsumu tsumi. Hajiya Uwa ce tace"Banda abunki Amina ai jariri ne yana girma zai Sauya..! Mamanmu tace"Mai sunan mallam fa Shamsiya ce Sak..Kila sai nan gaba zamu ga Jafaru..! Akayi Dariya Shamsiyan na gefe batace komai Amina nata Dariya sai da suka fito zasu tafi Hamida ta jawota Tana fadin"Amina wlh ki bari ba kyau kushe hallitar Allah..! Hanne tace"Kuma bata san me zata haifa ba! Amina ta toshe kunnenta tayi gaba Tana Fadin"Nagode da wa"azi Malama Hamida da malama Hanne..! Kyaleta sukayi ganin bazataji ba Washegari sun so su koma Mamanmu tahanasu tunda ya Jafar din yace ba suna ba Taro an dai yanka Raguna Mallam yaje yayi barka da kansa. Ranar kwatsam sun je makaranta sai ga Zainab tazo da karamar waya Tecno mai memory,Tsohuwar ta Anty ta ce aka bata akwai Memory aciki ita Amina waya ba Damunta tayi ba Shiyasa bata Damu ba Acikin yan ajinsu akwai masu waya Ranar an tashi Break Taji Zainab na ma wata Saratun ajinsu mganar ta Turamata Sabbin Wakoki Tana Daga sit dinsu tana karatun Wani Littafin da Zainab ta aro mata mai suna Yar Jagora. Duk da kunnenta baya wajen taji Sunan Radau acikin kanta. Saratu ta kalli Zainab tana Fadin"Ni ban da wasu wakoki Zainab..Sai dai ina da Sabbin wakokin AMINU buba Da yayi kwanan in kina so sai na Tura miki..! Kamar a mafarki taji ankira sunan ta Taba jin sunan ta kuma Haddace sunan acikin kanta. Da Zumudi a Murnan Zainab tace"Yauwa don Allah sakamin..Ina son wakokinsa..! Daga sama kawai suka ga Amina Sanda ta Dafa Saratu tana Fadin"Wani Aminu Buban..? Da mamaki suke Binta da kallo kafin Zainab tace"Mawaki ne mai Tashe Amina..! Ido ta zaro kafin tace"Da gaake..?kina da Hotonsa..? Zainab cikin mamaki tace"Hotonsa kuma..?a"a ni bani dashi wakokinsa kawai nakeji shima a wayar ya Kamal nasansu..! Saratu ce tace"Yayata nadashi in kina son ganinsa ki bari gobe zan turo miki..! Da sauri Amina tace"Yauwa don Allah ki turomin akwai wani dana sani ne in so nagani ko shi ne..! Da mganarta suka yarda da ita Washegari kuwa suna zuwa makaranta Saratu tace ma Amina ta Turo Hoton a wayarta Vivo Lokacin da Amina ta ga Hoton sai da Gabanta ya Fadi. Yana Sanye cikin Riga da wando Ja da Fari Wandon Ja ne Rigar ciki Fara sai Jaker dinsa ja Takalmin kafarsa Booth ne fari haka ma Facing cap din Kansa Ja ne mai Kalan Fari yayi Tsayuwar matasan wannan zamanin Fararan Hakoransa mai Wushirya duka suna waje a kasan Hoton an sanya A.A BUBA..! Sai alokacin Amina ta tuna yana ta Nanata mata bata sanshi ba..?Ashe cele ne shi to ita ina zata sanshi..? Ba waka suke ji ba ballatana kallo. Saratu ta karbi Wayarta tana kallon Amina Zainab isa ce tace"Shine..? Sai ta samu kanta da girgirza kanta Saratu tace"Kila suna ne yazo Daya..Shi wannan Aminu Aliyu Buba sunansa mawaki ne mai tashe yadda naji ana Fada bai Dade ba sunansa yayi Fice..! Amina na jinsu batace komai ba Zainab ce ta karba tana ganin Hoton kafin tace"Kyakyawa dashi kamar Bafullatani..! Saratu tace"Ance Bafulatanin Yola ne..Karatu ya kawosa kano..ya fada Harkan waka..! Amina ita Daga Lokacin batama jinsu Tana chan Tana Mirmishi Lalle Amina mai Sa"a ce yau ga Wanda Duniya ta sani ya Taba cewa tana Burgesa anya in ta Fadama Mutane zasu yarda da ita..? Taso gaban irin su Sa"adatu ne ta tabbata sai Haushi ya kashesu ita Kadai kawai in ta Tuna A.A Buba ranta sai yayi Fari kanta ya kara Girma Ho..Sai ita Amina Aminene Manya kasa..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo (Besty) Alherin Allah ya kai miki duk inda kike* *🅿️16* *Yola..* BAYAN WANI LOKACI..! Kwata kwata bai ji kiran sunansa da take yi ba sai da ta Daddage ta Dirkamai Duka a gadon bayansa kana ya dawo cikin Hayyacinsa Dago Shanyayyun Idanuwansa yayi ya zube akanta cikin kosawa yace"Haba Nenne..! Haba..! Ya ke fada yana sosa bayansa Hannu ta kai zata kara Dukansa ya mike Tsaye da Sauri yana Fadin"Haba mana Nenne..! Wannan ai cin zali ne..! Tana Hararansa tace"Awa na nawa a Tsaye akan ka ina ta mgana baka ji ba..? Anya Aminu wani abu baya Damunka..? Tun shekaranjiya da ka iso nake ganinka cikin Zurfin Tunani ko Mtsalan wajen aikin naku ne..? Bayansa yake sosawa kafin yace"Shine Zaki Saki karfin da Allah yayi miki ki Dake ne..? Haka ake yi Nenne..? Kunnensa take neman taja ya matsa yana Dariya yace"Tsaya..Tsaya..Wlh hannunki kamar na maza saboda zafi..Nenne akwai karfi..! Kinsan mu Jikinmj mai Laushi ne Nenne zata yi kisan kai..! Yana yi yana Dariya itama Dariyan take Farar mace ce,kamar sa sai dai itama bata da wani Tsawo kamarsa Suna da Diban kama ta Hasken Fatarsa ba wata babba bace domin Iyakarta wajen Shekaru arba"in da wani abu. Ganin ya shagala yana Dariya yasa ta Shamacesa ta Murdo Wuyansa yar kara ya saki yana Fadin"Wayyo Allah..Jama"a Haba Nenne zaki karyamin wuya ne..? Cikin Fada tace"Ka maidani kakar ka ko Aminu..? Ga Breakfast dinka chan tun dazu har yayi sanyi kana zaune tunda ka zauna sai faman Tunani kake yi..! Da sauri yace"To naji Sake ni in miki Bayani..! Sakinsa tayi kafin ya juyo Kafadanta ya Dafa yana Fadin"To banda abunki Nenne duk duniya wa nake dashi bayan ke..?kece uwata kece Ubana, kuma kece kakata..Dole nayi wasa dake..! Mirmishi ta saki kafin taja Hancinsa tana Fadin"Nima bani da kowa sai kai..Kasani ko..? Yana yar dariya yace"Sai kuma Sabuwar suruka in na kawo miki..! Baki ta washe gabadaya tana Fadin"Aminu da gaske kake..? Innalillahi a ina take..? Ganin yadda ta Rude ne yasa yace mata"Nenne..Haba..Nace in na samo miki Suruka bawai na riga na samu bane..! Duka taso Dirkamai ya Zura da gudu zuwa Bangaransa yana Dariya itama Dariyan take Lokaci Daya tana Fadin"Zaka zo ka sameni karyan Tsiya kake..! A tsakiyar kayattacen Dakinsa ya Tsaya Kafafuwansa ya Nitse kan Tattausan Cafet din Daya malale Falon,Hannunsa Duka ya saka saman kansa yana Birkita gashin kan nasa meke Faruwa dashi..? Yarinya karama taki barin Tunaninsa Tun sanda ya baro Dutse ko da rana Daya bai iya mantawa da ita ba a dukkan abunda yake yi Tunaninta da yanayinta da mganarta suna Gilma masa ya Dauka da gaske mganarta da Tsiwarta ke Burgesa sai dai yanzu da Lokaci ya tafi abun bai sauya ba. Duk Yanmata hadaddun Da suke Rubibi akansa bai ga wacce ta kasa barin Tunaninsa ba Irin Amina Yazo Yola gida ne domin ya Huta na kwana Biyu ammh tunda yazo bai da aiki sai Tunani ko yaso ya kaucema abun ya kasa bai kara Tabbatar da ba iya Burgesa yarinyar take yi ba Harda wani abu Dayake jansa wanda bai gama Sanin koma Miye ba,sai da yazo gida. Abu Daya ya sani zai Nemota kusa dashi Domin ya samu Tabbacin Burgesa take yi ko kuma wani abu ne Daban wanda baisani ba. Da wannan Tunanin ya karisa samam makeken Gadon Dake dakin ya Dauko Farar wayarsa Kirar Samsumg. Nura yaronsa ya Doka ma kira da Sanyin Safiya sai da ma ya Kira ya Duba Lokaci 10:00am na Safe tun motsa jikin Daya fita ya Dawo ya shiga Dakin Nenne suka gaisa yazo Falo ya zauna ya shiga Tunani Tunanin yarinya karama wacce Bai taba Tsamannin zai taba Haduwa da ita ba. Sai da yayi ma Nura Kira Biyu sannan ya Daga kiran cikin Alamun barci yace"Oga Lafiya kuwa..? Karamin Tsaki yaja kafin yace"Bansani ba..Dillah mallam ka wartsake..Wani aiki zan saka ka..! Da sauri Nura yace"Afuwan Oga ina Sauraranka..! Sai da ya gyara Tsayuwa kafin yace"Yarinyar da muka Hadu da ita kwanaki..Nake son kafin nan da zuwa Dare in ji komai akanta in nace komai ina Nufin komai..! Cikin Mamaki Nura Dagachan bangaran yace"Wata yarinya kenan Oga..!? Cikin Bacin rai yace"Bansan yawan Tambaya kasani Nura..! Shuru yayi mai domin bai gane wata yarinya ba Yanmatan ai suna da yawa ganin yayi shuru yasa yace"Ina yarinyar nan da muka hadu da ita a Dutse..Oh..Ba Dutse ba yama sunan garin da mukaje Shooting din wakar nan Last Month..! Nura yace"Munje Hadejiya da Gumel sai Jigawa wanne Daga ciki..? Aminu yace"Inaga Gumel ne in da muka Tsaya Shago siyan kati har naci karo da wata yarinya wata baka mai ido mai mgana tana da Tsiwa haka..! Baki Nura ya Hamgame yana jin Ogansa mamaki duk ya cikasa Cikin mamaki yace"Wannan yarinyar Oga..? Karama ce fa..! Da sauri yace"Ina Ruwanka..Do as i say..in bazakayi ba zan kira T..! Da Sauri yace"Zan yi..Zan yi..! Bai jira cewarsa ba ya Datse kiran yana Fadin"Nura yana da matsala...! Haka ya fada kafin yayi Cilli da wayar saman gado ya taka cikin Sassarfa ya Shiga Tiolet din Dake Cikin Bedroom din. Aminu Aliyu Buba Haifaffan garin Yola ne Bafullatani ne ta bangaran uwa dana Uba,mahaifinsa da Mahaifiyarsa hatsarin mota sukayi suka rasu tun yana da shekara Goma aduniya kuma shi kadai suka Haifa karamar kanwarsa tun kafin ayayeta Ciwon kyanda ya zama ajalinta. Sai Rikonsa ya koma Hannun kakarsa wacce ta Haifi Mahaifiyarsa,mahaifiyarsa tana da Tarin kannen da yayyi wadanda suke Uba Daya tunda alokacin matan babansu Hudu Aisha itace Wacce suka Fito Ciki Daya ita da mahaifiyarsa kuma Allah ya Doramata Kaunar Aminu tun sanda aka Haifesa yana karamin sa yana da kyau da kwarjini irin nasu na yara. Sadaukarwan da Aisha tayi ma Aminu mai girmane wanda baki bazai iya Fadi ba saboda shi tayi aure aure har Hudu baata zauna ba Saboda duk inda Tayi aure sai tace da Aminu xata tafi wanda yake kamar kani gareta yana da Jikin girma yasa ya kamota ita kuma gata Daman bata da tsawo. Yawancin Rayuwarsu a Yola sukayi an gaji da Mgana an kyale Aisha Domin tace matukar ba zata zauna da Aminu ba sai dai ta Hakura da aure da Kuruciyarta ta zauna agida tana kula da Aminu ta zamemai uwa da uba da yar"uwa shima komai ya samu itace Dalilinsa ta samu Sunan Nenne sunan Daya Bita kowa dashi yake Kiranta. Kakkaninshi suka taimakamai yayi karati har matakin Secondary Nenne iyakarta Diploma bata cigaba ba Lokacin shiga Jami"a sai Aminu ya nuna kano yake son tafiya ba gaddama aka kai mai Cuku cuku ya tafi Tunda bayan ma haka Mahaifinsa Alhaji Buba ya mutu ya barmai Tarin kaddarori gidaje da Filaye. Zuwansa kano ne mafarin fara wakarsa ammh bai taba Tsammanin ba Haduwarsa da wani abokinsa Oscar shima mawaki ne,Dakinsu Daya shima anan Buk din yake karatu Cikin ikon Allah kuma yana da Rabo acikin Harka cikin Lokaci sunansa ya fita bai samu matsala da kowa ba sai Nenne itace ta nuna tafi son ya maida Hankali a karatu ammh itama sai da yaja Ra"ayinta ta amince. Kafin ya gama Jami"a Sunansa ya fita waka ta karbesa kuma ya samu Alherai da ita ba adadi yanzu haka yana cikin mawakan da Yan Film suke Damawa dashi Tun shekaru Biyu da suka gabata yana kasuwancin shigo da Motoci da karafuna Da kudin gadon Daya gada sannan yana da Shagon sai da gwala gwalai anan garin kano. Yayi gida anan kano nashi na kanshi yaso ya Dauko Nenne su dawo Alhaji Babba yahana yace ba inda zai kaita Shiyasa ya gina mata gida kato shi da ita Ya Daukota suna zaune tare daga ita sai yan aiki da ya"yan yan"uwan tunda Duka auran duk da tayi bata zauna ba ballatana ta Haihu Aminu ne komai nata shima itace Duka Duniyarsa babu abunda bai ijiye mata na jin Dadin Rayuwa ba Domin komai ya Zama a wannan Duniyar itace Kan gaba. Yafi zama a kano saboda Harkokinsa,Sai kuma garuruwan da suke zuwa in zasu shooting din waka Aminu baya shaye shaye kuma baya Harkan mata sai abunda ba"a rasa ba Matashi ne dan kimamin shekara 30 aduniya ne mai ji da kuruciya da kudi Yanmata sun na kawo masa hari ammh bai taba maida kai ba Nenne ma ta matsamai yayi aure ita da Alhaji Babba ammh suma baya maida kai sai yace Lokaci ne bai yi ba Yana so yayi aure saboda Farincikin Nenne sai dai bai sa nan kusa ba Domin bai Taba jin wata mace aransa ba yasan suna sonshi ne saboda suna da kuma Kudi ammh Haduwarsa da Amina komai ya Sauya yasani yarinya ce ammh kuma Rayuwarta Cikin Burgewa Bata da damuwar komai ashekarunta kudi ko suna basu da Muhimmanci awajenta Har ya fito wanka Tunanin bai bar kansa ba yana son jin komai akanta Saboda yaga ta ina zai fara yana son ya kara ganinta nan kusa komawa Gumel ya kamasa Duk da wannan ne Lokaci na farko daya taba zuwa garin Agurguje ya shirya cikin manyan kaya cikin gari zai shiga ya gaida Alhaji Babba kuma in ya je da kananun kaya Daga shi har Hajja sai sun tasomai Shiyasa yayi shigar Farar shadda riga da wando da Hula. Daga Dakinsa kai Tsaye Dakin Nenne ya Nufa ya isketa tana gyara adon wata Sarkarta,bataji ma shigowarsa ba sai Hannunsa dataji ya saka ya karbi Sarkan yana Fadin"muga Abun da Nenneta take yi da bataji shigowata ba..! Sai Lokacon ta Dago tana kallonsa Cikin Farimciki tace"Masha Allah..Ka ganka kuwa..?kamar bakai ba..Hala gidan Alhaji babba zaka je ko..? Kai ya gyada mata yana Kokarin gyara mata sarkar lokaci Daya yana Fadin'Kina son sarkan nan Nenne..! Hannu ta mikamai Tana Fadin"Sosai..Bani kayana kagani sakashi zan yi..! Bai musa ba ya zagaya ta bayanta ya saka mata yana Fadin"Ko zaki shirya muje tare ne..? Kai ta girgiza kafin tace"Ina da Bakuwa..Hajiya Iklima ta kirani tacemin zata zo kada mu fita tazo bata sameni ba..! Dan baki ya tabe kafin yace"Ok..Bari na wuce ni..Sai an juma zan dawo domin zanshiga cikin gari mu gaisa da Friends dina mun kwana Biyu bamu Hadu ba..! Kai ta gyadamai kafin tace"Shikenan kada kayi Dare..Sannan ina Fatan ka Karya..? Da sauri ya gyada mata kai Saboda baya son ta takuramai kuma bayajin cin komai Dukawa yayi ya Sumbaci kuncinta kafin ya Fice da Sauri Ta Bisa da gudu tana Fadin"Aminu zan ci maka mutumci da Dabi"ar nan fa..! Tana jinsa yana Dariya yana Fadin"Haba Nenne watarana fa Madina zamu koma Dole mu koyi gaisuwan Larabawa..! Mirmishi take ita kadai Burinta ya gama cika Saura abu Daya Aminu ya samu matar aure ta gari taga ya"yansa shine Babban Muradinta. Ranar Wuni yayi zirga Zirga achan gidan kakanin nashi ma Chaa akayi mai kan mganar auran kansa Kadai yake shafawa yana fadin Lokaci ne bai yi ba ko abokansa na nan Yola suna ta mai tsiya domin su kam daga masu yara sai masu kokarin Karin ta Biyu. Bai shigo gidan ba sai bayan Isha"i shima sai da Nenne ta kirasa haka take Koda ya girma tana Tsaye kan Tarbiyasa ko yana kano Dare nayi zata Kira taji inda yake tana tsoron Gurbacewar Tarbiyan Matasan zamani akan Aminunta Tare sukayi Dinner shi da ita da Wasu yan Biyu Hassana da Husaina ya"yan kawartace Hajiya Iklima ta bar mata su kwana Biyu tunda suna Hutun makaranta Daman suna zuwa Aminu ya saba da yaran suna da shiga rai su suka Daukemai Hankali ya manta da Batun kiran Nura sai da yaga Kiransa wajeb karfe Tara na Dare sannan ya Tuna. Sabewa yayi ya koma Dakinsa baya so Nenne ta Fahimci komai yasanta yasan Zuciyarta yanzu sai ta Girmama abun Fiye da yadda yayi tsammani kiran ya katse sai kara kiran Nuran yayi yana Dagawa yace"Nura kada ka sanar dani sabanin abunda na saka ka..! Ajiyar zuciya Nura ya sauke kafin yace"Tun bayan da muka gama waya Na shirya na tafi Gumel Oga..Ban sha wahala sosai ba Saboda gidansu yarinya ba Boyayyen gida bane..Gida ne da ko kai na Fadama sunan zaka san sunan..! Cikin Mamaki Aminu yace"Wani suna kenan..? Kai Tsaye Nura yace"yarinyar tana Daga cikin Ahalin babban Malamin nan Sheick Yunus Abdulrahaman bazanga..! Aminu yace"Sheik Yunus Abdurrahaman Bazanga..? Nura ya gyada kai kamar yana ganinsa kafin yace"Eh shi Oga...! Aminu ya jinjina kai ai ba wanda baisan Mallam bazanga ba in baka sanshi a Fuska ido da ido ba kasanshi a Talabijin ko ajaridu ko kuma awajen wani Taro na Malaman sunna. Cikin Kosawa yace"Ina jinka..yarsa ce ko Jikarsa..? Nura yace"Shine bansani ba..Ban samu Cikakken bayanin Dangantar Mahaifinta da shi Mallam bazanga ba..Sai dai an bani Tabbacin kamar D'a yake garesa gidajensu suna jikin juna ne nan bayan inda muka hadu da yarinyar sannan Mahaifinta ne kan Duka kasuwancin Mallam din..Sannan iyalansu a Hade suke komai Tare suke Hatta Ragamar aurar dasu Mallam din ke gudanar da komai wasu suna Tunanin kanin sa ne wasu kuma suna Tunanin Shine Babbar D'ansa..! Aminu yace"Naji wannan ita yarinyar fa..?me ka sani akanta..? Nura yace"sunanta Amina Sa"idu Yarinya ce karama Tana aji Dayan babban Sakandiri yanzu a makaranta tana zuwa Hadda da Islamiya,Dokar gidan gaskiya yadda na samu Labari gidan Tarbiya ne basa fita Daga makaranta sai gida sannan basa Tadi da Samari ko auransu ana Tunanin auran Hadi ne sannan iyakarsu Sakandiri ake aurar dasu, su goma sha Daya ne agidansu itace Karama awajen Mahaifiyarta sannan matan babanta biyu..! Aminu ya sauke Numfashi kafin yace"Yanzu ba yadda zan yi na kara ganinta..? Nura yace"Ba mafita. domin ko makaramta Mota ke kai su ya dawo dasu..Mai bani Labarin ma yayi matukar mamakin Da nace masa mun ganta ya Tabbatrmin da Ahalin gida basa zuwa ko"ina..! Aminu ya sauke Numfashi kafin yace"Ya zama Dole na Hadu da ita..Gobe zan shigo kano..ka shirya zamu koma Gumel..! Daga haka ya Datse kiran ya bar Nura bakinsa Bude meke Damun AA.buba ne..? Wannam yarinya zai kare mawa duk matsayinsa..?Tsaki yaja acikin ransa yana kunkunin yadda Aminun yasa shi zuwa gumel ayau din nan Allah yasa Bawani sha wahala ba Tunda ba Boyayyen gida bane, shagon da suka fara haduwa ya fara isa Daya tambayesa ya tabbatarmai shima bai santa ba wani ne a kusa Dayaji Mganar da sunanta da yanayinta yace ya santa kanwar abokin kaninsa ne Shamsu ya"yan gidan Bazanga ne a bakinsa ya samu Duka Labaran Daya zo ya Fesa ma Aminu dawowarsa kenan ko Hutawa bai yi ba.. Indai ko Oga son yarinyar yake ya kwafsa yar yarinya yar cikinsa bakomai Cikinta sai rashin kunya. Aminu kuwa yana ji aransa ya zama Dole ya koma ya sake ganin Amina Saibyanzu ya kara tabbatar ma kansa bata sanshi ba gidan Malamai ba"a wani samun sakewa ballatana Har taji waka ko tasab sunanshi. Yana ji ajikinsa kamar akwai wani abu mai girma Tsakaninsa da yarinyar bazai gane haka ba sai yaje ya kara ganinta ya kara tabbatar da abunda yake ji akanta. ******** *BAYAN SATI DAYA..!* Gumel...! "Wlh in na yarda Allah Tsinan..Kin manta jiya ma da muka dawo agidanku na sauka kenan yau gidannmu zaki sauka yarinya..! Amina ta fada tana Faman Jan hijabin Hanne Hamida na gefe tana musu Dariya dukkansu kayan makaranta ne ajikinsu da Uban jakunkuna Hanne Fadi take"Sakeni Amina..Nace ne bazani ba..? Amina tace"In sake ki ki shige gida..?naki wayon..?Hamida karbe jakarta.. Hamida ta warce Jakar makarantar Hanne Tana Dariya ya Zeenatu tazo shigewa gida da Katuwar jakarta Sabe a Hannu ta bisu da kallo kafin ta Tabe baki tana Fadin"Miye haka..? Kudai bazaku bar yarinta ba..Kuna girma kullum kuna cin kasa..! Baki Amina Ta tura batayi mgana ba Hamida ce tace"Ba ruwana Amina ce..! Karamin Tsaki taja ta shige gida Abunta ya Abida ce Daga nesa ta hangosu kusan itace Karshen sauka Daga Motar,yau a waje idi ya saukesu motar ba Lafiya Dakyar ta kawo su gida gareji yace zai kaita shiyasa ya Saukesu anan waje su Sa"adatu tuni sun shige gida abunsu su Ya Akilu ne ke wajen jikin Motan. Abida ta kalli Zubairu tana Fadin"Kalli yaran chan..? Akilu yace"Bari na Tarkatasu su shige gida..! Yafada yana Daukan Sanda ya fara Tafiya yana Fadin"Ya shamsu..Eh gasu nan suna wasan banza a waje..! Kamar sun ga Shamsu da gaske suka Zura aguje su kuma suka kwashe musu Dadariya Abida ta shige get din gidansu ita da Zubairu Akilu yabi bayansu,su Amina suka Tsaya suna maida Numfashi Amina tace"Wlh Ya Akilun nan mugun dan saka ido ne..! Hamida tace"So yake ya zama makwafin ya shamsu tunda shi ya gama..! Akwai son yayi Displine..! Amina tace"Barni dashi Watarana zamu yi mganinsa ne..! Hanne tace"Badai kararara zaki sakamai ba irin na ya Shamsu..!? Atare suka Saka Dariya Tuna abunda ya Faru wanchan satin Amina ta samo kaikayi a makarantar Islamiyansu taji su mariya na Fadin abun na saka kaikayi ta tsinko ta Dinga tusama Mutane Cikin Hijabi a ajinsu suna ta Soshe soshe,Shine ta sakama Shamsu Saboda ya Rankwashesu ita da Hanne basu gama Rubutu da wuri ba har aka tashi sun bata musu Lokaci shine suka Fakaicesa da Daddare Amina taja Hanne sukaje suka Watsamai akan Katifarsa da Safe suna Daki sukaji Hajiya na Fadin shamsu wani abu ya Sameshi jiya da Daddare kwana yayi susa da wanka sai da mallam ya dinga mai addu"a. Sai da Amina ta kwanta Saboda Dariya Hamida ma bata sani ba Labari Hanne ta bata. Amina na Dariya tace"Ai mallam Auwal ya saka an sare Ganyen mai kaikayin..! Hamida tace"Ina Fatan kada ya Shamsu yaji Wlh sai na Lahira yafiki jin Dadin Amina..! Hararanta Amina tayi kafin tace"To in ma yaji wlh ke kika fada! Hamida tace"Ni kuma..? Amina ta Bude baki zatayi mgana keman Idonta ya Fada kansa yana Tsaye Daga Kofar gidansu bai yadda sun kariso da Motarsu ba Tana baya Nura ke ciki yana kallon Ikon Allah Sun fi awa Daya suna wajen nan agaban idonsu Motan makaranta tazo ta Sauke su Amina suka Firfito. Ko alama bata manta dashi ba gani su Hamida sukayi hankalinta ya koma Chan gabansu yasa suka juya suna kallonsa yana Tsaye sanye Cikin Riga da wamdo bakake sai ya Dora Farar Jaket ya saka F.cap ya Rufe Fuskarsa sai dai ya Janyeta kadan. Amina cikin mamaki tace"Laaa..Kai ne..!? Mirmishi ya sakar mata kafin yace"Nine..Amina kina Burgeni..! Fadin haka da yayi yasa ta washe baki ta fara takawa gabansa shima ya tako suka Tsaya daidai kofar gidansu Amina Hamida da Hanne suka saki baki suna kallonsu. Amina Hannu ta Fara tafawa tana Fadin"Kai..Daman ina neman ka..?Ashe kai mawaki ne bansani ba..? Ido ya zaro yana kallonta kafin yace"A ina kikaji..!? Kai Tsaye Amina tace"A wayar wata yar ajinmu mana..naji suna mgana suka ambaci mai irin sunanka nace anunamin Hotonka kuma Wlh kai ne..Yauwa daman ina ta so na Fada ma su hanne don Allah ba kai kace ina Burgeka ba..? Kallonta kawai yake yi yanjin wani Farinciki sai da ya ganta ya kara ganin yarintarta tana mgana ko Tsayawa ta kasa yi. Kai ya gyada mata yana kallonta juyawa tayi ta riko hannun Hanne da Hamida ta kawo gabanshi tana Fadin"Yauwa don Allah sake fada musu..Kila su yarda..! Tafada tana wani juya ido Dariya abun ya basa cikin gyara Tsayuwarsa yace"Amina Kina Burgenii..Wani ya Taba Fada miki u are so Beautifull..! Amina taji wani Sanyi acikin ranta Cikin Alhafari ta kalli su Hanne da mamaki ya sa suka kasa mgana tace"Kun ji ko..?ai in na Fada muku sai kuce Karya nake..Nima fa ina Burge mutane Kunga wannan babban mawaki ne yana tare dasu Umar.m sharif..! Dasu Ani nihu kasan su ko kilama abokan ka ne..? Take Fada tana kallonsa Cikin Dariyarta Kai ya gyada mata Cikin Dariyarta yace"Ai Ani nuhu abokina ne..yama ce yana gaisheki..! Ido ta zaro kafin tace"Da gaske.? Ya sanni ne..? Yana Danne Dariyansa yace"Sosai ai yasan Amina..Amina ta Gumel abakin Aminu..! Amina ta Dafe kirji Murna Duk ya Cikata Hanne taja gefen Hijabinta tana Fadin"AMINA kada wani ya fito fa ya ganmu fa.? Hamida kuwa uwar tsoro sai waige take yi kafin tace"Amina kin sanshi ne..? Hijabinta ta Fizge kafin tace"Dillah..ku na sanshi fa..Shagon chan muka hadu kwanaki da mamanmu ta aikeni..! Har yace ina Burgesa ko..? Tafada tana wani juya ido Kai ya gyada yana kallonsu Hamida kafin yace"Sosaima gaskiya kuma Laifin ku ne da baku taba Fada mata ita din abar Burgewa bace! Amina ta washe baki kafin tace"Kun ji ko..?yauwa gayamusu..Ni da suke cemin ina naga abun burgewa Sai ma na gundiri mutane da Halina..! Tafada tana bata Fuska da Sauri yace"Kada ki damu..Ni kina Burgeni..! Hamida taga Amina ta Zake da yawa hannunta ta Fincika tana Fadin"Amina kada wani ya ganmu fa..? Hanne tace"Bawan Allah don Allah ka tafi jidalin Amina ne kawai..In wani cikin yan gidanmu ya ganmu Dakai yau mun shiga uku..! Amina ta kwace hanmunta tana Fadin"Dillah sai me..?iyaka duka ne kuma baya kisa..! Hanne tace"Baba Mallam kinsan baya nan bamu da maceci sai Allah Amina..! Wa kika taba ganin ya tsaya da wani..?ko su ya Abida kin taba gani..? Amina ki shiga Hankalinki..! Sai kuma tayi shuru ta tsaya tana kallon Hanne kafin tace"Kuma fa hakane..muje..bawan Allah sai an juma..Yauwa don Allah ka kara gaida min Ani nihu..! Hamida tace"A ina kikasan Ali nuhu mu da ba kallo muke yi ba..? Amina tace"Dillah Ani nihun ne baki sani ba..?dan wasam hausa fa ki bari gobe zan nuna miki hotonsa a bakin Unity ashagon nan ma kusa da shagon Bola gasu nan kala kala! In Tana mgana Nishadi ke kamasa Shiyasa ya shagala yana kallonta baisan sun wuce ba suna gabda Shiga gidan ya Daga Muryansa ya Kirata. Amina..! Dukkamsu suka juyo suna kallonsa Cikin wani yanayi yana kallonta yace"Wlh da gaske nake yi kina Burgeni... Sannan KUma..INA SON KI..! DAM!! dukkansu gabansu ya Fadi Amina ta zaro ido ya sake Daga mata kai kafin yace"Wlh da gaske nake ina sonki.! Zan dawo ki jirani..! Yafada yana kallomta Hanne da Hamida ta kallah kamar sun ga abun Tsoro suka Rumtuma suka shige gidan da gudu kai ya girgiza kafin ya Furta"Finally dai na gano abunda ke Damuna Son yarinyar nan nake yi..! Daga haka yajuya ya fara Tafiya wajen Mota Nura na ganin haka ya Tuko motar zuwa gabansa da azama ya Budamai gaban Motar ya shiga ya maida ya Rufe suka fara barin anguwan ammh Idanuwam Aminu na kallon Kofar gidansu Amina kamar tatafi da ransa Nura na binsa da kallonn Tsausayi. Nura ya kada kai kafin yace"Ina muka Nufa Oga..? Idanuwaansa na shigewa kamar mai barci yace"Mu koma Hotel..Nura son yarinyar nan nake yi..Bazan koma kano ba sai na samu Soyayyarta..! Nura yace"Ta wata hanya..? Dokar gidansu ce ba sa soyayya kuma na Fada maka..! Bai damu ba kai Tsaye yace"Koma ta wata hanya ce zan sakata ta soni In ta soni komai mai sauki ne..! Nura ya kasa mgana ya fara Tunanin Amina mayyace ta kama Ogansa. Su kuma su Amina a haraban gidan sukaci Burki suka tsaya suna maida Numfashi. Hamida tace"Amina mutumin nan bai da Hankali ammh ko..!? Hanne tace"Ke ina ga wasa yake mata..! Duk Amina na jinsu karo na Farko yau aka taba cewa ana sonta acikin Idanuwaan Aminu gaskiya ta gani ita kanta Zuciyarta ta kasa Fassara yanayinta yasa ta Biye ma su Hamida da Fadin"Bai da hankali..Inaga bai da hankali..! Kai suka gyadata mata atare suka Furta"Gaskiya bai da hankali..! Da haka suka watsar da mganar sukanufi Cikim gida Ammh banda Amina ta kasa goge Kalaman Aminu ko wani juyi tayi acikin Ranta sai taji muryansa. Amina..Kina Burgeni..Kuma WLH INA SONKI.! Batasan Dalili ba taji abun ya zauna acikin ranta sannan tana ji tana so ta kara ganinsa taga wannan Gaskiyan Data gani acikin idonsa..! Mafarin komai...! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️17* Da gaske yake yi Duk abunda ya fito Daga cikin zuciyarsa bai gasgasta haka ba sai da ya koma kano ya kasa zama kwana uku yayi ya saka Nura ya Tukosa zuwa Gumel,batare da Amina ta sani ba yake Bibiyanta ahotel yake zama In garin Allah ya waye zai zo kofar gidansu Amina Daga baya domin yaga tafiyarsu makaranta da Lokacin dawowarsu da Lokacin Tafiyarsu islamiya wasa wasa sai da yasan komai na Amina sannan yana Bibiyan dukkan Motsinta,Batare data sani ba Nura gajiya yayi ya koma Abunsa Tunda yaga alamun Ogan nasa ya kamun da gaske. Baya sati bai shigo Gumel ba,Duk saboda Amina zai zo ya ganta yaji Sanyi aransa koda bata gansa ba koda bata sani ba ya gama yardan ma kansa Amina ta shiga ransa ta samu matsugunnun da bai zai iya cireta ba komai nata yana Burgeasa ne.. Amina bata son Aminu na binta ba Ba kuma wai don ta manta da mganarsa ba akowani Shafi na Tunaninta kalamansa bai bace mata ba sai dai Tundaga Ranar bata kara yarda sun kara mganar da Su hanne ba suma sun Dauki abun a wani abu dabam shiyasa suka watsar da mganar suka Cigaba da Harkokinsu. Bata taba katarin ganinsa ba,Sai watarana sun dawo daga islamiya,Idi bai zo Daukansu ba Motar tana ta basu matsala ya shamsu ya Tarkasu su ya Abida ne ke baya su kuma suna gaba su uku kamar koda yaushe Sa"adatu na baya tare da sabeeha da Umaima ya shamsu da su ya Akilu suna bayansu sun taso su gaba Kafa kafa Hira suke a tsakaninsu Labarin littafi Amina ke bama su Hannu kasa kasa suna Dariya sun kawo kofar masallacin Baba mallam kamar an ce ta Daga kanta sama ta Hangosa abakin Masallacin yana Tsaye cikin irin Shigarsa kamar ko yaushe da Jaket baka Baki ta saki da Hanci tana kallonsa Cikin mamaki Farinciki yaji yau daya ganta ta gansa Hannu ya Dagamata Lokaci Daya da Mirmishi. Su hanne sun juya suga me take kallo kamar ya sani ya Duka kamar yana Gyara igiyan Takalmi sai basu gansa ba Amina suka koma suna kallo kafin Hamida tace"Wa kike kallo Amina..!? Sake kallon wajen tayi sai kuma taga bashi a wajen ta fara waige waige Ya Nasir ta gani yana Daukan Buta sai ta Fara Tunanin ko gizo yake mata yasa tayi saurin cema Hamida bakomai..! Ta Dauka bashi take gani ba sai da washegari ta kara ganinsa Lokacin sun fito zasu islamiya,shima ya Ganta ya kuma mata Mirmishi gani na ukun da tayimai da Safe ne Ranar asabar zasu tafi Hadda ta fito tana jiran Hamida jikinta ya fara rawa Yana Daga Tsallaken su chan bakin wani gida Wannan karon bayan Mirmishi har sai da ya Daga mata hannu ta fara Tsorata tana Tunanin kodai ba Mutum bane Kila aljanine Datake ganinsa a ko"ina kuma ta kasa Fadama ko Hanne haka kurum bakinta yayi nauyin data gaza Furta komai. Daga Lokacin kuma duk sanda ta fito gida sai tayi waige waige ko zata gansa sai dai bata kara ganinsa ba sai ta yadda da Tunaninta kila gamo tayi da aljani. Harta da su Hamida sun fahimci kwana Biyu Amina ta rage karkasashinta da suka tambayeta sai tace bakomai basu damu ba sanin Halinta Lambo take halinta na tashi ne Lokaci bayan Lokaci kamar mai Bugawar jinnu. Bata kara ganninsa ba sai bayan Shudewar kwana Hudu tsakani ta kara ganinsa a gabda gidansu Ranar Wata Laraba sun dawo daga makaranta,Gidansu Hanne ta Tsaya sai da tayi sallar mangariba Hanne ta Rakota Mazan gidan duk suna masallaci Baba Mallan na wa"azi Har hanne ta rakota kofar gidansu suka Tsaya suna mgana yana Daga gefe basu ganshi ba har Hanne ta juya ta koma gida ita kuma ta juya zata shiga gida Taga mutum yasha gabanta. Ta firgita taso ta yanka Ihu ne sai ya Hasko hasken wayarsa lokaci Daya yana fadin"Nine..Amina..! Taji muryansa ai ta Haddaceta kamar Karatu Cikin tsoron da bata taba jiba ta fara waige akwai hasken a wajen Karo na farko taji mganar su Hamida in wani ya zo ya ganta fa..? Abu ne da bai taba Faruwa ba..! Tana ji yana Fadin"Amina kin bani Wahala..?wlh da gaske ina sonki..baki ga yadda na koma saboda ke ba...? Yake fada yana kallonta da Dukkan Zuciyarsa Jikinta ne ya fara rawa domin taji motsi tunani take ko wani ne zai fito Daga gidansu ta manta ba kowa Aba bai dawo ba kuma Ya Jafar yana masallaci wani Firgici ne ya shigeta Dayasa ta Damki hannun Aminu suka sha kwanar Dake Tsakanin gidansu gabanta ne ke Dukan uku uku kamar ta rike kaya haka tayi saurin sakinsa kafin tace"Don Allah ka daina bina..Kaga bansan ka ba..Ka daina Bibiyata kada kajamin mtsala..! Take Fada acikin idanuwanta yake ganin Tsoron wanda Daga gani tsoron ya shigeta Lokaci Daya. Cikin Gyara tsayuwarsa yace"To in na Daina Binki ni ya zanyi..? Wlh tallahi kin ji rantsuwan Musulmi ina sonki Amina sonki ya hanani zaman waje daya ki kalleni koda yaushe ina garin nan na kasa zaman Kano ballatana Yola koda yaushe korafin Nenne na ta daina gane kaina kuma Wlh duk kece Sila..! Yadda yake mganar ne yasa ta ke kallonsa acikin idanuwansa ta Hango gaskiya aciki. Sai dai ta tsorata wannan wani abu ne da bai dace yana Faruwa akanta ba Arude tace"Meyasa sai ni..?ni fa karamace akwai yayyina ga su ya Abida duk bakace su ba sai ni..? Kai Tsaye yace Mata"Ni ban sansu ba ni ke na sani..kuma ke Allah ya Saka Kaddaran haduwarmu Amina..! Amina ta zaro mai ido tana Fadin"To wlh ahir dinka da bina..Kada ka sakani Cikin mtsala in Aba ya Sani ko ya Jafar ko ya Nasir wlh kasheni zasu yi..! Ka rabu dani Amina ba kamar matar da ka sani bane yarinya ce ni ban gama karatu ba..! Da sauri yace"Nasani zan jiraki Amina da gaske nake ina sonki kuma na Rantse zan aureki..! Amina ta Dafe kirjinta tana Fadin"In wani ya sani zaka jamin bala"i daman nayi suna..Amina tayi suna ka rabu dani don Allah ban san me kake fada ba..Don Allah ka tafi ka kyakeni..! Yaji Rokonta bayaso ya ja mata matsala yasa ya ciro katinsa Daga aljihun wandonsa ya mika mata yana Fadin"Zan tafi badomin na tafin kenan ba..Zan tafi ne saboda kin Rokeni sai dai zan dawo zan rika Binki duk inda nasan zan ganki Amina banfara sonki da wasa ba Wlh..Wannan kati na ne da Lambobin wayata aciki duk sanda kikaji kina son mgana Dani ki samu waya ki kirani zan zo..! Kin karba tayi ta noke hannunta Tana Fadin"Kasheni kake so ayi in aka ganni Dakai..? Kai ya girgiza mata bai yi mgana ba illah Hannunta Daya kama ya saka mata katin kafin yace"Ba abunda zai faru..Ki sani Aminu Buba yana Tare Dake acikin kowani Bugawar Numfashinki Amina na barki Cikin Aminci..! Daga haka ko waige ya Fice Daga Kwanar Jikin Amina ya fara rawa ta Murza katin hannunta. A.A Buba tagani ajikin katin da address dinsa da jerin Lambobinsa kamar ta yardaahi sai kuma ta Fasa taji Ranta na janta data adana katin Kilan watan watarana yayi mata amfani yasa ta Dunkule katin a hannunta sai da ta leka ta Tabbatar daya tafi kana ta fito ta shige gida aharaban ta Tsaya tana maida Numfashi Cikin sikat dinta ta Boye katin bata so wani yagani bata Shiryama wannan Jidalin ba yafi karfinta wannan karon..! Cikin kayanta ta Boye katin Boyo mai Tsawon da ba wanda zai gani kuma koda wasa bata taba Fadama su Hanne ba. Bai yi karya ba Tun da karancin Shekarunta Ta Fahimci Aminu na cikin Duka bugawar Numfashinta ta Rage Walwala da yawan mgana Tun ballatana data Daina ganinsa data Kulle ido zata kwanta shi take gani da kuma Kunnuwanta na Sauraran Muryansa bata son so ba..Sai dai ta Fara Fahimtarsa a karance karancen Datakeyi sai dai tasan Shekarunta basu kai ta bama wannan a Tsarin a rayuwarta ba yanzu. Jadalin Gidansu soyayya ko manyansu basu yi ta ba ballatana ita saboda haka wannan Tunanin baya Cikin muhallinta. Su hanne da Hamida sun gaji da korafin Chanzawar Amina ranar Tana jinsu da Hanne ta shigo tana Fadama Mamanmu har yaya tana Tsakar gida alokacin Hanne take korafin sauyawar Amina. Zeenatu na wanki abakin Famfo tace"Nima na ganta kwana Biyu ba Tsiwa nace kila aljanun Salahancinta ne suka sauka..! Hamida tace"Allah Nafi son Aminar mu ta baya..Wannan shurun shurun bana sonshi..! Hanne tace"Ko ya Abida sai da tace Amina ta sauya..Sai Hajiya tace Hankali ne tayi girma yazo..! Mamanmu najinsu tace"Kwarai da gaskiyan Hajiya..Hankali da Natsuwar da'ake mata gori ne Allah ya bata yanzu..! Hamida tace"Mamanmu Amina kamar tayi gamo fa..?ko Aljanun Dare ne suka bata tsoro kinsanta da Fitan Dare ko tsoro bataji..! Ya zeenatu ta saka Dariya tana Fadin"Waya sani ko ta hadu da Cika Lora..! Gabadayansu suka saka Dariya Har Yaya Dake gyaran kubanta acikin Ranta tana Fatan Hankalin Amina ne yazo kada ace shurunta wata Tsiyar take shiryawa kamar yadda ta Saba. Amina nadaga cikin Daki tana jinsu Mirmishi tayi ta Furta"Gamo nayi Hamida..Tabbas na gamu da jidalin Danike kira ni Amina..! Satuttuka sun zo sun shude har an shiga wattani Amina bata kara Haduwa da Aminu ba,Sai abun yadan Fara Sakinta ta fara dawowa Daidai ta Fara Dawowa da walwalwarta har ya Zeenatu na fadin"Daman ai na Fada muku wanchan watan Salihan ne suka zo mata..! Lokacin baki ta Murguda mata tana Fadin"ni bani da Aljanu..! Sun saba gwara suyi mgana ta maida su ko Ya ya Amina ta sauya suna ganin Alamunta sannan in zasu fadi gaskiya basa jin Dadin ganinta asanyaye. Har ta manta dashi ranar jumma"a Bayan La"asar Mamanmu ta aiketa ta kaima Hajiya kuka da aka aiko musu dashi mai kyau Daga gusai bata so zuwa Hamida ce ba Lafiya Cikinta na ciwo yasa Mamanmu ta matsa sai taje. Tana Tura baki ta saka Hijabinta ta Fita Tana ji ya Zeenatu na Fadin"Mamanmu Amina fa bakinta take Tura miki alamun bazataje ba..! Mamanmu tace"Zeenatu fita daga idona..Bana son sharri..! Sai da ta Murmusa wani Lokacin bata san in akace ta zabi Tsakanin Mamanmu da yaya wacce zata zaba ba.. In tace zabi zatayi to sau goma mamaanmu zata zaba itace komai nata,Laifinta Dubu sai ta kare mata Ita da baba mallam Har Abada bazata manta dasu ba shi baya samun zama yanzu saboda suna ta zuwa gwaruruwa Da'awa ko ya zauna na dan kwamaki ne kuma suna makaranta sun Dade rabon da su samu Zama da Baba Mallam din Hakika tana kewarsa. Leshin Bikin su ya Zulahait ne ajikinta da Farin hijabin mamanmu Dogo ita nata duk sun Yamutse ba guga. Mamanmu ta wanke mata Hamida ba lafiya balle ta goge mata ya zeenatu kuwa ko mamanmu ta saka kafin ta Goge sai taci zagi da Mita da Dunguri in ma Zata gogen kenan Lokacin data fito kanta na kasa ko alama bata gansa ba Kamar inuwa taji daga gefenta da kuma jikinta ya bata ana kallonta Tana Dagowa suka Hada ido. Gabanta sai da ya fadi gabanta ta kallah Masallaci yana kulle ne Baba Mallam baya gari ba kowa sai yara Dake wasa da Famfo bakin masallacin bayanta ta kallah ba kowa yasa ta fara Sauri ta shige gidansu Hanne bata san ya Biyota ba Muryansa taji. "In kika shiga baki Tsaya munyi mgana ba..Wlh zan biki cikin gidan..! Amuryansa tasan zai aikata abunda ya Fada yasa ta Tsaya tsoro take ji wannan Jidalin yafi karfinta in wani ya ganta kashinta ya Bushe ko Baba Mallam bai isa ba sai su ya Jafar sun kusa Kasheta. Ta daga kafa taga yana Binta sai ta Rude kawai sai ta Mike maimakon ta shiga gidansu Hanne shima yabi bayanta kafa kafa har sai da suka sha kwanar Layin kamar tana jira ta Dakata azafafe ta juyo tana Kallonsa Cikin Juya manya idanuwanta Tace"Kayi wa girman Allah ka daina Bina..Zaka jamin bala"i..! Waka taba ganin yana Tsayawa da wani agidanmu..? Kada ka jamin bala"in in ba so kake akasheni in wani ya ganmu tare ba..! Yadda yake kallonta yasa ta gane baya Fahimtarta yasa ta Damke Ledar hannunta zata Ruga da Sauri ya riko Gefen Hijabinta Amina taji kamar ta Yanka ihu ballatana ma dataga wata Mota kamar ta ya Nasir da sauri ta Fizge Hijabinta tana Fadin"Innalillahi..Ka sakeni don Allah..! Da sauri ya saketa Lokaci Daya yana Fadin"Zan kyaleki Amina..Ammh sai kin jiyo kin kalleni kin ga yadda Sonki ya maidani..? Kamar bazata juyo ba yanayin muryansa yasa ta juyo tana kallonsa kallon ya shiga har cikin jikinta tana jin kamar Zazzabi zai kamata. Ya rame sai dai ya kara Fari Wayarsa ya zaro yayi wani Danne danne ya kara kunni Lokaci Daya taji yana Fadin"Gata nan Nenne..Don Allah ki Roketa..ta ce tana sona..kada ki rasa Aminunki Nenne..! Dagachan Bangaran Nenne tace"Bata wayar Aminu..Ni don ka kimin ne..da na Share kafata nazo har gabanta na Duka mata..! A speaker ya saka wayar Cikin ido yake kallon Amina kafin yace"Nenne ta ce..Itace Duniyata..Takasa gane kaina na bata labarinki ammh nace kina Wahalar dani..! Nenne tana jinki ki roketa don Allah ta Saurareni..! Amina bata gama mamaki ba sai da taji muryan matar tana Fadin"Amina..Kina jina..Amina don Allah ki Saurari Aminu wlh yana sonki..Da gaske yake Aminu bai taba zuwa ya Duka yana min magiya kan mace ba sai akanki Amina ba don ni ba..Don Allah ki tsaya ki Saurareshi Yana sonki so na Tsakani ga Allah..! Amina taji gwiwanta ya saki karamar kwalkwlwarta ta kasa Fassara mata komai Sai da taji Nenne tace"Ko na Duka kan gwiyoyina ne Amina..? Ina son ganin Aminu cikin Farimciki maraya ne bashi da kowa Amina don Allah ki tallafamai..! Amina taji kwalla sun cika mata ido Tana ji Nenne na fadin"Kina jina Amina..Amina..! Dakyar tace"Naji zan saurareshi Saboda ke Saboda ke..! Da sauri Nenne tace"Nagode Amina..Allah yayi miki albarka Nagode..! Take ta fada kamar zatayi kuka yanke Kiran yayi yama kallon Amina Cikin Galabaitar da yayi kwana Biyu da bai ganta ba yasha zata nemesa bata nemesa ba shi kuma ya kasa jurewa ya Fadama Nenne komai tayi tayi ya bari ta gayama Alhaji Babba sai atura manya Tunda gidan malamai ne yaki barinta yace sai ya samu Soyayyar Amina bai sani ba wannan kuskuran wannan Soyayar itace zata yi katanga Tsakaninsa da Amina har Abada Zanen kaddara ya riga ya zana bawa bai isa ya kauce masa ba. Yaga tana Shirin juyawa ne batace mai komai ba yasa da Sauri yace"Kin ce mata zaki Saurareni fa Amina..! Tsoro take ji wannan Tsoron ya shigeta Daga Fara Haduwa dashi. Tasani wannan abun bai Dace ba ammh bazata iya Ture alfarman matar nan taji nauyinta. Yasa ta waiga taga ba kowa sai yara Dake wucewa Daman anguwan bata da yawan Zirga zirgan jama"a Wani Lungu tagani kamar hanya yasa ta Nufi chan tana Fadin"banda karfin Gwiwan Tsayuwa Dakai a hanya .Ina jin Tsoro ka Shigo nan..! Bai musa mata ba ya bita Daga Farkon lungun suka Tsaya kanta na kasa tace"Meyasa sai ni.? Agidanmu bawanda na Taba ganin yayi wata soyayya kowa da Lokacinta yayi Baba Mallam zai turo mata mijinta haka akeyi tun kafin a haifemu har kuma yau da muke bata sauya ba..Ka tafi kabarni ban dace Dakai ba ni ba wacce Kake nema bane..! Bai barta ta Dire ba ya karbe da Fadin"Sai afara ta kanmu Amina..Ina sonki..Kuma soyayyarki bazata taba barina na kyaleki ba ki yarda dani..Ki soni na Rantse iki komai zai zama Daidai da kaina zan samu Malan namai bayani bazai hanani ke ba Amina..! Kamar yana da wani abu a mganarsa yana mgana tana jin gaskiya a mganarsa ganin ta tsaya tana kallonsa yasa ya fara bata Labarinsa Tundaga Farko har karshe sai taji Tsausayinsa maraya ne cikin Sanyin jiki tace"Allah ya jikansu da Rahma..! Ya amsa mata da Ameen yana Fadim"Kin ji kadan Daga Labarina Amina..? Ke nasan komai akanki bana bukatar ji..Kice kina sona ko Hankalina zai kwanta..! Ido ta zaro kafin tace"Komai fa kace..? Kai ya gyada kafin yace"Eh..Harda Bakin Tsiwanki nasani..! Sai ta rufe baki da Hijabinta tana kallonsa Yar dariya yayi lokacin Daya Hangi ledan hannunta yace"Wannan ledan fa..? Ina zaki..?na tsaya yau ne kawai ba Domin nasan zan ganki ba yau jumma"a ba makaranta sai dai jikina ke bani zaki fito..! Zuwa yanzu ta fara rage tsoronta Cikin Sanyinta tace"Sako ne Mamanmu ta aikeni na kaima Hajiya..! Kai ya gyada kafin yace"Zan so na ga mamanmu nima..Yaushe zan je na gaisheta ko kuma yaushe zan gabatar da kaina wajen Mallam..? Zai karbeni kuwa..? Wlh ba waka bace kadai Sana"ata ina saida Motoci da kayan Gyaransu sannan ina da shagon gwalagwalai anan kano..Nayi alkwarin zan rike ki Amana..! Amina ta katseshi da sauri ganin kamar baya cikin natsuwarsa yasa tace"Ba yanzu ba..Kada kaje ba yanzu ba..! Kai Tsaye yace mata"Saboda mene..? Bazata iya kallonsa ba yasa kanta na kasa tace"Yanzu ba Lokacin Daya Dace bane..! Shuru yayi mata akwai tsoro atare da ita yasa ya dan Sausauta mata kansa ya Shafa yana Fadin"Lokacin yayi Amina..Ko ba yanzu zamu yi auran ba ina son na Rika ganinki duk sanda naso..! Ido ta waro kafin tace"A"a bazai yuyu ba..! Shima kai tsayen yace"Zai yuyu Amina..tunda kin hanani bayyana kaina ki samamin mafita..Zan susuce akanki baki ga alama ba..! Amina tayi shuru ta kasa mgana ganin yadda ya marairaice yana kallonta ta kasa mai gaddama yasa tace"Sai dai mu rika haduwa anan lungu ko wanchan layin da muka Fara Haduwa..In wani ya ganni dakai agidanmu kasheni za"ayi.. Idanuwanta yake sha"awa in tana Taoro yasa yayi dariya kafin yace"To ta ina zaki san nazo..? Amina tayi shuru tana Tunani kafin tace"Sai ka rika zuwa bayan kwana Biyu..! Da gaske take yi ayadda ta Fada yarintarta ya gani yasa ya yi Dariya yana shafa sumar kansa yace"Amina ina aiki fa..?garin nan bansan kowa ba sai ke bazaki Tsausayamin Zirga zirga ba..In Nenne taji zatayi Fada dani nima zata kusa kasheni in taji ina yawo Tsakanin Titin Kano zuwa Gumel..! Sai da ya fada Taga wautarta Ido ta Juya ta rasa me zatacemai bata so ta Fadi wani abu yaji ba Dadi Tsausayi yake bata ashe maraya ne. Ganin tayi shuru yasa yace"Ina katin da na baki kwanaki..? Kai tsaye tace"Yana gida cikin Dirowata..! Kai ya gyada kafin yace"kina Daukan wayan Mamanmu ko..? Kai ta gyada kafin tace"Tab...Ni kadai ke Dauka...Bata mgana in ko su Hamida ne sai ta Rankwashi mutum..! Ta karishe Fada tana Dariya shima Dariyan yake yi kafin yace"Daga gani mamanmu din nan na sonki..Ko kice Auta..? Amina tace"A"a ina da kani Jawaad..Mamanmu ta Dabam ce..Kamar yadda kace Girman Nenne a wajenka haka Mamanmu duk da ba ita ta Haifeni ba nafi sonta akan Yaya..! Ido ya zaro yana kallonta kafin yace"Ba ita ce mamanki ba..? Tana Dariya tace"Kaima kaji mamaki ko..? Haka kowa ke fadi in aka shigo gidanmu Yaya kamar ba ita ta Haifemu dukkanmu mamanmu ce komai namu..! Gyara Tsayuwa yayi yana Fadin"Bani kadan Daga Labarin Mamanmu Amina..Naji ina sonta kamar Nenne ta..! Amina saboda Shaukin Labarin Mamanmu yasa Ta manta da Tsoronta da aiken da akayi mata ta shiga basa Labarin mamanmu da yaya da Aba da ya Jafar da su hamida ta karishe da Fadin"Ko sau goma akace in yi zabi Mamanmu zan zaba akan Yaya..Kwata kwata bata sona kullum bata Fadin Alherina..Mamanmu ko laifi nayi tasan shi bata Fadinshi sai ta Boye Laifina ko ya"yanta bata hada kansu Dani ni ta Dabam ce awajenta.. Kallonta yake sai yanzu yake ganin yarintatarta Uwa uwace kuma ai ta wuce wasa duk da alabarin ya Fahimci mamanmu macece ta kwarai ammh bai kai Amina ta Girmamata Fiye da Mahaifiyarta ba,sai dai ba yanzu zai nuna mata haka ba Lokaci bai yi ba sai nan gaba bai sani ba nan gaba na Tare da wani boyayyan Kaddara, kaddaran da bazata bashi Dama ya Nuna ma Amina Muhimmancin uwa ba. Ganin Lokaci ya tafi yasa ya kalli Amina yana Fadin"Shida ta kusa..! Lokaci Daya yana Kallon agogon Fatan Dake hannunsa Ido Amina ta Zaro kafin tace"Na dade..kada Mamanmu tajini shuru..! Kai ya gyada kafin yace"Hakane ki tafi..Ki Ari wayar mamanmu kimin Flashing zan kira in naga Nombar zamu rika mgana Amina ai zaki min wannan alfarman ko..? Gabanta na Faduwa tace"In aka ganni zan shiga uku wlh..! Yana Dariyan mganarta yace"Zaki boye ai ba wamda zai gani ko..? Saboda ni da Rokon Nenne..! Ya fada yana marairaice mata jin haka yasa ta Daga kai da sauri yayi dan Ihu kafin yace"Nagode..Zan jiraki kinji..! Da kai ta Dagamai kafin ta fara tafiya sai kuma ta juyo tana kallonsa hannu ya Dagamata kafin ta dagamai sai da tace"Yanzu Yolan zaka tafi..!? Kai ya girgiza mata kafin yace"A"a kano zan koma Amina daman nan din A hotel nake kwana yau nazo saboda na ganki muna da Shooting gobe in Oscar bai ganni ba ai na Shiga uku Amina..Nura ma in ya fara kirana sai ya Kasheni da raina..! Yadda ya fadi karshen mganar ne yasa ta yin Dariya tana wucewa da Sauri Lokaci Daya taji yana Fadin"Wlh Ina sonki Amina..Ni na sani ina sonki..! Har takai gidansu Hanne Mirmishi bai bar Fuskarta ba kamar almara wani Farimciki take ji yana shiganta Tunasa take da Duka kalamansa sai taji kamar tana yawo a gajimare. Sauri sauri tayi dataje gidansu Hanne Ko zama batayi ba Duk da Hanne tayi ta janta da Hira don ta zauna ta kosa ta ganta agida ta Nemi katin nan kada ace ya bace data Shiga uku. Ko Rakiyar Hanne bata jira ba Data Shiga Daki ta Dauko Hijabi Tana jin Ya Abida na Fadin"Amina yau Ba"a son zama kuma..Sai faman sauri take..! Hajiya ma sai da tayi mgana ita dai Amina gaba tayi koda Hanne ta fito ta wuce abunta Baki Hanne ta tabe kafin tace"Amina tsiyanta nada yawa..! Amina bata ji kwanciyar Hankali ba sai da ta Binciko Katin nan Cikin Dirowarta bayan ta gama yin Dai'dai da kayanta. Mamakinta ya ishi Hamida batayi dai mgana ba Ya Zeenatu ne tace"Wlh Amina ki kwashe mana kayan nan..Nasan Halinki sai kice kansu zaki kwana..! Amina batabi ta kanta ba Sai da taga Katin nan sannan ajiyar rai ya kwace mata da sai da suka kalleta Dukkansu Hamida tace"Me kike nema ne wai..? Amina tace"To kuma ina Ruwanki Uwar saka ido..! Hamida ta tabe baki tana Fadin"Ki gyara kayanki kuma da kanki Wlh..! Jin haka yasa Amina ta marairaice Tana Fadin"Kayya Hamida..Yi hakuri badake nake ba..Anty Hamida yar aljannah..Allah yasa ki auri Shugaban kasa muje Villah mu Bude Hanci wai waya ga Amina Aminene a Villa Jar Uba akwai Daga kai..! Yadda ta karkacen ne yasa Dole har ya Zeenatu sai da Dara tana Fadin"Ke ai Tun get din farko Sojojin Villa zasu Wurgoki waje..! Amina tace"Tab kaji ya Zeenan nan..Mune fa kalan masu kudi kalan yan gayu..! Take Fada tana wani Fari Zeenatu na Dariya tace"Aifa kalan masu kudi a bushe kirji gandas Amina kamar kin shafi kasan kabari Ko Hanne fa ta Fara Nanna banda ke suna chan makale a kirji kamar na maza..! Amina ta Chuno baki itama abun na Damunta kafin tace"Wlh nima abun ya isheni kaf yan ajinmu baki ga nasu ba Tumbul tumbul..Ni don Allah ko Hamida zata san min nata ne..? Kalli nata kamar Lemu sun yi Bulbul dasu..! Salati Zeenatu ta saka Hamida kuwa har da cin Tuntube wajen Fita ya Zeenatu tabi bayanta tana Fadin"Mamanmu ki fito..kiji Abunda Diyarki ke fadi..! Da gangan ta koresu suna fita ta Dauko Katin tana kallo acikin Haban Sikat din ta Boye shi ta fara maida kayan tana kwalama Hamida kira. "Hamida.Haba mana Hamidas..Zan yi miki zaman Daki na sati Daya zan tayaki gyaran gado..Yaya Hamida..Anty Hamidassassas..! Take fada Hamida na jinta tayi mata banza Daga Tsakar gidan tace"Bafa zan tayaki ba ki gyara da kanki..! Kamar Amina tayi kuka tace"Shikenan Baza"a ma ace Antyn ba Hamidan ba..Hamidu din..! Ba Hamida ba Hatta Yaya Dake Dakinta tana jinsu sai da ta Dara Mamanmu na cikin Bedroom dinta ko ta jisu ma bata fito ba Jawaad ne ke wasa ya kyakyalce da Dariya yana Fadin"Ita kuma Aminuu ba..! Zeenatu da Hamida suka saki Dariyan Amina na ciki na jinsu taji sunan Daya ambata yasa ta Daga Murya tana Fadin"Jawaad ina wasa dakai ko..? Wlh in na kamaka sai na yi kasa kasa Dakai..! Tagumi tayi tana maimaita sunan Aninu acikin ranta Tsikar jikinta sai da ya tashi wani yanayi ta shiga da batasan Dalili ba. Sai ta gama gyara kayanta Tsab har Hamida data shigo sai da tace"Yau wata rana Amina anyi abun kai..! Tana Hararanta tace"Yau jumma"a munafus aga ban gyara ba..! Dariya take mata Lokacin data fita alwalar mangariba ta shiga Dakin Mamanmu tana Tiolet din Cikin Dakinta yasa ta Dauki wayarta ta Sake a Sikat sai dakoma Daki tayi sallar mangariba Lokacin Yaya da Mamanmu da su Hamidi sun fito baranda kamar yadda suka saba suna Hira ta Lallaba ta shige Dakin mamanmu har cikin Makewayi ta kuma Sakama Kofar key. Kan abun bahaya ta zauna ta fito da waya da katin Duk yadda Tsoro ya Cikata kalaman Aminu na yana jiranta Cike da yakini yasa ta kwashe Daya Cikin Lambobin ta Doka mai Kira. Sai da ta shiga har taji an Dauka sannan wata zuciya tace"Amina me kika aikata..? Da sauri ta kashe sai dai ta makara Tunda yace ta kirasa yaji ajikinsa zata kira din yana ganin bakuwar Lamba yasan itace. Karar wayar yayi daidai da Daukewar Nunfashi Amina kafin gabanta ya koma ya Fadi Dam..! Ta rude yasa batasan ta Danna Dauka ba sai da taji muryansa yana Fadin"Hello Amina.. Nasan kece..Daman ina da yakinin zaki kirani..! Fitar muryansa kamar wani Sinadiri ne ajikin Amina hakanan taji kamar komai yana kwance mata wannan Tsoron kuma yana Fita Daga cikin kanta. Bata sani ba wannan wayar itace mafarin Kaddaranta Itace mafarin FITA ZAKKAN da tayi acikin Yan"uwanta da Danginta..! Yanzu muka shiga labarin da sauran mgana agaba..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️18* In wata Kaddara zata sameka Sanadin wani abu to baka da tsumi ballatana Dubara sannan Tsoro bashi da muhalli a wannan bangaran to kamar hakane ya faru da Amina inda ta san Sanadin Aminu zanen kaddaranta zai bayyana da tasani zatayi zatace Daman Tun farko komai bai faru ba. Amina bata taba tsintar kanta ahalin data tsinci kanta ba Yarinya ce mai son yabamata a nuna mata so da Muhimmanci zuciyarta karamace ba bu kowa acikinta shiyasa cikin Sauki Aminu ya samu Dama mai yawa akan Amina. Tun fara wayarsu ta farko abun bai Tsaya ba sai ya cigaba duk sanda Amina ta samu dama zata Dauke wayar mamanmu ta shige Tiolet dinta ko na Tsakar gida,flashing take mai yana gani kome yake yi zai ijiyeshi ya Kirata su sha Hira cikin abunda bai gaza sati Biyu ba, suka yi wani irin Shakuwa ta ban mamaki ko shakka babu Aminu ya samu Matsugunni azuciyan Amina tana sonshi tana kuma Tsausayamai saboda Maraya ne. Komai take aboye take yinshi bata taba yarda a Fahimci Halin data ke ciki Daman chan bata da tsoro sai da soyayyar Aminu yasa AMina ta koyi Munafunci da nuku nuku ko bata fito Fili ta Fada ba,kowa yasan tana cikin Walwala da Farimciki ba wanda yayi Tunanin wani abu daman ita Amina akullum cikin Jidali take da Tsiwa sai Chanzawar bai wani damu kowa ba Hatta dasu Hanne da suke tare da juna koda yaushe. Kafin lokaci yaja Amina ta gama sanin komai na Aminu duk halin Dayake ciki in sukayi waya sai ya Fadamata Amina ta zama kamar wata bangonsa yana Tunanin ranar Daya rasata baisan ina Rayuwa zata kaisa ba komai nata yana Burgesa komai tayi a wajensa mai kyau ne. Abokan aikinsa ba wanda baisan sunanta abaki ba Musamman ma Oscar,da Nura koda yaushe suna waya sai yace"Minata kinga Oscar ko..? Yau bai barni na Huta ba. ! Minata kinga Nura ko..? Yana sani yawan mgana...! Komai nsshi itace"Minata kinji me Nenne tace..? Wai bazata yarda na Daukeki zuwa kano ba Tare zaku zauna ayola kin yarda..?Ira iran irin wadanan zantukan Amina ta gama Haddacesu acikin kanta indai akan Aminu ne. Taki bari su kara haduwa wannan Tsoron bai saketa tana aikata abunda ko su ya Jadwa zamansu ba wacce tayi Tsaurin idonta sai dai ina Zuciyarta bazata iya bata ma Aminu ba Daya matsa ta amincemai yazo ya ganta Ranar Jumma"a da basu da Ismilya Daman sun yi mgana jiya da Daddare zasu hadu in da suka Hadu Na Karshe Alayin Gaban gidansu bayan La"asar. Haka kuwa akayi Tana idar da Sallar La"asar tace ma Mamanmu zata shiga wajen hanne ba wanda ya tankata sanin basu da Shamaki da gidan Baba Mallam Mazan duk suna masallaci suna Karatu ta sabe ta tafi koda taje har ya iso yana Jiranta,Ranar sun sha Hira Amina ta kara sanin Aminu sosai ta kuma gama yarda ma kanta itama In bashi bazata iya auran kowa ba Ko alokacin yayi yayi ta bari ya Turo a tambayan mai Izini Amina ta nuna ba yanzu ba tana tsoro ko Ss2 Bata kai ba ta Tura Saurayi gida ai su ya Jafar sai su kusa kasheta da ranta Tana Tunanin da Sauran Lokaci bata sani ba Daga ita har Aminun wannan Tunanin nasu shine ya bada kofar shigowar wannan kaddaransu kaddaran da zata Haramta musu juna har Abada kila da bai bi mganarta ba da Kaddaran tajasu zuwa gurbi ko matsayin da suke Fata Abu kamar wasa karamar mgana ta zama Baba Soyayya mai karfi ce Tsakamin Amina da Aminu agida ba wanda ya sani duk bayan sati uku yake zuwa ya ganta ta fita da Niyar zuwa gidansu Hanne sai su hadu alayin gaban gidansu wani Lokacin Nikab take sakawa saboda kaucema Idon Mutane wani irin so Aminu yake mata so mai zafin da komai zai iya yi kan Amina Yaso ta bashi dama ya Hidintamata ammh kuma taki yarda bata yi Tsaurin idon da zata karbi wani abu Daga wajensa ba Ranar da Dubunta ta Cika sai ta Mutu ta Dawo Saboda duka tasani akwai wannan Ranar watarana zata zo sai dai bata san yaushe ne ba ammh Tabbas akwai Ranar kin Dillanci. Zuwa Lokacin ba wanda Aminu bai sani ba agidansu Amina da gidan Baba Mallam ba,su ya Jafar kuwa har ya Haddace Labarinsu da su Sa"adatu da basa ga maciji Hanne da Hamida kuwa Koda yaushe suna waya rabi Duk Labarinsu ne Ya riga ya sani Hamida da Hanne sune gaban goshin Amina sannan kaunar Dake tsakaninta da Mamanmu kaunace da Allah ne kadai yasan Girmanta. Nenne kuwa koda yaushe suna mgana da Amina in yazo ko kuma in yaje Yola Nenne tana ganin abun kamar wasa sai kuma karamar mgana ta zama Ita dai jikinta bai bata ba tana ganin wannan hanyar da Aminu ya Biyo anya mai bullewa ce kuwa..? Tana Tsorom watan Watarana komai yazo ya Rikice tasha cemai"Aminu Anya bazaka Daina Biyema yarinyar nan ba..!? Kafita Hankali fa kai babba ne kana ganin wannan Soyayyar taku ta Boye ba wanda ya sani agidansu watarana in aka sani bazata Haifar maka da matsala ba..! In ta fadi haka Dariya kadai yake mata yace"Haba Nenne..Bafa komai mai Wahalar Meena ce..In tana sona ko Duniya zata hade bamai rabani da ita so kada ki damu babu abunda zai faru..! Kallonsa take yi bata cewa komai ba ganin idonsa ya Rufe ammh ajikinta Tana jin kamar zuwa gaba wannan zai zame ma Aminu kabule babba ma kuwa da bazai iya yin komai alokacin ba..! Babu wanda ya taba Lura da Halin da Amina ke ciki sai dai an fara Lura da ta na yawan Shiga bandaki ta Dade bata fito ba,Ranar Bandakin waje ta shiga tafi minti Talatin bata fito ba Da Daddare ne duk suna Tsakar gida abaranda suna shan Iska Aba ya Dawo yana Shashensa Yaya tatafi wajensa Mamanmu ce da ya Zeenatu da Hamida sai jawad Dayayi barci kan katuwar Tabarman da suka baza anan Baranda abincin Dare suka gama ci su ka koma Hirar Anty sakina da Tayi barin yan Biyu,Achan madina din ance ta Zubar da jini sosai sai tafi sati a asibiti achan Anty Amarya taso taje Baba Mallam ya hana yace akwai mahaifityar Sarood da ita kanta Sarood din suna kula da Sakinar sai dai ance Danmallam din zai zo akwai mganin Hausan da zai tafin ma Sakinar dashi. Duk Amina na cikin Bayin Tsakar gida tana jinsu suna waya da Aminu ya katse yace ta jirashi ya amsa wani kiran bata so ta fita kuma ya Sake kira ta shiga uku duk da wayar asilent take sakata kuma da sun gama waya take Goge Lambar tasa data Riga ta Haddaceta akanta. Tana nan Tsaye tsabar sakama rai bata Damu da inda take wajen Najasa bane,Hankalinta kwance take shigowa suyi wayarsu domin nan din ne kadai mafita inda Hankalin wani bazai zo kanta da wuri ba. Karaf taji Hamida na Fadin"Wai ina Amina ne..? Mamanmu tace"Ba ta na cikin Dakin ku ba..! Ya zeenatu na kishingide tace"Ina jin fa bata fito ba..Naga Daukan butatanta da shiganta Bayi indai ba yanzu ta fito ba to tana ciki..! Hamida tace"Kai meke damun Amina ne..? Kwanakin nan bata da aiki sai shiga bayi..Kuma sai ta Dauki Lokaci kafin take fitowa ko Basir ne ya kamata..!? Mamanmu tayi shuru kafin tace"Nima na Lura mgana ce kadai ban yi ba..! Ya Zeenatu tace"Ko basir din ne mamanmu..? Kinsan fa tana saka yawan kashi..! Mamanmu tace"Bari ta fito muji dai..Ammh yawan shiga bayin Amina bana Lafiya bane..! Duk Amina na jinsu sai jikinta ya Saki Yanzu wani amsa zata basu..! Bata gama Tunani ba Aminu ya sake kira sai ta manta da su mamanmu ta Dauka suka cigaba da Hirarsu. Bata da Tsammani taji Muryan Hamida gabda kofar Bayin tana Fadin"Amina..Amina..! Mamanmu shuru fa bata amsa ba..! Jin haka yasa Mamanmu ta mike tana gyara Daurin zaninta Lokaci Daya tana Fadin"Zeenatu ba Lafiya..Gayama Aba dinku da yaya na shiga uku ni Balaraba..! Take fada Cikin Rudewa Tunaninta Allah yasa ba masai Amina ta Fada ba basu sani ba Zeenatun ta Rude itama ta kwashi Sauri zuwa Shashen Aba ta Fadamai jin haka yasa Amina tayi Saurin katse wayar jikinta ya fara rawa saboda Sauri yasa sai taa danne wayar ta kasheta Gabadaya ta Turata Cikin Wandonta Hamida na shirin Turo kofar Makewayin Amina tayi Zaraf ta fito har tana Bangaje Amina. Sai Hamida ta saki baki tana kallon Amina datayi wani Fiki Fiki da ido. Daidai Lokacin da Mamanmu ta Kariso tana Fadin"Jijjiga Kofar makewayin Hamida a bude take..Ami..! Bata karisa ba ta ci karo da Amina Tsaye Cikin Sauke Numfashi tace"Alhamdulillahi..Wlh gabana ya Sare na zata kin fada masai ne..! Da sauri Amina tace"Masai kuma mamanmu..!? Tace"Yo eh mana..Wajen awanki Daya fa da shigarki bayi baki fito ba..ni har na saka Zeenatu ta Kira babanku da Yaya..! Amina bata samu Zarafin mgana ba sukaji Muryan Aba yana Fadin"Balaraba meke faruwa ne..? Sukaji Muryansa sai Amina ta Rude da Sauri ta matsa jikin Mamanmu tana Wurga ido. Hannunta ta jawo zuwa Tsakar gida Hamida ta biyo bayansu Lokacin da Yaya ke fadin"Me ya samu Aminan..? Zeenatu tace ta shiga makewayi tun dazu bata fito ba..! Badai wanda ta shiga tun kafin Aba dinsu ya shigo bane ko..? Hamida tace"Shine..Yaya mu mun zata ko ta suma ne ma abayin..! Aba ya kalli Amina na Tsawon Lokaci yana Nazarinta yadda take Fiki Fiki da idonta ajikinsa yaji bai yarda da ita ba. Cikin kaushinsa ya Kira sunanta "Amina..! Sai da gabanta ya fadi da Sauri ta amsa"Na"am Aba..! Kai Tsaye yace"Me kike yi a bandaki har na tsawon wani Lokaci..? Kan Amina na kasa tana kokuwa da Fargabanta tace"Bakomai Aba.. Ya zeenatu tace"In baki da lafiya ne ki Fada a nema miki mgani..Wlh Aba kusan koda yaushe Amina cikin shiga Bayi take kuma sai fa an manta da ita take fitowa..! Kallonta kawai yake yi yana kara nazarinta Hamida tace"Ni fa na Fara Tunanin ko Aljanu sun shafe ta ne..! Har fa bayin Dakin Mamanmu tana shiga ni Ranar ma da ta shiga na shigo sai na rika jin mganarta kasa kasa har da Dariya fa..Aba..? Kiris ya Rage Amina ta bata Dafe Kirji ba ta shiga uku Yaushe Hamida ta ji haka bata mata mgana ba.. Mamanmu ce tace"Mun shige su..Kuma shine baki Fadamin ba..? Hamida tace"na manta ne mamanmu..Ammh Tabbas Amina bata da Lafiya..! Kamar an Dasa Yaya da Aba haka suke bin Amina da kallo Mamanmu tana Salallami tana Fadin"Allah ya kaimu gobe zan shiga wajen Malam da kaina na Fada mishi Babansu kada fa ayi Shuru karamar mgana sai kaga ta zama Babba..! Ya zeenatu tace"Mamanmu gama Turaran Hayakin nan da Baba mallam ya bada kika taba Turarama ya Zulaihat da suka taba Bigeta a makaranta..? Yana cikin Dirowarki ki Turara mata yanzu agani in ma sune zasu bayyana..! Mamanmu tace"Yanzu kuwa Zeenatu..! Aba ne yayi gyaran Murya kafin yace"Ba fa wani Aljanun Dake Damunta..Ki tambayeta ko wani Cutar ne dabam..! Jin haka yasa da Sauri Amina tace"Aba basir ne..Zafi nake ji in naje yin bayan gida sai yaki fita..! Yadda ta fadi mganar yasa Dole ma ayarda Yaya ce tace"Ararrabi zaki sha yana mganin basir sosai..! Aba ya juya yana fadin"Ku jika ku bata ta sha in bai yi ba zan ma Nasiru mgana sai ya kaita taga Likita nan General..! Daga haka ya shige Falonsa,yaya kuma ta koma Daki ta Dauko Daddaken Ararrabinta da bata Rabo dashi ta Jikama Amina aruwa kadan ta bama Mamanmu hade da Sauran na Ledan tana Fadin"Tasha wannan yanzu..Gobe da safe ko atea ko koko sai ta kara sha insha Allah cikin zai saketa tayi bayan gidanta Lafiya lau..! Mamanmu ta karba tana Godiya ita ta tasa Amina sai d ta Shanye duka tas tana yamutsan baki Saboda Bauri bata Damu ba Hankalinta ya kwanta Tunda ta isa barka asirinta bai Toni ba. Tundaga Ranar Amina ta Rage shiga Makewayi tana waya Aminun, sai da aka kwana Biyu ta nemesa ta Fadamai Halin daake cikin Cikin Damuwa yace"Meena ki bar ni nazo naga Aba ko mallam..nagaji da wannan kumbikunbiyan..Da gaske nake yi ina sonki kuma auranki zan yi..! Amina sai ta marairaice tana Fadin"Ba yanzu ba Amin..Aba ko mallam baazasu taba Sauraranka ba Ko fa Ss2 ban shiga ba kuma aka"idan gidanmu sai kin kusa gama Candy ake Fara mganar auranki yanzu kana gani ko su ya Zeena bamu ji komai ba Har yanzu kuma basa su wuce shekarar nan mai zuwa ba ka Kara Hakuri akwai sauran Lokaci..sannan Zamu Rage waya na kwana Biyu..Gudun Faruwan wani abu wanda bazai mana Dadi ba.. Zan nemeka in na samu Dama..! Bazai iya mata gaddama ba Saboda yana sonta kuma baya so ya sakata acikin matsala. Atsukin Taji ance ya Danmallan yazo abakin Hanne sai dai kwana Biyu yayi ya koma Allah kuma yasa basu hadu ba,Don ko gidansu bai shigo ba,Tadai ji su Yaya nata jajanta Lamarin suna Fadin yace Sakina tasha Wahala sosai yaso ma ya taho da ita Mallam ne ya Hana shiyasa Anyi haka da kwana Hudu Labari yazo kan ya Zulaihat itama ta zame a bandaki Ta fadi itama tayi barin Cikinta,Tana asibiti washegari kuma Yaya da Hajiya Babba da Hajiya Uwa Mallam yasa Idi yakaisu kano inda mijinta ke aiki nan suka koma sukaje suka Dubata ya Zulaihat taso ta dawo gida sai ta samu Lafiya Baba mallan yace maza Tunda uwar mijinta na nan da kanwarsa sun isa su kula da ita tana ji tana gani su Hajiya suka Dawo Gumel suka barta. Sauran yan'uwa kuma sai a waya suka mata sannu da jiki har da su Amina da suka gama nacin abarsu suje Mallam yace ba wanda zai taka bama su ba,har su ya Abida Dake gaba dasu jin haka yasa kowacce ta maida maitanta. Amina sun cigaba da mgana da Aminu sai dai tana shiga Bandakin waje koda yaushe,Domin haka Mamanmh ta Dinga Dura mata mganin Basir Asibiti kuwa sai da Aba ya Tambayeta ta warke ko kuwa sai sun je asibitin tace ta warke shiyasa sai ta sauya Taku. Sai dare yayi in suna Tsarkar gida da an fara Hira sai ta fara hammar karya tace barci take ji ta shige Dakin Mamanmu chan kurya ta Kirasa da kuma taji motsi ta kashe wayar ta Boye ta Lafe kamar mai barci ba wanda ya Taba Fahimtar wani abu na Faruwa. Idon Amina ya Bude tasan menene Dadin Soyayya,Domin karance karancen datakeyi sun kara taimaka mata sosai,Bayan su Hamida ba wanda yasan Amina na karatun Littafan Hausa su kuma Aminansu ne bazasu taba fada ba,Sai dai koda yaushe suna mata Fadan ta Daina Abunda take yi ita kuma sai tace ina Ruwansu..! Kwanci tashi babu wuya a wajen Allah gashi har su Amina suna shirun Fara Jarabawar third Semester dinsu ns shiga SS2,alokacin kuma sun kwarari wajen wata bakwai tare da Aminu aboye batare da kowa ya sani ba. Sai dai akwai ranar da asirinta ya kusa Tonuwa Aminu yazo tayi karyan Tana gidan su Hanne Fitanta kuma ba Dadewa sai ga Hanne tazo nemanta Hamida tace ai yanzu Aminar ta fita zuwa wajenta. Hanne ta kalli Hamida cikin mamaki kafin tace"To bata je ba don ban ganta ba..! Cikin mamaki Hamida tace"Wasa kike ko..? Kusan fa duk jumma"a Aminar wajenki take kai har mangariba fa Hanne..! Hanne ta zaro ido kafin tace"Ni..? Yaushe rabon da naga Amina. ?ranar ne fa shima ana kiran sallar mangariba ta shigo sallah kadai tayi na Rakota gida..! Hamida ta koma ta zauna tana waige waige kafin tace"To wlh Amina na fita kuma tace wajen ki take zuwa Yanzu ma fa bata Dade da fita ba..! Hanne tace"To abun mamaki ina Amina take zuwa..? Hamida tace"Wlh bansani ba mu jira ta Dawo mu tambayeta..! Wasa wasa Amina har bayan mangariba bata Dawo ba Hanne da Hamida sun fara shiga Damuwa har gida Hanne ta koma ta tambayi ya Abida ko Amina ta shigo tace bata ganta ba. Ta sake dawowa ta Fadama Hamida,suka Rude suna wannan Tarardadin sai ga su ya Jafar sun shigo Sai suka kara Tsurewa kada su Farga ba Amina inda Allah ya Taimakesu har suka fita basu Lura ba Aminan ba,Suna Fita ba Dadewa sai ga Amina suna Daga cikin Daki sukaji ya Zeenatu na mata mgana tace Daga gidansu Hanne take Ya zeenatu ta harareta kafin tace"Hannen ai kina fita ta shigo..? Ko wata hannen dai ba wannan taki ba..? Amina sai ta fara Kifta ido kafin tace"Dakin su ta barni na kwanta bansan yammh tayi ba sai yanzu..! Ko kara kallonta batayi ba Jikinta asanyaye ta karisa Dakinsu kaifafun idanuwan Hanne da Hamida na kanta Hannunta take Boyewa Cikim Hijabinta kada su ga Zoben azurfan da Aminu ya bata yau batasan me zata ce musu ba. Ganin yadda suka Zuba mata ido ne yasa tace"Wai lafiya..? Wannan kallon kamar naci bashin ku..! Tafada Cikin Hararansu Adole sai ta barsa da mganar dake ransu. Hanne ce ta mike tana Fadin"Amina ina kika je..? Amina tace"Ina kuwa..? Ina zuwa akace kinzo gidanmu naga bazan iya dawowa ba na shiga Dakin ku na kwanta..! Hanne ta kalli Hamida itama ta kalleta suka koma suna kallon Amina datake wani Kifta ido alamun ba gaskiya. Hamida tace"Yanzu Hanne ta koma gida..Ya Abida tace baki zo ba..! Amina ta saki karamin Tsaki Lokaci Daya tana Cire Hijabin jikinta take fadin"Bata ganni ba ko Hajiya batasan na shigo ba..! Ruwanku ku yarda ko kar ku yarda..Ku Tsayama Zargina kukeyi na tafi yawon banza ko me..? Hanne tace"Bata kawo nan ba..Muna gujemiki matsala ne.. Kinsan Fita zuwa waje ba Tarbiyanmu bane Amina kada ki Fara Halin da kike Dade baki yi ba..! Amina ta Zabga ma Hanne Tana Fadin"Bangane ba..? Kinga Hanne don Allah ki kyaleni bama son Hayaniya..! Daga haka tayi saurin Fita Daga Dakin kafin su ganota Dakin Mamanmu ta Fada tana Kiranta. "mamanmu Mamanmu..Na dawo..! Tana fita Hanne ta kalli Hamida kafin tayi mgana Hamida ta Rigata da Fadon"Karya take yi wlh..Acikin idanuwamta naga Karya Hanne..! Hanne tace"Nima nasan haka To ina taje batasan Fadamana..! Hamida tace"Wayasanin mata..? Kila gidansu wannan Zainab isan taje aro Littafin Hausa kinsan Amina..! Hanne tace"Ai ba Littafi a hannunta..! Hamida tace"Zai iya yuyuwa bata samun bane..Ina zata Daya wuce nan..? Hanne tace"Hakane..! Daga haka suka bar mganar ammh kamar acikin sun kasa yarda da cewa Amina gidansu Zainab taje sun santa in ma chan taje zata gayamusu ammh abun mamaki yau Amina bata son Hada ido dasu suna Zargin akwai wani Sabon Al"amari game da Amina sai kuma basu san komenene ba..! Tunda Amina taga sun Fahimceta sai tace Aminu ya Dakata da zuwa gidan su Hannen Data ke Fakewa dashi an ganota yasa sai ya kwana Biyu bai zo ba sai su yi mgana ta waya. Watarana Ranar da ta zama mafarin bakaken Ranaku acikin Rayuwar Amina da bazata taba mantawa dasu ba. Ranar da suka gama Jarabawarsu ta Karshe wajen kwana Uku basu yi mgana da Juna ba tasan yana chan Hankalinsa atashe jinta shuru ita kuma bata samu damar Daukar wayar ba akwanakin Mamanmu na Makale da wayarta bata samun Daman Dauka duk hanyar da zata bi tabi bata samu Dama ba. Sai Ranar da Daddare Allah ya taimaketa Mamanmu ta ijiye wayar saman Mirror dinta Tana Dakin Aba tana gyaramai yau ita ke dashi. Bata Kira ba sai da taji Dawowar Aba da kuma Kai da kawon Mamanmu ashashen nasa sai da taji tsit alamun Tagama Zirga zirgan sannan ta shige Kuryan Dakin Mamanmu ta Kirasa yana ganin kiran ya biyo baya Tana Dauka ya Sauke Numfashi yana Fadin"Da baki kirani ba yau Meenata..gobe sai dai ki ganni agidanku..! Tasan zai aika shiyasa ta fara bashi Hakuri suna cikin mgana taji kamar Muryan Ya Zeenatu tana mgana da Sauri ta katse wayar,ta koma ta Lafe kamar mai barci sai dai abun da ya bata Haushi Falon Mamanmu Ya Zeenatun suka Dawo ita da Hamida suna Hira maimakon da da suke Falon Yaya ashe kanta ke ciwo ta kwanta Shiyasa suka barta ta Huta. Sanin in bata Lallashi Aminu ba zai ballo mata ruwa yasa tatashi ta Fito Falo tana mika kamar mai barci. Cikin Muryan barci tace"kun dameni ina barci Hamida..! Ya Zeenatu tace"Sai ki sauya Daki malama..! Bata ma Tsaya ba ta Tura baki tana Fadin"Na koma Dakinmu ni da Dakin uwata an koreni..! Tana jin Hamida na mgana bata tankata ba ta koma Dakinsu sam Tunanin ta Rufe kofa bai kawo mata ba ta Haye kan gado ta kira Aminu daman yana Jira ya Kirata suka cigaba da mgana Korafi yake mata kan ya gaji zai zo yaga Aba ko mallan ita kuma tana kokarin numamai Lokacin bai yi ba. Sam ta manta a inda take hankalinta ya Riga yayi gaba bata ji shigowar Kowa ba bataji motsin ba ko Tafiya kawai sai jin wata Gigitaciyar tsawar Muryan Aba ta karade Kunnuwanta Cikin kaushinsa yace"Amina..Amina Dawa kike mgana awaya..? Ba Amina kadai Hanjin Cikinta suka yamutse ba har da Aminu Dake Sauranta ya Rude domin Baya son Amina ta shiga matsala..yana ji ya kara Daka mata Tsawar yana Kara Fadin"Nace da Uban wa kike waya da Tsakar Daran nan Amina..? Tsawar da har Yaya sai da tadata ita Daga barci Mamanmu Zani a hannu Ita dasu Hamida suna Rigen rigen shigowa Dakin. Bayan ya shigo gida ne ya manta bai kulle gida ba yasa ya kara Fita ya kan yi Dube Dubensa atsakar gida kafin ya kwanta in sun manta da wani abu ya Kaudashi yana jin Hiransu Hamida bai leka Falon Mamanmu ba sai dai har ya wuce ya rika jin tashin mgana kasa kasa yasa ya Dawo da baya sai ya Fahumci Daga Dakin yaran ne. Kafafunsa suka jasa ya isa Bakin kofar Dakin Tar yaji muryan Amina tana mgana mamaki da al"ajabi yasa ya Daga Labulen Dakin ya Leka ya ganta kwance tabama kofa baya waya a kunnenta tana mgana duk da bayajin me tace cewa ammh yasan ko wata wayar ce bata Alheri bane. Har ya tako ya shigo Dakin agabanta bata sani ba Bai gama jin jikinsa ya Saki ba sai da yaji Amina na Fadin'"Haba Amin dina..Kasan nima ina sonka..Kuma nayi maka alkawarin Rayuwa Dakai har Abada..! Baisam Tunyaushe ta Fara ba sai da jikinsa ya fara mazarin da karkawan wani Bala"i ko yace wani Kangarewa ne ya samu Amina..! Amina fa itace cikin Dare tana waya da wani Gardi tana Fadamai tana son shi yar Amina da batasan komai ba.! Ganin yadda Amina ta yi sumar wucin gadi ne ga waya a kunnenta ta kasa Sauketa Saboda yadda Hanjinta ya Cure waje Daya. Aba ransa ya baci baisan ya karisa gabda da ita ba sai da taji wani gishiri Gishiri wajen bakinta Mari ne Aba ya Kamtseta dashu sai da bakinta ya Fashe wayar ta fadi gefenta Daidai Sanda Aba ke fadin"Ba mgana nake miki ba..Nace da Uban wa kike mgana da Daddare acikin waya..!? Amina sai ta Fara ganin hazo Cikin Daburcewa take fadin"Ba...ba..kowa Aba..ba kowa..! Ransa ne ya kara baci Bacin rai ya Kwashe sauran Hakurinsa baisan sadda ya Hada kanta da jikin gadon data ke kwance ba ji kake kummm...! Lokaci Daya ya hada da marin gefen Kumatunta yana Fadin"Zan miki karya ne..? Nace zan miki karya ne..? Yake fada Cikin bayanna bacin ransa Ihu Amina ta kwalla Saboda Ziyartan wani azaba Dataji asaman kanta da Aba ya,kumata Tuni wajen ya Fashe sai jini Daidai Lokacin da Aminu ya Katse kiran bazai iya jura ba bazai iya Juran jin Kukan Amina ba. Innalillahi kawai yake maimaitawa ya kasa zama yana Zagaye kyakyawan Bedroom dinsa a kano. Gabadaya su Hamida sun Rude sun kasa ma mgana Mamanmu ce da Sauri ta Dira gaban Amina Daidai Aba ya kara Daga hannu zai kara Sauke mata ta Tareshi tana Fadin"Babansu zaka kasheta ne..? Nace zaka kasheta ne..? Tafada Cikin Tsawa hannunsa na rawa ya Nunata yana Fadin"Kauce ki bani waje Balaraba..! Yau Sai yarinyar nan ta Fadamin Tun yaushe ta fara wannan lalacewar bansani ba..? Waya na kamata tanayi balaraba da wani kato tana Fadamai bazata iya Rqyuwa bashi ba wani shegen ne yake Lalatamin Tarbiya yarinya bansani ba..! Yake Fada yana saka hannu ya Ture Mamanmu gefe da hanzari ya Riko Amina tana Ihu ya jawota ya makata da kasa,Daman Sa"idu bai iya Fushi ba bai iya Duka ba in ya fara kamar zai kashe haka yake yi. Hamida da Zeematu suka Rike juna jikinsu na Rawa Hatta Yaya ta Rude Amina kuka take tana Dafe da kanta Aba ya saka kafa zai taka Amina yana Fadin"Zaki gayamin ko sai na kasheki na Huta..! Yaya bata bari ba ta rikosa da Sauri Tana Fadin"A"a kabi a hankali kada kayi Hukunci cikin Fushi..! Mamanmi kuwa Amina ta Tarairayo Jikinta ta fashe da kuka tana Taba jinin goshinta Lokaci Daya take fadin"Abbansu jini fa..Zaka kashemin Diyata ne..? Bai Saurareta ba wayar ya Dauko Daga Saman gado yana Laluban wajen kira Lambar Aminu ce ta karshe kuma ita ya Kira yana so yaji wani Lalataccen ne ina Tarbiya yana Daga waje yana kokarin Rusa komai..! Lokacin da Aminu yaga Kiran yana mgana da Nenne a Dayan wayarsa ne yana gayamata Halin da ake ciki ganin kiran yasa da Sauri yace"Nenne MEENA na kira..! Tana so tace mai kada ya Dauka kila ba Aminan bane ammh bai jita ba ya Datse kiranta ya Dauki na Amina. Aba a speaker ya saka wayar Daidai Sanda sukaji Muryan Aminu yana Fadin"MEENATA..meena Aba bai Dakeki ba ko..? Hankalina ya tashi! Su hamida suka kwalalo ido Amina ai sai taji miyan bakinta ya Tsaya Cak yau kafin safe kila sai dai Buzunta Aminene sai dai Tarihinta Aba yaji kansa ya Sara Cikin kaushin Murya Da takaici yace"Ba Meenar bace..Uban Aminan ne Sa"idu..Waye kai..?Meyasa ka zabi ka Lalatamin Tarbiyan da nayi Shekaru ina ginata..! Nace meyasa..? Aba ya karishe cikin Tsawar data gigita su mamanmu Hatta Aminu dagachan bangaransa ya kasa mgana baisan sadda ya Datse kiran Ba shikenan komai ya kare. Wannan Ranar daman yake gudu. Yanzu ta ina zai fara? Ko yace ba yaudaran Amina yake yi ba wazai yarda dashi? Abun ya Zama wani iri..Al"amarin yayi kwabewar da bai da wata mafita. Wannan shine mafarin komai Mafarin abubuwan dadama da zasu faru daga Rayuwar Amina da kuma Rayuwar wanda bai tsammmaci Aminar cikin Kaddaransa ba..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️19* Gabadaya jikin Aba rawa yake saboda Bacin rai idanuwansa sun rufe jijiyoyin kansa sun mike cikin Tsananin Fushin da ko su yaya sun Dade basu gani ba ya Nuna Mamanmu da wayar hannunsa yana fadin"Wayar waye wannan..? Nace wayar waye wannan Balaraba..? Ya karishe fada cikin Tsawa Lokaci daya yana sakar mata jajayen idanuwansa da suka sauya Launi Saboda bacin rai. Awannan gabar kowa bai da bakin mgana Yaya bazata kare Amina ba Daman Hamida da Zeenatu bazasu iya cewa komai ba Mamanmu ce Daman ke da wannan ikon itama ta rasa mafita Domin Amina ta bata komai wannan kiran wayar da kalaman Aminu ya gama tabbatar da cewa Amina ta aikata abunda ya Fada din. Amina kuwa jikin Mamanmu ta shige jikinta ba inda bai rawa shikenan ta gama wayo wannan Ranar daman take tsoro gashi tazo ta sameta bata shirya ba. Aba baya duka sai dai Fada baya Hukunci da kansa sai dai su ya Jafar ammh duk ranar da ka shiga hannunsa sunanka Sorry bai iya Duka ba in ya fara bai iya bari ba,Shiyasa wani Lokacin baya son bacin ransa kuma baya son yayi duka. Tasani komai ya gama baci bata kuma da kalmar da zata kare kanta ballatana Har Mamanmu ta samu kwarin gwiwar kareta kamar yadda ta saba. Aba ganin mamanmu tayi shuru ta kasa mgana sai kuka take taya Amina yasa yayi mirmishin Saman baki Mirmishin Dayafi kuka ciwo yace"Balaraba mgana nakemiki..? Nace wayar da Amina ke amfani da ita wayar waye..? Mamanmu ta Dago cikin wani yanayi kafin tace"Wayata ce..,ammh wlh..! Bai bari ta karisa ba ya Daga mata Hannu Cikin wani yanayi muryansa ta Cunkushe waje Daya yace"Basai kin ce komai ba Balaraba..Na Fahimci komai..Duk Abunda Amina ta aikata ko take aikatawa da saninki da kuma Daurin gindinki Balaraba..! Mamanmu ta Kallesa cikin wani yanayi haka ma Yaya bata samun Zarafin mgana ba ya cigaba da Fadin"Eh da saninki mana..in baki sani ba Meyasa kike barinta da wayar..?ai na Fada muku ku daina bari suna Daukan wayoyinku saboda gudun irin wannan ko ban fada ba..?ammh baki ji ba..Komai Amina zatayi mai kyau ko mara kyau Daidai ne awajenki Balaraba baki Taba nuna mata Tayi ba Daidai ba wannan ne so..?wannan ba So bane Balaraba..Kuma kin Cuceni kin Latatamin Tarbiyan da nayi shekaru ina ginata kan ya"yana bazan yafe miki ba..! Yake fada cikin wani yanayi muryansa kamar ya yi kuka,Yaya mamaki yasa tama kasa mgana ballatana Mamanmu data kafe Aba da ido zuciyarta na suya mamakin kalamansa ya kamata. Amina kuwa rudewa tayi da kalaman Aba da sauri ta mike daga jikin Mamanmu ta rarrafa gaban Aba cikin kuka take fadin"Aba Wlh Mamanmu bata sani ba..Bata sani ba..! Kafa yasa ya Shureta in ya kalleta ransa har wani kara baci yake,Dukewa tayi awajen tana kuka cikin Fusata yace"Karya kike ta sani..Tasan komai akanki..Balaraba tasan komai akanki Amina..Hadizam haihuwanki kadai tayi ammh Matsayin Uwa balarabace gareki baki yarda da kowa ba sai ita..Abun bakinciki ace kamarni acikin gidana na samu mai Bijirema Umarni na..SAnnan Tsorona Daya tun yaushe kika fara haka Amina..? Na Dade ina addu"an kada watarana ki Zama Zakkan da mutane ke Fada sai gashi Tun ba"a je ko"ina ba Abunda nake tsoro ya faru....! Yake fada cikin bacin rai kafim Lokaci Daya ya Dago Amina wuyanta ya Shake Cikin Zare mata ido yana Fadin"Ban yarda Dake ba Amina..Dom Ubanki ki Fadamin saunawa kika yarda yayi Lalata Dake..? Ki Fadamin yaushe kika san maza haka ban sani ba Amina Duk kafa kafan da muke ni da Baba Mallam a kanku..bamu tsira ba..? Ki fadamin nace kafin raina ya baci na Shakeki kimutu kowa ya huta..! Zuwa Lokacin Amina ta fara kokuwa da Numfashinta Yaya bazata ce komai ba Tana baya hankalinta atsshe Hamida da Zeenatu kuka Mamanmu kuma kalaman Aba sun gama kashe mata jiki ganin Amina ta kusa Mutuwa ne kada ayi kisam kai yasa Mamammu ta mike da Sauri ta isa garesa tana kokarin bambare hannunsa a wuyan Amina Lokaci Daya tana Fadin"Haba Abansu zakayi kisa ne..? Kalli fa zaka kasheta Amina bata Numfashi..? Take fada Cikim kuka Hannu yasa ya Tureta da karfi da sai da ta Fadi kugunta ya Bugu wani kara ta saki da yasa Yaya dasu Hamida sukayi kanta da yatsa ya nunata yana Fadin"Kada ki kara sakamin baki in ina ma ya"yana Hukunci balaraba..Domin ke ba Matata bace Yanzu NA SAKEKI Saki Daya..Tunda na Fahimci kin bada gudummuwa a Lalatamin tarbiyar Amina..! Ya fada Cikin bayyana bacin ransa Ba su Hamida Dake rike da Mamanmu ba Hatta Amina Dake kokuwa da Numfashinta sai da kalaman Aba suka Girgizata ta zaro ido tana kallon Aba Cikin Firgita da rawan baki Hamida hannu ta Dora akai Zeenatu kuwa hannun Yaya ta kamkame tana kuka wacce ta saki Mamanmu kamar bata da laka ta koma ta zauna Dabas kanta na juyamata ji take kamar amafarki komai ke faruwa Cikin Muryan da basu taba sanin Yaya tana dashi ba ta Kira Aba Cikin Tsawa"SA'AIDU..Me ka aikata haka..? In har baka gode mata kan Amina ba bazaka zageta ba..Kayi kuskure kayi kuskure Sa"idu kayi saurin gyarashi kafin Lokaci ya kure maka! Kallonta yake yi bai yi Nadama yace"Kema Kada ki kara sakamin baki..In kuma ba Haka sai ranki ya baci..! Yaya sai hawaye Amina ta zama bala'i tayi sanadin mutuwar auran matar da ta zama bango gareta Kallon Amina kawai take ta Durkushe tana wani kuka kukam Nadama da bakin ciki acikin Ranta Tana Tunanin Dama ace .Dama ace bata Hadu da Aminu ba Dama ace bata yarda dashi ba..Da duk haka bata faru ba me ta aikata..? Ta kashe auran Matar da ko Uwar data Haifeta bata kaita sonta ba Matar data kasance wata aba mai Daraja a wajenta ita kam Amina wannan Ranar bakar Ranace a wajenta soyayya bata mata adalci ba ta Datse mata komai alokacin da bata tsammaci Lalacewar abubuwa kamar yadda suke Faruwa ba. Kuka take kamar ranta zai fita ta Rararrafa ta kama Kafan Aba cikin kuka take fadin"Don Allah kayi hakuri..naji ni ka Hukuntani kayi ta Dukana har sai na Daina Numfashi ammh kada ka saki Mamanmu Na Rantse da wanda Raina ke hannunsa Mamanmu bata sam komai ba Wlh bata sani ba! Take fada tana kuka wannan karon ba Aba bane ya Tureta Yaya ce Lokaci Daya ta shiga Dima ma ta Dundu kota ko"ina Bataji bata gani tana kuka Tana Fadin"Kin yi asara Amina..Kin yi asara Tunda rashin jinki yasa,kikayi Sanadiyar Mutuwar auram matar da bata taba barinki ke kadai ba akowani Hali Tana Tare Dake..Kin Fita Zakka Amin Da gaske ne ke Zakka ce..Tunda kika Rama Alheri da Sharri..Ki ka kuma yi Sanadiyar Mutuwar auran da ya yi Shekaru na rasa da wani suna Zan kiraki ji nake in na barki da Raina bam Huce ba..! Kowa ya kasa hanata Yaya bada wasa take dukam Amina ba Fadi take"Abun kunya zaki jawo musu Amina..? Su kike ki kasheta ki huta..? domin ita kadai ke Daukema Jidalinki Amina kin fara bin maza? Aure kike so baki fada anyi miki ba.? Gwara na fara kasheki na Huta kafin ki zo ki Kashe sauran Rayuwanka da suke kare miki..! Dukanta take yi kamar bata cikin Hayyacinta Amina na kuka bakimta na Zubar da jini take fadin"Wlh yaya bana bin maza Wlh ni ba yar iska bace..! Bakinta bai mutu ba..Daman bazai taba Mutuwa ba yau da Mamanmu zata Ceceta bata ceceta ba tana gefe har alokacin Shock din Daya kamata bai saketa ba sannan ko tana son tashi ta kasa kugunta ya Bugu da Gadon Hamida ta kasa tashi Kuka take daga Zaune ba kukan kalaman Sa"idu kukan yadda Amina ke kuka Yaya na Dukanta Cikin karyewan Murya tace"Yaya ki daina dukan ta don Allah..Ki bari raina na kuna..! Yaya ta Dago idonta jajir tana Fadin"Yau dai..Yau dai Kadai ki bari na Shiga Lamarin yarinyar nan..Ki barni na yau kadai! Mamanmu sai ta kasa mgana Ya Zeenatu ne taga Abun ya rikice Aba na Tsaye bai yi mgana ba Shima baya son ya kara saka mata hannu ne sai ya Illlatata,Rugawa tayi ta Fice Daga Dakin ba Mayafi ba Takalmi ta nufi waje ita ta Bude gida sai gidam Baba Malam an Rufe get haka ta Dinga Bugawa da karfi megadi yana Lekowa ya ganta ya Bude Mata da Sauri yana Tambayanta ko Lafiya ina bata Tsaya Sauraransa ba da Farko Cikin Gida ta so ta wuce sai taga Falon Baba Mallam abude ssi ta kwashi gudu zuwa chan. Yana Tsaye gaban makeken Dirowan Dake falonsa mai shake da Littafai da Farin Gilashinsa da Jallabiya yana Duba wani littafi ne sanda Zeenatu ta Fado kamar an korota tana Haki Sama Sama Hakinta yaji da Numfashinta yasa ya Juyo da sauri ganinta Cikin wannnan yanayin yasa Hankalinsa ya tashi da sauri ya baro inda yake Tsaye ya kariso gabanta Cikin Dattakonsa yace"Zeenatu meke farruwa ne..? Ganin yadda ta Duke ne tana kuka Jikinta ba inda baya rawa yasa yace da Sauri"Kada kicemin wani abu ne Mummuna ya samu Sa"idu bayan yanzu bada Dadewa ba yabar nan wajen..!? Zeenatu na kuka Dakyar ta iya cewa"Aba..Ya saki mamanmu..Sannan ga yaya chan na Dukan Amina..Baba mallam kazo kafin su yi kisan kai..! Hankalinsa nan da nan ya tashi Cikin wani yanayi ya shiga maimaita"Innalillahi wani"inna ilaihirraju"un..! Muje gidan muje..! Yake fada yana karisa wajen Daya Ijiye wayarsa ya Daukota yabi bayan Zeenatu data Fice da Sauri Lambar Hajiya Babba ya Kira bai rude ba sosai Saboda yana ta Kiran sunan Allah.. Itama ta tsorata data ga Kiran nasa Domin bata Dade da komawa Shashen nata ba ba ita keda dashi ba Hajiya Nasara ce,Cikin Wani yanayi ta Daga Wayar tana Fadin"Mallam lafiya dai ko..? Cikin Dattakonsa yace"Ki sako mayafinki ki Sameni gidan Sa"idu..! Zumbur ta mike daga kwancen Datake tana Fadin"Innalillahi me ya Faru ne Mallam? Cikin Natsuwarsa yace"Bansani ba..Sai mun je zamu ji..Ki yi Sauri..! Daga haka ya Datse kiran cikin Sarsarfa ya Fice Daga falon bayan ya saka wayar tasa aljihu Tuni Zeenatu ta fice Daga gidan megadi ganin Mallam ya fito da kansa yasan ba Lafiya bai Tsaya tambayansa ba ya shiga mai Fatan Dawowa lafiya Gudu gudu sauri sauri Baba Mallam ya isa gidan su Amina kamar zai fadi Saboda Damuwa zeenatu na shiga Dakin ya shiga Saboda ya Jiyo kuka da mgana Har Lokacin Yaya Dukan Amina take yi Cikin Tashin hankali ya karisa gabanta baasusan da shigowarsa ba mganarsa kadai sukaji Daga sama "Kada ki Sake Dukanta HADIZA...! Ya fada Cikin Kaushinsa kamar koda yaushe,Cak yaya ta Tsaya sai Lokacin Aba ya gansa Mamanmu na gefe tana kuka tana ganin Baba Mallam tace"Yauwa gwara da Allah ya kawo ka..Mallam kalli Dukan da suka ma Amina..? Kashemin ita zasu yi.? Aminar Baba mallam ya kallah Goshi na zubar jini baki ma haka gabadaya bakin ya sumtuma sun sauya mata kammani Tama Daina kuka sai Hadiyar rai kawai Daidai shigowar Hajiya Babba cikin tashin Hankali ganin yanayinsu yasa tace"Wai meke faruwa ne..? Sa"idu..? Ba wanda ya iya mata mgana Sai Lokacin Mamanmu ta iya mikewa Dafe da kugunta Baba mallam ya kalleta Sau Daya ya kauda kai Hajiya Babba ya kallah yana Fadin"Hajiya kama Amina..bari na kira Idi yakai ku Asibiti mafi kusa a dubata tana Zubar da jini..! Sai Lokacim Hajiya Babba ta Lura da Amina da sauri ta karisa ta Dagota tana Fadin"Innalillahi waye yayi mata wannan Dukan..? Zaku kasheta ne..? Amina kuwa ganin Hajiya yasa ta fashe da kuka tana Fadin"Hajiya ki fadama Aba da yaya..Wlh bana bin maza..Ki kuma fadamai ba Ruwan mamanmu don Allah ya janye Sakin da yayi mata..! Hajiya ta ji ta shiga Tashin Hankali Cikin wani yanayi tace"Innalillahi Wani"inna Ilaihirraju"un..! Baba mallam bai saurari kowa ba ya Fiddo wayarsa ya Kira Idi Direba daman gidansa ba nisa yace mai ya Fito akwai Fitar da gaggawa yana Gama wayar ya juyo yana Fadin"Hajiya kuje har da Balaraba itama adubata! Hajiya ta kalli Mamanmu yadda ta kasa Tsayuwa tana Fadin"Mun shige su ni Zainabu..Wai me yake faruwa ne..? Baba Mallam bai mata mgana ba Aba ya kallah wanda kansa ke kasa yace"Biyo ni Dakinka..Ku kuma kuje Daga waje..Yanzu Idin zai iso..! Daga haka ya saka kai ya Fice Aba yabi bayansa Falon Aba suka isa Baba Mallam ya fara shiga Aba yabi bayansa su kuma Hajiya ta kama Amina tana kuka jini agoshi da baki Hamida ta kallah Dake gunjin kuka tace"Miko mata Hijabi Hamida..! Da sauri ta rarumo nata ta mika ma Hajiya ta saka mata Yaya kuma Ficewa Tayi Daga Dakin cikin yanayin da ba wanda ya gane. Hajiya ta kalli Mamanmu Tana Fadin"balaraba sako mayafinki muje..Allah yayi mana mganin wannan masifar data kunno mana kai da Daddaran nan! Zeenatu taje ta dauko ma Mamanmu Hijabi ta saka ta riketa Saboda Dakyar take iya takawa suka fita Kofar gida Har idi ya iso har ya fito da Mota suka shiga Hajiya da Amina da Mamanmu da Zeenatu Hamida kuma Hajiya tace ta koma gida Wani karamin asibitin kudi Hajiya tace Idi ya kaisu Saboda kada su bata Lokaci. Achan Falon Aba kuwa suna shiga ko Zama Baba Mallam bai yi ba ya Juyo yana kallon Aba cikin wani yanayin Bacin rai Aba kansa ya maida kasa Domin in yana gaban Baba mallam baya iya Daga kansa saboda Biyayyah..! Shuru na wani Lokaci yaji Baba Mallam bai ce komai shiyasa ya Dago kansa a hankali kafin ya bude baki zai yi mgana Baba Mallam ya Daga mai hannu Cikin Dattakonsa yace"Bana son jin komai yanzu..Kafin na tambayeka me ya faru..Ka maida Balaraba Dakinta in har kana so na Saurareka..! Aba ya Dago kansa cikin wani yanayi yace"Baba m...! "Bana son jin komai kayi abunda nace in har na isa Dakai..! Dole yasa Aba yace"Shikenan..Na maidata Dakinta na Janye Sakin Dake Tsakanina da Balaraba..! Sai alokacin Baba Mallam ya sauke Nunfashi ya samu kujera ya zauna yanuna Aba gefensa shima ya zauna kafin yace"Ina jinki...Fadamin abunda ya faru tundaga farko..! Nan Aba ya Sunkuyar dakai ya Sanar da Baba Mallan komai ya karishe da Fadin"Abu daya yafi min ciwo..Meyasa Balaraba ta Boyemun..! Sannan da Taimakonta ta Lalatamin Tarbiyar Amina Mallam..Na tabbata da saninta..! Kallonsa kawai yake ya Dade bai yi mgana ba sai chan nisa ya fara mgana cikin Kaushinsa kamar ko yaushe"Sa"idu kaifa mai ilmi ne..To ina Ilimin ka yake..? Me Annabi yace..? Kada muyi Fushi..Kuma mu daina Saurin yanke hukunci cikin Fushi..Meyasa da haka ta faru baka bari kayi bincike ba kafin ka yanke hukunci ba..Kana da Tabbacin ita Balarabar ta sani..? Baka sani ba..Kun taru kai da Hadiza kuna neman kuyi kisan kai..? Yanzu inda wani abu ya faru mara Dadi wa gari ya waya Sa"idu.? Kan Aba na kasa yace"Kayi hakuri Baba Mallam! Mirmishi yayi kafin yace"Akoda yaushe ina Fada maka Duka baya Tausasa yaro..Sai ma ya kara karangarar dashi Nasiha da Lallashi ne mafita Sa"idu ban ji dadi ba..Kana aibata yarka ina ji ajikina Bamu aikata barna Lokacin kuruciyarmu ba..Muma Daga cikin ya"yanmu ba Zamu samu bara Gurbi ba Sa"idu...! Aba ya dago yana Fadin"Yaron da take waya dashi fa Mallam..? Ansan meke Tsakaninsu..? Baba Mallan yace"Koma menene alheri ne Sa"idu..Baka haikema ya"yan wasu ba kaima da yardan Allah bamai haikema ya"yanka da yardan Allah..Wannan ai ba wani abu bane Komai zai daidaita Zan yi mgana da Amina yaron da suke wayar zan nemesa naji abunda ke Tsakaminsu in Yana sonta da Gaske ni zan ce ya Fito in nayi bincike na gari ne zan bashi Auran Amina Kamar yadda na Saba..! Aba ya saki baki yana kallon Baba Mallam bai samu zarafin mgana ba yaji yace"Kiramin Hadiza..Itama na nuna mata ta Daina yanke hukunci Cikin Fushi..Sannan ku daina aibata ya"yanku Dafi ne garesu..! Ba Musu ya mike ya fice koda yaje ya isketa tana ta kuka,Ya kalleta Cikin wani yanayi kafin yace"Kizo Falo na Baba Mallam na mgana..! Da haka ya fice share Hawayenta tayi ta saka Hijabi ta shiga Falon ta samu Baba Mallam yayi mata nasiha sosai da jikinta yayi sanyi Cikin wani Rauni Yaya tace"Mallam Amina ta fitta zakka..Tayi Sanadiyar da saki ya shiga Tsakanin Mahaifinta da matar da ta Zamemata komai a rayuwa..! Mallam ba Amina ce agabana ba Kuka nake Saboda Alherin Balaraba ya koma Sharrin awajem Sa"idu..! Baba Mallam yace"Wannan ya wuce Hadiza...Sa"idu ya maidata Dakinta Yanzu nan..Mganar Amina kuma ba Ruwanka zan yi mgaba da ita..,! Dukkansu basu kara mgama ba Domin Duk Abunda Baba Mallam yace daidai ne Yaya hankalinta ya kwanta Dataji cewa Aba ya maida Mamanmu sai alokacin taji Hamkalinta ya kwanta. Hajiya ce ta Kira Baba mallam awaya sukayi mgana basu ji me tace ba cewa kawai yayi sai sun dawo..! Suna mgana ya kallesu yana Fadin"komai lafiya..Amina goshinta ne ya fashe anyi Dinki sai Balaraba data Bugu kadan..suna hanyar Dawowa..! Kai suka gyada gabadayansu Baba mallam ya cigaba da musu nasiha yana Nuna musu illah yanke hukunci Cikin fushi da aibata ya"ya da kalamai marasa Dadi sunan nan sai gasu Hajiya sun Dawo falon Aba suka shigo Gabadayansu Hamida ta Tsaya Daga wajen Daman tunda suka tafi ta ke kuka Tasani Amina tana da Jidali sai dai bata taba Tsammanin Jidalin Amina yakai har ya huce yadda take tsammani ba Amina da plasta a goshinta bakinta kuma wankeshi akayi ya Kumbura mamanmu kuma mgani aka bata baba Mallam ya kalli Amina Dake Nanike da Mamamanmu kafin yace"Hajiya ki tafi da Amina ta zauna awajenki har ta samu sauki..Ke kuma Balaraba kiyi hakuri kin ji.. Sa"idu ya maidake Dakimki Don Alllah ina so har Abada bayan mu anan kada wani yaji wannam mganar..! Mamanmu tace"Insha Allahu mallam..Bakomai..! Baba Mallam yaji Dadi yana ta saka albarka kafin ya Mike shi da Hajiya wacce ta Riko Amina da hannunta ke cikin na Mamanmu kanta ta Dafa tana Fadin"Kada ki damu Har Abada ina nan a matsayin Mamanki Diyata.! Gobe zan shigo na Dubaki zan zo miki da kayanki..! Kai ta daga mata Zuciyarta ta Sauka Tunda Aba ya janye sakin da yayi mata radadin Dake ranta ya Sauka haka suka fito har kofar gida suka rakasu dukkansu Hamida ta rike ma Amina hannu sai haawaye Amina ta Rike Hamida tana Fadin"kuyi hakuri Hamida ku yafemin..! Hamida ta saka mgana har Hajiya taja Amina suka tafi wannan wani irin almari ne..? Bata fatan kara ganin mai kama da wannan Ranar. Achan gidan Baba Mallam kuwa Su Hanne duk sun yi barci Dakinta Hajiya takai Amina ta saka mata Ruwa mai zafi tace ta shiga tayi wanka ta gasa jikinta ita kuma ta Fice Shashen Mallam shi yake karanta mata abunda ya faru bataji Dadi ba ammh Tunda Mallam yace zai yi mgana da Amina shikenan komai zai Daidaita. Bata jima ba ta Dawo shashenta,Saboda Hajiya nasara tazo wajen Mallam koda ta koma Amina tayi barci Dayake an mata allura a asibitin Tsausayinta Hajiya taji wata Kaddaran bamu ke Dorama kanmu ba Allah ne..! Hajiya shimfida tayi akasa ta kwamta ta bar Amina akan gadon sai Washegari ne su Hanne su ka ganta Shima Hajiya ce tace su shiga su Duba Amina bata da lafiya kafin su tafi makaranta Allah yasa ma suna Revesition ne su Amina su kuma su ya Abida suna Mock ne. Da suka Tambayi me ya sameta sai Hajiya tace Zamewa tayi a bandaki Hanne tafi shiga Damuwa da Halin da Amina ke ciki,Sannan kuma Amina ta Riketa tana Fadin"Keda Hamida nayi muku laifi ku yafemin Hanne..! Bata iya gane komai ba,Sai da Suka je makaramta suka hadu da Hamida ta Fadamata komai Hanne ta shiga Tashun hankali Fadi take" kin ji ko.Hamida..? Amina ta Debo jidalin Dayafi karfinta..! Hamida tace"So nake ta kara jin Sauki..Sai mu turketa ta Fadamama yaushe ta fara aikata abu batare data sanar damu ba..! Hanne tace"Tabbas..! Da haka suka bar mganar sun fada a makaranta Amina bazata samu zuwa ba bata da lafiya bayan sun dawo ne suka shiga Har hamida gidan Baba mallam ta Duba Amina har da su Sa"adatu da yake an Fada Aminar bata da lafiya da ya Shamsu yaga bai ganta ba Hamida ta Fada acikin mota sanda Idi ya Daukesu Taji sauki sai dai Kumburin bakin kadan shima ya Sauka goshin ma yayi Sauki Mamanmu ma ta warware ta shigo har Fatan wake da Hanta tayo ma Amina Hajiya na mata tsiyan cewa ko ta mata kara ta bar mata Amina sai ta Biyota Mamanmu na Dariya tace"To karan me Hajiya..? Zan iya kara akomai banda Abunda ya shafi Amina..! Nan suka yi ta raha da Hajiya Amina taji Dadin ganin mamanmu ta Rumgumeta tana fadin"Mamanmu ki yafemin..! Mamanmu ta shafa kanta tana Fadin"Kada ki damu..har Abada matsayinki bai Sauya ba Diyata..Allah yayi miki albarka..! Su hanne suna son mgana da Amina basu samu zama ba itama tana so ta yi mgana dasu tana so ta fada musu komai Saboda taji sauki aramta tana cikin wani hali Bata barci Aminu na cikin ranta tana so tasan Halin Dayake ciki gashu bata san ta wacce hanya zata sani ba Duk abubuwan da suka Faru basu saka ya fita ranta ba yana nan a makale ta damu dashi ta Damu tasan wani Hali yake ciki. Tunda ga Ranar bata kara ganin Aba ba ballatana Yaya ammh har ya Zeenatu tazo sun gaisa su ya Zulaihat ma duk Mamanmu ta fada musu sun kira sun gaisheta kuma ba wanda yasan me yafaru sai dai ace abandaki ta Zame har su Anty Amarya sun shigo sun Dubata duk da tana ta Bin Diddigi Dalilin ganin Amina agidan. Sai da Amina ta kwana Hudu awajen Hajiya sannan suka samu kebewa da Amina suka tambayeta ta fada musu komai Hanne da Hamida suka Saki baki suna kallonta Amina ta cigaba da Fadin"Wlh bansan yaushe ne ba..Ban kuma sam Lokacin da soyayyar Amin ta shiga raina ba..Ammh wlh ina son shi ko da wannan abun ya faru ban ji ya Ragu araina ba ina nan kawai ammh ina cikin tashin hankali da Damuwa na san yana chan cikin Tashin hankali..! Hamida tace"Kina nufin wannan dai gayen da muka taba gani..? Amina ta daga kai Hanne tace"Amina kuskuranki ne..Meyasa baki barsa yaje wajen mallam ba..? Amina ta Dafe kanta tana Fadin"Bansani ba Hanne..Bansan haka zai iya faruwa ba..Gani nake kamar komai bazai yi daidai ba in yazo..Kuma wlh yanzu Ina son Aminu bazan iya Rabuwa dashi ba kuban shawara..! Hamida da hanne suka kasa mgana Hamida ce tace"Bamu ta cewa Amina..Mgana tana wajen Aba da Baba Mallan sai dai in zaki bi Shawaranmy kada ki nuna abunda ke Ranki..Ki bari har muga komai ya Daidaita..! Hanne tace"Nima abunda zan ce kenan..Gwara ki tsaya kiji abunda zasu ce..ammh koni kaina zan so ki Boye abunda ke ranki..Ina ji ajikina Ki rabu da wannan Mutumin Amina Shine Alherinki..! Amina kallonsu kawai take yi batace komai ba Rabuwa da Aminu ba abu bane mai Sauki,Abu ne da bazai taba yuyuwa ba Domin don basu san me take ji bane..! Shuru tayi musu kamar ta bar mganar sai dai ta kasa sukuni Baba mallam bai ce mata komai ba kuma yana zuwa Dubata,ammh bai ce mata komai ba,ga Damuwar halin da Amin yake ciki tasani kila ita tafishi kwanciyar hankali tasan yadda yake sonta Allah kadai yasan wani Hali yake ciki Kwana Biyar da Faruwar abun ta kasa Daurewa ta samu Hamida da Hanne ta Rokesu su samo mata waya ta Kira Aminu ko hamkalinta ya kwanta Hamida ta kalli Amina tana Fadin"Amina kada ki kara jawo wani Jidalin don Allah..! Hanne tace"In dai zata kirasa ta Fadamai ya rabu da ita zan Dauko miki wayar hajiya..Ammh da sharadin wannan shine na karshe..! Da sauri Amina tace"Naji Hanne..Naji..! So take kawai tayi mgana dashi Hamida kamar zatayi mgana sai kuma ta fasa,Hanne taje ta Dauko Wayar Hajiya Amina ta shige Tiolet din Dakinsu Hanne su kuma suna Waje suna Tsaro kada wani ya shigo su Lalace. Jikin Amina na rawa ta saka Lambar Aminu ta Kira tana Di..Di..Di..kamar Zuciyarta zata Fito gabda zata Tsinke Taji an Daga Cikin Sanyinsa akoda yaushe yayi sallama Amina Kafafunta sun fara rawa kawai sai ta sakamai kuka yana jin haka zumbur ya mike Daga kan gadon Hotel din daya kama yana Fadin"MEENATA..aminatu..Alhamdulillah..Amina na shiga wani Hali..Tun washegarin abunda ya faru ina garinku Amina kullum ina anguwanku ina ganin yan"uwanki ina so nayi musu mgana na rasa yadda zan yi..Meena kina ina ne..? Meena ina so na ganki ki taimakamin in banganki ba wlh zan lalalace Meenataaaa..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo besty* _Jinjina ta musamman gareka NAZIFI YARIMA..Nagode da karamcinka gareni na yaba matuka Allahu ya bar zumunci Ameen_ *🅿️20* Jin ta kasa mgana sai kuka take yi yasa ya kara marairaicewa yana Fadin"Meenata kina ji kuwa...? Ki yi hakuri ki daina kuka ki bari nazo Domin nasan ta yadda zamu Bullo ma al"amarin Kinji ko..? Gabadaya yadda yake mgana ya gama kashe ma Amina jiki Tsausayinsa ya kara kamata tasan yadda yake sonta tasan Halinsa bazai taba kwanciyar Hankali ba sai ya ganta sai dai bata da wannan Damar ayanzu komai ya gama Lalacewa. Tana jinsa cikin Damuwa ya kara Fadin"In zo Amina..?Don Allah kada kice A"a..Ina son ganinki..! Hawayenta ta share cikin muryan kuka akaron Farko tace"Bazai yuyu ba..Kayi hakuri Amin komai ya kare..! Ta karishe fada cikin kuka Tsabar yadda kalamanta suka gigita yasa ya koma ya zauna gefen gadon Daya tashi Cikin wani yanayi yace"Bangane ba Meeenata..? Me kuma ya kare tsakanina Dake..! Amina na Danne bakinta da kuka tace"Komai daka Sani ya kare..Soyayya ta dakai ta zama Tarihi kayi hakuri ba Laifina bane..! Sai kuma ta kara Fashewa da kuka kukan da Aminu yake jinsa kamar acikin Ransa. Cikin Fitan Hayyaci yace"A"a Amina kada kimin haka..Kada ki ce zaki Rabu dani alokacin da nafi kowa Bukatarki kinsan bani da kowa sai ke sai Nenne wlh in na rasaki Meenata zan Lalace ki bari nazo na ganki..Ki bari na bayyana kaina Amina Ina sonki Rashinki babban Gibi ne ga Rayuwata Amina ki taimakeni..! Yana mgana hawaye na Bulbulo masa kamar famfo batasan sadda ta saki kukanta da karfi ba,Lokaci Daya ta abude Kofar Tiolet din ta Fito tana Gunjin kuka,bata kashe wayar ba ta mikama Hanne da Hamida da suka yo kanta ganin tana kuka kan gadon su Hanne ta Fada ta na Sakin kukanta Wlh itama tana son Aminu kuma Rabuwa dashi babban Ciwo ne agareta ammh ya zatayi..? Aba zai kasheta in ya kara jin Labari makancin wannan,Zai iya mata baki Watarana shiyasa take tsoro sai dai tana Tsausayin Aminu tasan yadda yake sonta da gaske ne zai lalace akanta in ta rabu dashi. Hamida ce ta isa gareta tana Fadin"Menene Amina..?Don AllAh ki Daina kuka hakanan..? Hanne ce ta Lura wayar na tafiya yasa ta saka wayar a speaker daidai Sanda Aminu ke fadin"Meenata kina jina..? Don Allah kimin rai ki taimakeni na ganki..Wlh kwanana Hudu agarin nan Saboda ke in ban ganki bazan taba Samun natsuwa ba..! Ayadda yake mgana kowa yaji sa sai ya basa Tsausayi Amina kara Fashewa da kuka tayi zuciyarta na suya ashe ashe akwai irin wannan Ranar da Farinciki zai koma bakinciki bata Tsammanci Ranar nan kusa ba bata zata zata zo yanzu ba..! Hamida da Hanne jikinsu ya gama yin Sanyi Hanne ce tayi gyaran Murya kafin tace"Ba ita bace..sunana Hannatu ni yar uwartace..! Da Sauri Aminu yace"Hannen Amina..Hannen Hamida ai na ganeki..Amina tana bani Labarinku..Don Allah Hannatu ki taimakamin naga Amina don Darajan ma"aiki Salallahu alaihi wasallam..! Suka karisa gabadayansu Cikin tsausayinsa Hanne tace"Akwai matsala ne..abubuwa Dadama sun Faru wadanda bazasu fadu ba..Ina Kara Jadaddamaka Haduwarka da Amina bazai yuyu ba kayi hakuri..! Tana shirin yanke kiran ne yayi saurin Fadin"Koda na minti biyar ne..? Koda na ganta nayi mata sallama ne Hanne..?Amina itace ni Hannatu..Wlh in bata zan Lalace Hannatu..Nenne zata rasani zata rasani..! Dagajin yadda yake mgana kuka yake gabadaya sai hanne ta kasa mgana Cikin Tsausayi take kallon Hamida wacce ta Zabga Tagumi Ta rasa mafita sai Amina Dake kallonta idanuwanta Jajir tana kuka Dagachan taji magiyarsa Cikin Raunin Murya"Ki taimakeni Hannatu..Nayi miki alkwarin wannan shine na karshe..Don Allah ina son ganin Amina..Don Allah..! Hanne ta saki ajiyar rai kafin tace"Shikenan..Kazo da Daddare bayan Sallar isha'i..' Cikin Rauni yace"Meyasa ba yanzu ba Hannatu..!? Hanne tace"Ba dama ne..Kabari dai Daddare shima sai mun san yadda zamu iya ku hadun..! Suna jin Saukan Numfashinsa kafin yace"Nagode kwarai..Nagode Hannatu..Bazan taba mantawa da karamcinki ba..! Da haka Hanne ta Datse kiran Hamida tayi saurin cewa"Hanne kikasan me kika aikata kuwa..? Hanne tace"Ya zan yi Hamida..?Tsausayi ya bani..! Hamida tace"To yanzu ta yaya zasu hadu batare da wani ya sani ba..? Nidai ina Tsoro fa..Yadda abubuwan suka Lalace In muka kara wani laifin ba Amina ba har mu bazamu taba Fita ba Hanne..! Hanne shuru tayi batayi mgama ba sai chan tace"Zamu samu mafita Hamida..Kada ki damu..! Amina dai kukanta kawai take yi Cikinsu an rasa mai Lallashinta gabadaya Tsausayinta ya gama kamasu suna Tunanin har yaushe ne Amina ta bari ta fara soyayya har tayi wannan Zurfin basu sani ba..! Sai da suka gaji da jin kukan nata suka Fara bata hakuri kana ta Hakura ta Daina kuka sai dai idanuwanta sun kumbura ido ya sauya Launi saboda kuka har zuwa yammah sun gagara samun mafita Hamida ta kalli Hanne tana Fadin"Ki basa hakuri kawai Hanne..banga mafita ba..Waje fa kinsan su Baba mallam suna nan ta ina zasu hadu batare da wani ya gansu ba..! Hanne dai batayi mgana ba tana ta Tunanin mafita ba har akayi sallar Isha"i basu samu mafita ba Ya Abida ce ta shigo ta gansu zugun zugum Dariya tayi tana Fadin"Ku kuma Lafiyarku kukayi zugum kamar masu zamam makoki..?Ko Aminar ce taki Warwarewa har yanzu ku cigaba da Iskancin naku..? Cikinsu ba wacce tayi mgana itama bata Damu ba baki tatabe tana Fadin"Bakin Amina ya Mutu..Na Hamida da Hanne daman bai kai nata Tsini ba suma sun mutu..Allah Sarki..! Ta karishe Fada Tana Dariya wannan karon Mirmishi kadai Hamida tayi mata Ta fice daman wani Littafin koyon Turanci ta Dauka cikin Jakar makarantar ta fice. Hamida Bini bini ta kalli Hanne tana Fadin"Kin samo mafitan ne..? Sai hanne ta Girgizakai Cikin Damuwa Hamida kan ce"Jikina na Sanyi..Ina ji kamar wani abu zai faru Hanne..! Itama Hanne haka take ji ammh Tsausayin Amina take ji da Aminu Shiyasa ta kasa cewa A"a tunda Farko Tunanin wani abu tayi taja hannun Hamida suka fita Leke suka fara yi Domin ganin wadanda ke waje Allah ya taimaka ba kowa masallaci ma an Rufe ba Motar ya Jafar bata Ya Nasir kenan sun tafi gida Saannan Allah ya taimake su Aba ya Dawo da wuri ga Motarsa nan sannan sunji mganarsa afalon Baba Mallam da Hajiya Babba..! Hanne ta kalli Hamida tana Fadin"Na samu mafita..In..! "Su waye anan..? Gabansu ya fadi da sukaji Muryan ya Shamsu Cikin Daburcewa suka juyo Hamida ce tayi mgana"Bakomai ya shamsu cikin gida zamu shiga..! Yana Tsaye Daga kofar Dakinsu yace"Cikin gidam ina..? Da sauri Hanne tace"Zan rakata gida ne ya shamsu..! Kamar zai yi mgana sai kuma suka ga juya ya koma Daki ya Dauko Buta Makewayin Dake bayansu ya wuce bai karama kallonsu ba ganin haka yasa suka Sauke Numfashi Hanne taja Hannun Hamida suka Fice daga gidan zuwa gidansu wayar Hajiya tun mangariba ta Dauketa tana Hannun Hannatu. Gidan su hamida suka je suka zauna Har Aba ya dawo sannan Hanne tatashi tace zata tafi Hamida ta rakata mamanmu har tana Fadin"Hanne baki kwanciyar anan..!? Da sauri Hamida tace"Mamanmu Amina zata bari ita kadai in ta kwana anan..! Mamanmu tace"Kuma fa hakane..To maza ki rakata Hamida ki Dawo Dare yayi..! Da haka suka samu suka Fice Aba na Shashensa Yaya ta kaimai abinci suka Fice akofar gida suka Tsaya Hanne ta Leka Wani lungin jikin gidansu Amina Dake da Duhu kadan Tunda Kofar gidansu dana Baba Mallam gauraye yake da Hasken Gen da aka kunna Hamida ta nuna ma wajen tana Fadin"ZAn kirasa yazo ta nan su hadu..Ni zan Tsaya anan ki shiga ki Fito da Amina yau Hajiya Shashen baba mallam zata kwana zamu Tsaya Daga chan muna gadinsu kada wani yazo..! Hamida ta kalleta cikin Tsoro kafin tace"Kina ganin ba Matsala..? Hanne ta Sauke Numfashu tace"Insha Allahu..Ki fadama Amina kada ta bata Lokaci..! Kai hamida ta gyada ita ta Fara wucewa zuwa gidansu Hanne ita kuma ta koma kofar gidansu Amina ta Danna ma Aminu kira Daman ta adana Lambar da sunan Amina. Tana shiga kamar yana jira ya Daga Kiran kafin tayi mgana yace"Ina Hangenku tun dazu hannatu..Amasallacin gidanku nayi sallar mangariba ma..! Hanne ta zaro ido ta fara waige waige Daga chan gaba ta hango hasken Mota motan a kashe sai kuma aka Bude Mota aka fito Cikin son Tabbatarwa Hanne tace"Kai ne Daga nesa..Ka fito a mota..!? Cikin wani sanyi yace"Eh nine..! Da Sauri Hanne tace"To ka kariso da Sauri..Yanzu Hamida zata zo da Amina..! Daga haka ta datse kiran ta shigo gidansu Amina jikinta na rawa kada wani ya fito ya ganta Aminu da Sassarfa ya kariso duk ya rame kamar wanda yayi jinya yana Sanye da Riga da wando bakake ya saka wata Rigar Sanyi mai Hula ya Rufe kansa yana zuwa Hanne ta Leko sai da Tabbatar ba kowa sannan ta fito tana Fadin"Don Allah minti goma..Akwai Hatsari Aba na cikin gida hakama Baba Mallam sauran yayyinmu ma suna cikin gida kada ka bata Lokaci har komai ya Lalace don Allah..! Hulan kansa ya cire fuskarsa ta bayyana Cikin Muryansa kamar ta waya yace"Insha Allahu Nagode Hannatu..! Zatayi mgana kenan sai ga su Hamida sun fito Amina na bayanta da Hijabi tana Tafe kamar wata mara Laka ajikinta Allah ya taimake su ya Abida na Kitchen Hajiya kuma na shashen Baba Mallam suka samu suka Lallabo suka fito Allah yasa ba wanda ya gansu..! Tundaga nesa yake kallon Amina Hankalinsa ya tashi da suka kariso yaga saman kanta da Ciwo an cire Plastan tuni,Da hanzari ya karisa gabanta yana Fadin"Meenata me ya sameki ne..? Yadda yake kallonta haka take kallonsa Hawaye sun tarun mata ganin yadda ya rame hamida da Hanne sai suka koma gefe suna kallon Ikon Allah ganin yadda Amina ta Fashe da kuka Aminu ya Rude ya rasa ya zai yi Cikin wani yanayi yake fadin"kiyi wa Allah Amina kibar kuka ki Fadamin me yake faruwane..! Hanne ce taga Tsayuwar bata da Amfani kada wani yazo ya gansu yasa tace"Amina ku shiga nan.Kinsan dai Halin da ake ciki ko..? Tafada tana nuna mata lungun bayan gidansu da kai Amina ta amsa mata Kafin ta wuce tayi gaba shi kuma yabi bayanta su kuma sai suka koma Cikin Haraban gidansu Amina suka Labe Jikin Get gabansu na Fadi Fat Fat suna Tunanin anya basu yi ganganci ba..? Amina kuwa suna shiga dan lungu ta Fashe da kuka ta Duke Aminu yabita shima ya Durkusa Kamar yayi kuka yana Fadin"in kika cigaba da wannan kuka Amina zan iya shiga wani Hali..Kiyiwa Allah ki Fadamin abunda ya Faru..! Yadda yake mganar ne yasa Tsausayinsa ya kamata yasa ta Dago Cikin kuka ta fara Fadamai abunda ya Faru Tundaga farko sai dai ta boyemai Sakin da Aba yayi ma mamanmu akanta Ba saboda komai ba akwai Kunya ta ce an saki Mamanmu Saboda ita ta karishe Da Fadin"Soyayyarmu zata zama Tarihi ne Amin..Rabuwar mu shine Alheri Wannan abun da ya faru kadan ne akan wanda zai kara faruwa..Ni kaina nasan ba Domin baba Mallam na sona ba da yanzu wani Labari akeyi..Wlh bawacce tataba aikata abunda na aikata Bata sani ba..Ba Laifina bane Soyayyace ta jani inda ta kaini Ina sonka ammh kayi hakuri mu Kareta anan akuma yau Aminu...Don Allah kayi hakuri..! Kuka take kamar ranta zai fita Aminu yaji kamar ta Chakamai mashi da Sauri ya Mike yana Fadin"Bazai taba yuyu ba Amina..Ina bazan iya Rabuwa Dake ba..Laifinki ne da kin bari na gabatar da kaina da Duk haka bai Faru ba..! Yau ba sai gobe ba zan bayyana kaina Amina insha Allahu ke Rabona ce..! Jin kalamansa yasa ta Mike da Sauri Har tana neman faduwa tace"Kada kayi haka..Lokaci ya kure abunda zaka aikata bazai kawo mafita ba Amin..! Yana Kokarin Hana Idanuwansa zubar kwallah ya ke kallonta ta Duhun wajem Cikin wani yanayi yace"Menene Mafitan AMINA..? Kada kice mafitan itace na Hakura Dake..Wlh in haka ta faru Zan Lalace Amina akanki ki taimakeni kimin Rai don Allah..! Yake fada sai Hawaye Gwiwansa ya saka a kasa yana Rokonta Kada ta barsa Amina ta Rude batasan sadda ta saka Hannu ta Dago Kafadun Aminu ba Cikin kuka take fadin"Don Allah ka tashi..Na shiga uku..! Yana Dagowa bai yi wata wata ba kawai ya jawota ya Rumgume kam kam kamar wani zai kwaceta alokacin Inda tasan sanadin wannan Rumgumar Zanen kaddaranta zata fara na Tabbata da Amina bata amince ba in da Aminu yasan sanadin wannan Rumgumar Amina zata haramta garesa da har Abada bai yarda yazo ba..Sai dai ina bakin Alkalami ya Riga ya Bushe..! Amina ta kasa yin wani motsi ballatana ta kwace jikinta Tayi luf akirjin Aminu yana Fadin"Bazan iya Rayuwa baki ba Amina..Kinsan ina sonki..kinsan ina sonki in kika barni ina zan saka kaina..? Amina alokacin Tunanin bai bata ta kwace jikinta ba,tsausayin Aminu da soyayyarsa ya Rufe mata idon da bataji bata gani. Alokacin wani al"amari ya Faru wanda ya Faruwarsa ya Fallasa abubuwa Dadama kuma ya Watso wasu sirruka a waje alokacin kuma Zanen kaddaram Amina da wanda Allah ya Turo mata cikin Rayuwarta ya fara..! Suna cikin waannan yanayin suka ga an Dallaresu da Hasken Fitila Lokaci Daya Cikin Muryansa da ko barci Amina Take bazata taba bace Mata ba yace"Su waye anan..? Dam..! Gabanta ya amsa hakama na Aminu arude ta Dago kanta Daga Kirjin Aminu karaf Hasken Fitilan ya Hasketa Tar Cikin Faduwar gaba da wani yanayi ya Jafar ya Zaro ido Cikin Tsawa yace"AMINA..!!! Yadda ya Kira sunan ne ya Girgiza Zuciyar Amina Hanjinta suka Cure waje Daya kuma har Alokacin Tana Rike da Aminu shima yana Rike d ita Rudewa yasa sun kasa Sakin juna..! Hamida Daga cikin gida ta kalli Hanne tana Fadin"Hanne gabana na Fadi..Inaji ajikina mun rusa komai fa..! Ita kanta Hannen Jikinta rawa yake gabanta na Fadi Cikin Tsoro tace"Nima Hamida..Na farajin wani iri na fara Nadama fa Hamida..! Hamida ta Bude baki zatayi mgana kenan Muryan ya Jafar ta shiga kunnensu sanda yake fadin"Innalillahi Amina me zan gani..? Iskancin naki har yakai kikawo wani kato a kofar gidanku kuna shanshanci Amina..! Dam gabansu ya fadi atare suka kalli juna suka zaro ido kafin suyi Rige rigen Lekawa ta kofa sai da suka kusa Sakin Fitsari a wando ganin ya Jafar Tsaye bakin lungun da su Amina suke ya Hsskesu da Hasken Fitila Fuskar nan kamar an aikomai da Sakon mutuwa.! Hamida ta Damke hannun Hanne suna karkawa Lokaci daya suka Hada Baki wajen fadin"Mun shiga uku..Mun kara saka Amina acikin Bala"i..! Agaban idonsu ya jafar ya taka ya Shiga lungu sai gani kawai sukayi ya Tunkudo Amina saida Hijabin jikinta ya Hardeta ta Fadi yaraf Cikin Fitan Hayyaci ya saka kafa ya Shureta yana Fadin"Tashi Tashi munafuka yau Allah ya Toni asirinki..Daman wannan Idanuwanki bakomai a Cikinsu sai iskanci Kee Amina yarinyar dake Rumgume da wani kato Amina..? Tashi muje gaban Aba na Sanar dashi Abunda nagani tashi nace don Ubanki kafin nayi miki illah yanzu nan..! Yafada yana kokarin kara Shurinta da Sauri Aminu ya rikosa Cikin wani yanayi yana Fadin"Kadaina Dukanta..Don Allah ka Tsaya ka Bincika wlh ba abunda kagani bane gaskiya..Ina son Amina kuma auranta zan yi..! Ya jafar ya Fincike hannunsa bai yi wata wata ba ya Daga hannu ya Sharara ma Aminu mari lokaci Daya ya Nunasa da yatsa yana Fadin"kai har kana da bakin mgana Lallatacce kamar ka..?Allah ya isa Tsakanimu dakai Tunda kayi Samadiyar batamana kanwarmu kuma kabar kofar gidan nan kafin na Fito da matasan gidanmu su Illata ka yanzu nan..! Shi bai Damu da kansa ba Amina yake kallo tama kasa kuka Zuciyarta ya Soye ta riga ta sani ajikinta tanaji Ba wani Tsumi ba Dubara ayadda ya Jafar ya gansu Allah ne kadai zai iya Fitar da ita shiyasa ta kasa motsi ko mgana! Yana so yayi mgana bakinsa yayi Nauyi yana ji yana gani Ya Jafar ya isa ga Amina ya taso ta Bai yi wata wata ba ya Daga hannu Dama da Hauni ya Dauketa da maruka da sai da ta Koma ta Kife kamar zata Fadi ya Fizgota yana Fadin"Muje agaban Aba da mamanmu mai kareki..Ki Fada musu Tun yaushe kika fara Wannan Lalacewar Amina..! Ya karishe Fada yana ingizata gaba,Aminu ya taka ya Bisa ya Dagamai hannu yana Fadin"Karka Nuna min iskanku na yan Tasha..Nima In akabi ta wani Fanni na Fika tashanci wlh zan kara Dauke ka da mari Kaji ma na rantse in baka bace Daga gani na ba..! Ayadda Ya Jafar yake zai aikata Abunda ya Fada din sai ya koma baya Cikin Raunin Murya yace"Amina komai zai yi Daidai..Zan tafi Yola...su Alhaji Baba zasu zo nema min Auranki..! Amina tana jinsa tana so,tacemai kada yayi haka,ammh kuma a wannan gabar bazata iya mgana ba Domin mganar bata da wani amfani..! Hamida da Hanne suna jin Bude gidan ya Jafar suka Rumtuma zuwa Cikin gida ba inda jikinsu baya rawa Saboda Abunda zai iya Faruwa yau..! Haka Ya Jafar yake iza keyar Amina kamar wacce tayi sata Yana tafe yana Dukanta Fadi yake"Amina kece Rumgume da wani kato..? Yaushe kika fara wannan lalacewar..? Yana Fadi yana Dukanta Saboda Wani Bakinciki ke kara kamasa in ya Tuna da yadda yaga Amina Rumgume jikin wani kato..! Hanne da Hamida Dakinsu Hamida suka Fada suna Haki ya Zeenatu na kwance ta Mike tana kallonsu,Cikin wani yanayi tace"Lafiyarku kuwa..? Kasa mgana sukayi jin Muryan ya Jafar Tsakar gida yana Kiran sunan Aba gabadayansu suka kara Tsurewa Hamida da Hanne suka kamkame hannun juna,Saboda Tsoro ya Zeenatu ne ta Mike tana Fadin"Muryan Ya jafar nake ji..? Meya faru kuma..? Tafada tana mikewa Tsakar gida ta Fita Daidai Sanda Aba ya fito shi da Yaya Sai kuma Mamanmu data fito Daga Dakinta Dankwali a hannu Tana Fadin"Lafiya hayaniya me nake ji..! Ya Jafar Amina ya Tura gaban Aba sai da ta Fadi cikin Fushi yake fadin"Aba Gatanan ta fada muku tun yaushe ta fara Lalacewa..Yanzu nazo zan karbi mganin da za"a shafa ma mai sunan Mallam akansa kawai naci karo da yarinyar nan Rumgume ajikin wani Dan iskan kato ajikin gidan nan Aba..! Gabadaya jikin Aba sai ya fara rawa Yaya,kuma Kirjinta ne ya fara Lugude Yayinda Mamanmu ta saka Salati tana Fadin"Innalillahi...! Haka kawai take fada Hanne da Hamida dake cikin Daki suka kalli juna suka Gwalo ido,ya Zeenatu kuma zuciyarta sai da ta amsa Amina bazatayi haka ba Halinta bane..! Ba wanda ya Lura da Aba Jiri ya kwashesa sai da ya Saka kafa ya Ture Amina Dake gabansa takasa kuka sai na Zucci Domin kukanta bazai taba Cetonta ba..! Kadan ya Rage bai Fadi ba Yaya tayi Saurin Rikosa ta fashe da kuka Bango ya Dafa yana Fadin"Jafar fitarmin da ita Daga gidana..Ka fita da ita ban Haifi Dan da zai zamenin zakka ba ta ficemin Daga gida..! Yake Fada sai hawaye Sharr Mamanmu ta Fashe da kuka tana Fadin"Na shiga uku ni balaraba..In ka Koreta ina zataje Abbansu..? Wlh Amina bazatayi haka ba Halinta bane..! Ta karisa wajen Amina ta Dago tana Fadin"Amina ki tashi ki fadamusu karya ne..Abunda Jafar ke fada ba gaskiya bane..! Da manyan Idanuwanta Take kallon Mamanmu Lokaci ya kure bazata iya kare kanta ba batasan sadda tace"Gaskiya ne Mamanmu..Gaskiya ne ya ganni..Rum..Rumgume..! Bata karisa ba Mamanmu ta Dauketa da Mari Cikin kuka take fadin"Karya ne..Ba gaskiya bane..! Take Fada tana kuka kamar Ranta zai Fita Zuwa Lokacin hatta Hanne da Hamida sun fara kuka Aba kuma Yaya na Rike dashk Dafe da Bango Yana Hawaye..! Ya Jafar ya kalli Aba yana Fadin"Aba kadaina kuka..Wannan yarinya Dukan mutuwa zan mata yanxu nan..Wai har dan iskan yaron yana Fadin sonta yake yi zai aureta..! Aba ya girgiza kai yana Fadim"Na Rantse da wanda Raina ke hannunsa bazan aura ma Amina wannan yaron ba..Jafar Amina bazata samu abunda Take so ba..bata isa ba..! Yafada yana jin wani Takaichi da Bakinciki Ya Jafar Cikin mamaki yace"Dama kasan shine Aba..? Aba ya jinjina kai yana Bama Jafar Labarin abunda ya faru bai gama ba Ya Jafar ya Finciki Amina ya Fara Dukanta yana fadin"Kafin ki kashemana Uba ke zaki fara Binsa Amina..! Dukanta yake yi kamar Allah ya aikosa Ba wanda ya hanasa Yaya kuka take tana rike da Aba Dake fadin"Hadiza kamani muje ciki..Jiri nake gani..! Ya Zeenatu ma kuka take tana Fadib"Mamanmu ki cece Amina ya jafar zai kasheta..! Mamanmu Dukewa tayi tana Fadin"Jafar kadaina Dukanta don Allah..Jafar kabari..! Take fadi ko jinta bayayi sai ma Karisawa da yayi ya karyo ganyen Bishiyar Dake Tsakar gidan ya Shiga Lafta ma Amina wacce bata kuka ko kadan sai na Zuucii awannan gabar ta gagara tana jin kada ma wani ya Ceceta abarta ta Mutu ta huta ta saka Mamanmu kuka da Yaya,Aba ma yana kuka Saboda ita ai bata da wani amfani acikin wannan Rayuwar..! Hanne ce Jikinta na Rawa da wayar Hajiya Dake hannunta ta Kira Baba Mallam wanda mamaki ya kamasa ganin Hajiya zaune gefensa suna Hira Cikin mamaki yace"Yau kuma Zolaya kike ji ne Abu..? Kallonsa tayi kafin tace"zolayar mene Mallam..? Wayarsa ya nuna mata yana Fadin"Kirana akeyi da wayarki fa..! Cikin mamaki tace"To lafiya..?Wayata tana Daki na barta fa! Jin haka yasa bai ce komai ba ya Daga Kiran kukan Hanne ya fara ji tana Fadin'Baba Kazo gidan Baba Sa"idu..Ya Jafar zai kashe Amina da Duka kazo da sauri..! Baba Mallam Zumbur ya Mike Cikin tashin hankali yake tadin"Hajiya Wani abu ya sake faruwa..Muje gidan Sa"idu..! Hajiya ta fara salati Hankalinta tashe ta Rarumi hijabinta ta saka Baba Mallam na kan gaba suka Fice Daidai Anty Amarya ta fito zuwa shashen Mallan taga fitarsu Cikin gaggawa tasan ba Lafiya itama sai ta Rufa musu baya ganinsu sun shiga gidan Baba Sa"idu yasa aranta tasan ba Lafiya Domin Baba Mallam baya zuwa gidan Baba Sa"idu haka kurum wani abu bai faru ba. Cikin azama tabi bayansu Domin tana son Taga abunda ke faruwa..! Abunda Su Baba Mallam suka gani Sai da Hankalinsu ya tashi Ya Jafar yayi m Amina Dukan kawo wuka Baba Mallan ne ya karbe sandan Hannunsa yana Fadin"Jafaru ashe baka da Hankali ban sani ba..? Ya jafar na haki yace"Baba Mallam so take ta kashemana iyaye da bakincikinta..Shanshancinta ya wuce Tunanimku yau fa ganinta nayi a nan kofar gidan Rumgume jikin wani kato Mallam..Amina fa nawa take..? Har ta gama lalacewa haka bamu sani ba..Shine kafin ta kashe su gwara ita ta Fara Binsu..! Karaf manganganun akunnin Anty Amarya Data shigo Salatinta kawai akaji Tana Fadin"Innalillahi wannan yarinyar Tabbas zakka ce..Iskancinta nata har yakai haka bawanda ya sani..? Kallonta kawai sukayi kowa ya kasa mgana Hajiya,Amina ta Duka ta Rumgume jikinta Duk ya Fashe da Duka Fadi take"Jafar kayi dukan ganganci..Ba haka akeyi ba..! Mamanmu na gefe tana ta kuka ita da Zeenatu harta Jawaad Dake barci hayaniya ya tadashi ganin Dukan da Ya Jafar kema Amina sai shima ya Fara kuka..! Baba Mallam Hankalinsa ya tashi Ya kalli Jafar yana Fadin"Ina Sa"idun..? Da kyar yace"yana Dakinsa..! Baba Mallam ya wuce gaba yana Fadin"Hajiya ki taikama Mamana..Kai kuma muje Ciki..! Da haka ya tasa Jafar suka shiga Falon Aba Hajiya kuma Da Mamanmu suna Hawaye suka Daga Amina da Idanuwanta basa Buduwa Sai faman wash Wash take da kananun kuka Kilama ya Tardagata inji Hajiya Zeenatu ta kama musu suka yi Dakin Mamanmu da ita sai Lokacin Hamida da Hanne suka fito ganin Halin da Amina ke ciki suka Hade kai suna ta kuka Anty Amarya Fadi take"Ruwan zafi za"a Dafa ayi mata gashi..Allah ya kyauta bai mata karaya ba kinsansu in suka Fara Duka kamar mahaukata..! Hajiya taji kamar ta Make bakinta sai dai batayi mgama ba batama san ya akayi tasan wani abu na Faruwa ba domin Anty Amarya sai dai ta Fadama wani Halinta..! Ashashen Aba kuwa Baba Mallam suna shiga suka gansa kwance kan kujera Takure yana rawan Sanyi Fadi yake"Hadiza sanyi nakeji ki sakamin bargo..! Baba Mallam ya Duka agabansa yana Fadin"Ashh Sa"idu me zan gani haka..? Yana jin muryan Baba Mallam ya Bude ya Rarrafa ya tashi Zaune yana Cijewa Baba Mallam ya rikesa Hannunsa ya kamkame yana Fadin"Baba don Allah ina so cikin Almajiranka masu karatu ka Tallata Amina in akwai mai so..Bana so wunin gobe ya kare ban aurar da Amina ba..Ina jin tsorom wani abu ina Fargaba kada watarana Bakincikinta yayi ajalina..! Baba Mallam yace"Baza "ayi haka ba kana cikin Fushi Sa"idu. Mu Tsaya mu bincika zuwa gobe zan yi mgana da Mamantawa kan yaron Dake zuwa wajenta in har ya Chanchanta zan bashi Mamana..! Jikin Aba na rawa yace"A"a Baba..Na riga nayi Rantsuwa ko bayan Raina Amina bazata samu abunda take so ba..Bata isa ta fita Zakka ba..Kada ka Saurareta Nidai ko Waye ka aura mata ta bar gabana na Daina ganinta ko zan samu Saukin Abunda nakeji..! Baba Mallam yayi shuru yana kallon Baba Sa"idu ganin haka yasa ya kara Rike hannunsa sai Hawaye sharr yana Fadin"Kada kace A"a Baba Mallam Kayimin wannan alfarman a mtsayin ka na Uba gareni ka yafemin in har ahalima suna goga maka bacin suna ka yafemim..! Ya karishe Fada Cikin kuka,Da Jikin kowa saida yayi sanyi Baba Mallam yace"Kul..Kar na Sake ji..Kai jinina ne Sa"idu har gaban Abada..Kada ka Damu Zan aurar da Mamana kamar yadda ka Bukata sai dai bazan mata auran kaskasaci ba kafin waye wan garib gobe Allah zai bayyanamana Mijinta mafi Alherinta aduk inda yake Sa"idu kayi hakuri kada ka aibatata kila ita irin Tata Kaddaran kenan..! Aba bai Sake mgana ba Tari ya Sarkesa kamar zai sheka Ya Jafar da Yaya suna Rike dashi yaya kuka kawai take Yadda take ji aranta baya Misaltuwa ita ta Haifi Amina Radadin da kowacce uwa take ji in Wani Daga Cikin D'anta ya zama zakka..! Ganin Halin da yake ciki yasa Baba Mallam yace su tafi asibiti haka kuwa akayi Ya Jafar ya Tuka Motar Mallam dashi da Yaya suka tafi asibiti da Aba su Hajiya kuma suna tare da Amina da tasha gashi Ta samu Targade a Hannunta na Hagu da gocewar kashi a Kafarta Mamanmu da Hajiya suka Shafe mata da man zafi tana Hawaye sunayi Mamanmu ma kasa zama tayi ta koma Cikin Bedroom dinta tana kuka Anty Amarya na nan bata tafi ba da anyi abu sai ta Tafa Hannu tana Fadin"Oh..Allah dai ya shiryamana..An haihu dai a Ragaya..! Sai da Hajiya ta gaji ta tanka mata da Cewa"Ki kama bakinki Domin kema Uwace..Akwai Sa"adatu da Sabeeha agabanki bakisam ina Kaddara zata kaisu ba! Jin haka yasa ta Fara Fadin Hajiya na mata Mugun fata Cikin gatsali tace"Allah ya Tsareni kowa yasan ya"yana basu fita zakka ba..Daman ai wanda yasiya Rariya yasan zata Zubda Ruwa..! Ba wanda ya kara bi ta kanta kuma taki Tafiya kamar mayyah har sai chan Dare Baba Mallam ya Dawo Jinin Aba ne yayi sama An bashi gado ya Jafar na wajensa zai kwana sai alokacin suka koma gida bayan Baba Mallam ya kwantar ma da Yaya da suka Dawo tare ita da Mamanmu hankali da kalamai masu sanyaya rai sun Daina kuka Amina kuma ta samu barcin Wahala Baba Mallam yace zuwa da Safe mai gyaran Targade zai zo ya gyara mata. Sanda suka koma gida Dagashi har Hajiya sun kasa Runtsawa Fadi kawai Take"Na kasa gane meke Faruwa Mallam..? Nasan Jafaru bazai yi karya ba..Nasam jikina na bani Amina ba haka take ba..! Baba Mallam yace"Wani al"amari ne da Allah kadai yasan me ya Lullube aciki..! Nan ya shiga Fadamata yadda sukayi da Baba Sa"idu ta sauke Tagumi tana Fadin"Kai..wata sabuwa to menene Mafita..? Baba Mallam yace"zan kwana Istikara Zuwa Safe Boyayyan al'amarin zai bayyana Hajiya kema ki tayani..! Da kai ta amsa mai,Tabbas sun kwana Gayama Allah Hajiya ce ma wajen Uku na Dare ta kwanta Baba Mallam sai karfe 4 ya iya barci saman Darduma bai tashi ba sai da yaji wayarsa Dake cikin Aljihunsa na Ringing yayi Zumbur ya Mike yana Lalubota yaga DANMALLAM.. ! Ne ke kiransa ajiyar rai ya Sauke ya Daga wayar da Sallama Dagachan bangaran Umar ya amsa cikin Sanyinsa yana Fadin"Baba..Nasan yanzu asuba ne a Nageria shiyasa na Bugo Domin na samu ladan tashinka Duk da nasan kila ma kana masallaci..! Baba Mallam ya Mike a kasalance yana Duba agogon bangon Bedroom dinsa 4:55pm na asuba..! Cikin karfin gwiwa yace"Na makara yau Umaru..Naji Dadin kiranka Allah yayi maka albarka..! Ya amsa da Amen Cikin Farinciki kafin suyi sallama suna gama wayar Baba Mallam yayi kasake na wani Lokaci kafin Lokaci Daya Mirmishi ya mamaye Fuskarsa Hajiya ya kallah Dake barci ya karisa ya Bubbuga Gefen gadon yana Fadin"Hajiya..Hajiya..! Mika tayi Cikin Tattatusan lafazi yace"Ki tashi mun makara sallar asuba..! Mikewa zaune tayi tana Mutsike ido Lokaci Daya tana Fadib"Mallam kasamu mafita kuwa..? Wlh da yarinyar nan na kwana araina ita da Sa"idu..! Cikin Mirmishin data kasa gane masa yace"Kada,ki damu..Cikin ikonsa ya kawo mana Mafita tashi kiyi sallah ki shiga gidan Sa"idu ni kuma Daga masallaci asibiti zan tafi na Dubasa..! Kai ta gyadamasa tana kallonsa ya saka akyabbansa da Rawaninsa ya Fice acikin ranta tana Tunanin wata mafita Mallam ya samu wannan Fara'ar dake fuskarsa ta bayyana Koma wata Mafita ce ta zauna sosai acikin Ran mallam din.! Ina godiya sosai masu sharhi yan wattapad ina gaisuwa..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️21* Suna idar da Sallar Asuba Baba Mallam bai Tsaya ba Ya Nasir ya Tukasa zuwa asibitin Tunda shima nan ya sallaci sallar asuba Ya jafar tun Daran jiya ya kirashi ya fadamai kafin su tafi sai da Baba Mallam ya Umarci Shamsu daya kira Mallan ya"u mai Dori yazo ya Duba Amina..! Haka kuwa akayi gari na waye bakwai na safe Ya shamsu yazo da mai Dorin,Koda yaje Hajiya Babba tana gidan Amina jiki yayi Tsami sai faman kuka take ashe kadan tayi Domin wajen gyaran Targade da Goshewar data samu sai da ta raina kanta sai da su Hajiya da Mamanmu suka Riketa Hamida da Hanne suna ta kuka Ranar ko shirin zuwa Hadda ba wanda yayi acikin gidan sai dai chan su Sa"adatu ne Idi Direba zai kaisu..! Yaya kuwa Hada hadar abun karin da zata kai asibiti take yi ko afuska bata bayyana wata damuwa game da Amina ba Ita ta Aba take yi,ammh sai dai karkashin Ranta Damuwa ne Dankare wanda Tsabar kawaicinta yasa bata bari a Fahimceta ba, sai dai fa Uwa uwa ce kuma bazata Haifi abu da Cikinta tace kuma bata kaunarsa ba sai dai kawaici da wasu abubuwan da kansa Uwa ta kauda kai kan abunda ta haifa sanin Halinta ma ba wanda yabi ta kanta Domin kowa yasan Yaya bata taba Shiga Sha"anin Amina sai abun yaci Tura yakai mata makuran da zata tanka..! Ya bada mgani an shafa mata Cikin kwana Daya ammh Amina ta Fita Hayyacinta ta rame sai ido,Tasha wuya cikin kwanakin Wuyan da bazata taba mantawa da ita ba Hamida da Hanne sun fi kowa sanin Amina tafi kusa dasu shiyasa lamarinta yafi Damunsu gabadayansu suma Suku suku suke kamar basu da Lafiya sun tasa Amina da Tagumi tana kallonsu sai dai yau karon Farkon Bakin Amina ya Mutu bata mgana sai ido sai kuka acikin Ranta wani abu ne mai Girma Tana ji ajikinta komai yazo karshe ta rasa Aminu shima ya rasata sannan abu mafi girma tana jin kamar wata Kaddarace zata faru da ita yasa abubuwa suka kwabe mata Lokaci Daya sai dai koma menene Tayi alkawarin bazatace komai ba Tunda mai Faruwa ta Riga ta Faru babu Tsumi babu Dubara..! Dakyar Hajiya ta Lallasheta tasha Tea da Panadol Saboda Zazzabin Jikinta sai ta samu barci sai alokacin suka samu Daman karyawa Mamanmu da Yaya suna shirin Tafiya asibiti duk da sunyi waya da Ya Jafar yace ya Dawo gida Ammh Baba Mallan nachan suka barsa tunda safe Ruwan zafi ma Nasir ya koma gida ya Taho dashi Da kayan Tea..! Ya Abida ta shigo ta Duba Amina kafin su wuce Hadda ya zeena ma bataje ba su Sa"adatu ne suka tafi dasu ya Akilu sai Umaimatu,Misalin karfe Tara na Safe Hajiya Babba da Yaya da Mamanmu da Anty Shamsiya matar ya Jafar suka tafi asibitin da aka kwantar da Aba domin su Dubasa shi kowa kagani rai da zuciya ba Dadi. Wani private Hoptal ne Daki na Musamman Aba ke ciki Vip. Suna shiga Baba Mallam kadai suka Iske awajensa Aba din yana ta barci su Mamanmu suka gaisheshi Cikin girmamawa ya amsa yana Fadin"Mungodema Allah..Ya jikin uwar tawa?Nace shamsu yazo da Mallam ya"u sun zo kuwa..? Wannan karon Hajiya ce tace"Eh har ya gyaramata ya bada mgani an shafa mata tasha mgani koda muka fito ta samu barci.. Ya shi Sa"idun..Ya farka kuwa..? Baba Mallam yace"Eh ya farka da Safe jikinsa da sauki sosai bai dade da komawa barci ba koda Nasir ya bar nan muna ta Hira dashi..! Gabadaya suka amsa da Alhamdulillah mai sunan Mallam ne Dake bayan Shamsiya ya fara kuka Mallam yace Hajiya ta karbo shi ,ta kwatoshi daga baya Ta mikama Hajiya ita kuma ta mikoma Mallam ya saka Hannu Biyu ya karbesa yayi wayau Yayi girma kansa ya dafa yana Tofamai addu"a sai da ya gama sannan yace"Ciwon kunnin nasa fa.? Kan Anty Shamsiya na kasa tace''Yayi sauki..yadaina kukan tun jiya daddare..! Baba Mallam ya gyada kai yana Fadin"In muka koma gida zan bama Jafar wani mgani ku rika Digamai Daga Saudiya nazo dashi..! Kai ta gyada kafin tace"Jiyan ma Da daddaren wajen Mamanmu yacemin zai zo ya karbo masa wani mgani shine baidawo ba sai waya naji yana Fadamin yana Tare da Aba a asibiti..! Baba Mallam yace"Wlh kuwa..Ammh ai da sauki yana ta cewa ma a sallameshi ya koma gida..! Mamanmu tace"Daman ai baisan zaman asibiti..! Hajiya tace"Sai hakuri ya bari ko zuwa gobe ne in ya kara jin Sauki..! Suna cikin mganar ne Aba ya Farka Daga barcin daya kwasheshi suka fara Rige rigen mai sannu Mamanmu tana kokarin Taremai Filo Sai Yaya ta rigata sai ta sakarmata Ya jingina da Filo sannan ya tashi yana amsa gaisuwansu Lokaci Daya yana Binsu da kallo cikin Tsausayinsa Yaya tace"Ga Ferfesun kayan ciki nayo maka..In zubo maka zakaci..? Mirmishi ya saki kafin yace"Zubomin Hadiza..Nagode Allah yayi miki albarka..! Akunyace ta amsa ta Duka tana Zubamai Cikin Filet din da tazo dashi,Kadan yace ta zubamai ta mikamai ya karba Baba Mallan na Fadin"Ashe girkinta kake jira shiyasa bayan Ruwan Tea kaki cin komai..Duka abincin da matan yaran nan sukayi bai taba komai ba Hajiya..! Dariya tayi tana Fadin"Sa'idu ne fa..Tun farkon auransu Girkin Hadiza yasa ya faramin yajin cin abinci kaga Tunda yayimin yaji nasan Hadiza ta Curi Tuta..har yayi aure adakina Sa"idu ke cin abinci Mallam har haushi yake ji na kwace masa yaro.. Gabadayansu Dariya sukayi Saboda yanayin yadda sukayi mganar Aba ma sai da ya Murmusa bai ce komai ba yana kallon Yaya basu sani bane aduniya ita kadai ce macen da yake Fatan Har aljannah ta zama matarsa Saboda kyawawan Hallayarta Tunda suka zama miji da mata shekaru aruaru bai taba ganin Ranar data Daga Muryansa sama da tashi ba..Yana kokarin Boyewa ne Sai Hadiza matsayinta Daga Allah ne ko ya Boye Kaunarta bazai taba Boyuwa ba Tana da wani irin girma acikim Idonsa da Rayuwarsa da ba wanda ya sani ita yake kallo yana jin zuciyarsa na Sauka Duk da cikin Halin Dayake ciki ita kuma kanta na kasa tana da kunya ballatana gaban Hajiya da Baba Mallam..! Yaci kuma Ferfesun duka ya Cinye ya Dora da kayan marmari sai gashi garas dashi sai dai kallo Daya zakayimai kasan yana cikin Damuwa,Ya Jafar daman bai shigo ba sai gasu shi da Nasir sun shigo suka kara gaida Aba daganan su Mamanmu sukayi sallama dasu Jafar zai maidasu Gabda zasu fita Hajiya ta dawo wajen Baba Mallam daya mikama Jafar takwaransa yana jadaddamai yazo zai bashi wani mgani Jafar din ya Juya kenan Hajiya ta kalli Baba Mallam tana Fadin"Mallam naji bakace komai ba Har yanzu..? Kallonta yayi yana Mirmishi kafin yace"Nazir ya Kirani da Safan nan yace yana ta kiran wayarki baki Dauka ba..Sai daga baya Abida ta Daga kiran tace baki nan kina gidam Sa"idun..! Kauda mganar yayi ta sani tace"Ina na sani..Gida na bar wayar..Suna Lafiya ko..? Yace"Lafiya lau..Shehin ne dai ba Lafiya yacemin kwanansu Biyu asibiti Ciwon ciki ammh sun dawo gida shine nake fadamai nima ina asibiti ga yayansu Sa"idu ba Lafiya..! Hajiya tace"Assh..Allah ya Sauwake in na koma na natsu zam kirasa..! Kai ya gyada mata bai ce komai ba,sai ta kalli Aba da hankalinsa baya kansu ya Lula Tunanin Halin da Amina ta Jefasa Cikin Damuwa Hajiya tace"Sa"aidu wannan Tunanin babu Riba cikinta..Ka kwantar da Hankalinka ba wata mtsala insha Allahu..! Aba ya sauke Numfashi kafim yace"Hajiya in ban aurar da Amina yanzu ba..Watarana Jidalinta zai iya ajalina..Kinga Hadiza bata mgana ko..? Na rantse tafini jin Dacin Amina tafini Sanin Ciwonta Domin itace uwa gareta ina Tsoron yadda take shanye abubuwa watarana Amina ta Dauko abunda zai yi sanadiyar zuciyarmu ta Buga Dukkanmu mu fadi mu mutu..! Hajiya ta kama baki tana Fadin"Assh..Haba Sa"idu bama zai taba Faruwa ba..! Tari ya farayi sai kuma jikinsa ya fara rawa Da Sauri Hajiya tace"Mallam yace komai zai daidaita ko ba Haka ba..? Tafada tana kallon Mallam din wanda ke kallonsu bai ce komai ba Rawanin kansa ya gyara kafin yace"Insha Allahu..Zan Daura ma Amina aure in an idar da Sallar azahar da yardan Allah..! Baba Sa"idu da Hajiya suka kallesa da mamaki Aba ya rausayar dakai yana Fadin"Ina fata da bada wannan Lalattacen yaron da suka gama Lalacewa bane ko..? Baba Mallam ya yi mirmishin su na manya kafin yace"Bashi bane Sa"idu..! Hajiya tace"To waye ne Mallam..? Sai da ya kara Murmusawa kafin yace"Da wanda Allah ya kaddara..Shine dai wanda Allah daman ya Rubuta Mijinta ne dashi za"ayi..! Hajiya daman tasan bazai fada ba Tunda bai iya fadamata ba kuma bai Fadama Sa"idu ba to Tattabata bazai Taba Fadama kowa ba..! Aba ne yace"Kada ka Tursasama Mutumin Kirki sai ya aureta Mallam..Ka hadata da irinta sannan ka Sanar da kowaye halinta Baba..Kuma ina so aje a gwada Amina kada yazo wajen Lalacewarta ta Samo wata cuta..! "SA"IDU..! Baba Mallam ya katsesa Cikin Tsawa da Bacin rai kafin yace"Kul na Sakejin wannan mganar daga bakin ka..ina da yakinin Har Abada acikin zuru"ata baza"a samu bara Gurbi ba...Duk da Allah na Jarrabatan bayinsa ta kowani Fanni Ammh ta wannan gabar ban yarda ba..Amina bazata taba Rusa Tarbiyarmu ba Sa"idu ba abunda zan ce ma wanda zai aureta illah ya Rikemin ita Amana kuma in Cucuta koda abayan Idanmu ne Ban yafe MASA BA..! cikin kaushinsa ya karishe mganar da ta ja Hankalin Aba da Hajiya suka kalli juna bai kuma basu zarafin mgana ba ya kalli Hajiya yana Fadin"Kinsan suna jiran ki ko? Kai ta gyada kafin tace"Shikenan Allah ya kara afuwa..! Har ta juya zata tafi Baba Mallam ya Kira sunanta ta juyo Cikin bacin ran da bai barsa ba yace"Ki fadama su Balaraba kada wata cikinsu ta kira yaran nan dake gidan auransu tace zata Daga musu hankali ko Husai ban yarda afadamata ba..!bana so a adaga musu Hankali..! Hajiya tace"Insha Allahu ba wacce zata ji..! Kai ya gyadaa mata ta juya ta cigaba da Tafiya har takai kofa zata fita ya Kira sunanta wannan karon a Taushashe ta juyo tana Fadin"Mallam..! Kai Tsaye yace"Umaru ya kiraki kuwa..? Cikin mamaki tace"A"a rabona dashi Tun shekaranjiya da safe..! lafiya kuwa.? Mirmishi yayi kafin yace"Bakomai..Allah ya kaiku gida Lafiya sai na dawo.! Hajiya ta jinjina kai kafin ta Fice ya bita da kallo Daman ai yasan bazai taba Kiranta ba Shi ya Haifi Umar ammh yana Daraja kyakyawan Dabi"ansa..! Aba ne yace cikin Raunin Murya"Kayi hakuri Baba..! Hannu ya dagamai kafin yace"Nace ne kada na sake jin irin mganar makamancin wannan abakin ka..Ba hakuri nace ka bani ba..! Cikin Sauri Aba yace"Insha Allahu.. Sai alokacin Baba Mallam ya saki Fuska yana Fadin"Allah yayi maka albarka kaida zuru"arka Sa"idu.Har Abada ban taba Nadamar samunka Cikin zuru"ata ba..Ka warke da wuri ban shirya rasa Da"a na farko ba..! Ya karishe Cikin barkwamci Da sai da Aba ya Murmusa Lokaci Daya Hawaye suka cika kwarmin idonsa yake Fadin"Nagode Baba..Nagode Ban taba jin kai ba Uba kake gareni ba..Ina Alfahari dakai..! Baba Mallan yayi wani kayattacen Mirmishi kafin yace"Nima ina Matukar alfahari dakai Sa"idu..! ******* Tana cikin Tiolet din Bedroom dinta taji Ringing din wayarta Allah yasa ta Gama wankan ta Dauro babban zaninta ta fito wayar tana kan Mirror dinta ne Jikinta yana digan ruwa takai Hannunta saman wayar wanda taga yana kiran nata ne yasa taji gabanta ya Fadi..! "MALLAM..! haka kurum mallam awannan Lokacin bazai kirata ba,Dazu Shamsu ke fadin yana asibiti wajen Sa"idu Har wayar ta kusa yankewa bata Daga ba sai Daga baya ta Daga kiran tana Fadin"Assalamu Alaikum Mallam..! Dagachan Haraban asibitin Baba Mallam yace"Marliya kina ina ne..? Cikin mamakinsa tace"Ina gida mana Mallam..! Kai Tsaye yace"Marliya abunda ya faru jiya gidan Sa"idu kuskure ne da Rashin Fahimta ko..? Cikin Mamakinsa da Tunanin inda ya Dosa tace"Hakane..! Cikim Dattakonsa yace"To mu barsa ahaka..Kada na sake naji mganar nan ta fita..In har najita a waje Nasan kece..Bana son surutu da mgana Hajiya kinsani bata da wannan Halin Saboda haka ki kiyaye..! Anty Amarya taji ta Muzanta Ranta ya baci wato Hajiya ba ruwanta itace mai Surutu ko lalle ne Mallan dinnan.! Danne bacin ranta tayi tana Fadin"Ah..Wlh ban fadama kowa ba Mallam..yanzu dai nake shirin shiryawa na shiga gidan na Duba Amina ya jikin Sa"adun..? Fata ya samu Sauki..! Cikin son Dakile mganar yace"Yaji Sauki..Kada ki fita ko"ina nima ganinan zuwa. ! Bai jira cewarta ba ya Datse kiran yana wani nazari yasanta da kananun mgana sarai shiyasa ya taka mata Burgi in ba haka ba,kafin wani Lokaci ta gama Fesama ya"yanta su kuma su fara yawo dashi mgana har ta fita wacce bata da wani amfani.. Ita kuwa Anty Amarya Sororo tayi da waya a Hannunta mamaki bakin ciki da Kishi sun Turniketa wayar ta Dangwar nan saman gado tana Fadin"Aikin banza..Abunda kake son ka Rufe mallan bazai taba Rufuwa ba..Ko ba"a bakina ba Lalacewar Amina sai ya fita Duniya..! Abunda bai sani ba ta Fadama ya"yanta Sa'adatu da Jidda da Sadiya Jidda ce kawai bata Dauki mganar ba Ammh Sa"adatu har tana Fadin daman idanuwan Amina na rashin gaskiya ne sannan abakinta Anty Amarya tasan Amina na karancen karancen Littafan hausa Sadiya dai da Uwar ta fadamata batace komai ba Domin bata cika Hayaniya ba. Wayar Sakina tayi ta nema ta Tsegunta mata bata sameta ba Shiyasa da Tuni Labari ya isa Saudiya Arabia..! Tana shiryawa tana Tsaki ita kadai ta rasa me Hajiya Babba tafi su da Mallam yake Fifitata akansu ta manta tun Tale tale Take tare da Mallam din kwafa tayi afili tace"Daga ita har Sa"idun duk sai nayi mganinsu Algumgumai duk su ke zuga Mallam..Da basu da Tuni nice Tauraruwa awajensa da gidan gabadaya..! Abunda bata sani ba,ba irin Mallan ake ma haka ba ko ta manta Malami ne wanda bai zauna ba,kariyar Allah Tana Tare dashi kuma ilkonsa bazai bari acutar da bawansa ba..! Baba Mallam na asibiti kafin ya baro ya Kira ya Jafar yace ya siyamai Dabono da Goro mai yawa zai yi amfani dashi bai damu ba sanin kila Mallam din zai yi wani abu dashi sai dai abu daya ya bashi mamaki Dayace su samu sallar azahar anan masallacin gida shima gashinan zuwa..! Koda ya tafi Aba na barci Nurse tazo tamai allura kila tana saka barci ne shi kuma sai bai tashesa ba Idi Direba ya Kira yazo ya Daukesa zuwa gida Kai Tsaye Shashensa ya wuce domin ya Shirya Tunda azahar din ta kusa Shi kadai kawai yake jin karfin Gwiwa da alhafarin wani abu akaron Farko zai cika wani Burin Daya Dade acikin ransa bai Mutu ba kuma da Ransa..! Wanka yayi ya shirya Cikin Shadda Fara harda babban Riga dataji aikin Hannu ya Dora rawaninsa sai ya Fito Tar dashi Farin gemunsa na kyalli yana tashin kamshinsa kamar koda yaushe adaidai Lokacin ya samu wayar Jafar yana Fadamai ya siyo abunda yace asiya din Baba Mallan yace yana cikin gida gashinan Fitowa..! Bai Fadama kowa komai ba acikin gida yayi alwalansa ya fito Mutane basu wani mamaki ba in yana gari dashi ake yin sallah duk da akwai Limamin masallacin Mallam Muhammad Dayyab in Baba Mallam bai nna shi ke kula da masallacin har ya jafar da Ya Nasir suna bada Sallah da Mangariba haka ko isha"i Mallam din ke sakasu saboda gaba in watarana ya fadi ya Mutu ace akwai masu bin bayansa Koda Umar da Nazir basa kusa akwai Jafar da Nasir manyan dake bin bayansu..! Kowa ya zata Baba Mallam din zai bada sallah sai dai ana shiga masallacin yace Mallam Muhammad yajasu Sallar,to sai mamakin bai yi yawa Tunda yana haka sau tari dadama. Mallam Muhammad ya bada salla ana Idarwa Baba Mallam dake sahun gaba ya matsa gabansa sukayi kuskus kafin Mallam Muhammad din ya sanar da Daurin aure da za"a Daura shi yanzu Baba Mallam sai annuri yake yi Ya Jafar da Nasir Dake layi na Biyu ya yafito da Hannu Sai Shamsu Dake gefe duk suka taso suka kariso gabansa gaban Liman Mallan Muhammad..! Suna karisowa yace su zazzauna suka zauna nan gefensa Cikin Dattakonsa yace"Jafaru dauko sakon nan..! Ba Musu ya mike ya fita daman acikin Motarsa ya bar Huhun goron da Ledan Dabibon yaje ya Dauko ya kawo ya Mikama Mallam ya karba ya Mikama Mallam Muhammad yana Fadin"Araba shi Liman..araba ma Jama"a..! Ba Musu Limam ya bama Ladani Umarnin ya rabama kowa Dabino da Goronsa kamar yadda aka saba Cikin Kankanin Lokaci yabi layi layi ya bama kowa,Mutane basu yi mamaki ba sanin Daman amasallacin bazanga koda yaushe cikin kawo Daurin aure akayi shiyasa ba wanda ya damu ammh su Ya Jafar sun Tsargu ballema da suka ga yadda Baba Mallam ke ta Annushuwa kuma yana gaba gaba kan komai ko auransu Zulaihat bashi ya bada ba su ya Danmallam ne suka Zama Waliyansu..! Basu gama mamaki ba sai da Liman yace"Allah ya gafartama Mallam an gama Raba Goron da Dabinon har yayi saura ma..! Baba Mallam ya Jinjina kai kafin ya karkace ya zaro Bandir din kudi Sabbi yan Dubu Dubu ya ijiye gaban Liman Cikin Dattakonsa yace"Walicci zakamin Mallam Muhammad..? Cikin mamaki yace"Waliccin wane kuma Allah gafarta mallam..? Baba Mallan sai da ya kara Fara"ar Fuskarsa kafin yace"Waliccin Umarun Faruku zakamin aure zan kara masa ayau din nan acikin wannan masallacin..! Liman yace"To..To..Masha Allah ai babu Laifi Allah gafartama Mallam sai Waliyan ita yarinyan su matso afara siga..! Baba Mallam ya Murmusa kafin yace"Nine Waliyan Amarya..Ga Sauran yan"uwanta nan..! Ya nuna su ya jafar da suke zaune mamakin kalaman Baba Mallam ya cika su. Cikin karin mamaki Liman yace"Au kace Abun duk na gida ne..To masha Allahu..Ba bu laifi sai mu fara gabatar da siga ya sunan Amaryan..? Sai da Baba Mallam ya gyara zama kafin yace"Sunanta AMINA..AMINA SA"IDU..! Jafar da Nasir suka kalli juna kafin su juya suna kallon Baba Mallam Shamsu kuwa Kunni ya saki yana jin abun kamar almara..! Liman ya washe baki yana Fadin"To..To..Masha Allahu wannan abu yayi kyau..Allah yasa a kulla alheri..! Zamu fara gabatar da siga..Ladan ya Ciremana Lasifika..! Da Sauri Baba Mallan yace"A"a abarta Liman..! Liman cikin mamaki yace"Dokarka ce Allah gafarta Mallam ba"a Daura kowani aure cikin Lasifika..! Baba Mallam cikin Annuri yace"Na yau kadai na Sauke Dokar liman..So nake naji Sautin Tattabatuwar auran Uwata da Umaru so nake na ji Sosai acikin kunnuwana Liman..! Liman bai yi gaddama yace abar Lasifika,cikin Abunda bai fi mintina goma sha Biyar ba aka gabatar da siga aka kuma Tabbatar da Daurin auran AMINATU SA"IDU GUSAI da angonta Mijinta UMAR YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA akan Sadaki Naira Dubu Dari Cif..! Adaidai Sanda Muryan Ladan ta Karade Lasifikan yana kara Jaddada Daurin auran Amina da Umar din Akan Sadakin da uban Amarya kuma Uban ango ya Biya Mallam Yunus Abdurrahaman bazanga..! Awannan gabar Alkawarin Allah ne ya cika..! Zanen kaddara ya tabbata..! Auran ya Dauru.! "fallasa wasu sirruka ne..! Dalilin wannan auran za"a rasa rai..! Fuskokin wasu amintattu zata bayyana..! Zuciyoyin wadanda basu taba Tsammani ba zata girgiza..! Abunda basu taba zato ba ya faru alokacin da basu shiryama hakan ba..! Wasu sun makara..Saboda Alkalamin ya riga daya Bushe ko sunzo kafin Lokacin Allah bazai sauya wannan kaddaran ba SABODA RUBUTTACIYA CE..! Daurin auran daya Faru a kunnuwan mutane Dadama da suka cika da Dimbin mamaki wadanda da basu yarda ba Sa"idu ba dan Mallam bane yau suka kara yarda da mganar wasu Mutanen yadda Baba Mallan ke Hannu da Mutane kawai zaka Fahimci yana cikin Farimcikin da bai Taba tsintar kansa aciki ba shi ya Hana Jafar ko Nasir cewa wani abu suma sai sukabi ayarin yan gaisawa da Mutane suna faman amsa Fatan Alherai daga kowani bangare..! Baba Mallam Dakyar ya samu ya Fito daga masallaci su Jafar ya kallah yana Fadin"Ku scigaba gda amsan Fatan Alheri jama"a bari nayi wata waya..! Daga haka yayi nesa da Masallacin ya Fiddo wayarsa ya Kira Danmallam..! Tana gabda Katsewa ya Daga Kiran Cikin Mutuwar Jikin da Baba Mallam ya Saukarmai Tun Safe daya Kirasa yana Fadamai zai aura masa Kazamar yarinyar nan..! Cikin Farimciki Baba Mallam yace"Umaru..! Dagachan bangaram Muryansa a shake yace"Na"am Baba..! Bai jira cewarsa ba ko yanayinsa ba yace"Yanzu nan aka Daura auranka Da Uwata..Ayanzu din nan AMINA ta zama Amanarka Umaru..daidai da Rana Daya in kaci Amanarta ko ka Dannen Hakkinta Allah na kallonka sanna amatsayina na Mahaifinka ban YAFE maka ba Umar daidai da Rana Daya in ka Zalunci AMINA.! ya karishe Fada Cikin kaushin Murya Gabadaya sai yaji kamar Duniyar na Juyawa dashi wannan shine gaba kura baya Damisa..! Baba Mallam bai Damu da amsar ba ya Cigaba da Fadin"Ina Alfahari dakai..Yau ka cikamin Burina Umar..albarkata da addu"an Allah ya baka Zuru"ata tagari bazata yanke Daga bakina ba..Ina Rokon Allah yasa Amina ce Sillar Arzikinka da Daukanka..Ina ji ajikina Uwata ce Farincikinka watarana ko bana Raye alokacin nasan zaka Tuna dani Umar..! Jin Mallam kawai yake ta ina wannan kwailar yarinya zata zama Farincikinsa watarana..? An dai hadasa da aiki Yarinya kazama ga rashin Natsuwa da Taurin kai da rashin ji yana zaman zamansa Mallan ya Debo masa aiki Sai dai shi Yaro ne mai Biyayya har abada baya Fatan Ranar da zai Sabama Iyayansa..! Shiyasa Cikin karfin hali yace"Nagode Baba..Allah ya kara girma..Insha Allahu zaka sameni mai biyayya..! Baba Mallam cikin jin dadi yace"Nasani..nasan bazaka watsamin kasa a ido ba..Allah yayi maka albarka..! Ya amsa da Ameen Daganan sukayi sallama bayan ya tambayi jikin Aba yace da Sauki sannan suka rabu da juna da cewar shi Danmallan din zai kira wayar Baba Sa"idun Baba mallam yace ya Kirasa Jafar ya Tahomai da wayarsa da Safe..! Abunda kowa bai sani ba Tun Da Asuban nan da Danmallam ya Kira Baba Mallam yaji aransa wannan mafitan ne Allah ya nuna masa. Bai yi shawara da kowa ba kafin ya tafi asibiti wajen Aba ya kirasa suka Tattauna Komai Daga farko har karshe sai da ya Fadamai duk abunda ya Faru kwanaki da na jiya Daddare da kalaman Baba Sa"idu da Rokonsa garesa ya kuma Roki Danmallam Daya auri Amina ba domin Umarni ba sai domin daman Yana da Burin Hada Dansa ko yarsa da Ahalin Sa"idu..! Umar bai iya cewa A"a ba..Mallam ya wuce gaddama garesa Cikin wani yanayi ya amsa masa da cewa Ya amince wannan kalaman nasa su suka Tabbatar da Kaddaransa da Amina Kaddaran zama amtsayin miji da Mata..! **** Cikin wadanda Daurin Auran Amina da Danmallam ya shiga kunnensu yaya na ciki ita da Hajiya da Mamanmu kai kaf wadanda ke gidan sun ji hadda Amina uwar gayyar Domin tatashi alokacin Hamida ta taimaka mata tayi wanka tayi alwala tana Rama Salolinta ta idar kenan tana Zaune Saman Darduma alokacin ma Tunanin Aminu take da Tunanin Halin Dayake ciki. Kamar mafarki Taji muryan Ladanin nan yana bayyana sunanta da na Ya Danmallam amtsayin mijinta da aka Daurama taaure yanzu nan. Ta Rude kanta kamar ya Kulle domin bata gane komai ba Sama sama take jin Muryan Mamanmu Daga Tsakar gida inda suka zauna tun bayan Dawowarsu daga asibitu tana Fadin"Kunji Abunda naji kuwa..? Kamar Naji ana Fadin an Daura ma Amina aure da Danmallam..ku Saurara,kuji..! Suma sun ji din sai dai sun kara kasa,kunni Saboda su gasgata,Hajiya kuwa tun jinta na Farko ta tabbatar da Duk abunda taji gaskiya ne..Mallan ne fa tasani Daman shurunsa Zai iya zama koma menene..! To duk abunda akeyi a masallacin kamar agidansu akeyi saboda lasifukun masallacin akwai kara sosai,Radau suka sake jin wannan al"amarin Daya basu matukar mamaki Yaya Dake Dakinta Tana zaune ne sai da ta mike yayinda ya Zeena ta kwalalo ido tana Fadin"Wlh Mamanmu da gaske ne..Amina ce..! Hamida da Hanne suka kalli juna Cikin mamaki kafin Hanne ta Rumtuma Dakinsu Hamida tana Fadin"Amina..Amiaa..Kin ji an Daura miki aure da ya Danmallam yanzu a masallaci..? Kallonta Amina takeyi da manyan Idanuwanta da suka Zama wani irin Cikin wani yanayi tace"Naji..Naji Hanne..ammh bangane komai ba wani Danmallam din..? Ni Umar naji an ce fa..? Tafada cikin wani yanayi Hamida ce da ta shigo cikin wani yanayi tace"Shine Umar din Amina..Yayansu Hanne..Mijin Anty Sakina da Anty Sarood wanda ke zaune a madina..! Cak Numfashi Amina ya Tsaya ta Fara Kokuwa dashi bata samu zarafin mgana ba taji muryan Yaya tana Fadin"Hajiya kinsani..?meyasa kikabari Mallan yayi haka..? Amina bata dace da kamilalle irin Umar ba..Bata dace dashi ba sam..bai kamata kuyi haka ba..! Sai kuka,acikin ranta kuma wani Sasaauci taji Tana ganin kamar Addu"anta na Shekaru ne Allah ya amsa sai dai Tana jin Tsoro tana jin tsoron An Hada Kamili kamar Umar da Amina kada ta zama mai sonkai kada taso yarta Shiyasa tayi mgana..! Hajiya kuwa tana zaune sai Mirmishi take saki Annushuwa ta bayyana acikin ranta kafin tace"Sun Dace Hadiza..Duk abunda kikaga Mallam ya yanke mai kyau ne..Naki addu"a ne Allah yasa Alheri muka kulla..Allah yasa su aminan juna ne..! Da karfi Mamanmu ta amsa da Ameen tana sharan kwallah tace"Yaya Amina fa y'arki ce..Tayaya zaki rika Fadin mgana mara kyau akanta ya zataji in taji abunda kike fada! Tana mgana tana sharan kwallah..! Amina Daga cikin Dakinsu Hawaye suka kwanyomata tace"Naji..Naji Mamanmu naji..Gaskiya ta Fada ban dace ba..Ban dace ba..! Batasan Lokacin da wani kuka ya kwace mata ba Lokaci Daya tana Fadin"Wlh bansani ba..Bansan wannan kaddaran ke Bibiyata ba da Ban fara son ka ba Aminu..Wlh bansani ba..! Taausayinta ya kama Hanne da Hamida suka karisa gareta suka Rumgumeta suma sai kuka Riris kamar anyi mutuwa..! Zuwa Lokacin Wannan Daurin auran mai Cike da Bazata da mamaki ya kama Yaduwa a gidajen nan guda Biyu Anty Amarya sai da tayi suman Wucin gadi bata kara gasgata mganar ba sai Da shamsu ya shigo ya kara Tabbatar musu agabansu akayi ita da Hajiya Nasara,Haj.uwa na shashenta bata fito ba Duk da tasan abunda ya Faru domin taji..! Alokacin da Kowacce take kiran ya"yanta masu aure na nesa tana Fada musu Anty Amarya bata cikin natsuwa ballatana ta iya kiran wani ta Fadamai awannan gabar abubuwan sun bala'in shammatanta Abunda kowa bai sani ba alokacin Baba Mallam na cikin Falomsa na Shashensa tare da baki Daga Yola..! Yana gama wayar nan da Umar Motoci biyu suka gyara parking kofar Gidansu kuma wajensa suka zo ya karbesu hannu Biyu ya kuma Saukesu afalonsa zuwa Lokacin mutane sun fara watsewa..! Jikinsa yayi sanyi da yaji kamar yayi gaggawa AMINU ne saurayin Amina da iyayansa sun zo neman auran Amina da kuma ban Hakurin abubuwan da suka faru.. Ashe ashe jiya da dadaddre Aminu Daga Gumel yola ya wuce Allah ne ya kaisa Lafiya yaje gaban Baba Alhaji ya Fadamai komai yana kuka da Rokon suje Gumel suba ma iyayan Amina Hakuri su bashi auranta sai dai abunda bai sani ba sun makara..! Mallam yaga Dattakon Alhaji Baba yaji matukar kunya alokacin Dayake Fadamasu Amina ta haramta ga Aminu yanzu taron chan na waje na Daurin auranta ne..! Yana ganin wanda aka kira da Aminu ya tashi ya fita yana Rangaji hawaye Sunaa zuba Daga idonsa. Sai yaji jikinsa yayi sanyi yaa ji aransa kodai yayi gaggaawa ne..? Aminu Dakyar ya kai kansa Bakin Motocinsu da suka zo dashi Wayarsa ya Dauko biyu biyu yake gani da haka ya Kira Nenne..! Tana ganin kiransa gabanta ya Fadi Daman kiran nasa take jira tana Dauka tace"Aminu ya ake ciki..? Cikin karyewar murya yace"Na rasata Nenne..Nasara MEENATA.. Na makara Nenne an Daura mata aure da wani bani ba..! Yana gama fadin haka ya Datse kiran ya Sulale nan kasa Dirshen ya Hada kansa da gwiwa yana kuka kukan Rabuwa da masoyi Rabuwa ta Har Abada..! Nenne Dake cikin gidansu na Yola gidan Alhaji Baba yayyinta da kannenta sun zagayeta suna tambayata Lafiya Cikin fitar Hawaye ta kalli Mahaifiyarsu tace"Hajjo ya rasata..Aminu ya rasa Amina....an daura mata aure da wani kafin su isa..! Gabadaya suka hada baki wajen fadin"Innalillahi wani"inna ilaihirraju'un..! Sun sani Aminu zai samu matsala Kaddaran ta riga fata duk wani ahalin gidannan yasan yadda Aminu yake kuka yana rokon Alhaji Baba yaje yane masa auran Amina.. Ya Aminu zai yi..? Bakin Alkali ya riga ya bushe..! Zanen kaddaransa bata Amina bace..Kila na watace chan Dabam Inda ya sani..Dama..Dama ace bai Hadu da Amina ba..Dama ace komai daya faru mafarki ne..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* _Wannan shafin jinjina ce da godiya gareku masoyana a duk inda kuke masu Sharhi da masu fatan Alheri musamman yan Group dina na TA FITA ZAKKA COMMENTS SECTION da ku yan JANAF NOVELLA Tare da duka sauran gidajen marubuta da ake yin sharhin wannan Littafin nagani kuma na yaba naji dadi Allah ya bar zumunci gaisuwa ta musamman zuwa gare ku yan wattppdians kuma kuna kokari sosai nagode Allah ya bar zumunci.._ *🅿️22* Zuwa dare duk wanda ya kamata yaji Labarin Auran Amina da Danmallam yaji,kowa mamaki kamasa yake yi in yaji Domin agabadaya da Dubawa ta mahanga ta Dan adam Amina bata Dace da Rayuwar Danmallam ba sai dai Ina Allah shi ke Tsara dukkan Lamuran sannan kuma ya zartar ya riga ya Dora alkalamin kuma ya Bushe akan Amina da Umarun dan bazanga..! Aba yana asibiti ya jafar ya kirasa ya sanar dashi maimakon ya shiga bakinciki da takaici kamar yadda ransa ya darsu da Tunanin Baba Mallan yayi gaggawa domin Amina bata dace da Rayuwa irin ta kamili Natsattse Irin danmallam ba sai kuma sai yaji kamar zuciyarsa tayi son kai yaga kamar ita diyar tasa irin Mijin Daya dace da ita kenan baisan Lokacin Daya Daidaici gabas ba ya Fadi yayi sujudul Shukur ga Allah ya Dago yana Hawayen Farincikin da bai taba Zaton Daga jiya zuwa Dazu zai iya Fuskarta haka ba yadai ce zai aurar da Amina ammh acikin ransa yanajin kamar bai kyautu ba yana ji kamar wani al"amari zai faru ashe wannan al"amarin ne mai Daraja tuni kimar Baba Mallam ta kara Hauhawa acikin Zuciyarsa ya tabbata ko mahaifinsa Aminu gusai na Raye iyakar kaunar da zai bayyana masa kenan..! Bangaran Amina kuma tun Lokacin Dataji labari data fara kukan nan bata Daina ba,Har Hajiya Babba da mamanmu sai da suka taru akanta suna ta bata baki bayan sun Fatattaki su Hamida Dake tayata kuka,Agabansu sai tayi kamar taji Duka Nasihansu ta daina Abu Daya ke mata yawo Aminu ta kasa gane wannan wata irin kaddarace da zata Raba ta da masoyinta ta kaita inda Har Abada baza"a taba sonta ba..Wannan wata irin kaddarace haka take ta Tambayan kanta..! Hajiya Babba na tafiya Amina ta cigaba da gunjin kukanta har ta su Hamida sun daina sun koma suna Lallashinta,Ammh taki daina kuka Mamanmu kuma gajiya tayi ta rabu da ita ya Zeena ce ke kitchen tana samar da abunda zasu ci da wanda za"a kaima Aba Dake chan Asibiti suna Tunanin yasan abunda ke faruwa Tunda Baba Mallam baya Zartar da wani abu sai da saninsa shi da Hajiya Babba basu san wannan karon duka bai nemesu ba shi kadai dagashi sai Allah Daya barma Zabi bayaso yayi mgana da wani ko wata su ce ba haka ba shi yasa wannan karon ko Hajiya babba batasan me ya yanke ba Sai Daga baya..! Tun Mganar da Yaya tayi ma Hajiya Babba ta koma Daki ko motsinta ba wanda ya sake ji,Sai Lokacin da iskancin kukan Amina ya isheta sannan ta fito ba wanda yaji Shigowarta illah Dundun data Dirkama Amina agadon bayanta wacce ke zaune kasa ta Hade kai da Gwiwa tana gunjin kuka alwala ta Dauro Dakyar shima sai da Hanne da Hamida sukayi ta magiya shine ita batayi sallar ba ta koma tana kuka..! Dukkansu sai karan Dukan sukaji Amina ta bankare baya wannan Hannu shi kadai ne bata saba dashi ba Hannun Yaya ne..! Cikin bacin rai ta kalli Amina tana Fadin"Ai bake bace da kuka ba Amina..Umaru ne da kuka domin shi aka Gurbanta ma Rayuwa..Mutum kamili kamarsa an Hadasa da wacce bata Dace dashi ba Amina kamar ki ace kin san Namiji..?Daman nasan wannan Firiritan nan naki watarana sai yakai ga haka har kina mana wani kukan banza to wlh ki kama bakin ki ko na sake Dana miki Dukan da sai kin Raina kanki Sakarya wawiya mara Tunani kawai..! Ta karishe Fada Cikin Huci Amina na kuka tana Fadin"Wlh bana bin Maza..Ni ba yar iska bace..! Yaya tace"Shi Jafarun zai miki karya ne..?yaron da yace ya ganki Rumgume dashi Ubanki ne shi..?wlh in bakin ki bai Mutu ba,zaki sha wahala ke baki ji kunya da Tsausayin kanki ba..?Mahaifnki nachan kwance asibiti taa Dalilinki Tir da Halinki Amina Tir wlh..! Tafada Tana nuna ta da Hannu Cikin wani yanayi Hanne ce ta Dukar dakai Cikin wani yanayi tana Fadin"Don Allah yaya kiyi hakuri..Nasan Wacece Amina sai dai in kuskure akayi wlh bazata aikata abunda akace ba..! Yaya bata samu bakin mgana ba Mamanmu Data Daga Labule tun dazu Tana jin yaya tace"Hanne ku kyalesu..Duk abunda zasu fada sun Dade basu fada ba..Abu Daya na sani Amina ba Haka take ba..Amina bazata Watsar da Tarbiyanta ba..Akwai abunda ba Daidai ba..! Yaya tayi mirmishin Takaici kafin ta Juyo tana kallon Mamanmu Cikin Sanyin Muryanta tace"Yaushe ne Ranar da Amina zatayi kuskure ki nuna mata tayi ba Daidai ba..? Yaushe ne Ranar da zaki bi bayam gaskiya ba bayan Amina ba..? Mamanmu tace"Sai Ranar da na Tabbatar da gaskiyan kuke fada yaya..Ammh ayanzu har gaban Abada bazan bar Tsagin Amina ba..Amina Diyatace da nake mata soyayyar da ko ya'yan dana Haifa da cikina ban musu shi ba,Har abada bazan Daina Fadin kunyi kuskure Amina ba haka take ba..! Yaya Batace komai ba kawai ta girgiza ta raba ta gefen mamanmu ta fice Mamanmu ta bita da kallo kafin ta maida kallonta kan su Hamida tana Fadin"Ku bata baki..Bari akawo abinci taci tasha mgani..! Daga haka ta saki Labulen Dakin ta koma to a wannan gabar sai kukan Aminan ya tsaya cak kamar an Dauke ruwa Zuciyarta ta Bushe bata jira Lallashin kowa ba ta Gyara zama Daga zaune ta tada sallah domin jikinta har yanzu atsame yake bata iya Tsayuwa waje daya ta Gudanar da sallar ba..! Wajen karfe Tara na Dare sai ga Ya Jafar da ya Nasir sun zo Amina na Daki taji Ya Jafar na fadin"Ina ita mara kunyar Aminar .? Yaya Data Fito daga Daki tana gyara zaman Hijabin jikinta Da zasu tafi asibiti tace"Tana ciki..Tun dazu da taji Labarin abunda ya faru take kuka..! Yaya Jafar sai da ya Lailaya ashar kafin yace"Yar iskace bata Daku bane..Ai wannan auran Baba mallam ya Daurasa ne ba domin ya dace ba wlh..! Ya Nasir yace"Uhmm.Ni kuma ina ganin Daidai ne Jafar..Amina sai irin su ya Danmallan ne daidai dasu..! Ya Jafar yace"Kamanta ne shi fa ba irin mu bane bai da Hayaniya bai kuma kaimu Zafi ba..! Ya Nasir yace"Duk na yarda..Ammh kuma ya fimu Shekaru sannan cikin Ruwan sanyu yake Ladabtar da Mutum..Wlh ina ji ajikina Wannan al"amarin ba Tsarin Mallam bane Tsarin Daga Allah ne..Abu ne da Hasashe ko Tunanin mu bai taba kawo ba yanzu muka gama mgana da Ya Nazir shima haka yace..! Ya Jafar yace"Nima ya Kirani yana Tambayana sai dai ina mamakin waya fadamai..? Ya Nasir yace"Tab to har su Nazeem Dake Zaria sun ji Labari..Ya Danmallan din ne ban da masaniya ko ya sani..? Mamanmu na zaune saman Tabarma cikin baranda tace"Nima yaran nan sai kirana suke Zulahait dai tace min Aisha ta Kirata ta fadamata itama tace Abida ta sanar da ita da wayar Hajiya..Suma mamaki suke suna son ji ko gaskiya ne nace musu gaskiya ne..! Ya jafar yayi ajiyar rai kafin yace"Dawa dawa zamu koma asibitin..? Mamanmu tace"Da yaya zaku je ni bazani ba zan zauna wajen Amina..! Ya zeenatu tayi karaf tace"Ya Jafar don Allah zani..! Tana rufe baki Hamida da Hanne suka Fito suna Fadin"Muma zamu don Allah..! Sai da ya Hararesu kana yace"Bazaku ba..gobe da safanan za"a sallamesa..! Mamanmu ce tace"Kaje dasu don Allah Jafar..Oh na manta ina mai ciwon kunni..? Ya jafar yace"Yayi sauki sosai kin ma Tunamin ban karbi mganin da Baba Mallam yace nazo na karba ba..bari mu dawo..kuzo mu tafi Dare yayi kuma bana son rawan jiki yarinya ta natsu..! Ba musu suka shiga Taitayinsu Ya Zeenatu ce ta Dauko kwandon data Zuba abinci yaya daman da hijabinta Jawad na gefenta sai su Hamida sallama suka ma mamanmu suka Fice,ya zeenatu da Hamida Motar Ya Nasir suka shiga ashe matarsa na gaba Anty Fadila da ita za"aje..! Yaya kuma da Hanne suna Motar ya Jafar Koda sukaje Aba yaji Sauki sosai sun samesa yana cin kayan marmari ga Ferfesun kayan ciki ne,da suka tambayesa wa ya kawo masa..? Yace Hajiya Babba da Hajiya uwani yanzu suka fita Idi Direba ya kawosu ya riga ya koshi shiyasa suka ijiye abunda suka zo dashi Aba ya amsa gaisuwan Hamida da Hanne ya Kallesu Cikin kulawa yana Fadin"Ina Amina..? Hamida tace"Tana gida Baba..! Daman ta sani Amina na ransa ita din yarinya ce mai shiga rai kaunar da iyayanta Biyu suke mata Allah ne kadai yasanta sai dai baza su bayyanata ba Saboda kawaici da kuma Tunanin ba ita kadai suka Haifa ba Daganan bai kara mgana ba Jawad yaja kan jikinsa yana Tambayansa ya makaranta yana bashi amsa basu Dade da zuwa ba sai ga Baba mallam ya shigo Cikin shigar Alkyabbansa da Rawaninsan nan suka Ramkwafa suna gaishesa ya amsa cikin Sakin Fuska yana kallon Su Nasir kafin yace"Ashe nan kuka zo..? Kan Nasir na kasa yace"Eh Baba..Na kawo Fadila ne ganin bata zo ba..! Yana zama saman kujeran Dake gefen gadon Aba da Ya jafar ya tashi ya bashi yace Lokaci daya"Yayi kyau..Kun kyauta Allah yayi muku albarka..! Su hamida ya kallah ita da Hanne kafin yace"Naga zara ban ga wata ba..Ina mamana..? Wannan karon Hanne tace"Tana gida Ita da Mamanmu Baba..! Kai ya gyada kafin yace"In ta warware zamu daidaito ni da uwata insha Allahu..! Ba wanda yayi mgana sai Su ya Jafar ne suka Murmusa kawai,Baba Sa"idu ya kallah yana Fadin"Kai ai ka warke tunda naga har kana iya Daukan Jawaad..! Baba Sa"idu yace"Da sauki Baba..nacema ce su sallame ni yau sukace sai da safe in Likita yazo..! Baba Mallam yace"Gwara ka kara samun karfin jikin ka kafin ka koma gida..! Ganin suna gaisawa da Aba yasa su ya jafar sukayi shirin tafiya sai alokacin Baba Mallam ya kalli yaya yana Fadin"Hadiza bana son ganin wannan Damuwar afuskarki Daga gani kin ta kuka..Sa"idu ne babban banza shi ga inda ya kawomu ke kuma kina chan kina kuka har wata Cuta ta kamaki ta Miki illah ina amfaninta..?Ina ce Amina ce Matsalarku..?to ta fita Daga Hannunku ta koma karkashin ikon Umaru sai ku daina Damuwa..Ina ce ba Shikenan ba..? Yafada yana kallon Aba da kunya yasa ya Sunkuyar da kansa Yaya kuwa kanta na kasa batayi mgana ba har sukayi musu sallama suka fice suka bar Baba Mallam anan da Jawad daya makale ma Aba yaki tafiya Baba Mallam yace a kyalesa in zai taho zasu taho tare. ! ****** Tun bayan Fitarsu daga gidan ta Mike ta Leka Amina abinci ta Debomata Farar Shinkafa da Miya Kadan Amina taci don ma Mamanmu tana bata baki Tana Hadawa da Lallashinta Fadi take yi"Ki daina damun kanki ni nasan babu abunda kika aikata..Kuma mganar auran in baki so batare da kowa ya sani ba zan kira shi Danmallan din na Rokesa ya Sauwake miki..Ina Zaki iya da Sakina..?Matansa fa Biyu Kina yarinya Dake duka duka Shekarunki nawa Amina..?Sha Shidda fa Ko sha bakwai din Baki cika ba Har yanzu..Gaskiya akwai kwa ruwa acikin Hukuncin Mallam..! Take fada cikin bayyana bacin ranta Amina kallonta kawai take batayi mgana ba to me zatace..?Tayi mgana ai bai da amfani komai ya riga ya kare ta rasa Aminu ta gama rasa komai Mganar Rabuwa da Ya Danmallam kuma bata isa ba har gaban Abada bazata watsama Baba Mallam kasa a ido ba kamar yadda bazata watsama Mamanmu ba uwa uba gasu Aba da yaya bata Fatan wani abu ya kara Giftawa,Ta riga ta sani Kaddara ta,kaita wani bingiren da Har yanzu ta kasa dora kanta a inda kaddaran ta jata ta kaita in tana tunawa ma sai wani Rauni da Faduwar gaba su Lulleta waje ne da har Abada zatayi Daraja ba ta sani..! Har mamanmu ta gama bata tana ta Mita panadol ta bata tasha sai kuma ta shafa mata man zafi ajikinta Da Amina taji Dadinsa kwarai hawaye take yi da kukan zucci acikin ranta tana kara Ninka kaunar dake yi ma Mamanmu tana Fadin dama dama ana Sauya wani abu da Tuni ita Amina ta Dade da Sauya Yaya da Mamanmu amtsayin uwa..! Amina bata sani ba Allah yana Boyemana wani abun ne kafin mu sani saboda kila alokacin in ya bayyana mana bamu da karfin gwiwan da zuciyan da zamu iya Dauka..! Boyayyin Fuskokin wani Lokacin Alheri ne garemu kila sanda zasu bayyana Mun Tsaya da kafafunmu Raunin da zai bayyana garemu kadan ne..! Sai da ta tabbatar da barci ya fara Daukan Amina kana ta bar dakin Dakinta ta koma bata Dangana ako"ina ba sai Cikin Bedroom dinta tana shigowa wayarta Dake kan gadonta ta sake Daukan kuwwa alamun kira ya shigo Da hanzari ta karisa ta Dauki Wayar sunan wacce ke kiran yasa bata Tsaya bata Lokaci ba ta Daga Daman ta sani zata kirata itama din Jiran kiran nata take yin bayan Tabbattuwaar abunda basu taba Tsammani ba..! "Dayyaba Da saninki komai nawa ya Rushe..Dayyaba da saninki akamin wannan yankar bayan..Da Saninki kika bari yarinyar da ta Ratso cikin gabar aikina alokacin danake Hasashen ina gabda cin nasara..Na sani hakan zata faru shiyasa nake ta Kiranki tun dazu baki Daga Kirana ba..! Tunda ta fara mgana wannan kamilar Fuska mai cike da Annuri da Tsausayi ta rine ta koma Bakar fuska mai Cike da mugunta da rashin Imani Cikin Wata Murya mai cike da Amon Takaici da Bakinciki tace"Da sanina Bazan bari haka ta faru ba Madina..! Wlh ban sani ba..Kamar yadda kikaji abun Daga sama nima haka najisa..Shammatan mu Mallam yayi..Shammata mai girman da bamu Taba Tsammani ba Madina..! Dagachan bangaran Agidan Baba Mallam ashashen Anty Amarya itama Cikin Tsakiyar Bedroom dinta tana Tsaye gaban makeken madubin Dakin nata tana kallon Fuskarta Data wani yarkace na Wunin yau kawai tun bayan Samun Labarin Daurin auran Amina da Umar..! Cikin Muryanta mai Fadi da ba kowa ya santa da ita ba tace'"Lalle ko ya shammaceni Dayyaba..Sai da na Riga na gama Tsara komai..na gama Tunanin matsala tadaina shigomana cikin Aikinmu ashe suna chan suna Shirya ganina akasa..To basu isa ba..In a zaune suka kwana Ni Madina a tafe na kwana nayi alkawarin yadda bansamu Mallam ba ta bangaran Sakina Da Umar sai na Juya ragamar Mallam da duka abunda ya mallaka..Karya ne..Bayan sakina ba wacce ta isa Umar ya sota har ya Hada Jini da ita Sakina kadai keda Alhakin Haihuwa da Umar ita kadai ce Zata Haifama Mallam Yunus Bazanga Jika,Abaya nayi Sakacin da Har Ya"ya Biyu suka fara Fitowa daga Tsatson Nazir nayi sakaci Dayyaba..Sai dai kinsan aikin da mukayi ya"yan Nazir baza su taba Tasiri a wajen Mallam ba..Kacokan Burina na wajen Abunda Sakina zata Haifane..Sai da nace miki Mu kauda yarinyar nan Dayyaba kika ki bani goyon baya ta rasto cikin Aikin mu batare da Mun gayyaceta ba gashi nan yau Rana Daya ta Fadomin cikin Tsarina Tsarin da bazan taba bari ya Rushe ba Koda hakan na Nufin za"a rasa rai ne..Na kasa gane miki ko kin fara Sauya Ra"ayi ne na Sauya Duka Tsarina Dake..Kila kin hakura da Abunda Sa"idu yayi shekaru yana Kunsamiki ne shi da wannan Munafukar matar tasa..Ko kuma kin shagala kin Fara Kaunar wannan Hatsabibiyar yarinya Dake nemam batamin Shirina..! Fuskar MAMANMU nake gani ta koma Jawur idanuwanta sun kala sun sauya Launi jijiyoyin kanta har sun Daga Saboda Bala"i cikin wata gigitaciyar Tsawa tace"Dakata Madina..! Har Abada ni Dayyaba bazan manta Da Bakimcikin da Sa"idu shi da Hadiza suka Dade suna kunsamin ba..Wannan Kaunar wannan Tsausayin da Soyayyar da nake gani acikin Idanuwan Sa"idu kan Hadiza saura kadan su kaini kushewata Har Gaban Abada bazan yafe musu wannan ba..Sai sun Dandanan gudarsu bana yafiya.. ni din nafi Rama Sharri da Alheri..kamarni Sa"idu zai kallah gaban Ya"yana da Matarsa ya SAKENI madina kan wannan Shegiyar yar tasu..?Yarinyar da duk cikin ya"yan Hadiza nafi Tsananta saboda iyayanta sun fi sonta..Sa"idu ya Dade yana kunsamin Bakinciki ya fifita soyayyar Hadiza Fiye da tawa sannan yazo ya fifita ya"yan Hadiza Fiye da ya"yana Saboda Ban Haifi namiji ba ko..?akoda yaushe in na Bude ido na ga Jafar sai naji kamar na kashe kaina..Meyasa na barsa araye ban saka malamin mu ya Kashesa ba..Da yanzu ba haka ba Madina Da yanzu na Dade da kunsa ma Sa"idu da Hadiza bakin cikin da Har su koma ga Allah bazasu manta ba..Duk Saboda Cikar Burina na aro Fuskar da ba tawa ba Madina..Ina zaune cikin wadanda nafi Tsana ina Fifita ya"yam makiyiyata Fiye da ya"yana ina Faman kare ma wanchan yarinyar da bata da wani amfani a wajena...Madina Dukkanmu mafita muke nema saboda haka koma menene ki Fadeshi zan yarda zan amince zuciyata zafi take madina Amsa kuwar Sa"idu nake ji yana Fadamin ya Sake ni Saboda wannan Shegiyar yarinyar ina so suma su Dandana ina so suji yadda na daukii shekaru ina ji acikin raina..! Anty Amarya tayi Mirmishin Dayafi kuka ciwo kafin tace"Sakacin ki ne Dayyaba..Tun Lokacin da aikin malam ya Tsallake Jafaru ya koma kan Amina nace a kaudashi kika yi yarda..Da yau baya Raye Da wane d'a Sa"iidu zai yi takama..?yau gashi dan Zaki ya Girma harda albarka Haihuwan wani karamin Zakin Dayyaba anya ke naki Tsarin ba Doguwar Tafiya bace..? Da Sauri Mamanmu tace"Bana kallonshi a Faduwa Madina..Jafar da Abunda ya Haifa ba su da wani amfani kadan nake jira na karar da su..Yanzu ni Sa"idu zan fara mgani Tukunnah so nake naga bakimciki da Rauni acikin Idanuwansa Madina..! Kai Tsaye Anty Amarya tace"Za"a rasa rai...YAYA ZATA MUTU...! Mamanmu tace"TABBAS YA KAMATA TA MUTU..sai dai naso sai ta gama shakan bakincikin da na Dade ina Tanadama mata madina..! Anty Amarya tace"Yanzu Lokacin Daya kamata ta Mutu ne Dayyaba..Mutuwar ta ne kadai zai sa kiga wannan Bakincikim acikin Idanuwan Sa"idu..Mutuwarta ne zai sai nima naga Sa"idu ya koma abun Tsausayi ya dade yana min katsalanda Shi da Hajiya Babba..Zamu fara ta kansa ne kafin mu dawo ta kanta da Saninsa aka Aurama Umar Amina..Da saninsa ta shigo Tsarina nima wannan Damar nake jira da Zan Dandana ma Sa'idu koda Rabin abunda nakeji ne game dashi..Komai na ke kokarin samu Shi da Hajiya babba sai sun tare ni Dayyaba..! Cikin wata irin Dariya tace"TABBAS yakamata ta Mutu...! Zata mutu..! Anty Amarya tace"Zan kira mallamin mu Dayyaba zan sanar dashi ya yanke mata wa"adinta kafin wayewar gari bazan jira ba..bana son wannan karon asamu matsala..! Mamanmu tace"Nima haka..Wayewar garin gobe Ranar mu ce..Na kosa na kosa naga wannan bakimciki akallon da zan ma Sa"idu..Babban kuskuransa shine ya Fifita komai na Hadiza akaina..Babban Raunina Ina SON SA'IDU..! Anty Amarya tace"Shikenan kada ki damu ki Dauka an gama..Mganar kudi akwai wani abu a hannunki..? Mamanmu tace"ki kamallah komai in mun hadu zamu warware komai..! Anty Amarya tace"Shikenan..Mganar yarinyar nan baki ce wani Tsari zan kaita ba..? Mamanmu ta saki Dariyan Nishadi kafin tace"Ban damu ba Madina..Ni Kaina na sani Dagani sai ya"yana..Ki kaita Duk Tsarin da kika ga Dama..Koda Tsarin na MUTUWA NE..! Anty Amarya tace"Tsarin bana Mutuwa bane..Zata sha wahala ne kawai sai daga baya mu kaudata..Tsarin da na kai Balarabiyar nan Tsarin zan kaita Dayyaba..Hotuna zasu zama wajen Umar har Abada Sakina ce Zata Cigaba da amsa matsayin mata awajensa..Wannan alkawarin ne..! Mamanmu ta jinjina kai tana Fadin"Hakan yayi daidai..Daga gobe komai ya Dawo hannuna..Daga Sa"idun har ya"yan nasa..basu san Wacece Dayyaba ba..Balaraba Ita suka sani..! Dukkamsu Dariyan suka sheke da ita Dariyan cin nasara da samun Duniya lokaci daya suna yanke kiran atare..! Abunda basu sani ba wani abun Allah ya Riga ya kaddaran Faruwansa bakin Alkalami ya Riga ya Bushe..! Tabbas za"a rasa rai..Sai dai basu isa su Dauki ran wani ba..Daman chan ita ran Lokacinta yayi ne..! Suna gama wayar ta Wurgar da wayar saman gado ta fara Zagaya Dakinta Cikin kaushin murya take fadin"Allah Sarki Yaya..Yau za"a amsa kiran Allah..! Wayyo wayyo..! Haka take ta fadi sai kuma ta kece da Dariya kamar mahaukaciya kafin ta koma ta Duke kuma sai ta saki kuka Lokaci Daya tana Fadin"Ba haka naso na zama ba..Sa"idu kai ne sila..Na soka Tun kafin ka fara son Hadiza..Me na rasa baka taba sona ba..?Kasha bansan auran biyayya kayi dani ba..? Kasha bansan ka Tattara Zuciyarka ka bama Hdiaza ba..Wannan son shi ya ja maka kai da ita..Wannan Tsausayin shi zai kasheta Sa"idu..Ba Laifina bane..Laifin SOYAYYARKA CE..Bantaba son wani Namiji yadda na SOKA BA Koda bazaka soni ba nayi alkawarin baka isa ka so wani ba..Komai na ya"yanta ya zarce nawa..Duk yadda naso hakan bata Faru ba sai da na zama koma baya agidanka..Kasha bansani bane.?bakayi karya ba nasan Amina ta fara soyayya da wani..bakayi karya ba..Nasani naki fadamaka Saboda Daman ina son damar da zata kara Ruguza rayuwar Hadiza..ban so abunda ya faru ya Tsaya nan ba na so ne Tayi Cikin shege na Tsawartsaku gabadaya..ba Laifina bane..Yaya ki yafemin Sa"idu ya ja miki MUTUWA..! Take fada tana Hawaye Lokaci Daya Dadariya tana Tuna ranar data fara kama Amina tana waya da Aminu acikin bayinta bata nuna ta ganta ba..Hakan ya mata Dadi Domin bata kaunar cigaba Daga bangaran Hadiza ita da ya"yanta Tundaga Lokacin Da gangan take ijiye wayarta Har Aminan take samun Daman Dauka ta kuma fara Bibiyan Motsinta abunda kowa baisani ba Hatta Haduwar da take yi dashi duk tana sane..Taso ta shirya wani abu ne..Taso ta yi amfani da Amina ta Tsarwatsa Yaya da ahalinta sai dai Mallam ya shammesu matuka shammatam da basu taba Tsammani ba..! Abunda bata sani ba..Ba Mallam bane Allah ne ya Rubuta abunda ya Faru Daki Daki..Su basu isa su Hana Al"amarin Allah ya Faru ba..Zanen kaddaran ya zama kuma bawa bai isa ya goge shi ba..! Achan asibiti kuwa bayan fitan su ya Jafar Baba mallam bai kara cema Aba komai ba sai shine da kunya ta kamaasa yace"Nagode Baba..Allah ya kara Girma..Naji zabin da kayi ma Amina badomin kada nayi sonkai fa sai nace nafi kowa Murna da hakan..! Baba Mallam ya yi mirmishi cikin wani yanayi yace"Sai da ga baya naga kamar nayi gaggawa Sa"idu.Abunda kuka zata ba haka bane..Jikina yayi sanyi naji kamar na so kaina nima dana aurama uwata Umaru a karancin Shekarunta na yarinta..Da ace na sani da na jira..Kadan da na aura mata wanda ke sonta Tsakani ga Allah ya kuma dace da ita..! Yafada yana jin Tsausayin Aminu na kamasa yana Tuna yadda iyayansa suka nuna jimamin Lamarin bayan sun gayama mallan duk abunda Aminu ya fadamusu kan Amina ce ta Dakatar dashi na bayyana kansa sun yi sallama Cikin wani yanayi ya Rakosu har waje suka iske Aminu Cikin wani yanayi wanda Dole bawa ya Tsausaya masa..! Baba Mallam yaji Dama ace ya Jirakadan..Da duk haka bata Faru ba..Sai da ga baya yaga kamar yayi gaggawa..Da ace Nazeem ya aura mata..sai daga baya yace dama Nasir ne..Umar yayi ma Amina girma Tazaran Dake Tsakaninsu kamar tazaran kasa da sama ne..! Yaji da ace Aminu zai karbi Tayinsa Daya Aura masa Hanne ko Hamida Domin ya wanke kansa Daga wannan zargin sai dai ina Agaban idonsa suka sakashi a mota cikin wani yanayi suka Dauki Hanyar Yola..! Shi kanshi Aba jikinsa yayi sanyi da bayanin Baba Mallam tun ma Daya bude baki yana fadamai abunda ya Faru bayan zuwansu Aminu..! Dukkansu shuru sukayi sun kasa mgana sai chan Aba yace"Baba Komai fa Da kaga ya faru yau..tsarin Allah ne..Mu yi fatan wannan Auran ya zama Sillar warwarewan duka abubuwansu Allah ya amintar da zuciyoyinsu waje daya..! Da Amen Baba Mallam ya amsa abunda basu sani ba sun yi addu"an akan gaba ammh Allah ya Riga ya amintar da Ruhin Amina da Umar waje Daya Alkaalamin kaddaransu ya Riga ya Bushe! Sun dade suna kara Tattaunawa sai da Shamsu yazo shi da zai kwana da Aba ranar sannan Baba Mallam yayi mai Sallama ya koma gida Cikin Damuwa da Tunanin yayi gaggawa..! Abunda ya Dade bai Faru ba yau ya Faru Baba Mallam bai isa shashensa ba kai Tsaye shashen Hajiya Babba ya Sauka kuma aidon matansa duk da Ba ita ke dashi ba Hajiya Nasara ne..! Yana cikin Damuwar da ita kadai zata iya kwantar da mai hankali. Haka yaje mata yana Fadin"Zainabu anya banyi gaggawa ba..? Ina ji kamar na zalunci uwata..! Hajiya bata Fahimci mganarsa ba sai da ya warware mata na zuwan iyayan Aminu ya karishe da Fadin"Meyasa na Zabi Umaru..?Meyasa ban zabi Nazeem ko Nasir ba..?Uwata tayi kankanta Umaru ba Tsaranta bane..ba zata iya zama cikin mata Biyu ba Hajiya..Nayi gaggawa..! Yake fada lokaci Daya yana Cire rawanin kansa..! Hajiya taji jikinta yayi sanyi itama Sai kawai ta Riko Kafadan Mallam tana maimaita Hasbunallahi cikin ikon Allah shima ya shiga amsa mata har ya samu natsuwa zaunar dashi tayi kan gado taje ta Debo masa ruwa mai Sanyi yasha yayi hamdala sannan ta kallesa tace"Bakayi gaggawa ba mallam...Daman chan Amina bata da miji sai Danmallam..Ba Tsarinka bane naa Allah ne..Ina ji ajikina wannan aueran Alheri ne zamu ji Dadinsa Watarana..shi kuma yaron Allah ya basa wacce ta fi Amina haka Allah yaso..! Kalamanta sun kwantar mai da Hankali Cikin natsuwar daya samu yace"Ameen ya Allah zainabu Abu mai Tawagayen suna..Bani abinci in ci inji dadin saka miki albarka..! Dariya kawai tayi tana Ficewa Daga Dakin ya Bita da kallo aransa yana Tunanin Har Abada bazai taba samun macen kwarai irin zainabu ba..! Sai da ta dawo da farantin abinci ta Sauke agabansa sannan tace"Muna da bakuwa fa..? Yana Saukowa saman Cafet din Daya malale Dakin yace"Bakuwa kuma..? Tana kokarin zama gefensa tace"Eh Hajiya BATULA ce kanwar Uwani Tazo Dazu da yammah nan daga Tsafe..! Bai ce komai ba illah kai daya gyada ita kuma sai ta fara kokarin zubamai Tuwon shinkafa miyar ogun din da akayi..! ******* 2:30pm na Dare..! Acikin Tsakiyar Falon Hajiya Uwani Zaune suke ita da yar"uwanta kwara Daya da suka fito ciki Daya su ka kuma Taso acikin jerin ya"yan da Alhaji hamza mahaifinsu ya Haifa..! Tayi aure mijinta ya rasu da Dadewa sai dai bata taba Haihuwa ba..Kuma tundaga Lokacin bata sake aure ba kasuwanci take yi..! Haj.uwani Dakin da Umaimatu ke ciki ta kallah kafin ta sauke numfsshi Lokaci Daya tana Fadin"Anya Batula kina ganin ba Zunubaina ke shafan Umai ba..? Duba kiga irin wahalar da mukeyi akanta har yanzu taki Lafiya Sa"o"inta duka Mallam ya aurar dasu ita ba Boko ba ba aure ba gani cikin kishiyoyi bana so aga gazawata..! Wacce aka kira da Batula ta gyara zama suna kama da Hajiya uwani sosai..! Cikin Yar dariya tace"Bai kamata ki karaya ba tun yanzu Uwani..Matsalan Umaima Daga Allah ne kin sani duk inda mukaje haka ake fadamana..Na Fada miki zata samu lafiya..Yanzu dai mu ijiye mganar Umaima agefe mu yi wacce Itace Dalilin zuwana..! Haj.uwani ta gyara zama tana Fadin"Uhmm..Acikin Abunda muke so mu kauda Batula wani abun yazo ya kara shan gabanmu..Yakin ba yanzu zai kare ba Batula..Mallam yau da azahar ya Daurama Umar aure da Diyar Sa"idu Amina..! Batula ta zari ido kafin tace"Aure kuma..? Haj.Uwani tayi dariya takaichi kafin tace"Eh ba wanda ya sani sai da aka Daura mukaji..Kuma bai yimana bayani ba..Kina gani yazo ya shige shashen giwa bai nemi kowa ba..! Batula ta karkace kai kafin tace"Shine yasa kika Tadoni tundaga Tsafe zuwa Gumel Uwani..? Kai ta gyada mata karamin Tsaki taja kafin tace"Da kin fadamin tun awaya wlh da ban zo ba Wannan ai karamin aiki ne..Me zai gagaremu Yarinyar wai me take takama dashi data baki tsoro..? Haj.uwani tace"Ba komai yarinya ce karama Sa"ar Sadautun Amarya..Yanzu suke SS1 MA..! Batula ta karaa sakin Tsaki kafin tace"Abu mai sauki..Ai tunda muka iya kai Sakina kasa kowa ma ta auri Umar sai mun kaita kasa..Hajiya babba ta samu Mallam da duka komai nasa to ta bar shi haka bata isa ta bangaran ya"ya kuma ta miki Zarra ba..Kada ki manta mu mukasa akayimana aiki kan manyan ya"yansa da sukaki zama kusa da Hajiyan da Mallam din mu ka Tura kurciyan Umar Madina yadda bazai ji sha"awan Dawowa gida ba kuma muka Tura Kurciyan Nazir Lagos yadda Har Abada zai iya zaman Gumel ba..Abu kadan ya ragemana Nazeem da Uzairu su gama karatu su Dawo gida Lokacin sai mu maida Sa"idu mara amfani alokacin Mallam bai da wata mafita sai ta ya"yanki sune Jagora Uwani! Haj.Uwani Ta saki kayattacen Mirmishi tace"Kin manta baki Tunanin Jikokin ya"ya na ne kadai Mallam zai kallah yaji Dadi ba..Tunda Mama ta fadamana Mallam yana matukaar son ganin kwam Umar aduniya na Mike Tsaye,Duk Shigen Shigen Marliya sai da nasha gabanta Bata sani ba ko gobe Sakina ta samu Ciki sai ya Lalace Mama ta tabbatarmin Umar haka zai zo ya koma bazai taba ganin kwamsa aduniya ba..! Batula tayi dariya kafin tace"Wai itama balarabiyar madina din kin gama mata aikin..? Haj.Uwani tace"Tun yaushe..Tare suka sha mganin Mama cikin Ruwan Tea din da suka tako har Fadona na Hada musu sun koma ba Dadewa..Sakinar tayi bari har Umarun yaxo karban mata mgani da Marliya ta karbi mata na Hausa..Araina nace kyayi ki gama..Wannan gidan na Uwani ne da ya"yaanta..! Atare suka saka Dariya kafin Batula tace"To wani mataki zamu Dora sabuwar zuwan namu..? Haj uwani tace"Tsarin da na Dora na gabanta zan dorata..Duk da nasan ma Umar b abunda zai ci da wannan mara kunyar yarinyar sai dai kinsan Namiji baka rainasa..Awajena bata da wani amfani kamar yadda na Maida yaron nan NASIR mara amfani a wajen Mallam in ba ya gansa bama mantawa yake yi dashi..! Wata Dariya suka saka har da Tafawa kafin Batula tace"Don Mallam din da Giwar suna Tsaye ne..Ai da tuni burin mu ya cika..! Haj.uwani tace"Abu daya na kasa..Kai Maallam kasa shi da Hajiya..Mama tace har Abada bazan ci galaba akansu ba sai dai kan yaran Basa wasa da ibada sannan azkar kamar ya zama jikinsu in ba ikon Allah ba Sihiri bazai taba kamasu ba..! Batula tace"Shiyasa nace ki bar asaran kudinki..Mu koma inda Mama tace sai muga riba..! Haj.Uwani ta saki kayayyatacen Mirmishi kafin ta koma ta kishingida kan kujera Lokaci daya tana Fadin"Aikuwa naga Riba Batula...! Ashe ashe basu sani ba..Suna Tufka ne..Daga gefe wata Boyayiyar Fuskar tana Faman warwara..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️23* Rai bakon Duniya..! Misalin karfe 7:00am..! Gabadaya gidan Baba Sa"idu haka suka tashi zuciya ba sukuni,Wasu sun samu barci da yar natsuwa ammh akwai wadanda basu runtsa ba ciki har da Amina domin yadda taga Rana haka taga Dare ita ba kuka take ba Domin zuciyarta ta kekashe bata ma jin yin kukan abu daya ta sani bata son tuna inda kaddaranta ta jata ta kaita domin in tana tuna yau ita ta haramta ga Aminu sai taji gabadaya Duniyar na juya mata,Abu daya yake mata nauyi acikin kirjinta Aminu shi take so ta san wani hali yake ciki ammh babu dama sannan sai Aba da Yaya wanda bata taba tsammamin Fushinsu zai dameta ba abu daya ke damunta Shedar iskanci da suka Zargeta dashi sauran bata damu ba Domin ta aikata ammh abu daya ke sata bakinciki yadda aka kasa Fahimtar abubuwan da suka faru kan yadda suke..! Tun bayan data idar da sallar asuba bata jirga daga inda take zaune ba ta kalli gabas da katon hijabin haddarsu bangon Dakinsu ta kurama ido ita ba kuka take ba ammh kana ganinta kasan bata cikin natsuwarta cikin kwanakin nan gabadaya Amina ta Zafge sai idanuwa fuskarta tayi wani iri tayi zuru zuru Hamida da Hanne ne ke tare da ita acikin Dakin Domin Ya zeenatu ta fita Kitchen ita bata koma barci ba. Hanne ce ta gaji da ganin Amina ahaka yasa tatashi tsam ta koma kusa da ita tadafata tana fadin"Amina don Allah kiyi hakuri..Ki yi hakuri..Haka Allah ya kaddara miki! Kamar bazata tankata ba tama yi Tunanin bata jinta yasa ta kara Girgiza kafadanta tana Fadin"Ameena kina jina kuwa..? Sai alokacin Amina tayi motsi da bakinta Cikin wani irin Sautin da Hamida da Hanne zasu iya Rantsewa da Allah basu taba jin Amina cikin wannan Sautin ba..! Asaman lebenta mganar ta fito cikin karyewan zuciya da Rayuwa tace"Ina jinki Hanne..Tun jiya keda Hamida kuke maimaita kalmar nayi hakuri..Tawa kaddaran kenan baku Tunanin na Haddace wannan..? Tafada Lokaci Daya tana sakarma Hanne manyan Idanuwanta cikin wanu yanayi na neman ma tallafi Dayasa Hanne saurin kauda kanta Tana fadin"Na sani..Ammh ki sani mai hakuri shi ke da riba watarana..Ko Hamida..!? Hamida da duk jikinta ba Dadi tace"Sosai ma Hanne..! Tana jinsu gani take su din suna cikin Farinciki tunda rayuwarsu bata yi musu juyin waina kamar yadda tayi mata ba..! Kara murmusawa tayi wanda kana ganinsa zakasan ba Annuri ko jin Dadi acikinsa tace"Hakane..Nagode bazaku je hadda bane..? Ta fada tana son kauda mganar domin tasan bazasu taba gane wani Hali take ciki ba..! Hanne ce tace"Bazamu ji dadin zuwa baki ba Amina ki saki jikinki..Sati mai zuwa sai mu koma tare..! Amina taji kamar tayi kuka alokacin Dama dama ace baya zata dawo Da tafi kowa jin dadi bata samu zarafin mgana ba Hamida tace"Ni kaina bazan ji dadin zuwa ko"ina ba baki ba Amina..Tare muka tashi muke komai tare..Wh damuwarki tamu ce Amina don Allah kiyi hakuri..! Tana Fada sai kuka hakama Hanne sai ta rumgume Amina tana kuka hamida ma tazo suka hadu suka Rumgumeta suna Fadin"Amina wlh mu zamu shaidarki..mun sani Fahimtar hakane basu yi ba..! Amina cikin wani irin kuncin zuciya tace"Wlh ban taba iskanci ba..Bantaba kadaicewa da Wani Namiji ba da sunam alfasha ba..Abunda ya faru ranar Tsausayi ne..Wannan itace kaddaran daman datake jiran bawa koda yaushe..? Itace kaddarata sannan kuma natabbata na Fita zakkan da ake yawan Fadi akaina Tunda gsshi ni Tawa Rayuwar ta kare ba yadda ta kowa take karewa ba..Hanne da Hamida kun ji dadinku bakinciki bai gauraye jin dadinku ba..Wlh ayadda nake ji dama ace Ban hadu da Aminu ba dama komai kamar mafarki ne..! Take fada sai kuma ta fashe da kukan da ba Hawaye daga gani abun yana Fitowa ne daga kasan ranta ne Haka suka hadu suna ta kuka kamar wasu yara bame lallashinsu cikin wannan yanayin sukaji muryan Ya Zeenatu tana Fadin"Jawaad wai lafiyan ka kuwa..? Me yayan zatayi maka Dakake ta mata wannan uban kiran..! Muryan Jawaad sukaji a Tsakar gida yana Fadin"Ya zeenatu tun dazu nake tashinta taki tashi..! Tana daga kofar kitchen ta Hararesa yana Sanye da zani da alamu wanka yayi Cikin dan fada tace"Bazaka je ka shirya ba sai Idi ya tafi ya barka ko..? Cikin Tura baki yace"To ai ban ga Jallabiyata ba shine nake ta tashin Mama ta Daukomin taki tashi..! Domin kaf gidan nam Jawaad kadai ke kiran Yaya Mama shi har alokacin sunan Yaya bai kama bakinsa ba..!. Ya zeenatu da mamaki ya kamata tasan yaya bata barcin safe In ta idar da Sallar asuba sai gari ya waye tana Lazimi koda bata ga fitowarta ba Tasan tana da Bayi adaki kila ciki tayi Hidimarta ammh cikin son kwantar da Hankalin Jawaad yasa tace"Kila barci ne ya Dauketa bayan tayi sallah jeka ka Duba cikin Dirowa kila ka gani kayi sauri fa..! Har ya juya sai ya juyo yana Fadin"Batayi sallah ba fa ya Zeenatu..! Dam gabanta ya fadi cikin Fitan hayyaci tace"Bangane ba..!? Cikin yarintarsa yace"kuma fa bata motsi..! Karaf Sai a kunnen Mamanmu Dake zaman jiran wannan sakon ya isketa Mikewa tayi bakinta kamar ya Tsage Cikin Yar dariya tace"Komai ya kamallah..! Daga haka ta gyara yanayinta Lokaci Daya tana fitowa alamun barci a idonta tace"Zeenatu me ya faru nake jin hayaniya..! Zeenatu da Hankalinta ke tashe tace"Mamanmu jawaad fadi yake yaya bata motsi fa..? Ido ta zaro tana fadin"Bata motsi kamar yaya..? Tafada cikin bayanna Firginta Wanda ya fito dasu Hamida Daga daki har da Amina Da suke jin meke faruwa gabanta ke fadi jikinta ke rawa tana Fatan ba wani abu bane zai kara kutse Cikin Rayuwarta ba..! Ya zeenatu ce kan gaba wajen shiga Dakin Yaya har bedroom dinta jawaad suka kara samu akanta yana jijjigata yana faman fadin"Mama ki tashina ina jallabiyata..? Yake fada ammh ko gizau dukkansu kamar an dasasu sun kasa karisawa gareta tana kwance sambal Cikin Hijabinta,fuskarta tar ta kara wani Haske sai dai abu daya ya Sandarar dasu shine ganin Idanuwanta suna kallon Saman Dakin ammh kuma bata Motsi gabadayansu kamar an Sassake jikinsu haka suka kasa karisawa..! Jawaad daya gansu ya sauko yana jan Hannun Mamanmu yana fadin"Mamanmu taho ki gani..! Haka yake fada kamar rakumi da akala haka ya jata har gaban gadon yaya inda take kwamce daidai Lokacin da sukaji sallaman Ya Jafar Ya zeenatu kamar walkiya ta fice da Sauri kamar ta kifa a tsakar gida taga ya Jafar Bayansa Aba ne,Kaya ne ahannun Ya Jafar da bargo da Filo sai Kwandon abinci,Bata Tsaya ko Gaida Aba ba tace"Aba ya jafar kuzo ku gani Yaya bata NUMFASHI..! Dukkansu haka mganar ta shigesu Aba kuwa dakyar ya iya Tsayuwa da Kafarsa Meke faruwa ne..?,Tabbas wanu abu ya faru ko kuma zai faru Domin Tun jiya yake fama da Faduwar gaba da yanayi mara Dadi sai ya Danganta haka da Kila abunda ya faru ne na Amina ammh kalaman Zeenatu sun saka gabbansa kara Saki Cikin wani yanayi. Ya jafar ne ya tsaya yana fadin"Bangane bata Numfashi ba..? Aba bai Tsaya sauraransu ba ya taka ya shiga Dakin yaya jafar na ganin haka ya watsar da kayan Hannunsa yabi bayansa Zeenatu sai ta kasa Binsu kafafunta sun kasa Daukanta koda batasan Mutuwa ba Ta tabbata yaya MUTUWA tayi..! Ba wanda yasan da shigowar su Aba sai dai ganinsu kawai akayi Kamar Daga sama Hamida da Hanne da Amina sun rirrike hannun juna cikin wani yanayi Mamanmu tana ganin Aba sai ta fara sauya yanayinta Taga yadda take kallon yaya tana Sakin Mirmishin jin dadin. Kan jikinta ta fada lokaci Daya tana Fashewa da kuka sai kuma ta Mike ta Nufi Aba tana nunamai yaya Lokaci Daya tana fadin"Sa"idu duba ka gani..Kamar yaya ta MUTU fa bata motsi..! Kalmar ta Mutu shi ya shiga kunnen Amina da wani yanayin da har Abada bazata manta dashi ba..! Aba kuma sai ya Ture Mamanmu ya karisa gaban Yaya ya jafar na bayansa Cikin wani yanayi Kallonta yake yi yana kokuwa da Numfashinsa Allahu akbar ashe ashe mganar da sukayi jiya itace ta bankwanansu Allah ya jikanki Hadiza ya fada acikin ransa kafin ya Dago hannunta da yayi sanyi karau har ya fara sandarewa na dan Lokaci kafin ya saketa Mamanmu ta Dora hannu aka tana fadin"Ta Mutu ko..?mun shiga uku mun Lalace wayyo ni Balaraba..! Kan Yaya tayo da Sauri Aba ya Riketa yana fadin"Natsu mana Balaraba..Wa ya ce miki ta mutu..? Cikin dan Daburcewa tace"Bata Mutu ba..? Kallonta yake da dukkan zuciyarsa yana Faman karanto duk addu"an da tazo bakinsa shima natsuwarsa ke neman kwacemai yasa ya Saketa yana Fadin"Jafar je kazo da Mallam..! Da haka ya koma jikin Wardrope din Dakin ya jingina kansa yana jin kamar zai fadi Jawaad da ya fara kuka ya isa garesa ya Rumgumesa yana Fadin"Aba kace mama tatashi..! Sai Sa"idu yaji kamar ya Sulale kasa Ya sume saboda yanayin Dayake ciki rumgume Jawwad yayi kawai yana fadin"Kayi hakuri jawaad..! Haka kawai yake fadi zuwa Lokacin Kukan Mamanmu ya cika Dakin su hamida ma sun fara ita da Hanne banda Amina da ta kasa Fassara yanayinta ji take kamar ta Bude ido Taga komai ya koma mafarki ne..! Sai dai ina abunda take gani gaskiya ne domin ba Dadewa sai ga Ya Jafar da Baba Mallam sun sake shigowa Cikin Tsashin hankali Aba na ganinsa yace"Dubata Mallam ta rasu ko..? Baba Mallam bai Sauraresa ba sai da ya isa kusa da yaya ya kalleta na wani Lokaci ko bakasan mutuwa ba in ka kalli yaya zakasan ta amsa kiran Mahallicinta Cikin Fargaba yake da Tashin hankali Tun zuwan jafar dama ga Damuwar abunda ya faru gabadaya shi kanshi Baba Mallan fata yake yaya bata rasu ba baisan da wani ido zai kalli Sa"idu ya Fadamai Hadiza ta rasu ba..! Hannunta ya rike na wani Lokaci kafin ya saka kunnensa Saitin zuciyarta na wani Lokaci cikin Sanyin Jiki ya Dago yana kallonta kafin ya Juya yana kallon Aba da kaifaffun idamuwansa da na ya jafar suke kallonsa da su Hamida Mamanmu kuma Sai kuka take rusawa..! Aba ya kalli Baba Mallam yana Fadin"Ta rasu ko..?Don Allah in ta rasu ka fadamin..Na yarda da Allah ke kashewa kuma shi ke rayawa..! Baba mallam yayi mamakin Kalaman Aba aransa yaji salama Cikin Dattakomsa yace"Kayi hakuri Sa"idu..Allah yayi ma Hadiza RASUWA..! yafada Lokaci Daya yana Dafa kafadarsa alamun Lallashi abun mamaki bai ce komai ba illah matsawa da yayi ya shafe idonta sannan ya Dagata ya cire mata Hijabin jikinta ya Lullube kanta dashi Lokaci Daya yana Fadin"Allah ya jikan ki Hadiza..Allah ya kyautata zuwanki...Allah ya Sadaki da Mala"ikun Rahma hakika ke yar aljannah ce Laifin da kika aikatamin da ganga da wanda kika sani da wanda baki sani na yafe miki Duniya da Lahira Allah ya yafe miki kema yasa ki kwanta Cikin kabarinki Cikin Salama ke da kika tafi baki Gaggawa ba..Muma da muke duniyan Jiranta muke Allah yayi miki Rahama Hadiza..! Sai alokacin Muryansa ta fara rawa yasa ya Dakata Baba Mallam da ya Jafar dake kuka Suka amsa da Ameen Mamanmu ce ta fasa wani ihu ta Fadi kasa sumammiya shi ya shigo da ya Zeenatu Dake kuka itama ganin Yaya Lullube yasa itama ta fasa kuka tabi ayarin su Hamida Dake durkushe gaban Mamanmu suna kuka ya jafar ne yayi jarumtar fita ya Debo ruwa suka shafa mata sai gata ta farfado tana kuka tana mganganun Rudewa da yadda Mutuwar ta Daketa matuka..! Baba Mallam ne yace"Balaraba ba kuka Hadiza ke bukata ba sai addu"a ayi hakuri..kinji ko Allah ya jikanta..! Mamanmu fadi take"Yaya ta rasu..?Innalillahi..Wayyo Allah na..! Haka take fada tana kuka jikin ya Zeenatu dake ta kuka itama su sun samu Damar kuka ita Amina ta nan Tsaye kukan ma yaki zuwa mata maimaitawa kawai take yi wai yaya ta rasu..?ina wannan ai ba gaskiya ne yayan da jiyanan lafiyanta kalau..! Baba Mallan ne ya Dago Aba Dake duke gaban Yaya yana kokarin Daidaita Numfashinsa cikin lallashi yace"Sa"idu tashi.kayi hakuri ka nuna Jarumta..In ka rushe suma iyalanka zasu rushe..! Ba Musu ya Mike yana Rike Jawaad da Zuwa Lokacin ya Fahimci abunda ya Faru shekarunsa goma sha Daya yasan Mutuwa rumgumesa yayi yana kallon Baba Mallam Lokaci daya yace"Asanar ma da Mutane Baba..Jafaru kuma sai yazo da mai awon Likkafani domin ashiryata mu sallaceta zuwa gidanta na gaskiya..! Baba Mallam ya jinjina kai kafin yace"Shine abunda zamu mata mu nuna mata soyayyarmu.muje waje..Bazaku iya zama da gawa,kuna wannan koken koken ba..Bari naje na Turo Hajiya..! Ya jafar gaban yaya ya karasa ya Bude Fuskarta kafin yace"Allah yayi miki Rahma yaya.. Kuka ke neman kwacemai yasa ya fice da Sauri Su ya zeebatu suka kama Mamanmu dake kuka Sai alokacin Baba Mallam ya Lura da Amina cikin wani yanayi yace"Mamana sai hakuri kin ji..?Hadiza addu"an ku take Bukata kawai..! Abun mamaki kallonsa tayi da idanuwanta cikin wani yanayi tace"DA gaske yaya ta rasu..! Kai ya gyada mata kafin ya samu Zarafin mgana tace"Ba sai ka kira Hajiya ba..Ni zam zauma da ita har ku dawo..! Gabadayansu suka kalleta Har Aba da su Mamanmu Cikin Sautin Amon muryan data Sadaukar dakomai tace"Eh zan zauna da ita..Don Allah kada ku hanani..Ku barni na zauna da ita na wani Lokaci na karshe a Rayuwata..! Sai kuma taji kamar Rauni zai bayyanan mata sai ta Dake domin ji tayi kamar zuciyarta ta kara Bushewa ba wanda bai ji Tsausayinta ba Baba Mallan ya dafa kanta yana Fadin"Shikenan Mamana ki zauna da ita banda kuka kiyi ta mata addu"a..! Da kai ta amsa mai kafin ta Nufi gaban Yaya ta tsaya sai kuma ta Sulale ta Zauna da katon Hijabinta Cikin wani irin Sauti tace"Nan zan zauna..har Ku dawo baba Mallam..Ko bata ji Dumina ba..Zan tuna watarana na zauna da ita alokacin da Numfashinta ya bar jikinta..! Ba wanda ya tankata har suka fice Baba Mallam da Aba suka fita daga gidan su Zeenatu kuma tsakar gida suka koma suna ta kuka kafin kace me Mutuwar yaya ta Zaga ko"ina duk wanda ya kamata yaji wannan Mutuwar data girgiza mutane da Dama kowa akace yaya ta rasu sai yace Daman tayi ciwo ne..?Mutuwa ko babu ciwo ana tafiya..! Hajiya babba Mutuwar Yaya ta Daketa Matuka duka matan Baba Mallam suna gidan Baba sa"idu tare da Mamanmu da Yaran,Amina taki Fitowa Daga Dakin yaya tana zaune gaban gawan ba kuka take ba sai dai da ka ganta bata cikin natsuwarta Fata take taga komai ya koma ba yadda take gani ba Hajiya tayi tayi Amina tatashi ta koma Falo in da su Mamanmu ke zaune dasu Anty Amarya su hanne suna Dakin mamanmu sanye da Hijabai su da matan su ya jafar sun saka hijabai suna ta karatun Qur"ani suna Hawaye tunda Hajiya ta hana su kuka..! Ammh Amina taki tashi fadi take"Hajiya ki kyaleni..Wlh Lokacin Yaya na Raye ban taba zama da ita ko na minti biyar ba..?Bazaki barni na zauna da gawanta ba ko naji Dadi..! Daganan Hajiya tasan Amina ba kalau take ba,Sai ta kyaleta sai itane tazo suka zauna anan tare tana mamakin ko Kwallah Daya Amina batayi ba..! Tana fatan kada abunda suka faru da su saka zuciyarta ta Harbu da wani matsala.. Alokacin bataasan me Amina ke Tunani ba..Mganar Aminu ta Tuna da taba cemai ta fison Mamanmu akan yaya alokacin Dariya yayi yana mata kallon yarinta kafin yace"Meenata ke yarinya ce har yanzu shiyasa baki san girman uwa ba..Ammh Har Abada Uwa uwace bamai kwace wannan Matsayin Allah ne ya basu..Bazaki Fahimce matsayin Uwa ba sai Ranar da kika rasata ina mai Tabbatar miki ko muna tare ko bana Tare sai kin fi kowa kukan rasa yaya..Ga Mamanmu din da kike fada ammh Bazata iya kare miki wannan Jinin ba Amina..Bazata iya shafe miki makwafin UWA BA har Abada..! Sai ayanzu mganarsa take Dawo mata Domin abaya in ya fada bata Damuwa da mganarsa ashe ashe ranar ma tanan nan kusa abu Daya ke damunta Yaya ta bar duniya tana Fushi da ita da ZArginta sannan Tunda ta haifeta bata taba Hutawa da Jidalinta ba Abun yana Sakata jin kamar ta Mutu in ta Tuna bata taba zaman minti Biyar da yaya ba da sunan Hira ba..Anya bata zama asararriya ba kuwa..?Kaiconta ita Amina in akwai wacce Mutuwar Yaya zata kasassara to itace domin su ya Jafar har ta bar Duniya bata taba Daga baki akansu ba sai ita kadai da ta fita Zakka cikin ya"yanta..! Karfe Daya na rana aka saka za"ayi Jana"izarta zuwa Lokacin harta kannen iyayenta da suka rage na nan Gumel din sun zo sai wata goggonta goggo Jumai Sun zo suna gidan Sai su ya Zulaihat da suna Jigawa Labarin Rasuwar ya isketa sai ya Ikram da ke kusa duk suna nan gidan suna ta kuka Goggo Husai Mallam da kansa ya Kirata ya Fadamata,Ita ta shaidama Jadwa wanda akace sai da ta suma Mijinta na chan na nema musu Visar tahowa sai Mutanen gusai da Aba ya Kirasu ya shaida musu..! Jaleela kuma ya kira mijinta ya Fadamai shi ya Fadamata sai kuka Domin mutuwar farar Daya tafi shiga Jiki sosai ance sun samu Jirgi sun taho Ita da megidanta da ya"yanta da Ya Nazir da matarsa tafiyar su daya..! Sai ya Jamila Dake gombe ita din ma Mijinta aka kira aka Fadawa yace suna Tafe suma,Jawahir kuma da yan Gusai zata taho Allahu akbar rai bakon Duniya..! Zulfa ma an gayamata tana Hanyan Tahowa ita da Nazeem Uzairu na Exam,sai Zahra Dake parthercourt Itama Tafiyar Jirgi tace zatayi sauran Iyalan Baba Mallam na kusa duk sun ce suna Hanyar Tahowa..tunda Rasuwar ta Safe ce..! Dan mallam Dake chan Madina abakin Ya Nasir yaji Rasuwar Yaya Mutuwar data sanyayamai jiki matuka yana cikin makaranta sanda yaji Rasuwar ko kafin ya koma gida Sakina taji Labari itama cikin Tashin hankali ya fita nema musu Visar tafiya shi da Sakina Sarood nan zai barta Saboda kada Zirga zirgan tayi yawa..! Ko kafin karfe Dayan an gama Hada yaya,Hajiya Babba da Wata Tsohuwa daga Gusai da suka iso suka hadu suka mata wanka suka shirya har alokacin Amina bata bar dakin ba kuma ko Hawaye Daya batayi ba..! Kofar gida kuma ya cika Damkam da Jama"a tunda har agidan Radio an Sanar da Rasuwar zuwa Lokacin yan gusai sun iso sannan Ya Fati dake Dutse ta iso ita da Ya akila da Jidda ko"ina ya cika ba matsaka tsinke domin Yaya ta jama"a ce uwa uba kuma Aba dasu ya Jafar da abokan aikinsu sun cika wajen Allah sarki Aliyu abokin Danmallan yazo Jana"iza Tunda Umar ya fadamai yace sai yazo ya samu Janaza..! Gida bai kara Daukan Kuka ba sai da aka zo fita da gawa bayan an kira duka Ya"yan Aba domin su mata addu"a wadanda suka iso kenan Ya Jawahir da ya Jafar sune manya sai su Amina da su hamida addu"a suka mata da Fatan dacewa Har Hamida da Hanne sun duka gaban gawanta sun mata addu"a Amina kuma sai da Hajiya ta Dukar da ita gaban gawan tana Fadin"Mamah yi ma mahaifiyarki addu"a..! Sai ta zama out of Control yan"uwanta nata basu damu da Rashin kukanta ba susan bata Damu da yayan ba sai dai abunda basu sani ba awannan gabar Amina ta fisu bukatar uwa a raye domin ita ke cikin Tsaka mai wuyar da Uwace kadai zata Tsaya akanta da addu"a ammh kuma addu"a uwa ga ya"yanta har gaban Abada bata yankewa..! Tana gaban gawan Kanta sara mata yake yi gabadaya yan Dakin sun koma masu fararan kaya haka take ganinsu kuka take so tayi ammh ta kasa kawai sai ta Sulale ta Rumgume gawan Yaya tana Fadin"Ki yafemin Ki yafemin..MAMA..! Haka take ta fada cikin ihu Saboda tana so tayi kuka ta kasa sai Tsausayinta ya kamasu Da jawaad suke Tsausayamawa ammh Halin da suka ga Amina sai Rauni ya Tarun musu mamanmu na wajen tana ta kuka Hajiya Babba ke fadan ba kyau wannan kukan da suke mata..! Ya Jafar ne ya jawo Amina Jikinsa ya Rumgume su ya Nasir suka kama gawa zasu fice tana ganin haka ta fara Fizge fizge tana Fadin"Ku bar min gawanta..Don Allah ku bar min ita..! MAAMA...! MAAAAMMAA..!!!! Hake take fada cikin karyen Sautin da duka kowa yasan ba Sautin Amina bane Ana fita da gawan ta fara Bige Bigen da sai da tafi karfin Jafar su Hajiya suka taso suka sakamata karfi. Da Karfi take fadin"Ku dawomin da ita..Mamatace..! Haj Nasara na sharan Hawaye tace"Allah sarki..akace Uwa uwace Ko da akan Bola take kwana..!ba wanda yayi Tunanin Amina zata damu don Yaya ta bar gidan Duniya..! Ana gama Fita da gawan sai ta Daina ihu da Fizga ta koma kuma ta Sume musu kamar yadda aka kwashi mamanmu da ya Jawahir suma sun Zube kai anga Tashin hankali gida ya Rude da koke ba wanda akayi mamakinsa sai Aba ya nuna Jarumta ko Daya ba wanda yaga kukansa Dashi aka sallaci gawan Yaya aka kuma kaita makabarta yana rike da Hannun Jawaad da yaci kuka ya koshi..Aba bai yi kuka ba sai da Mallam yace ya matso shi da Ya Jafar da Ya Nasir da yan"uwanta suka sakata Cikin Kabarinta su ka kuma Debo kasa suka Rufe dashi sai alokacin yaji kuka ya taho masa Baba Mallam na bashi baki kan kabarinta ya Duka har su ya jafar suka gama mata addu"a bai tashi ba Fadi kaawai yake,"Tun zamana da ita bata taba Sabanin da gangan ba..Allah ya jikanki Hadiza har abada bazan samu makwafinki ba..! Dakyar Baba Mallam ya rikosa suka bar makabarta suka Dawo nan Haraban gidan Mallam aka Saka Dardumai da Tabarmu ana karban gaisuwan maza, mata kuma suna cikin gidan Aba ko"ina Kaje sai yabon yaya ake yi ba wamda zai Bude baki bai Fadi Alherinta ba an samu su Amina sun Farfado sai dai ita Tunda ta Farfado bata kara mgana ba kuma bata kuka tana kusa da Hajiya kogaisuwa akazo sai dai tabi mutane da kallo..! Sai Dare gidan ya kara Rudewa isowar sauran baki su ya Zahra da ya Zulfa da su ya Jaleela da yaya Jameela sai ya Nazir da Matarsa su ya Aisha duk sunzo karon farko zuwansu gida ba cikin Dadin rai ba,ya Sadiya ce bata zo ba suna Ameriaca inda Mijinta ke aiki tadai kira tayi gaisuwa..! Ita Mutuwa daman ai bata da Sabo..ko abinci ba wanda ya Nema duk da ana ta kawowa Sadaqa,haka wadanda Mutuwar ta shafa sukayi kwanan zaune suna kuka da addu"an Allah ya jikan Yaya su ya jafar kuma suna waje suna karban gaisuwa sai dai in Mazan sun nemi shigowa sai suyi musu Jagora..! Ko su saka su shamsu su shiga dasu hatta yan makarantar Islamiyansu da Hadda sun zo gaisuwa su da Malamanau da Dalibansu Sai alokacin akaji Amina tayi mgana data amsa gaisuwan mariya yar ajinsu Sa"adatu duk suna nan gidan suna tare dasu Hanne duk wani mai imani in yaga Amina sai ya tsausaya mata ta Fyade ta rame bata ci bata sha sai an matsa mata..! Ranar da akayi sadakar uku Goggo Husai ta iso da ita da Jadwa sai mutuwar ta Dawo sabo aka fara koke koken Zuwa yammah sai ga Yaya Danmallam da Sakina sun iso suma..! *AKWAI SOFTY COPY DA HARDCOPY NA LITTAFIN GIDANMU MAI BUKATA SAI YAMIN MGANA SANNAN LITTAFIN ZAMAN GIDANMU MAI CIKE DA KUNCI SHIMA ZA"A SAMESA A SOFTY COPY DA HARDCOPY KAN FARASHI MAI SAUKI A TUNTUBE NI TA WANNAN LAMBAR DOMIN KARIN BAYANI 09069067488* *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️24* Aranar dai Danmallam bai shigo cikin gida ba yana kofar gida wajensu Aba da Baba Mallam,Sakinar dai ta shigo nan cikin gida ana ta yi musu barka da sauka Daki daki ta shiga tayi gaisuwan kafin ta koma Dakin su Amina inda su Ya Jidda ke zaune..! Sai washegari da Misalin karfe shaDaya na safe suka shigo shi da ya jafar da ya Nasir da abokinsa Aliyu..! Dakin yaya suka fara shiga tunda nan su Hajiya Babba ke zaune ita da Haj.Nasara da goggo jumai sai jama"ar gusai,sai Amina da Tun da akayi Rasuwar tana Dakin Bata yarda ta kwana ako"ina ba Sai gefen hajiya wacce ke Tsausayinta tana kula da ita Su Hamida da Hanne da zafira da suka zo Dakinsu suke kwana su da su ya Abida sai dai wasu na Ragewa in Dare yayi su koma gidan Baba Mallan su kwana ammh hajiya Babba da Haj.uwani nan suke kwana Anty Amarya ce da Hj.Nasara ke komawa gida su da ya"yansu su kwana..! Sanda suka shigo Amina na Tsakanin Hajiya Babba da Mamata mahaifiyar Zafira sanye da Hijabin nan nata na Makaranta Tun da akayi rasuwar ko wanka batayi ba ballatana tayi Tunanin Sauya kaya gabadaya ta sauya kamar ba Amina ba mgana ba Tsiwa ba Hayaniya ashe ashe akwai Watarana da Bakin Amina zai mutu..? Daga Ciki suka shiga suka Durkusa suna gaida iyayan nasu Danmallam ya Dago kansa yana kallon Hajiya cikin Tausasawar Sautinsa yace"Hajiya ya karin hakuri kuma..?Allah ya jikan yaya Allah yasa ta huta..! Hajiya ta amsa da"Ameen ya Allah Hakurin duka namu ne Danmallan Fata kun zo lafiya..?Naga sakina ban ga Saratu ba..? Kansa na kasa yace"Tafiyar ba Shiri Shyasa ban taho da ita ba..Ammh tace ayi muku gaisuwa Haka ma Abu kattab yace yana muku gaisuwa shi da Mami Sara..! Hajiya tace"Mungode kwarai Allah ya bar zumunci..!Aliyu ma ya gaisheta ta amsa tana tambayan iyalansa yace suna Lafiya sai godiya Hajiya take yi tana Fadama Danmallam da Aliyu akayi Janaza in ji mallam..! Nan ya juya suka gaisa da Haj.Nasara da goggo Husai da mamata da sauran yan gusai ana ta Nunasa ana kuskus din fadin shine babban yaron Mallam dake madina..! Amina na jinsu tun sanda suka shigo Gabanta yake faduwa bata son ma ta Dago kanta ta ganshi Domin zuciyarta har alokacin ta kasa karban gaskiyan ta Auri wanda bai dace da Rayuwarta ba,Shiyasa tun sadda suka shigo kanta na kasa bata yarda ta Dago kanta ba ballatana ta ganshi..! Sai dai duk Gudun hakan da tayi bata Tsira ba,Saboda Ya Jawahir ta shigo da kulan abinci tana Fadin"Hajiya ga Alale an kawo daga gidan Mallam Sidi..iyalan nasa sun fara shiga Dakin mamanmu ne..! Hajiya tace"Angode Allah ya bada Lada..! Sai kuma ta kalli Amina Dake gefen hajiya Lokaci daya tana fadin"Amina ko zaki Daure kici abinci ne ga Alale an kawo nasan kina so..? Tafada Cikin Tsausayinta da ganin yadda Mutuwar ta daketa Fiye da Tunanisu kiran sunanta da Hajiya Tayi shi ya jawo hankalin Danmallan gareta Wanda kansa ke kasa har Lokacin Duke kan kafafunsa Daga chan gefe shi da Abokinsa Aliyu,Su ya Jafar sun fita tsakar gidan suna mgana da Ya Jadwa ne..! Daidai Lokacin itama Amina ta Dago Manyan idanuwanta da suka zama sune kadai afuskan nata ayanzu karaf kuwa suka Hada ido Hudu atare gabansu ya fadi ras..! Ambaton sunanta yasa abunda ya faru kwanaki hudu kafin wannan Rasuwar ya fadomai Alokacin abun na ransa yana Damunsa sai dai wannan Rasuwar ne ta shafemai wannan Tunanin,Kamar yadda yake kallonta haka itama take kallonsa Cikin wani yanayin da bai gane ba Shidai kallonta yake yi yana auna Mallam bai kamata ya aura masa wannan yar Cikinsa ba,Ba shi ya Dace ba ga Nazeem ko Nasir sune zasu yi Daidai da yarinyar bashi ba da bai hango da inda suka yi dacen da Mallam zai zabosa ya aura masa ita ba Bayan haka baya shiri da mara kunya ko Fitsarrre sannan yasan yarinyar nan Gangararriya ce gata kazama ga Rashin Natsuwa ga yarinta ayadda yake jin kansa Sakina da Sarood ma Nauyi suke mai ballatana an aura masa wannan yarinyar kamar an gayattomai Jidali ne da Rashin Sukuni acikin Rayuwarsa..! Ita kuwa ba kare masa kallo take yi ba Zuciyarta ta Kuntake waje Dayan data kasa gane komai ita dai tasan Sanye yake da Farin Boyel Riga da wando da Hula zanna Bukar,sannan ya kara Fari Gemunsa kuma kamar ya kara Tsawo sai dai kallo Daya zakayi mai ka san Jin Dadi da Hutu sun zauna mai Saboda yanayin Fatarsa da yanayin Murjewan jikinsa zaka Fahimci Hutu da jin Dadin Rayuwa sun samu kyakyawan zama awajensa..! Tana kallonsa ne tana jin kamar ta yanka Ihu acikin ranta ta kasa dora Mizanin komai domin tana ji kamar bata da Hankali Domin yin wani nazari kan Rayuwarta sai Hankalinta ya Dawo Jikinta kamar yadda ta kafe shi da ido shima a fakaicen yake kallonta sai dai abunda bai sani ba azahiri ne take kallonsa abidini kuma ta shiga wani yanayi ne yanayin da bawan da Allah ya Jarabta yake ciki..! Haj.Uwa ce ta sako baki tana Fadin"Ai da ruwan zafi ta fara sha Hajiya sai hanjinta su sake..! Wannan mganar ta Haj.Uwa shi yasa Danmllam Saurin Dauke kallonsa Daga gareta itama sai alokacin ta maida idanuwanta kasa tana Faman kokuwa da Numfashimta..! Hajiya tace"Eh kuma na sha"afa Domin tun Rasuwar nan banga Amina taci abinci ba sai ruwa..Sai Hakuri Allah daya fimu sonta ya Dauketa Mamah addu"an ku kadai take Bukata yanzu..! Mamata na gefe tace"Wlh sai hakuri ni Aminar ce ta bani mamaki..Yadda Mutuwar yaya ta Daketa na Dauka Ko zai Daki kowa banda ita Tunda Balaraba ta Kore mata Kishir ruwan uwa. ! Haj.Uwa ce tace"Uhm bari mamata..Kinsan Girman Daraja da Kaunar dake tsakanin uwa da abunda ta Haifa..?Mutum bai isa ya Fada ko ya kwantata ba..Allah Kadai yasan iyakarta..! Sai Dakin ya dau mgana kowa na Fadin albarkacin bakinsu yawanci mgana suke kan yaran bazasu maraici ba ga Balaraba wacce take Tsaye kan yaran Tun yaya nada rai bata san wahalan ya"ya ba komai Mamanmu ce..! Danmallam ganin mganar ta koma wani bangare yasa suka yi ma su Hajiya Sallama suka fice Amina ta Bisu da kallo gani tayi ma kamar ya kara Tsawo da zai fita sai da yadan Rankwafa duk Tsawon kofar yaya..! Dakin Mamanmu suka shiga inda take karban gaisuwa ita da Anty Amarya da Haj.Nasara sai sauran yan"uwanta ,Sai su Sakina Dake dakinta ita da Jidda da Su Zulfa,nan suka yi musu gaisuwa yaran kuma na Rawan jiki gaishesu basu jima ba suka fito suka shiga Dakin yaran Lokacin Jawahir da Jadwa sun shigo Dakin Suka gaishesu suka amsa kafin suyi musu gaisuwa basu jima ba suka Fice Daga gidan zuwa kofar gida inda ake zaman gaisuwa..! Sai da suka zauna chan Nesa da Tabarman su Baba mallam inda manyan Mutane ke zaune abokan aikin Aba da kuma Amintattun malamai abokan Da"awan Baba mallam,Sannan Danmallam ya kalli Aliyu yana Fadin"A cikin dakin da yaya da muka shiga kaga wata yarinya da Hajiya ta Kira da Amina..? Bai bama mganar Muhimmanci ba yace"Eh wacce ake cewa bata ci abinci ba Tun bayan rasuwar..? Da kai ya amsa masa kafin ya Cije baki yace"Wai ita Mallam ya aura min kwana Hudu da suka gabata..! Sai Aliyu yaji kamar bai ji da kyau ba ya kallesa yana Fadin"Bangane ba..? Dammallam yayi mirmishin Takaici kafin yace"Am serious abunda kaji gaskiya ne Aliyu..! Aliyu ya Dafa kafadan Danmallam yana fadin"Kai..Abu haka kwatsam Shehi.Oh wlh yarinyar Sweet Sisty ce Abokina kace kaima kabi shawarata kafara yin gaba kafin ni..! Kalamam Aliyu sun kara batamai rai Cikin Takaicinsa yace"Kai yanzu in nace maka da son raina na auri yarinyar chan sai ka yarda..? Tsiyana Dakai wauta..Wlh tallahi bazan iya da mata uku ba Aliyu.bama haka ba yarinyar tamin kankanta sa"ar autan Hajiya ce fa Hanne tare suke fa ina zan kai yar cikina Aliyu..?bana son jidali Allah ma ya taimakeni Sakina ta kwantar da Hankalinta Sarrod kuma bata da Hayaniya ammh ina Tabbatar maka auran yarinyar nan sai ya Rusani Aliyu kasanni bana son Hayaniya da Damuwa ya kake gani na Hada yarinyar nan da sauran matana..? Ba ka hangomin tashin hankali azama na dasu..!? Ya karishe fada cikin Rauni Aliyu ya jinjina kai yana fadin"Eh kaima kayi mgana..To ya abubuwan suka faru..Ai nasani Mallam baya aurar dasu sai sun yi candy..! Danmallam yace"Abubuwan da suka faru suna da yawa...Aliyu Abu Daya na sani Mallam ne ya Kirani ya Tambayeni yardata ba kuma neman izini ba Aliyu tayaya zan watsama Mallam kasa a ido..? Bazan iya ba..Yana da Kima da Darajan da ko Wuta yace na Fada zan fada Uwa uba kuma Diyar Baba Sa"idu ce har Abada jininsa nada Daraja awajena sannan Diyar yaya ce Allah ya jikanta ko kasa sun shafe idonta bazan ki karban Abunda ta haifa ba Aliyu Yaya Mutum ce Hajiya ta Fadamin bayan ita data Haifeni yaya tayi wahala dani Wahalan da ko ya"yan data Haifa bata musu ba kana ganin in naki karban abunda suka Haifa Allah zai yafemin Aliyu..? Yafada yana saka yakininsa da Kallonsa kan Aliyu da yayi Kasake yana kallon Umar din..! Bai basa zarafin mgana ba yacigaba da Fadin"Sai dai abu daya na sani..Meyasa Mallam ya Zabeni..? Bayan ni akwai Nazir,Ga Nasir ga Nazeem ayadda nake gani akwai kwaruwa yarinyace karama da batasan komai ba sai Shirme an cutar dani An cutar da ita Dukkanmu Rayuwar batayi mana Daidai ba Aliyu..! Awannan gabar ji yake kamar ya saka kuka sai dai ina Jarumtarsa bazata barsa ba..! Aliyu ne ke Bubbuga Kafadansa yana Fadin"Easy mana Shehi..Biyayya kayi kuma insha Allahu bazaka tabe ba..Komai da kaga ya faru tsarin Allah ne..Sannan da kake fadin gasu Nasir ai mallam din ya san dasu ko..?kuma ya Zabeka na Tabbata kamar yadda ya Zabeka cikin ya"yansa yana da kyakyawan yakinin bazaka basa kunya ba..Sannan kai din kafi su chanchanta kabar mganar yarinya ce Annabi ma ya auri Nana Aisha As tana da Shekara Tara ne kaga kuwa sunna ce sannan yarinyar nan ba karama bace yadda kake tsammani zata kai 16 to 17 fa Shehi ai kuwa batayi kankanta ba wadanda ma basu kaita ba anayi musu aure kuma su zauna Lafiya kuma mganar yar cikin ka yaushe ta zama yar cikinka..?Just 39yrs fa gareka Shehi ta ina zaka iya Haifanta banda Tsabar son girma da Sharri irin naka..! Sai da ya Murmusa jin kalaman Aliyu kafin yace"Ammh dai kasan da auran wuri nayi..Da yanzu ko ban haifi kamar ta ba na kusa..!? Aliyu na Dariya yace"Uhmm.Naji Ka dai kafin naji watarana yar cikin naka ta baka Wahala..! Ya karishe fada yana kallon sa kasa kasa karamin Tsaki yaja kafin yace"kasha kwaya ne..?ko ka fara Hauka inaga..Ni fa duk ba wannan ba Ina cikin Tashin hamkali ko su Sakina ban yi mgana dasu ba fa..! Aliyu yace"Tab..Ai sai kayi hakuri..Domin tama ji ta gama Tunda dai kuka zo nan..! Dammallam ya Sauke Numfashi bai yi mgana ba Diramar da zasu kwasa Kadai yake hangowa in Sakina taji Labari ganin haka yasa Aliyu yake ta Kwantar mai da Hankali tare da bashi Shawarwarin da zasu mai amfani kuma ya natsu yana jinsu aransa yana godema Allah Daya Hadasa da aboki nagari kamar Aliyu. Hakika an ga jama"a Domin kungoyin Matam malamai duk sun zo gaisuwa,Kowacce cikin masu auran nan Dangin mazajensu sun zo gaisuwa,Mutane ne suke ta Zuwa har abun yaso bama Mutane mamaki,sai dai kuma ba abun mamaki bane sanin Wacece Yaya shaidar duniya itace ta Lahira Tabbas yaya ta dace Kowa sai mamakin Aba akeyi ganinsa Cikin natsuwarsa ba wanda yayi Tunanin Mutuwar bazata Gigitasa ba..Sai dai ina wadanda suke son ganin gazawar tasa basu gani ba Tabbas Mutuwar ta tabasa sai dai ya Riga ya yarda da Allah ke kashewa kuma ya raya alokacin Daya ga Dama sannan kuma Ga Baba Mallam agefensa Koda yaushe cikin mai Nasiha yake yi da karamai karfin Gwiwa Kuma cikin ikon Allah komai yazo da sauki yana Tsaye kan kafafunsa Cikin Jarumta da Takwalli..! Sai da akayi addu"ar bakwai kana aka Rufe zaman gaisuwa akuma ranar Baki suka fara tafiya hatta yan gusai da yan bazanga maza da wasu daga cikin matan sun koma da Rana yaran dai duka suna nan,sun samu zama Tunda Mallam bai ce komai ba shi kuma so yake sai ya Hadasu yayi musu Nasiha sannan ya Umarci kowacce ta koma Gidan Mijinta Haka kuwa akayi ranar da yaya ta cika kwana Takwas da Rasuwa da Daddare a Falon Baba Mallam ya tarasu kowa da kowa banda ya Nazir da ya koma Tun ranar uku saboda aiko ko Umar da yazo basu hadu ba..! Yara da manya Harda Jawaad dake jikin Aba wanda tunda akayi rasuwar Aba ne komai nashi yanzu..! Mazan gabadaya suna zaune akasa ne gaban Baba Mallan hatta Aba yana zaune akasa ne sai su Hajiya Babba,da su Hajiya Nasara da Anty Amarya da Anty Uwa sai gefe Mamanmu ita ke zaune ita da yaran gabadaya Amina na can karshe kusa da Hanne kanta na kasa Tun bayan rasuwar sai yau tayi wanka shima sai da Hajiya ta nuna bacin ranta..! Bayan Bude taro da addu"a da Ya Nasir yayi Baba Mallam ya fi Minti Talatin yana musu Nasiha da jan hankulansu gabadaya harda Aba Daga karshe yayi musu Fatan suyi hakuri su Rumgumi wannan Rashin da fatan Allah ya haskaka kabarin Hadiza aka amsa da Ameen..! Ba zato ba Tsammani Mallam ya Fadi auran dayq daura Tsakanin Umar da Amina,Kowa daman ya sani wannan Mutuwar ne tasa ba wanda ya Tada mganar Sakina na wajen sai dai ta Riga ta samu Labari bakin Sa"adatu data tambayi Anty Amarya ta tabbatar mata,Bata wani damu ba Domin Anty Amarya ta mata alkawarin ba inda auran zai je ayadda aka Kullashi hakaza"a warware shi ne..! Danmallan Sakina yake kallo yaga yanayinta sai dai bai Fahimci komai ba Illah Mirmishin Fatan baki data Saki aranta Tana Tunanin kishi da wanchan mara kunyar yarinya ai bata Lokaci ne ta tabbata ko a kafa aka Daurama Umar ita sai ya kwanceta yayi ta kansa to me zai Dameta..! Dukkansu yaran sunyi Fatan Alheri batare da sun ji musabbin abunda ya Faru har Lamarin ya koma haka ba Sai dai sun san da abunda ya Faru haka kurum Baba Mallam bazai Sauya Tsarinsa na aurar dasu in sun yi Candy ba,sai dai tunda bai sanar dasu ba sai suka bar mganar hakanan..! Daganan addu"an tashi akayi ya sallamesu da Umarni goben goben nan kowacce ta shirya komawa gidan Mijinta Angode hakanan da Toh suka amsa suna ma godiya domim sun ga ma kokarim sa daya barsu suka yi kwanakin nan bai yi mgana ba..! Ya sallami kowa illah Hajiya Babba Dayace ta Tsaya ita da goggo Husai da Ya Danmallam sai Aba kadai yace yana son mgana dasu..! Amina ta mike zata fita Baba Maallam Dake Lura da ita ya Dago yana Fadin"Mamana kariso nan ina son mgana Dake..! Hannunta na cikin na Hanne ta zame ta fara tafiya zuwa wajensa tana jin yadda Ido ya koma kanta abunda bata sani ba Uban gayyar kansa na kasa ko Dagowa bai yi ba Duk da yasan itace Mallam yake kira da Mamarsa..! Har gabansa taje ta Duka kanta na kasa Lokaci daya tace"Gani Baba Mallam..! Tattausan Mirmishi yayi kafin yace"Na ganki Mamana..shin ko yima Babanki gaisuwa..?Gashi nan Sa"idu nake nufi..? Yafada yana Nunasa sai Alokacin ta Dago tana kallon Aba Rabonta da ganinsa gani mai kyau Tun ranar da aka kaisa asibiti sai yau dataga ya Rame yayi baki yana cewa ya Tsufa sai yau taga Tsufansa ta bayyana yana Sanye dajallabiya Mai ruwan madara da Bakin wando kansa ba Hula Furfuransa duk ta bayyana Idanuwansa sun Zurma ciki alamun akwai rashin Barci da kwamciyar hankali..! Batasan sadda tace"Aba ka rame..Ka dade kana cemin ka fara Tsufa ban taba ganin tsufanka ba sai yau..Sai yau bayan kasa ta Rufe idon yaya..! Take fada cikin raunin Raunin da Tun da akayi rasuwar bata saukan mata ba sai yau datake ganin Aba agabanta da yanayin daya koma..! Kowa afalon sai da jikinsa yayi sanyi Aba kwalla ta kawo masa yana kaunar Amina kaunar Hadiza ne ta shafeta ba saboda komai ba sai Saboda kammaninta da Hadiza! Cikin Dauriya yace"Na Dade da Tsufa Amina..Sai yanzu ne tsufan ya bayyana..bayan na rasa Hadiza..! Akaron farko Amina ta fashe da kukan daya rike mata zuciya in Tana ganinsu ya Jadwa na kuka sai taji su gwara su yaya bata bar duniya tana Fushi dasu ba gwara su sun samu kyakyawan Mu"amala ita fa bata da wani abu da zata Dorar Tsakaninsu in yaya ta saka baki a lamarinta to na Bacin rai ne ba na Dadin rai ba..! Kuka take kamar ranta zai fita cikin kukan ta Rarrafa gaban Aba ta kama kafarsa tana fadin"Aba ka yafemin..Don Allah ka yafemin kada kai ma ka rasu ka barni baka yafemin ba kamar yadda yaya tatafi ta barni tana Fushi dani..! Haka take fada tana wani irin gunjin kuka,wanda duk mai Tsausayi da Imani sai ya Tsausaya mata hatta kuwa da Danmallam Dake gefe sai da ya Dago ya kalleta cikin wani yanayi..! Hajiya baya ta juya tana sharan kwallah Baba Mallam ne mai Dakiya yana Binsu da kallon Tsausayi..! Jawaad yayi barci shi yasa Aba ya kwantar dashi kan kujera sannan ya saka Hannu ya Dago Amina yana Fadin"Hadiza bata rasu da Haushinki ba Amina..Komai kikayi sai dai tace Allah ya shiryaki..Bata taba aibataki b .....Addu"ata gareki mai kyau ne Amina..! Hajiya babba ta amsa da cewa"Kuma addu"anta baza ta taba fadi abanza ba.Da yardan Allah zaku yi alfahari da Amina Hadiza zatayi alfahari da Amina ko bayan kasa ta shafe idanuwanta ne..! Yanayin falon ya koma na Jimami Barin ma yadda Amina ke kuka Data Rumgume Aba tanayi kuka mai Cin rai Baba Mallam ne yaga kukan yayi yasa yace"Mamana tashi nan bar kukan nan hakanan kina tadama Babanki Hankali..! Sai Lokacin ta bar jikin Aba ta sulale kasa tana Fadin"Ka yafemin Aba..! Yana kokarin Dauke Hawayen idonsa yace"Ban taba rike ki ba Amina..Komai kikayi min na bacin rai ina yi miki uzuri Wlh..Hadiza koda yaushe fadi take mu yi mata Fatan Shiriya mu yi fatan Allah yasa in ta Girma ta sauya..Na yafe miki Duniya da Lahira Amina Allah yayi miki albarka..! Tana kuka take amsawa da Ameen kafin ta Rarrafa gaban Baba Mallan rikota yayi ya Tadata ya zaunar da ita gefensa ya saka Gefen rawaninsa ya Share mata Hawaye yana fadin"Bar kuka..Addu"a zaki rika mata in kin Tunata kinji ko..? Kai ta gyada mai tana sharan majina Hajiya Babba tace"Kabarta tayi kuka Mallan tun fa rasuwar nan banga tayi kuka ba..! Sai Alokacin goggo Husai ta tanka"To zainabu sai kuma abarta ta tadama Mutane da Hankali..? Tana Raye bata huta da Jidalin Amina ba bayan ta rasu bazata barta ta Huta Cikin Salama ba..! Da sauri Baba Mallan yace"Husai kibar wannan mganar..Hadiza zata Huta cikin kabarinta da yardan Allah Shaidar duniya itace ta Kiyama..! Dole ta koma tayi shuru domin ita bata da wannan Sakewan da yara shiyasa Tuni taso Sa"idu ya bata Amina tatafi da ita da Tuni duk wannan Tabaran ta daina shi Ita gani take harda da Laifin Sa"idun da su Mallam din..! Nan Baba Mallam ya cigaba da Lallashin Amina har sai da ta bar kuka sannan ya kalleta yace"nima zan baki Hakuri Mamana..Nayi miki laifi nayi sonkai..Na rabaki da wanda kike so na aura miki Da"a na..! Sai kunya ta kama Amina ta kalli Baba Mallam da manyan Idanuwanta kafin tayi mgana Ya saka baki ya Kira Umar Dake gefen Aba kansa na kasa kamar baya Falon Gaban Baba Mallam yazo ya Durkusa Cikin Sanyin sa yace"Gani Mallam! Ba zato kawai yaji ya Damki hannunsa ya Hada cikin na Amina cikin Dattakonsa yace"Ga Amanar Hannun Mamana nan Umaru..Ko bayan raina ban yarda ka saki ba..Ko Laifin me ta maka ka Duba girmana ka mata afuwa ka yi juriya kan Hallayarta ka zama mai mata Nasiha yayinda ta bata maka Sannan Daga karshe ina fatan zaka riketa Bisa gaskiya da Amana sannan ka kwantatanta adalci Tsakanin matanka..,! Gabadaya sai jikinsa ya Mutu hannuwan nasu yabi da kallo kamar yadda Amina itama take bin Karamin hannunta Sarke cikim Tattaausan hannun yaya Danmallam mai cike da gargasa da kallo..! Bakinsa yayi nauyi da wannan Abunda Mallam yayi shiyasa ya jinjina kai kafin yace"Insha Allahu Mallam..Allah ya kara girma..! Ya amsa da Ameen har Lokacin hannayensu na Sarke da juna Hajiya Babba ta kallesu farimciki ya cikata Cikin wani yanayi tace"Yadda kuke rike hannun juna..Allah yasa ko a Lahira tare zaku tashi rike da hannun juna..Allah ya Hada zuciyoyinku Waje daya..! Gabadaya aka amsa da Ameen Aba na gefe yama kasa mgana Alherin Baba Mallan garesa ai mai girma ce..! Goggo hussai tace"Sai faman bashi Amana kuke yi kun manta Amina..?Kai Umaru kalleni nan..Kada ka damu da mganar Mallam ko ta Hajiya..Amina sai da wuta..In tayi maka ba Daidai ba kaci Zarafinta kada kayi mata da Sauki Domin kai zaka sha Wahalanta Ahtto..! Tafada bilhakki da gaskiyanta Dayasa Hajiya ta Murmusa tana fadin"Ke fa Goggo ce Husai..! Tace"Ai na sani shiyasa nake Fadamai gaskiya..jidalin Amina ai Allah kadai yasan shi Har Hadiza ta bar Duniya bacin ranta Daya kan Amina..Allah yasa ta samu ma uwar goyo ta gari ai da ba Domin Balaraba ba da Amina kuma sai Allah..! Amina na jinta ita yanzu komai ma ya zama mai Sanyi awajenta in da abayane ta Tabbata Sai ta Tura mata baki tayi gunaguni kamar baya ammh yanzu sai taji ta kasa bata cikin Hayyacinta har yanzu Aminene bata Dawo ba Amina ce da kanta yanzu..! Ta manta da Hannunsu dake Waje Daya sai da taji ya Sabule hannunta Sannan ta Dago suka hada ido Saurin Dauke kansa yayi saboda wani irin abu yaji acikin ransa kamar na Tsausayi itama kanta ta Dukar tana wasa da Hannunta gabadaya kalaman Baba Mallam sun gama riketa ita kuwa me ta aikata ne..? !Da Alherin Baba Mallam da Hajiya ya Lullbe Rayuwarta haka..? Har Abada bazata manta dasu ba kamar yadda bazata manta da kaddaran data Hadata da Masoyinta Aminu ba..! Baba Mallam yayi gyaran Murya yana Fadin"Umaru me ka yanke kan Mamana..?Ina Nufin kana da wani Tsari ne..? Kansa na kasa har Lokacin yace"Tsari na na Ubangiji ne Mallam..ba ni da wani Tsari..! Sai dai bazan ki duk abunda ka Zartar ba..! Baba mallan yaji Dadi Cikin Fara"a yace"Naji Dadin haka shiyasa na Tambayeka..Zan yi ma Mamana adalcin da nake yi ma kowa..Bazata Tare ba sai ta gama makaranta Umar..Nan da shekara Daya da wani abu kenan tunda Hajiya tace suna aji Daya na Babbar makaranta sun kusa shiga Aji Biyu..! Zata kamallah makaranta da Walimar sauka zan hadata da sauran yan"uwanta Hamida da Hannatu da Sa"aadatu na aurar dasu ita kuma sai ayi Bikin Tarewarta alokacin bazan karbi Uzurinka ba na baka Lokaci ka Tsara komai inda zaka ijiyeta da yadda zaka zauna da iyalanka..! Goggo Husai tace"Mallam me zai hana tunda anriga an Daura ayi Tarewan ba Nisa? Kai ya Girgiza kafin yace"A lokacin Auransu nayi gaggawa Husai..ban kuma bama yaran nan dama ba Husai..Bana so na kara maimaita irin haka Shiyasa na Dibi wannan Lokacin bana Fatan wani Daga cikin su yaji aransa ban mai adalci ba..! Ba wanda bai gamsu da mganarsa ba Ya Danmallam kamar ya goya Mallam haka yaji dama Fargabansa ace ya tafi da ita ko kuma mganar Tarewa Amina kuwa acikin ranta itama Hamdala Take yi Domin bata shirya ba..Bata Shirya karban wannan Kaddaran ba Har yanzu..! Goggo Husai tace"Shikenan..Ni na Dauka zaka hadata dasu Zeenatu ne.? Kai ya girgiza kafin yace"A"a ai ba Sa"aninta bane..So mganar su ma tana nan Rasuwar nan ne ta hanani nayi mgana yaushe ne zasu fara Jarabawar Fita ma kikace Hajiya..? Hajiya tace"Sati na sama Abida tacemin Mallam.! Cikin Dattakonsa yace"Zan bama Mazajensu dama zasu fara zuwa su gana dasu..Mai son Zeenatu dan wajen Aminina Mallam Hamza ne Dake Gombe,Babbar D'ansa Ahmad Soja ne..Sai mai son Abida na gida ne Jikan kawuna Lawali na Bazanga Dake Jamus..? To yaron wajensa ne Yana Porthercourt yana aikin Zanen gidaje ko wannan Gaisuwan da suka zo shi kawu Lawalin ya karamin mgana..! Goggo Husai ta fara fadin"Masha Allah..Allah yasa a kulle alheri..! Aba ma yayi fatan Alheri shi da Hajiya Baba mallan ya kalli Danmallam yana Fadin"Baka ce komai ba Umaru..? Cikin Ladabinsa yace"Hakan yayi mallam..Allah ya saka da Alheri ya kuma kara girma..! Cikin Fara"a yace"Ameen Allah yayi muku albarka..Tashi kaje ka Dauki iyalanka kuje gidanku ku huta..Ina fatan zaka kwana Biyu kafin ka koma..? Cikin Kankantar dakai yace"Jibi zamu koma Mallam..Saboda aikina na iya adadin kwanakin da aka bani kenan..! Baba Mallan ya Jinjina kai yana Fadin"Shikenan Allah ya kaimu..Mamana tashi ki bisa ka rakata har kofar gida ko wajen Hajiya zaki kwana..? Kai ta girgiza kafin tace"Eh..! Da sauri domin bata son ahadata dashi jin haka yasa Danmallan yayi musu sallama ya Fice daman shima Takuramai Mallam zai yi ko Cikin gida bai koma ba ya Kira Sakina awaya yace ta fito su tafi..! Amina kuma sai da tattabatar da sun tafi Domin taga Budewar get da Fitan Mota ta kuma tabbatar da Shine sannan tayi musu sallama ta wuce shashen Hajiya..! Koda taje har ya Abida tayi barci sai ya Aisha ce da ya Zulaihat ke zaune ashen nan sukayo Dadi taji Dataga su hanne da Hamida Zafira sun koma gida Tun jiya..! Bata ma kowa mgana ba Kujearan falo mai zaman mutum uku ta Dungule akai tana Sauke ajiyar rai su kuma sai suka sauya hira daman Hirar Aminar Suke da Al"ajabin Auranta da Yaya Danmallam,Sai dai kuma ko su Hanne da sukasan Dalili basu ce komai ba Domin Sirrin Amina Wajensu bazai Taba Faduwa ba koda ba awaje bane na gida ne..! Sai awannan ranar Amina ta samu barci Domin batasan Dawowar Hajiya ba Washegari kuma su ya Jawahir suka fara tafiya,sun yi kuka Lokacin sallama kafin yammh gida ya Rage sai ya Jadwa da Goggo Husai da Goggo Jumai duka sun koma Gidajensu har su ya Zahra..! Chan gidan Baba Mallam ma Duka sun koma gidan auransu gida yayi tsit dayan washegarin kuma Ya Danmallan suka koma shi da Sakina Basu hadu da Amina ba itama Goggo Husai taji Tana mganar Tafiyar tasa..! Tun Ranar ashashen Hajiya suke kwana har Hamida sai da su goggo Husai suka samu Visa suka tafi gida ya zamana ba kowa yasa Hajiya tace su Amina su koma basoda Mamanmu kada kadaici ya Dameta..! Kwana Goma sha daya da Rasuwar yaya suka koma gida ya rage daga Amina sai hanida sai zeenatu da Jawaad sai mamanmu da Aba. ! Sati biyu da rasuwar suka koma makaranta Boko da Islamiya,Saboda zasu fara jarabawa su ya Zeenatu har sun fara Neco..,! Komai ya tafi kan tsari sai dai Abu Daya ne yayi ma mamanmu cikas Wannan Raunin data so gani awajen Sa"idu bata gansa ba sai ma wani Takwalli Daya shigesa..! Ko sau daya bai zubar da Hawaye agabanta ba..! Balle taga Rauninsa ko kananan kukan gulma take sai dai ya kalleta yace"Muma fa jiranta muke yi Balaraba..Hadiza batayi gaggawa ba..! Fatanmu Allah ya rahamsheta..! Bata gani ba har yau bata gani ba..Sannan Gurbin yaya har Abada Sa"idu bazai taba bata ba..bayan Mutuwar taso komai ya zama karkashinta abunda bata sani ba Allah ya riga ya Rubuta kaddaran kowa ciki harda nata in ta Kauda yaya to ba Lalle ta samu cikar Burinta ba zata samu wani wanin kuwa har ta koma ga Allah bazata taba samun sa ba..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️25* *BAYAN WATA DAYA..!* Acikin Wata dayan daya gabata na rasuwar yaya komai ya fara dawowa daidai,Wadanda akayi ma rashi sun Dauki Dangana da Tawakkali,Mussaman Aba da su Amina da yanzu ta fara dawowa da Walwalarta sai kuma yanzu take matukar kulawa da Jawaad tana Taausayinsa gani take daga shi sai ita sukayi rashin yaya basu da wata matsala Domin mamanmu tana Tsaye kansu da Fuskar da suka santa da ita,ya taimaka wajen dawowa da walwalar yaran har wadanda ke gidan auran nasu,Uwa uba ga Hajiya babba da bata bari sun yi kukan maraici ba Duk da ga Mamanmu tare dasu tana zaryan zuwa Dubasa barin ma in Taga Amina ta kwana Biyu bata leko ba Acikin kamshin Nasaran da Mamanmu take gani ta Samu bayan kasa ta Shafe Idon yaya abu Daya ne zuwa Biyu na Farko ta samu yardan yan"uwa da Duka Dangin Baba Sa"idu sannan Aminci Data gina shekaru masu yawa da yaran bai gurbace ba yayi mata amfani sosai gabadaya su ya jafar da komai nasu yana Tafin Hannunta ne tun yaya nada rai yaran da ita Suke shawara sai dai yayan taji Daga bakinta to har yanzu bata Sauya Zani ba ballatana yanzu da ba Uwarsu sai Duka yardan da Amanan ya koma kanta Harta kuwa Jafar da Abaya yake da Kulafunci nuna yaya ce uwarsa ba Ita ba shima yanzu wani girma yake bata kamar me yana ganin ta tamkar makwafin yaya..! Gida ya zama nata ita kadai Yaran suna Tafin Hannunta sai dai Abu Daya ya Gagareta Samun SA"IDU yadda take so,Sannan kuma wannan Raunin da taso gani atare da Sa"idun bata gansa ba,Sai ma wani Jarumta da Takwalli bata so ta gansa Tsaye kan kafafunsa ba taso ace yana kwance ne yana Fama da wannan Babban rashin sai Taga akasin haka sai dai bata Sare ba ai ta Rabasu Wannan kallon kauna da Tausayin Sai dai in ya Bita chan Lahira ya nuna mata anan Duniya dai ta gama Shiga Tsakaninsu..! Bayan Bakwai da rasuwar yaya ta kasa gane kansa ya daina cin abinci baya Fara"a baya Hira da ita ballatana mgana mai Dadi haka zasu kwana su tashi in ba ita tayimai mgana ba shi bazai ce mata ba  tasan wani Lokacin bai da Hayaniya ammh tasan Rashin mganarsa yafi Faruwa akanta In yaya ce keda Turaka kusan Raba Dare suke suna Hira cikin Nishadi bata san Darare nawa ta bata cikin bakincikinsu ba Domin tana Daga Dakinta in Dare yayi tana jin tashin muryoyinsu In kuma ranar itace keda shi Daya gama cin abinci yayi wanka Sai ya fara Hamman barci tana mai Hira sai ya fara barci ma"ana baya son Hirarta ta Dade tana kunsan bakincikin Sa"idu shiyasa bayan Rasuwar yaya ganin zai bata wahala yasa ta sa madina ta kai ma malaminsu korafi aka Samo mata kansa shine har ta Fara Tunanin Burinta ya fara cika Sa"idu da komai nasa yana Hannunta.. Tunda yanzu In ya dawo aiki yaci abinci yayi wanka ya kan zauna su yi hira koda bazai amsata yadda take so ba ammh cikin kaso goma tana da Nasaran kaso Takwas aciki Abunda ya Rage mata shine ta fara sanin komai nasa kamar yadda yaya ta sani sai dai har zuwa yanzu yaki bata Damar haka! Yau ma kamar kullum safiya ranar asabar ce ta hutun karshen mako,Ba kowa agidan duk sun tafi Hadda,Sai ita kadai da Aba bai fita yau da wuri ba,Kamar yadda ta tsiro dashi yanzu Gari na wayewa kafin Aba ya fita sai ta Chaba kwalliya Kamar wata yarinya bayan makircin karkashin kasa har da na Kissa Madina tace ta Dinga Hadawa duk a Kokarinta na sai taja Hankalin Sa"idu akanta gabadaya..! Abunda bata sani ba ita zuciya ba"ayi mata Dole kan abunda tagani kuma tasan dashi ammh ta nuna bata so..Sannan duk da tana son mai kyautata mata bata cika bashi matsayin daya Zarta wanda ta zabe ta da kanta ba koda bai taba mata wani abu na Alheri ba..! Zaune suke afalonsa yana karyawa ita kuma tana gabansa kamar mai kirga yawan Numfashinsa Hira take yi mai yana jinta yawancin Labaranta ba wasu masu amfani bane,Shiyasa yake mata Shuru kawai batare daya tanka ta ba,Har kuma gobe bazai daina kukan Rashin Hadiza bai jin zAi iya mantawa da ita. Jin tayi shuru yasa ya Dago Daga cin Soyayyan Dankalin data soyamai ya ganta tayi Tagumi tana kallonsa Cikin dan mamakinta yace"Lafiya..?Me kike Tunani..? Alokacin bakincikin Tambayarsa taji Saboda tafi kama data rainin wayau ta Zauna tanayimai Hira yayi mata banza sannan ya Dago yana ce mata Lafiya..?Saurin Daidaita kanta tayi ammj bacin rai yasa Kiris ya Rage Dayan Fuskar tata ta bayyana. Cikin sosa ido da hanci ta fara fadin"Yaya na tuna..Bana iya kwana na Wuni ban yi kukan rashinta ba..Ballatana in na gifta Dakinta sai naji gabadaya Duniyar ta Juyamin baya..! Tana Fade tana matso hawaye kamar gaske ya Dade yana kallonta kafin ya maida kansa ya cigaba da cin Dankalinsa yana jinta tana Fadin"Wlh nima sai naji Duniyar duk ta isheni Abbansu..Dama nima na mutu kamar yadda yau ba yaya adaron Duniya..! Sai da ya Kurbi Tea din Dake hannusa sannan ya Dago yana kallonta Cikin Sanyinsa na koda yaushe yace"Zo nan Balaraba..! Baki ta bude tana kallonsa Ganin haka yasa ya gyada mata kai alaman tazo ba musu ta mike ta isa kusa dashi ta zauna Juyowa yayi suna kallon juna Hannayenta ya kama Duka ya Rike yana Tuna Nasihan Baba Mallam aranar da Hadiza tayi arba"in da Rasuwa ya Horar dashi Kada rashin Hadiza yasa ya cutar da Balaraba ya sani Ko sau Daya ya Danne mata Hakki Allah zai tambayesa..! Cikin Idanuwanta ya kallah kafin ya fara fadin"ki daina Fadin haka Balaraba..Mutuwa ta Allah ce..Hadiza batayi gaggawa ba sannan muma da muke Duniyar jiranta muke..Ko yau ko Gobe zamu mutu..Saboda haka ki Sani Hadiza tatafi ba domin tana son Tafiya ba..Addu"rmu take Bukata ba kuka ba..Don Allah in kin Tunata,ki Dinga mata addu"a don Allah..! Kai ta gyada tana kara Jan hanci Lokaci Daya tana fadin"Wlh Abbansu na kasa ne..Kullum in na tunata sai nayi kuka..Barin ma in na Juya naga gidanan yanzu Dagani sai kai yau babu Yaya..Sai naji kamar nayi ta kuka har Abada..! Sharr sai hawaye suka Zubo mata Taausayinta ya kamasa yasan ita mai Hidima ce agaresa shi da ya"yansa har Abada wannan kyautatawar nata yana cikin ransa kuma yana gode mata. Hannu ya Sanya ya share mata Hawaye cikin Tattausan murya ya cigaba da fadin"Haka Allah ya Tsaara..Daman chan ita din bamai Tsawon rai bane..In kina wannan kukan zaki tadamin da hankali naga kamar na gaza ne balaraba..Sannan in kuka ya Haifar miki da Damuwa ina zan saka raina ni da ya"yana da kike zama mana tamkar wata inuwar gingiya mu Rabe ki mu ji Dadi..! Wlh tallahi nayi rashin Hadiza sai dai nasani da yau baki cikin Rayuwarmu da Raunin mu ya fi bayyana..Allah ya Dauketa ne saboda yasan ina Dake..Na tabbata ko ni yau Allah ya Dau raina ke zaki zama madadina da madadin Hadiza..Girmanki a idona mai girma ne Balaraba..Yau zan gode miki bisa Hidimarki gareni da ya"yan Hadiza da  baki bari sun yi maraici ba..! Tunda ya fara mgana take kallonsa Zuciyarta ta cika da Farincikin da shekaru aruru basu sa tayi shi ba sai yau..Daman haka take so ta zama Komai na Sa"idu da ya"yansa wanda basu da wata Dama sai ita ta Kasance itace jinsu da ganinsu kuma tayi nasara bayan Shekaru ashirin da wani abu akallah yau ta fara Hango kamshin nasara cikin Wahalar data Dade tanayi..! Ammh sai bata nuna ba sai ta Sadda kanta tana fadin"Basai kamin godiya ba..Aikina ne nayi maka Biyayya da Hidima mganar yara kuma ka bari bana so..Tun yaya nada rai yaran suke ya"yana Har ga Allah ina masu kaunar da banayi ma ya"yan cikina..! Cikin Farinciki yace"Nayi kuskure..bazan kara Fadin haka ba Allah ya jikan Hadiza ke kuma Allah yayi miki albarka..! Ta amsa cikin Farinciki acikin ranta da Ameen Ameen..! Tare suka karisa karyawan cikin Farimciki ranakun da Balaraba bazata manta dasu ba acikin Rayuwarta..! Ita ta kwashe kayan da suka bata zuwa Kitchen sannan ta Dawo Dakin nasa. Sai ganinsa tayi Tsaye yana saka agogon Hannunsa na fata cikin Mamaki tace"Fita zakayi..? Bai kalleta ba yace"Ina so na fita saboda akwai wadanda zasu zo Diban kwai yau..Sannan masu aikin gonar mallam ta bazanga sun kirani Suna bukatar taki nasu yaja baya gaskiya shine nake so na fita na leka Mallam muyi mgana sai na Kira Jafaru naji ya zamu yi..! Farinciki ya cikata abaya fa sai dai Ya fadama yaya irin wannan batun ammh yau babu yaya Dole dai kanwar nakin itace komai cikin Alhini tace"Na Dauka yau zaka tayani zama..Tunda yaran duk suna makaranta..! Ta karishe Fada cikin Shagwaba kamar wata yarinya Mirmishi kawai yayi yana Fadin"Bazan dade ba zan dawo..Daukomin Hula in saka..! Ba musu ta shiga ciki Ranta Fes ta Zabomai hula kadan shaddan Jikinsa kalan Sararin samaniya ita da kanta ta sakamai ta feshesa da Turare ta Daukomai Bakin Takalminsa Budadde ta Gogemai ta bashi ya saka ta Dauko Wayarsa da key din Motarsa ta mikamai ya karba yaana yaba Kokarinta akansa cikin yabamanta yace"Allah yayi miki albarka..! Kanta na kasa ta amsa da Ameen Fita yayi tabi bayansa sai da suka zo Tsakar gidan sannan ya Tsaya Dakin yaya ya kalla na wani Lokaci kamar ita zai gani tana zaune kofar Dakinta Cikin baranda kamar yadda ta saba Sai dai ina mai Rabawa da Riga ta raba..! Mamanmu kuma Tuni Farincikinta ya Gudu ganin inda yake kallo cikin Kissa ta kalli wajen kafin ta Sauke Numfashi Tana fadin"Kaima sai kaji kamar zka ganta ko..!Nima haka nake ji Koda yaushe..Su kansu yaran sun kasa sakewa Wuni suke cikin Dakin musamman ma Amina gani take kamar yayan zata Dawo watarana..! Kai ya jinjina yana kokarin Daidaita kansa yace"Nayi tunanin ko na Dauko Goggo Jumai ce tazo ta zauna Dakin yayan..tunda chan gidan nasu fa ba kowa ko ya kika gani..? Mamanmu taji kamar ta saka kuka Yaya ta rasu ammh bazata Huta ba..! Cikin Danne abunda ke ranta ta kallesa kafin tace"Ka raina kulawar da nake basu ne..? Cikon Daburcewa yace"Me ya kawo wannan maganar kuma..? Sai ta fara kuka tana fadin"Eh mana ka raina ne..In ba haka ba meyasa zakaje ka Dauko goggo Jumai Salon mutane suju suce bana rike su Amina Tsakani ga Allah in ko ka jamin wannan Shedar bazan taba yafe maka ba Sa"idu..! Sai ya Rude ya Rikota yana Fadin"A"a fa ba Haka nake nufi ba..Kada kimin mumman Fassara..! Cikin Jan hanci tace"sai dai in ka janye mganar Dawo da goggo Jumai sannan zan yarda ba haka kake nufi ba..! Da sauri yace"Na janye..Daman Dake kadai nayi mgana ko Mallam ban yi mgana dashi ba..Itama goggon da wuya ta yarda tunda wajen jikanta Take zaune dake Hadeja..! Sai alokacin ta saki ranta da Fuskarta tana Fadin"Bana son abunda zai min Shamaki da yarana..Ina matukar kaunarsu kamar ni na Haifesu mussaman Diyata Amina..! Mirmishi yayi bai ce komai ba ya Fara Tafiya tabi bayansa ganin har sun fita Koridi yasa ya Juyo yana fadin"Na zama dan gata kenan..Rakiya za"ayin har waje kenan..? Sunkuyar dakai tayi tana Dariya sai kawai ya kalleta yana fatan kada ya Dannen hakkinta domin karfi hali kawai yake yi. Har bakin get ta rakasa Motarsa tana Gidan Baba mallan sukayi sallama har zai fita ya juyo yana fadin"Kin Duba Cefanan kayan abincin da Jafaru ya kawo jiya kuwa..? Tace"Na duba komai yayi..! Yace"Ba abunda za"a karo..! Kai tsaye tace"Sai dai goldenmorn saboda yaran nan..Sai Cornfkles naga Kwali Daya ne .! Kai ya gyada kafin yace"Shikenan zan fadama Jafar zai kawo anjuma..! Daga haka sukayi sallama ta Bishi da Allah ya Kiyaye hanya. Yana wucewa ta koma cikin gidan Tana takun Daidai kamar wata Sarauniya sai da tazo Tsakar gidan ta Juya ta kara juyawa kafin ta kyalkyace da Dariya tana Fadin"Burina ya cika..Abunda na Dade ina neman ya Kusa Tabbata..Sa"idu ya zama nawa Dashi da komai nasa..Ni Dayyaba duniya Sabuwa..! Sai kuma ta fara Dariyan kamar tayi hauka Karan wayarta Dataji shi ya Sa ta Ruga zuwa Dakinta sunan wanda ke kira yasa gabanta ya fadi ta Dauka da Sauri tana Fadin"Gabana ya fadi madina..Kada ki cemin min kuskure ma wannan karon..? Tsaki Anty Amarya taja Dagachan bangaran kafin tace"Kice zaki kuskuremin Dayyaba..! Da mamaki tace"Ni kuma..? Kai Tsaye tace"Eh mana..Tayaya zaki shanyani ina jiranki ban ji wata mgana Daga bakin ki ba..? Ko Saboda na taimaaka miki kin samu cikar Burinki ni kuma sai ki ki bani Damar da zan cika nawa..?Auto kin samu Sa"idu atafin hannunki Dayyaba zaki juyamin baya..To baki isa ba..In kikace zaki haka na Rantse har ga Allah zan sakaki a Tara ba uku bama.. Cikin Tashin Hankali da Sigan Lallashi Mamanmu ta fara fadin"Haba Madina taya zaki min wannan Fahimtar..?Sa"idun ai bai gama zuwa Hannuna ba ke kinsani kuma komai zan yi yanzu sai da Lura kada ki mamta Fuskarmu ta Balaraba da Marliya akasani ba"asan Fuskar Madina da Dayyaba..Ina sane da aikin mu kan Amina Dayyaba..ina sane so nake nabi komai Daki Daki yadda in komai ya Lalace baza"a taba zarginmu ba..! Sai alokacin ta sauke Numfashi tana Fadin"Kinsan abunda yasa Sakina bata Damu ba..Saboda nace mata zan Lalata wannan auran zai zama mara amfani Dayyaba..Kuma ke zaki mun wannan kokarin bana shiri da yarinyar..Ke kin jata ajikinki tana ganin girmanki Fiye data uwarta..Bana son na gaza..Sakina ce kadai Tauraruwa agidan Umar Dayyaba..kina saka Amina ta samu Baba Mallan tace mai bata son wannan auran zai rabashi,Sannan shi kanshi Sa"idun ki hillacesa ya Furta ma Mallam kinsa akan auran Daganan Mallam zai kullacesa Burina Zai cika ma ganin baraka Tsakanin Mallam da Sa"idu sannan Wannan yarinyar ta fita Daga Tsarina..! Mamanmu tace"Kada ki damu yau zan fara aikin mu..nayi miki alkwarin yau zan Turata gobe zaki ji Labari mai Dadi..! Cikin Farinciki tace"Dakyau..Nasan zaki iya..In hakan ta faru ki Sani Sa"idu zai kara zama naki ke kadai har gaban Abada..! Atare suka saki Dariyan Nishadi da Tunanin Duniya ta Bude musu sabuwa abunda basu sani ba Alkwarin Allah bazai taba tashi ba sannan Dan Hakin Daka raina watarana shi zai tsole maka ido..! ***** Sai shidda da wani abu na yammah suka dawo daga makaaranta Karfe hudu suka tashi Hadda suka shiga Islamiya,Amina da Hamida sai da suka Biya suka gaida Hajiya babba da ke Fama da kafa. Sun fito Daga Dakin Hajiya Babba suka iske har ya Abida ta baje afalo da passQ tana Faman dubawa Daga Dawowarta dayake sun yi nisa a jarabawarsu sun kusa gama Neco zasu fara Weac,su kuma su Amina sun gama Exam hutu suke yi sai in sun koma zasu shiga SS2..! Amina ta kalleta tana fadin"Ubanki Boko..Boko..Bokoko..! Abida ta Dago tana kallonta cikin Harara tace"Allah yasa dai ba ni kika Zaga ba Amina..? Da sauri Amina tace"A"afa..Ni Ubanki Boko nace..! Kai ta gyada kafin tayi kyaci tana Fadin"Da kin Daku na Rantse..! Amina ta Murguda mata baki tana Fadi kasa kasa"Sai dai ki Daki wannan mai Dogon wuyan..! Ta jita sai dai bataji karshen ba Hanne da Hamida ne sukaji suna kunshe Dariya Saboda tuna wanda zai auri ya Abidan da Mallam ya basu izini su zo su gana,Har na ya Zeenatu yazo shi dai bai da Muni sai bakin masifa kamar na Zunubi na ya Abida kuma Fari ne girman Lagos tunda hannun yayan babansa ya tashi Dake lagos Jikinsa na Hutu ne sai dai kamar mace har muryansa kamar ta mata yaa wani Lamgwabe kai sai Dogon Wuya rana Daya sukazo su Amina saboda Bala"i sai da suka Labe suka gansu haka suka dinga Dariya,sai kuma suna Tsokanar su kasa kasa suna Dariya..! Yau ma ya Abida cewa tayi"Amina maimaita abunda naji kince..? Amina tace"La cewa fa nayi ina Uncle Jalil..? Wata uwar harara ta banka mata kafin tayi Tsaki ta cigaba da abunda take yi yasa su ka kwashe da Dariya ta Dago tana kallonsu Suna ganin haka suka Danne bakinsu suna zare ido ganin haka yasa. Ta mike tana fadin"Yaran nan kun ranani Wlh yau sai naji Ubanku..! Ganin ta Nufosu yasa suka Rumtuma Hanne ta shiga Dakinsu su kuma su Hamida suka fice aguje ganin haka yasa ta Dawo tana fadin"Hanne sai dai in bazaki fito ba..Marasa,kunya ko naga wanda Baba mallam zai kawo muku..Gwara Amina ta ga nata ku  ba"a sani ba ko wasu kala ne don mai garinku..! Hajiya babba tana Daki tana jinsu Dariya takeyi ita kanta ranar da Jalil din yazo ya gaisheta sai da tayi Dariyan yadda yake karya wuya Gwarama Auwal din Zeenatu sai dai shi kato ne ga baki..! Aguje suka shiga gidan Mamanmu na Alwala bakin Famfo ta gansu sun fado har ta tsorata ta zabura tana fadin"Lafiya..? Hamida ce tace"Amina ce ta Tsokano ya Abida shine ta biyomu..! Tsaki taja kafin tace"Shine zaku shigo da gudu wlh har kun tsoratani..! Daga haka ta cigaba da alwalanta Hamida ce ta zube kan Tabarman da suke shimfidawa duk dare su zauna zaman hira kafin kowa ya nemi makwanci. Amina kuwa Dakin yaya ta shige taga ya zeenatu na zaune tana karatu itama ganin yadda Amina ta shigo yasa ta Dago tana fadin"bana son hayaniya ki koma Dakin mamanmu..! Amina ta kalleta da Hijabinta na Hadda bata cire ba cikin Danne Dariyanta tace"To..! Ta kama Hanyar fita tana fadin"Baki baki..baki fentin Allah bana Mutum ba..! Zeenatu ta bita da kallo Lokaci Daya ta bata rai gaskiya Amina ta fada Auwal akwai baki gashi kato Allah na Tuba ina zata kaishi..! Hamida fashin Sallah take yi Amina ce kadai ke sallah ita tayi alwala tayi sallar mangariba,itama bata Dade da yin wankan tsarkin ba. Suka fito waje suna Hira abinci suka Dibo ita da Hamida suna ci Shinkafa da wake da Miyar Jajjage suna ci suna Santi Mamanmu na cikin Daki tunda ta shiga sallah bata fito ba ita da ya Zeenatu..! Da aka kira isha"i ma awaje Amina tayi Sallarta bayan ta idar suka cigaba da Hira da Hamida Amina mantawa take tana da aure in ba wani ya Tuna mata Ba Hamida da Hanne ce tunda sukasamu Amina ta Dawo yadda take  basa Dauko mganar da zai Dagula mata Lissafi. Mamanmu ce ta Leko tana Fadin"Ina Jawaad..?naga ban gansa bane..! Hamida tace"Muna dawowa makaranta yaga Aba ya manne masa suna Falon Baba mallan yanzu..! Kai ta gyada kafin tace"Amina zo ina son ganinki..! Ba musu Amina ta mike ta Bita Ciki Hamida bata damu ba sanin Sirri Tsakanin mamanmu da Amina sun saba komawa tayi ta kwanta saman Tabarman. Mamanmu ce kan gaba har cikin Bedroom dinta ta zauna gefen gado tana fadin"Taho ki zauna nan mgana nake som muyi..! Ba musu Amina ta zauna tana fadin"Lafiya kuwa mamanmu..? Mirmishi tayi lokaci Daya tana Dafa kafadan Amina kafin tace"Bakomai mgana zamu yi ki natsu ki Saurareni.. Amina ta natsun tana jinta Mamanmu sai ta gayyato damuwa afuskarta kafin tace"Amina kinsan ina kaunarki ko..?Kaunar da ko Hamida bata same shi ba..? Amina tace"Bama ni ba Mamanmu kowa ya Shaida Amina ce kadai Diyarki..! Cikin Fara"a tace"Yauwa Diyata shiyasa na damu da rayuwarki sosai..Abunda ya faru na rasuwar yaya shiyasa ban Daga mganar ba..Ammh abun na raina Amina ko barcin Kirki banayi..! Amina ta kalleta da mamaki kafin tace"Menene yake hanaki barci mamanmu..? Cikin Sauke murya tace"Kan auranki Da Danmallam ne Amina..Sam baku Dace ba..Kina karama dake ta ina zaki iya auran wanda ya kusa haifanki uwa uba kuma kishi da mata Biyu..Ni ban ma jin balarabiyar Sakinar dai Daman chan ita da uwarta ba kaunar mu suke yi ba inaga kuma aure ya Hada..! Shuru Amina tayi jikinta yayi sanyi bata son tuna yau ita matar aure ce..Har yau bata karbi wannan kaddaran ba ta kuma kasa zama ta fuskanci da gaske ne abunda ya faru..! Yasa ta kasa mgana har sai da mamanmu ta cigaba da bata mgana da kuma nuna mata illah auran kuma ta yarda da ita matuka ta kuma san gaskiya ta fada barin ma inda tace"Amina a kuruciyarki naso ki sami Saurayi kamarki ki aura..Ba Umar ba..Ba sonki yake yi ba wahala kadai zaki sha ahannunsa da matarsa..Me zai hana ki fito fili ki Fadama Baba Mallam bakya son auran nan..?na tabbata zai saka Danmallam ya sakeki ki auri wanda kike so yama sunan Surukin nawa..? Amina ta Kalleta da Idanuwanta da suka fara ruwa cikin karyen Murya tace"Aminu..! Mamanmu tace"Yauwa Aminu..Ashema Amina ce da Aminu. kada ki damu da zarar ya sakeki  zan san yadda nayi kika auri wanda kike so nayi miki alkwari kin san dai ban taba miki alkwari na gaza cikashi ba ko..? Amina ta gyada kai tana Zubar kwallah kafin tace"Ina tsoro Mamanmu..In Aba yaji wlh zai Kasheeni..Kuma ni bazan iya kallon Baba mallam da Hajiya babba nace bana son jininsi ba kamar in nayi hakan ban kyauta ba..! Kamar ta kwadaa mata mari haka taji ammh sai ta cije tana Sassauta murya tace"Kada ki damu da wannan Zan san yadda zan yi..Aba dinku ni zan bashi mgana shima ai ya Fahimci an kwareki wlh..Nasan Hajiya da Mallam zasu fahimceki nasani..! Kidai kije kiyi mai mgana na Tabbata zaki ga abunda nake fadama miki..! Amina na sharan kwallah tace"To me zan ma Mallam din..? Mamanmu ta gyara zama tana Fadin"Yauwa ko kefa..?Kuka Zaki sakamai kina fadin baki son auran don Allah yasa Danmallan ya Sake ki shikenan..! Amina ta jiku da Hawaye kafin tace"Kina ganin ba matsala mamanmu..? Da sauri tace"Babu matsala nace miki zan tare komai nice fa Ko Duniya zata juya miki baya ni ina Tare Dake..?ko na taba juya miki baya..? Amina ta girgiza kai da Sauri tace"Yauwa to tashi kije..Ki bari sai Aba din ku ya shigo gida sai ki tafi Wajen Mallam din..! Da kai ta amsa mata ta kasa mata Musu,Ammh tana ganin kamar abunda tasata tayin bamai kyau bane Tayaya zata Bijirema Aba da kuma Baba Maallam anya in tayi haka batayi Butulci ba..? Sai dai kuma ta kasa yima mamanmu Musu har ta baro Dakin ta bar mamanmu na Hararanta cikin Takaichi kafin tace,"Shashasha..! Amina kuma Dakinsu ta koma ta kwanta kan gadonta tana kukan yadda Rayuwa ta juya mata baya aduk ranar Duniya sai ta tuna da Aminu tayi kuka,da kuma kewarsa tare da Tunanin Halin Dayake ciki..! Bata da mai gayamata kuma ita bazata nemi taji ba Tun bayan Mutuwar yaya tayi alkwarin daina Zame kowa Jidali so take ta wanke kanta wajen Aba kada ya kara ganin bakinta ammh kuma meyasa mamanmu zata ce sai tayi haka..? Tana kwancen taji Shigowar Aba,chan kuma sai ga Mamanmu tazo Dakin tana tashinta yi tayi kamar mai barci tatashi tana sosa ido. Mamanmu tace"Tashi kije Aba din ku ya shigo shi da jawad..! Dole ta mike tana Tsaye kanta har ta saka Hijabi tare suka fita ta iske hamida na barci ma saman Tabarma har kofar gida ta rakata ta bude mata gida tana Fadin"In kin dawo ki shigo Sai ki Rufe..Ko kuma kiyi kwanciyar ki Bangaran Hajiya kada Aba din ku yaji Dawowarki..! Hawaye ya cika idonta yasa ta kasa mgana,Haka ta wuce sum sum har Zuwa gidan Baba mallan megadi kansa yayi mamakin ganinta Tara na Dare har ya wuce,sai dai bai yi mgana ba. Gabadaya kamar an cire mata wani karkashi Jiki a sukuku ta karisa har Falon Baba mallam data ga haske acikin Alamun bai kwanta ba. Ta Dade tsaye ta kasa shiga tana saka tana warwara,Har sai da taji mganar Baba Mallam daga ciki yana Fadin"Waye anan..? Jikinta sai ya fara rawa cikin Inda inda ta Daga Labulen falon ta shigo Tana fadin"Nine Baba mallam..! Mamakin ganinta yayi da Daddaran  nan zaune yake kan kujera mai zaman mutum Biyu sanye da Shigarsa kamar bai ma Sauya kaya ba Harda Rawaninsa da Farin gilashinsa yana Duba wani littafin Larabci..! Cikin mamaki yace"UWATA..! Jin sunan daya kirata yasa taji Rauninta ya fara bayyana kaawai sai ta Fashe da kuka kukan data ke rikewa Baba Mallam ya ijiye littafin hannunsa yana fadin"Ashh..Kari so naji waye ya tabanin Uwata..! Dole ta karisa gabansa ta Zube tana kuka ya Dafa kanta yana fadin"daina kuka Fadamin damuwarki ni kuma nayi miki alkwarin Magance miki ita..! Sai taji Wani irin kaunar da bata jinta ba kan Baba Mallam ya taso mata  tayaya zata iya kallon wannan Dattajon mai Farin Alheri taki jininsa taki Alherin daya kulla da ita duk da Rashin Fahimtar dake Tattare da Rayuwarta gaskiya bazata iya ba..! Kawai sai ta sulale kan kafar Baba Mallam tana Cigaba da raira kukanta.. Cikin Damuwa ya saka Hannu yana Shafa kanta zuwa bayanta Allah ne ya Hada wannan Kaunar kwatankwancin kaunar da yake ma Sa"idu..! Cikin wata murya yace"Kiyi hakuri Mamana..Ki yi hakuri nasan ban kyauta miki ba..Na aura miki Umaru Jinina sai daga baya naji kamar nayi son kai..ban kyauta ba kamar na Zalunceki..! Da sauri Amina ta Dago Idanuwanta Jajir cikin kuka tace"Har Abada bazaka Taba Zaluna ba..Na karbi wannan gatan da kayi min na yaba..Allah yafini yabawa Baabaa..! Kawai sai yaji sukuni sukunin da bai Taba samu ba Tunda ya hada wannan auran cikin Tausasawa yake fadin"Allah yayi miki albarka..Nagode sosai .Allah ya jikan Hadiza da gafara..! Da amin take amsawa ta na godema Allah da baisa ta tafka wannan abun kunyar ba watsama Wanda Alherinsa ya Lullube rayuwarta data iyayanta gabadaya..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Sadaukawa ga Halima yusuf gwarzo Besty Alherin Allah ya kai miki a dukkan inda kike Ameen* *🅿️26* Ranar Hajiya Uwani keda Shashen Mallam shiyasa ta chaba ado tana tashin kamshi ta ko"ina,Ta shigo da Fara"arta sai dai kuma ya mamaye hakan da bakincikin ganin Amina gaban Mallam suna hira saboda Takaici ji tayi kamar ta koma da baya sai dai sun riga sun ganta bata da yarda zatayi sai ta Saki Fuskarta ta Kakaro Dariya da Mirmishi ta Dora Saman Fuskarta..! Baba Mallam ya dago kansa Daga kan Amina ya sauke kan Hajiya uwa data Tsaro kwalliyanta cikin Doguwar rigar shaddanta Nan da nan ya saki Fuska yana kallonta acikin matansa kaf ko Anty Amarya bzata gwadama Uwani Kwalliya da kamshi ba Duk da Ta kwana Biyu a duniya bata yarda ta zauna ba gyara ba ita din yar Kwalliya ce kowa ya sani.! Cikin Fara"arsa da Sautinsa yace"Lale da zuwa Hajiya uwa..Uwanin Alheri uwanin Yunusa daman yanzu nake Fadi araina ko an tsaya yanga ne yanmatancin ne ya tashi! Kanta sai ya kara girma ta kariso Cikin takun mata har ta kariso gefensa ta zauna sai Amina ta matsa gefe Tana gaisheta ta amsa Tana Fadin"Ka fahimci abunda ya Tsaidani ko Mallam..? Yana kallon Fuskarta yace"Na fahimta..Uwani uwayen kwalliya da ado..! Dariya tayi Tana kallon Amina da kanta ke kasa tana wasa da Gefen Hijabinta cikin Fara"a tace"Allah yasa ban katse Hirar surukanta ba. ! Sai da ya kalli Amina kafin yace"Ko da Sakina bana Surukanta Uwani..Ballatana Amina..Itadin Uwatace..Hira muke ta Tsakanin Uwa da abunda ta haifa kin kum san bamai iya raba wannan soyayyar..! Tana Mirmishi tace"Ba shakka kam.Ko na koma sai kun gama ne Mallam..? Kai ya girgiza kafin yace"A"a ai bazata kare ba..sai dai mu barsa zuwa gaba..Mamana tashi kije shashen Hajiya ki kwana zuwa safe Dare yayi su Akilu sun kwanta ballatana na Taso shi ya rakaki..! Amina batayi gaddama ba ta mike tana musu sallama ta fice zuwa shashen Hajiya babba tana jin sukuni aranta da bata Furta abunda Mamanmu da tsarata mata da batasan ina zata kai kunya ba..! Sai da Amina ta fice sannan Hajiya uwa ta gyara zama tana fadin"Mallan kayi mgana da shamsu kuwa..? Kai Tsaye yace"bai kirani ba meya faru..? Cikin kwantar dakai tace"Kudin hannunsa ne duk suka kare wajen Registration,yace min yana son aturamai wasu kudin..! Dayake shamsu ya samu gurbin karatu a Federal Universty Dutse ne har ya tafi..! Baba mallam kamar bazai yi mgana ba sai chan yace"Nayi mgana da Aliyu abokin Umaru yace min har Daki ya samu nan Kusa da makarantar bai ce Komai ba..Ammh zan kira shi Shamsu naji kinsan ba kasafai zaka rika sakarma yara kudi domin sun Tsallake gaban zuwa karatu ka rika saka ido kada watarana sakewarka ta saka su jawo maka wani abun mgana zan yi mgana dashi kuma zan saka shi Aliyun ya Bincikamin inda bukatar wani Abu zam ma Sa"idu mgana zai Turamai Insha Allahu..! Hajiya uwani gabadaya takaici ya Rufeta,kamar ta saki kuka haka take ji sai dai bata nuna ba sai ma kai data Rausayar tace"Shikenan hakan yana da kyau Mallam ka bincika din..! Daga haka ta tsuke bakinta tana wani Nazari har yaushe ne ya"yanta zasu zama na Farko wajen Mallam bayan ya"yan Hajiya Babba da Sa"idu Burinta na shekaru bazai cika da wuri ba kenan. Shi ya katse mata tunani da Fadin"Ya jikin Umaima ina Fatan ta daina Ihun nan cikin Dare..? Ya famo mata inda ke mata kaikayi Cikin Karin Damuwa tace"To yayi sauki za"a ce Mallam..Anya ba mganar malamin nan gaskiya bane..? Cikin Kallon sama sama yace"Dayace mene..? Sannan wajen wani malami kika kai min yata ban sani ba..? Sai alokacin tasan tayi barambarama ai baisan sunje har Niger kan matsalan Umaima ita da Batula ba..! Cikin Inda inda ta fara mgana da sauri ya katseta cikin Kaushinsa yace"Ina kika kaita kuma me malamin da kika bashi yarda Fiye da Ubangijinki yace..?in kikamin karya wlh zan ci Mutumcinki in nayi bincike na gano gaskiyan mgana..! Sai Jikinta ya fara rawa tasan Halin Mallam in bata Fadamai ba bazaman Lafiya ita kuwa dake cikin Kishiyoyi har uku mezai sa ta dinga Fada da Miji..! Da hanzari tace"Wlh ba da son raina naje ba labarinsa naji ance yana bada mganin Aljanu..k.. "Ki amsamin Tambayata..! Katseta yayi cikin bacin rai bakinta na rawa tace"Niger ne..Mukaje kuma..kuma yace ne wai Ture ne akayimin bai sameni ba ya Fadama Umaima..! Wani wawan Tsaki yaja kafin yace"Wa ya rakaki wajen..? Kai Tsaye tace"Kanwata Batula ce..! Yana kallonta cikin bacin rai yace"Ba tun yau ba na lura da Batula ta yarda da Bin malaman nan makaryata makiyan Allah kema shine ta jaki kikai min ya gaban wani mushuriki da sunan neman mgani akwai abunda zai baku wanda Allah bazai baku bane..?Meyasa wani Lokacin baku da Tunani ne Uwani..! Da sauri ta tareshi ganin yadda Ransa ya baci tace"Wlh ni da batula muka je..Ban je da Umaima ba..! Cikin bacin rai yace"Ko baki je da ita ba kin kai laluranta gabansa kin Tallatamai shi kuma ya cikaku da karyansa..Banda Hada fada da karya waye zai miki sihirin da har zai koma kanta..?To ban yarda da wannan ba Ni ya'ta Lalurarta daga Indalahi ne kuma garesa nake nema mata waraka in ta warke wannan ikonsa ne in bata warke bama wannan ikonsa ne..Kada na Sake ji koda wasa wata mgana irin wannan in haka ta sake faruwa komai ma zai yi faruwa zan dauki mataki mummana akanki kin ji na Fadamiki..! Ya karishe faada cikin bayyana bacin ransa da sauri ta Sulale kan Gwiwoyinta tana fadin"Kayi hakuri mallam..Insha Allahu haka bazata kara faruwa ba..! Bai kalleta ba yace"Bana son Rabuwar kai kan mata na da yara na..Nayi shekaru ina hada kan iyalaina Waje Daya..Nan duniya bayan ku da Iyalan Sa"idu bani da wani Ahali da zan kallah nace nawa ne sai ku..To ki sani in kina Biyema mganar malaman karyan nan zaki haifarmin da Gaba cikin Gidana kuma in hakan ta faru Uwani zaki sha mamakin hukuncin da zan yanke akanki Wlh..! Gabanta ya fadi taya ya komai zai kwace mata Burinta bai cika ba yasa ta kwantar dakai tana ta basa Hakuri sai da taga ya Hakura sannan ta Sauke Numfashi ta koma ta zauna tana kokuwa da bacin ran dake taso mata..! Ba domin ta kasa galaba akansa ba da Tuni Mama ta samo mata kan mallam ya zama sai yarda tayi dashi sai dai ina ta gaji da kashe kudi akansa ta Hakura Allah yana tare dashi kuma ya kare bawansa wani abu bai isa ya Cutar dashi ba sai dai ko in ya so..! Ganin yadan sauko har suna Hira yasa ta Sako mganar dake cin ranta"Mallam ya mganar Amina da Danmallam ne..!? Naji bakace komai ba haryanzu..? Kai tsaye yace mata"Har gobe sunanan a matsayin miji da mata..wani abu kike son sani kuma..?! Ya kalleta cikin son Tabbatar da abunda yake Tunanin take son ji game da lamarin. Da sauri ta sauya mganarta da cewa"Maallam mganar tarewa fa..?ai tunda angama mai wahalar itama sai yayi mata Visa da Shedar zama achan kamar yadda yayi ma Sakina ya Tafi da matarsa ni aganina zai fi mallam..! Ya dade bai yi mgana ba har ta Fidda rai kafin taji ya sauke numfashi Lokaci Daya yana fadin"Bazan yi haka ba..zan bama Mamana daman da bana ma kowacensu..Bazata tare a matsayin matar Umaru ba sai ta gama makaranta ma"ana in sunyi Candy in Hadata da yan"uwanta in aurar dasu..! Hajiya uwani da Farimciki ya cika sai ta kanne cikin wani yanayi tace"Nan da shekara nawa kenan Mallam..? Kai Tsaye yace"Hajiya tace alissafi Shekara Daya da wani abu in bai kai Biyu bama..! Ranta Fari tas kafin Lokacin nata Burin ya cika wato ma ta kwantar da Hankalinta Amina bata cikin Tsarinta yanzu tunda mijin ma baisan da ita ba kuma tarewar ma ba yanzu ba hakan ya Bala"in yi mata Dadi har sai da Fuskarta ta Nuna cikin dan yanayinta tace"Gaskiya kuma fa hakane..Ko Sa"idu kada yaga anyi mata Rashin Adalci..! Wani banzan kallo yayi mata Kafin yace"ko Sa"idu ina da iko da Kansa ballatana abunda ya Haifa..Ko cutar dashi zanyi bazai taba mgana ba..Ballatana ba wannan Tsakani na dashi.Kauna ce da Biyayya Tsakanin Uba da abunda ya Haifa..Kada ma na Sake jin wannan mganar Sa"idu namin Biyayyar da ko ya"yan dana Haifa basa min yana wahala dani da Dukiyata batare da na yankamai albashi ba gayamin cikin Tarin mazan da na Haifa akwai wanda ya zauna Dani yake wahala dani kamar Sa"idu..? Kai ta girgiza ta kasa mgana Miyan bakinta ya kafe cikin Dattakonsa yace"To ki saka aranki Sa"idu Shakikana ne..Kafin na same su shi na Sama kuma ina masa kwatakwacin kaunar da Uba zai yima abunda ya Haifa..Ki saka wannan aranki..! Daga haka bai jira cewarta ba ya mike  Dauke da Littafinsa ya Nufi Cikin Bedroom dinsa yana Fadin"Ni na shiga ciki sai kin shigo..! Da kallon Takaici ta bisa kamar tatashi ta Makesa haka take ji Sa"idu rai Daya ya hana Burinta cika agabanta Mallam ke fadin yafi yemai ya"yan daya haifa Dariya tayi acikin Ranta Saboda itace silar rashin zaman Umar da Nazir agaban Ubansu ballatana su taimakamai bata so su sha gaban ya"yanta Yanzu kuwa Burinta yana gabda cika Nazeem ya kusa gama makaranta sannan Tsumi da Tanadi ya karanta wato Economics sannan yayi Degrre dinsa na Biyu kan abunda ya shafi Kasuwanci yana Dawowa zata san yadda zatayi Sa"idu ya matsa ya bama mai waje wajensa ya kasance shine kan duka Dukiyar Mallam din Kafin Uzairu shima ya gama yazo su hada hannu hango kanta Take shekara Biyar masu zuwa ita Amtsayin Hajiya babba..Ya"yanta ne masu gidan ita ce mai Bada Umarni da mgana da yawun mallam wannan Tunanin yasa ta farinciki ta tashi Cikin Takunta ta nufi Bedroom din mallan tana cigaba da Tsara wasu abubuwan acikin ranta..! Amina kuwa sai washegari Hajiya ta ganta saboda sanda ta shigo gabadayansu sun yi barci Ya Abida ce kadai idonta Biyu tana karatu hanne ma ta Dade da yin barci. Da safe ko gida bata koma ba kayan Hanne ta saka da hijabinta na Hadda Tunda guda Biyu hannen gareta. Suka tafi Hadda Hamida bata je ba bata da Lafiya ciwon mara Ya zeenatu ke fadama da Amina taga bata ga Hamidan ba..! Sai da yammah da suka Dawo Amina ta Dawo gida ita Da hanne suka Duba Hamida taji sauki ma,Hanne bata jima ba tayi musu sallama ta wuce gida Mamanmu daman jiran Amina take yi taji ya ake ciki tun Safe Aanty Amarya ta Kirata taji Labari mai Dadi ba wani bayani shiyasa Hanne na Tafiya taja Amina kuryan Dakinta Tana Fadin"Ya kuka yi da Mallam din..? Amina ta Sadda kanta kasa kafin tace"Mammanmu na kasa..Bazan iya kallon Baba mallam nace bana son jininsa ba..Bai kamata na rama Tarin Alherinsa da sharri ba..Sannan in Aba yaji Wlh sai ya kusa kasheni agidanan..! Ta karishe kamar tayi kuka ba Domin mamanmu ta kai zuciyarta nesa ba da sai ta kaima Amina Duka yadda Wani Takaicinta ya kamata ammh duk da Haka sai da ta Tureta tana Fadin"To Shikenan tunda kin kasa..sai kije..Sakina ta gasaki don Ubanki..bakuma zaki taba Daraja ba Tunda baya Sonki..Kuma matar Cushe bata Daraja .! Yadda ta Zageta ta kuma Tureta yasa tasan ranta ya baci da Sauri ta riko Hannayenta tana fadin"Ba haka bane mamanmu..Wlh na kasa ne bazan yi kallon Baba mallam nace mai bana son auran nan ba..! Mamanmu da kanta har ya fara ciwo Saboda takaici tace"Shikenan na fita Acikin mganar nan..Ba ruwana daman yancinki zan kwatan miki..! Amina taji kanar tayi kuka kafin tace"To ke kije mana ki fadamai mamanmu..! Hararanta tayi kafin tace"Saboda ni ce nake son rabuwa da shi ko..?ba inda zani ke kika sani ni sakamar min hannu Ke ji chan ki karata Wlh Amarya da Sakina bazasu barki ki zauna Lafiya ba.! Amina tace"Tab..Sai dai ni ce bazan bar su zauna Lafiya ba Mamanmu..! Ta razana gabanta na Fadi tace"Bangane ba..? Amina tayi dariya kafin tace"To ai ba Tsoronsu nake ji ba..mamanmu ai Amina nake kirarina badai ta Mutum ba sai ta Allah su din banza! Basu isa suyimin Abunda Allah bai min ba..! Ta dade tana kallon Amina sai taga kamar Shagube tayi mata shiyasa cikin son tabbatarwa tace"ko kin fara son Danmllan din ne..? Ta fada cikin Hararanta Amina ta Zaro Ido kafin tace"Ni..?Allah ya kyauta..ni Aminu kadai nake so..! Ta Karishe Fada cikin wani yanayi Mamanmu ta sauke Numfashi kafin tace"Na Dauka kin fara son shi ne nace Ke kika sani..Domin Danmallam dai ya fara Tsufa auran wuri ne bai yi da kuma Haihuwar da bai samu ba..Kadan ne Aba din ku fa ya Girmesa.. Amina ta zaro idanuwanta suna shekk tace"Kai Mamanmu ko Aba fa bai Tsufa ba ballatana ya Danmllam..! Mamanmu tace"Eyee..Kina son shi kenan Tunda ke baki ga tsufansa ba..? Tafada tana Dungure mata kai Amina ta Dafe wajen tana fadin"Allah ya Tsari Amina..wannan ne zan so..Ya taba fa cemin banda natsuwa kuma ni wai kazama ce..! Ta fada kamar alokacin yake fada mata Takaicin abun na Dawo mata Mamanmu ta kwace hannunta tana Fadin"ni sakeni..Kekika sani..Ba ina neman hanyar kwatan miki yanci ba kina bani kunya ba..Na barki dashi..Kin dai ji kazama yake ce miki Allah kadai yasan kuma wata kalma zai kara Jifanki dashi in ya ganki agidansa an riga an Tusamai ke..! Amina ta Tura baki kafin tace"Sai na rama wlh..! Mamanmu ta kalleta cikin Tunanin mafita ko mgana batayi ba ta Tura Kofar Tiolet din Dakinta tana Fadin"An kira sallah..! Amina fita tayi ranta yadan yi sanyi ganin kamar mamanmu ta Dauki Zafi da Farko ammh Taji Dadi taga Daga baya ta saki ranta ajiyar rai ta sauke Tana jin kaso mafi yawa daga cikin Damuwarta suna yayewa Samun uwa irin Mamannu is a Bleessing..! Mamanmu kuwa har Aba ya Dawo ta kasa samun wata mafita tana ganin ta bangaran Amina ba nasara Dole zata Jaraba ta bangaran Sa"idu ta Latsa ta gani ko zata ga Jini..! Shiyasa koda ya dawo tayi wanka ta Shirya cikin riga da zani na Atamfa Hamida ta saka ta gyara Shashen nasa Dazu dataji Saukin jikinta Kayan abincinsa kuma tun kafin ya Dawo akai kai komai ciki. Sanda ta fito duk suna Tsakar gida kan Tabarma suna Hira an kunna Gen akwai haske shiyasa basu shiga sun kwanta ba..! Ganin bata ga Jawad ba yasa ta kalli Zeenatu Dake fama da karatu tace"Ina Jawaad..? Hamida ce tace"Aba na shigowa ya makale masa..! Mamanmu kamar ta saki Tsaki yaron nan zai zame mata ciwon ido sai ta rabashi da Uban taga ya zai yi shege kawai..! Mirmishi ta saki kafin tace"Ni ina Dakin Abban ku. Ku kwanta da wuri ke Zeenatu saboda makaranta Gobe..! Da toh suka amsa mata har ta wuce suka cigaba da Hiransu Amina da Hamida suke ta uban gaddama sai da Zeenatu ta Daka musu Tsawa tace sun dameta.! Koda ta shiga Shashen Aba ta iskesa zaune shi da Jawaad suna cin Tuwom Shimkafa Miyar shuwakan data Girka Dazu da yammah Saboda Aba din Ranta ya kara baci ganinsa Dare Dare kan cinyar sa yana bashi Tuwon abaki Dakyar ta iya shigowa cikin Dakin tana kokuwa da yanayinta..! Kan kujera ta zauna Tana fadin"Sannu da zuwa..Ka shigo ina wanka..! Da yauwa ya amsa mata yana fadin"Haka yaran suka ce..! Kafin ya cigaba da cin Tuwonsa yana Tambayan ko Jawad ya koshi ya Dagamai kai alamun eh Mamanmu tace"Daman Gulma ce irinta Jawad..Bai dade da gama cin nasa ba .! Aba yace"Kinsan yaro..Ballatana ko abaya Jawad dani yake cin abinci ko da riga yaci nasa ne..! Takaici bai barta tayi mgana ba Tana kallonsa har ya gama cin abimcin tatashi ta Dauki Faranti ta Fito dashi Ta mikama Amina tana fadin"Saka shi a Kitchen Amina..! Da Sauri ta zo ta karba ita kuma ta koma ciki ta ga Jawaad ya gyara zama kan cinyarsa yasa ranta ya kara baci ta kalli Jawad tana Fadin"Jawad tashi kaje dakina ka kwanta..! Tunda tun bayan rasuwar yay wani Lokacin in ya saka Rigima wajen Aba yake kwana ita kuma bazata iya Daukan wannan ba ta gama da Uwarsa kuma shi yazo ya rika sakata Damuwa ba..! Aikuwa make Kafada yayi alamun bazai je ba Aba ya kalleta yana Fadin"Kyalesa in yayi barci sai ki kaisa..! Takaici bai kara sa tayi mgana ba ta koma kan Daya daga cikin kujerun falon ta lafe ta maida hankalinta kan Tibin Dake falon cikin tashan Larabawa tana ji Aba ya maida hankalinsa kan jawaad yana Biyamai karatun da sukayi yau a makaranta Tun tana jinsu tana Gumduma ma Jawaad zaki aranta har ta fara barci Sama sama taji Aba na Kiran sunanta ta Bude ido tana kallonsa cikin Mamaki yace"wai har kin yi barci..? Har jawad yayi barci na mika shi wajen Zeenatu nace yayi Fitsari kafin ya kwanta..! Mikewa zaune tayi Dakyau tana sosa idonta kafin tace"bansan sanda barcin ya kwasheni bane..! Kai ya gyada kafin ya wuce ciki yana Fadin"Bari nayi wanka..! Da toh ta Bisa kafin tatashi tabi bayansa Yana shiga wankan ta Fitomai da jallabiya da gajeran wando ta koma ta zauna tana jiran fitowarsa Daya fito ya ganta sai da yayi mamaki cikin mamakin yace"Baki kwanta ba..? Kai Tsaye tace"Eh ina son mgana Dakai ne..! Bai damu ba yace"Bari nayi shafa"i da wuturi ke kin yi ko.? Da sauri tace"Eh saboda bata so yace sai tayi alhalin ba Damunta yayi ba Khamsul salatin ma dole take yinsu. Sai da ya saka Jallabiyan ya Shimfida Darduma ya tada salla har ya idar tana zaune ganin haka yasa bai Tsawaita addu"a ba ya juyo yana kallonta kafin yace"Ina Sauraranki..! Gyara zama tayi tana Tattaro Jarumta da wani Kalan Tsausayi tace"Abban Jawad daman kam mganar Amina ce..! Cikin dan Fargaba yace"Amina..?me Aminan ta sake yi kuma..? Da sauri tace"Kwantar da Hankalinka batayi komai ba..Kawai ni ke son mgana Dakai kam Auran da mallam ya hada Tsakaninta da Danmallam na wajem Hajiya..! Kallonta yake yi ko Kiftawa bai yi ba cikin mamakinta yace"Ina jinki..Sai me ya faru kuma..? Mamanmu ta gyara zama tana Fadin"Tsakani ga Allah Abbansu baka ganin an kwari yarinyar nan..? Cikin kosawa yace"Ina jinki..jeki kai Tsaye kan mganarki..! Mamanmu bata Lura da yanayin kallonta da yake yi ba ta cigaba da Fadin"To gani nayi shi ba sa"anta ba In fa aka duba ya kusa haihuwanta in da auran kauye yayi..Ina Amina zata kai shi..?Sannan ga tarin Kishiyoyi har Biyu Abbansu a shekarun Amina batasan Dubarun zama da Kishiya ba,Shiyasa naga bari nayi maka mgana gaskiya aduba wannan al"amarin..! Kallonta yake yi yana kokuwa da bacin Ransa kafin cikin Kaushin Murya yace"Ita Aminar ne tace miki bata son Dubarun zama da kishiyoyi ba..?To don Ubanta agidan nan Tsakanin mata Biyu ta taso..Gidan Baba Mallam kuma Hudu garesa reras gayamin wani karatu ne ya Ragemata bayan na wadannan gidajen..? Sai mamanmu ta Daburce cikin Inda inda ta fara fadin"Ai kasan yarinya ce..Allah na Tuba ko hamida girman jiki ne..Ammh sai wannan shekaran ne suka shiga sha shida fa..Ina zata kai Umar..? Akwai zalunci gaskiya..! Kai Tsaye yace"Naji an zalunceta..Yanzu me kike so ayi..!? Ta zata ya yarda da mganarta ne yasa Cikin Fara"a tace"Yauwa..Mallam kawai zaka je ka fadamawa baka son wannan Hadin na tabbata zai saka Danmallam ya saketa..! "KE BALARABA..! Aba ya Daka mata Tsawa da sai da ta Tsorata cikin Bacin rai mai Tsanani yace"Ita Aminar ne ta aiko ki kizo ki Fadamin naje na samu Mallam na Fadamai bata son auran Umar..?Tana so ya saketa..? Mamanmu Sai taji ta kasa mgana Mikewa yayi cikim bacin rai yana Fadin"Dake nake mgana..! Cikin kwantar da Murya tace"ba yadda ka Dauka bane..Wlh basu dac..! "daman waya ce sun dace..! Ya katseta cikin Tsawa kafin ya Cigaba da fadin" A yanayin Rayuwar Umar Kwata kwata Amina bata Dace dashi ba..Ita din ba ajinsa bane..Kinsan waye Umar kuwa..?Kyakyawan Asali Ubansa Malami ne, da ba iya Nageria ba kasashen Duniya sun san da zamansa Umaru nada shaidar Degree guda Biyu akan abunda ya shafi Qur"ani da Hadisai Balaraba tashin Madina karatun Madina garin ma"aiiki Kinsan adadin iliminsa..?Koyarwa yake a Babbar Jami"ar Musulunci ta Madina Shine kike fadin an zalunci Amina domin an aura mata Mutum nagari mai kamala da nagarta..Mai Sanyi mai biyayya da gudun mgana Shine kike fadin an zalunceta..?To bari kiji ba ita aka cuta ba Shi aka Cuta..Shi aka Tauye Balaraba ammh bai Bude baki yayi mgana basai ku..!?to ni Ubanta banda Sanadin Ubansa da ko Filin jirgin sama bazan taba Tsallakewa ba..! Ya karishe fada cikin bayyana bacin ransa har jijiyon kansa na mikewa. Mamanmu kuma ta Daskare Rashin Sukuni ya shigeta tasan ba Nasara wannan gabar bata ci nasara ba sai dai bata sare ba cikin Lallashi tace"Kayi hakuri abun bai kai harda gori ba..! Dakatar da ita yayi yana fadin"Ko ni Sa"idu ban isa Mallam yayi Umarni akaina na Tsallake ba ballatana abunda na Haifa ki Fadamin gaskiya Aminar ce ta aiko ki ko..? Mamanmu ranta ya gama baci shiyasa tace"Yarinya ta fadi Ra"ayinta ne Abbansu kada kaga Laifinta..! Bai jira cewarta ba Fuuu ya fice yana kwala Kiran Sunan Amina Tun daga Cikin Dakin har ya fito Tsakar gidan Mamanmu ta rufamai baya gabanta na Fadi. Amina da suke hira da Hamida da taji kiran Aba sai da gabanta ya fadi kuma sai suka ganshi agabansu kwatsam cikin Tsoro ta mike tana fadin"Gani Aba..! Yadda idanuwanta sukayi ne saboda Tsoro sai ya ganta kamar Hadiza Shiyasa sai ya Sauke Murya yana Fadin"Zo nan..! Lokaci daya ya juya ya Raba gefen Mamanmu ya koma Falonsa Amina ta koma Daki gabanta na Fadi ta Dauko Hijabinta ta saka tabi bayansu Hamida da Zeenatu sukayi Tsuru Tsuru suna Tunanin me ya faru kuma..! Dukkansu a tsaye ta gansu Aba da Mamanmu sai ta kara Rikicewa yasa ta Zube gabansa cikin Rawan baki tace"Gani Aba..! Cikin rawan murya sai yaji Fushinsa ya Sauka sai yaji Tsausayinta komawa yayi ya zauna yana Sauke Numfashi kafin yace"Amina..Ni waye a wajenki..? Sai da ta kallesa sannan tace"Kai Baba na ne..Mahaifina..! Cikin Jinjina kai cikin wani irin Sauti yace"Indai ni mahaifinki ne Amina..Ki sani ko bayan raina kika bijirema Auran Jinin Baba Mallam ban yafe miki ba Amina..! Ba Amina kadai ba hatta Mamanmu ta firgita cikin wani yanayi Amina ta Dago ta na kallon Aba cikin Taruwan Hawaye aidanuwanta. Ganin haka yasa ya Daga mata kai yana Fadin"Eh haka nace..Ban yafe miki ba Amina..Sannan zan sallama ki acikin ya"yana..Bazan jure ganin Abunda na Haifa ya Bijirema Mutumin da ya zama gata na ba..Mutumin da ya Lullube Rayuwata da Duka Alheransa..ki Tuna da wannan..! Da haka ya mike ya shige ciki ya bar su nan Amina ta kalli mamanmu sai hawaye sharr. Mamanmu tayi saurin cewa"Tashi kije zamu yi mgana da safe..! Ba musu ta mike ta fice bayan ta share hawayenta tana fita su hamida suka fara Tambayanta Lafiya Mirmishin Daya fi kuka ciwo tayi kafin tace"Bakomai..! Daga haka ta shige daki kokarin Daidaita kanta take yi domin tayi alkwarin daina bayyana rauninta kan wasu abubuwan..! Ko washegari kasa ce mata komai tayi mamanmu ta tuna yadda suka kwana Aba bai kalleta ba tasan kwabarta tayi Ruwa da Safe ta Fadama Madina komai ita kuma tace bama zai sabu ba auran nan  bazai Daure ba koda ya Tabbata din.! Amina kuma ko hanne bata fadamata abunda Aba ya fadamata ba,sai dai ta Dauki nauyin mganar acikin ranta tana jin kamar abu ne mai wahala.! Haka Rayuwar ta cigaba da Tafiya su Zeenatu suna cigaba da Jarabawarsu sun gama Weac sun fara Neco gefe Daya kuma ana cigaba ana cigaba da Shirin Bikinsu wanda Baba mallam yace nan da wani Lokaci za"ayi Auran nasu kamar yadda Tsarin yake..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️27* A kwana atashi ba wuya a wajen Allah gashi har kwanaki sun wuce an shiga sattitika sannan an shiga wattani Tunda su ya zeena sun kamallah Jarabawar fita babban Sakandiri sai kuma mganar auransu ne ya taso gadan gadan kamar yadda kowa ya sani ne Mallam baya aurar da ya"yansa sai kin sauke Qur"ani da Haddan sauran Littafai Sannan Bisa ka"ida Makaratanr Haddarsu zata Shirya Walimar sallama data Bada kyatttuka kamar yadda aka saba. To wannan karon bata Sauya zani ba shiryen shiryen ke gudana Tunda nan da Sati uku Baba mallam yace za"a Daura auran a mika amaran a Dakunansu Ya zenatu kaduna za"a kaita ita kuma Ya Abida porthercourt inda Mijinta ke aiki. Ta kowani bangare shiri ke gudana Sai dai shirin yafi girma a bangaran gidan Baba Mallam kamar yadda aka sani Hajiya Babba ke da Alhalin komai a hannunta hatta kayan Daki sun gama komai Na Abida Ya Zahra ke da Alhakin siyan komai Tunda ita ke poethercourt ita hajiya ta turama kudi ta siya manyan kayan achan Kananun da sukayi saura ne aka siyesu anan,na Zeenatu ma ya jidda Dake kano aka barma komai ita tayi siyayyan komai ranar Jere kadai take jira babu abunda bata siya ba kamar Yadda Hajiyan ta tsara komai,Dayake Aisha ta bar kaduna aiki ya maida mijinta Abuja. Tunda aka Tsaida Lokaci ya Abida da ya zeenatu suke ta rama atsaye sai wuya da ido kowa yasan sun fi Damuwa akan sauran da aka aurar duk sun yi sanyi barin ma ya Abida dake da Zakewa ammh yanzu ta koma Ruwan sanyi,Ko su Amina sai sun gaji da Tsokanarta sun kyaleta bata ma bi ta kansu kamar baya ballatana ya Zeenatu daman bata cika sakar musu ba Sai dai tafi ma ya Zulaihat sakewa da Mutane da Sakin Fuska..! Ana biki Saura kwana goma Hajiya tace aje ayi jere kaduna Na Abida sai ana gobe Daurin aure Haj.Uwani zata tafi ita da ya Aisha su hadu da su Zahra su yi jeran kafin Amarya ta kariso..! Masu tafiya jeran ya zeenatu Anty Amarya ce sai Haj.Nasara sai matan Ya Nasir da ya Jafar shamsiya da Fadila suka tafi kano suka kwana Daya daman already kayan dakin sun isa kaduna Washegari suka wuce suka ma Zeenatu jere a gidanta mai kyau da tsari,Anan gidan suka kwana Har da Jidda sai da Safe suka shigo Motar Haya zuwa Gumel ya Jidda ta hau ta kano..! Tuni shiryen shiryen ya cigaba da Tafiya ta kowani bangare Amina ta fi kowa Murna ganin Ya zeenatu zata tafi ta bar musu daki daga ita sai Hamida in taga hanne na Damuwa Dakin Hajiya bakowa sai ita kadai Dariya Amina ke mata tana fadin"Ke fa banza ce..Bama kiji Dadi ba Daga ke sai Hajiya ki sha Shagalinki.! Sai hanne tace"Kadaici zai dameni Amina..! Sai Amina tace"Sai ki dawo gidanmu da zama ko Hamida..? Sai Hamida ta gyada kai hanne baki take turawa tace"Uhmm kema waya sani ko daga nasu Bikin sai naki Amina..! Aranar da Hanne ta fadi haka sai da suka kwana Amina bata mata mgana ba Tana Fushi da ita Sai da Hajiya ta shiga mganar tayi Sasanci Ta kalli Hanne tace"Ki bata Hakuri hanne..Ko ni ce mamah haka zam miki Fa..Ai sai naga kamar kin gaji dani ne kin kosa na tafi..! Jin haka yasa Amina ta Sassauta Fushinta tace"Hajiya hakane fa..Kamar ta gaji dani..Ni ba inda Zani ina nan tare daku ko Hajiya..? Ta fada idonta na tara maikon Ruwa Hajiya na Danne Dariyan tace"Da yardan Allah ma kuwa..! Da sauri Amina tace"Yauwa Hajiya..Mun shirya..! Tafada tana kallon Hanne har da bata Hannu suka kulla Hajiya na Dariya ita da Hamida harda ya Abida Dake falon acikin ranta tana auna yadda zama zai gudana Tsakanin sanyi da Miskilanci da Dattako da kuma Masifa da Jidali da Rashin kunya awaje daya Lalle akwai kallo kuwa..! Su Amina wannan karon kansu yayi girma saboda su,su Abida suka sanya akan abunda za"asu raba wajen Walima su ka fara Bude Hanci suna Daga kai suma sun girma ba yara bane Tunda ana sakasu a sha"ani ba yan aiki aka maida su ba kamar baya..! Tare dasu akayi Donot da Samosa da Dublan din da za"a raba agidan su ya Jafar suka hadu da su Anty Shamsiya,Sai kuma abincin da za"ayi aranar,waina kuma Gida za"ayita Mamanmu zasu yi da bakin gusai in sun iso Hajiya kuma ita tayi abun Rabo na Amare mug din shan Tea da Maficai da kofuna sai Jaka mai kyau Haj.Uwani tayi Key holder na Rabo Haj.Nasara kuma tayi robobi masu Murfi Dauke da yaji aciki Anty Amarya tayi Turaran wuta,Ta shiga Bikin sosai bata koma baya ba komai da ita ake yi har Amina na gulma Saboda Sakina take wannan Shigewar har sa"adatu wannan karon bata ware kanta ba Haka Anty Amarya tace mata Kada ta ware cikin yan"uwanta duk tsiya suna Tare bata mgana da Amina itama bata mata sai dai su yi mgana da Hamida ko Hannatu..! Bangaran Kayan da amare zaku saka Baba mallan ya bama Hajiya Komai a hannunta an dinka musu kala uku uku Less Daya amtafofi Biyu masu kyau da Tsada sai Dogayen Riguna bakake guda biyu sai aka Dinka musu Hijabai Farare har kasa na walima sannan kuma ta Dinka ma su Amina Atamfa da Hijabi fari sai kuma su Matan Baba Maallam din suma Atamfa ce iri Daya harda Mamanmu na Fitan Biki kamar yadda aka saba Allah Sarki ba yaya da komai tare ake yi musu..! Biki ya rage saura kwana uku Ranar agidan ya jafar suka wuni har Dare suna yin meatpie din da za"a saka a Takeway,a kasa suka tako zuwa gida Tunda duk ba mazan gidan ya Shamsu yana Dutse ya jafar kuma basu dawo ba Akilu ne da Zubairu kuma Baba mallam ya hana su Daukan Mota! A kofar gidan Baba Mallam suka hangi ya jafar da ya Nasir da Aba awaje suna mgana sai wani mutum basu ganesa ba,Gabadayansu gidan Aba suka shige,Har da Sa"adatu su ya Zeenatu ne agaba su Amina na baya sai da suka shige gidan sannan Amina ta jawo Hannun Hanne suka koma baya zatayi mgana kenan ta Rufemata baki sai da suka Shige korido kana ta Saki bakinta cikin mamaki Hanne tace"Menene wai..? Amina ta Tabe baki kafin tace"Ke baki ga sa"adatun nan bane..? Sai wani shigemana take yi yanzu..? Hanne tace"To ina ruwanmu..Daman mu bamu gujeta ba itace ta janye jiki Damu Tunda yanzu kuma ta Dawo shikenan..! Hararanta Amina ke yi har ta gama mgana kafin tace"Sai gamu marasa zuciya sai mu biye mata..?Kune naga kuna mata Dariya ni ko kallo bata isheni ba wato taga yanzu mu ba yara bane muma mun girma Dole ta shigemana..Ni gaskiya ku sallameta in kuna son na rika Binku keda Hamida..! Ta fada har tana yarfa Hannu,Hanne tace"Ko bakomai ai yar"uwarmu ce Amina..Naka ai sai naka..! Amina tayi karamin Tsaki kafin tace"Yar"uwarki dai ni ban hada komai da ita ba .! Hanne ta rike baki tace"Ehye..?in dai kuwa Kikace baki hada komai da Sa"adatu ba nima baki Hada dani ba Domin Uban mu daya da ita..! Amina tace"Ke dabam ita dabam..In kuma kin Dauka hakanne to haka din ne..Ni fa Hanne basai kin min gorin Sa"adatu yar"uwarki bace ni kuma bare ce.! Hanne ta saki baki kafin tace"Yaushe nace miki bare Amina..? Cikin kufuluwa tace"Bansani ba..! Tazo zata wuce fuu Hanne tace"Da kike mganar yar"uwata ce..To in dai baki karbi gaskyan Sa"adatu yar"uwarki bace ita din kanwa take gareki..! Sai alokacin Amina ta waigo Cikin wani kallo tace"Kanwata ta gidan uban wa..? Kai Tsaye hanne tace"Kanwar MIJINKI ce..Kanwar ya Danmallam ne ai shi bai isa yace ba kanwarsa bace..! Amina taji kamar ta Tsinke hanne da Mari sai kawai taja Tsaki mai girma kafin tace"Sai dai kanwar Ubana bata Miji ba..! Daga haka ta wuce afusace ta bar Hanne na rakata da Dariya Tayi Tsaki yafi sau goma in ta Tuna da Abunda Hanne tace shiyasa suna shiga Dakin mamanmu taga Sa"adatu kwance kan kujera ta Fara sakin tsaki tana Fadin"Ni fa bana son shisshigi..Abaya an nuna kai da banza duk Daya sai yanzu kuma azo ama wani Haba Haba dakai..Munafunci ne bana so..Kowa yayi ta kansa..! Take fada tana Hararan gefe ya Abida na Dakin kuma tasan da Sa"adatu take itama Sa"an tasan da ita take yi ammh bata nuna ba Tunda abun nan ya Faru na wattanin baya Anty Amarya tace mata ko musu ta sake yi da Amina sai ta sani ammh yarda ta Tsani Amina ko Hanya bata Kaunar ta hadasu sannan karin bakincikinta da taji labarin auran dake tsakaninta da ya Danmallam Haba ai ba"a duba ba ba Sa"anta bane sannan Anty Sakina tafi karfin ta Hada Miji da Amina don ma Anty Amarya ta kwabeta da kame bakinta da kanta cikin mganar ne da yau sai Amina ta raina kanta maimakon haka sai ta nuna kamar ma bataji ba ya Abida ce ta tanka Tunda tasan Halin Amina cikin Fada tace"Amina ki mana shuru..Wlh bazaki Fara mana jidalinki da Daddaran ba..In kuma kika ki wlh bar ganin na yi sanyi yanzu sai mu Taru mu nada miki na jaki..! Amina ta Hura hanci kafin tace"Mu ta kanmu kowa yayi ta kansa..Dariya ba fa so ba mai hali bai bari ba.! Cikin waka take fada tana nuna Sa"adatu da baki ya Abida sai ta kasa mgana gashi mamanmu bata Dakin tana Tsakar gida wajen su hanne. Amina cigaba da wakarta tayi tana fadin"Takun yayi..Wasu sun saki Reshe sun kama ganye...Warrrr..! Sai ta watsa ma Sa"adatu hannu data juyo tana kallonta sai ta Daga mata ido ta Juya kafin ta fice ganin ya Abida ta Biyota ta gudu ta fice tana Dariyan Shakiyanci Ya Abida ta kada kai kafin tace"Kai Amina sai fatan Allah ya shirya. ya Danmallam zai sha fama..Sa"a kiyi hakuri kin ji ko..! Sa"adatu tayi wani munafukin Mirmishi kafin tace"Bakomai ya Abida..Amina yar"uwata ce kuma haka take..Kinga tunda musan Halinta sai muci mganin da zama da ita kamar yadda su hanne sukayi..! Ya Abida tace"Yauwa Sa"adatu na..! Dariya kawAi tayi tana son ya Abida bata da Damuwa sam kaf cikin ya"yan Hajiya Babba da Hanne ne basa shiri itaama Saboda Amina ne..! Abida aranta tana Tunanin ina Amina ta iya wakar nan su da ba waka suke ji a agidan ba,Abunda bata sani ba a wayar kawarta Zainab Amina tasa wakar Warr. Agidan zasu kwana shiyasa suka Firfito waje ana Hira baki sai gobe zasu fara sauka ya Aisha ma gobe zata iso ita da ya Jamila da ya zulfa"u duk agoben zasu iso ya Jadwa ne bazata zo ba jamila da Jawahir ne kadai zasu zo har ya jalila bazata samu zuwa ba abun yayi kusa kusa da Rasuwar Yaya da suka zo Baba mallam ne ma yace duk suyi zamansu sai nasu Hannatu saboda kada Zirga zirgan tayi yawa .! ****** Baba maallam na gaban Makeken Dorowansa na Littafai Dake falonsa Sanye yake da Jallabiya Mai ruwan zuma kansa ba Hula fufuransa ta bayyana sai Farin gilashinn da ke karamai karfin gani Falon akwai hasken Wutan gen ko"ina tar,kansa na chan kasa yana so ya Dauko wani Littafi Anty Amarya ta shigo Falon cikin kwalliyarta Ita ke da Shashen ayau din dazu ta iso taga yana Tare da su ya jafar da su Aba sai ta koma sai da Tara ta wuce goma saura sannan ta Dawo domin ta tabbatar da zuwa Lokacin Mallam din shi kadai ne..! Har ta kariso bayansa bai sani ba sai da ya Dauko Littafin ya Juyo sannan yaci karo da ita bai nuna Razana ba illah kallonta da yayi yana Fadin"Da girmanki marliya sai ki shigo ba sallama..? Ido ta Juyamai Kafin tace"Nayi baka ji bane..ina nan na Tsaya ina karema Mijina kallo sai yanzu na Lura ashe ashe Mallam ya Tsufa bansani ba..! Ta karishe fada cikin yar Dariya Shima Dariyan yayi kafin ya wuce gaba tabiyosa abaya cikin Sanyinsa yace"Sanda aka bani auranki Farin gashi bai gama cika kaina ba marliya..Kuma ahaka kika gani kikace kina sona ko ba haka ba..? Ya fada yana zama kan Daya cikin kujerun falon mai zaman Mutum Daya tana Dariya ta zauna ahannun kujeran tana fadin"Ah..Ni yaushe nace ina sonka..?Kuma ka rufeni da rawaninka bansan haka farin gashi ya Cika kanka ba..! Tafada tana jan gashin nasa yar Dariya yayi kafin yace"Ai lokacin bai kai haka cika ba..Bayan na aureki ne kika Ida Tsufar dani Marliya..! Yafada yana kallomta Baki ta Rike tana Dariya tace"Mallam!. Saurin tareta yayi da fadin"Dole na fadi haka..Naga yau Amaryan tawa Gori take ji da tsokana..! Dariya take yi tana fadin"Kodai ka Tsufar dani mallam? Mirmishi ya saki kafin yace"Ko nan da shekara ashirin muka kara tare..Mallam dinki zai cigaba da kallon yarintarki Marliya..! Sai kanta ya fashe ta fara Mirmishi Ta sani duk cikin matansa tafi kowaccensu Kuruciya kuma Tsakani ga Allah sai kana da kuruciya ake Damawa Dakai. Bata samu zarafin mgana ba wayarsa Dake saman Center table din Dake falon ta Dauki Kidan Larabawa Gabadaya hankalinsu ya koma kan inda wayar take cikin Daidaita Natsuwarsa yace"Hanzarta mikomin kada ta katse..! Da azama tatashi ta Daukomai sai dai ganin sunan mai kiran yasa nan da nan Ranta ya baci ABU NA..! Hajiya ce wannan Keda sunan tun auranta da Maallam ta sanshi dashi abu na kamar wani yaro mtseewa tsaki taja acikin Ranta kafin ta mikamai wayar yana Fadin"wake kirana..? Sai da ta koma Kujeran dake gefensa kafin tace"Ina ga Hajiya ce..! Tafada tana Daidaita yanayinta Abu Daya ke batamata rai sufa da sunayensu yayi Saving a wayarsa ammh ita Hajiya kai Tsaye yake nuna ita din ta Dambace komai zai yi kafin ya aiwatar dashi ita da Sa"idu sai sun fara Tabbatar dashi sannan..! Tana jinsa Daya karbi wayar yana Fadin"Hajiyar ce ma ba musu ba..! Kiran ya katse sai yabi bayan kiran tana jin sandda Hajiyar ta Dauka da Sallama ya amsa yana Fadin"Hajiya..! Bata ji me tace ba sai dai taji yace"Kizo shashena ki sameni daman nima ina son mgana Dake..! Daga haka bata san me tace ba yace yana Jiranta ta katse kiran Sai da ya gama sannan ya Dago yana kallon Anty Amarya kafin yace"Amarya..Amarya..! Dan juya ido tayi kafin ta dan Tura baki na Shagwaba Mirmishi yayi kafin yace"Yanzu dai kimin hakuri adana duk wannan amarcin naki zuwa anjuma..Ina so na gana da Hajiya na minti talatin in ba Damuwa..! Yake tayi kafin ta mike cikim basarwa tace"ba damuwa..in kun gama sai ka Taboni..! Cikin jin Dadi yace"Shikenan Allah yayi miki albarka..! Aciki ta amsa ta fice tana kunkuni ahanya suka Hadu da Hajiya tasha Lullubinta suka gaisa ta wuce Anty Amarya ta bita da kallo tana Fadin"Tsofai tsofai dake bazaki hakura da miji kibar ma yara irin mu ba Mtsewww Jaraba..! Take fada har ta fada shashenta Hajiya batama san tanayi ba Falon Mallam ta karisa sukayi mgana kan Kayan garan Amaran ne da Tsarin da za"a cire musu sai abincin Bikin da na yan Daurin auran,Baba Mallam yace su bar abincin Daurin aure Mallam Hamza ya Dauki nauyin mutane bayan Daurin aure zasu je suyi Reception abincin gara kuma yace a Diba kamar yadda tsarin yake..! Bayan sun gama mganar Hajiya ta mike zata tafi tunda ba ita keda Mallam din ba shi ya Tsaidata da Fadin"Zainabu kunyi mgana da Da'nki kuwa..? Tana Daga Tsayen tace"Sa'idu..? Yar dariyq yayi kafin yace"Sa"idu..Sa"idu..Ke da Sa"idu bansan wanda yafi wani kaunar wani ba..Nan fa muke mgana dashi gani ni Ubansa ammh sai ya tsallakeni komai nace sai yace Mallam kuyi mgana da Hajiya yadda tace haka zaa"ayi..Anya Zainabu baki kwacemin Sa"idu ba..! Hajiya na Dariya tace"Ni ban kwacesa ba..Ammh ai kowa yasan Sa"idu na Zainabu ne..Kayi hakuri dai da aron da nake baka..! Mallam yace"Ai na ma gode..Tunda ana bani aronsa! Dukkansu dariya sukayi kafin tace"Nazir kake mgana..?Mun yi mgana dashi dazu yace sai Ranar Daurin aure zai zo..matarsa kuma yace saboda aiki yara kuma ga makaranta..! Baba Mallam yace"Bama shi ba..Ai shi nasam zan samu labarinsa awajenki..Umaru fa nake mgana..! Hajiya ta tabe baki tace"Sai kace min Danka. kanin Sa"idu sai nafi ganewa..! Mirmishi yayi kafin yace"Zauna muyi mgana nasan kema bai kiraki ba..! Hajiya ta zauna gefen Mallam tace"Jiya ya Kirani mun gaisa Daganan bai ce min komai ba badai wata matsala bane ko..? Mallam ya Sauke Numfashi kafin yace"To matsala ne kan matansa..! Hajiya tace"Topha me ya faru..? Mallam yace"To ni ma bansan Farkon abun ba..Yadda dai Abu kattab ya Kirani ya fadamin kan zuwa wannan Sha"anin ne..! Hajiya cikin mamaki tace"Daman ba Danmallam din ya kiraka ya Fadamin ba..? Mallam yace"Kema kinsan bazai Fadamin ba..Sa"idu ya Kira sukayi mgana nima yanzu bayan fitansu Abu kattab din ya Kirani mukayi mgana..Kan zuwa Sha"anin nan ne yace yaso yazo shi kadai saboda zirga zirga da kashe kudi kuma ko wata biyar basu yi da komawa ba,gashi ba wasu kudi a hannunsa sai yace zai taho shi kadai sai Sakina tace zata zo ita zata Biya ma kanta kudin jirgi,To bayan haka ita Saratun daman yace tayi hakuri ta zauna har su dawo ga karatunta tunda tana hada Degree dinta anan Jami"ar musulunci to bai kuma sani ba ko Sakinar ce ta Zugata har ta amimce sai ta fara mai boren itama sai ta taho shine yace duka su hakura bazai zo da ko daya ba Sukayi ta Hayaniya yayi musu yaji yaje ya kwana acikin makaranta shine ita Saratun taje ta Fadama Abu Kattab din shi kuma ya Nemo Umaru yayi musu Sulhu ya kuma bama Umaru Umarni Daya Taho da Sakina Ita kuma Saratun ta zauna ta jirasa har su dawo Tunda tataba zuwa kinji Abunda ya Faru..Kuma dazu fa mun yi mgana dashi bai ce min komai ba yadai cemin zai taso gobe zai kwana ajidda Daga jidda zai shigo Jirgi zuwa Kano..! Hajiya tace"Allah ya kyauta..! Mallam yace"Amin fa.bana so Kattab yaga kamar na nuna Umaru dana ne..Da sai nace itama Sakina ta zauna ban ga abunda zata zo yi ba..! Hajiya tace"Barta tazo ba ruwanka..Inkana da iko da Mijinta ita fa..? Cikin Dattakonsa yace"Ko bata tashi agidana ba..Kamar ya"yana Haka na Dauki matan ya"yana Saboda haka na isa da su gabadayansu ballatana ahannuna tatashi na kuma aurama Umaru ita..! Hajiya ta mike tana Fadin"Gwara da baka ce ba..Allah ya sauke su lafiya..! Ya amsa da Ameen daganan sukayi sallama ta fice ya bita da kallo bai tana ganin mace mai kawaici da kauda kai iron Hajiya ba to sai marigayiya matar Sa"idu su kan suna da kauda kai kan abunda suka Haifa yasan Hajiya bata taba saka baki kan Umaru da sakina ba,ko abaya ballatana yanzu..! Anty Amarya ya Kira yace ta shigo Ya sallami Hajiya ba jimawa sai gata ta Dawo ta kara sabunta kwalliyanta yayi ta kallonta yana yaba mata kanta nakara Fashewa.! ***** Tun washegari bakin nesa suka fara isowa yan Gusai ne farko su ya Jawahir har da Zafira akazo duk da ba"azo da mamanta ba ta Makalema Ya Jawahir sai da ta saka baki aka barta tazo suka Hade dasu Amina sai Ihu da Murnan ganin juna Tunda su ko sha"ani ake yi sai dai su mamanmu su je su kan bamai barin su. Bayan sun iso ba Dadewa sai ga ya Zulfa"u ta iso ita da Uzairu yana shirin kamallah karatunsa gabadaya na Degree Ya Nazeem dai yace shima sai ya gama Project dinsa zai dawo ya Aisha ma ta iso ita da ya Sadiya da suka Dawo da ga America ciki ma gareta su Sa"adatu haka suka ozare jiki daga su Amina an ga Yar"uwa. Amina tace daman munafukace su hanne dai basa mgana Amina ce ta iya wannan jidalin. Ranar laraba su ya Jamila suka iso da ya Nazifa da ya Fatima sai ya Akila da ya ikram dake kusa ya Zulahait sai wajen yammah ta iso Daga jigawa gida ya cika da baki sai Hada hadar Biki akeyi. Da daddare misalin karfe 9pm na dare su ya Danmallam suka sauka su Amina bama su sani ba sai da Sabeeha tazo kiran Ya Sa"adiya Dake nan gidan Aba wajen su ya Zulaihat tazo ga Anty Sakina sun iso. Ya zulaihat na wajen tace"Daman da ita zai zo..? Ya Jawahir tace"Ni har shi na Dauka bazai samu zuwa ba..Tunda har goggo Husai ma ita da Ya Jadwa bazasu samu zuwa ba..! Ya Jamila ta kada baki tace"Ya za"ayi kuce bazai zai zo ba..kuma kunsan zai zo komai rintsi shine fa Babba..! Amina da su hanne na wajen Amina tana jin sun iso bata kara mgana ba ta Hade ranta ganin hanne da Hamida na kallon ta suna kuskus zafira dai na gefe bata son abunda suke fada ba. Ya zulfa ce ta Kalli Amina kafin tace"Ki tashi ki chakare Aminene..Miji ya sauka fa..! Amina taji ta muzanta ta fara Fiki Fiki da ido sai suka saka mata Dariya Gabadayansu har suna Tafawa kawai sai tatashi Fuu ta fice Daga Dakin daman suna Dakin yaya ne gabadayansu su hanne suka rufa mata baya jawahir tabi Amina da kallo kafin tace"Amina sai dai Allah ya tarota..! Basu kuma hadu da Sakinar ba sai Washegari wajen walima suka Ganta,Su Dayake basu zo da wuri ba,sai da suka gama Hada komai na Rabon,da wainar da akayi da abinci almajirai sukayi gaba dashi su kuma ya Uzairi ya Dauko kayan rabo a Mota..! Atamfansu ta ankon su ya Aisha suka saka da sabbin Hijaban da Hajiya ta Dimkamusu,Su sukayi rabo ita da Hamida,Hanne da Zafira sai Sa"adatu data gayyato su mariya yan ajinsu Amina taso ta tada fada su hanne suka taushe ta akayi komai aka gama An bama ya Zeenatu kyaitan murya da Tajwud sai kuma ya Abida na Tsafta da Sanin Hadisi. Sai nasihan aure da mallanm Datti Shugaba yayi musu Amina bata ma san Sakina na wajen ba taje tana Raba musu Takeway din da suka saka Nama da Meatpie domin kajin gidan gona sun sha wuka. Da ta bata sai taki karba sai da Sabeha ta karban mata,Amina sai alokacin ta kalleta ta wani Kalleta Sakai sakai itama kuwa ta rama ta wuceta aranta tana fadin"yi sabgrki in yi tawa..Baki gabana..! Ita kuma sakina tana mamakin girman Amina taga ta kara tsawo ba kamar rasuwar nan ba. Karfe shida da wani abu aka tashi Walimar ammh su sai dare suka baro makaranta sai da suka daidaita komai sauran kayan rabon da abincin Daya ragu suka bama Sauran Daliban makarantar.! Da suka Dawo amaran suna gidan ya Jafar su suma chan suka wuce suka kwana sai da safe suka Dawo gida sukayi wanka suka saka atamfarsu Sabuwa suka koma gidan suna ganin Shiryawan Amare bayan sallar Jumma"a za"a Daura auran..! Hajiya Shashenta ya cika da baki yan"uwanta daga maiduguri sun so sannan Dangin mallam yan bazanga sun iso tun jiya,Soyayyan Naman kajin da aka soya tun jiya tace ma Haj.Masara ta ijiye a wajenta tana so ta bama baki sai taje Shashen ta Karbo Tunda duk ba yaran sai Haj.Nasara tace ta kaima Anty Amarya Ajiya data ga Baki sun cika Shashenta. Gashi Anty Amarya sun tafi porthercourt ita da  ya Aisha da yagana kanwarta sai Haj.Uwani Tun safe suka bi Jirgi Wayar Anty Amaryan ta Kira sai tace mata ta Tambayi Sadiya ita tabama ajiya tace in Hajiyar tazo abata..! Saboda Jama"a da hayaniyar Biki yasa Har Hajiya ta shiga Shashen Anty Amarya ba wanda ya Lura da ita Danginta cike da Daki duk da bata nan,Sakina ce a tsakiyarsu an yi mata Rumfa tana fadin"Ai baku sani ba..Da naga yarinyar sokuwa ce yasa na Zugata nace mata saboda yayi amaryane yaki zuwa da ita Nageria kunsan Larabawa da kishi..Daman kuma tamai Bore lokacin da na Fadama ta Mgamar auransa da Amina..Koni fa bai fadamin ba dana Turkesa sai cemin yayi ai yasan naji da muka zo gaisuwa da abun ya bani haushi sai na Hadamai famfo wajenta ita kuma ta hau kai ta Dinga Bore Wlh duk Sanyinsa sai da ta kaisa bango..Naso ne ta kuresa ya Saki wawiyar banza..! Gabadaya suka saka Dariya wata acikin yan"uwansu na Dutse tace"Dakyau..Sakina cikin Ruwan sanyi tayi waje ta baki waje..! Sakina tace"Wlh ai bana nuna mata ina Kishi da ita..Nuna mata nake yi mun zama Daya sakaryan ta yarda..Cikin sauki nake hadamata Tarko tana fadawa..! Ya Sadiya na wajen tace"kinsan larabawa ba wayau wani Lokaci kuma basu san kishi ba..! Sakina tace"Basu san komai ba..Sai son miji! Dariya suka saka gabadaya sai Sadiya tace"Sai ma Amina tatare ku zama ku Uku sai Show din yafi kyau..! sakinaa tace"Ai bama zata taren ba..kinsan Allah na yarda dakaina yadda aka Daura auran nan haka zata kare anan agaban iyayanta Daga karshe har su gaji su raba auran ni bata gabana..nafi karfin na Hada miji da wannan kwailar Allah ya Tsareni..! Suka saka Dariya wata mai zakin murya tace"sai dai ki bar mata Mijin..! Sakina tace"Kwarai da Dai in Rab'u da abu ta sanshi..Gwara na bar mata gabadaya..! Idonsu ya rufe basu ga Hajiya Tsaye agabansu ba sai da tagama jin komai sannan ta kara Rafka sallama suka juyo suna kallomta arazane sai ta nuna musu su yara ne cikin Haba Habanta tace"Shigowata kenan ina ta sallama shuru..! Da sauri Sadiya tace"Bamu ji ba Hajiya..! Sai tace"Kuna nan baku je kun Debo abinci ba..Sadiya ina sakon da Amarya ta bar miki ki bani..! Da sauri ta mike tana fadin"Yana Daki Hajiya bari na miko miki..! Gabadaya sun yi tsuru tsuru barin ma Sakina da kanta ke kasa Hajiya ta kalleta Cikin takaici tace"Sakina baki je wajen kannen naki ba ashe..? Cikin Daburcewa tace"suna ina ne Hajiya..? Tace "Suna gidan su Jafaru..Kuje keda su Sadiya ku taho dasu an kusa Daurin auran kunsan kuma da an Daura za"a wuce dasu..! Jin haka yasa ta mike jiki na Rawa tana Fadin"Yanzu kuwa hajiya..! Sai ga Sadiya da Botikin nama ta mikama Hajiya ta karba tayi godiya ta fice sai da ta fita wata cikin kannen Anty Amarya tace"Allah yasa Hajiya bata jimu ba..! Sadiya tace"Inaga bata ji ba gaskiya.. Sai alokacin Sakina ta iya Sauke Numfashi. Abunda basu sani ba Duka mganganunsu Hajiya taji su sannan mgnganinsu sune silar Faruwan wani abun da basu mutane da yawa basu taba zato ba..! Har takai shashenta abun na cin ranta ta kuma Kudirci kafin a gama Bikin nan sai ta nuna ma Sakina ita din banza sai dai kuwa in zata bar ma Amina Danmallam ne ammh Zama Daram in ji mai Naguda..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️28* Karfe biyu da rabi na rana aka Dauran auran su ya zeena bayan an idar da sallar jumma"a ana Daura auran Hajiya ta kira ya Fatima awaya tace su taho dasu Abidan malam zai yi sallama dasu zasu tafI kada Dare yayi ga yanayin Tsaron kasar tamu daya riga ya lalace sai fatan Allah yabamu zaman lafiya. Gabadayansu suna gidan ya jafar har su Amina,tunda amaran suka ji an daura auran suka fara kuka su ya Jamila na musu Dariya suna fadin muma hakanan akayi mana kuma gashi mun zauna..! Amina ce harda wakar"Su sukace suna so..Da basu ce suna so ba..Da ba"a basu shi ba..! Ya Abida na kuka cikin Hijabinta ta Leko Tana hararan Amina Lokaci Daya tana fadin"Kema yarinya kwana nawa ne..?Keda ma zaki bar kasar bar ma wasu dariya..! Tana fadin haka sai bakin Amina ya Mutu ta yamutsa fuska kafin ta Tura baki tace"Tab..Wlh in na je Allah ya Tsinan..! Ya nazifa na wajen tace"Kin je ma kin gama zuwa yarinya..! Amina ta kara Hade rai tana faman kunkuni aka saka mata Dariya gabadaya har da su Hamida daganan ta Hade rai bata kara mgana ba har suka shirya komai suka Tattara kayan amaran da suka cire waje Daya su Amina suka bamawa suka fara yin gaba su Uzairu zai zo da Mota ya Daukesu sauran kuma suka taka da kafarsu tunda ba wani nisa. Koda suka iso kofar gidan ba Jama"a sosai,Amina ita hankalinta ma baya ma wajen kallon jama"ar wajen duk Rashin kunyarta bata juran kallon Taron maza. Bata ma Lura da ya Danmallam Dake bakin wata bakar mota ba Shi da abokinsa Aliyu suna mgana su Hanne ne suka ganshi,Hamida Dake kusa da Amina ta tabota tana nuna mata barayin da suke Lokaci daya tana Fadin"Amina kalli mijinki..! Amina tabi inda Hamida take nuna mata da kallo,Suna dagachan nesa ne ba lalle su gansu ba,dukkansu suna Tsaye jikin Motar ne Danmallan yana Sanye cikin Shadda kalan Sararin Samaniya Dinki riga da wando tazarce anyi Dinkin zamani na matasa masu ji da kansu sai hula zanna bukar Zaran yanayin aikin shaddan Jikinsa kafarsa cikin Bakin Rufaffan Takalmi na Fatar damisa sai bakin agogon Fata Dake tsitsiyan hannunsa na Hagu bashi ke mganar ba Aliyu Dake kusa dashi yake saurareshi shi key din Mota ne ke hannunsa yake kadawa Lokaci bayan Lokaci yana Sassauta yanayin Fuskarsa. Sai da gaban Amina ya fadi da Sauri ta kauda kai ta sani ita bata isa tace Ya Danmallam ya dace da ita ba Tazaran Dake Tsakaninsu mai girma ce,kana kallonsa zaka hango Tsantsan kamala Dattako da sannin addini sannan uwa uba kwarjinin da Haiba ta mutumin da yasan addini sosai da sanin ya kamata sannan da yana kyau, kyau irin na fatan kowacce mace zabinta ya kasance haka..! Bata son mgana saboda ranta ya riga ya baci shiyasa taja karamin Tsaki ta kauda kanta sai ma ta kara Sauri ta shige gidan bata son wata mgana ammh Hanne da Hamida sai suka saka Dariya har suna Tafawa Allah yasa Zafira na baya tare da yan garinsu. Hamida ta kara riko gefen Hijabinta tana Fadin"Amina ki kallesa mana..Kai wlh ya Danmallan yayi kyau matuka..! Amina ta Juyo a Fusace daidai sanda suka shiga get din gidan Baba mallam tace"Ba mijina ba..A"a ubana ne..Nace sai dai Ubana Hamida haba..Kin Dameni..! Hamida da hannu suka kalli juna suna kunshe Dariya Hanne tace"Mijinki ne..Kuma ko bakomai ya Danmallan yana matsayin Uba ne agareki..! Amina ta kalleta shekeke kafin tace"Allah..?Aiban yi mamaki ba..Kowa ya ganni yasan auran son zuciya yayi da yar cikinsa..! Hamida da Hanne suka zaro ido Hanne tace"Amina kin ma kanki karya..Kaf gidanan ko ya Nazir bai kama kafar ya Danmallam akomai ba wlh..Baki magodema Allah ba kin Samu miji Kamar sa bama..! Cikin Hargowa Amina tace"Ban gode ba..Domin bani nayi tallar kaina ba..Da kike mganar duk gidanan ba kmarsa to ni ina ruwana..Kinsan dai ina da Aminu..Kudi kyau nasaba ga yarinta bai isa ya nuna mai ba..! Sai kawai ta saka musu kuka abunda basu taba gani ba in ta Tuna da Aminu bata iya Boye rauninta har Abada bazata taba mantawa dashi ba ko wani Hali yake ciki yanzu Allah masani..! Jikinsu yayi sanyi suka kasa mgana ganin su zafira suna kokarin shigowa ne yasa ta juya ta fara tafiya suka mara mata baya Hanne na Fadin"Allah baki Hakuri Amina..Ammh aragama yayana ko Saboda ni..! Amina ta Daga murya tana Fadin"Saboda ke..?ai ke din ba Mutumcinki nake gani ba Hanne..Ki kyaleni kada ki Tunzurani na yi miki Tijaran da zaki ji Haushina..! Hamida tace"Hanne abar mganar..! Daga haka suka kyaleta har shashen Hajiya sun shiga ba Dadewa sai ga Amaran da yan gusai,ba kamar wanchan karon ba Amina wannan karon batayi ra"ayi ba shiyasa da su Hanne suka ce tazo su raka amaran Nasiha Shashan su Haj.uwani da Nasara da gidan Aba Amina tace sai sun dawo ita ba inda zata jin haka sai suma jikinsu yayi sanyi suka ki binsu Zafirace dataga sunki zuwa sai ta Bisu. Basu fito ba sai da Zafira tazo tana Fada musu amare zasu tafi ssannan suka fito Lokacin ma suna Falon Mallam ana musu nasiha da bankwana sai fito da kayan abinci su Ya Akilu suke motocin amaran suna kwasa suna sakawa acikin Booth ya Zeenatu Tawagar angoyen ta suna shirye harda mace Daya wacce zata tafi da amarya suka zo ya Abida dai tafi gata tunda su Anty Amarya na chan sai gobe zasu dawo.. Suna wajen sai gasu Haj.Nasara da Hajiya babba da goggo yakura sun fito dasu,kafin su ma mazan ne suka fara fitowa su ya uzairu da su ya Nasir ya Danmallanm da abokinsa Daga baya suka fito baba mallam da Aba sune ke rike da Amaran zuwa motocinsu Ba yau aka saba biki agidan ba ammh wannan na Dabam ne kamar yadda amaren suke na Dabam haka suke ta kuka kamar ransu zai fita Zeenatu da Abida. Ana fito dasu suka kyalla ido suka hango su Amina suka kwace daga rikon Baba mallam suka nufesu Abida ta Rukunkume hanne tana kuka Zeenatu ta rumgume Amina da Hamida tana kuka duk da sun girmesu sune sakon su na kusa dasu akwai shakuwa sosai a Tsskaninsu. Amina bata taba tsammanin zata yi kuka domin su ya Abida zasu tafi gidan mijinsu ba ammh yadda suke kuka suna rike su ne da kuma yadda Hamida da hanne ke kuka sai Amina ta fara Tsausayin kanta tana Tunanin in da gaske ne ta auri ya Danmallam kenan watarana itama zata iya Tsintar kanta cikin wannan yanayin sun bala"in bata Tsausayin da batasan sadda ta fara kuka ba takamkame Zeenatu suna kuka ita da Hamida ganin haka yasa Abida da Hanne suka zo suka hade suka yi Rumfa suna ta kuka kamar anyi mutuwa sai kallo ya koma garesu hajiya bata awajen ta koma cikin gida Haj.Nasara ne sai dangin mamanmu dana Aba na gusai. Baba mallam tsaye kawai yayi bai ce komai ba ya jafar ne ya fara fada shi da ya Nasir suna fadin iskanci banza kukan uban me suka hadu suna ma mutane..! Baba mallam ya kallessu yana Fadin"Ku kyalesu suyi kukan rabuwa da kannensu da gidansu..Gida fa ba kamarsa kuma aure ai yakin mata ne ko domin ku din maza ne shiyasa baku san wannan Raunin ba..! Jin haka yasa sukayi shuru ya Danmallam bai ma san abunda ke faruwa ba suna haraban gida azatonsa amaren sum mika Aba kuma an kirasa a waya ya kebe agefe. Haj.Nasara ne ta kalli Baba mallam tana Fadin"Maallam Uku tayi fa..Tafiyace kuma agabansu..! Goggo yakura tace"Abidar kuma Angon yace jirgin karfe hudu zasu bi zuwa chan kuma ta Dutse zasu tashi..! Baba mallam bai ce komai ba ya juya yana fadin"Ina Umaru..? Ya Jafar yace"Yana daga cikin gida mallam..! Kai Tsaye yace"Kiramin shi..! Ba musu ya juya ya shiga ya kirasa sun ma hadu dasu ne zasu fito ya fadamai kiran mallan din sun fito kenan sai ga su Sakina da Sadiya da Tawagan yan"uwansu sun fito su ga Tafiyar amaran. Daman Aliyu ya rako zai koma sai ga Kiran mallam sai ya isa wajensa yana zuwa Mallan ya dafa kafadarsa yana Fadin"Ka ga matarka da kannenka chan sun hade kai suna ta kuka. taimakeni ka lallasomin su kafi su Jafar sanyi su yanzu sai su ce zasu kai musu hannu..! Inda mallam ya nuna mai yabi da kallo Takaici ya kumesa su din yara ne da zasu zauna suna ma mutane kuka kamar wasu marasa hankali sai karin wani takaicin wai matarsa shi fa har ga Allah ya Dauka Sakina ce da farko sai da ya kalli wajen yaga su hanne ne Tunanin sa ya basa wannan kazaman yarinyar ce bazai iyama mallam gaddama ba yasa ya kada kai yana Fadin"Shikenan mallam..! Ko kafin ma ya isa garesu su ya Zulaihat sun isa suna faman lallashinsu su saki juna Sakina na gefe ta kame tana kallon kowa Daya bayan Daya sai ta ga Danmallam ya isa wajen yana mgana batajin me yake fadi,Ranta ya baci kishi ya Rufemata ido ganin Amina awajen badai ita yaje yana Lallashi ba..! Sadiya ce tace"Ya sakina ga ya danmallam chan yana Lallashi..! Bata tankata ba ta wuce fuu sai da ta isa wajen ne sannan taTsinkayi mganarsa yana fadin"Haka kurum zaku zo kuna ma mutane kukan banza..? Kukan jin dadi kuke yi ko na menene..?Ko kuma an dake ku ne..Dillah ku sake su bana son Sakarci..! Cikin Kiftawan ido suka Saki junansu suna Cigaba da gunjin kuka Daya bayan Daya ya kallesu kafin yace"Kowacce ta kama bakinta kafin nayi kasa kasa daku..! Bai gama rufe baki ba suka yi shuru suna ajiyar rai Amina da Hanne suna rike da hannun juna kansu na kasa Amaran ya kallah sun yi Dama dama da Hijabinsu da hawaye da majina kafin yace"ku kuma ku wuce ku shiga mota..! Da sauri ya Nazifa tace"Bari mu rikesu..! Haj.Nasara na Dariyan su Amina tace"Danmallam da ka roki mallam ya bari su je koda kai Zeenatu ne zasu ji Dadi..! Ko amsata bai bata ba illah su Amina Daya kalla cikin Taushinsa yace"Haj.Ba inda zasu je me zasu je suyi kuka..?Kowaccen ku ta koma cikin gida kuma ku cigaba da kukan ku gani Tunda anyi mutuwa ne..! Sum sum suka mike hanya maimakon su koma gidan Baba mallam sai suka koma gidan Aba ko motsin kirki sun kasa Baba mallam baya wajen ya koma Falonsa shi da Aba Sakina ranta yayi Dadi ganin ba mgana mai Dadi Umar ke fadama su Amina ba sai ta saki Fuskarta. Su Haj.Nasara suka ssaka amaran Amota tare da rakiyan yan gusai da yayyinsu da kannensu suna kuka kamar ransu zai fita suka mika hanya sai Fatan Allah ya Kiyaye su. Kafin La"asar kofar gidan ya zama wayam ba Jama"a Danmallam gidansa ya koma ya Huta Aliyu kuma ya koma Dutse dazu. Hankula basu kwanta ba sai da Amare suka natsu adakinsu Jidda na Tare da Ya zeenatu a Kaduna sai gobe zata koma kano hakama Abida sai Dare suka sauka su Anty Amarya sun gama gyara komai gidan Zahra suka koma zasu kwana sai gobe zasu dawo..! Su Amina kuwa ba wamda ya kara ganinsu har aka kwana suna Dakin yaya chan suka yada Zangonsu ammh fa duk sun yi sanyi ba ya zeenatu ba Abida gida yayi shuru sai su kadai kuma aranar ma su zafira suka koma harda ya Jamila,sauran baki ma suna ta wucewa tunda an gama Biki sai kuma Taro ya tashi. Su Anty Amarya da wuri suka iso wajen La"asar,suka yada zango Shashen Hajiya suna fadamata karan Dangin mallam tunda uban yaron dan bazanga ne kuma matsayin kawu uban yaron yake ga mallam..! Hajiya Babba ta kudira abu aranta sai dai batace ma kowa komai ba ta bari sai angama Hayaniyar biki sannan zata Furta abunda ta yanke. Sai ranar Lahadi gidan ya watse harta yaran sun koma gidajen auransu,Ranar Hajiya keda shashen Baba mallam bayan sallar isha"i Mallam da Aba sun dawo shashen mallam din kamar yadda suka saba suna Hira. Sai ga Hajiya ta shigo Cikin mayafinta yanzu shashen nata ita kadai ce Hanne ta mata yaji tana tare da su Amima agidan Sa"idu. Lokacin da tayi sallama ta shigo gabadaya suka dago suna amsa mata Mallam ya tareta da Mirmishi yana Fadin"Zainabu abu mai Tagwayen suna..Uwargida sarautar mata..! Yar dariya tayi batace komai ba Aba ne yace"Kuma Amarya ba..! Baba mallam yace"A"a uwargidan dai Ni da zainabu ai mun tsufa kodon baka san tsufan ta..! Aba na Dariya yace"Allah ya kara girma mallam..! Hajiya na zama gefen mallam tace"Ameen kyalesa Sa"idu..Marliya ce Amarya barni in rike Tsufana..! Aba yace"Haka za"ayi Hajiya..An watse taro lfiya yau ina sauri ana jirana na fita ban leka mun gaisa da ban gajiya.ba..Angode Hajiya Allah ya kara girma..! Hajiya tace"Ameen bakomai..Tunda naga ban ganka ba nace uzuri ya rikeka..Ina yaran nan..?Hanne ma tamin yaji wai shashena ba Dadi ba kowa..! Baba mallam yace"Daman ni na sani..Ranar da Abida tatashi..Sa"idu da Balaraba zasu ja Hannatu..! Hajiya tace"ba ruwansu mamarkace da Hamida suka jata..! Mallam na Dariya yace"To shikenan ku kyalesu ke hajiya kiyi zamanki ke kadai tunda kin zama giwar mata ki aurar da naki ki hada har da wanda ba naki ba..Allah ya kara girma da Lafiya Hajiya..! Tana Mirmishi ta amsa Ameen kafin Aba yamike yana fadin"bari na shiga gida..! Hajiya ta kallesa tana Fadin"koma ka zauna Sa"idu mgana nake so muyi..! Ba musu ya koma ya zauna Baba mallan yace"Tunda na ganki daman nasan akwai mgana..! Hajiya tace"Ina Danmallam..? Bai shigo wajenka ba..? Baba mallam yace""Yau kwata kwata ban gansa ba bai shigo anguwan tamu ba..yadai kirani da Safe ya gaisheni..! Aba yace"Yaje gidan gona yau..Tare mukayi La"asar dashi ma..! Hajiya ta fito da wayarta tana Fadin"Bari na kirasa.! Daga Aba har Mallam ba wanda yayi mgana har ta Kira Danmallam bayan sun gaisa tace yazo gida shashen mallam gata nan tana jiransa. Daganan ta datse kiran Mallam ya koma ya kishingida jikin kujera daman da yaga Yadda Hajiya ta shigo yasan yau Rigima take ji kuma ga Duk alamu kawaicinta ne ya kare kan Umar yau zai sha Fada..! Tunda ya Dawo daga gidan gona bai kara Fita ba yana gida,Cikin Dakinsa Sakina kuma tana falo tare dasu Sa"adatu da suka zo mata yini,Sallar mangariba ce ta fitar dashi sai da ya Tsaya yayi sallar isha"i a Hanya sannan ya shigo gidan sai kuma yaga su Sa"adatu basu tafi ba ya farama Sakina Fadan meyasa sukayi Dare Cikin Basar da mganrsa tace"Nan zasu kwana fa..! Kallon bacin rai yayi mata kafin ya kalli Sa"adatun datayi Fiki Fiki da ido yace"Ke mallan yasan kun zo nan zaku kwana..? Kai ta gyada alamun A"a Harara ya sakar mata kafin ya wuce cikin Dakinsa Uzairu yaso ya kira yazo ya kaisu gida sai gobe yaso ya leka chan din sai ga Kiran Hajiya gabansa sai da ya fadi ba kasafai Hajiya ke kiransa ba yasan akwai wani babban Dalili kuma tace afalon Mallam. Ko zama bai yi ba ya fito ransa bace Daman shi da Sakinan haka suka zo kowa na Harkan gabansa ya riga ya Dauke mata Tunda ya Lura bai isa da ita ba,Yayi alkwarin wlh bazai koma da ita ba nan zata zauna bashi da kudi bazai matsa ma kansa ba kuma ta nuna tafi son zaman nan din tabbas zata gane bata da wayau..! Yadda taga ya fito yana cika yana batsewa sai da ta sha jinin jikinta da Sauri tace"Bari na kira Anty ko cikin mazan nan wani yazo ya kaisu..In kuma Idi na nan shikenan..! Ko kallonta bai yi ba ya fice yana cema Sa"adatu"Dauko Hijabanki mu tafi..! Daman ita da Sabeeha ne suna Shirye tunda yayi mgana basu ga ta zama ba suka mike tama kasa bin bayansu Saboda mamaki tabe baki tayi aranta tace sai kuma kayita yi ni dai na Riga da na nazo..! Tsawon mintuna Talatin sannan ya shigo Falon a waje ya ijiye motarsa ya Sauke su Sa"adatu suka nufi Cikin gida yadda ya iske Aba da Mallam ga Hajiya yasa yaji kafafunsa sunyi sanyi Jikinsa ya basa wani Laifi ya aikata Domin Hajiya ko mallam ko Aba suke da Alhakin Zartar da kowani Hukunci..! Gefe ya zauna bayan yayi sallama kansa na kasa ya gaishesu suka amsa mai Cikin Sakewa har mallam na mai Tsiyan"Umaru na kusa daina ganeka..Ka koma sak Balarabe..! Ballatana daman shigar Jallabiyace ajikinsa mai Kalan ruwan madara kansa ba Hula gashin kansa ya bayyana..! Kansa na kasa bai ce komai ba Aba ne yace"Ai yama koma Balaraben Mallam harta Harshensa ya koma nasu..! Mallam na Dariya yace"Na bar ma Kattab.ni nan ya"yana sun isheni..! Hajiya na jinsu batace komai ba Sai da ya Dago yana fadin"Hajiya gani nazo..Allah yasa Lafiya..! Hajiya tace"Eh na ganka..! Mallam mganar tarewar Amina ne dakace nan da wata shekarar ina so ka ijeta gefe..Ba shawara bace mallam Umarni ne amatsayina ta mahaifiyar Danmallam...Zai tafi da matarsa chan inda yake aiki..! Daga Mallam har Aba da Danmallam baki suka saki suna kallon Hajiya wacce Daga yanayin mganarta zakasan ba wasa aciki. Danmallam gabansa ke fadi Hajiya zata Takaitasa ina zai kai wannan yarinyar a yanzu kuma..? Mallam ne ya katseta da Fadin"Meyasa abaya kika yarda da hakan yanzu kuma kika ce ba haka ba..? Kai Tsaye Hajiya tace"Kada ku matsa sai kun ji Dalilina don Allah..Bazan Fadama kowa ba..abaya na yarda da hakan ne saboda ina ganin shine Daidai ammh Shekaranjiya na Fahimci munyi kuskure Mallan..anyi mai Wahalar an Daura aure To me zamu jira..!Biki ai ba Dole bane..Saboda haka in zai koma ya tafi da matarsa shine mganata..! Aba ya bude baki yace"Hajiya hakan kamar ba adalci bane..Shi ai bai yi shirin haka ba..Ta yaya Lokaci daya kuma atakuramai..? Hajiya ta karkace kai tace"Sa"idu ina da Dalilina..Ni ba shiri nake so yayi ba..Ko ya shirya ko bai shirya ba Insha Allahu da Mamah zai tafi in har na isa Dashi..! Tafada tana kokarin mikewa da Sauri Mallam yace"Koma ki zauna Zainabu..Muyi mgana..! Ba musu ta zauna Umar ya kallah yaga kansa na kasa sai zufa yake yi sai ya bashi Tsausayi bai da Hayaniya sam mai Biyayya ne da bin Umarni. Yasan bazai taba musa mata ba har abada. Cikin Salama ya kalli Hajiya na wani Lokaci kafin ya koma ya kalli Danmallan lokaci Daya yana Fadin"Umaru kaji abunda mahaifiyarka tace..Kuma bakace komai ba..!? Sai da ya Hadiye wani miyau mai zafi kafin yace"Mallam bani da tacewa..Duk abunda Hajiya tace shi za"ayi..! Baba mallan yace"Kana da inda zaka ijiyeta in ka tafi da ita ne..?Ko kuwa zamanta achan bata da takardan zama ba Takura bane..? Sai da ya Dade bai yi mgana shi kuma Mallam Dubara yayimai su samu su lallaba Hajiya yasan da matsala rana Tsaka ya tafi da Amina gari ba kusa ba kuma ba kasarsa ba sannan abu Lokaci Daya ba shiri..! Yasa yacemai haka domin ya samu ya kwaci kansa yana so Hajiya tabi komai a sannu sai dai baya so taga kamar yaki Sauraranta da kuma bata goyon baya.. Cikin Dattakonsa yace"Muna Sauraranka..bakace komai ba..! Hajiya tace"Mallam basai mun jirasa ba..Koda bashi da inda zai ijiyeta sai ya tafi da ita ai ba'a Daji yake kwana ba..! Da sauri mallam yace"A"a ba"a haka..Ki bari yayi mgana kada ki manta kasar dayake aiki ba Kasar sa bace nan din dai nan ne Kasarsa..! Dole tayi shuru shi kuwa ya kasa mgana Aba ma haka Domin hajiya Fuska ta Hade ba Fara"a ballatana su ga wani Rahma tana so ne ta Nuna ma Sakina da Amarya Danmallam ya zauna acikinta na wata tara..! Cikin karfin Hali ya fara mgana yana Fadin"In da son samu ne mallam.Hajiya ta bari in na koma sai na Fara cikun cukun sama mata takardan zama a kasar..sannan da wajen zamanta gidan da nike ciki karami ne Ni da Sakina da Sarood ma maallam maneji mukeyi yayi mana kadan gidana na nan yafisa girma Wlh Tallahi na rantse da Allah in na Tafi da ita zamu Takura mallam..Sai dai bazan iya bijirema Umarnin Hajiya ba..Sai ta fara shiri Jafar zai zo ya kaita ayi mata passport saboda Visa Nan da kwana Hudu nake so na koma..! Daga Aba har mallam Tsausayinsa ya Rufesu Umar mutum ne mai Ladabi da Gudun bacin ran iyayensa,Hajiya kuwa bata Damu ba illah kada kai datayi tace"Ko ya ya ne dai tunda da inda zata zauna kamar sauran ka tafi da ita..Ka tafi da ita nace UMAR..! Sai da ya dago kansa jin ta kira sunansa cikin wani yanayi yace"Shikenan Hajiya yadda kikace haka za"ayi..! Sai kuma ya bata Tsausayi ammh in ta Tuna mganar sakina da yan"uwanta sai ranta ya baci so take ta gani ko zata bar mata mijin ne kamar yadda tace. Yasa bata damu ba sai ta saki Fuska kafin tace"Allah yayi maka albarka..! Ya amsa da Ameen cikin sanyinsa. Maallam yayi mirmishin su na manya kafin yace"Hajiya..Hajiya manya..Kiyi hakuri zan yi wata mgana ni ba Umarni zan baki kamar yadda kika bama Umaru ba Alfarma zan tayasa riko tunda shi ba"a bashi Dama ba Sa"idu kuma bazai iya tsalleke mganarki ba shima ammh ni ai ina da Damar mgana ko ba haka ba..? Kai Tsaye tace"Ina jinka..! Maallam ya gyara zama yana Fadin"Daman zan ce ki yi hakuri don Allah duk da bamu san meyasa kika kawo wannan mgnarnan ba..Maimakon ya tafi da ita cikin Takura Zainabu me zai hana ta tare anan gidansa Dake nan Allah barshi in ya koma ya gama Dukkan shirinsa nima ina goyon bayan yazo ya tafi da ita inda yake aiki Tunda an riga an yi mai Wahalar..! Hajiya tayi shuru kafin tayi mgana Mallam ya rigata da fadin"Alfarma mukace..Don Allah ayi hakuri ayi mana..! Yafada cikin sigan lallashi Sai Hajiya tayi Laushi Cikin Dan kauda kai tace"Na amince ammh nima ina da Sharadina..! Mallam yace"Bakomai tunda kin amince shikenan muna sauraranki..! Hajiya tacigaba da fadin"Na amince da mganarka..Sai dai Abu Daya nake so in ya tafi bazai Dauki Lokaci ba .In ya Dade sosai wata Biyar ko Shida..Sannan Mamah zata tare agidansa goben in Allah ya kaimu bana son bata Lokaci..! Mallam yace"Gobe kuma..?anya gaggawa ba aikin shedan bane..? Da sauri tace"Haka kuma wani Jinkirin matsala ne mallam..! Ganin yadda ta Cije ne yasa yace"Ammh kinsan nace sai ta yi Jarabawar gama sakandiri ko..? Hajiya tace"Zata rubuta a Ss2 din ba shikenan ba..! Mallam yace"Shikenan..mungode..! Kafin ya maida kallonsa kan Umar yana fadin"kaji mahaifiyarka..na roketa alfarma kuma tayi mana sannan kaji itama sharadinta ko..? Kansa na kasa yace"Naji mallam..na amince Allah ya shige mana gaba..! Mallam yace"Ameen cikin gidan naka Dakuna nawa ne..? Yace"Uku ne sai falo da Kitchen..! Sakina na cikin Daya da Sarood tazo nace ta bata Daya sai nawa..! Mallam zai yi mgana Hajiya ta Rigasa da Fadin"Zata zauna anaka Dakin..Mganar jere kuma ba bukata Tunda kowaccensu ba ita ta saka kayan gidan ba..Bana kowaccensu bane..Sai dai ka sani zaka samar ma Amina nata Muhallin anan domin ayi mata Jerenta kamar ko wacce ya' acikin gidanan..! Mallam bai ce komai ba sai Danmallam ne yace"Insha Allahu Hajiya..! Ko Aba ya kasa mgana Ganin haka yasa Mallam ya sallami Danmallam yayi musu sallama ya fice Aba ma ya Mike jikinsa sanyaye yayi musu sallama Hajiya ta kallesa tana Fadin"Sa"idu ka sanar ma Balaraba da ita Mamah..Da safe zan shigo insha Allahu gobe agidan mijinta zata kwana..! Bai da tacewa ya amsa mata da toh ya ficen bayan fitansa mallam bai tada mganar ba domin yasan tana da Dalilinta sha"anin mata sai abarsu. Aba haka yajema mamanmu da mganar sai ta sakamai kukan nawa Amina take da hajiya zata mata haka bai Saurareta ba ya Kira Amina ya Fadamata Sakon Hajiya ranar su uku kwana sukayi kuka kamar anyi mutuwa kukan sabo da kuma Rabuwa da Amina. Adaran Mamanmu ta kira Anty Amarya ta fadamata ta Zunduma ashariya tace mamanmu tasan yadda za"ayi Amina ta Bijirema Tarewarta aikuwa da Safe ta kira Amina ta sata adaki tana kuka tana fadin za"a cutar da ita kowace sai da ta gama makaranta aka mata aure banda ita ta Rika Tusa mata mganganu da sai da Amina taga haka din ne ita za"a kwareta an cutar da ita mamanmu tace taje ta samu hajiya ta fashe mata da kuka tace batason tarewan tasan zasu kyaleta Amina ta yarda da hakan domin bata hasko ma kanta ta zama matar aure ba yanzu Haka ta Zurma Hijabi Fuska kozai kozai tasha kuka ko su Hanne basu san ta fita ba Sai dai tana shiga gidan ta baro shashen Mallam kenan dan lungun Dake tsakanin shashensa da na Anty Amarya taji tashin murya sama sama Abunda yasa taja ta Tsaya sunanta taji ana ambata..! "Dayyaba..In har AMINA tatare a matsayin Matar UMAR..na sabama Sakina alkawarinta..Alhalin na mata Rantsuwan in har ina Raye auran Amina da Umar haka zai kare a gantale ba Fa"ida..Ammh yanzu komai zai lalacemin in har yarinyar nan ta tare agidan nan Kashin mu ya gama Bushewa Fitar da ita shine babban aiki..! *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK 1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *🅿️29* "Gaban Amina ya fadi ras jin Sunanta da mganar da ke tashi akanta Labe ba Dabi"anta bane ammh sai ta kasa yin gaba sai ta ja ta tsaya ta kara kasa kunnenta tana sauraran muryan Anty Amarya Tar tana mgana cikin bacin rai da takaici. "In ya kulata din fa Dayyaba..?Kada ki manta Namiji ne ko bai kulata domin yana sonta ba na tabbata zai iya kulata watarana saboda Hajiya da mallam..Ayadda yarinyar nan ke da Tasiri a wajensu matukar tatare agidan Umar Tauraruwar Sakina zai koma baya ne..Ni kuma nayi alkawarin matukar ina Raye Sakina ce kadai Mowa agidan Umar..Kuma sai na tabbatar da na cika mata wannan alkawarin Indai bata Haihu da Umar ba alkawari nayi ba wata macen data isa tazo ta Haihu..Ita kadai ce Tauraruwa kuma Sarauniya..! Amina mamaki ya kara cikata gani take abun kamar amafarki,so take ta Tabbatar da zarginta yasa ta Leka lungun bayanta take hangowa dayake ta Juya bayane tana mgana ta waya,Sai dai ko daga barci tatashi Ko ta baya ko ta gaba zata shaida Duka matan baba mallam ba ta murya ba Daga yanayinta ko kaffara ba zatayi ba Anty Amarya ce sannan gaa ma Muryanta nan na fitowa duk da Bada karfi sossi take mganar ba..! Baki ta rike tana kara mamakinta Sanda taji tana Fadin"Na bar komai a hannunki..Don Allah ki san yadda zaki yi kada Tariyar ta Amina ta tabbata..In har auransu Kuskure ne to kada ma wannan ya zama kuskure Dayyaba..In ya zama Kuskure zamu yi shekaru kafin mu iya gyarashi..! Kiyi gaggawan yin wani abu..! Amina taji kanta ya sara abaya tasan Anty Amarya ta Tsaneta,Ammah bata taba tsammanin Tsanar nata yakai haka ba meyasa bata son ta Tare a gidan ya Danmallam...?Wata zuciya tace Saboda Sakina mana Tunda Diyartace to ammh da wa take waya..?Waye take cema yayi mata kokarin kada Tariyanta ya tabbata..?Ta shiga Rudi Kwakwalwarta ta toshe ta kasa Tunani Abu daya ta kama Anty Amarya bata so ta tare saboda Sakina Abun kamar almara sai taji kuncin Dake zuciyarta ya yaye Daga rashin son Tarewar zuwa son ta tare din ba son ya Danmallam take ba har Abada Aminu ne aranta Sai dai zata taren sai Taga yadda Anty Amaryan da Sakinan zasu yi da ita munafukam banza Har itace zasu ma Burauba to sai ta taren Uban daya Fasa sai ya Hanata.. jidalinta kadai ya ishesu daga Sakinar har Mijin nata basu isheta kallo ba Maimakon ta wuce shashen Hajiya Babba kamar yadda Mamanmu ta Tsara mata sai kawai ta fasa ta kada kai ta juya zuwa Haraban gidan tana Tafe tana auna maganganun Anty Amarya tana Tunanin adanginsu wacece Dayyaba..?Ta gama Tunaninta kaf bata ganota ba to wacece take cewa ta bar komai a hannunta..? Tana wannan Tunanin ta kusa cin karo da Akilu ya fito daga Falon Mallam Sanye da Uniform ajikinsa sai da ta gansa ma ta tuna yau Monday suna da makaranta. Shekeke yake kallonta ganin ta Dauke kai zata wuce yace"Ke Amina bazaki makaranta bane..!? Mamaki ya bata suna da son Girma shi da Zubairu gwara ma Akilun ya basu shekara Daya da wani abu Zubairu fa saurin girma yayi Hajiya tace tsakaninsu ko wata Biyar bai kai ba An riga sakashi makaranta Shiyasa ya Tsere musu da aji Daya ammh sai su rika nuna abu kamar sun wani basu Shekaru barin ma Akilun nan dan Rainin Hammata ne..! Kasa kasa ta juyo tana kallonsa da Kumburarrun idanuwanta kafin kai Tsaye tace"Eh..! Kallonta yake cikin bude ido yace"Eh fa kikace..To saboda mene ko baki da Lafiya ne..? Amina ta gaji da yadda ya wani Tsareta da tambayoyi kamar Ubanta Cikin Kufuluwa tace"Bansani ba..! Baki ya rike yana fadin"Amina ni ma kike cema baki sani ba don Uwarki..?Ni sa"anki ne..? Daman shi abu kadan zagi kamar ba Jinin Mallam ba Amina ta Bude manyan idanuwanta kafin tace"Wlh badai uwata ba..! Ya Zaburo Cikin bacin rai yana Fadin"Sai tawa uwar kenan..! Ta matsa da Sauri tana kunkumi tace"Ai uwa bata fi uwa ba Ehe..! Akilu Duka yake son ya kaimata Bai ji Fitowar Mallam ba sai mganarsa. "kai Akilu kaniyarka nace..! Matar yayan naka zaka Daka dayake baka da kunya ko..? Dukkansu suka juya Baba mallam ne Cikin Akyabbansa da Rawani Tsaye kofar Falonsa yana kallonsu Bai ji Mganarsu ba Fitowarsa kenan Daga Daki yaji Akilu na fadin shi Sa"anta ne yana Lekowa yaga zai kai mata hannu. Akilu na ganin Baba Mallam ya Rankwafa yana fadin"Allah ya kara girma Baba..! Amina kuwa gaisheshi tayi ya amsa yana fadin"Mamana Daga ina da Safan nan..? Amina ta sharara karya da cewa"Nazo gaida Hajiya ne..! Baba maallam ya Murmusa yana kallonta kafim yace"Yar gidan Hajiya..To kin gaishetan ne..? Amina kanta na kasa ta Daga kai Baba mallam Akilu ya kallah yana Fadin"Bana son na kara ganin wannan Sakarcin..In har zaka Daketa ashe zaka sa ka hannu ka Daki Umaru ko..? Akilu ya Dago kansa yana kallon Mallam kafin ya juya yana kallon Amina da kanta ya fashe ta Hura Hanci tana Juya ido shifa tun sanda aka Daura auran Amina da ya Danmallam yake Tsausayamai ko shi da yake yaro daidai da ita bazai iya da Amina ba ballatana ya Danmallam wanda bai da Hayaniya mai sanyi ne shi.Ai Tsab zata jazamai hawan jini in kuma ta Hadu da Sauran ciwo Tsab zata Karisa shi Lokacinsa bai yi ba. Dukar da kansa yayi yana Fadin"Ayi hakuri mallam baza"a kara ba..! Yaji Dadin haka nan da nan ya saki Fuskarsa yana fadin"Ko kai fa..?Allah yayi muku albarka..! Ya amsa da Ameen ya mike yana kallon Amina Data fakaici idon mallam ta Zabgamai gwalo Rai ya bata yana Kada mata ido ita kuma tana wani Juyamai ido. Sai da ya shige Dakinsu sannan Mallam ya kalli Amina yana Fadin"Ina Sa"idu..? Yana gida ko ya fita ne..Au ga motarsa ma ashe yana gida kenan..! Amina tace"Eh yana gida mallam Mallam yace"Yauwa in kin je gida kice mai ina son ganinsa saboda da wuri zan fita! Amina tace"Mallam tafiya zakayi..? Mallam yace"Zaria zani Cikin makarantar ABU akwai wani Taro da aka gayyaceni a Depatment din Islamis Studies shine Uzairu zai kaini yau nakeson mu dawo bana so muyi Dare..! Cikin Sanyinta tace"Allah ya Kiyaye hanya..! Ya amsa da Ameen uwata Daganan tamai sallama ta wuce ya bita da kallon Tsausayi har yau bai daina jin yanayin kamar bai kyauta ma Amina ba,Hajiya tataso da wannan mganar kuma bazai iya musa mata Ba bataba ja da mganarsa ba yasanta sarai tana da Dalili ammh Tunda bata Fadamai ba bazai matsamata sai yaji ba Jiya yayi istikara akan al"amarin kuma yaga Hasken Amina Tatare agidan Umaru zasu rakasu da addu"an zama Lafiya da Zuru"a Dayyaba..! Amina Jikinta a sanyaye ta shiga gida ba Kowa a tsakar gidan Har Falon Aba a kulle alamun bai fito ba Sai ta wuce Dakin Mamanmu. Bata afalo sai ta kutsa kai Uwar Dakinta Kamar yadda ta saba kai Tsaye hankalinta baya tare da ita Shiyasa har bata jin shigowar Amina ba,kalma Daya Amina ta jita Cikin kunnenta. "Kada ki damu bani nace ba..Ki kwantar da Hankali......! "Mamanmu..! Gabanta ya fadi dam jin muryan Amina abayanta Jikinta sai ya fara rawa ckin rawan jiki ta juyo tana kallon Amina Dake kallonta Cikin mamakin ganin yadda take rawan Jiki ga Zufa na keto mata ta saman goshinta. Cikin Fargaba da wani irin Tsoro tace"A..A..mina yaushe kika shigo..? Amina tace"Yanzu na shigo mamanmu..! Tana jin sadda ta Sauke ajiyar zuciya Da sai da ta kalleta,Cikin mamakin ganin yadda tayi Firgai Firgai kamar wacce tayi karya agaban Sarki. Hannun Amina ta riko Daya jike da Zufa ta zaunar da ita gefen gado tana Fadin"Kin gayama Hajiyar abunda nace..? Amina ta samu kanta da kasa Fadama mamanmu komai da Farko ta shigo da Niyyar Fadamata har wayar dataji Anty Amarya nayi ammh yanzu sai ta kasa Haka kurum kamar an Rufe mata baki an sauya mata mgana taji ta tana fadin"Eh na fada mata..! Tana ganin sadda ta washe baki tana Fadin"Yauwa to me tace..? Amina gabanta ne ya fadi bata so zargi ya shiga ranta Kodai kodai mamanmu ce suke mgama da Anty Amarya Da sauri tace A"a mamanmu ba muguwa bace ba mamanmu bace ba ita bace watace ta Dabam ita Tana yin komai Saboda Farincikina ne. Da sauri ta Kauda wannan Tunanin da Fadin"Tace na koma gida gatanan zuwa..! Mamanmu tayi shuru tana Tunanin anya Hajiya zata janye mganar ta kuwa..? Duk da Mallam da Safen nan Amarya tace ya Tarasu ya fada musu Tariyar Amina ayau dinnan Ganin kallon da Amina ke mata yasa Ta fashe da kukan makirci tana Fadin"Amina duk abunda kikaga inayi Saboda ke ne .Ina so na ga Rayuwarki ta Inganta kamar ta kowa Amina..Danmallam bai dace dake ba..Matansa Biyu Amina ina zaki iya Kishi da mata Biyu mace ma irin Sakina..Uwarta Kinsani na sani bata Kaunarmu Amina zasu yi komai Saboda su ga bayanki ni kuma na Shirya Saboda ingata Rayuwarki Sai inda Karfina ya kare,na gwammace na rasa komai Ciki kuwa har da Rabuwa da Aba dinku Saboda ke Amina..! Ran Amina ya cika da Tsausayin Mamanmu aranta take jin mamanmu bazata taba Cutar da su ba,da sauri ta Rike Mamanmu tana fadin"A"a mamanmu kada kice haka fa..Insha Allahu saki bazai kara shiga Tsakaninki da Aba ba..Ki daina Fadar haka don Allah bana jin Dadi..! Mamanmu tana Jan hanci tace"Tun jiya muke tsiya dashi Nidai nace ban yarda ki tare ba sai kin gama makaranta kamar kowacce ya haba..Ai wannan rashin adalci ne shima Maallam din bai Duba ba Gaskiya..Ni bazan yarda ba na Fadamai sai dai koma miye ya faru din..! Amina tayi saurin cewa"A"a Mallam bazai taba kaini inda za"a cutar dani ba..Shi da Hajiya suma bangarena Jikina ne Mamanmu kamar yadda kike sona haka suke kaunata don Allah na Rokeki kada ki saka baki ran Aba ya baci don Allah..! Mamanmu na kara matsan kwallah tace"Ni daman ban ce basa kaunarki ba..Bama ke ba Duka Ya"yanmu damu kanmu suna kaunarmu nace ne su Dubaki don Allah kin yi kankanta da Daukan wannan auran..! Nidai in kina so nayi shuru kada nayi mgana koda Hajiya tazo Aba dinku ya kiraki ko yayi mgana ki Taimakeni ki Fadamai Bakisan wannan Tarewar da auran gabadaya in kuma kika kasa Fada ni zan Tubure nace ban yarda ba Duk da yace in nayi mgana zai yanke igiyar auranmu ban damu ba Zan iya yin komai Saboda ke Amina..! Amina Sai kuka itama jin kalaman mamanmu Cikin kuka tace"Naji zan fada..Don Allah mamanmu kada kiyi mgana Ran Aba ya baci..na rasa yaya alokacin da bansan Dadinta awajena ba..Kema kuma bana so na rasaki..In kika tafi kikabar gidam nan ina zamu..?Wazai Rikemu..!? Ni da Hamida zamu lalace mamanmu..! Da Sauri ta Rumgume Amina Tana Mirmishin nasara kafin cikim karyewan murya take fadin"Bana so a Gurgunta miki Rayuwa ne Amina..! Haka take fada tana jan majina karshenta dai Amina ce ta share hawayenta tana Cigaba da bama Mamanmu baki har tayi shuru kafin ta kalleta tana Fadin"Tashi kije Dakin ku..Abun karyawanku na Kitchen bari naje Nagani ko Jawad yagama Shirin Tafiya makaranta..! Daga haka ta mike ta fice tana Dariyan Nasara duk karya ta Fadama Amina tun DAran jiya datayi mganar da Aba bata kara cemai komai ba Shima bai ce mata ba ita shegiya ce da zata bata goma ko Daya bata gyaru ba Saboda Amina ta Samu Sakin Farko ta Tabbata Sa"idu zai iya Sakinta Saboda mallam da Hajiya duk da ta samo kansa din ammh gwara ta Kiyaye in har Makircinta bai yi ba zatace ma Madina ta Kira malaminsu arufe bakin Hajiya da mallam din kan mganar Tarewar kowa ya Huta..! Amina ma Dakinsu ta koma ta Iske Hamida da Hanne kozai kozAi ba Fara"a kallonsu tayi kafin tace"Miye haka kowacce ido kamar Nama..kunyi wani Figai figai kamar Kajin da aka Tsoma acikin Ruwan zafi..!? Yake Kadai Hanne tayi mata batayi mgana ba Amina ta Cire Hijabin Jikinta tana Fadin"Mamanmu tace abun karyawan mu na Kitchen Hamida tashi ki Dauko mana..! Hanne ta Dago daga kwancen Datake tana kallon Amina cikin mamakin kamar ba itace ta kwana kuka ba. Cikin Dashewar murya tace"An fasa kai ki gidan ya danmallam din ne..? Amina tace"A"a me kika gani..? Hanne tace"Naga kin saki jikin ki ne..! Amina tayi wani Mirmishi, Mirmisshin da ya bama su Hamida mamaki Kafin tace"Ya zan yi Hanne..? In ba saki Jikina ba za"a fasa ne..? Daga auran har Komai da komai da suka Faru bani na Tsarama kaina ba Allah ne..bakomai shima wannan din kaddartace..Abu Daya ne zai dameni zan Rabu daku..Bazan iya Rayuwa baku ba zamu daina zuwa makaranta tare zamu daina kwana tare zamu daina Fada zamu daina cin abinci tare zamu daina zuwa Hadda Tare zan koma ni kadai..Wlh in na Tuna haka sai naji kamar zan yi hauka..! Kawai sai ta saka musu kuka bata so ta Fadamusu abunda taji haka kurum Taji bazata iya fadama kowa ba,suma kansu Abunda ke sakasu kuka kenan suka mike dukkansu suka Rumgumota suna ta kuka suma kukan kewarta suke Amina Bangaran jikinsu ne in Tayi nisa da su zasu shiga uku ne. Suna wannan kukan sukaji Sallamar Hajiya shiyasa suka Tagaita Falon Aba mamanmu ta shigar da ita sun Dade suna mgana kafin su fito Aba fita yayi yayinda Hajiya ta kalli Mamanmu tana Fadin"Balaraba ina yaran nan suke ne..? Daman Tun da tazo tana Dakinta Hankalinta yaki kwanciya balle dataga sun dade suna mgana da Aba su ka kuma gama ya fita bai ce mata komai ita fatan ta yasa Hajiya tana Rusa mganar tariyan ne Shiyasa cikin Damuwa tace"Suna ciki Hajiya..Karki so ki ga yadda suka Tada Hankalinsu hamida da hanne..! Hajiya tayi Dariyansu na manya ta wuce tana Fadin"Sakarci ne..ai ba Mutuwa zatayi ba..banda abunsu ai suna Tare da ita koda yaushe tunda tana kusa..! Mamanmu ta Daskare tana Bin bayan Hajiya da kallo me take nufi..,? Kasa shi ga Dakin tayi sai da taji Hajiya na kiranta sannan ta shiga Dakin taga Amina zaune gaban Hajiya Hamida da Hanne na gefe suna Sharan kwallah. Cikin Dariya tace"Tayani Lallashin ya"yan nan naki balaraba sun tasani suna min kuka..! Mamanmu tace"Nima Hajiya da zan samu mai lallashina ina so..Kukan ma ai na yi shi Hajiya..! Hajiya tace"Balaraba hakuri zaku yi nasan zaku ji mganar Daga sama ko..?to me zamu jira..?,an gama mai Wahalar zaman me zatayi... Zaman bai da Fa"ida Tunda yana da Gida anan sai ta tare abunta sai Hankalin mu yafi kwanciya..! Mamanmu ta ji kamar Kafafunta sun kasa Daukanta Dakyar tace"Hajiya Karatun Amina fa..? Hajiya tace"zata cigaba da zuwa Duka makarantrta..Zata dai zana Jarabwar Fita a wannan shekaran tare dasu Akilu Saboda yadda muke so in Danmallam ya koma ba Dadewa zai zo ya tafi da ita..! Mamanmu ta zaro ido tana fadin"Madina Hajiya..? mirmishi tayi kafin tace"Insha Allahu..! Ai sai mamanmu ta koma ta zauna akasa Dabas tana fadin"Allah Sarki Amina..! Sai ta fara jan Hanci Hajiya na Dariya ta Mike tana Fadin"Haba balaraba da girmanki keda yara zasu yi kiyi musi Fada..? Bafa komai tana kusa kafin su tafi..Hsmida da hanne kuyi hakuri kubar kuka In Mijinta ya koma zaku rika zuwa ku tayata zama makaranta kuma Dagachan zasu rika zuwa kuma Tare baku Rabun baa Tukunnah..! Hanne ta washe baki kafin tace"Da Gaske Kike Hajiya..!? Kai ta gyada mata tana Fadin"Har da mallam ma munyi mganar.. bai dai ce komai bane.. dukkansu sai Dariya Hajiya ta kalli Amina tana Fadin"Mamah kin amince zaki Tare agidan Mijinki ko.? Amina kanta na kasa ta Daga kanta mamanmu har tana Murnan Amina zata ce bataso sai tasha mamakinta Hajiya taji Dadi ta Dafa kanta tana Saka mata albarka kafin tace ma su hanne"Ku taimaka ku hadama Amina kayanta Waje daya tun daga Littafan makarantar ta da komai har kayan sawanta nan da Sati daya mallam zai mata Sabbin dinkuna. Ta Tsefe kanta Ku rakatanan nan gidan Magajiya ayi mata Kitso mai kyau da kunshi duka suna yi agidan kun ji ko..! Da toh suka amsa mata Kafin ta kalli mamanmu Dake Zufa tace"Balaraba zan wuce..Sai zuwa anjuma inaga Sai Dare zaku kaita..! Mamanmu ta Mike dakyar tana Fadin"To Hajiya Allah yasa hakan yafi zama Alheri bari ni na Tsefe ma ta kanta na wanke mata su hanne sai su hada kayan..! Hajiya tayi Dariya kafin tace"Ameen ai Amina Diyarkice Balaraba nasan zaki mata komai..! Daga haka ta fice mamanmu ta Rakata bata Dawo Cikin gidan ba Daga Haraban ta Tsaya bayan Tafiyar Hajiya ta Danna ma Madina kira. Kamar tana jiranta ta Daga kiran tana Fadin""Ya ya an dace..? Mamanmu tace"Ba Nasara madina..! Dagachan bangaran Anty Amarya ta Laila ashar kafin tace"Basu isa ba..Karyansu..! Mamanmu tace"ki kira mallam..Shawara ta a Danne bakinsu ammh in ba Haka ba kwabar mu na Shirin yin ruwa..Yanzu Hajiya ta bar gidan nan..! Nan ta shiga bata Labarin duk abunda ya Faru. Anty Amarya tace"Wannan Shegiyar yarinya makira ce Dayyaba..Zata zame mana ciwon ido..! Mamanmu tace"Uhm..Nima ina ta mamakinta sai mun gama mgana ta yarda sai daga baya ta sauya..! Amarya tace"Tsaya Tsaya..Baki Fahimci wani abu ba..Kodai ta ganoki ne..? Mamanmu tace"Kai a"a gaskiya bana jin haka..Sai dai tsoron Aba dinsu da kuma kunyar su Hajiya..! Anty Amarya tace"bari na Kira mallam..! Daga haka ta katse kiran Tana kokarin kiran mallam din ne Sakina ta Shigo Cikin Bedroom din nata a yarkace agyale a Hannu Cikin Numfashi take Fadin"Anty kin ji abunda naji..Wai yarinyar nan zata tare yau.Yanzu Umar ke fadamin Anty har yana cemin zata zauna adakinsa kinji fa..! Tafada cikin wani yanayi Anty Amarya sai ta fasa abunda tayi niyya ta maida wayarta saman madubi ta kama Sakina ta Zaunar gefen gadonta tana fadin"Kwantar da Hankalinki..muma da Safe mallam din ke Fadamana ba Kulle kullen kowa bane sai Hajiya babba..matar nan ta Zame min ciwon ido wlh..! Sai Sakina ta saka kuka tana Fadin"Ni dai wlh Anty in dai yarinyar nan ta tare agidanan bazan koma ba..ai wannan ci baya ne..Taya zan hada miji da Amina haba Anty..! Cikin sigar Lallashi take fadin"Haba Sakina bani nace kiyi hakuri ba..Bazata tare ba na Fadamiki..! Sakina tace"Haba Anty..Kince auran haka zai kare gashi kuma ana Fadin zan zauna waje daya da ita..! Amatsayin kishiyoyi Haba don Allah wannan ai Tsabar ci baya ne..! Anty Amarya ranta ya baci ta mike tana Fadin"To shikenan kiyi yarda kika ga dama Tunda baki ga Kokarin da nike yi akanki ba..,! Daga haka ta Dauki wayar ta ta fice Daga Dakin Sakina tatashi ta Fita tana kuka har Falo tana Fadin"Anty Wlh in har yarinyar nan ta tare agidan nan bazan zauna ba sai dai na koma Dutse..! Anty Amarya ta juyo tana fadin"In ma ta taren sai me..? Ba Madina zaku koma ba.zan san abunda zan yi in kuka koma sai dai taji Shuru daga ita har iyayen nasa..! Sakina ta Rushe da kuka ta fadi kasan Cafet tana fadin"Anty Umar yayi Rantsuwan bazai koma Dani Madina ba..Nan zamu zauna har sai yaje ya Dawo..! Anty ta Zaro ido tana fadin"Mun shiga uku..! Sai ta koma ta zauna tana fadin"Meya faru yace haka..? Sakina tace"Saboda rigiman da mukayi na zuwa wannan bikin Tunda yace bazani ba na matsa shikenan ashe yayi bakam da niyyar in nazo bazam koma ba..,! Anty Amarya ta yi Tsaki kafin tace"Ai Sakarcim ki ne Sakina..Baki yi Shawara Dani ba kika aiwatar da abunda kikaga dama..Kin kuma sani Tunda ya Rantse bazai tafi dake ba din..Kin manta kun taba yin haka Farkon Tafiyarku..! Sakina ta kara Fashewa da kuka ta Tuna Lokacin farkon auran su ne da ya tafi da ita Hajiya bata da lafiya zai zo Dubata tace sai tazo yace in tazo nan zai barta sai ya sake Dawowa ta zata Fade yake sai da suka zo ya tafi ya barta Sai da tayi wata Takwas sannan yazo suka koma shima sai da Mallam ya kirasa yamai fada bai da Saurin Fushi ammh in ya Zuciya Bashi da kyau..! Tana ta kuka Anty Amarya ta mata bazan karshenta ma tashi tayi ta shige Dakinta ta Kulle ta barta anan  Mallam tayi ta kira bai Dauki wayarsa ba kila yana cikin wani aiki ne ranta ya baci ga kukan sakina gashi kuma ta raasa mafita yasa ta fita Falo tana Fadin"Sakina wlh in baki min shuru ba sai naci Ubanki..! Tsit Sakina tayi tasan ran Anty ya baci Cikin Fusata tace"Duk uban wa yaja in bake ba..Ki rika yin abu gaban kanki ba Shawara sai ki koma Chan Dutse ni bazaki zauna anan ki kasheni ba ina ji da kaina nima..! Kara jan Tsaki tayi tana juyawa ta koma Ciki Sakina ta rakata da Fadin"kiyi hakuri Anty..! Umar baisan ta fito ba yana gama Fada mata mganar Tarewan Amina ta Zaro mayafi Ko kudi bata Dauko ba Allah yasa Pos dinta akwai yan Chaji da mai adaidaita ya mata Tijara. *Ina cigiyar wani Tsohon Littafi na MAMAN KAUSAR mai suna WATA SHARI"AR wanda ya samu Comp Doc dinsa yamin mgana ta wannan lambar 09069067488* *Janafty* *TA FITA ZAKKA..!* _(Aminene)_ *BOOK1* *Wattpad:JamilaUmar351* *Mallakar:Janafty❤️* *Kar'shen Littafi na D'aya* Dole Mamanmu ta cire komai aranta kada a ganota bayan fitan Hajiya ita tayi ma Amina Tsifa ta wanke mata kanta tas,su hamida kuma suka Hada ma Amina kayanta waje daya kamar yadda Hajiya tace suna yi suna hawaye domin sun san zasu yi kewar Amina kewa mai yawa,Wadanda ba"a wanke ba Mamanmu tace su bar mata zata wanke kafin su dawo daga gidan Kitso,Su ukun suka tafi Raka Amina wacce suka kasa gane yanayin data ke Ciki Fuskarta ba fara"a kuma ba Damuwa sosai Kadahan kadahan Bayan fitansu Mamanmu ta kwaso sauran kayan Amina ta wanke ta shanya bata so tayi wani abunda za"a Fahimci Ainihin Fuskarta,Bayan fitansu Ta kira Jafar awaya tana kuka tana Fadamai yayi ma Aba mgana a bari Amina ta karisa karatunta ammh Jafar ya nuna mata mganar Baba mallam ce Aba ya kirasa ya fadamai shima ya yarda da hakan Amina ai Jidalinta sai ita barinta ma ai wani Damuwar ne duk da yaga ta Rage wani abun ammh gara a kaita gidan Mijinta kila in tana da Rabon hankali Tayi,ganin ba Nasara yasa ta maida akalan Kiranta kan goggo Husai itama dai da Farko taso ta bi bayan mamanmu sai da ta Kira Aba sukayi mgana ya Fadamata komai sannan ta Fahimta ta Kira mamanmu tana kara bata Hakuri ita a tunaninta tana Tsausayin Amine ne batasan so take a hana Tarewar Amina ayah din nan ba sai dai Bakin Alkalami ya riga ya bushe..! Duka yaran nan kaf sai da ta Kirasu tana kuka tana fada musu Rayuwar Amina na cikin wani hali su Jadwa sun yi Na"am da mganar mamanmu Amina tayi kankanta ba zata iya zaman kishi da Sakina ba sai dai ya zasu yi? su basu isa suce wani abu ba..Mganar Hajiya da Baba mallam ko Aba bai tsallaketa ba, ballatana su da Fatan Alheri kawai suka bi kanwar tasu Domin awannan gabar basu da abunda zasu iya yi. Ganin duka ba sa"a sai ta Kira Kanin Baban Aba na gusai. baba Salihu tana kuka take fadamai abunda ke Faruwa shima Hakurin ya bata ya nuna mata Amina ta isa aure har ta gota sannan gatan da Mallam yayi ma Sa"idu ko su Dangin ubansa basu yi masa ba..Saboda haka Sa"idu Mai yima mallam Biyayyah ne su kuma bazasu taba Katsaladan kan abunda ya Shafe su ba Tun Aminu nada rai Mallam ke amsa sunan Uba ga Sa"idu ballatana da kasa ta shafe idonsa ko su yan"uwansa Suna Alfahari da Mallam bama Sa"idu kadai ba Saboda haka tayi hakuri ai mallam din ya Kirasa sun yi mgana kuma yayi Na"am da mganar tunda an Daura auran tarewar shine mafi Alheri. Mamanmu ta rasa mafita ko"ina taje ba Sa"a sai alokacin ta kara yardan ma kanta Mallam Ya riga yayi nisa mai Tardosa sai ya Shirya. Shiyasa ta yanke shawaran kiran Anty Amarya ta fadamata kokarin da tayi ba asamu mafita da sannan taji ya sukayi da mallam din kuma bata Dauki waya ba,Ita kadai agida abun Duniya duk ya Isheta ko girki ta kasa yi Jawad ne kadai yaje makaranta Hamida da Amina basu je ba da Hanne suna chan gidan Kitso Mamanmu kanta Sara mata yake yi domin har ta fara Hango yadda abubuwa zasu lalace da yadda Madina zata Dauki lamarin ta santa Sarai taki Daukan wayanta ne zatace Batayi mata kokari ba,Data san yadda ta kasa zama shiga nan fitan nan da tayi mata uzuri ta tabbata in ta Zake da yawa auran nata daya Rage igiya Biyu Sa"idu zai iya Tsinketa ta shiga uku..! *****" Bayan wani Lokaci sai ga Anty Amarya ta sake fitowa daga cikin Dakinta Fuskar nan duk a jagule Sakina ta kallah wacce ke kuka tana yi tana faman toshe bakinta kada kukan ya fito ammh kallo daya zakayi mata ka fahimci yadda ta Yarkace lokaci daya. Wani katon tsaki ta kara saki tana kallon sakina Lokaci daya tana Fadin"Kukan me zaki dameni dashi Sakina..?Yau duk kwabewar komai ta Sanadinki ne sanadin shegen kafiyanki da Taurin kanki.! Ayadda take mgana daga gani ranta ya gama baci Sakina ta gama Saki da lamarin tasan bata da wata mafita sai Anty Amarya yasa cikin karyewar murya tace"Kiyi hakuri Anty..Wlh ban zata abubuwa zasu lalace mana haka ba..! Anty Amarya tayi kwafa tana Sake Duba wayarta kafin ta fara Zagaye Falon Tana sakin tsaki ita kadai Lokaci bayan Lokaci tana kara Duba wayarta kafin ta kalli Sakina tana Fadin"Kin isheni da wannan koke koken naki..in har bazaki yi min shuru naji da abu daya ba to.. ki tashi ki koma inda kika fito ko kuma ki hau Mota ki koma Dutse Bazan iya da iskancinki ba..! Sakina ta kalli yadda idanuwan Anty Amarya suka Yi jajir tsabar tashin Hankali sai jikinta ya karayin sanyi Domin tasan duk abunda take yi saboda ita take yi da sauri ta share Hawayenta ta na kara sunkuyar da kanta cikin muryan wacce tasha kuka tace"Na bari Anty nabi Allah na Bki.Bana so na koma gidan Umar..Bazan iya hada zama da wannan yarinyar ba..Sannan in na Koma Dutse wajen wa zan zauna..?,Sannan so kike makiya su yi mana Dariya Anty..? Anty Amarya ta harareta kafin tace"Sun dade basu yi ba koma me ya faru ai ke kikaja..Sakina bakya jin shawara..Sannan kin raina kokarina a kanki to zan tsame hannuna ga ki ga Umar din sai naga abunda za"a fasa din..! Da sauri Sakina tace"Don Allah ki yafemin Anty bazam kara ba..! Anty Amarya ta kalleta tana Saussauta bacin ranta domin ji take kamar ta kamata tayi ta duka ko zata wuce haushinta Sakina batajin mgana ta lalata komai Ayadda tasan Halin Mallam bazai yi mgana ya Saba ba..Ta bangaran hajiya ne taso suyi Amfani da Amina su samu nasara ita din ma Shegiyar yarinyar ta zame musu ciwon ido Shawaran Dayyaba tabi ta kira mallam domin ya Rufemata bakinsu Sai dai bai Dauki kiranta ba kuma bai kira ba ranta yana bace ne sannan ga Sakina da mganganunta na banza yadda kanta ke sarawa ji take kamar tayi ta kurma Ihu lokaci Daya abubuwa sun lalace mata kuma ta kasa samun Mafita..! Sakina ce ta katseta da Fadin"Kin ji Anty Ki yi hakuri don Allah..! Sai alokacin ta sauke numfashi Tana Fadin"Naji zan hakura..Ammh da sharadin bazaki sake aikata wani abu ba sai kin nemi shawarata..Sannan ki Rage kafiya da Taurin kai in kikace haka zaki cigaba da yi Bazaki taba cimma nasara ba sakina komai da kika gani dan taku ne..Sannan sannu sannu ai kwana nesa ne watarana Burin mu zai cika..! Kai ta gyada mata tana Fadin"Insha Allahu Anty yanzu menene mafita..? Ta bude baki ta bata amsa kenan wayarta ta Dauki kara tana Dubawa taga Mallam ne ai hannu kawai ta Dagama Sakina ta wuce Dakinta tana amsa wayar. Cikin Damuwa ta fara mgana daidai Sanda ta shigo Cikin Dakinta"Mallam ina ta kiranka baka Dauka ba..! Hankalina ya tashi ina cikin matsala..! Dagachan bangaran wata kakkausan murya wacce ba Tausasawa acikinta Sake take kawai irin na manyan mutanen masu katuwar murya mara Tsari mai ban tsoro naji yace"Hajiya Madina ina kan wani aiki ne..Lafiya akwai damuwa ne..? Cikin sauri tace"Sosai ma mallam..Kan shegiyar yarinyar nan ne da ka taba yima Dayyaba aiki ya fada kanta..wacce na Fadamaka Malam ya aura ma Umar ita..To itace zencen tarewarta ya taso yau yau Mallam ka taimakamin nayi iya bakin kokarina ta bangarena ba Nasara. ! Wata dariya ya saki mai Ban tsoro kafin yace"Ai daman na Fada muku..Tunda ta Tsallako aikin da ba nata ba a kawar da ita shine masalaha..Nasani ne watan watarana sai ta shigo Tsarinmu Tsundum..! Anty amarya tace"Yanzu duk ba wannan ba..Yanzu bakin mallam da Hajiya zaka Rufemin in mganar tarewar ta sha ruwa sai muyi mganar Turata inda uwarta taje mallam ko Dayyaba ta amince ko bata Amince ba..Bana ragama duk wanda yace zai shiga Tsakanina da Burina..! Dariyan ya kara saki kafin yace"ki bani minti goma zan kara kiranki..! Kit ya Datse kiran sai ta koma ta zauna gefen gado tana share zufan goshinta Dayyaba ta cuceta tun farko taso ta bari su kawar da Amina tace a kyaleta ita din bazata zame musu matsala ba sai gashi yanzu Ta zame mata ciwon ido bata fatan Amina ta Tare agidan Umar tana hango Tarin abubuwan da bazata so faruwarsu ba nan gaba.. Abunda bata sani ba Bakin Alkalami ya Riga ya bushe..Da sun sani..Dama ace suna Tara sani da Allah da basu bar Amina ba..Domin watarana itace Sillar bankadaran sirrikansu..! Itace kuma zata Shiga Tsakaninsu da cikar Duka Burikansu..! Tana zaune tana faman Tunanin mafita Minti goma na cika Mallam ya Sake kiranta Hannunta na rawa ta Dauka bai bari ma ta fara mgana ba ya Fara mgana cikin Sauri da karfi yana Fadin"Kin makara Madina..Kin manta na Fadamiki Mallam yunusa yafi karfinki..?Na fada miki bayan ke acikin matansa akwai wacce taso ta mallakesa bai samu ba itama an fadamata Allah yana Tsare bawansa Mijinku yana da Tsari mutum ne mai Ibada da addini aljanun mu bazasu iya Tunkaransa ba..! Da sauri Anty Amarya ta katseshi da Fadib"Hajiya fa..? Sai da yayi jim kafin yace"Bazan iya Tankwara zuciyarta Lokaci daya ba Madina itama bazaune take ba..Sannan Lokaci ya kure miki..Nagani Dole yarinyar ta tare..Na hango wani Duhu sannan naga Haske guda Biyu na wata da kuma kananun Taurari Madina sai dai acikin hasken Duhu ya mamaye ganina ban fahimci wani abu ba..! Anty Amarya taji kamar tayi Fitsari Saboda Tsoro Cikin rawan murya tace"Menene Mafita mallam kaina ya Kulle..? Mallam yace"Muna kan Bincikenmu ne Madina..ammh Zata tare tabbas..Sai dai zan kara Lalata Tunanin yarinyar wajen kara yawan Tsiwarta da rashin Da"a ga shi Mijin..Sannan na saka tashin Hankalin a Tsakaninsu yadda zaman bazai Dade ba zai lalace na fada miki Aiki Daya muka taba yi kan Shi yaron ya kamasa yanzu haka aljanunmu baza su iya Tunkararsa ba,Yana da Tsari sannan iyayansa Biyu suna Tsaye a kansa ne Shiyasa aikin namu zak fi karfi kan yarinya da dama Tun farko mun samu nasara akanta Sarrafa Tunaninta bazai mana Wahala ba..Kada ki yi wani yunkuri..Zata tare tabbas in kika hana Faruwar haka Madina wani kullin zai Lalace kuma Faruwar haka tamkar Rugujewar Duka aikin ki ne ki kiyaye..! Kit Kawai taji Anty Amarya Cikinta taji yana Faman juya mata Innalillahi kawai take fadi afili in Har asirin data Binne ya bayyana ta shiga uku ta Lalace Cikinta ne yayi wani yi kara Kuuuu..Data saki waya ma bata sani ba,Ta kwashi gudu zuwa Tiolet kafin ya Zubo mata tana hawa kan sit din Kikaji Zuu..Zuuu..Sai kuma zufa ta koma ta jingina da bango tana ajiyar zuciya Yadda take jin kanta kamar zai Rabe gida Biyu..! Mafita take nema ido Rufe kafin komai ya kwace mata ta Dade kan masai din tana zawo zawon tsoro da Firgita kafin ta Dauraye jikinta ta fito Tana ji ana kiran wayarta sai da ta Fito ta Duba Dayyaba ce Tsaki taja Domin duk itace silar lalacewar komai nata in da ta amince sun Kauda Amina da yanzu wata mganar ake yi ba wannan ba,Ta fara Tunanin ko Dayyaba ta na so ta juya mata baya ne saboda ita ta samu cikar nata Burin eh mana ko bata samu duka ta fara Hawa matakin nasara Yaya ta bar gidan Duniya ya'yanta sun dawo karkashinta sa"idu yanzu nata ne ita kadai ai kadan ya rage mata ta cika Burinta ita kuma yanzu abubuwa sun fara Lalace mata daga wannan sai wannan kuma duk sanadin wannan shegiyar yarinyar da shiyasa bata taba kaunarta ba..! Gefen gadon ta koma ta zauna tayi Tagumi hannu Biyu tana Tunanin mafita ta Dauki tsawon Lokaci ahaka batasan sakina ta shigo ba sai da taji Muryanta saman kanta sannan ta Dawo Hayyacinta yadda idanuwanta suka Fada ne Lokaci Daya yasa Jikin Sakina ya kara yin sanyi cikin Damuwa tace"Anty na jiki shuru ne tun dazu shiyasa na shigo naga ko Lafiya..Na sameki cikin Tunani ina ta mgana baki jini ba..!? Anty Amarya ta kasa mgana Sakina ta Kurama ido na wani Lokaci kafin tayi Zaraf ta mike tana Fadin"Ke wani ya ganki sanda zaki shigo..? Da sauri ta Girgizakai ajiyar rai ta Sauke kafin tace"Tashi tashi maza mu tafi..! Sakina tace"ina kenan Anty..? Tana kokarin Daukan Hijabinta Cikin Wardrope dinta tace"Gidanki zan maidake sakina..Dole zaki koma Domin chan din ne ya Dace Dake..! Sakina ta saki baki kafin tace"Yanzu sai naje nayi zaman kishi da wannan yarinyar..?Haba Anty kin manta kin Fadamin hakan bazai faru ba indai kina Numfashi..! Anty Amarya da ranta ya gama baci ta Juyo tana Fadin"Ke sakina kada ki koma don Ubanki..In kin koma kinci Ubanki nace..to gani da Numfashina Amina zata tare agidan da na gama Tsara ke kadai zaki dinga juyi acikinsa..Wannan karon ba kamar Zuwan wannan balarabiyar nan bane..Wannan mganar ta girmama Hajiya da Mallam ne kuma kinsan babu mai ja da su..ki zauna kina ji kima gani Amina zata tare ta samu Ciki ta Haihu ni dake mun zama yan kallo,ke ba auran ba,ba kuma miji ba Sannan ni kuma kin jamin raini sannan kin saka mafarkina na mallakan gidanan ya tashi a banza Sakina Kada kije ki koma ki zauna ni Dake mu Taru mu rushe gabadaya..! Ta karishe Fada cikin wani yanayi Lokaci Daya tana komawa ta zauna gefen gado tana jijjiga kafa kamar ta Rufe Sakina da Duka haka take ji. Sakina ta fashe da kuka kishi da Bakincikinta sun cika mata Kirji Cikin Wani yanayi tace"Haba Anty wannan yarinyar fa..?Wlh bazan iya jure zaman waje daya da ita ba..Dama zaki rokar min Umar ne ya amimce ya koma da ni Madina shikenan sai na Biki mu tafi..! Anty Amarya ta mata kallon Tara saura kwata kafin ta mike tana Fadin"Kinga in zaki tafi ki zo mu tafi..In bazaki jeba shikenan mu koma mu nade hannu mu zama yan kallo..Wahalarmu tatashi a Tutar babu..! Anty bata kara bi ta kanta ba ta Fice Daga Dakin kada ta cigaba da zama Sakina ta cikamata ido ta kaimata Duka Tana zaune afalo tana jiran taga Sakina zata fito ko kuwa kasa Zata watsa mata a ido sai gata ta fito Idanuwanan sun kumbura saboda kuka Anty Amarya tayi Mirmishin Nasara kafin ta Mike tana Fadin"Muje na maidake..Karaya ba Halin Madina bane..Ita Nasara insha Allahu Tamu ce Sakina..Kafin su kaita zasu tarar dake agidan Mijinki..Ita ai aro muka bata nan da wani Lokaci zata zama tarihi..! Sakina sai taji ta samu natsuwa Daki Anty Amarya ta koma ta Dauko wayarta ta Karamar jakarta ta saka Sakina gaba suka fice daga gidan ba wanda ya gansu,Mallam kuma shashensa a kulle kila ya fita adaidaita suka samu suka hau zuwa kofar arewa..! Buga get din sukayi megadi yazo ya Bude musu bayan yaga sune,Sakina na kan gaba Anty na bayanta suka Shiga Falon gidan da sallama ba kowa Tsit kamar ba Mutum acikin gidan Anty Amarya tabi Falon da kallo kafin ta kalli Sakina tace"Naji gidan tsit..Ko ya fita ne..? Sakina ta zare mayafin Jikinta tana Fadin"Bana jin ya fita..ga motarsa chan a haraban gida..a dakinsa na barosa koda na fito Dazun..! Anty Amarya ta samu Daya Daga Cikin kujerun falon ta zauna tana Fadin"Shiga kicemai nazo ina son mgana dashi..! Sakina ba Musu ta Nufi Dakinsa Knooking ta farayi taji gyaran Muryansa kafin ta Tura kai ta shiga Dakin komai nashi Baki da Fari ne makeken gado da wardrope sai Cafet sai Madubi,Yana kwance kan gado yayi kwwnciyar Ringigine yana kallon p.o.p din Rufin Dakin yayi matashi da Hannayensa bai da Riga Dogon Wando ne baki ajikinsa Gabadaya Kirjinsa yana waje inda Gashi suka kwanta Luf. Idanuwansa suna Rufene kamar mai barci sanda ta shigo Dakin yana jinta ammh bai Motsa ba saboda Halin Dayake ciki baya Bukatar hayaniyar kowa akansa yana jin sanda ta Fita bai yi kokarin hanata ba saboda ba shi da kwarin gwiwan Daukan kokenta na banza shi kanshi inda zai yi kukan Dayaji Dadi Ransa gabadaya a jagule yake tsammanin abunda bakayi Tsammani ba baida Dadi sam. Gefensa ta zauna tana Fadin"Habibi Anty na Falo tana son mgana Dakai..! Kamar bazai yi mgana ba ta kafeshi da ido tana kallomsa yadda taga kamar yadan Fada mata a fuskarsa da Wuyansa. Ji kawai tayi yace"Karata kika mata sakina..? Yafada cikin Sanyim muryansa kamar koyaushe,Da sauri tace"A..a..! "A"a ko Eh..! Ya fada Lokaci Daya yana Bude Idanuwansa kuma ya tashi Zaune yana kallonta sai taji ta Daburce ta kasa kallonsa idonta na kasa tana wasa da Zoben hannunta. Bai kara ce mata komai ba ya Zuro Santala santalan kafafunsa suka nutse saman Italian Cafet din Dake Dakin ya Mike Tsaye yana Fadin"Kije gani nan zuwa..! Ba Musu ta mike ta fice Daman ta Kosa ta Fita Kwarjininsa yafi na koyaushe bata so ya Tsareta da wannan kallonsa da yake sakawa ka kasamai gaddama ko Karya. Wajen Anty Amarya ta koma tana Fadin"Gashi nan zuwa Anty Don Allah kiyimai mganar tafiyata..! Anty zatayi mgana kenan Kamshin Turaransa ya sanar da su zuwansa Falon suka Dago suna kallonsa atare Jallabiya ya sanyo saman wando jikinsa Fara Tas da ita,Anty Amarya ta kalli Sakina tana fadin"Koma kasa ki zauna mara kunya..! Ba musu ta sulale a kasa shima saman Cafet din ya zauna yana gaisheta ta amsa tana kallonsa ganin yadda yanayinsa yayi wani iri duk da daman bamai gane yanayinsa koda yaushe haka yake. Kansa na kasa Anty Amarya tace"Ina gida dazu sai ga Sakina tazomin da kuka..ni Hankalima ma har ya tashi na Zata matsala kuka samu..Sai Daga baya take Fadamin wai ka Fadamata Amina Zata tare yau shine tazomin tana min kuka kaji wani Sakarci Umar..? Kansa na kasa shidai bai ce mata komai ba Sakina ce ta Dago tana kallonta ta Rakata da Harara kafin ta Dauke kanta ta maida kan Umar tana Fadin"Tana fadamin haka ban yi mata da wasa ba nayi mata Fata Fata..Nace wannan ai Sakarci ne..Mallam ya Fadamana da Safe zemcen Tarewar kuma in banda abun Sakina Amina ai kanwa take gareta keda zaki kwantar da Hankalinki ki jata ajiki ki Riketa amana kamar yadda kike rike Sarood ai kece babba Kece zaki samar da zaman Lafiya agidan Mijinki ammh baki dunga wannan Sakarcin ba..Gatanan Dukanta ne kadai ban yi ba sai ta fara kuka tana bani Hakuri nace bani zata bama Hakuri ba sai zata zo ta baka hakuri nace mata me zai dameta ai bata tashi Hankalinta Lokacin auranka da Sarood ba sai kan Amina ta gida ku zaku hade kai ma a matsayinku na yan gida Daya haba Sakina.. In kaji yadda na dinga mata fada sai kace na Sauraramata ta gane kuskusranta Daman kishi ne na hallitar mata ya Rufemata ido..Shine data gayamin bakasan ta fito ba na Daukota kafa da kafa nazo baka Hakuri..Dom Allah Umar kayi hakuri ka kuma Cigaba da Hakuri Nauyi ne ya karu a Kanka sai ka kara Hakuri kasan mu mata sai a hankali Wani Lokaci ana taromu ne muna karkacewa..! Ta karishe fada tana yar Dariya kansa na kasa yana Sauraranta aransa kuma Dariya kawai yake yi wai ta mata Fada Sakinar ce zatayi ma Fada daman baisan yadda batason damuwarta bane sai dai ko ba domin Sakina ba Anty Amarya Matar Uba take garesa zai bata girmanta yasa ya jinjina kai yana Fadin"Bakomai Anty komai ya wuce..! Anty Tace"Yauwa nagode..Allah ya Zaunar daku lafiya ya kade Fitina..! Da ameen ya amsa kasa kasa Sakina ke Zungurin kafarta yasa ta gyara Zama tana fadin"Sannan naji wata mgana Umar..Sakina tace min kace baza ta bika ba madina ba yanzu..? Sai alokacin ya Dago kansa ya Kalli Sakina kafin yace"Eh Anty..Bata fada miki yadda mukayi da ita bane..? Anty Amarya tace"Ta fadamin nayi ta Fada kamar zan ari baki..Wlh bansani bane dasani ba zata zo ba don Ubanta Sakarci ke Damunta..Don mai garinku bashi Hakuri yanzu agabana..! Tafada tana Dungurin kan Sakina wacce ta rankwafa tana Fadin"Kayi hakuri..! Kallonta yake yi bai yi mgana ba yana Rokon Allah kada kafin ya koma Sakina ta Cikashi taga dayan kalansa Taga bacin ransa. Ganin yayi shuru yasa Anty Amarya tace"Ta baka Hakuri Umar don Allah ka yafemata in ka tashi komawa sai ta Bika ku koma tare..! Umar ya Dago kansa kafin yace"Anty mi batamin komai bafa..Mgana Dayace na riga na Rantse bazata Bini ba..Nan din Datake so nan zata Zauna Insha Allahu..! Sakina ta kalli Anty Amarya itama ta kalleta Cikin Takaicinta alamun ta kara Rokonsa tayi mata bata sani ba Duk yana kallonta aransa yace zaki gane baki da wayau ne sakina..! Anty Amarya tace"Kadai yi hakuri..In ba kudin Visar ne ni zan Biyamata sai ku tafi taren kaji..! Kai Tsaye yace"Chan din in ta taka ta koma to bada yawuna ba Anty..nima ban rasa kudin da zan Biyamata ba kawai Ra"ayina ne bazata Bini ba..Ita ta sani nayi Rantsuwa kuma akanta bazan yi kaffara ba Wlh anan zata zauna sai sanda naje na dawo..! Sai dukkansu suka kasa mgana Anty Amarya ta mike tana Fadin"Shikenan gwara kayi mata haka ko zatayi hankali..Ni bari na tafi.Allah ya kyauta..! Ya mike Tsaye yana fadin"Ameen Anty Idi ne ya kawo ku..? Anty Amarya tace"A daidaita muka zo..Idi kila sun fita da mallam ne..! Da Sauri yace"To bari nazo na kaiki gida..! Da Sauri tace"A"a ka bar shi kawai Nagode..! Daga haka ta kalli Sakina ta Harareta Kafin ta fice Umar ya fita ya Rakata har waje ta samu adaidaita ya biya mata Drop suka wuce. Daganan bai koma gidan ba takawa yayi da Kafafunsa zuwa masallacin Dake gaban gidansa Uku da wani abu Lokacin La"asar ta kusa cikin masallacin ya shiga ya zauna yana Faman Tunanin ta ina zai fara zama da yarinyar nan gabadaya Bata dace da Rayuwarsa ba ga Sakina ita kuma kamar wata karamar yarinya ta fara rashin jin mganarsa Lallabatan Dayake yi yasa ta fara Tunanin ya sakar mata ne tarika abunda taga dama..! ***** 8:30pm Misalin karfe  Takwas na Dare Hajiya Babba da Hajiya Uwani suka shigo gidan Sa"idu domin tafiya da Amina wacce tunda suka dawo daga gidan Kitso gabda mangariba,Anyi ma Amina Kitso mai kyau da kunshi ja da baki,salla kawai sukayi ko abinci basu ci ba ya Jafar da ya Nasir suka Shigo Daga masallaci suke suka Kira Amina Dakin yaya ba abunda basu Fadamata ba, ba Lallashi bane Fada ne da Umarni ya jafar ya Jaddadamata bar ganin zata koma chan da zama Wlh Tallahi ya rantse ya kara rantsewa intayi wani abun da ta saba na iskancinta Har chan zai taka ya mata Dukan Tsiyan ya Nasir ma yayi nashi Fadan shidai fadi yake kada Allah yasa tayi hankali Tagani wuya ce zai sa tayi hankali Tunda suka fara mata Fada take ta kuka kamar ranta zai fita,Basu Dade ba suka yi ma mamanmu sallama suka tafi Shikenan fa Amina ta cigaba da kuka su Hanne ma suka kama ko abimci sum kasa ci,Duk da suna jin yunwa Dakyar mamanmu ta matsa Amina tayi wanka ta shirya cikin Less din Bikin su ya Abida riga da sikat da Hijabi Fuskarnan duk ta Kode saboda kuka. Sanda Hajiya suka shigo sai Amina ta Kara gasgasa cewa da gaske fa Wani Sabon Shafin Rayuwar ya kara Bude mata batare data shirya ba,Barin ma d Su ka shigo da su Ya Akilu suka Dauki kayan Amina ghana Must go uku Duka an cika harda Takalman makarantarta da Jakarta komai nata dai an hada mata Hajiya tace su kai Falon Mallam Amina ta waiga taga wajen Dirowarta wayan ba komai kawai sai ta sulale kasa tana ta kuka Mamanmu kuwa baya ta juya tana Sharan Hawaye makirci da kuma rashin mafita Hamida da Hanne kuka suke kamar ransu zai fita Harda Jawad ma kukan yake yana rike Amina yana fadin"Ya Amina ina zaki je kina ta kuka..? Hajiya dai bata ce musu komai ba Hajiya Uwani ce tace"Kai kubar kukan nan hakanam mana Balaraba har da kema..? Keda zaki lallashesu..Kudaina kuka ku taso muje ku raka Amina Dakinta..! Hajiya tace"A"a Mallam ya Kira Danmallam shi zai zo ya Dauki matarsa su tafi..! Sai su ka kara saka kuka Haj.Uwani na Dariya tace"To kuyi hakuri Bayan kwana Biyu sai kuje ku wunin awajenta ko..!? Wayar Hajiya ce ake kira yasa ta Daga tana Fadin"Kun gani mallam ne ma..! Da sallama ta Daga Kiran Mallam ya amsa Dagachan bangaran yana Fadin"Hajiya kuna ina ne..?Ga Umaru tundazu yazo yana jiranku..! Hajiya tace"Gamunan yaran ne ke ta koke kokensu..! Mallam yayi Mirmishi kafin yace"Ku taho dasu dukkansu mu lallashesu hajiya..Ba su ba har ni zan yi matukar kewar Mamana..! Daga haka ya katse kiran Hajiya ta kalli Mamanmu tana Fadin"Balaraba Hakuri zaki yi..Dauko Mayafinki ki mika Diyar taki Falon malam..Haj.Uwani Taimaka ki Lallaso su hannatu mallan yace muje gabadayanmu..! Mamanmu na Sharam kwallah ta Sako Hijabinta ta riko Amina Dake kuka Hajiya uwani kuma ta Lallaso su hanne suka mike suka fito tare Hajiya Babba na gaba Tare da Mamanmu da Amina dake kuka cikin Hijabinta su Hanne da Hajiya uwa na baya Har da Jawad shima yana Hawaye har falom Baba mallam Dake cike dasu Aba sai su ya Jafar da Ya Danmallam Yadda Aka shigo da Amina na kuka ko Aba sai da anbun ya tabasa Danmallam kuwa aransa yasan ya shiga uku Kwalin panadol zai siya kafin ya koma domin shi da ciwon kai Salamu alaikum sun kulla abota Gaban Aba da Mallam suka Direta Hajiya tace"Gata nan ka mika amanarta Hannun Da"nka..In yaci Amanar Amina Ka fadamai Bazan taba YAFEMAI BA..! Tafada cikin son tabbatar da mganar Danmallam kansa na kasa bai ce komai ba Aba ne zai yi mgana Hajiya ta katse shi da Fadin"Kayi mata fatan Alheri Sa"idu! Shiyasa ya kasa mgana Amina ya kallah yadda take kuka ya tabasa sai kawai ya Dafa kanta yana Fadin"Allah yayi miki albarka Amina..Allah ya albarka ci auramku..Nima na Fada kuma zan kara Fara koda Sau Daya in kika Sabama ma Umar gashi nan Amina BAZAN TABA YAFE MIKI ba..! Cak kukanta ya tsaya kowa kuma Aba yake kallo shi kuma ya kara kausasa Muryansa yace"In kika basa Wahala Amina keda Allah..In kika Bijirema Umarninsa Keda Allah..In kika Zame masa Damuwa keda Allah Amina..ki zama Haske garesa sai Allah ya Haskaka lamuranki..Allah ya baku zaman lafiya..! Yana gama Fadin haka ya mike da Sauri ya fice yana Boye kwallarsa Jawaad yabi bayansa yana kiran sunansa Mamanmu tabisa da kallon Takaici tasan waya tuna yaya ce..Kai Wannan soyayyar dai ko bayan rai ma Ana mararinta. Baba mallam yayi shuru bai yi mgana ba sai da Hajiya tace"Kaifa Mallam me zakace..? Maallam cikin wani yanayi ya mike yana gyara Rawaninsa yace"Umaru taso..! Ba Musu Danmallan da Jikinsa ya Mutu ya mike sanye da shadda Jikinsa Riga da wando Mai ruwan kasa Dinkin Tazarce,ya isa gaban Mallam yana kokarin Dukawa ya saka Hannuwansa ya Rikosa suka karisa gaban Amima ya Duka da kansa ya Dagota yana Fadin"Taso taso..Taso Uwata..! Ba musu ta mike kanta na cikin Hijabi ya Hada hannunta dana ya Danmallam Dukkansu sai da sukaji wani Dum a Atsakiyar kansu. Su Hajiya ya kallah yana fadin"Ku zu mu yi musu rakiya..Ina marliya da Nasaratu suke..? Hajiya zatayi mgana keman sai gasu sun shigo kai Tsaye Mallam yayi gaba Yana tsakiya Amina da Umar suna gefensa ya hade hannayensu waje daya yana fadin"Ku biyoni..! Ba musu suka bisa a baya Hamida da Hanne suna ta kuka har Haraban gidan Wajem Motar ya Danmallam Ya jafar ya Bude gaban motar Mallam ya kalli Dammalam yana fadin"Taimaka mata ta zauna mana..! Sannan ya sake su ba musu Umar ya Taimakama Amina ta shiga Mota ta zauna yana rike da hannunta sai alokacim Mallam yace"Kaga yadda ka rike hannunta tundaga Falona har nan waje...? Sannan ka taimaka mata ta shiga motarka..!? To ina so ko ba Raina Umaru kada ka saki Hannun Amina..Da Dadi ba Dadi ka Zama mai Tallafa mata ka zama Ubanta,yayanta,Mijinta Uwarta da yan"uwanta bango mai Bangon Alheri Umaru..! Kansa na kasa yace"Insha Allahu Mallam..! Mallam ya kalli Amina yana fadin"Mamana kiyi masa Biyayyah..In kikamai gaddama bazan ji Dadi ba..Allah ya zaunar daku lafiya kuje..Addu"armu da alBarkanmu na Tare daku har abada..! Shima Hawayen ne suka cika idonsa yasa ya Juya Amina taga ana shirin Rufo mota da ita ga su hanne tana kallo suna kuka ita kadai zata tafi kenan ai sai gani akayi ta wuntsilo Har sai da Danmallan ya riketa Saura kadan ta Fadi kasa hanne ta Tunkara ta Rumgumeta ta fashe da kuka sai Hamida ma ta kara mata Rumfa suka Durkushe suna wani kuka mai Shiga ran mai Saurare Baba mallam Dagachan ya tsaya yana Fadin"Hajiya ku rike su hannatu..Kai kuma Umar rike hannun matarka kuje..! Daga haka ya juya ya koma Falonsa Hajiya Uwani da Haj.Nasara suka kama su Hamida sai Amina ta koma Wajen mamanmu ta fada Jikinta sai kuka ko ya jafar sarkin zafi bai yi mgana ba ya Danmallam dai na gefe yana kallon ikon Allah yara kamar masu aljanu Hajiya ta bambare Amina Daga jikin Mamanmu ta Tura ta Mota ta Rufe tana Fadin"Ku tafi UMAR..! Sai yau ya taba jin ta kira sunansa ya kalleta ta kallesa sai kawai ta juya tana Fadin"Allah ya baku zuru"a tagari..! Da Mirmishi saman bakinsa yace"Ameen Hajiyata..! Anty Amarya ji tayi kamar ta Kurma Ihu agaban idonsu ya shiga bangaran Direba ya Tada Motar Amina na kallonsu Hanne da Hamida suna kuka ta mika hannu ta Glass tana kallonsu sai taji kamar zata shide Tunda suka taso basu taba Rabuwa da juna ba sai yau batasan haka Hamida da Hanne suka zama jinin jikinta ba sai yau da taga Rabuwa da su Kirkiri. Sanda Megadi ya Bude get suka sulala waje ya dauki hanyar gidansa sai Amina ta Juya baya bata ga Hanne ba,Ba Hamida sai ta Juya tana kallon ya Danmallam Dake Driving hankalinsa baya wajenta,Kenan ya Tabbata shine mijinta..! Gidansa zasu koma..? Ina Aminu..? Shikenan ta rasashi..!? Ta tun yasha Fada mata in bai aureta ba zai lalace..! Yau zata je ta kwana in da ba hanne ba Hamida ba mamanmu..! Kawai sai taji Duniyar tayi mata Tsit ta kama kanta ta girgixa kafin ta Daddage iya karfin muryanta ta Saki wani irin kuka..! Lokaci daya tana Fadin"Wayyo Allah na na shiga uku..Bazan iya ba..Don Allah ka maidani gida..! Ihun data saki yasa har sun hau kwalta Kansa ne ya sara ya saki Sitiyarin ya Dafe kansa kawai sai Motar ta kwacemai ta fara yawo saman Titi ya manta sam Tuki yake yi ihun Amina da kukanta sun Shiga kunnensa sun Haukata Tunaninsa Hayaniya nadaga cikin Abunda yafi Tsana arayuwarsa...! *Alhamdulillah anan na kawo karshen Littafi na daya da Labarina na ta fita zaka,Nagode ma Allah domin baiwarsa ce kuma ikon sa ne bazan Tsawaita mgana ta ba kun riga kusan yanzu aka fara wasan akwai tarin abubuwan da zasu faru a kashi na Biyu na cigaban wannan labarin a baya naso nayi sa Cmpt dinsa Hardcopy ne ammh Sakamakon Rikon Wasu masoyana yasa na amince zan yi sa Softcopy ammh da Sharadin in kun siya Over 150 a paid group sannan bazan fara posting ba sai nan da Sati Daya zuwa sama in na gama Hutun dana Dauka ga masu son su Fara payment din su zasu Biya N500 Via 0552179550 Jamila umar Gt bank sai a Tura Shedar biya ta wannan lambar 09069067488, masu Turo kati kuma sai ku Dauki hoton katin ku Turo kai Tsaye ta wannan lambar 09069067488,Mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi Kausar aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223 sai na jiku ina gaida masoyana a ko"ina afadin Duniyar nan wanda na sani da wanda ban sani ba..Sannan ina mika jinjinata ga Groups din da suka yi sharhi kan wannan labarin da masu sharing dinsa da yan Wattpadian dina Allah ya saka da Alheri Allah ya bar zumunci Maassalam* *TFZB2001* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Yana dafe da kansa kwata kwata baisan motar ta kwacemai ba sai da yaji ta fara yawo a kan titi sannan ya dawo hayyacinsa yana kokarin kamo Sitiyarin motar ne Amina Data ke kuka cikin karan sautinta taga wata babbar mota tayi kansu gadan gadan sai gabanta ya fadi,Kukanta ya Dauke da batasan sanda tayi tsalle sai gata jikin Danmallan cikin rawan jiki Ta kwalla kara tana Fadin"Wayyo Allah babbar mota...! Wani bakinciki da takaici su kusa kasheshi,bai samu damar mata mgana ba sai da ya daidaita Motar sannan ya gangara gefen hanya yayi parking kafin ya juyo yana kallon Amina wacce ke rike dashi Saboda Tsoro ran sa bai kara baci ba sai da yaga gabadaya Hawayenta da majinanta ta gama gogemai saman kafada wani irin kallon kyama da Haushi yake binta dashi ita batama Lura ba saboda bata cikin natsuwarta ga Halin datake ciki ga Razanan da tayi na ganin babbar Mota ta nufesu gadan gadan. Ganin sai zare ido take yi taki sakinsa yasa ya saki wani siririn Tsaki kafin ya Daka mata tsawa yana fadin"Ke...! Sai alokacin ta dawo Tunaninta ta Dago tana kallonsa ganin irin yadda yake Hararanta ne yasa tayi saurin Sakin rigarsa data cukwikwiye da hannayenta ta koma kujerarta ta zauna da Duwawunta tana maida Nunfashi Lokaci daya da ruwan hawaye suna gudu Bisa kumatunta. Ransa ya kara baci da ya kunna Hasken motar yaga yadda Maikon hannunta ya sakamai Shatin Datti ajikin Rigansa baisan sadda ya kalleta cikin bacin rai yana fadin"Ke wata irin kazamar yarinya ce mara natsuwa..?Ko sau daya tak a rayuwarki bazaki yi wani abu da zai nuna ke mace bace..? Yafada yana kallonta cikin Idanuwansa da suka fara sauya Launi Saboda bacin rai. Bata dago ba kanta ta kara maidawa kasa tana sharan kwallah kalmar kazaman daya fadamata bata Dameta ba kamar yadda yace mata mara natsuwa duk sanda ya fadamata haka sai ya sakata kuka yanzu ma Kukan ta fara Tana neman kara baremai baki da Sauri yace"Kika kuskura naji ihim dinki Wlh sai kin raina kanki..kinsan Zafin hannuna kuwa..?Baki sani ba na su Jafar kika sani to kika bari kika kaini bango da wannan banzan kukan naki wlh in na mareki sai bakin ki ya juya Hagu..Uselesss kawai..! Yafada Cikin Kufuluwa acikin ransa yana Faman kokuwa da yanayinsa Gabadaya an kuntatama rayuwarsa yanzu banda a kashesa da ransa Lokacinsa bai ba..?yi ta ina zai iya zama da wannan yarinyar..?Kukanta kadai ya isa yasa Hawan jini ya kamashi..! Ko kara kallonta bai yi ba ya maida kansa wajen kokarin tada Motar ammh sai me sai yaji kukan na kwace mata da sauri ya juyo yana kallonta Cikin mamaki ganin haka yasa tayi Saurin saka Hijabinta ta Danne bakinta Hawaye kamar famfo suna zuba bai mata mgana ba ya tada Motar suka hau kwalta ya fara Tafiya kenan kawai yaji ta bare baki ta saki kuka Da waani karin mamaki ya kara Binta da kallo yama rasa me zai ce mata,Hannunsa Daya rike da Sitiyari Daya kuma Dafe da kansa yana Bin ta da kallo ji yake kamar ya Tsaya a hanyar nan yayi wurgi da ita kalli Daga gidan mallam zuwa gidansa yarinyar nan har ta fara chazamai kai. Saboda bacin rai baisan sadda yace"Au kukan kike yi ko .? To wai ma tsaya me akayi miki ko kuma uban me kike so..? Cikin kukan tace"Ni kamaidani gida..bazan iya kwana wajen da ba Hanne da Hamida ba..! Harara ya jefa mata kamar ya Daketa Haka yake ji Cikin Fusata yace"To anki a maidake din..Sai kiyi abunda zaki yi in kin isa..Haba..Wannan iskancin ya isheni wlh bazaki je kina Damuna da wannan kukan banza naki ba mganinki zanyi..! Amina sai ta kara wage baki tana Fadin"Wayyo ni..Hanne...Yiyiiyiiii..Hamida..Wajen su zan je na shiga uku..Yiyiiyiiii..! Reras fa hake ta kuka Danmallan yayi zaune kawai mganarsa ta kare Ya rasa ma abunda zai ce mata kawai ya Cigaba da Tukinsa bayan ya Dauke kansa,Tsabar bala"in yarinyar nan kansa har ya fara saramai ina Dalili ganin bata yi shuru ba yasa ya Daka mata tsawar da yasa ta kama bakinta Cikin Daga Sautinsa yace"To baza ki koma wajen su ba ko zaki yi kukan jini ne..Salon ki je chan ku cigaba da yima mutane iskanci da raini ko..? To anan ni zan gyara miki zama wlh in baki min shuru da bakin ki anan wajen ba..Daganan Gidan gyaran Hali zan kai ki inda ake ladabarta da kangararrun yara marasa jin mgana irin ki sai kinyi kwana arba"in cikin mari kinji ma na Rantse..! Amina ta kallesa tsab tasan zai aika sai hankalinta ya fara tashi maimakon tayi shurun daya ce sai kawai ta Duke kasan Mota hannunta Bisa kai ta rushe da wani kukan dayafi wadanda tayi sauti da kara Fadi take"Don Allah kayi hakuri..Don Darajan iyayenka kayi hakuri..! Wlh kadan ya rage bai Bugama wani mai adaidaita ba saboda yadda Ihun ya shiga kansa ransa yakai kololuwar baci in ya zauna acikin motan nan zai iya ma yarinyar nan Lahani yasa baisan sadda ya Gangara gefen kwalta ba ya faka Motar a fusace ya Bude bangaransa ya fita Amina kuwa ta zata ita ya tsaya ya Daka yasa ta koma ta Lafe jikin kofa tana Rufe bakinta Cikin kuka sai taga ya fita ya Rufe kofar da karfi kamar zai ballah. Bayan Motar ya koma ya Dafe kansa cikin wani yanayi yake maimaita Hasbunallahi wani'imal wakeel..! Bai saurara ba sai da yaji ya Dawo Cikin natsuwarsa ya zai yi da wannan Fitinanniyar yarinyar da ke neman chajamai kai..? Wlh bazai iya zama da yarinyar nan ba Tun aTarihin rayuwarsa bai taba Daga Sautinsa irin na yau ba bai taba Fada irin na yau ba ko Sakina ta batamai rai baya Biyemata yana da Hakuri da kawaici sai ta Dade tana abunta bai Dago ya kalleta ba shi in ya tashi nashi Lokaci Daya zai yi shikenan kuma ya huce ballatana Sarood da bata da Hayaniya banda ma dan matsalan da suka samu da zasu taho Bikin nan. Karamin Tsaki yaja kawai afili yana kokarin samo ma kansa mafita Visar sa zai yi kokari ta fito Cikin Satin nan ya kara gaba kafin yarinyar nan ta kai shi bango yayi mata Dukan mutuwa Tunda ya Lura Baba mallam ya gama batata sannan su jafar ba Hukunci suke mata ba wani Burauban nata Harda iskanci da rashin natsuwa. Ya lura ba yarinta bane Tsabar iskanci ne da samun wuri banda haka kamar ita tasan ta iya waya da Saurayi a boye har suna haduwa..?ai shi sanda Mallam ke fadamai yana ta fadin yarinta ke damunta jinsa kawai yake wannan abun ya wuce yaro yayi sa tana Sane da duk abunda ta aikata shine Hajiya ke son ya kwasheta ya kaita Madina wlh ya tabbata watarana sai ta jawo silar abunda zai sa a Dauresa in ma bata yi sanadiyar barowarsa kasar ba gabadaya bama. Yana cikin wannan Tunanin wayarsa Dake gaban aljihun rigarsa ta Dauki kara,Daukota yayi ganin mai kirasa yasa ya saki ajiyar rai da salama da sauri ya Daga kiran yana Fadin"Ka kira alokacin Dayace Aliyu..! Ko sallama bai tsaya yayimai ba Tsabar Tashin hankali Aliyu dake zaune afalon gidansa ya gyara zama yana fadin"Shehi ango..Angon Sixty.. Tsabar Rudewar ne yasa yau Shehi ya manta da sallama..? Ya fada cikin shakiyancinsa Umar ya Saki karamin Tsaki kafin yace"Salamu alaikum..Na sha"afa ne Aliyu kaina ya Fara ciwo wlh..! Aliyu yajisa cikin wani yanayi yasa yace"Meya faru ne..? Baka koma gidan bane ko baka je gidan Mallam din bane..? Daman sunyi mgana Kafin ya fita Daga gida Cikin Kar ya Sauti yace"Na je gidan mallam..Bakasan wani abu ba..yarinyar nan fa suka hado da ita Aliyu..! Aliyu yace"Wata yarinya..? Danmallam ya Dafe kansa kafin yace"Kazamar yarinyar nan mana..! Aliyu yace"Nifa ban gane wata yarinya ba Sakina wai kake mgana..? Yafada cikin Danne Dariyansa Umar ransa ya baci cikin Haushi yace"Sakinar ce kazama Aliyu..? Amina fa nake maka mgana da nace maka Hajiya ta matsa sai ta tare yau din nan abu kamar za"a gudu..Ko kuma ana jirana Aliyu..! Aliyu ya saki yar dariya kafin yace"Au to..Kaine ka fadi sunan yarinya kaki kana ta fadamin kazama ni to ya zan yi na ganeta..? Wai yanzu kana nufin kuna tare..?To tana ina..? Yafada daidai sanda Aliya matarsa ta shigo Falon ganin yadda yake zaune yana waya ne yasa jikinta ya bata da Umar yake mgana Hararansa take ta kasan ido domin itama tashin Datayi Da Sakina taje Daki sukayi mgana Wlh tafi sakina Jin kishi da wannan auran Rainin da Umar yayi haba in ba Raini ba wannan kazamar yarinyar ta ina zata iya hada miji da ita komawa baya ne wlh,Ta fadama Sakina kada ta Sake ta bari ta shigar mata Dakin miji sai ta zata sun zama Daya da ita kenan sai dai ta nemi Dakin kwana Tun da Sakinar ta fadamata Labarin Tarewar ranta yake bace Har Aliyun taji Shima Haushinsa take ji tunda ya shigo take fadin rai yana ganin haka shima ya shareta bai bi ta kanta ba. Ganin yadda ta zubamai ido ne Umar na fadin"Wlh Aliyu yau kadai dana Dauko yarinyar nan har na fara gajiya..Can u just imaging kuka take min amota har tana wayyo Allanta har barazanar kaita gidam mari nayi taki yin shuru kafadamin ya zanyi..Wlh kaina har ya fara ciwo na rasa ya zanyi..? Yafada lokaci Daya yana Dafe kansa dayake Saramai Tun dazu Aliyu, Aliya yaga tana kallonsa yasa ya mike yana Fadin"Shehi me yayi zafi..? Kai da zakayi lallashi sai ka Bige da zuwa gidan mari..! Yafada yana Dariya Lokaci Daya yana Ficewa daga Falon zuwa bedroom dinsa yana jinta tana raka sa da fadin"Girma dai ya fadi wlh..! Shi yasan kan mganar domin tun da yadawo take sakin tsaki Lokaci bayan Lokaci sai tace an dai ji kunyar Wlh mutum ya rasa wazai aura sai yar Cikinsa ko batayi mgana ba yasan da Umar take so take ya tankata shima yau gidan nasu ya koma yakin Biyafara banda mata ma mata ne ina Ruwanki da batun gidan wata kai abun na bashi mamaki..! Sai da ya shiga Dakinsa ya kulle sannan yace"Ina jinka..na baro Falo ne..kasan nima yau gidana irin gidanka ne..Aliya na taya Sakina kishin ka yo musu amarya da karamar yarinya wai kama raina su..! Ya karishe fada yana yar Dariya Umar ya saki hanci kafin yace"Bangane tana taya ta Kishi ba..!? Nan Aliyu ya labartamai abunda ya faru Danmallam ya shafa gemunsa yana Fadin"Meyasa mata suke da karamin Tunani ne..?,Ita Aliya Daman haka take..!To yau in kai in zaka kara aure ya kenan..? Inaga baka ba kara aure Aliyu..! Aliyu yace"Wane ita..?Har ta isa wlh tallahi sai dai in banga wacce nake so ba..Ina da sha"awar kara aure Shehi in kaga ban yi ba to hakan na cikin Abunda Allah ya Tsaramin ne..! Umar yace"Lalle akwai yaki..Aliya zata cin na ma gidanka wuta..! Yafada yana yar dariya Aliyu yace"In ta fasa..Ni fa ba irinka bane da zan zauna anamin iskanci ban ci ubam Mutum ba..Wlh ban kai ka Hakuri ba Umar..Ina da kawaici ammh ba kowani Lokaci ba yanzun ma Daka ga na kyaleta Lokaci na bata in ta bari na tankamata sai ta raina kanta ni ba Sakaran Namiji bane ka sani..! Umar na yar dariya yace"Allah dai ya kyauta..! Aliyu ya amsa da Ameen kafin yace"Wai ina ka barta ne..? Umar yace"Tana cikin mota..Kaina ya fara ciwo wlh kukanta zai sakamin Dagaaawar jini Aliyu..! Agogon Wayarsa Aliyu ya Duba kafin ya maida wayar kunnensa yana Fadin"Shehi Dare fa yayi..Pass 9 goma ta kusa..ka lallabata tayi hakuri kasan Rabuwa da gida..kuma kada ka manta aure yakin mata..Sannan ita ga yadda abubuwa suka zo shehi Dole tayi kuka..Gata yarinya ce karama Kasan kaima sai ka kara Hakurinka sannan Hajiya da Mallam sun zama gatanga gareta Dolene ko baka so kayi Hakuri da ita na dan Lokaci ne nan da wani Lokacin in ka fara cin amarci kana jin Dadinta zaka bani Labari mutumina..! Danmmalan ya saki Tsaki kafin yace"Ammh dai Aliyu kai mutumin banza ne.. ko..? Bai jira amsar sa ba ya katse kiran yana Fadin"Ko kunya Bai ji..Yana mganar wannan abun da wannan yarinyar..! Tsaki yayi kasa kasa kafin ya maida wayarsa aljihu sai da ya bata Lokaci kafin ya Dawo Motar budewa yayi ya lekata ganinta nan kasan kujeran ta Dunkule yasa ya shigo Motar karan Rufe motar ne ya Dawo da ita cikin Tunanin data Fada na gata chan agidan kangararru an sakamata mari. Tana ganinsa ta zabura tana Kokarin kara sakamai kuka wani banzan kallo yayi mata kafin yace"Ki bari naji ihim dinki ki gani..Wlh na rantse yau sai kin kwana gidan mari karyan iskanci kike da rashin kunya chan akwai Uban ninki a tacewa..! Bakinta ta kama tana Hawaye Tsawa ya Daka mata kafin yace"Tashi ki hau Kujera..! Da Sauri jikinta na Rawa ta koma ta zauna tana Danne Bakinta ko kara kallonta bai yi ba ya Tada Motar suka fara tafiya Amina ko Tsoron za"a kaita gidan mari ga kuma tsoron zata je wani gidan inda ba Hamida ba Hanne Ta tsorata dashi duk muguntar su ya Jafar tana ganin ya Darasu tunda su basu taba cewa zasu kaita gidan mari ba,Shiyasa duk son kukanta ta bame Bakinta gam sai da na zucci a haka suka iso gidan Danmallam Dake kofar arewa. Yana hon megadi yazo ya Budemai get din gidan ya sulala da Motarsa parking space sai da ya gama Daidaita motar kana ya kashe ta ya Fito har Lokacin Amina na zaune ta kasa Motsi sai da ya fita yana gaisawa da Buzun megadinsa yaga bata fito ba kai ya girgiza Booth ya Bude ya Fito da Kayanta ya ijiyesu nan Kofar Falon kafin ya isa wajen motar ya Bude mata Murfin yana fadin"Sai nace ki fito sannan zaki fito ko me kike nufi..? Dasauri ta fito tana faman sharan kwallah ko kallonta bai yi ba yayi gaba ya barta nan tsaye yana kallonta bai ce mata komai ba ita kuma Tsoro take ji kada tayi wani abu yace zai kaita gidan mari duk da bata taba zuwa ba,Ai Baba mallam na kai ziyara Lokaci bayan Lokaci yana zuwa tare da Aba ko su ya shamsu har jawad an sha zuwa dashi tana jin labarin yadda ake gana musu azaba abakinsu ina zata yi wani abu wannam mara Imanin ya mikata chan kafin Su Baba mallam su ji labari su je su karbota ta kusa mutuwa..! Shi kuma yana ganinta Tsaye yayi kamar bai ganta ba Yasan in ya bar mata kayan bazata iya Dauka ba yasa ya Fara Dauka yana shigar mata dasu Cikin Falon gidan Yazo Daukan na karshe ne ya Dago yana kallonta cikin Haushinta yace'"Shima sai nazo na kama hannunki na shigar dake gidan sannan zaki shiga..? Jin haka yasa tayi saurin wucewa gaba shi kuma yabi bayanta. Tana shigowa Falon suka hada ido da Sakina data fito daga Dakinta Cikin kwalliyarta Less ta saka riga da Sikat sun kamata ta shaba kwalliya kamar wacce zata je gasan kyau na Duniya bakinta Cingam ne tana Taunawa kas kas kafarta cikin wani takalmi mai Dubu kallon kallon suka tsaya yi da Amina cikin kyama da wani Tsana take kallonta ita kuma Amina sai ta kasa gaba ballatana baya saboda ganin Sakina shima daya shigo ya ganta sai yayi kamar bai ganta ba Tun bayan tafiyar Anty mgana bata Kara Hadasu ba Dakinta ta shige shima ya shiga nasa har ya je amsa kiran Mallam bai sata a ido ba jidalin Dake kansa sun ishesa inda zata gane da ta barsa ma yaji da abunda ke Damunsa..! Ta gefen Amina ya raba ya wuce ko barayin Sakina bai kallah ba Dakinsa ya Nufa zai Bude yaji a kulle Cikin mamaki ya juyo yana kallon Sakina kafin yayi mgana ta wucesa zuwa kan Daya daga cikin kujerun falon ta Zauna ta Dora kafa Daya kan Daya Tana cigaba da Taunan cingam tana kas kas..! Ransa ya baci ganin Amina Tsaye awajen yasa ya sausauta Cikin sanyinsa yace"Waya kulle Dakin nan Sakina..? Ina key din..? Sakina ta kallesa Cikin wani Bakinciki yau ita ce ke shakan Numfashi da wannan yarinya a matsayin Mijinsu Daya gaskiya Umar ya gama Cutar da ita. Kai ta kauda batayi mgana ba ya kara Sausauta Murya yana fadin"bada ke nake mgana ba Sakina..? Sakina ta wani kallesa a karkace kafin ta Hura bakinta ta saki kwan cingam din Dake Binta ta wani Rausayar Dakai Cikin Wani yanayi tace"Makullin na hannuna..Ni kuma na kulle Dakin..! Bai ji mamaki daman yasan ita zata kulle ba kowa ba cikin son kara nazarinta yace"Saboda me yasa kika Kulle Dakin bayan na Fadamiki Hajiya tace yarinyar nan ta zauna aciki..! Sakina ranta daman yana bace ne ga Kishi kawai sai ta mike tana fadin"Wlh Umar baka isa ka Tozartani ba..Ni zaka wulakanta bayan auran wannan yarinyar da kayi ban ce komai ba..Shine saboda a kara Kuntatamin sai ace Dakin mijina zata zauna..? To wlh bazata sabu ba...Ko Mijin bazan raba da wannan kuchakar yarinyar ba ballatana Dakin miji..Bazai taba yuyu ba..! Tafada tana bayyana bacin ranta Hannu kawai ya kama a kirji yana kallonta Amina ma ita take kallo ita aranta ma Dadi taji Allah yasa taki Bude Dakin ya maidata gida. Cikin Kaushinsa yace"To yanzu ya kike son ayi sakina..? Kai Tsaye tace"kai ka sani..! Daga haka ta koma ta zauna tana Jijjiga kafa Lokaci Daya tana Hararan Amina Dake ta sharan kwallah. Bai ce komai ba ya kalli Amina yana nuna mata hanyar Dakin Sakina Lokaci daya yace"Zo ki wuce..! Kamar tayi mgana sai kuma ta fasa ganin yana mata wani kallo Sakina da mamakinsa ya cikata na ganin Dakin daya nuna ma Amina Dakinta ne. Sai dai batayi mgana ba sai da taga Aminar ta nufi bedroom dinta sannan ta Mike kamar kububuwa sai gata gaban Amina ta tare gabanta Cikin Zare mata ido tace"Kan uba..Badai Dakina ba..Allah ya Tsareni wannan kazamar ta shigarmin Daki..! Sai Amina ta Tsaya ta kasa gaba ballatana baya Umar yana Tsaye inda yake yana kallon Sakina da Idanuwansa da suke kokarin bayyana yanayin dayake ciki. Kokarin Daidaita kansa yake yi yasa bai yi mgana ba Sai da yaga Sakina ta Hankada Amina sai da ta kusa kaiwa kasa tayi Saurin Dafa Kujeran Dinning Sakinar kuma ta jawo kofarta ta Rufe da makulli tana fadin"Yau ni Sakina naga Rainin hankali..Dakin nawa zaka saka Kishiyata..?Allah ya tsareni ma da ta zama kishiyata Har Abada..! Take fada tana jijjigan Jikinta Danmallan yayi tsai yana kallon wani waje bai yi mgana ba. Babu makullin daki ko daya a hannunsa na Gidan duka yana hannun sakina Sauran kuma suna gida wajen Hajiya,sannan akwai wajen Jafar,Shi bai taba Hausan makullayen gidan sa su zauna awajensa ba. Bayason su yi wani abu gaban wannan yarinyar girmansa ya Zube shiyasa ya dinga maimaita sunan Allah har ya samu ransa yadan sauka Cikin Sanyinsa ya juya yana kallon Sakina kafin ya mika mata hannu yana Fadin'"Naji bazata zauna adakina ba..da Dakin ki ba.Bani key din Dakin Sarood sai ta zauna aciki..! Shekeke take kallonsa sai dai taji shakkansa Lokacin daya kara sakarmata wani Kallo yana fadin"Ko shima bazaki bani ba..? Jin haka yasa ta nufi kofar Dakin ta saka makulli ta Bude kada ta basa ya Bude Dakinsa tunda duka suna Hade ne waje daya gwara Dakin Sarood din ita kam banda nata Dakin kuma shima ban da nashi. Tana gama Bude Dakin ta koma gefe tana kallonsa bai kara ko kallon inda take ba ya kalli Amina Dake dannen kukanta yace"Shiga..! Ba musu ta shige shi kuma ya Dauki ghana dinta guda Biyu yabi bayanta Tana Tsaye Tsakiyar Dakin ko zama ta kasa yi bai ko kalleta ba ya ijiyemata kayanta nan ya fice tana bin Dakin da kallo ya sake shigowa ya ijiye mata Dayan ghana din ya Sake fita wannan karon har yana bame mata Kofar ta bisa da kallon ganin ya Ficen ne yasa ta sulale nan kasan Cafet din Dake Dakin ta hada kanta da Bango ta fashe da kuka,kukan da ko Rasuwar yaya batayisa ba kukan kewa da rasa wani abu a Rayuwa ta yaya zata fara zama in da ba hanne ba Hamida ba mamanmu.! Tuna haka yasa ta kara sakin wani kukan ta dora kanta jikin gadon ta cigaba da Rera kukanta,Bata ma ji shigowarsa ba sai karan bude kofa taji tana Bude ido ta gansa ya shige wani kofa Dake Dakin ya kullo,sai tayi tsit tana ware idonta da sukayi zuru zuru da kuka duk ta wani yarkace ko motsi bata karayi ba ita azatonta uwar Daka ya shiga shiyasa ta kasa motsi sai chan taga ya fito Fuskarsa na Digan ruwa alamun alwala yayi ko barayinta bai kara kallah ba ya sake Ficewa ya bame mata kofar yana Fita ta Dora hannu akanta ta fashe da kuka tana fadin"Na shiga uku ni Amina..! Sai kuka harda Birgima a kasa kamar wata yar yarinya ita kadai bamai lallashinta. Tanayi tana rufe bakinta kada ya jiyota ya shigo,yadda take kukan sai ka Tsausayamata kuka ne Dake fitowa Daga kasan ranta. Sakina tana tsaye tana jijjiga jikinta ya fito nan saman cafet din falon ya Daidai gabas ya tada sallah Shafa"i da wuturi yayi sannan ya zauna yana Tasbihi da hannayensa ko barayin Sakina bai sake kalla ba har ya gama yayi addu"a ya shafa Rigarsa ya Cire ya rataye ta nan saman kujera daga shi sai dogon wando ya samu Filon filon kujerun ya jera saman kujera 3siter ya kwanta Kansa na kallon Rufin Falon hannayensa kuma ya Saka ya Dunkule su waje daya ya Dora su saman Filo kansa na kai. Wayarsa daya ciro cikin aljihun rigarsa ya ijiyeta nan saman center Table din Dake falon,Sakina sai Binsa take da kallo ta kasa mgana sai alokacin kuma jikinta yayi sanyi mganganun Anty suna dawo mata da tace kadatayi wani abun da ran Umar zai baci tabi komai a sannu ammh ita Kishi ya Rufe mata ido da kuma mgaganun Aliya dazu da sukayi mgana ita ta kara tunzurata. Takowa ta farayi cikin Falon Cikin Sanyin jiki a gabansa ta Tsaya tana kallonsa kafin ta sauke numfashi tace"Bari na bude maka Dakin ka..! Baice mata komai ba ta koma ta Bude Dakin sannan ta Dawo gabansa tana Fadin"tashi ka shiga ciki Habibi..! Mikewa yayi ta Dauka zai shiga Cikin ne sai taga ya isa ma kunni wutar Falon ya kashe duhu ya gauraye wajen gabadaya ido ta zaro tana Fadin"Habibi...! Ko kallonta bai yi ba ya koma ya kwanta Har da Juya mata baya Sakina taji ta Muzanta Sai ta Duka gaban inda yake kwance tana saka hannu ta riko hannunsa tana fadin"Habibi..Dom...! "In kika kara tabani Sakina wlh tallahi zan sharara miki mari..Zaki ga Oder side of me da baki taba gani ba..! Ya katseta Cikin Tsawa Daidai Lokacin daya juyo yana kallonta Cikin hasken Dake shigowa ta windows din Falon Baya Sakina taja tana zaro ido kafin tace"Ni zaka mara Habibi..? Ni kace zaka mara saboda ka kawo wannan kazamar yarinyar nace bazata shiga Dakin ka ba..? Wani matsiyacin kallo yake binta dashi bayaso yayi wani abu Saboda Amina na gidan yasa ya koma ya kwanta ai sai Sakina ta saka kuka ta Durkushe a wajen tana Fadin"Shikenan..Nagode yanzu har ka fara wulakantani saboda wannan yarinyar Habibi..? Saboda na hana ta shiga Dakin ka kakemin ihu haka..? Yar Cikin ka ce fa karamar yarinya da bata isheka komai ba..! "Karamar yarinyar da kike mgana akanta yanzu Daya kike da ita a wajena Sakina..Dani da mutanen da sukasan abunda suke yi..! Ya katseta a fusace,Sakina ta ji kukanta ya Tsaya Cikin mamaki tace"Daya fa take dani kace Umar..? Saboda ma ya tabbatar mata yasa ya Mike Zaune yana fadin"Eh..Kamar yadda kike matata haka take matata..Kamar yadda igiya uku ta hau kanki..Nawa itama suna kanta Sakina..Saboda haka dake da ita Daya kuke awajena..! Galala tayi tana Binsa da kallo Kafin tatashi Fuuu ta je ta kunna wuta Haske ya bayyana kafin ta Dawo gabansa tana kallonsa cikin karaji tace"Maimata abunda ka fada..Dazu baka kallon idona yanzu kuma idona na cikin naka nake so ka maimata Umar..! Karamin Tsaki yaja ya koma ya kwanta yana Fadin"Sai ki sani na maimaita din..! Sakina idonta ya rufe ta mike tana Fadin"Har gaban abada bazan zama Daya da wannan kazamar yarinyar ba..Wacece ita..?Yaushe take..? Wlh ita bata isa in yi zaman kishi da ita ba in nayi da Sarood ita bata kai wannan matsiyan ba..Amina ba Sa"an auranka bace Umar ba sa"an zaman kishina bace..! Kamar ya Rufe ta da Duka haka yake ji kai Tsaye ya mike zaune yana kallonta yace"Wacece ita kike tambaya Sakina..? Kinsan wacece ita ai..in ma kin manta bari na tuna miki..Ita diyar BABA SA"IDU ce kuma Diyar YAYA ce..Sannan Unarnin HAJIYA DA MALLAN NE..Ta riga ta Hada mutane masu Daraja atare dani..Ko ba aure Tsakanina da ita ni me rike Amina ne acikin gidan nan Sakina ballatana da aure Tsakanina da ita in kina Tunanin Zata bar gidan nan to kidaina kamar yadda zaki zauna itama haka zata zauna..Kuma da kike mganar Ita ba sa'an aurena bace..Daman sai sa"an auranka zaka aura..? Wlh in da ana bin chanchanta har Abada Dake sakina baki CHANCHANTA dani ba..! Yafada yana nuna ta da yatsa cikin fushi ido ta zaro mgana take son yi ya hanata Cikin Kaushinsa yace"Ba shawara nake nbaki ba..ba kuma Umarni ba.ki natsu ki zauna lafiya da yarinyar nan domin zamanta Daram acikin gidanan in kika ki natsuwa ke kika sani ni dai tafiya zan yi..in kin kama girmanki ta girmamaki in baki kama ba ta fiki iskanci sai ku goga wata dai bata isa ta kori wata ba..! Sakina taji jikinta yayi sanyi me kalaman Umar suke nufi..!? Gabanta ya fadi kada kishinta ya Bullo mata wani sabon aiki Dakyar ta Hadiye miyau tana Sharan kwallah tace"To don Allah in ka tashi tafiya ka tafi dani Habibi..wlh bazan iya zama da yarinyar nan anan gidan ba..! Umar ya kalleta daga sama har kasa kafin ya koma ya kwanta yana Fadin"Sakina na yi rantsuwan bazaki koma ba yanzu Ki tashi ki bani waje bana son yawan mgana kaina ya riga ya fara ciwo..Kada zamanki agabana yasa na rasa Control dina..! Batayi musu ba ta mike Cikin kaushinsa yace"Ki kashe min hasken da kika kunna min..! Ta juyo tana kallonsa kafin tace"Bazaka ko..! Kallon da ya bita dashi ne yasa tayi Saurin yin gaba Hasken ta kashemai ta Fada Dakinta gabanta na Fadi Gabadaya mganar Umar na ita ma bata Chachanta dashi ba ya Tsorata ta In ta Kira Anty ta Fadamata tasan sai taci Zagi Allah yasa ba abunda suka Binne bane yake son ya bayyana ba.. Da sun shiga uku kuwa..! Mafarin komai in ya lalace ai sun gama yawo..! *28 September 2022* *Janafty* *TFZB2002* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Karfe hudu na asuba ya farka kamar yadda ya saba,Kwata kwata bai ji dadin barcin ba akan kujera sannan zuciyarsa tana cunkushe ne ya dade bai samu barci ba kuma kasala ya rufeshi ya kasa tashi yayi ko nafila ne. Sai da asuban ya shiga dakin nasa yayi wanka ya dauro alwala Jallabiya mai ruwan madara ya saka da Hula ya Dau cashabahansa ya fice zuwa masallaci ko ta kan Sakina bai bi ba ballatana wata Amina. Sai shidda saura ya shigo gidan,yana shigowa tsakiyar falon suka ci karo da Sakina ta fito daga dakinta yarkace yarkace da ita idanuwanta sun kumbura sannan kanta ba dankwali kanta ba kitso gashinta ya baje kansa tana sanye da rigar barci mai taushi iyakarta gwiwanta ayanayin yadda yaganta sai da ya kara kallonta ganin yanayinta. Kamar zai mata mgana sai kuma ya fasa ya dauke kansa zai shiga Dakinsa Da hanzari ta daga kafa zata bisa jin takunta yasa ya Dakata bai juyo ba taji muryansa yana fadin"Ina zaki..? Cak ta tsaya jikinta yayi sanyi kanta ta maida kasa kafin tace"Da..Dama zan gaisheka ne Habibi..! Shuru yayi mata bai yi mgana ba taga yana shirin shigewa ya barta yasa tayi saurin cewa"Ina kwana Habibi..! Kamar bazai tankata ba sai kuma ya amsata kamar baya so da Lafiya Lokaci daya ya shige dakin nasa ya banko mata kofa saman fuskarta baya taja Hannunta Dafe da kirji tana fadin "Na shiga uku ni Sakina..! Kasa tsayuwa tayi kamar mahaukaciya haka ta kwashi gudu zuwa Dakinta saman gadonta ta koma ta Zauna gabanta na fadi meta aikata kenan .?Jiya ko barci batayi ba in ta tuna Kalaman Umar zuwa gareta. Taso ta kira Anty tun jiyan sai ta kasa Tasab Halin Anty in taji abunda ta aikaata sai ta Zageta saboda haushi Saboda sai da ta tausheta akan kada tayi wani abu sai ta tambayeta yanzu in ta Kirata ta fadamata abunda ya faru ta tabbata sai Anty ta mata fada sosai. Sai dai bata da wata mafita Anty zata kira ta fadamata abunda ke faruwa ko zata samamata mafita. Wajen shidda da rabi ta dokama Anty Amarya kira tun da taga kiran tasan ba Lafiya cikin Tashin hankali ta Daga kiran tana fadin"Sakina kada ki fadamin kin kara aikata sakarcin naki ..? Sakina tafara Fiki Fiki da ido tana fadin"Anty...! "Don ubanki ki fadamin abunda ya faru..! Sakina cikin sanyi ta fara fadamata Duk abunda ya faru jiya har zuwa yau Anty Amarya ta mike Har hijabin jikinta datayi sallar asuba na neman Hardeta ta fadi ta Dafe jikin gadonta Cikin Firgici tace"Kikace Umar da kansa yace baki Chanchanta dashi ba..!? Sakina tace"Wlh haka yace Anty..! Anty Amarya bakinciki suka kusa kasheta alokacin cikin Tsawa tace"Sakina na rantse da wanda Raina ke hannunsa in kishin ki na banza yayi sanadiyar Tono Abunda muka Binne da Dadewa babu ruwana..zan zame kaina ne na barki ke kadai..Kin kuma Tabbatar ma kanki wannan kokawar tafi Karfinki..! Jin haka yasa Sakina ta kara Rudewa kawau sai ta saki kuka tana Fadin"Anty don Allah kiyi hakuri..Ba laifina bane..Kishi ne ya rufemin ido kinsan ina son Umar bazan juri ganinsa da wasu matan ba..Sannan Aliya tacemin kada na barta ta zauna Dakin Mijina..! Anty Amarya ta lailayo Ashar ta saki kafin tace"Aliya Burauban ki Sakina..Ina ruwanta da wannan mganar ban fada miki kada kiyi wani yunkuri sai nace ba..? Da kika kwantar da hankalinki Lokacin Sakaryan balarabiyar nan ba gashi yanzu muke da riba ba..Itama in kin kwantar da hankali kamar haka zata zama nayi alkawarin ko zan rasa komai Amina bazata yi zaman kishi Dake ba Sakina ammh shegen Taurin kan ki yana neman jawo mana matsala..! Sakina na sharan kwallah tana Fadin"Nidai Anty ki fadamin ya zan yi..?Wlh ko son ganina bai yi ina mgana Dakyar yake amsa mun..! Anty Amarya tace"sai kin bata komai kizo kina Damunna da kukan banza..Yanzu ina ita Aminar..? Sakina ta tabe baki kafin tace"Tana chan Dakin Sarood..Tun jiya bansan isalinta ba..! Anty Amarya tace"Shi kuma fa..? Sakina tace"Ya dawo daga masallaci ya shiga Dakinsa ya kulle..! Anty Amarya tace"To ki tashi ki shiga kitchen ki hada breakfast ki yi wanka da kwalliya kije ki tasosa ki basa Hakuri..Mganar Amina kuma kada ki shiga mganarta ki koma gefe ki zama yar kallo kawai a na nan ana aiki akanta kin ji ko..? Sakina ta gyada kai kafin tace"Anty Dakyar ya Saurareni fa..! Tsaki Anty Amarya taja kafin tace"To Tunda bazai Saurareki ba..ki Zauna..! Daga haka ta katse kiran tana Huci ita Kadai adaki Sakina fa Bata san ciwon kanta tasan kudin data kashe kafin Umar ya kalleta da sunan so..? Tasan wahalan data sha kafin Umar ya kalleta da kalmar aure..? Batasani ba shiyasa take son bata komai ba bazata yi wannan saken ba in abubuwa suka fara Lalace mata bata samu Cikar Burinta ba anyi ba ayi ba kenan ko zata rasa komai sai Sakina ta zama Tauraruwa awajen Umar da danginsa gabadaya Wata mace bata isa ba kuma tayi kadan. Ashe Sakina duk zaman data ke yi batayi sallah ba,Sai da suka gama waya da Anty tatshi ta Dauro alwala tayi sallah sama sama ta Daura Zani saman rigarta ta fita zuwa Kitchen,Sakina ta iya girke girke Anty Amarya bata barin ya"yanta haka tasan duk cikar ya mace in bata iya Girki ba Saura ce shiyasa ba wacce bata koyama girki ba hatta da Sa"adatu da Sabeeha..! Cikin Hanzari take aikinta Cikin Lokaci ta kamallah Doya ta Dafa sai tayi miyar kayan miya ta yayyanka mai kwai,Sai ta Dafa Ruwan tea ta soya Buredi da kwai saman Dinning ta jera komai kafin ta gyara Kitchen din sannan ta koma Daki ta shiga wanka. Bayan ta fito ta shirya Cikin Doguwar rigarta ta atamfa ta gyara gashinta tayi Daurinta na Maryam babangida..! Gabanta fadi yake bata san wani Tarba Umar zai sake mata ba ta zata Ya kulle kofar ne sai da ta Tura taganta a Bude Cikin Takunta na Takama ta shiga Dakin da sallama sanin Halinsa yanzu sai ya maidata waje. Yana zaune a kasa saman Darduma yana karatun Qur"ani a hankali cikin Sautinsa mai Dadin Sauraro Dakin tabi da kallo komai neat,Gado ne kawai sai wardrope sai ma"ajiyar takalma sai cafet babba da ya malale Dakin gefen gadon ta zauna tana Jiransa ya idar da karatun ammh wajen Minti Goma sha biyar bai rufe karatunba sai ta fahimci in tayi shuru to sai rana ta Dago zai tashi daga wajen nan. Gyaran Murya tayi kafin tace"Ina kwana..Wajen ka fa nazo Habibi..! Ta karishe Fada Cikin shagwaba. Yana jinta yayi kamar bai ji ba sai da ya kai inda yaga damar Tsayawa sannan ya rufe Qur"ani ya Daga hannu Sama yana addu"a tare suka shafa ya mike ya ijiye Qur"anin saman Side drower din gadon,Yana kokarin Ninke Darduman ne tayi saurin mikewa ta karba bai hanata ba ya sakarmata Ta ninketa ta maidata wajen zamanta tana gani ya hau saman gado ya kwanta harda juya mata baya. Bata damu ba ta Durkusa saman kafafunta tana fadin"Don Allah kayi hakuri Habibi..Da abunda ya faru sharrin Shedan ne da kuma Kishi.. Ammh nayi alkawarin bazan kara ba..! Kaji..! Kamar bazai tanka ba sai chan taji yace"Zaki kara Sakina..! Da sauri tace"Allah bazan kara ba..! Ajiyar rai ya sauke kafin ya juyo yana kallonta Lokaci daya yace"Ya wuce..! Mirmishi ta saki kafin tace"Nagode..Ga breakfast chan na gama Hada maka ka taso muje ka karya..! Lumshe ido yayi kafin yace"Am ok..Bana jin yunwa..! Marairaicewa tayi tana fadin"Haba Habibi..Ko baka hakura bane..? Da Sauri yace"Bani da riko kema kin sani..! Jin haka yasa tace"To in hakane ka taso muje..abunda kafi so na Dafa maka Doya..! Muskutawa yayi ya mike zaume yana Fadin"Naji..Zan yi wanka ne ganin nan fitowa..! Taji dadi sosai ta mike tana Fadin"Bari na taimaka maka Habibi..! Duk yadda yaso ya yakiceta bata yarda ba Tun yana kin sakin mata har ya sakarmata ita ta taimakaima ya Cire kayansa ta hadamai ruwan wanka ya shiga yayi wanka daya fito ta taimakamai ya shirya Cikin Riga da wando na pakistan sannan ta Tarosa Hannunta Cikin nasa zuwa Falon har saman Dinning jikinta na rawa ta yi Sarving dinsa kallonsa tayi tana zubamai Ruwan tea din dayaji Ganyen shayi masu kamshi tace"Kana so da yawa ne Habibi..? Kai ya girgizamata kafin yace"Rabin kofi..! Haka kuwa ta sakamai ta Turamai gabansa baya son madara siga ya kara kadan ya fara sha Bai san yana jin yunwa ba sai da ya gansa gaban abinci Rabonsa da abinci tun jiya da rana.. Ita Tea ta hada maa kanta tana Hadawa da Buredi da kwai shi kuma yana cin Doya daman mutuniyarsa ce. Ranta yayi mata Fes ganin ya sauko har suna dan mgana jefi jefi Shine ma yace mata"yana da kyau in ana cin abinci a Dakata da mgana har sai an kamallah..! Daman sai yayi mgana bai cika son tana mai mgana in suna cin abincin ba yasa tayi shuru tana kurban tea tana kallonsa shima kuma in ya Dago suka hada ido sai yayi mata Yake kawai. Sai da ya kusa gama cin abinsa sannan Amina ta fadomai arai kamar ya Tuna da wani abu ya Dakata da komai yana kallon Sakina Cikin wani yanayi yace"yarinyar nan ta fito kuwa..? Wani irin Kallo tayi mai kafin tace"Wata yarinya kenan..? Yadda ya kalleta ne yasa tayi Saurin gyara mganarta da cewa"Bansani ba..Nidai ban ganta ba..! Tsam yayi yana wani Tunani bata ci abinci ba,Ba domin yadda Hajiya da maallam suka saka shi a Tsakiya ba da sai yace ta Dauwama adakin ai yunwa ba"a mata iskanci sai dai in ya kyaleta Allah zai kamasa kuma Hakkin mallam da Hajiya na wuyasa..! Tuna haka yasa ya kalli Sakina kafin yace"je ki kiramin ita..! Ido ta Zaro kafin tace"Ni kuma..? Kai Tsaye yace"Eh ko bazaki ba..? Jin haka yasa tace"ban ce ba..! Tashi tayi tana Tura baki ta wuce ya Bita da kallo daman yasan lambo Tayi Sakina ai bazata Daina Halinta ba. Afusace ta Buga kofar ta shigo Tana bin Dakin da kallo lokaci daya tana wani yamutsa Fuska nan kasan Cafet ta Hango Amina ta Dunkule waje daya acikin Hijabinta,Ga ghanas dinta nan inda ya ijiyemata ko kauda su batayi ba Ranta ya kara baci Cikin kufuluwa tace"Kee...! Cikin Tsswa Amina bata jita ba Domin barci ne na wahala ya kwasheta bata sani ba Jiya yadda taga rana haka taga Dare bazata kwatanta kwana awajen da ba Hanne ba Hamida ba bata taba tsamanin wannan ranar ba ballatana ta Shiryama zuwanta Tunda ta shigo Dakin ta zube anan kasan Cafet ko motsi bata karayi ba tayi kukan har ta gaji ga Tsoro Daki ita kadai abunda bata saba ba,Bata iya barci ba Tsoro da Fargaba da kewa basu barta ba Dakyar ta Rarrafa da Asuba ta shiga Toilet din Dakin tayi alwala tazo ta Rama Sallar Isha"in da ake Binta jiya da kuma Sallar asuba shine fa tana nan zaune bata ma san barci ya kwasheta ba. Sakina jin tayi banza da ita kuma taki Motsi yasa ranta ya baci a Tunaninta da gangan tayi mata yasa ta isa kusa da ita ta saka kafa ta Shureta daya sa Firgigit Amina ta farka Daman a Tsorace take cikin muryanta da Bata Fita sosai saboda kuka tace"Wayyo..! Sakina ta saki Tsaki kafin tace"Baki ce wayyo ba sai nan gaba..Badai kin ce dani Zaki kishi ba yarinya..Ai wayyo Salamu Alaikum..! Amina ta bita da kallo da kumburarrun Idanuwanta Hancinta ya Toshe da majina sai ja take ga kuka ga sanyin Dakin Domin A.C a kunne kuma fanka ma haka ita kuma bata yi Hausan tashi ta kashe su ba. Sakina ta koma da baya tana mata wani kaskantattacen kallo kafin tace"Kazama kawai..Sai ki taso yana kiranki..! Amina ta kalleta da mamaki kafin tace"Shi wa..? Cikkn Shakewar murya Sakina ta ga tama raina mata wayau yasa ta juya tana fadin"Uban ki ba..! Amina ta bita da kallo har ta fita itafa bata gabanta ita yanzu kokuwa take da wannan Sabuwar rayuwar shiyasa Zagin Sakina bai ma Dameta ba kamar bazata je ba Domin jiri take gani in ta mike ammh Tuna Kalaman ya Danmallam yasa ta mike jiri na Dibanta ta fice Daga Dakin zuwa Falo Daidai sanda Sakina taja kujera ta Zauna Dammallam na zaune bai ce mata komai ba sai ga Amina ta fito tana Layi Cikin hijabinta kamar zata fadi Daga nesa ta Tsaya tana kallonsu kafin tace"Gani..! Daga sama har kasa yake kallonta alamu sun nuna ko mai yarinyar nan batayi ba tunda ga jiya kenan ganin yadda Fuskarta ta Kumbura ne ya bashi mamaki Sakina kuwa Kamar ta yi Tsaki haka taji da taga yana kare ma Amina kallo bata ma lura da kallon kyama yake binta dashi ba..! Saboda mugunta sai da tafi minti Goma a Tsaye tana neman faduwa sannan yace"kizo ki ga abun kari nan.! Amina da Tagaji da Tsayuwa tace"Ni na koshi..! Ko kallonta bai yi ba ya maida hankalinsa wajen cin Doyansa Sakina ta juya tana kallonta ta Harareta bata ma ganta ba ta juya tana Faman Kama Hijabinta ta koma inda ta Fito nan inda ta baro ta koma ta zauna ta Hada kai da gwiwa ta fara Rera sabon kuka Allah sarki sai yanzu ta kara Tabbatama da kanta da cewa tayi maraici tazo inda ba mamanmu ba Hamida ba Hanne,Wadanda sune ita in basu Rayuwar Amina bazata taba cika ba Aminu ne ya fado mata arai ko wani Hali yakeciki..? Tasan da shi ta aura ta tabbata zai lallasheta zai mata komai Saboda yana sonta ammh kalli inda Kaddara ta kawota inda ba"a san Darajanta ba Daga megidan har matan gidan basu da Imani Allah ya isanta wlh bazata taba yafe musu ba mugaye kawai..! Tun daga Lokacin Amina ko motsinsu bata sake ji ba tun tana Daurewa har ta kasa Cikinta ya kulle yunwa take ji ga jiri ga rashin barci sai mulmula take saman cafet dafe da Ciki tana faman kuka ita kadai Zata mutu acikin wannan gidan wayyo ita Amina..! Umar kuwa agida ya wuni bai Fita ba sai da yammah da ya kira Jafar yazo suka hadu shima iyakarsa haraban gidan bai shiga b,Mganar Visa dinsa sukayi so yake cikin satin nan ya koma Madina bazai iya sake wasu kuma kwanaki ba,gabda mangariba Jafar ya tafi shi kuma Daganan masallaci ya wuce sai da akayi sallar Isha"i ya dawo ya iske Sakina tayi sabon wanka bayan ta gama girki ta gyara gidan yana tashin kamshi Sai ransa yayi fari,Yana son Sakina saboda Tsabtarta,sannan uwa uba kuma kwalliya,yau din ma ta tsuke cikin Riga da wando,ko Dankwali bata saka ba gayu take ji yau din,Ko bai yi mgana ba tasan ya yaba tunda yana ta kallonta yana mirmishi. Abincin mara nauyi tayi musu Faten Dankwalin Turawa da hanta sai Coffea data hada musu tare suka zauna suka ci abincin su kafin su dawo Falo su zauna Sakina ta Dora kanta saman cinyar Umar shi kuma yana wasa da gashinta,Hankalinsa na wajen kallo a tashar Sunna Tv Qur"an,sakina kuma har ta fara barci bata damesa da mgana ba sanin Halinsa hira in ya sota suna yi bai so ba kuma baya son ana damunsa Duniya ta mata sabuwa yadda taga ya manta da Halittar Amina acikin gidan Kamar wasa wayarsa ta Dauki Sautin kidan Larabawa Sakina ta Bude ido tana fadin"Habibi kamar ana kiran wayarka fa..! Chan saman dinning ya barta da sukaci abinci,Yasa ya Daga kansa yana Fadin"itace..! Mikewa tayi tana fadin"Bari na Dauko maka..! Sanda ta karisa ta Dauko wayar sai da gabanta ya fadi ganin sunan mallam,sai da Annurinta ya Dauke tsayawa tayi har wayar ta katse jin ta Shuru yasa ya dago yana kallonta kafin yace"Waye ke kirana..? Sakina ta kariso ta mikamai tana Fadin"Mallam ne..! Gabansa sai da ya fadi ya karba da Sauri Lokaci daya yana fadin"Dauke min karar nan..! Ba musu ta Dauki Remot tayi kasa da Volume din shi kuma yabi bayan kiran Mallam Da sallama mallam ya daga Kiran Umar ya zamo daga kan kujera kamar yana gabansa yace"ina yini mallam..? Mallam na zaune afalonsa Gefensa Hajiya ce yaa amsa yana fadin"lafiya lau Umaru ya wajen iyalan naka..? Ya amsa da lafiya kalau kansa na kasa kamar yana gabansu Sakina na kallonsa ta gefen ido a duniyar nan Umar na bala"in ji da mutanen nan guda Biyu mallam da Hajiya na ukun su kuma wannan Mayen Baba Sa"idun inyana mgana dasu kamar ya kwanta musu saboda Biyayyah..! Mallam yace"Masha Allah..lafiya yau baka shigo anguwan namu ba..? Nace to bari na kiraka naji Allah yasa ba Rigiman me sunan mamana bane har yanzu bata bari ba..Domin yanzu nan yan"uwanta suka tashi daga nan tun jiya suke kuka ko makaranta ba su je ba suna ta koke koke sai da na kira su yanzu nayi musu nasiha na lallashesu da cewa su bari tayi ko sati Daya ne sai suje su mata yini..! Danmallam yayi shuru bai yi mgana ba Mallam ya gyara zama yana fadin"Ina ita maman tawa..?ina fatan ta Daina kukan ko..? Danmallam kansa na kasa yace"Eh ta bari Baba..! Runtse ido yayi yayi karya Domin bai san ko ta bari ba.. Mallam yace"Madallah Sai kayi hakuri Umaru kaji ko..?Mamana yarinya ce karama yanzu bata da kowa sai kai..Kai zaka zama mai mata Tarbiya Tunda ta bar karkashinmu..In tayi ba Daidai ba kamata nasiha cikin jan hankali,Duka ko Tsawa basa gyara Tarbiya jan mutum ajiki da nuna mai so shi ke sa ya rage wasu abubuwan..Don Allah Umaru ka kula da Mamana..itace karama acikin matan ka ba lalle ta kai su wasu abubuwan ba..ku rika mata uzuri in ta aikata wani abun Umaru..! Kansa na kasa ya gyada kai kamar Mallam na ganinsa kafin yace"Insha Allahu..! Mallam ya cigaba da fadin"Ina ita abokiyar zaman nata..?fata dai ba wata matsala..?? Cikin Ladabi yace"Babu mallam..! Mallam ya jinjina kai kafin yace"Dakyau itama Saratun nayi waya da Mahaifinta namai bayanin komai har ita nace abani nayi mata Nasiha sosai..ina rokin Allah ya hada kanku..Sannan kai kuma Allah ya baka ikon yin Adalci..! Umar ya amsa da Ameen Ameen daganan yayi shuru kafin yaji mallan yace"Ina ita maman tawa..! Ko tayi barci ne..? Umar ya runtse ido murya kasa kasa yace"Eh..! Mallam yace"To shikenan Allah ya zaunar daku lafiya..ga Hajiya nason mgana Dakai..! Bai gama zufan karyan daya yi ma maallam ba Hajiya ta karbi wayar suka gaisa kafin tace"In fatan Amina taci abinci kafin ta kwanta..? Dakyar yace"Eh Hajiya taci..! Kai ta kada kafin tace"Shikenan ka kula da ita kaga dai yarinya ce..Wlh ban yarda ka hada kai da matanka ku cutar da ita ba..Domim ba sa"ar su bace..! Yana jin Hajiya bai iya mgana ba ta cigaba da fadin"Ina mganar mu ta kwana..? Sannan yaushe zaka koma..? Kai Tsaye yace"Ina so cikin satin nan Hajiya Visa na nake jira..! Hajiya tace"Kake jira..?Ita Sakinar fa..? Kai Tsaye yace"Nan zan barta..Sai na Sake dawowa..! Hajiya ta bude baki tana kallon mallam shima yana kallonta kafin tace"to ka dai samar ma Amina wajen zama domin na fada maka da ita zaka tafi in har ka sake dawowa..! Insha Allahu yace mata,Sannan ta cigaba da fadin"Mganar karatunta da islamiya da Boko zata cigaba da zuwa..ammh nace ta huta na sati Daya..Idi Direba in ya Dauko su hanne Daganan zai biya ya Dauketa in suka Dawo ya sauketa agida sai sun dawo islamiya sai ya maidata gidanta..! Shi dai nashi dan bi ne yasa yace"Duk yadda kika ce haka za"ayi hajiya..! Hajiya tace"Shikenan..Allah yayi muku albarka gabadayanku..! Ya amsa da Ameen Ameen yana fadin Allah ya kara girma. Daganan sukayi sallama ta katse wayar,Sauke wayar yayi ya koma ya Jingina da kujera yana Neman yafiyar Allah yayi ma iyayensa karya karo na Farko arayuwarsa..! Sakina kuwa kallonsa take yi Ta gama Sarewa tunda taji yama Furtama Hajiya bada ita zai koma ba Tabdijam akwai Daru in dai ita da kazamar yarinyar nan zasu zauna awaje daya..! Mamaki ya kamata Da taga ya mike Tsam cikin Mamakinsa tace"Habibi badai barci ba ko..? Kai Tsaye yace mata"A"a..! Bata gama mamaki ba taga ya nufi Dakin da Amina ke ciki har Lekasa sai da tayi gabanta na faduwa ita dai bataji me mallam da Hajiya sukace mai ba ammh tabbas suna da alaqa da Shigarsa wajen Amina komawa tayi ta Zauna tana girgiza kafa tasan halinsa da sai tabisa Dakin taga abunda zai mata.. Shikuwa kai Tsaye ya Tura kofar Dakin ya shiga da sallama,Sai dai sallamansa ta makalene daya ci kusa cin karo da Amina Da azaban yunwa da ciwon ciki yasa ta gangaro har kofar Dakin,Baya yaja da Sauri yana kallonta Lokaci daya yana karema Dakin kallo hatta jakunkunarta yadda ya shigo dasu haka suke kofar Bayi a Bude ta barsa tana nan cikin Hijabin nan ko wanka yana da Tabbacin batayi ba ga ruwan hawaye nan da majina duk ya bushe mata abaki batama san ya shigo ba kwance take hannunta Dafe da Cikinta kamar mai barci Ransa ya baci da wannan kazantar,wlh ba domin mallam da Hajiya sannan kada Allah ya kamasa da Laifin Saba musu ba bazai leko Dakin nan ba kamar ma Zarnin Fitsari nan da nan yaji zuziyansa ta fara tashi toshe Hanci yayi da hannunsa kafin yace"Ke...! Kamar a mafarki taji muryansa da Sauri ta Bude ido suka hada ido harara ya sakarmata kafin yace"Miye haka..?Tashi zaune..! Da Sauri tatashi Ta koma ta Jingina da gado sai hawaye kamar an Bude Famfo. Cikin Bin Dakin da kallo yace"Fitsarin kwance kikayi..!? Bata kallesa ba ammh aranta sai da tace ita bata Fitsarin kwance ammh a sarari sai ta girgizamai kai Cikin Takaici yace"Baki da baki ne..? Muryanta a shake tace"A"a..! Kallonta yake yi yana kauda kai kafin yace"To zarnin nan da nake ji daga ina ne..? Kanta na kasa ta kasa mgana Tsawa ya Daka mata kafin yace"Ina mgan kina jina ke kurma ce..? Da Sauri tace"A bayi ai nake yin Fitsarin ..! Sai kuma ta sakamai kuka karamin Tsaki yaja kafin yace"Banda kina kazama a ina aka taba yin Fitsari ba"a kora ruwa ba..Sannan a kasan tiolet din kike tsuggunawa kina yi bakya hawa Sit din..? Kai ta gyada mai alaman hakane ransa ya kara baci kafin yace"Kin ma yi wanka..!.? Nan ma tace "A"a..! Ya kara kallonta kafin yace"Lalle kazantarki ta shahara..! Ya sake bin kayan ta da kallo kafin yace"Wadanan kayan fa..?waye zai kauda miki..?Ke banda kazanta baki iya komai bane..? Nan ma kai ta gyada mai cikin mamaki yace"Eh fa kikace..? Sai ta kara Saka kuka cikim kukan take fadin"Ni ban iya ba..agidama Hamida take min ko mamanmu..! Galala yayi yana kallonta aransa yana Auna yadda aka gurgurta rayuwarsa da aka auramaaa wannan yarinyar. Kofar Tiolet ya nuna mata yana fadin"Maza tashi ki shiga ki sa ruwa ki wanke zarnin fitsarinki..Sannan ki Tabbatar da kin yi wanka sannan kizoki Sauya kayanan dake jikinki..! Kasa tashi tayi sai da ya Daka mata Tsawa sannan ta mike jikinta na rawa cikin Haushi yace"Dilla cire wannan Hijabin sai wari yake..Tun jiya abu na Jikin ki baki cire ba saboda kazanta..! Bazata iyamai musu ba na farko tana Tsron Rashin Imaninsa na Biyu kuma mganar Aba Dayace in tayi mai gaddama bai yafe mata ba. Hijabin ta cire ta Tsaya Tsumi tsumi tana kallon kasa tiolet din ya nuna mata yana fadin"Oya shiga..! Tafiya ta farayi sai jiri ya kwasheta zata Fadi da hanzari ya saka hannu ya Rike hannunta kafin ya saketa ta Fada,kan gado Cikin mamaki yake kallonta tana kuka tana Dafe da Cikinta tana fadin"Wayyo Cikina..! Kai Tsaye yace"Yunwa ko.? Kamar tana jira ta dagamai kai yar Dariya yayi kafin yace"Ai ita yunwa ba"a mata iskanci..Duk Taurin kanki ai gashi nan ta koya miki hankali..! Tsaki yaja ya fice Daga Dakin ta bisa da kallo aranta tana addu"a da Fatan Allah yasa abinci zai kawo mata domin ta kusa rasuwa..! *Janafty* *Janafty* *20/09/2022* *TFZB2003* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Sakina na zaune inda Umar ya barta taga ya sake fitowa cikin mamakinta sai taga ya nufi Dinning ya Dauki katon mug ya tsiyaya ruwan tea ya saka madara da Milo sai siga bata iya shuru ba sai da tace"Habiba yau kuma Tea zaka sha da madara..? Saninsa tun abaya madara bata wani Damesa ba,Bai mata mgana ba taga ya Dauki mug din ya nufi Dakin da Amina take wajen kallonsa kadan ya Rage bata fado daga kan kujera ba sai da taga shigansa sannan ta maida kallonta acikin ranta tana fadin kan uba..! Shi kuwa yana shiga ya iske Amina inda ya barta kwance tana numfashi Sama sama,Kai tsaye yace"Tashi zaune..! Ba musu ta mike tana wani karya wuya saboda yunwa mikamata Kofin yayi ta karba tana wani lankwashewa Cikin bada Umarni yace"Shanyesa yanzu..! Ba musu ta kafa kai ta fara sha Jikinta da Hannunta na rawa Lokaci Daya yana tsaye ya jingina da wardrope din Dakin yana Binta da kallo ganin yadda jikinta ke rawa yasan taci Ubanta da yunwa yaji dadin haka shifa Tana cin Darajan masu Daraja ne ammh ba domin haka ba ko zata mutu ne bata isheshi kallo ba wlh. Duk da kyamkyamin Dakin dayake yi bai fita ba yana Tsaye yana Nazarinta Abun dariya ya basa Daya ga karamar kafarta Dauke da Jan lalle tare da Hannayenta wai nan shi akayi mawa ko. ? Shi allah kada ya nuna mai sanda zai kula wannan yarinyar wacce bakomai acikinta sai iskanci da rashin kunya. Yana wannan Tunanin baisan tashinta ba sai kakarin amai da ya jiyo a Tiolet lekata yayi yana fadin"Ke miye haka..? Amina na Duke daga cikin Tiolet tana maida numfashin wahala tace"Cikina ne ke juyamin..! Tafada tana kara Dafe Cikinta Saboda yadda yake Hautsina mata Ta Dade bataci komai ba shiyasa Dan mallam karamin Tsaki yaja bai yi mgana ba Sai ga Amina ta fito tana layi ta sake fadawa saman gadon Cikin mamaki yake kallonta ganin harta gaban Riganta ya fara baci da amai haka gefen bakinta zuciyarsa yaji ta Fara tashi yayi saurin matsawa baya yana Fadin"Ke meyasa kin cika kazanta ne..? Aman da kikayi wa zai wanke miki..?Sannan ji bakin ki da gaban rigarki duk amai baki da Hankali ne..? Ya karishe fada yana kauda kansa Sabida bayason kallonta kyama take basa ita kuma ga ciwo ga fadansa kawai sai ta fashemai da kuka tana Fadin"Nifa banda lafiya in na mike jiri nake gani..! Daure Fuska yayi yana fadin"To ba anan ba maza mike ki wuce Tiolet ki Tabbatar da kin wanke kazantar ki sannan ki tube kayan jikin ki,kin yi wanka..Wlh kada ki bari na Dawo na iskeki a haka ranki zai baci..! Kukanta ta karama Volume tana fadin"Wlh bazan iya ba..! Tsawa ya Dakata mata Lokaci Daya yana Fadin"Zaki tashi ki wuce ko sai na saka miki hannu..?Tunda kika zo gidan nan kike sakani mgana ki yi abunda nace tun kafin na yarda da Shawaran zuciyata na kaiki inda ake gyaraama irin ku zama..! Ai bai gama mgana ba Amina ta mike tana Kuka ta shige Tiolet din Kamar ta Fadi Jikinta ba karfi Tsaki yaja ya Fice aransa yana Jinjina kazanta irin na Amina bai taba Zaton haka take ba. Sakina ta na nan inda ya barta Tana jiran fitowarsa,kusa da ita yaje ya zauna yana sauke numfashi sai yanzu yaji ya shaki iska ammh Dakin chan wlh ba yanayi mai Dadi ganin yadda ya Zauna yayi ne yasa ta gyara zama tana Fadin"Meya faru Habibi..!? Bai kalleta ba ya mike yana Fadin"Abinci ya yi saura..? Cikin mamaki tace"Menene..? Yana Tafiya wajen Dinning yace"Zuba ma yarinyar chan a filet ki shigar mata dashi..Sannan Daga yau ki rika Dafa abinci da ita kin ji ko..? Sakina kadan ya Rage bata Danna ma Umar ashar ba sai ta Tuna mijinta ne ammh sai da ta Hararesa kafin tace"Nine ma zan rika girka mata abinci ina aika mata Dashi Daki ko..? Kai Tsaye yace"Haka nace..! Sakina ta kallesa Daga sama har kasa kafin tace"Saboda wani Dalili..? Ka manta kai kace Matsayina da nata Daya ne..? Bai son doguwar mgana yasa yace"Saboda ita yarinya ce..Kuma Amana ce a wajenmu..! Sakina ta yi shewa kafin tace"yarinya kuma suka aura maka ita..? Amana kuma ai takace ni dai ba wanda ya bani wata amana..! Gani yayi zata raina masa wayau yasa yace"Su wa kike mganar sun auramin ita cikin Raini Sakina..? Yafada yanayinsa na sauyawa ganin haka yasa tayi saurin cewa"Ni fa ba su nace ba..kawai dai kai ma baka taki adalci ba..Zan Dafa abinci ammh wlh bazan Dafa mata na Bita dashi adaki ba in ta fito shikenan in bata fito ba ita ta sani..! Tana gama Fadin haka ta Mike Dauke da wayarta zata shige Dakinta ya Daga Muryansa yana fadin"bazaki zuba mata ba kenan..? Juyowa tayi kafin ta kallesa Duk da ta tsorata da yadda ya Hade ransa ammh wlh bazata zauna tana Boyin boyin Amina ba, yasa kai Tsaye tace"Eh..Kai ka zuba ka kai mata tunda ta zama Dolenka ammh bani Sakina ba..! Daga haka ta shige ta barsa ya bita da kallo bayason Fitina ne yasa bai bi ta kanta ba ya isa ga kular abinci ya Dauki Filet ya Bude ya zubama Amina Daidai ya rufe ya Daukar mata Ruwan gora guda Daya mganar Mallam kawai yake tunawa yasa zai taimaketa kada Cutar yunwa ta mata Lahani fatansa Visar  sa ta fito wannan Satin ya saka kafa ya tafi sai yaga karyan iskanci daga ita har Sakinan sai su kashe junansu shi ba ruwansa. Sanda ya koma Daki tayi wanka sai dai abun haushi kayan jikinta ta maida nan kasan Cafet ya ijiye kayan hannunsa yana hararanta  kafin yayi mgana ma ta mike jikinta na rawa tana fadin"Ban..baga kayan bane..! Ghanas dinta ya nuna mata yana Fadin"Ai kinsan kayanki ne acikin nan ko suma sai na ciro na saka miki..? Da Sauri ta girgiza kai ta wuce sumi sumi wajen jakunkuna ta Duka ta Bude Daya taga Littafan makarantar ne aciki sai da ta Bude Dayan ne taga kayan a goge sai da tayi hawaye tasan aikin Mamanmu ce ko Hamida aranta tace Allah sarki Hamida da hanne ina kewarku..! Wata Doguwar riga ta Dauko na Material sai bakin dankwali,zata maida ta rufe yace"Ciro wani Hijabin ki Cire na jikin ki malama..! Ba musu ta ciro aranta ta kudira ta gama mai gaddama gashi mara imani ga mganar Aba ayadda take din nan bata fatan ta kara yin wani abun da Aba zai yi Tir da ita,Tayi alkawarin har Abada an dai kaimasa kararta. Kayan ta Dunkule Cikin Hijabinta ta gabansa ta wuce zuwa Tiolet chan ta Sauya kayan ta Sake fitowa da na hannunta yana Dakin bai fita ba ganin zata maida masu Dattin Cikin jakar yasa yace"ke wai meke damun ki ne..? Masu dattin zaki maida Ciki kuma..?Common maida su Tiolet akwai kwando Dogo ki saka aciki nan zaki rika tara kayan Dattin da kika cire..! Sumi sumi ta koma ta saka a inda yace sannan ta kara fitowa abinci ya nuna mata yana fadin"Ki zauna kici..Wannan shine na karshe da zan kawo miki abinci ruwanki ne ki Fita ki nema ruwanki ne ki zauna da yunwa..Kin ga dai ishara ko..?,Ita yunwa ba"ayi mata Taurin kai..! Ba musu ta zauna Daman yunwar take ji dan Tea din Data sha ta Amayar dashi kama hanyar fita yayi kafin ya Juyo yana kallonta har taja Filet din gabanta Hararanta yayi ta kasan ido take kallonsa kanta na kasa cikin Sanyinsa yace"Ki tabbatar kuma kin sanya duka kayanan cikin wardrope bna so na kara ganinsu anan wajen kin ji ko baki ji ba..? Da kai ta gyada mai kafin tace"To..! Bai kara mgana ba ya fice ya ja mata Kofa kamar tana jira ta Fara cin faten Dankalin hannu baka hannun kwarya sai da ta da shi duka ta kora da ruwa sannan ta kara da sauran Tea din Dazu su Amina har ana lashe Filet,Sai Lokacin taji ta dawo daidai Ajiyar rai ta Sauke ta yaye Hijabin jikinta tana kara shan iska sai da ta huta sannan tatashi taje ta wanke hannu,ko ta kan Filet da kofin batayi ba ta fara Bude kayanta tana watse su a kasa domin bata son ya sake shigowa ya gansu Allah kadai yasan me zai mata in batayi abunda yace ba tana Tunanin su ya jafar ne mugaye sai yanzu take fahimtar akwai wanda ya Shafe su a mugunta ya Danmallam Tana da tabbacin daga shi har shegiyar gajerar matar nan tasa basu da Imani gwara ta bisu a sannu su wanye Lafiya. A wardrope din ta saka kayan kamar yadda yace,ba komai acikinsa sai Rigar barci Daya da Jallabiya guda Biyu Saman Madubi kuma sai Tararuka Amina ta matsar da su gefe ta saka kayanta aranta tana fadin ita yar Saudi bata ijiye kayanta anan ba kenan..? Har da littafan makarantar ta da takalmi da jakar Cikin wardrope ta Nausa su ta hada da ghanas din duka ta Tura kada dai yazo ya gani kafin ta gama bayanta ya kage ta koma ta zauna bakin gado tana Tuna Hamida afili ta Furta"Allah sarki Hamida kin sha Fadamin watarana baki tare dani zan tuna dake..Sai gashi Kaddaran data Rabani dake ko kwana Daya ban yi Cikinta ba na Tunaki hamida..! Sai hawaye ta tabbata da Hamida na nan tare da ita duka wannan aikin ita zatayi Kan gadon ta koma ta Dunkule tana kukanta na fama sai da taji sanyi ya isheta ne sannan ta tuna batayi sallar mangriba da isha"i ba..dole ta mike ta koma Tiolet din ta Dauro alwala tazo ta Daidai ci gabas tayi sallarta tana idarwa ta kwanta nan Saman Cafet din tana Tunanin rayuwarta a wannan gidan,Sai kuma ta fara kuka kewar yaya ta isheta Sai kuma ta ji mutuwarta ta dawo mata Sabuwa sai kuma ta tuna da mamanmu da su Hamida sai kuka wiwi har barci ya kwasheta tana kuka bata sani ba. Da safe tana tashi da filet da kofunan taci karo tana idar da sallar asuba ta makara sai da gari ya waye ta tashi ta Dauke duka harda goron ruwa ta fara Tunanin in da zata kai domin in wannan dan bala"in yazo ya gani kashinta ai bushe. Yanke shawaran fita tayi ta kai kitchen daman ya sa mata sabon suna wai kazama ai in yaga wannan sai ya kara kiranta da Hujja.. Koda ta fito shuru falon ba kowa sai da ta leka ta tabbatar da ba kowa sannan ta fara Tafiya Sadaf Sadaf zuwa Kitchen ai tasan hanyar tunda sun taba zuwa. Tana shiga kitchen din nan ma ba kowa sai dai tas kitchen din ba Datti kamar ba"a girki a wajen saman Cabinet din kitchen ta ijiye kayan hannunta ta juyo kenan zata fito suka kusa cin karo da Sakina data ganta sai da gabanta ya fadi ta ja baya tana Zare ido. Sakina Dake sanye da Riga da wando na plazo ta kalli Amina Daga sama har kasa cikin kaskasci kafin tace"Me ya kawo ki kitchen dina..? Amina ta kalleta taso tace ne bata sani ba ammh kuma bata da wannan karfin gwiwan yanzu ta kanta take yi yasa batace mata komai ba ta raba ta gefenta zata fita ran sakina ya baci ta Finciki hijabinta ta Dawo da ita baya ta Shake mata wuyan Hijabi tana Fadin"Ke don ubanki ni nake miki mgana kina sha min kamshi..? Tafada tana Zare mata ido Amina ta kalleta ammh ta kasa mgana aranta Tana Tunanin Sakina tazo Lokacin da Bazata iya maida mata martani ba..Ammh ta bari wanchan mara imanin ya tafi wlh bata zagi Aba a banza ba sai ta rama mai. Ido ta dago karaf suka hada ido da Danmallam dake tsaye daga falo yana kallonsu yana sanye da Jallabiya baka da Hula Cashaba ce a hannunsa kamar Dawowarsa kenan daga masallaci. Amina tana ganinsa sai da gabanta ya fadi da sauri tace"Kiyi hakuri abu na kawo..! Sakina zatayi mgana kenan taji Muryansa daga bayanta yana Fadin"Saketa Sakina..! Sai Lokacin ta juyo tana kallonsa sannan ta saketa ammh sai da ta Murje mata kafa da takalmin Dake kafarta Amina taji azaba ammh bata nuna ba Da sauri  ta fice Daga kitchen din kamar ta kifa ko barayinsa bata kallah ba ta koma Dakin datake tana shiga ta Dafe kirji tana Sauke Numfashi kamar wata mara galihu haka ta koma saman cafet ta zauna tayi Tagumi bata son hawa gadon ne bata saba da irin shi ba sannan ta saba kwana cikin mutane,akwai watarana ma da ita da Hamida suke kwana agado daya hamida tayi ta mitan ta matseta ammh Amina ta mata Burus wai ga inda Rayuwa ta kawota ita kadai kamar mara galihu. Tunda ta shigo Dakin bata kara jin motsin su ba sai chan rana Sakina ta shigo Lokacin har barci ya fara Fizganta koda ta Bude ido sai taga ta Dungurar mata da Filet din abinci tayi Tsaki ta fice Daman yunwar Amina take ji domin tayi alkawarin daina zama da yunwa in ta mutu Danmallam da matarsa basu da asara. Data gama da Filet din ta fita takai kitchen bata ga sakina ba yasa ta Tsaya ta Bude Fridge ta Dauki ruwa ta sha ta Koshi ta koma Daki da Daddare ma Sakinar ta kawomata Fuskar nan tata kamar Hadari saboda hadewa,Ta ballama Amina Harara Dake zaune taba kallonta sai da ta fita taji Dariya ya kamata aranta tace bani kadai yake ma Mugunta ba harda matar tasa tasan badomin shi ba Bata isa Sakina ma ta kalleta ba.. Kamar ta sani tun abunda tace mai jiya da Daddare ya dinga Daure mata shiyasa sai ta ganshi sai ta zuba abincin ta kaima Amina tana cika tana batsewa shi dai ko kara bi ta kan Sakina bai yi ballatana Amina,ita kuma Sakina Dadinta Daya ganin Aminar da ita da banza duk daya a wajen Umar sannan suna waya da Anty Amarya tana fadamata komai ita tace tarika bama Amina abinci ba komai suke da nasara.. Washegari tun safe Umar ya fita kan mganar Visa dinsa kano yaje tunda ta chan zasu tashi sai dare ya dawo an samu Visar nan da kwana Hudu zasu tashi,Farinciki ya ishesa sai kuma aranar yaje chan Gida bayan tafiyarsa da Amina sun hadu da Aba yayi ta mai fadan kada ya saurarama Amina in tayi mai wani abu yayi mganinta kada ya Ragamata shidai bai ce komai ba. Taya ya zai biyema Aba ya taba Amina hajiya ko mallam su ji labari ai sai su Tsine mai ya samu dai ya lallaba ya kara gaba ba"a gansa ba ballatana ace wani abu. Tare da mallam sukayi sallar isha"i Daganan ya shiga cikin gida ya gaida matan mahaifinsa,Shashen Hajiya ne na karshe,ya shiga tana zaune afalo tana gyaran farcenta ya zauna nesa da ita a kasa suka gaisa tana tambayansa Amina yace tana lafiya. Shuru na wani Lokaci kafin ya muskuta yana fadin"Hajiya na samu Visa ina ga nan da kwana hudu zan tafi..! Hajiya ta Dago tana kallonsa kafin tace"Allah ya kaimu..Allah kuma ya Tsare..! Kansa na kasa ya amsa da Ameen kafin Hajiya tace"Yanzu ba da ita Sakinar zaka koma ba kenan..? Kai Tsaye yace"Eh Hajiya..! Hajiya tace"Ai shikenan ma da nazata da ita zaka koma nayi ma mallam mganar Hamida da hanne su koma chan su taya Amina zama har ku dawo..! Yana jinta bai ce komai ba tacigaba da Fadib"Ammh tunda ta na nan shikenan..Sai dai kafin ka tafi zaka siya mata ko karamar waya ko Danmallam..? Kansa na kasa kafin ya Dago yana Fadin"To Hajiya sai a siya mata..! Hajiya tace"Ya kamata gaskiya tunda kaga itama Sakinar nada wayarta. sannan in ka tafi chan sai ku dinga mgana ta wayar da zaka siya mata hakan zai fi..! Danmallam dai nasa cewa to ne Domin Gata kan Amina ta fisa gata a wajen su Hajiya. Shuru ya kara giftawa na wani lokaci kafin tace"yaran nan ma yan"uwanta har yanzu basu saki da kewar Amina ba..Nace zasu je mata cikin Satinan tunda ma zaka tafi bari in ka tafi sai su tafi su mata ko kwana Biyu ne nasan zataji Dadi..! Dan mallan kansa na kasa aransa yace"Zataji dadi tunda abokan iskancin nata suna kusa da ita..! A fili kuma bai ce komai ba Hajiya ta shiga Fadamai zata je maidguri Cikin watanan yar yagana zatayi aure ya Dago yana fadin"Hajiya daman tana da wata ya agabanta ne..?Na dauka Suhailu ne kadai autanta..! Hajiya tace"A"a tana da karamar ta zaituna itace zatayi aure..! Bai wani damu ba yace"Allah ya kaimu hajiya..Allah ya bada zaman lafiya ke kuma Allah ya kaiki lafiya ya Dawo Dake..! Ta amsa mai da Ameen kafin tayi mgana Hanne da Hamida sun shigo Falon suna ganin ya Danmallam suka natssu suna gaishesa ya amsa yana kallonsu ganin yadda sukayi wani iri Hajiya ta kalle su tana fadin"Nasha chan zaki yi kwanciyar ki hanne..! Hanne batayi mgana ba kanta na kasa Hamida ce tace"ni ce zan kwana anan Hajiya..! Hajiya tace"Shikenan yau dai kun ma Balaraba Yaji..Ita kadai sai jawadu..! Basu ce komai ba kansu na kasa Hamida ke taba hanne ita kuma taki mgana Hajiya ce ta gansu Dariya tayi kafin tace"Ku sha kuruminku..Karshen sati zaku je kuga Amina..! Baki suka washe suka hada baki wajen Fadin"Da gaske hajiya..? Hajiya tace"Yanzu ma muka gama mgana da yayanku..! Suka wani daka Tsalle suka Rumgume juna wani kallo yayi musu dayasa suka natsu waje daya ganin haka yasa ya mike yayi ma Hajiya sallama ta amsamai tare da cewa"Kace ma Amina su hanne na nan zuwa zasu zo mata da sako tayi hakuri..! A kasan makoshi ya amsa ma Hajiya kafin ya fice Daga Shashen yana jin ihun yaran bayan ya fita kai ya girgiza kaawai. Falom Mallam ya koma sukayi sallama shi da Aba ne suna mgana Daganan ya shiga motarsa zuwa gida koda ya koma Sakina ta gama komai taci kwalliya tana jiransa ta tarbesa ta taimakamai yayi wanka ya sauya kaya suka fito saman Dining suna cin abincin sai alokacin ya kalli Sakina yana fadin"Kin kaimata abinci..? Sakina ta amsa mai da kai,Yaji dadin haka kai tsaye yace"Allah yayi miki albarka..! Tana Mirmishi mugunta ta amsa mai da Ameen Ameen domin ta gama wasa wukanta jira take ya saka kafa ya Tafi sai Amina tayi nadama wlh. ********* Washegari.. 9:30am. Adaidaita ta shiga yana ta Gudu da ita kamar zai bar garin gumel da ita sannan naga ya Tsaya bakin hanya inda ba yalwar giftawan abun hawa Fitowa tayi sanye da Hijabi Dogo har kasa ga Nikab a Fuskarta karamar Jakarta ta Dauko ta bashi kudinsa kafin ta fara tafiya ta mike wata Hanya tayi tafiya sosai kafin ta fara Hango ta tana zaune saman wani Dutse tana jiranta sai da ta tazo gabanta sannan tace" Aci balbal Fitilar sharri..Ko babu mai kina kai safe. Kwalba ko kin fashe da sauran sharri kibiyar ajali kike mai Ratsa rigar karfe..Madina ikon Allah gabanki Fari bayanki baki..!gaba salamun baya salamun damisa mai maida Fatar kura nama..! Wata irin Dariya Anty Amarya ta saki Lokaci Daya tana mikewa tsaye hannu ta bama ta Tsayen suka tafa ji kake tas..kafin tace"Ban kai ki sharri ba Dayyaba..Domin ni daman chan ban taba aron Fuskar salihai ba..ke kuma fa kin fini zama kwalbar sharri..An aminta Dake kin ci Amana sannan a yarje miki kin yi ha"inci..! Tare suka kara saka Dariya kafin ta yaye Nikab din data Rufe fuskarta sai ga Mamanmu ta bayyana..! Cikin wani yanayi tace"Babu abunda zan ce da ke madina..Sai Allah ya Cika miki naki Burin..! Saura kadan na gama mallakan Sa"iduna a hannuna madina kiris ya rage .! Anty Amarya dake sanye itama da Dogon Hijabi tace"Kwarai naga alama..Ammh meyasa kika batamin Lokaci kinsan tun yaushe nake tsuggune anan wajen ina faman jiranki..!? Mamanmu tace"sai da ya fita sannan na samu na fito daga gidam..Kinsan dai yanayin da ake ciki..Lokacin da yaya nan ne nake samun fita akai akai in nace zan shiga gidanku yanzu kuma gida ni kadai ce Hamida na makaranta ita da jawaad..Kuskure kadan zan yi sai kiga na bata komai..! Anty Amarya tace"kiyi hanzari ina kan hanya ne..! Ba musu ta Bude Jakarta ta Dauko Kudi masu yawa ta Damkama Anty Amarya tana fadin"Shashashan wai fa bani yayi nayi ma Amina siyayyan kayan amfani shine nayi sama dasu..! Anty Amarya tayi dariya kafin tace"Shegiya Balaraba...! Mamanmu tace"kul..Dayyaba nake in kika Kirani balaraba kamar kin Ragema Kwalba sharri ne..! Tare suka kasa Dariya kafin Anty Amarya tace"Mallam fa ya fara korafin kin Daina zuwa yanzu sai dai nazo ni kadai kada ya fara Tunanin ko dan kin Samu Biyan Bukata ne..! Mamanmu tace"ki kai masa wannan kudin na karin kudin aiki ne..Mganar zuwana kuma in zaki koma dani zamu koma nace miki nan da Sati Biyu zan je gusai bikin gidansu..Sai na Fake da Guzuma na Harbi karkasa..! Anty Amarya tayi dariya sosai kafin ta Fito da jakarta babba ta Tura kudin aciki kafin tace"Shikenan bari nayi hanzari..bana so nayi Dare..! Kallonta tayi kafin tace"Kwana zaki yi..? Kai Tsaye tace"Eh in nayi Dare sai gobe zan dawo..Zuwan daman na Sakina ne so nake Mallam yayi aiki kan Umar ya koma da ita madina..! Bana son zamanta da wannan shegiyar Yar taki..! Mamanmu ta bata rai kafin tace"A"a fa ki bari madina..Allah ya Tsareni ni Uwar Zulfa nake da Zahra kuma uwar Hamida...! Anty amarya tayi dariya kafin tace"Mamannu...Mamanmu ..! Tana kwaikwayon muryan Amina aatare suka fashe da Dariya suka tafa Kafin mamanmu tace"Uwarta na kabari..! Wani Tsari kika rakata ne ni ban kara ma bi ta kanta ba tun sanda ta bar min gidana..! Anty amarya tace"Tsarin auran ya zo a banza ya kare a banza..Domin Sakina ta tabbatarmin ita da banza Duk Daya suke awajensa..Kinga kenan haka zata gaji da zama har mallam da Hajiya da suka kulla abun su gaji su Rabashi..Sannan nace ma mallam ya kara mata rashin kunya da Tijara tayimai ya Sako shegiya..! Mamanmu tace"Ni kuma Daga Lokacin zan karata gaba..Bana son na kara bude ido na ganta agidan nan har Abada gidanan nawa ne ni da ya"yana..! Anty Amarya tace"Kadan zaki jira..Burinki zai gama cika..! Ni ce dai naga Tafiyata akwai Tsawo..Burina kawai sakina ta samu Ciki ta Haihu in hakan ta Faru kamar na gama cika duka Burina ne..! Mamanmu tace"Kema lokaci kadan ya Rage..Dukkanmu wahalar mu bazata tashi a banza ba..! Anty Amarya tace"Tabbas..Domin bazan gaza ba..Sai naga abunda ya Turema Buzu nadi..Zan tafi yadda ake ciki zan kiraki..! Mamanmu tace"Ki sanar da mallam Sa"idu ya fara zuwa hannu..Ammh ina so ya zama ni nake fadi yana amsani.. Anty amarya tace"Kamar yan amshin Shata kenan..! Gabadayansu dariya suka saka kafin su tako atare har bakin Titi kowacce Adaidaita Dabam Dabam suka hau Daya ta koma cikin gari Daya kuma ta Mika hanyar tashar garin na Gumel..! _SHIN KINA DA LABARI AKAN HAƊIN SABAYA KOKUMA IN ƘARA MIKI BAYANI AKANSA DOMIN WANNAN HADIN INGANTACCE NE BA IRIN WANDA KUKA SABA AMAFANI DASHI BANE_ Shi wannan din SABAYA COCONUT FLAKES ne, duk wani hadi da ake nema na gyaran jiki akwaishi aciki duka hajiyata, naturally zaki cicciko babu abubuwan illa aciki. *Ina ƴan mata da zawarawa kai harma da matan Aure? To ku matso kusa ga Sabaya wanda akayi hadinsa da coconut flakes kuma kun san kwakwa ba karamin taka rawa yake wajen gyaran jikin 'ya mace ba, SABAYA COCONUT FLAKES zai taimaka wajen ciko da duk wani lungu da saƙo na jikin mace, ta dawo mul-mul da ita tamkar jinin ƴan Chadii.* *yana sa ƙirjin mace ya ciko sosai, idan ma ƙirjinki a kwance yake sabaya na iya miƙar dashi ya koma kamar na buduwar ƴar shekaru sha 18. Duk wannam aikin na SABAYA COCONUT FLAKES ne shi kaɗai 💃💃💃, bayan haka yana ƙara ni'ima a jikin mace gamida ƙara mata ɗumin jiki. Ga matar Aure kuma yana ƙara mata juriya wajen gamsar da mai gidanta cikin sauƙi. Tareda ɗorewar nishaɗin su gabaɗaya.* *Hajiya maza ki nememu don ki mallaki SABAYANKI, don kema ki zama mace mai aji kuma ƙasaitacciya, karki yarda ki zauna yarkace-yarkace kamar kin fito gidan Yari😂, Gyara shine Mace Hajiya, idan bakya gyara jikinki sunanki mata maza, ko kuma in kiraki da suna wadda ta rako mata duniya Kawai🙅‍♀️* *_Domin niman ƙarin bayani ku tintiɓeni kai tsaye ta wannan lambar:_* +234 706 548 1260 *_Muna tura kayan mu ko wani gari da zarar kinyi order 💃. Kuma duk akan farashi mai Rahusa🥰 muna maraba da masu siyan daya ko sari..mungode sai kunzo🙏 07065481260 *Janafty* *TFZB2004* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* BAYAN KWANA BIYU. Amina ta gaji da kuka ta daina domin ta tabbatar ma kanta ita inda kaddaranta ta kawota kenan bata da wani tsumi ballatana Dubara kukan tayi shi har ta gaji ta hakura cikin kwana Biyun nan duk ta rame tayi Firgai Firgai ba walwala bata da sakewa sai zama waje daya da zaman kunci tundaga ranar bata kara saka Ya danmallam a idonta ba itama taji dadin haka sannan In yana gidan ta lura Sakina zata kawo mata abinci sau uku arana in kuma ranar baya gida to sai dai ta sha yunwarta sai dare bamai lekota ita kuma bazata iya fitowa ba har alokacin akwai sauran tashin hankali da kuma kokuwa da abunda ya sameta sannan uwa uba kuma rashin Sabo da inda take zaunen. Amina bata wanka rabonta da wanka Tun ranar da Umar ya Tursasata tayi bata kara ganin ruwa ba sallah ce da ta zame mata dole take yinta sai abinci in Sakina taga dama ta bata wannan kam tana ci domin ta tabbatar ma kanta in ma bata ci ba sai dai ta Mutu daga sakinar har mijin nata ba wanda ya damu da ita acikin gidan sai filet din sun taru take fita dashi kitchen bata bari su hadu da Sakina domin har yanzu bata shiryama wannan rigimar datake janta dashi ba. Ruwa kuwa bata matsama kanta ba na Tiolet take tara ta sha abunta Daki ba Shara ba komai Amina ita dai ta Wuni aciki ta kwana aciki ne kadai aikinta in kewar su hanne ya isheta taji kamar ta gudu gida sannan tana kewar makaranta abaya ranta baci yake yi in Monday ta zagayo ko Asabar sai gashi yanzu ido rufe take kewar makaranta tana ji dama ace tana da wannan damar da kewa bata isheta ba taji tana son zuwa makarantar ba Dama baba mallam bata kara ganinsa ba ballatana Hajiya kai wani Daga chan gidan ba wanda tagani balle taji ita ya makomar karatunta tunda yazo nan ya sar da ita bai damu data rayu ko karta rayu ba Allah sarki rayuwa tasan su hanne suna cigaba da zuwa makarantarsu tasan kuma yan ajinsu suna ta tambayanta kila sun fada musu an mata aure har an kawota gidan wannan mara Imanin. Abunda bata sani ba shi Danmallan mantawa ma yake da ita agidan Shiryen Shiryen Tafiyarsa kadai yake yi Sakina sai da ta ga tafiyarsa tasa ta taso sannan Hankalin ta ya tashi Ana saura kwana Biyu Jirgin su ya tashi Ranar ya dawo da Daddare taji suna mgana da Aliyu ta waya yana Fadamai zai Dauki kimanin wata bakwai Cikin na takwas kafin ya Dawo. Hankalin Sakina ya tashi duk da sun yi mgana da Anty ta Fadamata ta kwantar da hankalinta mallam ya tabbatar mata da cewa ko Umar ya tafi Bazai iya sukuni ba sai ya Dawo ya Tafi da ita saboda in ya barta anan ai anyi ba"ayi ba kenan Ga zamanta da wannan kazamar yarinya ga kuma rshin miji a kusa ta ina zata samu Cikin in baya nan bayan duka kokarinsu kenan yau ta ganta ta samu juna ya Tsaya mata ba ya bare kamar yadda yayi mata har sau uku ba. Kafin ya gama waya ta Durkushe gabansa tana ruwan hawaye kallo Daya yayi mata yasa kwanan zencen sai ya shareta,Shifa gabadaya sha"anin mata ya fara fita kansa yau sai da ya yi ma Sarood fada soaai bisa yadda ta Kirasa tana kuka tana mai korafin ya tafi ya manta da ita tunda yana da mata har Biyu anan to ta gaji in bai dawo ba zata Biyosa bai hanata ba yace tazo ammh ta sani nan zata zauna itama bai kuma fadamata ga shi dawowa ba ya riga ya gama Shakan takaicin su gabadayansu ba Sakinar ba,Ba sarood din ba dukkansu ba kwanwar lasa bane,A baya sai yake ganin Sarood mai Hakuri ashe itama kyallece haka kawai ya fadamata ya Datse kiran yayi Rantsuwan in har tazo wlh sai dai ta Dauwama a Nageria ita da Madina sai da ziyara ai shima ba kasarsa bane cin arziki yake yi shi yanzu Damuwarsa daya yadda Hajiya ta Dage sai ya nema ma Amina muhallin Zama a Madina Tsakani ga Allah zai Takura baisan ta ina ma zai Fara ba kuma yadda Hajiya ta kafe din nan ko mallam bazai iya Tankwasata ba shima baya so ya fara Saba Umarninta tunda bata taba katsalanta kan sha"aninsa da matansa ba wannan ma Saboda yar gold ce. Sakina ganin yaki bi ta kanta yasa ta fara jan Hanci tana fadin"Yanzu Habibi haka zaka tafi ka barni sai bayan wata bakwai ka dawo..? Kana ganin ko ta bangaran addini kayi Daidai kenan..? Suna Cikin Bedroom dinsa ne yana zaune gefen gadonsa tana sanan Cafet yayi mata kallon sama da kasa kafin ya Dauke kai Sakina ta riga ta tabbatar ma kanta bazai taba Sauya Ra"ayinsa ba. Shiyasa ta mike tana fadin"Shikenan kasan dai ni macece kuma in da Hakki a kanka..In sha"awata tatashi Watarana har na cutu kai da Allah Umar..! Ta karishe fada tana jan majinan kuka,har ta fice yana kallonta kafin yaja karamin tsaki bata san shi bane sai yanzu zata san shi ko ajikinsa komawa yayi ya kwanta yana jinsa kamar akan kaya ya kosa ya Bude ido ya gansa a madina matsalan Sarood karamace tsakaninsu ne ya lura in bata ganin Sakina tafi Hankali da natsuwa da kuma Hakuri ammh in dai tana Ganin Sakina akusa da ita tafi korafi da kananun mganganu. Sakina na fita Dakinta ta koma tana Shesahekan kuka ta daga waya ta Kira Anty wacce ke shashen baba mallam alokacin sun gama cin abinci kenan dukkansu yaransun fita sai su dake falon gabadayansu har da Hajiya Babba suna hira kan yadda Zaman lafiya da rashin Tsaro ya yawaita hirar Tsakanin Mallam ne da Hajiya Babba sai Haj.Uwani Haj.Nasara na gefe tana saka baki jefi jefi,Anty Amarya ne keda Mallam aranar shiyasa tana gefe tana kallonsu bata saka baki daman tana da yawan ware kanta acikinsu Wayarta na Hannunta sanda kiran Sakina ya shigo sai taki Dauka sai da taga Kiran yaki ya kare ne sannan ta tashi ta fita ba wanda ma ya lura da ita sai Hj.uwani da take ta sakin munafukin Murmishi Domin duk wani Motsin Marliya ai a tafin Hannunta take duk ta gama kokarin nata sai ya tashi a banza.. Sai da ta isa shashenta sannan ta Daga kiran Sakina Dayaki karewa Cikin Fada tace"Miye haka sakina..? Kina kirana da wannan daran in Kika bada Kofa aka ganemu fa..? Kuma mijinki na gida in ya fara Zargina fa..? Ke meyasa baki da Hakuri ne..? Sakina cikin kuka tace"To Anty yau fa naji yana fada in ya saka kafa ya tafi sai bayan wata takwas fa zai dawo..! Anty Amarya tayi Tsaki kafin tace"To shi ne me..? Sakina tayi kasa da Murya kafin tace"Anty kin manta ne..?in yana chan a ina zai ganni har auratayyah ya shiga Tsakaninmu na samu Cikin da muke Fata..? Sai alokacin Anty Amarya ta Dawo Cikin Hayyacinta cikin Tashin Hankali ta Dafe kanta kafin tace"Kin gane duk nasan da wannan..Na fada miki mallam yace ko ya tafin zai dawo ya tafi dake Sakina ki daina Damuwa..! Sakina tace"Nidai Anty mu tafi Taren hankalina zai fi kwanciya..!.Anty tace"To sai dai in Tuntuba ta bangaran Mallam,Ammh ta bangaran Umar kina ganin abunda yace min bazai saurareni ba in na matsa ma sai ya fara Zarginmu..! Ki bari yau ni ke da Turakan mallan in wadanchan matan nasa sun watse zan mai mgana naji..! Sakina tace"Yauwa Anty nagode don Allah kimai mgana don Allah..! Anty Amarya tace"Naji zan mai mgana nace..Ki kuma ki daina Damuwa ki kuma rika hakuri kada wannan zalaman naki ya bata mana aiki..! Da toh sakina ta amsa daganan sukayi sallama Anty Amarya tayi Tsaki afili ta Furta"Sakina tana da matsala wlh..! Daganan Toilet ta fada domin ta sake Sabon wanka so take ta ruda mallam da nata salon yadda bazai mata gardama ba. Achan Falon mallam kuwa bayan Fitan Anty Amarya itama Hj.nasara tayi musu sallama ta koma Shashenta ya Rage daga hajiya sai mallam Sai Haj.uwani Dake zaune gefen Hajiya Bisa kujera mai zaman mutum biyu Cikin kissarta data shiga Jikinsu gabadaya domin Hajiya ta yarda da ita Dari Bisa dari hakama mallam. Sai da ta kalli Hajiya kafin tace"Oh Hajiya wai bawanda zai koma ya Dubomana Amina..?Tunda Suka tafi fa ba wanda yabi bayansu..! Hajiya batayi yunkurin mgana ba Mallanlm ne ya Murmusa kafin yace"Kamar wasu yara kanana Uwani..? In ita Amina yarinya ce ai Shi Umaru yana da Hankali na tabbata kuma zai kula da ita..Sannan ai ba ita kadai bace Sakina na tare da ita sannan ko Dazu nan mukayi sallar isha"i dashi kinga kuwa suna nan lafiya..! Kafin tace wani abu Hajiya ta amshe mganar da cewa"Daman ina da niyyar su hanne su je mata..Na bari ne tayi ko Sati ne ta saba da chan kada su je yanzu ta fara koke koken suma ba Tunani ne dasu ba haka zasu hadu su kara Tada mata hankali..! Haj.uwani tayi mirmishi kafin tace"Hakane kuma hajiya..ni daman nace ne ko zamu lekata Amina wlh da ita nake kwana araina Tsausayi ta bani Ranar da zasu tafi..! Mallam yace"Da haka kowa ya saba..kema ai haka kika yi ta kuka ranar da zan taho dake daga Tsafe .! Har Hajiya gatanan tayi wannan koke kokem ko ba haka ba Hajiya. ? Hararan wasa hajiya ta sakar mai batayi mgana sukayi Dariya Dukkansu mallam ya cigaba da fadin"Zai koma ma jibin nan..in ya tafi su je su ganta su wunin mata sai taji Dadi..! Hajiya tace"Eh har kwana ma sai suyi mata..Uwani ai mun girma da zuwa gidan yranmu yanzu sai dai in wani abu ya taso wanda ba"a Fata..! Haj.uwani ta rausayar dakai kafin tace"Ammh in ya koma nan zai barmana ita ko..? Hajiya tace"Eh nan zai barta ita da Sakina zasu zauna agidan su..! Haj.uwani tayi mirmishin jin Dadi kafin tace"to Allah ya zaunar dasu lafiya..! Gabadaya suka amsa da Ameen basu wani jima ba sukayi mai sallama suka fita,Hj.uwani bata koma Shashenta ba ,shashen Hajiya suka yada Zango suna hira sai hillatan Hajiya take yi tana jin wasu sirrikan saboda ko Mallam bai Fada maata abu ba zata jisa abakin Hajiya harta matakin da Hajiya ta Daukan kan tafiyar Amina madina sai da ta fada mata Hj.uwani tace"Wlh gwara haka hajiya..Yazo ya tafi da matarsa..Ni fa marliya ban yarda da ita ba..so suke su mallake Umar din shi kadai to ta Allah bata su ba..! Hajiya tace"Ameen da yardan Allah Amina da Danmallam mutu ka raba. ! Aran Haj.uwani sai da tace ba Ameen ba afili kuma ta amsa da Ameen kafin tayi ma Hajiya sallama ta koma Shashenta Cikin Farincikin da sai da ya Bayyana akan Fuskarta Umaima ta leka ta isketa tayi barci gyara mata Bargo tayi ta fice ta koma Dakinta,Tana shiga tayi wani Shewa lokaci Daya tana Fadin"Cikin ruwan sanyi..Burina zai cika..! Wayarta ta Dauka Dake saman Mirror ta Kira Batula kanwata tana Dauka ta Sakin mata Shewa tana fadin"Batula albishirinki..! Dagachan bangaran Batula tace"Goro Uwani Sikari baki farin banza..! Dariyar Nishadi ta saki kafin tace"Tsarin da muka dora yarinyar nan su Hajiya sun taimaka mana ya tafi Daidai batula..! Batula tace"kai don Allah..?,Bani na sha..! Nan uwani ta warware mata komai ta Karishe da fadin"Kinga jibi zai koma kuma sai ya Dau Lokaci kafin ya Dawo..Zuwa kafin ya dawon na riga na Dorata kan Tsarin koda ma zai kulatan watarana kamar Sakinar ce haka ko ta samu zai bi Rariya..! Batula tace"Dakyau..Hakan yayi kyau sai dai kada ki yi sakaci har adauki wani Lokaci bata hau Tsarin ba kinsan yadda zaki yi ko ta Halin kakane ...Cikin kwanakin nan Namiji fa baka shedarsa..! Haj.Uwani tace"Naso haka sai dai tunda suka tafi batazo ba..Sannan naso na sakama Hajiya Tunanin muje mu Dubata taki bada Dama..ammh nasan zata zo jibi fa zai tafi Batula wlh ina da Tabbacin Mai mata kamar Sakina da balarabiya bazai kula Amina ba kinganta ne..? Kwaila ce fa ga kazanta ga rashin Natsuwa ina da tabbacin bazai taba kulata ba..! Batula tace"Shikenan tunda kina da yakinin haka..Sai dai ina tsoron kada su shammacemu..! Haj.Uwani tace"Na yarda da aikin Mama..Ba wanda ya isa ya shammaceni Batula sai dai ni na shammacesu kamar yadda na saba..! Dariya suka saka gabadayanau kafin su cigaba da mganarsu sun manta cewa Allah ne ke zana kaddaran bawa ba Mutum ba,abunda basu sani ba shine Komai da zai faru nan gaba Allah ya riga ya Tsara faruwar hakan Lokacin kawai ake jira. Tabbas Uwani zata Tsammanci abunda batayi tsammani ba. Bama ita kadai ba iri irenta ma zasu tsammanci abunda basu taba Tsammani ba..! Anty Amarya sai da ta chanchara kwalliya,ta fesa turaruka sannan ta koma Shashen mallam cikin gayunta,Mallam bashi a falo yana cikin Bedroom dinsa chan ta Bisa ta iske ya fito wanka kenan ya sauya kaya zuwa saukakkiyar Jallabiya mai ruwan madara furfuran kansa duk yana Waje ne tana shigowa da sallama ya amsa mata yana Binta da kallo Lokaci daya da Mirmishi Gefen gado ta nemi waje ta zauna tana kallonsa kafin tace"Mallam kayi wanka baka jira ni nazo na tayaka ba..! Mirmishi yayi mata kafin yace"Na Hutassheki ne marliya..! Mikewa tayi ta isa garesa ta amshi Man dayake shafawa a Hannunsa ta Lakuto tana tayasa shafawa Lokaci Daya tana fadin"Aikina ne fa..Kada kamin Rowan lada mana mallan..! Yana kallonta yace"Mun girma marliya wannan aikin duk na Dauke muku yanzu..! Marairaice masa tayi tana fadin"A"a nidai ban yarda mungirma ba....! Yana yar dariya yace"Baki yarda mun girma ba..?,To in ke kina da yarintarki ai yunusa kan ya Tsufa..! Tura bakinta tayi kafin tace"Ni dai wlh Mijina bai Tsufa ba..Yaro ne Danye Sharaf..! Dukkansu yadda ta fadi mganar yasa sukayi Dariya atare ita ta karishe Shafa mai man suka koma saman gado suka zauna mallam ya mike kafarsa tana shafamai man zafi Saboda sun faramai Tauna kuma aki"da ne duk Dare sai ya shafa yake kwanciya Tana shafamai suna Hiransu samasama sai da ta gama hillatansa sannan ta kallesa kafin tace"Ni ko mallam yaushe Danmallam zai koma ne..? Kai tsaye yace mata"Jibi in Allah ya yarda yacemin jiya..! Kai ta Rausayar kafin tace"Ya sanar dakai nan zai bar Sakina..? Mallam yayi shuru kafin yace"A"a bai sanar dani ba..! Anty Amarya ta gyara zama tana fadin"To ni dai baisan me ya faru Tsakaninsu ba..kasan yaran nan su yi ta shirme basa neman shawara ashe sanda zasu taho Bikin su Abida yace ta Zauna achan ta matsa sai tazo Shine fa yace bazai koma da ita ba yanzu..! Mallam ya yi shuru yana kallonta kafin yace"Haka akayi .? Anty amarya tace"Eh mallam ita kuma Sakinar ta damu tana ta kirana tan kukan wai na rokesa ya koma da ita bazata iya zama ita kadai ba nidai Fada nayi mata nace Laifinta ne da nace bazan saka Baki bane tace nayi maka mgana don Allah ka Rokesa ya tafi da ita..! Har ta gama mgama yana Nazarinta Kafin ya sauke ajiyar rai yace"Naji batunki marliya kinsan Allah ni bansan ma duka anyi haka ba..Umaru da na ne ammh bana hirar iyalansa Dashi..Tsakani na dashi Hirar duniya sai kuma ta aiki in ta kama sai kuma ta Rayuwa haka ammh ni bana shiga Sha"anin ya"yana da matansu kinsani marliya..Umaru mijin Sakina ne sannan bansn meya faru Tsakaninsu ba domin ina Mahaifinsa ya gama tsara abunsa sai na kirasa nace masa ya Sauya..kina ganin hakan ba rashin girma bane..? sannan kuma shiga Hurumin da ba nawa bane tunda dai bai Tuntubeni da mganar ba..! Ya karishe fada yana kallonta itama shi take kallo jikinta yayi sanyi domin taga ba Nasara,girgiza kai tayi cikin sanyin jiki kafin mallam ya cigaba da fadin"To kin gani bai kamata nayi mai mgana ba..Sannan ai ba ita kadai zata Zauna ba ga mamana nan itama nan zai barta sai ya sake dawo wa ki bata Hakuri ta zauna inda mijinta ya ijiyeta..! Anty Amarya sai ta kasa mgana Shuru kawai tayi,Ganin kamar yanayinta ya Sauya ne yasa Mallam yace"Kiyi hakuri marliya..kema kada ki saka baki wannan ba Hurumin mu bane..! Da Toh ta amsa mai tana kokarin nuna komai ba komai bane kada mallam ya Fahimci yanayinta.. Washegari ta kira sakina ta lallasheta akan tayi Hakuri da mganar Binsa ta bari in ya koma mallam ya tabbatar mata zai dawo domin ya koma da ita Tunda Sarood bata da wani amfani kamar Hoto take. Sakina ta yarda ta Hakura ammh tace yana tafiya itama Dutse zata je tayi Sati Daya ta huce daga Bakincikin yadda zata fara zama da Amina agida Daya Matsayin Mijin su daya. ********** Ana gobe tafiyar Danmallam Da Daddare Sakina ta Fadamai Tana so gobe in ya tafi zata je Dutse ta gaishesu,bai ce mata komai ba alokacin sai da safe domin jirginsu 12pm zai tashi zuwa Jidda,lokacin yayi wanka ya shirya Cikin Shigar jallabiya Fara da bakin wando sai Hula yana Fesa jikinsa da Turaransa na Arab Sakina ta shigo Dakin Cikin Shigarta na kwalliya kamar ko yaushe sai da ta isa kusa dashi ta karbi Turaran Hannunsa ta karishe Fesamai bayan ta gama ta maida Turaran kan Madubun Dake Dakin ta Rumgumesa tana Fadin"Zan yi kewarka Habibi..! Shima riketa yayi na wani Lokaci kafin ya dago kanta ganin Hawaye ya Cika idanuwanta yasa ya Girgizamata kai yana fadin"Kada kiyi kuka..Ki batamin kwalliya..! Jin haka yasa ta kara Narkewa tana mai yar shagwaban zai tafi ya barta nan ya lalace wajen ya lallashinta sai da karar wayarsa ta katsesu sannan ya Saketa Wayarsa Dake kan gado ya Dauka ganin Aliyu ne yasa ya Daga yana Fadin"Badai har ka iso ba..? Dagachan bangaran Aliyu yace"To akace maka ni irinka ne..Gani Falon mallam muna jiranka..! Umar yace"Ina Jafar ya iso..? Aliyu yace"To mu da bamu da sabuwar Amarya Swt sixteen ai duk mun Hallara..!tsaki yaja kawai ya Katse kiran yana girgiza kai yana Tunanin Aliyu bai da girma sai na Jikinsa. Sakina ta kuramai ido tana kallonsa Hannunta ya rike yana fadin"Muje su Aliyu nachan gidan mallam suna jira na..! Marairaicewa tayi kafin tace"To haka zaka tafi baka karya ba..? Yana kokaron Daukan jakan kayansa yace"Kinsan bana iya sakama cikina wani abu in zan hau jirgi..Kada ki Damu zan ci wani abu ko achan ne..! Saman kafadansa ta Dora kanta tana fadin"Zaka tafi bakace min komai ba..! Kai Tsaye yace"Name fa..? Ta karkace kai tace"Na tafiyana Dutse mana..su Daada nake son naje na gaishesu tun fa Bikin Sadiya ban koma ba..! Kai Tsaye yace"Kije ammh ba yau zaki Tafi ba ki bari gobe..! Da sauri tace"Saboda mene Habibi..? Har na kirasu nace fa ina tafe yau..!. Hancinta yaja kafin yace"Saboda Haka nace..Kuma ba Sati zaki yi ba..kwana Uku na baki..! Baki ta Bude tana kallonsa sai ya Rufe mata bakin da nasa ya bata sumba mai tsawo kafin ya saketa Jakarsa ta amsa ya Riko hannunta suka fito Har Falon,har ga Allah ya manta da Amina sai da ya kalli Dakin sannan ya Tuna da ita Hannun Sakina ya saki kafin yace"Jirani ina zuwa..! Tana hararansa ya shige dakin Sarood wanda ya zama na Amina yanzu..! Barcinta take sha sosai domin barcin da batayi bane kwana Biyu take ramasu ga Filet da mug nan har da Sauran Buredi a kasa dataci ta Rage sannan Dakin duk ya Hargitse ga Hijabai nan da kaya saman gadon bata Kwashe ba,Amina sai jiya ta Sake wanka shima kayan jikinta ne suka isheta tayi wanka ta sauya tayi Daidai kan gado tana barci Daga ita sai Zani Tayi Daurin gaba ko Riga bata saka ba.! Kamar zai tasheta domin zarni da wari ya ishesa yasa kawai yayi Tsaki ya fice Daga Dakin yana Fitowa yaci karo da Sakina inda ya barta tana kallonsa shima ita yake kallo kafin yace"Sakina..! Ta amsa da Na"am cikin Kaushinsa yace"Zan tafi kada ki shiga shirgin yarinyar nan ki kama girmanki..in kin yi Girki ki bata..Sannan gobe in zaki Tafi ki Fadamata domin ta Rika fitowa tana sama ma kanta wani abu..Ban son Rigima Allah in naji wani abu ke zan bata ma rai saboda ke na bar ma Amanar gidana..! Sakina ta Tura baki kafin tace"Ni fa bazan dinga mata girki tana kwance ba..Itama ai matarkace sai ta fito ta girka nama na kaima kayi Adalci..! Kai tsaye yace"Wannan me ta iya banda kazanta..? Sakina ta Hura hanci kafin tace"Sai tayi kazantarta taci kayanta Daman bani zata mawa ba..! Kai ya kada kafin yace"Allah ya kyauta sannan Hajiya tace zata koma makaranta nan Idi zai rika zuwa Daukanta..! Aran sakina tace to ni ina Ruwana batayi mgana ba shima bai ce komai ba ganin zai tafin yasa ta rikesa ta sakamai kuka ganin haka yace ta sako mayafi su tafi gidan mallam tare jiki na rawa ta je ta Dauko hijabi suka Fice shi ya tuka Motar da kansa bayan ya sallami megadi itama Sakinar ya bata katin bankinsa guda daya suna Mota yace mata"Na amfanin yau da kullum in ya taso ke da yarinyar nan kuyi amfani dashi..kayan abinci kuma in ya yi kasa Jafar ko nasir zasu kawo..! Karba tayi kafin tace'Ni dai ka daina Hadani da kazamar matarka meyasa baka bata nata ba..? Kai Tsaye yace"Saboda kice babba sannan kuma kin Fita Hankali..kuma Amanar komai da komai a Hannunki na bari..! Bata kara mgana ba har suka iso ita Cikin gida ta shige shi kuma Falon mallam suka gaisa Aliyu nata kallonsa yana Dariya cikin gida ya shiga yayi ma Duka matan sallama Shashen Hajiya ne na karshe yana Duke gabanta tana fadin"Allah ya sauke ku lafiya..Allah ya Tsare..! Yana ta ansa mata da Ameen Yana shirin tashi tace"Ina wayar da nace ka siya ma Amina ka ko siya ne..? Sai alokacin ya tuna kansa na kasa yace"Na manta Hajiya..ammh yanzu zan barma Jafar kudin zai siya mata..tunda su zasu rakani Airport shi da Aliyu..! Hajiya tace"Ai ya shigo mun gaisa..Sannan ka shiga gidan Sa"idu kuyi sallama da shi da balaraba..! Da toh ya amsa mata ya tashi ya fice ta Bisa da Fatan nasara. Bai koma falom mallam ba sai ya wuce gidan Aba ya iskesa ma yana shirin Fitowa haka ya tarbesa ko zama bai yi ba sukayo sallama ya kira Mamanmu suka yi sallama Fadi take Allah ya Tsareka Umar..Allah ya bada sa"a ina Diyata Amina..? Ina fatan tana lafiya..! Kansa na kasa yace mata tana lafiya har Haraba ta rakosa tana ta addu"a sai da suka fice da Aba ta saki shewa kafin tace afili"Komai na tafiya daidai..yadda muka Tsara..! Wajen goma da wani abu suka mika Hanya Jafar da Aliyu zasu rakasa Filin Jirgi,Sakina kuma har suka tafi bai kara ganinta ba. Ita kuwa tana Shashen Anty Amarya sai da ta tabbatar da sun tafi sannan ta fito ta mata Anty Amarya sallama Domin ta fadamata ne ya barta tatafi Dutse,bata fada mata yace sai gobe zata tafi ba sanin bazata barta tatafi ba in ta fadamata gaskiya. Gida ta koma ko ta kan Amina bata bi ba,Ta hada kayanta akwati Cike da kaya ta kulle Ko"ina harda Kitchen sai da ta kulle ta saka key din a jaka Dakin da Amina ke ciki ne kadai ta bari sai falo tayi Ficewarta Ta sanar ma da megadi zatayi tafiya ammh akwai wata yarinyar agidan ya bita da Allah ya kiyaye Su Danmallam ko Kano basu kai ba Sakina ta kama Hanyar Dutse ko ajikinta. *Janafty* *TFZB2005* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Sun isa Filin jirgin mallam Aminu dake kano shabiyu saura na rana sai dai sun iske jirgin su Danmallam da zai tashi zuwa Jidda da misalin 12pm na rana an fasa ya koma sai 3pm na rana sakamakon Weather babu kyau an dan samu Tsaiko kadan jin haka yasa Umar yace Aliyu da Jafar su koma kawai basai sun jira ba Tunda an sauya Lokaci. Basu wani jima ba suka mai sallama suka tafi daman da motar Aliyun suka zo kafin su tafi sai da Umar ya bama Jafar akan ya siyama Amina waya domin in ya sake yatafi bai siya ba Kashin shi ya bushe wajen Hajiya shi kanshi Jafar yayi mamakin jin yace har da layi zai siya mata ya mata Rigister. Sun koma gida da Labarin Tsaikon da aka samu su maallam suka bisa da Fatan Alheri Aliyu bai tsaya ba Daganan yayi sallama dasu mallam ya Dauki hanyar Dutse.. Amina bata san wainar da ake toyawa ba,sai da ta gaji da barci sannan ta tatashi shima kiran sallar azahar ya tasheta da ake ta kwalawa a wani masallaci dake kusa dasu sannan ta iya tashi gabbanta duk sun gaji Tsami ma kafafunta ke mata sosai,Dakyar ta iya mikewa taja jiki ta shiga Tiolet ta Sha ruwa a famfo sannan tayi alwala tazo tayi sallah sai dai kuma yunwa take ji,Ammh duk da haka bata fita ba ta koma ta kara nadewa a Tunaninta Sakina zata kawo mata kamar yadda ta saba sai har wajen uku saura na Rana bataji motsin kowa ba cikinta har ya fara Curewa waje daya yana mata Rugugi. Tunawa da tayi sakina ba Imani gareta ba Daga ita har megidan sai su barta ta mutu basu da asara shiyasa ta mike ta taimaki kanta kayan datayi amfani dasu da safe ta Dauka ta fita zuwa Falo tana leken sakina sai dai bata ganta ba ko motsi ma babu agidan. Bata gama mamaki ba sai da taga Kitchen a rufe sannan Hankalinta ya tashi,Sai alokacin ta Lura duka Dakunan suna kulle ne mamaki ya kara kamata to ina yan gidan suka shiga ne..? Tabe baki tayi daga baya aranta tace ina Ruwanta dasu sun dade basu tafi ba suma shekara waya damu..! Nan saman Dining ta watsar da kofin da Filet din,kamar zata koma daki sai wata zuciyar tace mata bafa kowa agidan ki sha iska tuna haka yasa ta koma falo ta samu kujera ta zauna tana kara bin Falon da kallo tana nazarinsa baki ta tabe ko ajikinta. Sauran buredin data rage da Safe ya Taimaketa shi ta Samuka ya cikamata Ciki,Har barci ya Dauketa nan saman kujera bata sani ba sai bayan La"sar ta tashi tayi mamakin irin barcin Datake yi kwana biyun nan,Tashi tayi ta koma Daki tayi sallah sannan ta kara fitowa Ciki dai ba abinci shiyasa duk ta kasa sukuni Allah ya taimaketa a saman Dinning Sakina ta manta da kayan Tea su Amina ta samu ta sha da Ruwan Sanyi tunda ba na zafi ta kuma Samu katon Buredi a wajen ta hada dashi taci ta koshi tayi Dam ta koma Daki aranta tana fadin kafin su dawo nayi barci Domin ni bana Tare da yunwa..! Sai dai kuma har akayi mangariba bata ji Duriyar kowa ba sai Hankalin Amina ya fara tashi Har sake fitowa tayi ta Duba ba wanda ya Dawo ta koma ta zauna tayi Tagumi sai kuka tana Tunanin yadda Sakina da Mijinta suka zama marasa imani suka tafi suka barta ita kadai agida wannan Rashin Imani ne Allah ya isanta Bata yafe ba in wani abu ya sameta su da Allah..! Bata kara Tsorata ba sai Dare yayi Amina tsoro ya cikata gashi nepa sun Dauke wuta Duhu ya cika gidan ita kuma batasan inda ake kunna Solar ba batama san da ita agidan ba,Ga shi Daga waje Hadari ya Hadu Farkon Damuna,sai ta kasa zama itace Dakin ta ko falo ta kasa zama sai ta zauna motsi kadan dataji sai ta mike tana waige waige ta fara Firgita sai kuka Amina Bilhakki da gaskiya take kuka saboda Tana tsoron saukan ruwa barin ma in ana iska ko tsawa,tana wannan kukan aka fara iska mai karfi winduna na kadawa da Labulai sai Amina taji kamar ta yi iska ta ganta agida Bayan mamanmu ko Hamida saboda tsoro Daki ta koma ta Dunkule kan gado tana Kuka Lokaci daya da makyarkyata Idanuwanta a kulle gam bata so ma ta bude ga ko"ina duk Duhu Hankalinta gabadaya ya tashi banda Salati da wayyo wayyo babu abunda take yi. Adaidai Lokacin aka tsuke da ruwa mai karfi kamar da bakin kwarya,Ga iska ga Rugugin Tsawa Amina ta rasa ina zata sa kanta taji dadi gabadaya ta Tsorace,ta kamkame jikinta waje daya,ta tusa kanta cikin Filo tana rufe kunnuwanta ga iska sai kada winduna yake yi da Labulai kamar zasu balle Fitsari kamar Amina zatayi a wando Saboda Tsoro hawaye kuwa ya wanke mata fuska da majina bata sanin ma sanda yake fitowa wani na Fitowa wani na Kara fitowa. Adaidai Lokacin Adaidaitan da Danmallam ya hau daga Tasha zuwa gidansa koda ya fito rike da Jakarsa sharkaf yake da ruwa,har diga yake yi sai rawan sanyi yake kudi ya bama mai adaidaitan baisan ko nawa bane Saboda yayi mai Hallaci tunda suka sauka atashar Gumel aka fara Ruwa shi yana da Allagis din Ruwa ya tabasa komai kankantarsa sai yayi mura da Zazzabi in ma bai kwantar dashi ba yayi ta taran masu adaidaita suna cewa baza su shigo Cikin gari ba Dakyar wannan ya Daukosa ganin yana rawan sanyi Ganin irin kudin Daya basa ne yasa ya Leko yana fadin"Nagode yallabai Allah ya kara Budi..! Da kai ya amsamai lokaci daya ya wuce zuwa Bakin get din gidansa ya kwankwansa har sau Biyu shuru Wayarsa ya ciro a aljihun wandonsa yaga ta Mutu daman ba chaji tun suna Filin jirgi Take buga Battery low,sannan kuma ga ruwa ma ya tabata domin sosai ta jike,Kara buga Get din yayi Allah yasa Buzun megadin yaji ya fito da sauri ya leko lokaci Daya yana haskasa da Fitilansa mai Haske ganin Danmallam da kansa yasa Cikin mamaki yake kallonsa bai Damu ba yace ya Budemai get da Sauri ya Budemai karamar kofa ya shiga gidan megadin ya bisa yana tambayansa bai samu tafiya bane..? Eh kawai yace mai lokaci Daya ya Nufi Kofar da zata sada sa da Falon gidansa so yake ya samu yayi wanka da Ruwan zafi ya kwanta,jikinsa kamar ba Nasa ba. Sai da yana shiga Duhu ba Haske abun ya bashi mamaki yana Tunanin ko Sakina ta kwanta ne kafin a Dauke Wuta ba"a kunna Solar ba,Isa Cikin Falon yayi ya isa inda makunnin Solar yake ya kunna Haske ya gauraye duka gidan falon yake bi da kallo ganin sa Tsab ba kuma Hayaniyar kowa Bai Damu ba ya kama Hanyar Dakinsa sai dai kuma me..?Sai yaji sa a rufe Mamaki ya kara kamasa sai ya Nufi Dakin Sakina yana kiran sunanta nan ma yaji kofa a Rufe bai kawo bata nan ba ya fara mata knooking yana Kiran sunanta ammh Shuru..! Amina na dunkule akan gado tana rawan jiki taga lokaci Daya Haske ya kawo leko da kanta tayi sai taji dan sanyi a zatonta nepa sun kawo wuta ne,Sai rabin hankalinta ya kwanta ganin haske sai dai kuma me sai taji kamar tana jin motsi saurarawa tayi sai kuma bata karaji ba sai da ruwan yadan Dauke sama sama taji ana kiran sunan Sakina sai ta kara Tsoracewa kara Dunkulewa tayi saman gado jikinta na rawa kamar a mafarki taji an shigo Dakin data ke sai Amina ta kara shigar da kanta Cikin Filon ba inda jikinta ba ya rawa addu"a kadai take yi duk abunda yazo Bakinta sai ta fada Hawaye kuwa kamar an Bude famfo. Kamar a mafarki taji muryansa yana Fadin"Ke...ina Sakina..? Haka ya fada yana Tsaye daga kofar Dakin yana binta da kallo Cak ta Tsaya da rawan jikin sai da ta Leko ta filon ta hangesa Tsaye sannan ta sauke Numfashi Cikin Dan salama ta Dauke Filon Fuskarta ta mike zaune tana kara Dunkule Hijabin jikinta. Kallonta yake yi ganin hawaye Chaba Chaba a fuskarta yasa yace"Me yasa same ki kike kuka..? Ina sakina taje ne..? Kanta na kasa tace"Ni bansani ba..Ni kadai ce agidan..kuma tsoro nake ji ina ta jin motsi..! Sai ta kara fashemai da kuka bai Damu da kukanta ba Fadi yake yi"Sakina bata nan..? Cikin alamun Tambaya Amina ta Dagamai kai kafin tace"tun dazu ba kowa agidan sai ni kadai agida..Tsoro nake ji don Allah ka maidani gida..! Bai ma Saurareta ba gabadaya ransa ne ya baci kenan Sakina bataji mganarsa ba sai da tatafin yau kyafci yayi kawai yana Sakin Hucin Zafin zuciya,Allah ya kaddara bazasu tashi ba Koda ukun tayi matsalan bata kau ba nan aka sanar dasu sai jibi zasu tashi da Daddare yaso ya kama Hotel anan kano har zuwa jibin sai kuma yaji ya kasa gwara ya dawo gida bayason ya Wahalar da su Jafar yasa bai kira kowa ba ya tafi tasha ya hau motar Gumel sun fara tafiya Motar ta samu matsala wajen awa biyu kafin agama gyaran koda suka shigo gumel an yi issha"i sannan sun zo ana ruwa kamar da bakin kwarya,Shi ba ya iya Fakewa ako"ina shiyasa ruwan ya Tabasa sallar kadai ya tsaya yayi a wani gidan mai,kamar zai wuce gidan Mallam sai kuma ya fasa saboda bayama son sun san Tafiyarsa bata Yuyuba. Sai gashi ya dawo ya iske wannan Rainin da Sakina tayimai gashi bai da key din kowani Daki acikin gidan Suna wajen Hajiya,Sannan akwai wani hannun Jafar yanzu kuma Dare yayi bazai yuyu ya kira yace a kawomai ba sai ya Tada musu hankali a yanayin Dayake ciki ko Ta kan Amina bai bi ba dake sharan hawaye Jakar hanmunsa ya Sabule nan saman Cafet ya taka ya nufi Cikin Tiolet din Dakin ya Rufe. Ransa sai da ya kara baci ganin yadda kazantar Amina ya maidashi ga kayanta nan data cire saman kwandon wanki bazata iya Budewa ta saka ba sannan ga pant din ta nan da ta wanke basu fita ba ta shanya ajikin Famfo ransa ya kara baci bayin Daga gani an Dade ba"a wankesa ba Bashi da wani Zabi sai nan Tiolet din Shiyasa bai fito ba sai da yayi wanka ammh kuma sai da ya wanke Bayin tas sannan ya iya yin wanka da ruwa mai Zafi ya gasa jikinsa yana jin yunwa ga Mura ta kamasa ga kuma Sanyi Dayake ji Towel ya Dauro a kugunsa ya fito kayansa kuma Cikin kwandon wankin ya Bude ya saka yana Fitowa suka hada ido da Amina yadda ta Zabura sai da ta bashi tsoro Ido ta Runtse ta sheka da gudu ta Fice Daga Dakin tana fadin ta shiga uku da Harara ya Bita kafin yaja Tsaki Afili ya Furta kazama kawai. Lotion din Sarood dake saman madubi ya shafa saboda komai nasa na Dakinsa,Jakarsa ya Bude ya sanya Jallabiya baka mai kauri kauri Saboda yana jin sanyi kan gadon yabi da kallo duk kaya ransa ya kara baci kamar zai Dauketa mata sai kuma ya fasa ya fita Falo ya ganta zaune saman cafet ta Dunkule waje daya asaman kanta taji mganarsa yana fadin"Wanene zai Dauke miki wadanchan kayan da kika zubema mutane akan gado..? Agidanku haka kika ga anayi..?Ina amfanin Wardrope din Dake Dakin..? Amina ta kasa Dagowa itafa tunda ta gansa ba riga jikinta ke rawa ashe haka yake da girma itafa saboda Tsoro ko kallonsa ma batayi ba azatonta bai da rigan ne Har lokacin. Shiyasa ta kasa Dagowa tsawa ya Daka mata yana fadin"Ina mgana kina banza dani ni sa"anki ne..?Zaki zo ki kwashe kazantarki ko sai nazo na Tattakaki..! Jin haka yasa ta mike jikinta na rawa tana fadin"Ka..yi hakuri..! Hanyar Dakin ya nuna mata cikin fushi ta wuce sumi sumi tana tsoron yakai mata hannu haka ya tasata gaba sai da ta kwashe kayan saman gado ta Tura cikin wardrope a yamutse ya Dakamata Tsawa yace ta kwaso ta Ninke su hakanan ta kwaso ta ninke ta saka aciki tana sharan kwallah bayan ta gama ya nuna mata kofar Tiolet yana fadin"Shiga ki Tararra kazantar da kika shanya ki Samu waje ki boyesu da safe ki fita dasu bola..! Amina ta kallesa kafin tayi mgana ya Rigata da fadin"zaki wuce ko kuwa..? Da gudu ta shiga ta Tatarra kayan har da Pants din ta Tusa cikin kwandon Tana kuka fadi take"Mamanmu..Hajiya..mallam..! Yana jinta har dasu Hamida ta Kira Dariya ma ta bashi ya tabbatar ma kansa yarinyar nan bata da kunya iskancinta kadan ne. Haka ta fito tana Labe labe tana sharan kwallah kallo Daya yayi mata ya fice daga falon yunwa yake ji sosai kuma ga shi ba wani abu zaune yake saman kujera yayi Tagumi ya rasa mafita har na tsawon wani Lokacin ganin ba mafita yasa ya gyara kwanciyarsa saman kujera mai zaman mutum uku sai dai ina Sanyi da Zazzabi suka Damesa ga shi har Lokacin ana yayyafa kamar ma ruwan zai Dawo Takurewa yayi waje Daya saboda bargon Dakin Amina ko Sanyi  zai kashesa bazai iya saka Jikinsa aciki ba ya tabbata ya fara Warin Datti. Har barci ya fara Dibansa yaji ruwa ya Dawo da iske tashi yayi ya Zuge Duka wimdunan falon sannan ya koma ya kwanta yana Faman kokuwa da yunwar Dake damunsa Ko achan Filin Jirgi Tea kadai yasan sha shima bada yawa ba tun kuma shine acikinsa. Yana bukatar yasha ruwan zafi ko zai gasamasa ya"yan Hanjinsa sannan kuma da Zafin da jikinsa ya Dauka kafin wani Lokacin Hancinsa ya toshe Saboda Mura. Yana kwancen yaji wata Tsawa da akayi shi kanshi sai da ya Bude ido Lokaci daya da walkiya mai Haske da Sauri yace"Bismillah...! Kamar ihunta yaji kafin ya mike yaji ta, ta fadomai ajikin jikinsa tana rawan jiki yana Daga kwancen yajita kan jikinsa yadda ta kamkamesa kamar zata balla sa yana ma yi mamakin karfin hannun yarinyar. Kokarin riketa yake ammh taki basa Dama kanta take tusawa saman kirjinsa da Karfi Tana kuka lokaci Daya tana fadin"Na shiga uku..Ka boyeni Tsawa..Tsawa...! Haka take fadi jikinta na rawa sai kuma ta fara wani abu irin na kakkafewa Saboda an karayin wata Tsawar ganin haka yasa shima sai ya Riketa ya fara Tofamata addu"a ganin yanayinta ya fara tunanin wani abu. Addu"an dayake tofamata yasa sai ta bar kafewan ta koma ta kamkamesa ta fashe da wani kuka mai cin rai har Muryanta na Shidewa fadi take"Wayyo mamanmu...! Haka take fada Cikin kuka duk yadda yaso ya cireta acikin jikinsa ya kasa kamkamesa tayi kamar zasu zama abu Daya tana kuka Danmallan yaji wani bakon al"amarin daya Faru dashi wanda bai taba Faruwa dashi ba ko da akan Sakina ne. Wani irin Dumi yaji jikinsa ya kara Dauka wani abu ne yake yawao ajikin jikinsa Tunda ga yatsun kafarsa har saman kansa nan da nan yaji sa cikin wani yanayin yanayin da bai Taba Riskan kansa ba. Hannuwansa yasa duka Biyu ya Dafe bayan Amina yana Lallashinta lokaci Daya yana Tofa mata addu"a sai aka samu tayi sanyi da kukan data ke yi,Neman yake yi ya rabata da jikinsa ko zai daina jin yanayin dayake ji,ammh ina ta rikesa gam taki Sakinsa ga sanyi ga Iskar ruwa tunda kamar ruwan ya Dawo ne da Bakin kwarya yasa ya mike rike da ita har Cikin Bedroom din da Amina ta baro,Saman gadon ya so ya kwantar da ita ammh Amina taki yarda yana so yaga Fuskarta taki bari sai boye kanta take yi a jikin jikinsa Danmallan ya kalleta sosai yana kara nazarinta meke damun yarinyar nan..?Addu"an ya cigaba da tofa mata sai jikinta yadan saki kadan ammh kuma taki sakinsa gam take rike dashi Cikin Sanyin murya yace"Sakeni mana..An daina Tswan baki ji bane..! Amina taki sakinsa fadi kawai take"Don Allah ka boyeni tsoro nake ji..! Dole ya koma ya zauna saman gadon yana Rike da ita addu"a bata bar bakinsa ba har sai da yaga ta Dawo Cikin natsuwarta sannan ya kyaleta bayan ya kalleta yace"To sakeni..! Da sauri ta sakesa ta koma gefe ta lafe jikin gadon tana raba ido Sauka yayi Daga kan gadon sai gata itama ta Dirko ta rirrikesa juyowa yayi yana kallonta kafin yayi mgama tayi saurin Fadin"Don Allah kada ka fita ina jin Tsoro..! Cikin idanuwanta yake kallo yaga gaskiyanta itakuma kanta ta maida kasa sai hawaye,Cikin Taushinsa yace" ba fita zan yi ba..Nan kasan Cafet zan koma na kwanta ke ki kwanta saman gadon..! Cikin Tsoro ta ce"To..to...to..Don Allah ka da ka fita..Wlh tsoro nake ji..! Ta karishe fada da kuka karo na Farko da ta bata bashi Tsausayi sai ya Tausasa Murya yana fadin"bazan fita ba..ki koma ki kwanta in kin ji tsoro sai kiyi addu"a..! Kai ta gyada mai cikin Sauri yana Tsaye rike da hannunta ya maidata kan gadon ta kwanta tana Raba ido sai Hawaye sharr ganin haka yasa yace"In baki bar kuka ba zan yi tafiyata..! Jin haka yasa da Sauri tace"Toto...To...Don Allah kada ka fita..! Kai ya gyada mata kafin ya Dauki Filo ya jefar a kasa zai kwanta tana binsa da kallo ganin zai kwanta a kasa yasa ta mikamai Bargon Dake kan gadon tana Fadin"ka shimfida bargo ya Danmallam..! Juyowa yayi yana kallonta kafin yace"Kefa..? Kai Tsaye tace"Bana lulluba dashi..! Kamar bazai karba ba sai kuma ya sa ka hannu ya karba Domin yana jin Sanyi,Kwanta wa yayi sannan ya Rufe kafarsa da Bargo sai da ya tabbatar da baya wari lafiya kalau yake shi. Dukkansu idonsu biyu sun kasa barci Yana jin motsinta sai ta tashi ta lekasa sai tagansa sai ta koma ta kwanta Shima bai iya barcin ba yana mamakin Lamarin Amina ne ya fara Zargin yarinyar nan na da wata matsalar da bakowa ya Santa ba. Har barci ya fara Daukansa Yaji ihunta Da Sauri ya bude ido ya mike Lokaci Daya sai gata ta Dirko Daga kan gado ta Fadomai,Tana wani rawan jiki Cikin tashin hankali ya riketa yana faman kiran sunanta bata ji ba Fadi take ye ya Boyeta Tsoro take ji Dakyar da addu"a ta Dawo Daidai sai kuka Rumgumesa tayi gam tana Fadin"Ya Danmallam kayi ma girman Allah ka hawo gadonan mu kwanta..Ko ka maidani gida wlh agida in na tsorata abayan mamanmu ko na Hamida nake iya barci..! Tsausayinta ya kamasa bai iya mata gaddama ba tana rike dashi suka karisa kan gadon sannan yace mata"To sakeni ki hau gadon..! Ba musu ta sake sa ta hau gadon shima ya Hayo yana hawa ta kara Rikesa baki ya saki kawai yana kallonta kafin yace"Kina addu"a kuwa in kikaji irin wannan tsoron..? Kai ta gyada sai hawaye kafin yace"To me kike karantawa..? Amina sai ta Rushemai da kuka baki ya Saki kawai yana kallonta Ya fara Zargin wani abu na Damun yarinyar nan,kansa ciwo yake yi yasa ya samu yalallasheta ta bar kukan yana dora kansa saman Filo tabisa ta Danne kamar zata maida shi Ciki Danmallan ya Dafe kansa kawai yana Salati ita bata san in tana tabasa yanayinsa na Sauyawa bane. Ta gefensa ya zura hannu ya kashe Hasken Solar Dakin ganin Duhu yasa Amina ta saka Ihu Saurin Daka mata Tsawa yayi yana fadin"In kika sake min Ihu zan tashi na yi tafiyata Wlh..! Jin haka yasa tayi Tsit ta koma kan kirjinsa tana Sauke Numfashi Wani al"amari ne da Allah kadai ya bar ma kansa sani yanayinsa yake ji yana Hauhawa Tare da tafiyar Numfashin Amina Dake kan kirjinsa abunda bai taba Tunanin zai Faru dashi ba in yayi Duba da wasu sabbin Abubuwan da suka faru dashi bayan auran Sarood. Lamarin ya faru ne batare daya shirya ba ko nace sun shiryama hakan ba Dukkansu,Umar bazai iya Dora komai akan lamarin dayake shirin Faruwa ba,Amina bata Farga ba Domin tana cikin Tsoro sosai,shiyasa sai da abun yayi nisa ta Farga tayi kokarin kwace kanta sai dai ina Bakin alkalami ya Riga ya bushe..! Acikin wannan Daran ana cikin Tsuga wannan ruwan na Farkon Damina Wani al"amari ya Faru Tsakanin Amina da Danmallam,Umar ya karanto addu'ar da Annabi ya koyar damu acikin Ransa yana kuka,kukan kokowa da yanayinsa ya Ratsa Amina Ratswar da zai zama silar abubuwa Dadama wanda bawa bai tsammani ba.. Wasu basu zata ba..Tsammanin Abunda basu yi Tsammani bane zai Farun.. Alkwarin Allah ya sake cika. Zanen kaddaransu ya hadu. Allah ya amintar da Ruhinsu ya Gauraye jininsu waje daya batare da masu kokarin hana Faruwar hakan sun Farga ba..! *Janafty* *TFZB2006* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Shudewar tsawon mintina Talatin kafin Umar ya mirgina gefen Amina kansa ya nausa kan filon da suke kwance akai dashin yaji alamun hawaye ammh baisan Lokacin da hawaye suka fito daga cikin idanuwansa ba abu daya ke masa yawo a saman kansa na lamarin daya faru tsakaninsa da Amina abunda bai Taba zaton zai iya faruwa ba ko da zai Faru bai taba tunanin shi nan kusa ba.. Yana jin kukan Amina cikin sarkewar murya Tsausayinta ya kamasa sosai sai alokacin abubuwan da suka faru suka Dinga dawomai Daki ashe ashe komai da ya faru saboda wannan ranar ce..? Ashe auran gaggawan da Mallm yayi masa da Amina saboda wannan kaddaran ne..?Ashe Matsawan da Hajiya tayi kan tarewar Amina saboda wannan Kaddaran ne..?Ashe Fasa tafiyarsa duk yau duka Tsarin na Ubangiji ne da faruwar abunda ya faru Tsakaninsa da Amina Duka Tsarin na Ubangiji ne Lalle sarki ne Tare da Godiya ga Allah shugaban Hallitun Duka Duniya. Abunda ya faru bazai iya kwantanta ya akayi ya faru ba sai dai abu Daya ya sani komai daya faru kudurin Allah ne Kaddaransa ne wanda bawa bai isa ya gujemata ba. Bai taba Zaton agaban Amina zai iya Zama namiji ba tun la"akari da abunda ya faru dashi bayan auransa da Sarood in dai yana tare da ita shi ba Namiji bane har yau har gobe bai Taba kasancewa da ita ba bai taba Zargin kowa ba koda Sakina ce kuwa Tunda la"akari da ita a kanta Lafiyarsa kalau sai dai ya barma Allah lamarinsa yana ta addu"a daga baya Daya ga kamar yana cutar da Sarood din yayi mata mgana kan ko zai sauwake mata ne saboda kada ya cutar da ita sai dai taki yarda ta ce zata zauna dashi Har Allah ya basa lafiya,bata taba sanin a wajen sakina Lafiyarsa kalau ba sai da Sakina tayi barin nan suna madina ta fara Zargin wani abu na Faruwa wanda bata sani ba Da tayimai mgana sai ya fadaa mata gaskiyan cewa akanta ne bai iya Zama Namaji ammh a wajen Sakina Lafiyarsa kalau bata kara mai mganar ba tundaga ranar,sai dai ta Dauke mai ba kamar farko datake kokarin nunamai bata Damu ba. Ko tsirara zai ganta bazai taba jin Sha"awarta ba shifa in ba Sakina ba bayajin sha"awar kasancewata da wata mace ko Amina wlh bai ji haka ba Abun yazo ne lokaci daya ne jin Sha"awar da Faruwar abunda ya Faru Duka Lokaci kalilan ne jinsa yayi mai lafiya Fiye da yana Tare da Sakina ma. Amina ta sha wuya sosai sai dai yaga Dauriyanta matuka sosai domin yayi Tunanin zata yi mai ihu fiye da Tunaninsa sai kuma batayi ba kuka dai ta shashi har ta godema Allah Kiran sunan mamanmu da Hamida dasu Hanne kamar hadda har dasu mallam da Hajiya da su ya Jafar dukkansu sun sha kira Harda yaya Dake Kabarinta cikin salama sai da Amina ta kira sunanta. Acikin Duhun Dakin ya Dago kansa yana kallonta ta nade cikin  Hijabinta daya yaye mata cikin Fitan Hayyaci sai kuka take muryanta har ya Dishe Saboda tsoro ta koma chan gefe ta takurai kamar wacce za"a ce kyas ta gudu zazzabi ne ke neman kwantar dashi ammh hakanan ya mike ya Rarrafa ya sauka Daga kan gadon ya lalubi makunnin Wutar solar ya kunna sai yaga nepa sun maido wuta sannan Ruwan ya Dauke sai garin yayi wani sanyi lokaci Daya da wani yanayi mai Dadi. Jallabiyansa ya Laluba ya saka yana mai jin kunyar kansa na abunda ya aikata ma karamar yarinya har ya shige Tiolet bai iya kara kallon Amina ba itama kunya da wani yanayin datake fama dashi tun Faruwar lamarin ta kasa ma ta yi wani Tunani sai kuka. Tana jin karar saukan ruwa a bandaki ta kara dunkule jikinta waje daya sai kuka abunada ya faru ya shammaceta matuka Domim bata taba zatonsa nan kusa ba ayadda abubuwa suka faru da ita Daki Daki ashe ashe bata gama Karban nata kaddaran ba..?wani na tafe bata sani ba..? Bata gama Daukan abunda ya Sameta ba ga wani babban lamarin ya sake kanayayyeta,wai yau itace kwamce gado Daya da ya danmallam har..Har yayi yayi mata..! Sai ta kasa karisa lamarin acikin ranta sai ta saka kuka kawai tanasan abunda ya faru da ita an gayamusu a islamiya sannan kuma tasan irin wannan abun a karance karancen datakeyi ammu batataba auna shi akanta ba har Abada..! Ko da ta hasoshi akanta bata Daukesa nan kusa ba ta Daukesa wani Lokaci mai Tsawo kafin ta riski hakan sai dai ina Bakin Alkalami ya riga ya Bushe yayi Bushewar da ba wanda ya isa ya Hana Faruwar abunda Allah ya Zartar. Tana jin Fitowarsa tayi luf ta Daina kukan Fili sai dai na Boye shi kuma ita yake nazari yana Tunanin yadda zai taimaka mata Gabadaya jikinsa yayi sanyi sannan kuma kunyar Amina yake ji sosai yau ace shi ya Haikema wannan kazamar yarinyar me yafi wannan Abun kunya..? Karisawa yayi bakin gadon yana kokarin Daidaita kansa Jallabiyan jikinsa ya maida jikinsa na Digan ruwa baisan ko karfe nawa bane Saboda wayarsa tunda ta mutu tana Falo saman kujera bai sake bi ta kanta ba. Zama yayi gefen gadon yana kiran sunan Amina cikin sanyinsa. Kira biyu yayi mata bata amsa ba sai ya tashi ji tayi kamar zai hayo gadon yasa tayi Saurin Bude ido muryanta ta Dishe ta amsa da"Na"am...! Bata yarda ta iya Hada ido dashi ba sai ta maida kanta ta kwanta Hawaye na Bin gefen kunnenta. Shima bai kalleta ba saboda kunya kai ya kauda kafin a sanyaye yace"Ki yi hakuri ki bar kukan nan..ki taso na Taimaka miki ki gyara jikinki..! Amina taji wani abun banbarakwai wai ya Taimaka mata duk da Haka take gani a Littafan hausa,ammh ita kam bada ita ba daman ita da Aminunta ne ammh yaya Danmallam bazata iya mikewa ta Hada ido dashi ba sannan jikinta fa ba kaya haka zai ganta..!? Tana wannan Tunanin taji mganarsa yana Fadin"Ko bazaki iya tashi bane..? Amina taji kunya ya kara kamata Duk da Zafin dataji kasanta da jikinta ya Dauka gabadaya ta kasa yin wani motsi ganin haka yasa ya fara Tattare hannun Rigan Jallabiyansa ganin haka yasa tace"Ba..bani da kaya to..! Sai kuma Hawaye sharr ko Sauraranta bai yi ba ya hau kan gadon ya isa gareta Amina ta Fara kuka tana fadin"zan tashi da kaina..Don Allah ka bari..bani da kaya..! Bai Tsaya Sauraranta ba ya Dauketa Cak ita da Zanin gadon ya shiga Cikin Tiolet da ita Daman ya tara mata Ruwan Zafi Cikin jazucci ya toshe rariya ya sakata Ciki Lokaci Daya yana Zare mata Zanin gadon data nade jikinta dashi Amina ta yanka ihu ga na azaba ga na Bata da kaya gaban Mutumin data ke jin kunya fiye da kowa a rayuwarta Sannan bama Haka ba Amina bata da Dabi"ar bayyana Tsiraicinta ko da su Hamida ne bata da wannan Sakewar ballatana gata yau gaban Ya danmallan wanda bata taba kawo ma ranta aure dashi ba ballatana wannan Babbar al"amarin ya gifta a Tsakaninsu ba. Shi kuwa duk da yadda ihunta ya cikamai kunni kansa ya cigaba da Sarawa bai kyaleta ba Idanuwansa na Runtse yana fadin"kiyi hakuri..Kiyi hakuri..Kiyi Hakuri ana asif..Ba da gangan bane..! Sai larabci ya tashi Amina na jinsa ta kasa mgana sai kuka itama idanuwanta ta runtse bata son kallonsa hakanan yana jin kunya yana komai ya taimakamata ta gasa jikinta saboda yasan yanayin. Ita kuwa bata yarda ta Bude ido ba ballatana su hada ido wannan abun da kunya shi kanshi don ya zama Dole ne ga Kunya gashi bai da lafiya Har Lokacin Hancinsa a toshe yake ga Zazzabi ga mura. Sai da ya tabbatar data gasa kanta sannan ya juya mata baya yana fadin"Kin iya wankan Janaba..? Innalillahi Amina ta fada aranta ta rasa ina zata sa kanta taji Dadi wannan abun kunyar har ina jin tayi Shuru ya fara mata bayani Dallah Dallah yadda zata gane sosai Ita dai bata san ma ya juya baya ba domin bata Bude ido ba har ya gama mata Bayani ya fice Daga Tiolet yana Jadaddamata tayi yadda yace mata. Sai da taji karan Rufe Tiolet din ta Bude ido sai ta ga ya fita kirjinta ta fara bi da kallo ganin yan kananun nonuwanta atsaye ihu ta saki mai Hade da kuka Danmallam ya cuceta haka ya Tasata ya kare mata kallo ta Tabbata sai da yagama Zaginta ganin yan nonuwan nata kamar Lemon  tsami Saboda kankanta Tiolet din take bi da kallo ganin zanin gadon daya Daukota dashi ya Watsa sa cikin kwandon wanki tana Hango Jini ajikinsa Domin taga ya baci. Wankan Tsarkinta tayi tana yi tana kuka Sai da ta gama ta Dauko Zanin gadon nan ta kama inda ya baci ta wanke jinin haka kurum take jin bai kamata ta barsa ba. Sai da tagama kuma ta rasa tayaya zata fita bata da kaya ko zani babu acikin Tiolet din,Kasanta Zafi yake mata asannu ma take iya tafiya Cikin kwandon kayan wankin ta fara Kokarin Duba abunda zata saka kamar wasa taji shigowarsa Lokaci Daya da fadin"Kin ga...! Mganarsa ta makale ne sakamkon juyowa da tayi ta kallesa sai kuma ta kalli kanta kafin ta yanka ihu ta koma ta Duka tana kare jikinta cikin kuka take fadin"Don Allah ka fita..Ka fita nace..! Haka take fada tana wani irin kuka Daman Zani ya Dauko mata Cikin kayanta ya miko mata baya ya juya mata bayan ya ijiye mata Zanin nan saman fanfon tiolet din ya Juya ya Fita yana Dafe kansa sai da ta tabbatar da ya fita sannan ta iya tashi ta dauki Zanin ta saka tana cigaba da Sharan kwallarta. Lallabawa tayi ta Leko ta jikin kofa sai taga baya Dakin sannan ta iya fitowa  Tana tafiya sannu sannu ko Mai bata Tsaya shafawa ba jikinta na Haduwa waje Daya ta Rarrafa ta koma kan gadon ta kwanta ta Rufe jikinta da Bargo Tana jin gabobinta na ciwo sannan ga Zazzabi na neman Rufeta,Sanyi take ji gashi ta fara rawan sanyi Hakoranta na Haduwa waje Daya. Shi kuma ihun Datake yi ne baya so sannan ga Halin Dayake ciki yasa ya bara mata Daki ya koma Falo ya Dunkule saman kujera zazzabin bai Damesa bama yadda kansa ke wani Saramai shiyasa ya kasa tashi yaje ya Duba Amina Idanuwansa Biyu aka kira Sallar Farko na asuba yana kwance Cikin matsanancin ciwon kai sannan ga faman kokuwa da Numfashinsa yasa ya kasa tashi ballatana ya Duba Amina sai da yaji an Fara kiran salla na Biyu awasu masallatai ya iya Rarrafawa ya tashi, yana cikin wani Hali Sakina ta Cutar daahi yanzu da Dakinsa na Bude ko panadol sai ya sha sannan yana da mganin mura tunda baya rabo da yin mura Lokaci bayan Lokaci. Sai alokacin ya koma Dakin Daya baro Amina Halin daya isketa sai yaji nasa ma ba komai bane koda ya yaye bargon Jikinta ya jike da Zafin Zazzabi sannan ta kasa barci sai jan Numfashi take daya taba jikinta sai da hankalinsa ya tashi bai Tsaya ba ya Fada Tiolet ya Dauro alwala ya tafi yana kallon Amina Dake neman shidewa rasa ya zai yi da ita yayi ba Mota a hannunsa gidan Baba mallam ya barta sannan key din na wajen Jafar. Kuma yanzu ba lalle ya samu abun hawan da zai kai su asibiti ba,Shiyasa ya karisa gareta ya Ciccibota saman jikinsa yana fadin"Amina ki yi hakuri kin ji ko..! Ba mota a hannuna sannan yanzu asuba ne ba lalle mu samu abun hawa ba balle na kaiki asibiti..! Amina hannunsa ta kamkame sai kuka Hawaye na bin wasu shima Riketa yayi gam Hannu Daya kuma yana Faman share mata hawaye gabadaya ya shiga wani yanayi tsausayinta ya kamata ganin yadda Take neman shidewa sai ya Tsorata ammh bai bar natsuwarsa ba sai ya shiga Tofe ta da addu"a yana Shafa mata a goshi zuwa kirjinta cikin ikon Allah sai ta Fara Sakin numfashinta asake bai daina mata addu"an samun Sauki ba har barci ya fara Fizgarta aransa yasani ko yunwa sai ya mata Illah Shima yunwar har da ita ta sashi yake jin jiki Ganin ta samu barci yasa yana ji ana Sallar asuba ya kasa tashi Saboda Duka Amina tana kan jikinsa ne shiyasa bai yi kokarin tashi ba har aka idar da sallar asuba sai wajen karfe shida ta farka da kuka lokacin Har gari ya waye ga Haske nan ta Window din Bedroom din. Bai Tsaya ma wani Lallashinta ba yace"Amina ki bar kukan nan kaina na kara Daukan zafi wlh..Bari nayi sallah muje asibiti..! Haka ya koma ya kwantar da ita ya Isa gabas ya tada sallar ko kafin ya Idar Amina ta cika Dakin da kuka Dole yana idarwa ya mike yana neman mata wani Hijabin da kayan da Zata saka. Doguwar riga ya Daukomata Amina na kuka tana Faman rintse ido wai kar ya tabata ya Daka mata Tsawa yana Fadin"Dillah kima mutane shuru..Taimakom ki fa nake son nayi ko baki ga halin Da kike ciki bane..? Jin Muryansa cikin Fada yasa ta koma tayi Gum sai hawaye shi ya saka mata kaya har pant shi ya saka mata saboda ya gansu Cikin kayanta Bra ne bai gani ba kuma bai nema ba Tunda bai ga abunda zata sama bra ba. Ta daa ita yayi Tsaye ya Zura mata Hijabi yace tayi sallah bari yazo fita yayi zuwa Haraban gidan suka gaisa da Buzu megadi ya fita waje chan bakin Titi ya samu adaidaita suka Dawo Tare sannan ya shiga Cikin gida ya Taho da Amina Walet dinsa kadai ya Dauka wayarsa kuma yasata a chaji Tana kashe. Sai alokacin Megadi yatuna da Sakina ta fadamai akwai wata agidan sai sannu yake jeramata cikin Hausansa. Ganin yanayin ta yasa Umar ya Dauketa Cak sai cikin adaidaitan tana faman hawaye ba kukan Fili tunda yayi mata Tsawan nan. Wani Asibitin kudi ya kaita likitan Dake kula da asibitin abokinsa ne Tare sukayi primary babansa ne ya Budemai asibiti yana kula dashi sun ci sa'a kuwa sun same shi acikin asibitin Lokacin da Nurse ta shiga Office dinsa ta Sanar dashi Umar bazanga  ne yazo wajensa nan da nan ya bada izinin a shigo dasu. Halin da suka shigo da Amina yasa ko gaisawa ma basu yi da Umar ba yace ya Dorata saman gadon marasa Lafiya Dake office din ya fara Attending dinta shi kuma ya samu kujera ya zauna ya Dafe kansa..! Daga yanayinta da kukan datake yi ya Fahimci wani abu Nurse ya kira ya Fadamata abunda zata karbo masa a phamarcy cikin Lokaci sai gata ta Dawo. Amina tunda taga yana Hada allura ta Fara Ihu ganin da gaske ita za"ayi mawa ta fara zumduma musu ihu,Dr Ghali ya Dago yana kallon Danmallam Dake Dafe kansa yace"Bazanga ina ga fa muna bukatarka anan wajen..! Cikin wani yanayi ya taso kansa ma Saramai yake yi ganinsa a wajensa yasa Amina tayi tsit sai Zaran jajayen ido take cikin wani yanayi yace"Dr yi mata..Bana son hayaniya kainq kamar zai cire..,! Dr.Ghali Cikin nazarinsa yace"Ai tunda kuka shigo na Fahimci 2 patient ne..! Shi dai bai ce komai ba kansa ya kara Dafewa Nurse din dake Dakin ta Rike Amina da karfi aka mata allura Fadi take"Wayyo Mamanmu..Wayyo Allah na Aba..,. Nurse din tana ta lallashinta tana Fadin"Is ok..ai an gama Haba Sister na ki Daina kuka mana an gama baki gani bane..! Amina kukanta take yi bata Saurara ba Dr Ghali na Dariya yace"yanzu zamu ji shuru barci zata yi..! Ko minti goma bata kara ba Amina kaji Tsit sai barci Dr.ghali ya samu Damar Nenan jijiyanta ya saka mata Drip guda Daya. Sannan ya Sallami Nurse din Danmallan ganin hijabin Amina ya Yaye rigarta maa haka har ana ganin Cinyarta yasa ya saka hannu ya gyara mata yana kallonta cikin Lokaci daya ta Rame. Dr.Ghali ya kallesa yana fadin"Ta samu barci kar ka damu bazanga..! Juyowa yayi yazo ya zauna inda ya Tashi kafin yace"Bata fa ci abinci ba Tun jiya..! Dr yace"kada ka damu in tatashi zata ci..bari na Duba ka naga meke damunka dai kafin mu gaisa..! Umar ya Dafe kansa yana Fadin"Ciwom kai ne da mura ne sai Zazzabi..! Tasowa yayi da abun awon Bp yazo ya aunasa kafin ya kallesa yana Fadin"Bp dinka ya yi sama kadan Bazanga..! Sai Murar dakace shiya saka maka ciwon kai..! Aransa fadi yake ai ihun Amina kadai ya isa bp dinsa yayi sama. Mgani ya Rubuta a takarda ya saka Telephone ya Kira Nurse din Data fita da sake shigowa yace taje phamarcy ta karbo masa mganin ba Dadewa sai gata ta dawo da mganguna Da yawa a leda da Tambarin asibiti. Dr.ghali ya Fito dasu yana mai bayanin nasa da na Amina sai da ya gama sannan yace"In ruwan ya kare zata farka sai ku tafi gida..Sannan kai sai ka sha naka saboda kan ya Fadamaka..! Umar ya girgirza kai kafin yace'No sai na koma gida..,! Dr ghali ya jinjina kai kafin yace"Bazanga aure ka kara ba labari..? Aliyu dai mun hadu last yace min ka sake auran wata balarabiya ammh kuma sai naga wannan ba ita bace sannan kuma yarinyace wannan..! Umar ya rasa me zai ce gashi ya Tsare shi da ido daman tun abaya ghali Haruna akwai son ji kwakwaf bakinsa yaji kawai yace"Matatace..Mallam ya auramin ita..! Dr Ghali ya Bude ido yana yar Dariya kafin yace"i see..na zata zakamin wasa ne..Kasan na Fahimci komai fa..Gaskiya kai gentel ne Bazanga baka jimata rauni ba duk da tana karamar yarinya kayi abunda ya Dace..Sannan abu Daya ya wahalar da ita tana jin yunwa sanda abun ya Faru shiyasa ta jigata.. Ammh na mata alluran barci sannan ga Drip nan na saka mata zai taimaka wajen Dawo da Karfin jikinta ga mangunanta na pain reliver dana ciwon jiki in kun koma taci abinci mai kyau sai ka bata tasha ta kwanta ta huta..Kaima kana bukatar Hutu..Ango..Ango ya sha kamshi..! Dariya Umar yayi kawai bai yi mgana ba,shi ya kauda mganar Amina suka shiga hirar duniya yana tambayansa yana madinan har yanzu..? Sannan suka gangaro Hirar yan ajinsu da sukayi makaranta Tare wasu sun taka matsayin manya manya a gwannati sun Dade suna Hira har Umar yaji ya dan warware kadan awa Uku Amina ta kwashe tana barci sannan ta Farka Lokacin Drip ya kare Allah ya taimaka tatashi ba kuka ita kanta taji karfi ajikinta sai abunda ba"a rasa ba Nurse din nan ya Kira ta Cire mata Canulan ya Sallame su Danmallam ya rike hannun Amina bayan ya taimaka mata ta sanya Hijabinta ayadda ya rike ta Hannunsa Daya rike da ledan mganin sai da suka Burge Dr.ghali matuka yaga sun bala"in dacewa matukar sha"awar auran yarinya mai irin shekarun Amina ya kamasa. Godiya Umar yayi ma Dr.ghali sukayi Musabaha Dr ghali yace"Allah ya bada zaman lafiya bazanga .! Aciki ya amsa da Ameen,suna gabda Fita Daga offoce din yace"Kada ka manta ta dinga shiga ruwan zafi..! Kai ya jinjinamai kafin su fice Har wajen asibiti yana rike da hannunta Adaidaita ya samar musu suka shiga basu koma gida ba sai da ya biya dasu wani Reataurant ya siyan musu abinci Takeway biyu sannan ya siya kaza da Youghourt da Hollandian sannan suka koma gida. Yadda ya fita da ita haka ya maidota Allah ya taimaketa ta Daina kuka sai dai da gaske tasha yunwa Takeway din Jallop din shinkafa da nama yayi mata shi kuma yayi ma kansa na Tuwon shinkafa miyar agusi. Amina duka ta cinye shinkafa ko lallashinta bai yi taci ba saboda yunwa tana ci jikinta na rawa. Bayan ta gama ci ya bata kazan taci Rabi ta Dora da madaran youghourt bata Shanye duka ba sannan taji ta koshi shi ya zauna ya balla mata mganugunanta tasha duka ba gaddama ammh kanta na kasa bata iya Hada ido dashi. Sai da ya rakata Daki ta kwanta Bisa gado,ya lullba mata bargo sannan ya Dawo Falo yaci nasa abincin ya sha Holladian ya Sha mgani shima ya koma kan kujera ya kwanta ba"a Dauki Lokaci ba wani barci mai nauyi ya kwashesa..! *Janafty* *TFZB2007* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Tunda ya kwanta bai tashi ba sai karfe biyu narana da wani abu Allah ya taimakesa daya tashin ciwon kan ya sauka harda muran ma ta fara sakinsa bai ji dadi ba tun jiya yake rasa salla cikin jam"i abunda baya faruwa dashi sai da wata lalura mai karfi. Dakin da Amina take ciki ya shiga har Lokacin tana ta barci sanin Halin Datake ciki yasa bai tasheta ba Tiolet ya shiga ya Dauro alwala ya fita Falo yayi sallah jin sa yake yi sakayau kamar ansauke mai wani kaya mai nauyi ajikinsa nan kan kujeran ya cigaba da zama yana Tunanin makomar abunda ya faru Tsakaninsa da karamar yarinya irin Amina inda Allah ya Rufamai asiri natsuwarsa acikin jininsa take bai ce baya rasa natsuwarsa wani Lokacin ba ammh bai cika rasa shi duka ba yanzu da ya zo ma Amina da karfi ya jimata ciwo har ta kai da wata matsalan da asirinsa ya Dade da Tonuwa in kuma Hakan ya faru akwai kunya da kuma zubewar kimarsa ko mallam da Hajiya baya fatan su ji labarin aika aikan daya aikata ita kanta yarinya yana ta mamakin Dauriyanta da jarumtar ta sosai ta bashi mamaki bai taba zaton zata iya Daukansa ba,Duk da abun ba wani Dadewa akayi ba sannan abu ne da yafaru dukkanasu basu da zato ko Tsammani. Gajiya yayi da zaman shuru yasa ya tashi ya kunna Tv tashar Sunna tv ya saka yana sauraran wa"azin Dr.Jabir mai hula har la"asar tayi ya tashi yayi sallah baya so ya fita ya bar Amina ita kadai ta farka ta fara kukanta na Fama har kuma Lokacin bata tashi ba ya Lura kamar akwai mganin Dake sakata barci aciki shiyasa ya barta ta Huta ba laifi ai taji jiki tana Bukatar Hutu. Sai wajen Biyar da Rabi na yammah Amina tatashi shima din ya shiga ya Dubata ne ya isketa zaune kan gado tana ganinsa ta dukar dakai bata son suna Hada ido shima dim kunyarta yake ji yasa ya kauda kansa yana fadin'"Ya jikin ki..? Kanta na kasa ta amsa da cewa da Sauki Tiolet ya shiga ya Hada mata ruwan zafi ya fito yana fadin"Tashi kiyi wanka..Kiyi sallar dake kanki..Azahar da la"asar..! Batayi gaddama ba ta Sauko daga kan gadon tana jin kuzarinta ya fara Dawowa sannan jikinta ya Daina mata Ciwo kamar dazu sai dai har Lokacin kasanta na mata Zafi Tafiya kadan kadan take yi kamar yar koyo zata wuce ta gabansa ba zato taji hannunsa saman kanta ya taba Lokaci Daya yana fadin"Zazzabin ya sauka..!? Cikin sigar Tambaya duk da sanda ya Tabatan dukkansu sai da tsigar Jikin su tatashi da sauri ta gyada mai har jikinta na rawa ta shige Tiolet din da Sauri ya Bita da kallo. Darduma ya shimfida mata ya ijiye mata Hijabi sannan ya koma Falo kada ya Takura mata sai bayan wani Lokaci ya Dawo ya isketa ta gama Sallah bai Tsaya ba ya fita ya Dauko mata Ragowan kazan dazu da youghourt,ya bata daman kamar ya sani Cikinta kamar an yi yasa sai dai bakinta ne ba Dadi ya tasata sai da ta Cinye ta Dora da mdaran sannan ya bata mgungunanta na Rana lum da ido ta dinga yi tana so ta kwanta nan kasa ya Hanata Cikin Sautinsa yace"ki zauna mganin yabi jikinki..Kika kwanta zaki iya yin amai..! Amina ta ji hawaye ya kawomata cikin Sanyin murya tace"Barci nake ji..! Mikewa yayi yana Fadin"Ba kyau barcin yammah dazu ma don naga baki tashi bane..! Ita dai batace komai ba ta maida kanta kasa Filo ta ga ya Dauka ya Fita tana ganin haka ta kwanta saman Cafet ba zato ta ga ya sake dawowa Saboda kada ya ganta yasa ta mike da Saurin da sai da kasanta ya amsa ta Cije baki tana fadin"Wash..! Kallonta yayi kafin yace"Sannu..Ki taso muje falo ki zauna..yammah tayi kwanciyar bata da amfani..! Bataisa tayimai gaddama ba ammh da zai gane da ya barta anan ta zauna din bata son hada ido dashi ko zama kusa dashi ammh bai kyaleta kafa kafa ya Satasa suka koma falo kan kujera mai zaman mutum daya ya zaunar da ita bayan ya kara mata Filo shi kuma ya koma mai zaman mutum biyu ya zauna Lokaci daya ya maida kansa wajen kallon abunda ake haskawa a Qur"an tv Saudi domin ya sauya tasha. Bai kara ma ko kallon barayin Amina ba sai chan ya duba barayinta sai yaga tana barci a zaune mirmishi kawai ya Saki yana da tabbacin mganin akwai mai sa wannan barcin bai tasheta ba sai da aka kira sallah bayan ya Dauro alwala yace taje daki tayi alwala tayi sallah zai tafi masallaci ya dawo Daganan ya fice. Kamar yadda yace haka tayi sai bayan data idar da sallar shuru shuru bai Dawo ba ta fara jin tsoro ita kadai agida Falo ta koma ta Rakube kan kujera tana Zaran ido abu kadan ke sakata kuka yanzu sai kuka Allah ya Taimaketa akwai wutar nepa. Shi kuma bai bar masallaci ba sai da ya Tsaya yayi sallar isha"i yaje Atm ya cire kudi saboda na hannunsa sun kare Allah ya taimakesa ba banki Daya garesa ba,Guda uku garesa anan gida sannan yana da Biyu achan Saudiya ba domin haka ba da Abunda Sakina ta aikatamai da kashinsa ya Bushi wato haka take so koda ya tafin yunwa ta kashe yarinyar Mutane tajamai bala'i wlh Nageria tayi kadan shi da Sakina sai ya nuna mata shi ke auranta ba ita ke auransa ba! Restaurant yaje ya siyo musu abinci da abun sha sannan ya Dawo koda ya Dawo tara ta kusa Amina ya samu nata kuka shi ya zata ma ko ciwon ne ya Dawo ya fara tambayanta ina ne ke mata ciwo..!? Cikin Hawaye tace"Tsoro nake ji..Ni kadai agida..! Bai yi mgana ba illah abinci da yace ta Sauko taci ferfesun ganda ya siyo ma kansa ita kuma na kayan ciki sai Fruit salat saboda a yanayin datake ciki yasan zata ji dadinsa sai ruwa da Maltina da yawa,kuma taci sosai saboda barinta yayi ya koma Daki yayi wanka ya Sauya kaya zuwa wata Jallabiya koda ya fito ta cinye duka harda shan romo tana ganinsa ta koma ta nade waje daya kanta na kasa bai nuna ya Fahimceta ba tambayanta yayi ko ya isheta ta Daga kai Fruit salat din ya Turamata gabanta yace ta sha,cikinta ya cika yasa bata sha da yawa ba mganinta ya bata ta sha bayan ta tabbatar mai da tayi sallah yace taje ta kwanta kamar ya sani barci take ji ammh sai ta kasa tafiya Tsoron kwanciya take yi ita kadai ganin haka yasa yace mata ta je in ya gama abunda yake yi zai shigo..! Dalilin dayasa tatafi taje ta kwanta kenan ba jimawa sai gashi ya shigo shima kadan yaci gandan ya sha mgani nan kasa ya shimfida bargo ya kwanta Alokacin har Amina tayi barci batama sani ba shi ya cire mata Hijabin Jikinta data kwanta dashi Saboda tasha iska ko motsi batayi ba bayan ma mgani ya Lura tana da nauyin barci. Shima yana kwanciya bai Dade ba sai barci saboda na muran yana saka barci karfe hudu na asuba ya tashi yayi wanka ya fice zuwa masallaci sai 6 ya dawo ganin Amina bata da Niyar tashi ya tasheta yace tayi sallar kamar mashayiya haka tatashi tana Idar da Sallar ta koma ta kwanta tana samun Hutu sosai. Shi kuma yana falo yana kallon labarai wayarsa tun jiya ta cika ammh Hakanan yaki kunnata baya so ma wani yasan yana nan Tafiyarsa shekaranjiya bata samu ba sai yau,Sai wajen 8am na safe ya leka Amina tana ta barci bai tasheta ba ya shiga Tiolet kayan data tara a Kwandon wanki ya kwashe harda zanin gado yaso ma ya Kira mai musu wanki ne sai kuma ya fasa,Gwara ya wanke su da kansa yasan in ya tafi bai wanke ba akwai matsala Amina bata san ciwon kanta ba Tukunnah ko kuma yace ba"a koyamata ba Daga yanayin yadda bata iya komai sai tace Mamanmu ko Hamida ke mata Daga gani su suka batata ammh ace kamar ta ace batasan gyara ba sai kazanta. Ta harabn gidan akwai wata Kofa inda suke da famfo da tankinsu na ruwa nan ne sukayi wanki ko shanya in wani abu ya faru na gaggawa,nan ya kwashe kayan ya fita dasu Allah yasa Megadi na Dakinsa bai gansa ba ba Omo kwata kwata agidan sai da ya Fita ya siyo ya Zage ya wanke zanin gadon nan tas da kayan Amina pants dinta kuma Data wanke basu fita ba ya Zubar a Bola domin bazai iya wanke mata ba, ba domin yana kyamarta ba yana da kyamkyami sosai ne sosai bazai iya wankewa ba,Ammah ai karshen kyamkyami kuma ai ya kare tsakaninsa da Amina tunda mai afkuwa ta riga ta afku Abun da ya kusa bashi Dariya Har da Vests cikin kayanta shi yaushe Rabon da ya ga ana sa Vest aransa yace shi ne madadin Bra dinta shi kadai yana wankin yana Dariya har alokacin in ya Tuna Haduwarsa da Amina sai yaji wani iri acikin Ransa yanayi ne da bazai iya Fasaara shi ba ammh yaji matukar mamakin yanayin daya shiga Lokacin kasancewa da ita ko shi yasa Aliyu ke son auran irin su masu kananun shekaru..? Yadan gano sirrin kadan duk da Abun bai wani Samesa Yadda yake so har yaji ya ishesa ba an Dai Taba kawai an bari shima Tabawan kamar kudirin Allah ne. Tas ya wanke su ya Daureye ya shanya su saman igiya sannan ya koma Cikin gida ya Zage ya gyara falon ya Share saboda duk yayi kura saboda isar da akayi shekaran jiya.. Dakin da Amina take ciki ya koma har Lokacin tana barci Zagewa yayi ya shiga Tiolet ya wanke shi Tas ya zo kuma ya gyara Dakin ya share duk ya Gaji bayansa har ciwo yake yi bai zauna ba wanka ya shiga yayi ya fito ya Saka Jallabiya baka ya Dauki walet dinsa ya fita yaje ya siyo musu abinci da katan din Faro sai na maltina Saboda Amina da kuma Tafiyarsa. Sanda ya dawo ta tashi Daga barcin Kuma tayi wanka batare da yace mata ba Sai dai kayan jiya ta maida sai yace ta Cire ta sauya wasu ita daman tayi wankan ne saboda ta Lura yadda yake son wanka kamar kwado koma batayi ba sai yace tayi shiyasa tayi ammh yaushe zata jure wannan aikin kamar wata yar ruwa..! Atamfa ta saka Riga da Sikat sai Alokacin yake ganin Rashin girman Jikinta tsawo dai gareta ba Kiba,Ammh a shekarunta in da tana da manyan gabbai da Tuni tayi Jiki Tunda Hamida da Hanne sun fita Girma yan kirjinta yake kallo kamar yayi Dariya abun chan manne Lalle kwaila ce Tabbas kwailace ya aura kuma kwailan nan ne ta Daukesa Tsab Allah mai iko domin ya yarda da akace abun ba daga shekaru ne ko Girma ba..! Chiips ne ya siyo mata shi kuma Ruwan zafi yace su bashi achan yazo dashi ya sha Tea da buredi ita kuma ta Dora da maltina tayi gatsa ta sha mgani da ruwa yace taje ta kwanta Haka ta mike tana Tafiya sannu sannu ya Bita da kallo Hankalinsa ya kwanta ganin har tafiyarta ta Fara Daidaita ya Fara Tunanin in ya tafi yau Amina bazata iya zama agidan nan ita kadai ba ita kuma wanchan baisan yaushe zata Dawo ba..! Shi kan shi akwai gajiya ajikinsa yasa ya kwanta saman kujera sai barci sai gabda azahar ya farka Sauri Sauri yayi alwala ya tafi msallaci bai Tsaya ba Illah abinci da siyo ma Amina da kayan su Fruit ayaba kankana lemo da Sauransu koda ya dawo ta tashi tayi sallah tana kwance ammh ba barci take yi ba. Inda yayi wanki ya koma ya kwashe kayan Tunda sun bushe ya kawo su Falo ya zauna ya ninke mata sannan ya Shigar mata dashi har Cikin Wardrope ya saka mata yana Fadin"Mai wanki duk bayan sati daya yake zuwa karba..Ki rika Hada kayanki wadanda suka kamata banda Undies nasan ba hankali kika cika ba sai ki Hadamai da Vest dinki..! Kunya ta kama Amina taji kamar ta Nitse shikenan ita kuma ya gama ganin komai nata Zanin gadon ya Ciro ya kalleta yana Fadin"Tashi na Shimfida..Kije falo na siyo miki abinci da Fruit..! Kamar zata fita sai kuma ta fasa ta kallesa yana kakkabe gadon zai shimfida Zanin gadon tace muryanta kasa kasa"Kawo na shimfida..! Ko kallanta bai yi yace"Ki wuce nace..!. Da sauri ta wuce har tana Hardewa sai da taji wani iri a kasanta duk da ya fara warkewa sosai ta ke tsarki da Ruwan zafi tana gani a littafan Hausa in haka tafaru kuma tana so ta warke shiyasa batayi wasa ba sannan kuma Ai da sukaje asibiti Dr haka ya fadarmuau hakan. Tana fita ta jawo ledojin priderice sai kayan Marmari  Ayaba kadai taci sai kankana cikinta ya cika sosai mganinta na Dakin ita kuma tana jin kunyar komawa ba Dadewa sai gashi ya fito da mganin ya zauna gabanta yana Fadin"Matso na nuna miki yadda zaki sha kowanne..! Ba musu ta matso ya nuna mata Duka kuma ya tabbatar da ta gane ya bata ganin bataci abinci ba ya Tambayeta tace sai an juma ta koshi. Da kanta ta maballi mganin tasha ta koma gefe ta Rakube kanta na kasa shima bai bi ta kanta ba ya sha Kankana kadai ya mike ya bar mata falon ta Bisa da kallo aranta tace ashe yana da Mutumci wani lokacin..! Wanka ya shiga Sauri Sauri yake yi Saboda yana so ya isa kano da wuri kuma Motar haya zai bi jirgin su karfe Takwas na Dare zai tashi zuwa jidda. Sannan kuma wa zai kira yanzu yace mai bai tafi ba..?Kowa na da uzurinsa sannan kuma basusan an samu wannan Tsaikon ba,Duk da yasan sun neme sa a layinsa na Saudiya zasu ji a kashe layinsa na nan kuma bai kunna wayar ba yasan zasu yi Tunanin gajiyar tafiyace yasa bai Dora Layin ba yana da Tabbacin harda mallam ya Kirasa yaji ya ya sauka bai samesa ba..har ya shirya cikin Pakistan riga da wando masu ruwan madara yana Tunanin mafitar yadda zai yi da Amina baza ta iya zama ita kadai ba sannan Hajiya bazata taba yarda ya maidata agida ba. Tunanin kiran Hajiya yayi yace ko su Hanne ta saka idi ya kawo su yasan Aminar zata ji dadi da wannan Tunanin ya fito Cikin Shirin Tafiya Rataye da Jakarsa Amina ya iske tana Barci a zaune ya Dade yana kallonta karamar Fuskarta har ta Fada sai yaji Tsausayinta gashi zai tafi ya barta ba wani babba kusa da ita Allah yasa ma taji Sauki sosai. Fuskar yaya yake gani a Fuskarta sai yau ya kara kare ma Amina kallo yaga ba inda ta bar yaya a kama,Baisan sadda ya Furta"Allah ya jikan ki yaya.! Afili yana kara kallon Amina lokaci Daya yana kara ganin yarinta muraratun a kanta ganin har Biyu ta gota yasa ya karisa gabanta ya Durkusa yana Buga jikin kujeran Data jingina tana barci lokaci Daya da Kiran sunanta. Firgigit ta mike tana Raba ido sai ta gansa a gabanta Tuni jikinta ya Fara rawa tana kokarin tashi ya Rike duka Hannuwanta yana fadin"Ki natsu mgana zamu yi..! Duk da ta natsun ammh ta kasa kallonsa Kanta na kasa tana kallon yadda ya rike da hannunta sosai. Cikin Taushinsa yace"Ya jikin ki..? Fata kin sami lafiya..? Kai ta gyadamai alaman eh Cikin bude murya kadan yace"Da baki zaki amsamin..! Sai da runtse ido kafin tace"Eh da sauki..! Kai ya kada kafin yace"Ba inda yake miki Ciwo..? Kai ta kara dagamai kafin kuma da Sauri tace"Ba ko"ina..! Shuru ya gifta na wani Lokaci kokarin Kwace hannunta take yi yaki Sakinta wani yanayi take ji Daya riketa shi kuma sai faman kai da kawon mganar yake yi kafin yayi shahada ya kira sunanta. Amina..! Amsawa tayi ammh bata Dago ba shima bai Damu ba cikin Taushin lazafi yace"Abunda ya faru Tsakaninmu Sirrinmu ne ko..? Yafada yana kallonta kanta na kasa bata yarda ta Dago ba ta gyadamai kai Cikin jin nauyi shima ya cigaba da Fadin"Yauwa to kuma kinsan duk wanda yake fadan sirrin aure Allah zai kona sa ko..? Ba kyau nasan an fada muku a islamiyanku ko..? Nan ma kai ta gyada mai kafin ya cigaba da Fadin"To ina so abunda ya Faru Tsakamin mu ya tsaya iya mu Biyu..Kada ki sake ki Fadama kowa kin jini ko..? Sai alokacin ta Dago ta kallesa suna Hada ido tayi saurin maida idonta kasa shima Fuskewa yayi kafin yace"Kin ji ko baki ji ba Amina..? Cikin sanyi tace"To Allah fa..? Ai ya sani ko..? Mamakinta ya kamata sai bai nuna mata Cikin yanayinsa yace"Eh Dagani sai ke sai Allah..Daman ai shi yana Sama kuma yana kallon Duk abunda muka aikata..! Bana so ki fadama kowa..Koda Hajiya ce ko mallam ko Aba ko Hannatu da Hamida. ! Kai tsaye tace"Harda Mamanmu..? Da Sauri yace"Har da ita kada ki Fadamata in kuma kina so Allah ya Konaki Ranar Lahira shikenan..! Yafada da sigan ya Tsoratarwa Amina mamakinsa ya kamata me ya maidata ne..?Sauma kiramana shashasha kenan..! Da bata san me take yi ba da zata bama wani wannan Labarin mai kunyar Fada ita ba Haka take ba ko da ya ganta yarinya tana da wayau..! Shi a dole zai mata wayau sai abunda ya bata Dariya har sai da ta Murmusa kafin tace"naji insha Allahu bazan Fadima kowa ba..! Jinjina kai yayi Cikin jin Dadi kafin yace"Good naji Dadi..Ki kula da kanki kinji ko..?Kirika wanka sau uku ko Biyu arana sannan ki rika shan mganinki kin ji ni..? Nan ma kai ta gyada mai ba Zato kawai taji ya saka mata kudi a Hannunta ganin yan Dubu Dubu yasa ya Zare ido kafin tayi mgana ya mike yana fadin"Ki rike su a hannunki..Ni yau zan koma..! Zaro ido Amina tayi kafin tace"Ina..?Madina..? Kai tsaye yace mata"Eh tafiyar ma bata yuyu bane da Tuni na tafi..Jafar zai kawo miki waya zamu rika mgana ..!ina dai gargadinki kada ki Fadama kowa..! Amina bata ma jinsa Tunaninta na kan yadda zata zauna ita kadai agidan nan gashi bata san ina gajeran matarsa taje ba tun ranar bai kara mganarta ba..kafin ya ankara Amina ta Fashe da kuka cikin mamaki yake kallonta kafin yace"Kukan me kike yi..?cikin kuka tace"Wlh bazan iya zama agidan nan ni kadai ba Tsoro nake ji ka maidani gida..! Kai Tsaye yace"Nima  naso hakan sai dai  Hajiya da maallam bazasu bari ki koma ba..! Amina na Jan majina tace"Gidammu zan koma bazasu sani ba..! Dariya mganarta ta basa da sai ya Dara kafin yace"In jiwa..? ai da gidanku da gidan mallam Duka Dayane Dole zasu sani..Ki daina kuka zan kira Hajiya ko Hannatu sai tazo ta Zauna Dake kafin Sakina ta Dawo..!. Jin sunan Hanne Daya ambata yasa ta bar kukan ta Dago tana kallonsa kafin tace"Da gaske..? Kai ya gyada mata wani mikewa tayi kafin tace"Yauwa harda Hamida don Allah ya Danmallan kaji..? Ashe tasan sunansa kallonta yayi kafin yace"Wato ku hadu ku fara rashin ji ko..? Kin san dai yanzu ba da bane ko..? Da Sauri Amina tace"eh wlh babu abunda zamu yi..! Kai ya jinjina mata kafin yace"Shikenan sai su zo..! Tsalle ta Daka tana Hawaye tana Dariya zafi taji a kasanta yasa ta Duke tana Wash wash Kallonta yayi kafin yace"Ki rika kula da kanki fa..Kina da Sauran Rauni..! Bata Dago ba ta mikamai kudinsa tana Fadin"Babu abunda zan yi da kudi..!. Shi kuma yace"Ki rike a hsnnunki. zaki koma makaranta Dis Coming monday ki rika yin kudin Break sannan in kina Bukaar wani abu in Sakina ta Dawo ita zaki rika tambaya kina jina ko..? Kai ta gyadamai ammah aranta tace Tab wannan matar muguwa din. Afili kuma cewa tayi"Allah ya kiyaye hanya..! Ya amsa da Amen yana kallonta kanta ya Dafa kafin yace'Allah yayi miki albarka..Na tafi sai in kuma na Dawo..! Sai kuma taji kamar kar ya tafi yana mata Kirki na kwana Biyu wayarsa ya Dauka anan wajen kayan kallo ya Fice ta rakasa da kallo sai da ya Dade da Fita sannan ta koma ta Zauna da kudi a Hannunta tayi Tagumi haka kurum taji kamar kar ya tafi sai dai kuma taji Dadin da su Hanne zasu zo Dadi ya isheta.! Shi kuma yana Fita Tasha ya wuce Direct Allah ya taimakesa ya samu Motar kano ta kusa cika ita ya shiga kuma Motar nada Lafiya sun yi gudu kuma koda biyar tayi yana Filin Jirgin Aminu kano,bayan yayi sallah ne ya kunna wayarsa ya Kira Hajiya.. ****** Hajiya na Cikin Bedroom dinta tana Duba littafin 40 Rabbana Hanne na Tsaye awajen Wardrope dinta tana gyara mata kayanta Jiya mai wanki da guga ya kawo wayar Hajiya Dake kan madubi ta fara kuka alamun kira Hanne tafi kusa da wayar yasa Hajiya tace ta miko mata. Tana Dauko wayar tace"La Hajiya ya Danmaallam ke kiranki..! Hajiya ta ijiye abunda ke hannunta kafin tace"To ya natsa kenan tunda ya kira..! Bata Tsaya Duba lambar ba ta Daga Kiran Lokaci Daya tana amsamai Sallamarsa cikin Sanyinsa ya gaisheta ta amsa tana Fadin"Kun sauka lafiya..?Mallam nata kiran ka bai samu ba Nima har da Safe na gwada layinka nachan ban samu ba..! Cikin Taushinsa yace"Hajiya ai ban tafi ba..Sai yau ne zamu tafi jirgimu zai tashi da karfe takwas na Dare. ! Hajiya ta Bude baki kafin ta Dago wayanta tana kallon Lamba sai Lokacin ta Lura lambarsa ta nan ne saboda ta chan Danmallam2 ta sakamai. Cikin mamaki tace"Ikon Allah to meya faru ba wanda yaji labari don ko da Safe Jafar ya shigo nan nake tambayansa yace shima bai samu wayarka ba..! Umar yace"Matsalan hazo ne Hajiya shiyasa tafiyar bata yuyuba aranar..! Hajiya tace"To Allah yasan hakan shi yafi Zama alheri..! Ya amsa mata da Ameen kafin yayi shuru itama jinsa shuru yasa bata yi mgana ba sai da taga bai da niyar mgana sannan tace"Danmallam lafiya kuwa..?ka kira kuma kayi shuru..? Ya sosa kansa kafin yace"Hajiya ina Filin jirgi kanon tun dazu..! Hajiya tace"Madallah Allah ya Tsare..ya wajen su Aminar ina Fatan Lafiya ko..? Cikin Kasa da Murya yace"Suna lafiya Hajiya..Daman zence ne in ba Damuwa Hannatu da Hamida su tafi yanzu su je su zauna da ita gidan ba kowa..! Hajiya tace"Bangane ba kowa ba Sakinar fa..? Kai Tsaye yace"Bata nan Hajiya..! Bata Damu da tace ina taje ba tace"Allah ya kyauta..To yammh tayi kuma mallam baya gida sannan Gobe jumma'a suna da makaranta Danmallam.. Kai Tsaye yace"Hajiya kiyi hakuri su bar makarantar ta gobe su je su kwanan mata Biyu..In sakina ta Dawo Shikenan sai su dawo gida..kinga tayi kankanta da Zama ita kadai.. sannan ita ma Ranar monday sai ta fara zuwa makarantar..! Hajiya tace"Shikenan bari na Tura su yanzu Daman na bari ne sai Asabar sai su hakura da Haddar su je mata tunda kuma ga wannan laluran bari na nemi ko Uzairu ne ya kai su sabod maallam da idi ya fita..! Danmmallam yace"Uzairu ya Dawo ne..? Hajiya tace"Eh jiya ya Dawo..! Kai Tsaye yace"Hajiya ki basu keys din gidanan su tafi dashi..!. Hajiya bata da bin Diddigi kai Tsaye tace shikenan daganan sukayi sallama ta bisa da Fatan isa Lafiya..tana gama wayar Hanne data kasa kunni taji ta cikin jin Dadi tace'Hajiya wajen Amina zamu..? Hajiya ta mike tana fadin"Eh da naso sai jibi ne ammh yace kuje yau sakinar bata nan..!. Hanne ta Daka Tsalle tana Murna Hajiyw tace"Daman na gama Hadamata komai jiya ma kinsan a kawo Dinkunanta da mallam yayi mata Sabbi yanzu shiga gidan Sa"idu kice ma Balaraba zaku wajen Amina in tana sako ta bada..! Ai da gudu Hanne ta fita Tana murna Hajiya kuma ta fara Hadaa Sabbin kayan da mallam ya Dinkama Amina kala goma da Hijabai sai ita kuma ta mata Turaran wuta da Humra sai Dambun nama dasu Samosa duk an yi package dinsu sai kamshin girki kala kala har da curry har da su Cake sannan ta Siya mata Sabbin panta da sikat da Vest. Ba jimawa sai ga Hamida da Hanne kamar bakinsu zai Tsage saboda murna Hamida ta Dauko kayanta kala Biyu Hanne ta bama Hajiya Turaran Tsinke guda Daya a ledansa wai inji mamanmu akai ma Amina.. Hajiya mamaki ya kamata ko jiyan nan Sa"idu ya sake fadaa mata ya bama Balaraba kudi ta yi ma Amina siyayyan abun Bukata shiyasa ta aika mata ammh sai taga wannan abu haka..? Abun ya bata mamaki ace wajen Amina fa za"aje koda Sa"idu bai ce ya bata kudi ba ta Dauka kayan da zata Hadama Amina sai yafi ma wanda ta Hadamata ammh sai bata saka kokonto aranta ba ta barshi a kila bata siyan mata bane tukunah sai Daga baya..! Hajiya batace komai ba ta Hada Cikin kayan sannan ta Dauko musu keys din gidan ta basu sannan tace Hanne ta Diban ma Amina sinasir din da sukayi da Miya su kai mata jiki na rawa suka Diban mata a coolers suka saka miya Dabam sai murna suke yi Hajiya ta Jaddada musu ranar  Lahadi idi zai Zo ya Daukesu sannan taja kunnensu da su natsu da sakon su gaida Amina..bata yi gaban kanta ba sai da ta kira mallam sukayi mgana da Farko cewa yayi"Hajiya yara nan su kadai agida kina ganin zai yuyu.? Kodai Aminar ta dawo gida kawai har Sakinar ta dawo..! Hajiya tace"Hakan ba mafita bace in mukace haka bazata saba da gidan auranta ba gwara ta zauna watan watarana zata saba..! Da haka mallam ya yarda da Hujjanta yace su Hamidan su tafi da kanta ta Kira uzairu yazo ya kaisu da Daya daga Cikin motocin gidan Daman tun jiya daya Dawo key din motar ke hannunsa. Har suka tafi Hajiya bata Daina mamakin Balaraba ita sai kawai taji abun yayi mata wani iri. Sai da ta koma shashen nata ta ga Sinasir din datace su hanne su dibar ma Amina saboda sauri sun manta dashi kawai ta girgiza tana mirmishi suna ta zumudi dole su manta. Ita kuwa mamanmu Rana Tsaka kawai hanne tazo tace Hajiya tace ta bada Sako zasu wajen Amina.. Ita har ga Allah mantawa ma take da wata Amina kudi kuma tabi ta kansu  Shiyasa ta Dauko wannan Turaran Tsinke wanda mamata ma ta bata shi ya Dade bata taba amfani dashi ba tamikama hanne domin bata taba Zaton Sa"idu yayi zencen ya bata kudi da Hajiya ba. ganin suna ta Murna yasa batace komai ba gwara Hamidan taje ta gano wani irin Halin da Amina ke Ciki don ta tabbata Sakina bazata mata wasa ba ita fa a gayyas gida yanzu ya Rage daga ita sai mijinta Jawaad yanzu in Aba ya Dawo yadaina zuwa saboda samunsa tayi tajamai kunni yaro kuma da Tsoro ko Aba ya Dawo ko ya kirasa daya zo sai yace yana da Homework sai ya tafi hakan yafi ma Mamammu Duniyarta take so taci ita kadai bata san Takura. *Janafty* *TFZB2008* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Amina tana rakube a falo tsoro duk ya cikata tunda Danmallam ya fita take duban idon su hanne ammh har Dare ya fara shiga ana gabda kiran sallar mangariba bata gansu ba Tsoronta Allah kada Dare yayi basu zo ba bazata iya kwana ita kadai ba Tana jin tsoro. Tana zaune kan kujera a rakube saman kujera tana fiki fiki da ido,kamar mara gaskiya ko kwakwaran motsi bata yarda tayi ba, saboda tsoro,Saboda yanayin Datake ciki yasa ko karan Bude get bata ji ba sai ihun kiran sunanta da Hanne da Hamida suke mata kamar daga sama haka taji tana kyalla ido kawai taga Hanne da Hamida da kaya niki niki a Hannunsu,bata san sadda ta Diro daga kan kujera ba duk da yanayin Datake ciki bai sa ta tsaya ba Cikin Farin ciki da murnan da Rabonta da tayi har ta manta ta fada Jikin Hanne Tana Fadin"Oyoyo..oyoyo..! Haka take fada sai hawaye sharr kafin ta Saki hanne ta Rumgume Hamida tana Fadin"Nayi kewarku..Nayi kewarku ba adadi Hanne da Hamida..! Ta fada tana sharan kwallah suma sai da kwallar ta kawo musu suka kara Rumgumeta suna fadin muma mun yi matukar kewarki Amina. Hannunsu taja tana fadin su kariso mana Bakinta yaki Rufuwa Saboda Murna basu Tsaya a falo ba sai Dakin Data kan gadon suka yada Zango Hanne da Hamida suna ta bin Gidan da Dakin da kallo. Amina Murna yasa ta rasa me zata basu kallonsu tayi tana fadin"Kuna jin yunwa.? Ga Abincin chan da ya danmallan ya siyomin kafin ya tafi zaku ci na Dauko muku..? Binta kawai suke da kallo har ta Fice sai gata ta Dawo da shi a Hannunta Hade da maltina,tana shigowa Hamida tace"Mufa mun koshi Sai dai anjima..! Amina ta Dago tana fadin"Hanne kema bazaki ci ba..? Hanne tace"Mun ci abinci agida..Sannan ni ba abincin siya zan ci ba girkin Amarya Amina zan ci..! Hararanta Amina tayi kafin tace"ai sai ki ci abinci bayan matar gidan ta Kulle Kitchen dinta ta tafi bansan inda taje ba..! Hamida ta zaro ido kafin tace"Bangane ba..? Hanne ta karbe da cewa"Naji Hajiya na Fada ammh inaga ya Danmallam ya mata mgana ga keys din gidan gabadaya na wajen Hajiya tace nazo miki dashi..! Amina ta tabe baki batayi mgana ba, Hamida da Hanne sai binta suke da kallon kurillah Amina sai ta Tsargu ta balla musu harara kafin tace"Wai kallon fa na miye..? Hamida ta kalli Hanne suka Tsintsire da Dariya Amina sai ta sha kuni Tana Fadin"Bana son munafunci hanne da Hamida..! Hamida tace"Ba wani gulma munga kinga sauya ne Amina kin rame sannan kinyi wani sanyi kamar bake ba..Eye Amarya Amaryan Ya danmallam to ya amarcin ne da Dadi ko ba Dadi..? Amina sai Hararanta take yi kafin tace"Sai dai ango..Sannan ba Amarci ba amaro..! Gabadayansu suka saka Dariya Farimciki ya cika Amina bakinta yaki Rufuwa Hanne ce tabi Dakin da kallo kafin tace"Dakin waye wannan hala..? Amina tace"Na Sarood ne..! Hamida tace"To ba kayanta a Dakin ne..? Amina tace"Dillah kun isheni ko bari ma na Tambayi mutanen gida baku yi ba..Hamida shegen son jin kwakwaf to da kayanta zaki ganni aciki ne..? Hamida na Dariya tace"Allah ya baki Hakuri Daga tambaya..! Amina ta mata banza ta zauna kusa da Hanne tana Fadin"Hanne ya su Hajiya da Baba mallam..ke kuma Hamida yasu Mamanmu da Aba ina Jawaad su ya Zeenatu sun san an kawo ni nan..? Ta fada a marairaice kamar zatayi kuka Hanne ta tura mata Ledan Hannunta tana fadin"Kowa lafiya..Ga Sakon hajiya tace mu kawo miki Sannan tana gaisheki sosai..! Hamida ma tace"Mamanmu ma na gaisheki Aba da Jawaad duk suna lafiya sannan kowa yaji kina gidan ya Danmallam sunce duk a gaisheki..! Sai Amina ta jawo leda ta fara fito da kaya bakinta yaki Rufuwa Fadi take yi Duk ni kadai wannan..? Tana Daga kaya da Hijaban tana fadin"Wannan nasan aikin baba mallam ne..! Ta daga su yaji da kayan da Hajiya ta Hadamata tace"Wannan kuma na Hajiya ne..! Hanne tace"Kamar kin sani ta kasa sukuni komai sai tace na Amina ne..! Amina sai hawayen Farinciki Fadi take nagode nagode sosai Kafin ta kalli Hamida tana fadin"Hamida ina abun Dadin da mamanmu ta bada ki kawo min bana son wasa fitomin dashu kafin raina ya bci..! Tafada tana mikamata Hannu Har da shan kuni. Hamida sai taji wani iri ta kasa mgana Domin ita dai mamanmu bata bata komai ta kawoma Aminar ba Hanne ce ta ceceta ta Dauko mata Turaran  wutan da mamanmu ta bata ta Saka ma Amina a Hannu tana fadin"Ga shi in ji mamanmu..! Amina ta karba tana jin Dadi tace"Kai nagode sosai nayi kewarta sosai Allah Sarki mamanmu..! Haka take ta fada suna Binta da kallo Sai da tagama gani duka sannan zata kwashi kayan ta maida a ledan Hamida ta hanata ta karba tana fadin"Bari na jera miki Cikin Kwabarki..! Amima tace"Wayyo Anty Hamida i miss u..! Ta fada tana Rumgumeta Hamida ta kwace jikinta tana fadin"Ni sakeni..Dole kiyi missing dina anan bamai miki nasani..! Amina tace"Wlh kuwa kamar kinsani..Ya Danmallam ne in yayi mun masifarsa nake dan ninkewa shi baya son ganin Datti.. Hanne tace"Tab baki san kyamkyamin ya danmallam bane baya shiri da kazami sam Amina sai a Rage son jiki..! Amina ta Harari Hanne kafin tace"In an ki fa..!? Hanne ta mike tana Dariya tace"Sai a Daku..Don Wlh keda megidan ne ba ruwana.! Jin haka yasa Amina tayi shuru su kuma suna mata Dariya Hamida ta Bude Wardrope din taganshi Tsab Cikin mamaki ta juyo tana kallon Amina kafin tace"Amina kece yau da gyaran kayanki..Lalle aure dabam ne..! Amina ta tabe baki kafin tace"Bani na gyara ba shi ya gyara ni fa tunda nazo gidan nan ban saki jikina ba sai yau dana ganku..! Atare Hamida Da Hanne suka Hada baki wajen fadin"Shiwa..? Amina ta kallesu kafun ta ce"Bansani ba..! Lokaci Daya tana juya musu ido Dariya suka kwashemata da shi Hamida tace"Soyayya ruwan zuma ka sha ka bama masoyi..! Amina taki cewa komai ta kyalesu suna ta mata iskanci Hanne ta taya Hamida suka gyara ma Amina kayanta suka jera nasu suma da suka zo dashi suka tsinke da labarin makarantar su da Amina sai dai ta tambayi wance da wance sai jin Dadi take yi Amina ta Dauka Aminene ta tafi kenan sai ta gane cewa har yanzu Aminene na nan Rayuwa ce ta sakata tayi sanyi nan da nan kewar makaranta ya kamata Cikin Jin Dadi tace"Ai ranar monday nima zan koma in ji ya Danmallam..! Hanne tace"Naji yana fadama Hajiya.! Hamida tace'Yauwa gwara ki Dawo Wlh daga Unity har islamiya ba Dadi baki Amina..!. Amina tace"Nima bakusan yadda nake kuka in na tunaku bane kamar in yi Tsalle in gani agida..! Hamida tace"Wlh muma Hajiya take Lallabamu da mallam in sukaga muna kuka ko mun Damu Saboda baki nan..! Hira ce kawai ta Tsinke kamar bakin su bazai gaji ba Daga Dakin Amina Kitchen sukaje suka Bude Hanne ta Sassaka ma Amina su Samosa da danbun namanta a Fridge kar ya lalace suka kuma jera maltinan aciki Duk da akwai lemuka kala kala aciki Sannan suka Diba samosan Hamida ta soya musu. Sai alokacin sukaje sukayi sallar mangariba Amina kamar an bata Kujeran Hajji Saboda murna yau gata ga Hanne ga hamida Bayan sun idar da salla su ka koma Falo sukaci Takeway din nan suka hada da samosa suka kuma sha Tea suka Dora da maltina ransu Fes gashi akwai Wuta basu Dauke ba Amina bata manta da shan mganinta ba bayan sun yi sallar isha"i ta Dauko Zata sha su Hamida suka tambayeta tace tayi Zazzabi ne basu matsa mata ba Tunda daman sunga ta rame kadan sai suka yar da da mganarta.. Afalo suka baje suna Hira Hanne ta kuna kallo gabadaya Tasoshin na wa"azi ne dana addini Ta kashe ta Dawo ta zauna tana fadin"Na manta gidan ustazai ne nan ba"a kallo..! Hamida ta yi Dariya kafin tace"Ko agidanku ai ba kallon kike ba..! Amina tace"Gulma da iyayin Hanne mana..ku wai ina Sa"adatu ne..? Hanne tace"Tana nan mun manta da mun mata mgana mun zo da ita..! Amina ta Harari Hanne kafin tace"Wlh da kuwa daga ke har ita ba matsiyaciyar da zata shigomin gida..! Hanne ta Bude baki ita da Hamida kafin su kalli juna su hada baki suna Fadin"Uhm masu gida da miji..ammh nan ana kuka ana ba"a so..! Ashe dai ana son ya Danmallam din..!.Hanne ta karishe Fada tana Dariya Amina ta karkace baki tace"Allah ya isa Tsakanina daku..Kuma Wlh wuta..! Suka karisa mata da bal bal..! Suna Dariya ta tashi tana jefansu da filon Kujera tana fadin"Munafukai kawai..! Sai da suka gaji suka koma suka zauna Hamida tace"Wato Hanne Halin mutum zanen dutse Amina ko ta Sauya akwai wasu hallayanta da Har Abada bazata sauya su ba..! Hanne tace"Kamar Taurin kai da Tsiwa da Fada..! Amina ta kallesu ta harare su batayi mgana ita kanta ta zata ta koma Ruwan sanyi ammh Sanadin zuwansu yasa ta Fahimci Aminene bata Mutu ba Doguwar suma tayi ta Fara Farfadowa yanzu. Sai kusan goma na Dare suka je suka kwanta achan dim ma wata Hirar suka Dasa tuna irin abubuwan da sukayi suke yi suna Dariya Amina in ta Fara Dariyan mugunta har da Hawaye yau gata ga Hanne da Hamida suna kwance waje Daya Amina ce a Tsakiya Hamida tace"Wai har yanzu baki daina shegen tsoron nan ba..Ke in ba kin kwakwume mutum ba bakya iya barci..? Hanne tace"Ga ya danmallam sai ta Rika kwantamai abaya in suna barci..! Amima ta balla musu harara kafin ta juya ta yi Daidai hannunta kan Cikin Hanne kafanta kan kafafun Hamida suna Tureta tana kara Dorawa Dole suka gaji suka kyaleta Daga haka sukayi addu"an barci suka kwanta. Dayake sun riga sun saba da tashin asuba kiran sallar farko suka tashi suka yi alwala sukayi Raka"atul Fijir sukayi sallah sannan suka koma barci su Hanne an samu waje sai goma na Safe suka tashi suka shiga Kitchen sune har store sai da suka Bude babu abunda babu na kayan abinci kamar ma ba"a Dade da Zuba su. dankalin Turawa Amina tace su soya da kwai haka kuwa akayi Hamida ta Fere Dankalin ita da Amina Hanne ce mai soya kwai wajen Rabin Kires suka soya yazo yayi musu yawa ga Tea nan suka Ragesa cikin su ya cika Hanne tace"Ko zamu kaima megadi ne..? Hamida tace"Ke ina ruwanki ga matar gida batace ba..! Amina data gama shan mganinta ta koma ta kwanta saman Cafet Cikinta ya Cika tace"Uban matar gidan ce Ina ga da wannan gajerar matar yayan Hanne kike mgana itace mai gidan..! Dariya sukayi kafin Hanne tace"Kema me gidan ce wlh..Gashi Dalilin ki har mun Dankwali arziki ko ba Haka ba Hamida..! Ta Daga mata kai suna Dariya har da ta tafawa Amina tayi karamin Tsaki kafin tace"Yan iska kawai..! Sukace sun ji ba bakomai karshenta saman Dining suka maida suka rufe amjima zai musu amfani. Amina Daganan barci ya kwasheta su koma sai suka tashi Hamida ta gyara Dakin da suka kwana da Kitchen Hanne ta gyara Falo suka goge shi Tas sun nemi burner nasa Turaran wuta basu gani ba sai suka kunna na Tsinke Gidan ya Dau kamshi Sai da suka gama Amina tatashi ganin aikin da sukayi ne yasa tayi mika tana Fadin"Dadina da Kawayena akwai aiki kamar Dawakai..! Baki suka saki suna kallonta Hamida tce"Zaki ga Dawakai nan da jibi in muka tafi in kika fara yi da kanki..! Amina tamarairaice kafin tace"wai ku nan da gaske tafiyar zaku yi..? Hanne tace"Wlh Hajiya tace Ranar Lahadi idi zai zo ya Daukemu..! Amina tace"Tare dani kenan domin kafar ku kafata..! Suka Sheke da Dariya kafin Hanne tace"Wa ?ai kin zo kenan yarinya har Abada..! Hararansu tayi ta tashi ta shige Dakin nan ta gansa tas har da Tiolet Hamida ta wanke shi Tas kwanciya tayi kan gado tana kara jin Dadin ganin su Hanne Tare da ita. Su kuma basu kwanta ba Wanka sukayi Hanne ta farayi sannan Hamida da suka ma Amina mgana bayan sun Daketa tatashi Tana masifa Hanne tace"Ki tashi kiyi wanka malama sai ki kwanta..! Amina ta koma ta kwanta tana fadin"Jiya nayi wanka..Wlh ni yau bazan yi ba haba kamar wata kwado..! Basu yi mamaki ba Saboda susan Amina bata shiri da wanka Hamida tace"Amina da fa da yanzu ba Daya bane..Ke yanzu matar aure fa kazanta bana ki bane..! Ko kallonsu batayi ba Hanne tace"Ita ta sani..kishiyoyi dai har Biyu gareki kuma Duka yan gayu ne sannan ya Danmallam bai shiri da kazanta..! Hamida tace"Kuma bazamu ji Dadi ya raina mana ita ba ko kishiyoyinta su ran mata ba..! Amina ta Dago kanta kafin tace"Da ku da Kishiyoyin duk naci ubanku na Zauna Lafiya..! Hamida ta kalli Hanne suka Hada ido suna kunshe Dariyansu tana ganinsu tayi banza dasu daman Hanne da Hamida akwai gulma sun kware wajen munafunci. Haka Amina ta wuni batayi wanka ba sun gaji da mata mgana sun kyaleta da Rana basu yi girki ba sauran kwan daya rage suka ci suka kuma kara soya samosa suka ci suka hada da maltina da Daddare kuma suka Tarun ma Dambun mana suka ci suka kwanta Washegari Hamida da Hanne Dakyar suka ga Safe suka kwana Murdawan Ciki da Zawo Amina Daman akwai Lafiyan ciki bakomai ke bata mata Ciki ba. Haka ta Dinga musu Dariya Hamida tace"Hanne Amina wlh muguwace tasan cikinta ita lafiyansa kalau ba sai tace kada mu ci da yawa ba..! Hanne daman nada ulcer tana Mai da Numfashi tace"Ni sam na manta inda Ulcer ma..! Amina me zatayi ban Dariya Cikin Dariya tace"Hajiya ni tace ku kawo ma abu ammh Saboda maita ku sai an ci komai daku kadan kuka gani..ma..! Haka ta wuni yi musu Dariya Ranar ban da Tea basu iya cin komai ba sai da Daddare da suka ji sauki Zawon ya Tsaya da ciwon ciki sannan suka Dafa Doya sukayi miyar kwai suka ci suka kwanta. Washegari ma barcin su suka sha sai sha Biyu suka tashi suka karya da Sauran Doyan jiya suka gyara gidan Amina na zaune tana kallonsu An samu Amina tayi wanka jiya ammh yau kam tace bazatayi ba ta gaji sudai sukayi suka Sauya kaya Daganan aka Fara Tunanin me za"a Dafa. Amina tace Hamida tayi musu wainar Fulawar datake yi agida mai Dadi Tunda ga Yajin da Hajiya ta kawo mata . Nan da nan suka yarda da mganar Amina suka Dunguma zuwa kitchen suna neman Faluwa sun sha mamaki Fulawa buhu Guda ko kwata ba"a taba ba Nan suka Diba suka kwaba suka saka kwai ma"ishi suka yanka albasa Hanne tayi Gireting din kayan miya da suka gani Cikin Freezer harda nama wanda Amina tace soya shi za su yi Hanne tace sai dai Ferfesu basu da lafiyan ciki..Amina na Dariya tace"A soya yafi Dadi..! Hanne tace"Muguwa muguntarki ta kare miki Amina..! Sai Dariya Amina ke kyatatawa har tana Hawaye. ******** Mamanmu na kitchen tana soya kifin da Aba yaba Jafar ya kawo Dazu wayarta Dake tsakar gida kan Tabarma ta Dau kara alamun kira Gidan ba kowa sai ita kadai Hamida suna gidan Amima jawaad kuma sun tafi Hadda. Burin Mamanmu ya cika ita kadai ke juyi a gidan Sa"idu sai abunda tace akeyi sai kuma an nemi Shawaranta. Fitowa tayi da Sauri bayan ta juya kifin Dake kan gas kada kafin ta Dawo ya Kone. Tana Daukan wayanta taga Madina ke kiranta sai da gabanta ya fadi Bata rai tayi afili ta Furta"Har Abada madina baza ta barni na Huta ba Haba wannan kawwazzaba dame tayi kama mtswww..! Ta ja wani Dogon Tsaki kafin ta Daidaita kanta ta Daga kiran tana Fadin"Buhun Sikari baki Farin banza ba..! Dagachan bangaran Anty Amarya ta Katseta da Fadin"Ba bu abunda zaki Fadamin Ya sanyayamin rai Dayyaba..Ki ma yimin shuru kawai..! Mamanmu ta marairaice kafin tace"Me kuma ya faru..? Allah yasa ba kwabarmu ce zatayi Ruwa ba..! Anty amarya tace"Kwabata dai Zatayi Ruwa Dayyaba...aike kin samu abunda kike so shiyasa kika maidani Wata Shashasha ko nema na baki yi Dayyaba Tunda na gama Taimaka miki kin samu Sa"idu a Hannunki ni kuma kin kasa taimakamin nawa Burin ya cika ko..? Ni ban raba Maallam da Sa'idu ba sannan ta bangaran Sakina har yau ba wani mgana mai Dadi..! Mamanmu ta Harari wayar kafin tace cikin karyewan murya"Haba Madina meyasa kin cika gaggwa ne..? Kin Tsaya na gayamiki irin kokarin da ni ke nan ina yi miki akan abubuwa su Daidaita kuma da kike Fadin na Samu Sa"idu ai ban ga samunsa ba Domin har yanzu akwai rina akaga Hajiya da mallam sun sha gabana..mganar Sakina kuma ai mun gama mgana kince zaki sa ka mallam yasa turama danmallam son ko ya tafi sai ya Dawo ya Dauketa sannan mu na Fatan Zata samu ciki kuma zai zauna Zata Haifesa da yardan Allah mganar Shegiyar yarinyar nan kuma Amina sai dai su mallam su gaji su Raba bazai Taba wani amfani ba..! Sai alokacin Anty Amarya taji ta dan Sauka Cikin Saukan Numfashi tace"Dayyaba ni Hankalina yaki kwanciya gani nake yi abubuwa duk suna ta lalacemin Tsarina duk ya lalace..Umar din ya tafi ni Kawai Burina ya Dawo ya Dauki Sakina su koma,in har ya tafi mallam yace ba lalle ya dawo nan kusa ba kinga mallam da Hajiya haka zasu gaji da ganinta ahaka su raba auren daman wanchan balarabiya Hoto ce itama in ta gaji zata kara gaba ne.. Mamanmu tace"Sosai ma ina amfani Zama da miji Hotiho ba wani amfani ina mai Tabbatar miki bazata zauna ba..Ki kwantar da Hankalinki Saura Kiris burinmu ya cika kada ki manta Sakina ba Juya bace tana samun cikin yana Barewa ne..! Anty amarya tace"Dayyaba shine abun Damuwata ko an samu cikin baya Zama na fara Tunanin akwai wani a kasa..! Mamanmu tace"Ko..? Kanar na menene..? Anty amarya tace"Ciki wajen sau Hudu da an sanu sai ya lalace anya Dayyaba..? Mamanmu tace"To kin sa malam ya Duba mana kuwa..? Tace"Eh ya Duba yace bai ga komai ba..Ammh ni haka kurum nake ji akwai wani wanda muke Tufka Daga Gefe yana mara warwara ko shakka bana yi.. kinsan daman ya taba Fadamin acikin matan mallam akwai wacce itama bata zauna ba..bai dai Fadamin sunan kowa ba. Mamanmu tace"to wa kike Zargi..? Anty Amarya tace"Cikin matan mallam ne dai..Ko Haj.Nasara ko Hj.Uwani..Akwai wacce acikin su bata so mu cimma namu burin..! Mamanmu ta zaro ido kafin tace"in ma sune to saboda mene..? Anty amarya tace"Saboda cikar Burinta itama..Kamar yadda muke son mu cimma namu Burin..! Mamanmu tace"Tabdijam akwai kura Tsugunno bata kare mana ba..! Ni fa basu nake zargi ba ina Tunanin ko dai Hajiya ce bata so Sakina ta Haihu..? Anty amarya tace"Ba Hajiya bace..Bata yar da za"ayi ta hana Sakina Haihu wa kada ki fa manta Umar D'anta ne..zata fi kowa son ganin kwansa a duniya..! Mamanmu ta jinjina kai kafin tace"Kuma fa hakane..! Ni ban ma taba kawo wannan Tunanin ba sai da kika Fada na gane zai iya Faruwa..! Anty amarya tace"Ai ki bar mugu..Bai da kama Dayyaba..Da mugu nada kama da Tuni Sa"idu da ya"yansa basu baki Dukkan yarda ba..Da mugu nada kama da Yaya bata taba Sakin miki Ragamar ya"yanta ba har Abada..! Mamanmu ta bata rai kafin tace"Bangane ba..? Ki sa min jaye mugaye zaki ce..! Anty amarya tayi wata Dariya kafin tace"Ban kai ki mugunta ba Dayyaba. ina mai kara gayamiki ban kai ki ba..Domin ko ni sanda kika zomin da Fuskarki ta Dayyaba domin mu Hada Hannu na Girgiza ballatana Sa"idu da ya"yanku..? Ina mai Tabbatar miki kiji Dadinki yanzu ammh in alalan geren mu ya tashi yin Ruwa da Tsami wlh naki sai yafi Nawa Tsamewa..! Mamanmu tace"Da izinin lahi bazan ga haka ba..Ni Dayyaba Nasara na sani ba Faduwa ba Madina..! Dariya tasake yi kafin tace"Muna fatan haka yanzu ba wannan ba yaushe zamu hadu..? Ya kamata mu sauya Tsarin mu sannan mu san ta yadda zamu gano wanda ke kokarin batamana aiki..! Mamanmu tace"Ina so mu hadu bana samun Lokaci ne gida ba kowa sai ni kadai..Hamida bata nan tana gidan Amina..! Anty Amarya ta Zaro ido kafin tace"Wata Aminar..? Mamanmu ta tabe baki tana fadin"Wacce kika sani mana..Bakisan suna gidan Amina ita da Hanne ba Tun Ranar alhamis da yammah Hajiya ta turasu..! Anty Amarya ta mike Daga Zaunen Datake gefen gadonta tana fadin"Kan burauba..Bansani ba..Naji dai jiya Sa"adatun na fadin bata ganinsu a Hadda ban maida mganar mai ma"ana ba shiyasa ban bincika ba..Na Shigesu Dayyaba Sakinarma tun aranar da Umar ya koma tana Dutse..! Mamanmu tayi shewa kafin tace"Au to..Aiko tayi wauta suna chan ta bar musu gidan suna Yadda suka ga Dama..! Anty Amarya bata jira cewar Mamanmu ba ta yanke kiran ta bar Mamanmu da Hararan waya Lokaci Daya ta Ijiyeta nan kan Tabarma ta koma Kitchen tana fadin"Kawai kin zo kin Tsaidani kan mganar banza..Badai nawa Burin ya cika ba..Ban Damu ba..In dai ni na samu abunda nake so Uban kowa kada ya samu..! Bana kaunar Amina ta Dawomin gidan nan zata lalatamin Tsarina Yadda tatafi tatafi kenan har Abada Shegiyar yarinya mai kama da Uwarta..! Haka tayi ta manganganu ita kadai.tana ciga da suyan kifinta Duniya tayi mata Dadi. Anty Amarya kuwa Lambar Sakina ta Kira sai da kusa katsewa ta Daga ko Sallamanta bata amsa ba ta fara Fadin"To shashassha..kina nan kwance ga Amina chan da su Hamida suna yadda suka ga dama da gidanki. ! Sakina na kwance ne sai da ta mike tana Fadin"Bangane ba.? Nan Anty ta shaida mata abunda mamanmu ta fadamata Sakina tace"Kuturun uba.... to ubansu zasu ci na kulle ko"ina har Kitchen fa..! Anty Amarya kamar ta Zageta haka taji cikin Tsawa tace"Dayake ke kadai ke da key din gidan ba..? Karki manta Uwarsa ma na dashi kuma na tabbata sun tafi dashi ki cigaba da zama agidan da nayi Burin ki Rayu ke kadai tun ba"a je ko"ina ba yana neman ya zama ba naki ba..! Daga haka ta Datse kiran tana Faman Huci Dagachan Dutse kuwa Sakina ta Diro Daga kan gado ta Fada wanka sai yanzu ta Dawo Cikin Hayyacinta. Allah ya taimaketa akwai wani yayanta zai taho kano shi ya Daukota har Gumel har kofar gidanta ya ijiyeta sannan ya wuce alokacin Shida na yammah har tayi san da ta abuga get din megadi yazo ya Bude mata bata Tsaya amsa sannu da zuwansa ba taja akwatinta ta nufi Cikin Falon. Amina da Hanne suna Zaune Saman Cafet hamida na Saman kujera suna Hira sannan ga filets nan da suka gama cin wainar Fulawarsu nan da Ferfesun naman rago da sukayi ga Kofuna ga abun maltinan da suka gama sha Falon dai kaf ba Kintsi  Saboda  tunda suka gama suka koma gefe suna Hira sun ma manta yau zasu koma gida Tsabar yadda Rayuwa tayi musu Dadi gaddamace ta Sarke Tsakanin Hanne da Amina kan lokacin Bikin su ya Abida Amina na Fadin yadda Hanne ta manne ma Sa"adatu saboda yar"uwatance ita kuma Hanne tana kokarin nuna ma Amina Daga su har Sa"adatu duk Dayane hamida kuwa bata sako bakinta ba sanin Halin gaddaman Amina ko bata da gaskiya bata saki. kwata kwata basu san Sakina ta Shigo ba ashe ta Dade Tsaye taba Bin Falon gidanta da kallo yadda ya zama. Ranta in yayi Dubu ya baci akwatin Hannunta ta saki ji kake garam lokaci Daya ta Rike kugu tana fadin"Kutumar Uban chan Falo na ne ya koma kamar gidan abinci? Lalle yau zaku gane baku da wayau duk sai naci Ubanku daga ku har kazamar data jawo ku..! Ta karishe fada tana Cire gyalenta ta Ci Darama dashi Tana jifan su Amina da wani matsiyancin kallo wadanda sai alokacin suka san da wanzuwarta afalon Hamida da Hanne ne suka Tsorata Amina kuwa ko ajikinta itama kallon rainin ta maida ma Sakina kafin ta tabe baki ta kauda kai. Hanne ce da Hamifa suka mike da Sauri Jikinsu na rawa Hanne na faman Fadin"Sannu da zuwa Anty Sakina..! Ita kuma Hamida ta fara Tattara filets din tana fadin"Kuyi hakuri yanzu zamu share mu gyara ko"ina..! Sakina ta kariso Falon tana Hararansu Lokaci Daya tana fadin"Dilla kumin shuru..uban wa ya baku izinin zuwarmin gida batare da sanina ba.? Hannu hamida tabi da kallo kafin tace"Kan uba har kitchen dina ma kuka Bude kuka shiga kuna min kazanta..? Yau zan ga wanda zai Rabamu daku acikin gidan nan..! Amina mamaki kamata yayi ganin yadda Hamida da Hanne suke bata Hakuri jikinsu na rawa sai Faman Zaginsu take yi ranta ya baci ta Dauka tayi sanyi ashe batayi ba batasan Sadda ta Mike ba sai jin muryanta sukayi tana fadin"Dillah ku daina bata Hakuri..Kun zo din ai ba gidan Uban kowa bane nan..Gidan mijina ne kamar yadda yake gidan mijinta sannan kada ta manta nan din gidan yayanku ne ko sama da kasa Zata Hade shi din jininku ne wata fa..?Yar karo ce..Saboda haka ku saki jikin ku ku Wala ba wacce ta isa ta Daga muku Hannu ina gidan nan wlh..! Ta karishe Fada itama tana Hararan Sakinar da manyan idanuwanta. Hamida da Hanne suna ta kyafta ma Amina ido bata bi ta kansu ba Sakina ta nuna kanta tana fadin"Wai dani kike..? Amina ta karkace baki tace"Ban kira suna ba..Ammh in kin Tsargu ba ruwana..! Sakina taji ranta ya kara baci Tayi kukan kura tayi kan Amina tana Fadin"Yau sai naci Ubanki acikin gidan nan.! Su Hamida suka shiga Tsakani suna bata Hakuri Hanne sai ta Fara kuka tana fadin"kiyi hakuri yanzu zamu gyara ko"ina Hanida ko ba"a zo Daukan mu ba yanzu zamu tafi..! Amina datayi ke Tsaye Cikin mamakin ko Sakina Dukanta zatayi tayi Shewa kafin tace"Wlh badai ubana ba..kin gama Zagin Ubana na kyaleki..! Sakina tace"Sai nawa Uban ko..? Amina ta Tura dankwali Gaban goshi kafin tace"To nidai ban ce ba..Ko banza nasan Darajan tsohon wasu..! Sakina ta Harzuka haka take Zagin Amina har tana fadin"Badai ke yar iska bace ko...? Bari  zan kira  habibin Wlh bazan iya Zama Da kazama irin ki acikin gidana ba. ! Amina tace"Gidanki ko gidanmu..? Malama ki kara Min jaye..! Mu uku keda wannan gidan Dake da ni Amina da yar balarabiya baki da kuma yadda zaki yi..! Ran sakina ya baci tana mamakin yadda yarinya karama ta zauna tana Fada mata mgana Hamida da Hanne na Faman bata Hakuri suna fadin zasu tafi. Amina ta kallesu tace"kudai wlh bazanye ne..To uwarki ce ita..kun zauna kuna ta wani bata Hakuri tana Kara Zagin ku..bazaku gyaran ba tayi abunda zatayi..! Hanne tace"A"a Amina mu muka bata bari mu gyara mu zo mu tafi..! Amina tace"In kun tafi Allah tsinan naga mai fita agidan nan..! Ta fada tana wani juya ido kafin taja Tsaki Sakina taji kamar tayi Bindiga ta koma ta Dauko akwatina Kamar Kububuwa ta wuce ta Bude Dakinta ta Shiga tana Tunanin yadda zata yi Biji Biji da Amina Umar ya ja mata raini wajen wannan yarinyar. Tana shigewa ta banko kofa Amina tayi Tsaki ta koma ta zauna hakanan taji Ranta na kuma kamar tayi Bindiga haka take kada kafa tana Girgiza jikinta Hamida da Hanne suka Bita da kallo basu tankata ba Azaton su Jidalin Amina ya ragu ashe karuwa yayi basu sani ba hamida ta tatattara komai Takai kitchen ta Hada wanke wanke Hanne kuma ta Fara gyaran Falon Amina na Zaune tana kada kafa Ranta na mata wani Zafi kamar ana Hura mata wuta ita kanta Hanne bata taba ganin Amina tayi irin wannan ba,Shiyasa bata tankata ba itama batace mata komai ba..! *Janafty* *TFZB2009* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Hamida da Hanne cikin rawan jiki suka gyara komai Hanne ta share falo ta goge shi tas hamida kuma ta kintsa Kitchen din ta wanke kwanukan da suka bata ta goge kitchen lokacin har an fara sallar mangariba a masallatai yasa suka wuce dakin da Amina take suka isketa Ta fara salla,suma alwalan suka Dauro suka zo suka jera da Amina suka tada salla har suka idar Amina bata musu mgana ba suma ganinta cikin wannan yanayin yasa suka mata shuru. Tana ganinsu suna hada kaya sai ranta ya kara baci Haka kurum take jin wani zafin zuciya wanda ko a baya ba irinsa take ji ba tasan dai tana Saurin Hasala ammh Bata da Saurin Harzuka kamar na yanzu sai ta Danganta haka da Tafiyar su Hanne Abunda bata sani ba wannan zafin zuciyar da aka kara mata ne maimakon tayi shi ga wanda akayi Domin sa sai ya kuskuremai Bashi a kusa da ita sai abun zai tsaya ga wanda ke kusa da ita da kuma wanda ke bata mata rai a kusa. Sallar da tayi ne ma yasa taji dan Dama Dama ammh ranta yagama baci da abunda Sakina tayi mata yau ji take yi daman ta Tabata da sunan daambe da ta gane bata da wayau a yadda take jin kanta da karfi sai sun kwashi yan kallo domin karfin jikinta ya Dawo sannan ta warke kasanta ma batajin wani ciwo ruwan zafi da mgangunar nan sun tainaka mata wajen dawowa da ita Daidai shiyasa ko su Hanne basu Fahimci komai ba tota ina ma zasu gane..? Amina ta fi su Budewar ido kan irin abubuwan nan saboda ita tana karance karancen Littafan hausa su kuma fa dukum ne su basu riga sun san wasu abubuwan kamar yadda ta sani ba. Suna cikin Hada kayan ne suka ji knooking daga kofar falon Amina ta Dago tana kallonsu hanne ma ta kalleta kafin ta mike tana fadin"Ina ga Idi ne..! Ba jimawa sai ga shi ta dawo tana Fadin"Shine Hamida..Hajiya tace maza maza ya Daukomu gobe akwai makaranta..! Hamida batace komai ba ta Zura Hijabinta haka Hanne suka Dauki Ledan kayansu Hamida ta kalli Amina Dake Zaune tana kallonsu tace"Amina mu zamu tafi.. Amina tayi kamar bata ji su ba kuka taji yana neman tasomata Hanne ce Cikin karfin hali tace"Kiyi hakuri ai gobe zamu biyo mu Dauke ki..Ki shirya da wuri..! Hamida da Hanne suma karfin hali suke kada su yi kuka ganin yadda Amina Tayi ganin ta musu banza yasa Hanne taja Hannun Hamida suka Fice Daga Dakin Amina na ganin haka ta mike Zaraf ta biyosu falon tana Fadin"Yanzu wai tafiya zaku yi..? Ku bari gobe mana basai mu tafi makarantar tare ba..! Hanne tace"To ai uniform din mu na gida kuma kinga Hajiya ce ta aiko a Daukemu..! Amina bata kara mgana ba kawai ta Juya ta koma Dakinta ta Zauna gefen gado sai kuka wiwi kamar wacce aka Daketa Tana jin karan Bude get tasan su Hanne sun tafi kawai sai ta kwanta Saman Cafet ta cigaba da kukanta kuka mai Cin rai rabin kukan na kewa ne da Zaman kadaici rabin kukam kuma na kuncin zuciyar da ta rasa Dalilinsa wani Kululune ya Tsaya mata  arai yaki wucewa tana Tunanin in tayi kuka zata samu sauki. Sakina kuwa ko da ta shiga Dakinta ko gani batayi Ranta ya gama baci tana Tunanin karamar yarinya kazama kamar Amina ce zata tsaya tana Zaginta Lalle sai ta gane bata da wayau Zata Kira Habibi ta Fadamai Rashin kunyar Amina sai ya Dauki mataki akanta domin ita bazata iya Zama da ita haka ba Allah nagani. Wayarta ta Dauka ta kira Lambarsa ta Saudiya ta shiga sau biyu bai Dauka ba ta Duba Lokaci bakwai Saura na Dare su achan zai zama tara da wani abu kenan bai isa ya kwanta ba Duk da Tun da ya tafi sai jiya ta kirasa suka gaisa bai tsawaita mganar ba yace mata yana Aji ne in ya koma gida zai kirata kuma bai kara kiranta ba. Ganin bai Dauka ba Sarood ta kira ita kan ta Dauka suka gaisa take tambayanta Habibi ta sanar da ita baya nan ya tafi Cikin gari masallaci Har yanzu bai shigo ba. Sakina ta gyara zama tana cema Sarood  ta rokar mata Umar don Allah ya zo ya Dauketa yaki komawa da ita Madina Sarood tace mata kawai zata mai mgana da haka suka rabu Sakinar ta Lura kamar Sarood din bata son Wata Doguwar magana da ita tana sota kawomata Labarin Amina sai tayi Saurin Dakile mganar da cewa Tana girki ne kada ya kone.. Abunda bata sani ba ita kanta Sarood din tunda ya Dawo sama sama suke domin daman kafin su tafi sun yi Rigimar tahowa tun Tarkon da Sakina ta Hadama mata ita kuma ta Fada har sai da Mahaifinta ya shiga mganar To kishi da kuma takaicin abunda ke Faruwa Tsakaninamsu ya Rufemata ido gani take yi yana chan yana jin Dadinsa da Sakina da Amaryansa ita kuma ya barta anan ita bata ga Tsuntsun ba ga Tarko shiyasa taso ta Biyosa batare da sanin ko iyayanta nata ba Sai dai kalmar daya fadamata na sai tazo ne ya bata tsoro yasa ta fasa zuwa Tasan Halinsa kaifi Daya ne. To kwana Hudu Tsakani ya Dawo Tunda ya Dawo ta sakamai Rigimar ita bazata yarda ba, da gangan yake yi Ba wai bazai iya kadaicewa da ita bane meyasa shi da Sakina Lafiya kuma gashi har yayi amarya itama tasan ai lafiya kalau meyasa sai itane bazai iya Raba ba . Alokacin akwai gajiya tare da shi,Shiyasa bai biyemata ba sannan kuma ta wani Fannin tana da gaskiya ta wani Fanni kuma bata dashi Saboda ai ba Laifinsa bane sai da yace su sanar da manya mganar in da cutarwa tace taji ta gani sai kuma Daga baya ta Bullo da wata mgana Ba domin ma Su din ba su cika yarda da Sihiri ba, da haka yasan zatace Duk da shima lamarin ya bashi mamaki ammh bai Taba Zargin wani ba ga Allah kadai ya Dogara shiyasa yake Neman waraka daga garesa..! ****** Amina batayi wani barcin kirki ba Saboda kuncin zuciya sannan ta dinga Tsorata acikin barcinta da Daddare barcinta sai ya zama sama sama ne tasan a gida bata iya barci sai acikin mutane ammh Tsoronta bakai na yanzu ba ko ya ta kwanta ta fara barci sai taji kamar ana Tabata sai ta Tashi a Firgice daganan sai kuka in tayi addu"a ne ta koma sai barcin nata yadan yi Tsayi. Yau da wuri tatashi ga rashin barci sannan tasa ka Komawa makaranta aranta yau din tayi wankanta sannan tayi sallar asuba Saboda zumudi Amina ko Karyawa bata tsaya tayi ba ta Saka Uniform dinta dake goge Daman Hamida tun agida ta goge mata ta fito da Jakar makarantar data Islamiya ta tura ta islamiyar da Hijabin cikin jakarta saboda chan zata zauna sai sun dawo daga islamiyar yammah Ta saka Safa da Takalminta ko Falo bata fita ba kuma bata ji motsin Sakina ba. Tun bakwai na Safe ta gama shiryawa tana zaman jiran su Hanne cikin kudin da Danmallam ya bata ta Dauki Dubu Daya yau zasu ci su sha ita dasu Hanne su Sa"adatu kuma Sai dai suga anayi yan bakinciki. Har takwas saura sai ta fara Tunanin ko dai sun tafi ne sun barta ayadda tayi Shirin zuwa makaranta yau sai ta kama gabanta don bazata fasa ba Kamar daga sama taji Hon din mota dayake motar tasu akwai kara bata gama Tantancewa ba taji Muryan Hanne na Kiranta tayi Zaraf ta Fito Daga Dakinta bayan ta kulle kofar Hanne na ganinta ta washe baki Tana Fadin"Amina Aminene ikon Allah..! Amina tayi Fari da ido kafin tace"Kwarai ba dai ta mutum ba sai ta Allah wlh..kainuwa Dashen Allah .! Hanne tayi Dariya kafin ta kalli jakar Amina Datake neman rinjayanta tace"Meye kika sako ajakar ko Abun Dadi ne na amare..? Tafada sanda suka fice Daga Falon Amina tace"Uban na Amaren ne..Hijabin islamiya ne da Jakata..! Hanne tace"Kin ga kuwa Sai da Hajiya tace na Tuna miki kada ki manta..! Amina tace"Ina zan manta..yarda na kosa na ganni a makaranta..! Hanne na Dariya yace"Yau watarana Amina na murna zata makaranta..! Amina ta murguda mata baki kafin tace"Yau Litini to munafuka..! Hanne na Dariya suka fita Daga gidan Dayake Idin bai shigo get ba Tunda suka fito yan motar suka sako ido suna bin Amina da kallo musamman Sa"adatu. Amina na shiga motar Idi kawai ta gaisar banda su Akilu da suka wani kame agaba Zubairu ne yace"Amina ba gaisuwa..? Wani kallon Tara saura kwata tayi mai kafin ta Dauke kanta Akilu yace"Kaima da wata mgana..So kake ta raina ka. Ta karo iskanci mana tana ganin ta matar ya Danmallam..! Tana jinsu ta musu banza kusa da Hamida ta zauna tana fadin"Baki ganni bane ko kimin oyoyo..! Hamida tace"Tunda kika shigo nake washe miki baki kikayi kamar baki ganni ba..! Ta Rumgume Hamida tana fadin"Sorry ban lura ba..Wata ke min kallon banza na maida mata.. Ta fada tana Hararan Sa"adatu Dake kallonta Daga sama har kasa Sabeeha kanwarta ce tace"Ya Amina daman gidan Anty Sakina kika dawo..? Amina tace"Eh Sabeeha baki sani ba..? Yarinya ta girgiza kai kafin tace"Shiyasa bana ganinki..! Sa"adatu ne ta Harari kanwarta Shiyasa tayi shuru Hanne kusa da Sa"adatu ta zauna Amina ta kalleta Cikin mamaki kafin tayi ma Hamida rada tana fadin"Hanne fa munafuka ce..Dubeta ita adole mai yar"uwa..! Hamidai dai Dariya tayi batace komai ba. Har suka isa makaranta Amina bata kara ma Hanne mgana ba da aka Sauke su ma ana Assamble ne Hanne na ma Amina mgana tayi kamar bata jita ba ta Nufi Zainab isa Dake Faman Daga mata Hannu Amina bakinta yaki Rufuwa ganinta a makaranta ashe ma karatun wani Lokaci zuwansa Rahma ne sai da aka kaita wannan kurkukun gidan nan ta san da haka. Ba dadewa aka gama Assamble din suka Tafi aji yan ajin su Amina sai mata ya jiki suke saboda Rashin Lafiya su Hanne suka ce tayi Saboda Hajiya ta gargade su kada su sake suce aure tayi har Sa"adatu sai da ta kira ta ja mata kunne. Gabadaya Amina sai taji ta kamar a aljannah ta saki jikinta sosai ana tashi Break taje ajinsu Hanne ta ta jasu Shagon makaranta ta siya musu banza ta siya musu wofi Hamida ke Fadin"Amina ina kika samu kudi haka.? Amina ta Kalleta tana shan Nutrimilk din data siya tace"Mijina..!. Tafada Cikin gatse Hamida da Hanne suka kalli juna kafin su Tsintsire Da Dariya Hanne tace"masu miji..To tunda ya bar mana kudi zamu ci mu sha ko Hamida..!? Suka tafa atare suna Dariya Amina tace"Kuma kika bama sa"adatu abuna Alah ya isa Hanne..! Hanne tace"kai wannan kiyayyar Dake Tsakaninki da Sa"adatu bansan irinta ba..! Amina ta wuce fuu tana fadin"Kika dai bata in na yafe Allah tsinan kin ji ma na fada miki..! Daga haka ta koma ajinsu ta siya ma zainab maltina ta bata,Daman sun fi Shakuwa tun Jss1 tana juran Jidalin Amina Sa"adatu na shigowa Amina sai da ta kalleta sannan ta ga Nutri dinta tana sha aranta tace bakinciki kan sai dai ya kasheki Amina kam tafi karfinki haka kurum ita Amina bata kaunar sa"adatu kuma hakan ya samo asali ne da yadda ta Tsani Anty Amarya. Sai biyu da rabi Idi yaje ya Dauko su suka koma gida mota na Tsayawa Amina ta Dira sai gida Hamida da Hanne suka bita da kallo Akilu ya rike baki yana fadin"Ya dammallam dai an Hadasa da kwaila..! Shi da zubairu sai Dariya suke yi. Amina da gudu ta shiga gida tana Kiran sunan mamanmu da Karfi da Jawaad taci karo ya fito daga Kitchen yana shan ruwa yana ganinta ya jefar da Kofin hannunsa ya Nufeta yana Fadin"Yaya Amina oyoyo.! Amina ta jefar da Jaka ta Cafeshi Taso ta Dagasa sama ne taji yafi karfinta ta Sauke shi tana fadin"Jawaad din yaya ya kara girma..! Cike da Tsantsan murnan yaga yar"uwansa yace"Ya Amina ina ta kuka da baki nan ina ta cema Aba ya kaini wajenki yace ba yanzu ba..! Sai Amina taji kwalla ta taso mata ta Kama Jawaad ta Rumgume cikin wani yanayi take fadin"Watarana zaka zo inda nike kaji jawaaad..! Kai ya gyada mata ita kuma tace"Daga yau kullum zaka dinga ganina kaji ko..? Baki ya washe yana fadin"Da gaske..? Jakarta ta Dauko ta Zage ta fito da sweets din data siyamai ta bashi ya amsa yana ta Tsalle tana Dago kanta suka Hada ido da mamanmu da tunda ta shigo da Kwakwazo ta jita tana kuryan Daki tana Faman Lissafim kudin da Aba ya bata yau da Safe na siyan Turaranta Datace mai ya kare ba gaddama ya tambayeta kudin tace mai 10k ya ciro ya bata,ita kam yanzu bata cikin wani bakinciki Burinta ya cika in ma bai cika ba kadan ya Rage mata. Alokacin da Amina ke mgana da Jawaad hararansu take yi tana Tsine musu acikin ranta in ma tana da wata Damuwa sune su Jaleela suna gidan auransu sai su Dade basu zo ba Jawaad ne da Jafar  wanda har yanzu Ta kasa shan gabansa ta Lura shima a Tsaye yake ammh zai yi Laushi Tunda Sa"idu yayi Laushi Amina Datake murnan ta Rabu da ita kuma sai gata Koda yake daman Ai Jiya ta shiga wajen Hajiya gyara kanta Tunda Hamida ta Dawo ta bata Labarin sha tara na arzikin da mallam da Hajiya suka Hadama Amina sai taji ta muzanta kafin Hajiya ta fara Dora zargin akanta yasa ta shiga tana mata kame kamen bata san da zuwansu Hamida ba shiyasa bata siya mata komai ba ammh Zata  siya mata su humra ta kai mata da kanta kudi ne bashi a Hannunta shiyasa. Hajiya babba bata kawo komai aranta ba sai ta nuna ma Mamanmu bakomai kada ta Damu Amina bata bukatar komai yanzu to anan nema Hajiyar ke fadamata Tsarin Amina zata koma makaranta sannan nan zata Dinga wuni sai yammah in sun Taso islamiya sai idi ya maidata gida. Amina na hada ido da Mamanmu tayi Falati da Jakarta ta Nufeta cikin murna tana fadin"Oyoyo mamammu..! Itama ganin haka sai ta saki Ranta Bakinta har kunne ta Rike Amina ta rumgumeta tana fadin"Oyoyo yata Amina..Nayi kewarki..! Amina tace"Nima haka mamanmu..kullum sai nayi kuka in na Tuna daku ina Aba..! Ta fada tana Sakin mamanmu Daidai Lokacin da Hamida ta shigo. Mamanmu tace"Aba dinku yana Lafiya Amina ya bakon waje..? Hamida ta fadamin irin Dibar albarkar da Shegiyar Sakinar nan tayi muku..Nidai ki Daina kulata kada ta nakasamin ke baki kaita karfi ba..! Amina tayi Dariya kafin tace"Haba mamanmu ita din banza..?Wlj ba cika baki ba ni Amina Aminene nafi karfinta wlh ta taba nin watarana Tagani..Sai ta raina kanta..! Mamanmu ta saki baki tana kallon Amina kawai gabanta na Faduwa ashe bakinta bai mutu ba jiya da Hamida ke fada mata ta sha mamaki ta Kira Anty Amarya sukayi mgana tace kokarinta Daya Umar yazo ya tafi da Sakina sai Amina taci iskancinta ita kadai Mamanmu tace tabbas..! Hamida ita ta Dauke ma Amina Jaka takai Dakinsu Mamanmu kuma ta shiga kitchen ta Debo mata abiinci da ruwa,Ta sakata gaba kamar ta bata a baki sai Dukan ruwan cikinta take yi ko zata ji wani abu Hamida Dakin su ta shige Tayi sallah ta Debo abinci dama ta shigo Dakin da suke korarta Mamanmu tayi saboda tana so sai taji yanayin zaman Amina da Danmallam kafin ya koma Madina. Shiyasa Amina na cin abincinta Mamanmu ta gyara zama tana Fadin"Ni ko Amina Allah yasa Danmallam dai kafin ya koma bai miki komai ba ko..? Gaban Amina ya fadi ta Dakata da cin abinci ta Dago tana kallon mamanmu Cikin mamaki ita tunaninta ko ta Fahimci abunda ya shiga Tsakaninsu ne yasa cikin sauri tace"Name ne mamammu..? Ni babu abunda yayi min..! Mamanmu ta sauke Numfashi kafin tace"Yauwa Allah yasa ma baya shiga Harkanki..! Amina tace"To ina ruwana dasu..! Ni har ya tafi ma ban gansa ba..! Ya cika fada haka yayi tamin masifa ranar da muka tafi Daganan..! Mamanmu taji Dadin haka yasa tace"To ai kin gani irin wannan abun na Gudar miki yasa naso araba wannan auran kika ki bani Dama..! Amina tace"Bakomai Mamanmu hajiya da Mallam sun wuce komai a wajenmu..Sannan ni nayi alkwarin Aba bazai kara bacin rai saboda ni ba..! Mamanmu tayi shuru tana kallon Amina kafin tace"Hakane kuma ammh ki Daina tankama Sakina Da shi din ne dai da nace ki yi tamai Fitsara har ya gaji ya sako min ke na aura miki mai sonki Aminullah..! Amina tayi Tsai tana kallonta sai taji bata ji Dadi ba datace a asakota Saki fa ba Kyau ance sai al'arshin Allah ya girgiza sannan ita karan Hauka ya Cijeta  da zata ma ya Danmallam rashin kunya sai dai Sakinar itace Daidai da ita. Daganan bata kara mgana ba Mamanmu kuma sai janta take da Labari Amina ba domin Rokon Umar ta Boyema mamammu komai ba,,sai saboda Tana jin kunyarta da Tunanin in taji abunda ya faru zata yi mata Fada kila ma ranta ya baci shiyasa bata gayamata ba.. Ita kuma mamanmu adole Allah zatayi ma wayau batasan bakin Alkalami ya riga ya bushe ba,Haduwar jini ta Haifar da gudan jinin da zai yi Sanadiyar Fallasan duka sirrukansu. Amina sai da taci ta koshi tayi sallah kan gadonta ta fada tana Fadin"Nayi kewarka gado na..! Take fada tana Shafa gadon Hamida na kallonta kafin tace"Sai a Daukesa akai miki chan..! Amina tace"Da naji dadi kuwa..! Hamida ce tace"Hajiya sai da tambayeki fa Amina..! Amina ta mike Tana fadin"Bari na shiga..! Uniform dinta ta cire ta sauya dana gida akwai wasu cikin kwabarta na gida hamida ta rakata gidansu Hanne. A bakin shashen Hajiya suka ga Haj.Uwa tunda taji zuwan Amina ta kasa zama tana ganinsu ta washe baki Tana fadin"Ga Amina Amarya..! Sai kunya ya kama Amina ta Dukar dakai tana gaisheta Hannu taja tana Fadin"Au bazaki shiga Shashena mu gaisa ba..? Yar"uwarki ma Umaima bata da lafiya jiya ko barci bamu yi ba..! Amina tace"Allah sarki bansani ba..! Hamida tace"Mun manta ne bamu Fada miki ba..Jiya kwana tayi ihu mallam da su ya Akilu suka kwana suna mata karatu..! Amina taji Tsausayi ya kamata sosai Ta kalli Hamida tana fadin"muje na Dubata Hamida..! Da Sauri Hajiya Uwa tace"ai ita sun shigo sun dubata da Safe..Ke dai muje Diyata Amaryan Umaru Faruqu..! Tafada tana jan Amina Hamida sai bata bisu ba tunda taga kamar Haj.uwa ta fi son Amina ita kadai. Sai ta juya ita ta shige Shashen Hajiya babba. Kafa kafa Haj uwani ta dinga yi da Amina har shashenta kai tsaye kuma har Dakin da Umaima ke kwance tana barcin Wahala duk ta kara ramewa sai Dogon wuya Amina ta kalleta Cikin Tsausayinta tace"Allah ya bata lafiya..! Haj Uwani ta kalli Umaima sai ta fara Sharan kwallah kafin tace"Wlh ciwon nan na Umai ya fara damuna Sa"o'inta duk suna Dakunansu har da ku ma kannen bayanta ita ko kalli Halin Datake ciki..! Amina tace"sai hakuri Allah ya bata lafiya..bari na tafi..! Haj Uwa tace"Bazaki tafi ba sai kin sha wani abu muje..! Ta kaita har falo ta zaunar da ita kan kujera tana fadin"Umaru dai ana Madina ko..? Amina tace"Uhm..! Daganan bata kara mgana ba mamaki abun ke bata Duk da Tasan Hajiya uwa bata da matsala ammh bata janta ajiki kamar na yau sai kawai taji bata yarda da ita ba. Tana nan zaune sai gata ta fito da Jug da kofi ta kawo gaban Amina ta ja Center table ta dora lokaci Daya tana Fadin"Lemon kankana nayi tun Safe kinganshi nan yayi sanyi zaki ji Dadinsa Amina..! Amina ta yi kasake tana kallonta ganin haka yasa ta Zauna gefenta tana Fadin"Kada ki damu nan Umaru ke karyawa indai yana gari dagashi har matansa abinci shashena basu da Shamaki dashi..! Amina dai batace komwi ba ta Dauka ta Tsiyaya kadan Ta Daga kofin takai Bakinta Hj.uwa na kallonta zuciyarta Cike da Farinciki zata aiwatar da Tsarinta Cikin Sauki kamar yadda ta Saba.! Amina acikin ranta taji bazata sha wannan abun ba,ba domin tana Zarginta ba sai domin cikinta ya cika sannan in ta fada mata bazata yarda ba Sai dai kamar an kwato bakinta Ta Furta. Bismilallahi..! Sannan ta Kurba kadan Haj.Uwa taji kamar an sakata acikin Aljannah Ta Bude zatayi mgana kenan Kukan Umaima ya katseta tatashi da gudu tatafi Dakin tana cema Amina tana zuwa..! Tana shigewa Amina ta Dawo da na bakinta wanda bata gama Hadiye ba jin wani makaki a makogwaronta waige waige ta farayi ganin Haj.Uwa bata fito ba yasa tatashi Sadaf Sadaf ta shiga Kitchen dinta ta Juyesa a wajen wanke wanke taga yana wani yauki mamaki ya kamata da sauri ta Bisa da Ruwa ya wuce sannan ta samu ruwa ta Kuskure bakinta ta koma Falo da Sauri ta ijiye kofin ta zauna kenan sai gata fito Idonta kan kofin tana ganinsa ba komai ta wani Saki ajiyar rai kafin ma ta zauna Amina ta mike tana cemata zata tafi Cikin Murna da Cikar Burinta tace"To shikenan Aminatu Sai na shigo shashen Hajiyar..! Harda Dari biyar ta bama Amina tace bazata karba ba ta matsa mata ta karba Amina ta fice cikin mamaki sannan uwa uba kuma Makogwaronta bai yi mata Dadi ba Tunda tasha wannan lemon Tana Fita Haj.Uwa ta Daga Kofin kafin ta Sheke da wata Dariya a Fili ta Furta"Kema kin Hau keken beran kamar yadda na Dora na bayanki..! Sai ta wani Saki shewa Duniya Sabuwa..burinta ya kusa cika Nazeem Sauransa wattani kadan ya gama makaranta Uzairu kuma ya gama Degree dinsa na farko Services ma yake shirin tafiya ta fara Hango kanta a matakin datake Wahala Shekaru masu yawa. Abunda bata sani ba Kafin nata Tsarin Ta manta Allah ma da nashi..? To nashi ya riga nata sannan abunda Allah ya rubuta shi zai faru wannan gudan jinin sai ya fito Duniya wannan Cewarsa ne..! Amina haka taje Shashen Hajiya ba cikin natsuwarta ba cikinta nata Juya mata sai dai bata cema kowa komai ba suka gaisa da Hajiya tana ta Tambayanta ko ba matsala tace mata eh Dakin su hanne suka shige suna Hira Amina ta kasa natsuwa sai da ta shiga Tiolet ta dinga Tura Hannunta Cikin baki sai da ta samu Wannan dan Lemon daya shiga Cikinta ya fito harda Abincin data ci sai da ta Amayar dashi tayi sauri ta wanke wajen ta fito su hanne suna chan suna Hira basu ji karan Kakwazon aman nata ba. Sai alokacin ta samu salama. Allah yayi ikon sa Ko tasha wannan nganin bazai zauna acikinta ba sai ya fita saboda ba koda yaushe kake aikata abu kaci nasara ba daga Lokacin daka fara Hango nasara Daga lokacin kila Lokacin bayyanan wasu abubuwan ne. La"asar nayi suka shirya suka tafi islamiya irin su mariya sai kallon Amina  suke domin Sa"adatu ta Fesa musu Amina ta auri yayansu mijin Anty Sakina to sanin Halin Amina Shiyaasa ba wanda ya Tareta da mganar har aka tashi. Suna Dawowa gida Amina taso ta Tsaya wai taga Aba da Mallam Hajiya tace maza ta wuce idi ya maidata gida Mallam yana Hadeja sun je bude wani masallaci ba yanzu zai dawo ba shi da Aba Dole Amina taje tayima mamanmu sallama ko mangariba agidan ta tayi ta sai kunci take yi. Aranar dai bata Hadu da Sakina ba sai Washegari da Idi ya maidota da yammah ta ganta afilo suka kalli juna kasa kasa kowacce ta kauda kanta bata Damu da abinci ba, tana ciko Cikinta Kafin ta Dawo da Safe kuma Tea kadai tashe sha watarana ma haka take Tafiya. Asatin nan kaf haka Rayuwar Amina ta cigaba da gudana kudin hannunta sai da ta gama kashe ma su hanne gbadaya sannan Hankalinta ya kwanta Ranar jumma'a daga makaranta bata koma gida ba Ta jira sai da Mallam da Aba suka Dawo ta gaisheshesu Aba sai mamakin Amina yake a idonsa yaga kamar ta kara mishi girma sannan tayi hankali Kadan Mallam kuma kamar ya maidata Ciki saboda so Shiyasa bata koma gida ba sai Ranar Lahadi da yammah Mallam yace tayi kwana Biyu saboda Har da Hajiya bata so ba Ammh Tunda mallam ya saka baki shikenan. Jafar kuwa sam ya manta da Kudin wayar da Danmallam ya barmasa ya siya ma Amina sai da Umar din yaji Shuru ya kirasa sannan ya Tuna Hakuri ya basa aranar bayan ya Dawo Daga wajen aiki ya biya ya siyama Amina waya karama Nokia sai washegari ya siya mata layi yayi mata Rigister sannan yazo ya kawoma Hajiya wayar Tunda Aminar na makaranta Hajiya ita har ta ma manta da Batun wayar sanda ya kawo mata Cikin wardrope dinta ta saka wayar sai kuma Allah ya mantar da ita har Amina ta dawo ba ta bata ba. Wajen kwana Hudu da Jafar ya sanar ma da Danmallam ya siya waya ya kaima Hajiya ta bama Amina sannan ya Turama sa Layin Aminar sai dai tun Washegarin ranar yake ta faman kiran wayar a kashe sai ya fara Tunanin kodai Hajiya bata bama Amina wayar bane.? Shi kuma ya kasa Hakuri ya rasa meke Damunsa Daidai da rana Daya Tunda ya Dawo madina Zuciyarsa bata manta Amina ba. Wannan yarinyar daya ke kira kazama Kwaila itace ya kasa mantawa da ita ko Sakina da suka Dade tare baya jin nauyi da wani Damuwa da ita akan yadda yake ji kan Amina wani al"amari ne da Ubangiji ya barma kansa sani abu Daya ya sani yana matukar son yaji muryanta sannan yaji lafiyanta baya fatan ace yau yabar baya da kura. Sannnan yarinyar itace ya Hada Abu mai muhimmanci da ita abunda bai Taba Hasaahen zai iya Faruwa Tsakaninsa da ita ba.. Abunda bai sani ba Addu"an Hajiya da Mallam ne Allah ya amsa sannan Addu"ar yaya ce Allah ya amsa ya Amintar da Ruhin Amina da Umaru waje Daya..Aminci na har Abada..! *Janafty* *TFZB2010* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* *Bayan kwana biyu..!* _Area:Prince Naif ibn Abdulaziz Road,Aljami"a P.O Box 170,Madina Saudi Arabia_ Shigowarsa kenan Cikin kayataccen Office dinsa mai girma da Fadi yana Hawa na Hudu ne a bangaran ofishin Malaman makaranta ta Madina bangaran Shashin Qur'an and islamic Studies babban Shashi ne mai Dimbin Tarihi a cikin babbar Jami"ar ta Musulunci Dake madina. Littafan hannunsa ya zube bisa Babban Tuburin dake cikin Ofishin kafin ya samu waje ya zauna Hular kansa ya cire Lokaci daya yana shafa Sumar kansa data fara Tohowa.! Gajiya ce ajikinsa domin yau tun Safe ya bar gida yana da ajin karfe takwas na Safe zuwa goma sannan bayanan ya shiga na goma zuwa sha biyu daganan kuma suna da meeting da zasu yi na malaman shashin Dayake koyarwa gabadaya Sakamakon yau Alhamis ya tashi da azumin Lada kamar yadda ya saba so yake ya tashi ya isa babban masallacin Cikin makaranta yayi karatun Qur"ani kafin lokacin Sallah yayi ammh ya kasa tashi kasala Tare da Gajiya sun Taru sun lullubesa. Kansa ya kwantar kan kujeran Dayake zaune idanuwansa suna lumshe kamar mai jin barci nan kuwa ba barci yake ji ba Tsabar Tunanin abunda ya faru tsakaninsa da Sarood jiya da Daddare ne ya Addabesa Shi bai taba Daukan matsalan sa da Sarood mai girma ba sai jiya daya kara jaraba Kusanta ta abu yaci tura kamar dai baya da ya riketa ajikinsa tafiya ta fara tafiya sai yaji komai ya koma ya kwanta a duba da abunda ya faru tsakaninsa da  Amina ya Dauka Komai zai yi daidai tsakaninsa da Sarood sai kuma yaga akasin haka,Bai taba Daukan abun da Serious ba sai jiya Saboda abun kamar zai yuyu sai kuma abu yaki yuyu shiyasa wani Lokacin baya son rabarta kar yajamata matsala tunda ita macece Tana da Rauni Fiye dashi sannan shi yana da wata matar ita fa..? Shi ne kadai mijinta kuma Wanda zai Biya mata Bukararta in ta taso. Ajiyan ya dauka komai yazo karshe Ganin yadda abun nasu ya fara kamar gaske sai dai ina Yana zuwa gabar sai komai ya kwanta yaji bai iya Tabuka komai abaya ya Dauka Sha"awan ce ke Daukewa shiyasa girman nasa bata Mikewa alokacin ammh Daga Jiya ya fara Zargin da wani abu Saboda shi kanshi yayi mamakin yanayin da ya shiga jiya da Taimakon addu"a ne kawai ya iya Sarrafa kansa. Sarood kuma kwana kuka tayi bai ga Laifinta ba tayi hakuri wajen wata bakwai ba wani labari Tabbas akwai Cutarwa acikin zamansa da ita Dakyar ya samu ya lallasheta bayan ya mata alkawarin zai Binciki kansa Domin ya sama musu mafita da wannan Tunanin ya barta agida ya fito zuwa makaranta ya kasa samun Mafita,ya rasa da wa zai Tattauna wannan matsalan da Farko kamar ya Kira Mallam kunya da nauyi bazai barsa ba yayi Tunanin Baba Sa"idu kuma sai ya fasa Tuna yanzu ba Da bane..In abaya yana yayansa ne yanzu har da karin Surukanta Tunda ya aura masa yarsa ta Cikinsa da Kunya ya Kirasa yana Fadamai bai iya kwanciya da wata mace Abokiyar zaman yarsa duk da yasan Waye Baba Sa"idu auran Amina bazai taba Chanza Tsakaninsu ba Sai dai shi din ne Bazai iya ba yana jin nauyi,Hajiya kuma ba wannan Sakewar Tsakaninsu,koda ma akwai ita uwa ce bazai taba iya fadamata wannan mganar ba Aliyu ne ya fadomai arai aboki kuma Amini garesa da shi kadai ne ya kamata ya Tattauna wannan matsalan dashi. Shawaran kiran Aliyu ya Zauna aransa bai Tsaya ba ya tashi Zaune Dakyau ya Fiddo wayarsa cikin Aljihun Wandon Pakistan din Dake jikinsa kafin ya kira lambar Aliyu layin Amina ya kara kira wanda Jafar ya Turo masa ammh kamar kullum ana Kara fadamai wayar tana kashe ne. damuwarsa ba Daya bace har da Damuwar rashin jin Aminaa har Jafar ya sake kira a jiyan yana kara tambayansa ko ya kaima Hajiya wayar..? Jafar ya kara Tabbatar mai da wlh ya kaima Hajiya wayar ta kuma Ta tabbatar mai  zata bama Amina wayar sai dai baisan meyasa har yanzu bata bata ba ammh zai je ya mata mgana sai Danmallam din ya hanasa yace zai kirata da kansa shi kanshi Jafar yayi mamakin yadda Danmallan din ya Damu da sai an bama Amina waya wannan yarinyar da baisan yaushe zatayi Hankali ba ko Shekaranjiya ya ganta sun dawo islamiya suna tafe ita su Hamida sai Mgana take cikin ihu Suna bakin masallaci kofar gidan Baba mallam har sai da Nasir ya kada baki yace Amina in aure bai gyara ba to bazata taba yin hankali ba shima ya yarda da mganarsa..! Bai kira Aliyu ba kamar yadda ya kudira daga farko sai ya maida akalan kiran nasa ga Hajiya, mallam sun yi mgana dashi da Safe agogon Dake kafe a afishin nashi yabi da kallo yaga karfe 12 da wani abu na rana yana Tunanin achan Nageria yanzu Tara ne da wani abu na Safe. Wayar Hajiya ta shiga gabda zata katse ta Daga kiran cikin Sallamarta ya amsa mata Cikin Ladabinsa kafin ya Fara gaisheta ta amsa tana Fadin"Lafiya lau Danmallan ya madinar da wajen aikin ka..? Ina Saratu ina Fatan tana lafiya..? Kansa na kasa kamar yana gabanta yace"Duk muna Lafiya Hajiya..aiki kuma alhamudulillah cikin Nasara da addu"arku..! Hajiya tace"Masha Allah Allah ya taimaka..Allah ya kare ka Dammallam ya baka Zuru"a Dayyaba..yadda kake mana Biyayyah Allah ya jikan ka ya baka mai jin kanka kaima..! Addu"a hajiya yasa yaji kamar yayi kwallah kaunar Mahaifiyar tasa na kara shiga ransa. Cikin muryan sa mai cike da Zati da Haiba yake amsa mata da Ameem Ameen. Mallam da mutanen gidan ya tambaya tace duk suna Lafiya kafin yace"Hajiya yau she ne tafiyarki maiduguri.? Hajiya tace"Satin na sama ne zan tafi inaga Ranar Laraba..! Kai ya jinjina kafin yace"Allah ya kaimu zan turo ma Jafar sako..Ki kaima Goggo ta kara Allah ya bada zaman lafiya..! Hajiya cikin Farinciki tace"Angode Allah ya kara Wadata Allah ya Dafa maka..! Ya amsa mata da Ameen kafin su yi shuru na wani Lokaci jin shurunsa yasa sai ta Fahimci yana so yayi mgana ne. Cikin Dattakonta tace"Danmallam me kake so kace ne..? Ya sosa kansa kamar tana gabansa kafin yace"Hajiya jafar yace ya kawo miki waya ko..? Hajiya tayi yar Dariya kafin tace"Eh wlh ya kawomin tun kwanaki na Shafa"a ne ban bama Aminar ba..Dayake bata zama Da sun Dawo makaranta abinci kadai suke ciki sai su tafi islamiya da sun dawo kuma nake sawa akaita gida ni kuma Shaf na manta..Ammh bari in ta Dawo yau zan bata insha Allahu..! Kansa na kasa kamar yana gabanta yace"To nagode Hajiya Allah ya kara girma..! Ta amsa da Ameen Daga haka sukayi sallama Hajiya ta zauna gefen gadonta Tana kara nazarin meyasa Danmallam ya Damu da Amina ta rike waya Daga baya alhalin ita ta kawo Shawaran siyan waya Daga baya da suka Tattauna da mallam sai ya nuna mata illar hakan saboda Har yanzu Amina yarinya ce sannan Karatu ne agabanta,in ta rike waya yanzu zai Shagaltar da ita daga karatunta in Saboda su rika mgana da Mijinta ne ga wayarsa ko ta Hajiya duk wacce shi Umarun ya kira zai yi mgana da Amina shiyasa bata maida kanta kan bama Amina wayar ba ko ayanzu ma Datace mai zata bata tadai cemai ne kawai ba domin zata Tsallake Shawarar da mallam ya bada ba.! Danmallam kuwa suna gama waya da Hajiya sai ga kiran Sakina ya shigo Yana ma kokarin kiran Aliyu ne kamar bazai Dauka ba sai kuma ya Kashe ya Kirata Tuna yau kwana Biyu basu yi mgana ba Shifa har yau Haushinta yake ji kan abunda tayi mai In ya tuna yadda ta kulle ko"ina ta tayi tafiyarta shi abu daya ya Damesa yadda ta tafi ta bar yar Mutane acikin gida in da yunwa ya kamata ko kuma wani abu ya Sameta ai da ya shiga uku wajen Hajiya da mallam kila sai sun kusa mai baki. Sama sama daman yake da ita in ya kirata shima saboda sauke Hakki da Nauyin Dake kansa ne ba da domin haka ba sai ta kara Raina kanta. Tana Dauka ko Sallama batayi ba ta Fara fadin"Habibi..! Rai ya bata kafin yace"Bana fada miki..Ki daina daukan wayata baki min Sallama ba..? Tuna haka yasa tayi Saurin mai Sallama ya amsa mata yana tambayanta lafiyanta tace"Lafiya lau Habibi ya aiki..? Yace"Alhamdulillah ya naji kamar kina kwance ne..? Gyara kwanciya tayi kafin tace"Wlh kuwa ban tashi ba..Tunda nayi sallar asuba na koma barci..! Cikin mamaki yace"To Haka Aminar ke tafiya makaranta bata yi kari ba kenan..? Sakina ta bata rai kafin ta tabe baki Tace"Wacece haka..? Yana jinta sai bai tanka ba Sanin Halinsa yasa tace"Kace min wannan kazamar matarka taka..Ohon mata Daman na Fada maka bazan dinga mata Bauta ba, ba zamanta nake yi ba..! Sai kuma yaji bai ji Dadin sunan Data kira Amina ba Duk da shine silar saka mata sunan sai yaji bai Dace ba Domin karshen kazanta kenan ya Ratsa Amina ahakanta,aiko kazanta ya kare. Tattare naman goshinsa yayi bai yi mgana ba yana kokarin Daidaita yanayinsa Sakina ta cigaba da Fadin"Da Safe ake zuwa Daukanta makaranta ni bana ma sanin Tafiyarta..Sannan bata Dawowa sai yammah ranar jumma kuwa in tatafi makaranta da saafe sai Lahadi da yammah take dawowa sai mu yi kwanaki bamu hadu ba in ma mun Hadu bata min mgana sai kallon banza Habibi yarinyar nan ta gama Rainani bata da kunya Ranar fa Har Zagin Ubana tayi bayan tafiyarka ba Dadewa..! Yana jinta bai ce komai ba aransa yasan Amina zata aikata A dan Sanin da yayi mata da labarinta dayaji Sama sama Zata aikata sai dai bai yarda ba Sakinar ce ta fara Zaginta ba yasan ta Sarai Itama Sakinar bata da Hakuri. Yana jinta tana cigaba da Fadamai Rashin mutumcin Amina shidai bai ce komai ba illah"Kiyi hakuri zan kirata zan mata fada..! Sakina tace"To tana da waya ne..? Kai Tsaye yace mata"A"a chan gida zan kira abata na mata fada..! Sakina taji Dadi yasa ta gyara kwanciya tana kara shigewa Cikin blamket tace"Habibi yaushe zaka zo ka Daukeni..? Ni in bazaka zo ba sai Su Jafar su Nemin Visa na taho..! Yana jin mganarta yamata shuru Sai da ta fara magiya tana Fadin"Don Allah Habibi kayi Hakuri na tuba nabi Allah na bika..Wlh Daga yau bazan kara saba Umarninka ba..! Ta karishe Fada Cikin kukan Shagwaba Saboda ko jiya sun yi mgana da Anty ta tabbatar mata da cewa mallam ya sanar da ita Umar zai zo ya Dauketa Dolensa..! Shiyasa ta tadamai da mganar ita a Tunaninta komai ya zama yadda suke Fata abunda basu sani ba ba kowani Lokaci Allah ke basu nasara ba akwai lokacin da aikin da suke da yakini a kansa zai basu mamaki..! Sai da ya gama jinta sannan yayi gyaran Murya yana fadin"Sakina na Fada miki abaya zan kuma kara Fadamiki a yanzu..in har ni mijinki ne mai baki Umarni ki bi to bazaki Dawo madina yanzu ba..Sai nan gaba in kin gaji da zaman gumel din..! Sakina jikinta ya fara rawa  gabanta na Fadi ta ce"Habi..! Bata karisa ba ya katseta da Fadin"A wanchan Lokacin sai da nace kada ki zo..Kika jin mganata kikace sai kin zo..Biki nawa ake yi baki san zaki je ba Zan ce miki ki shirya mu taho..? Abaya bake kika bani Shawaran Dauko ki na kawo ki garin nan ba Ni nayi Ra"ayin haka,kamar ni nace ki Hakura da zuwa Bikin su Abida Tunda ba an gama sha"anin bane akwai wasu masu zuwa kika jin mganata kika kuma Zuga Sarood itama ta Tada min rigima Duk Saboda nace ki Zauna bani da kudi sosai sai wani lokacin..! Sakina ta kwaso Rantsuwa bai bata Dama ba ya cigaba da Fadin"Ita mahaifinta ya Dakatar da ita bata Biyoni ba..Ke kuma kika Biyo ni kikazo to kuma Miye na jin Zafi Domin nace sai nan da wani Lokaci zaki koma..? Ai kina son zaman nan din ne shiyasa nayi miki abunda kike so..Wlh itama Data sake ta Biyoni Dukkan nan zan barku nayi Tahowata lokacin da na Sanu Dama da Hali sai nazo na Taho Daku a kallah dai nayi muku abunda kuke so kada kuce nayi miki rashin Daidai.. Kinsan Wlh rantsuwa ce ko..? Sakina sai in na Samu Lokacin nazo sai mu koma Tare in kuma kika ce zaki Biyoni bansani ba to ba da Izinina ba..! Daga haka ko cewarta bai jira ba ya Katse kiran yana Faman kokuwa da Bacin ransa Sakina kuwa kamar tayi Hauka haka ta mike tana Laluban wayar Anty sai dai bata Sameta ba Kasa Zama tayi ta mike tana Safa da marwa acikin Dakin tasan Waye Umar kaifi Daya ne in yayi mgana baya Sauyata ammh sai da ts saki jiki da Anty da ta tabbatar mata da cewa zai zo su koma Tare,sai dai wannan Jadadda mganar tasa yasa ta kara Sarewa a baya ma acikin ranta har ta Tsara in bai zo ba zata yi Visa da kudinta ta bisa sai dai ya ganta ai tasan Hanya ba inda bazata kai kanta ba A madina ba.! Sai gashi furucinsa ya sa wannan Tunanin ya bace mata tasan kuma tunda yace bada yawunsa ba in ta Sake ta taka wani abun ne kuma zai Faru na Dabam wanda bata Fata wayar Anty Amarya tayi ta Kira kamar zatayi hauka bata Sameta ba Shi kuwa yana katse kiranta ya Kira Aliyu saboda yanayin Yan"uwansa duk suna Nageria ne yasa yake saka Kudi mai yawa saboda yafi Sauki shi ya Kirasu da su Dagachan su kirasa. Kiran farko Aliyu Dake wajen aiki shima acikin Office dinsa ya Daga kiran yana Fadin"Ango..Kaga angon Amina Larabawan Madinatul munawwara..! Umar yayi Dariya kafin yace"Taka Sallamar kuma kenan..? To Allah ya shirya Sallamu Alaikum..! Aliyu na Dariya yace"Wa"alaikas salam Shehi mun tashi lafiya..? Daganan suka gaisa kamar yadda suka saba kafin Umar yace"naji hayaniya kana wajen aiki ne hala..? Aliyu yace"Eh wlh tun Safe ma.! Umar yace"Daman mgana nake so mu yi..! Tana da muhimmanci sosai..! Aliyu yace"To ina jinka ai ina Office dina ne.! Umar ya gyara zama kafin yace"Matsalace dani na rasa wa zan Tunkara shiyasa na zabi na Fadamaka..! Nan ya fadamai Halin da suke ciki shi da Sarood. Aliyu ya Saki baki ya Rufe sau ba Adadi bai sani ba kafin yace"Bangane ba ita Sakinar kuma Lafiya kalau kake in ka Rabeta..? Umar yace mai eh Aliyu yace"To Amina fa ka jarabata ka gani..? Sai ya kasa mai mgana sai da yaji Shuru sannan Aliyu yace"Common Mutumina Saboda mu gano matsalan ne yasa kaji ina Tambayanka..! Sai da ya Runtse kafin yace"Itama Lafiya kalau..! Aliyu yayi ajiyar rai kafin yace"Umar kune malamai ya"yan malamai adan Sanina da ilimina na hasaso wani abu..! Umar yace"Me ka Hasaso..? Aliyu yace"Al"amarin ka kamar Sihiri kamar kuma shafan Aljanun mutanen Boye..! Umar yayi shuru yana wani Tunani kafin yace"Sihiri kuma..? A"a sai dai in Shafar aljanun in na rabeni bazan musa ba..ammh ni kam wazaimin Sihiri ni bani da abokin Fada kai Sheda ne Aliyu..! Aliyu yace"Hakane sai dai shi Rayuwa bata ga haka..Kana zaman zamanka baka Damu da kowa ba wani na chan yana Bakinciki da duk wani Cigabanka..! Umar yayi ajiyar rai kafin yace"Sai dai shafar Aljanun Aliyu..Bazan musa ba Ammh ina Tunanin ko ta bangaran Sarood ne..? Ina da yakinin yadda na tsare kaina da addu"a azakar Safe da Rana da Karatun Qur"ani da Ibada aljanu bazasu Shafeni ba insha Allahu..! Aliyu yace"Duk zai iya yuyuwa hakan din ma.! Danmallam ya Dafe kansa kafin yace"to menene mafita.? Aliyu yace"Ni dai a  a shawarata ka Shawarci mallam na Tabbata shi zai san wani abun da bamu hango ba..! Umar yace"Ina jin kunya fa..! Aliyu yace"Lalura ce Shehi..Sannan Maallam ba kunya Tsakaninku..! Umar ya jinjina kai kafin yace"Hakane Shikenan zan yi Tunanin hakan nagani in munyi mgana zan kiraka kaji yadda mukayi Dashi..! Daganan sukayi sallama bayan Aliyu yace yana jiransa. Duk yadda Danmallan yaso ya Kira mallam sai yaji ya kasa yafi dai yadda da mganar Aliyu na shafar Aljanun yafi kuma yarda data bangaran Sarood ne ya yanke shawaran in ya koma gida zasu yi magana yasan wasu mganguna anan madina na irin haka da kuma addu"o"in Tsarin Shafar mutanen Boye zai saka ta Jaraba ta gani in abun bai yi ba bai da wata Mafita sai na kiran mallam din. Aliyu kuma mamaki ya cika sa na wannan lamarin ya fi karkata ga Sihiri ne saboda wani abokin aikinsa da suke Tare anan hakan kusan ya Faru dashi da ya kara aure shi ma Ba wani motsi  tun yana shuru har mgana ta kaima Manya Mahaifiyarsa ce yar gidan malamai nan aka gano Shihiri ne sannan kuma ana Zargin Uwargidansa tayi mishi da aka Mike Tsaye da addu"a da mgungunar karya Sihiri Tuni aka wuce wajen shima yaso Shehi ya yarda da mganar sa ammh sai yaga bai amince ba sai ya bar sa a Inda Tunaninsa ya karkata sai dai yana Fatan In ya kira Mallam din adace.! ******** Bayan sati Daya..! hajiya bata samu Tafiya Biki ba sai Ranar alhamis idi ya kai su ita da Hajiya uwa datace zata rakata ba wanda yayi mamakin hakan daman in dai sha'ani na Hajiya ne Hj.uwa tana gaba gaba sanin tasu tafi zuwa Daya da Hajiya babba ba kamar su Nasara da Anty Amarya ba kafin su tafin Jafar ya kawo mata 30k in ji Danmallam ta kar ba tana ta godiya ta nuna ma mallam ya saka albarka shima ya bada kudi da kayan abinci suka tafi dashi Kwana Daya idi yayi ya juyo sai sun gama Biki zai Dawo ya Daukesu Su Amina sun so Hajiya tatafi dasu tace su yi Hakuri su zauna Saboda makaranta sannan kwana Daya Tsakani Ranar jumma"a Mamanmu ta tafi Gusai Biki Amina da Hamida da Hanne sun so su bita Tunda Hajiya bata tafi dasu ba ammh itama tace su Zauna Saboda makaranta Daman Amina ta ma mallamm gana ya basu Hakuri yace su bari wani Lokacin saboda karatunsu,Dole suka Hakura ammh Tundaga Ranar ganin Hajiya bata nan Amina ta share Kafa Tayi zamanta Daganan suke zuwa makaranta da Aba yayi mgana Mallam yace ya kyaleta watarana ba sai an mata mgana ba zata san muhimmancin gidan auranta har yanzu Amina yarinya ce. Amina kuma Harkan gabanta take yi kamar ba matar aure ba in ba gidan ta koma ba mantawa take yi da wani aure ballatana Danmallan ko Sakina Abu Dayane bata manta dashi ba Har yau shine Abunda ya Faru Tsakaninsu Ko barci ta kwanta sai ta Tuna abun kunya take ji da nauyi in ta Tuna abunda ya Faru Ranar yau itace kan gado ita da Danmallam har wani babban lamari ya faru Tsakaninsu sannan bazata manta da yadda yagama gane mata jiki bakincikinta Daya yan nonuwamta Daya gama gani Tasan ya gama rainata Haushi take ji nata sunki girma ga Hamida Da Hanne har Hajiya ta siya musu Braziya ita kuma sai vest saboda ba su da wani girma sosai in ta tuna Haka sai ta Tura baki tana kunkuni kamar yana jinta ko yana ganinta. Yanzu Ta rage tsoro tunda Tare da su Hamida take kwana sannan koda aka shiga Damina ko ana ruwa Tsakar Dare ba ruwanta tana makale bayan Hanne ko Hamida hankalinta kwance. A jidalinta kam babu abunda ta Rage sai Dambe ne kadai ta Daina ammh Fada a makaranta da siyan fada ko bada ita akeyi ba sai abunda yayi gaba Ballatana gata ga Hamida ga Hanne bata da wani Danuwa ranar ma A Hadda suka yi fada da Samira ta kan kujeran zama Amina ta mike ta Chakume Wuyan Hijabin Samira zata Jata da Dambe Mariya ta kada baki Tace Amina yanzu fa kin girma tunda ke matar aure ce wannan abun da kike yi bai kamata ba..Ku su hanne ku Fadamata gaskiya in zataji to..! Amina sai taji ta Muzanta Ido ya Dawo kanta sai taji kamar ta Shake mariya ta kalleta ta murguda mata baki kafin tace"Ubanki na aura ammh ko..? Wannan mganar yasa mariya ta kai kara wajen Mallam Datti akan Amina ta Zagi babanta Case din da sai da ya Jafar yazo makarantar mallam ya aikosa ya kashe mganar Tunda Mallam Dattin ya kira mallam awaya ya Fadamai. Ranar ya Jafar yaso ya Daki Amina sai Mallam ya hana ya kuma yi musu gargadin  har Abada Amina ta wuce Duka awajensu..ko ba domin darajan auran Dake kanta ba Domin Darajan Danmallam Dake mijinta bazai ji Dadin su daketa ba in yaji Labari. Ya kuma fada musu suma Amina Uzuri Amina har yanzu yarinya ce dole ya kyaleta ita kuma sai ya Bita da Nasiha tamai alkawarin Insha Allahu bazata kara ba,Daga dai ranar ta kulla Gaba da mariya sannan Sa"adatu ta sha Habaici kala kala Domin ita ta yada Labarin Hanne da Hamida su dai yan bada Hakuri ne Amina bama jin mganar su take yi ba suna dai bata Bakinsu ne. Hajiya sun yi mgana dashi Danmallam din tana chan maiduguri yana so ya kara mata mgana  ammh kuma ya kasa ita kuma tana Sane ta bari ne sai ta Dawo tamai bayanin abunda mallam yace. Har Haj.uwa sai da ta Fadamawa itama tace shawaran mallam tayi saboda Kada a rabama Amina hankali Daga karatunta,aranta kuma Tana Tunanin meyasa Danmallan ya Damu da Amina alhalin kowa yasan wannan auran ga yadda yazo sai dai ta kasa sanun amsa. Sati Daya Hajiya sukayi Idi yaje ya Daukosu suka Dawo Mamanmu kuma sai da tayi kwana goma sannan ta Dawo Amina kuma Hajiya na Dawowa ta Tattara ta riga komawa gidanta tana kwana sai su hadu da Sakina ammh basa ma juna mgana Sakina gabadaya Tsanar Amina take ji Saboda gani take yi komai ya Faru ita ce sila Anty Amarya tace ta cika gajen Hakuri ta Daina kiranta in bata da mgana mai Dadi Ita kanta Anty Amarya a Rude take abubuwa duk sun shagule mata Tafiyar mamanmu Gusai sun hadu a Dutse sun koma wajen malamaminsu ya Tabbatar musu da cewa Umar zai dawo ya tafi da Sakina Sannan Burinta zai cika itama mamanmu ya Fadamata Sa"idu na hannunta sai abunda tace suka Zubemai makudan kudi Anty Amarya ta koma Gumel ita kuma ta koma Gusai saboda kada a Fahimci Tafiyarsu Daya. ******** Umar sunyi mgana da Sarood itama ta yarda kila shafan Aljanun ne suka fara amfani da mganin da ya siyo mata a Islamic Chamet na irin abunda suke Hasashe shima ta bangaransa ya Dake  da Addu"a ammh bai kara Jaraba kusartar ta ba ya bari sai ta gama amfani da mganin sannan. *Janafty* *TFZB2011* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Bayan Sati daya da dawowar su Hajiya Daga maiduguri Ranar wata lahadi da misalin karfe goma na Safe sai ga Aliyu a falonta Danmallam ya aikosa tun daga Dutse har gumel wajen Amina. Hajiya mamaki ya cikata Lokacin da Ta fito falo suka gaisa da Aliyu yake sanar da ita yazo neman Amina ne mamaki bai bar Fuskar Hajiya Babba ba ta kalli Aliyu Dake zube saman Cafet din falon nata kansa a kasa cikin ladadinsa kamar abokin nasa Sai da ta gyara zama kafin tace"Amina..? Cikin sigar mamaki kansa na kasa yace"Eh Hajiya..Yace nazo ne na kawo mata waya yana so zasu yi mgana.. Hajiya tayi wani kayattacen mirmishin su irin na manya kafin tace"To ban da abun Danmallan don wannan sai ya Tadoka tunda ga Dutse har Gumel..haka ake yi..? Ai da ya kirani sai na basa Aminar suyi mgana sannan ni nace zan kirasa nayi mai bayanin yadda mukayi da mallam kan wayar da jafar ya kawomin sai na manta zuwana Bikin nan sannan da na dawo ma ban zauna ba Sabga tayi yawa..! Aliyu kansa a kasa bai ce komai ba shima so yake ya gama da Hajiyar ya fita ya Tsitsiye Shehi yaji Dalilin sa na neman yarinyar daya gama Cema kwaila kazama. Hajiya tacigaba da Fadin"Tashi ka tafi abunka Aliyu Amina bata nan suna Hadda Yau ma inaga da wuri zasu dawo Saboda hutu zasu yi sun fara Jarabawar tun awanchan satin ne In ya kiraka ka Fadamai ya kirani muyi mgana..! Aliyu kansa na kasa ya mike yana Fadin"Shikenan Hajiya Allah ya kara girma mungode..! Ta amsa da Ameen da Fatan ya gaida iyalansa daganan ya fice zuwa shashen maallam yamai sallama suka Hade da Anty Amarya ya gaisheta cikin Ladabi ta amsa tana kallonsa cikin mamakin ganinsa da Safe haka sai dai bata Tsawaita mamakinta ba Sanin Aliyun yana zuwa gaida Hajiya da mallam Lokaci bayan Lokaci koda Danmallam din baya kasar Shashen mallam ya koma yamai sallama zai koma domin nan ya fara shiga suka gaisa bai dai zauna bane ganinsa suna mgana da Aba yace bari ya shiga ciki ya gaida Hajiya Mallam bai kawo ma kansa shima wani abu ya kawo Aliyu ba sanin Yadda yake Darajasu Dalilin kawai suna iyayen Abokinsa Umar. Sallama sukayi yana ta sakamai albarka da Fatan Allah ya kaisa gida Lafiya kiran Danmallam bai shigomai ba sai da ya bar Gumel ya dau hanyar Dutse Gefen titi ya samu yayi fakin sannan ya Daga kiran nasa Daga chan bangaran Danmallan yayi mai sallama kamar yadda kowa yasan shi da zarar ya Dauki waya da sallama itace Farko a bakinsa Aliyu bai wani amsa sallamarsa ba yace"Shehi wai miye sirrin ne..? Umar yace"Sirrin na mene..? Aliyu yace"To gani nayi ka bi ka Rude kan karamar yarinya sa"ar yarka ta Fari kuma kwaila..kuma kazama ka tadani Tundaga Dutse zuwa gumel haka Hajiya ma ta Dinga mamakin wannan aikin naka..! Umar ya Dafe kansa dagachan bangaran kafin yace"meyasa ka bari kuka Hadu da Hajiya..? Aliyu yace"Dole kuwa mu hadu don Daga Falon mallam shashenta naje neman Amina ta tabbatar min da batanan suna makarantar Hadda..! Umar yace"Kash..Da tace haka sai kayi Tahowarka ba sai ka fadamata Dalilin zuwanka ba..! Aliyu yayi wata Dariya kafin yace"Ai aikin gama ya riga ya gamu Shehi tuni na Rattafamata komai tace in munyi mgana Dakai na sanar maka ka kirata zaku yi mgana .! Umar yayi shuru kafin yace"Kai dai baka da biyan Bukata duk ka bata komai ni fa kunyarta nake ji shiyasa ban kirata ba ita da mallam..! Aliyu yace"Oho zakace haka mana Tunda na gama Biya ma Bukata akwai ai watarana ba agama ba..! Umar yace"Naji bakomai dai nagode zan kirata yanzu..! Aliyu yace"Ni fa baka Fadamin sirrin ba..! Umar yace"Wani sirrin kenan..? Aliyu na Dariya yace"Sirrin abunda ya susuta ka kan Aminatu mana..! Umar ya saki karamin Tsaki kafin yace"bansani ba..! Aliyu ya saka Dariya kafin yace"To to..Nagano Sirrin ma..Shiyasa jiya daka kirani bakace min wannan kazamar yarinyar ba kai Tsaye ka kira sunanta Tabbas yanzu ta tashi Daga kazama kwaila ta koma Sweet Amina..Ko Honey ce..? Umar ya tsaki again kafin yace"Kai fa Dan iska ne..! Daga haka ya Datse kiran Aliyu yabi wayarsa da kallo yana Dariya sosai in ya Tuna sanda aka aurama Umar Amina yana ta fada yar cikinsa ne ina zai kaita sai gashi kaji sa shuru ya shiga komar yara ya kasa sukuni. Duk da yayi matukar mamakin yadda Komai ya faru Tsakanin Amina da Shehi sai dai bai Tsananta ba Sanin Tsakanin miji da mata sai Allah ammh Shehi ya bani a wajensa ya Dinga Tsokanarsa kenan. Yana Mirmishin ya Tada motarsa ya bi hanya yana kara Dariyan Abokin nasa yana kuma Fatan yasa Amina ta mai mugun kamun da sai ya raina kansa.! Bayan Tafiyar Aliyu Hajiya tayi ta Tunanin me yasa Danmallan ke son mgana da Amina haka da har ya kasa Hakuri..? Bata samu amsar ta ba sai tayi Tunanin kila yana so yaji Lafiyanta ne sannan ya tambayeta ko tana Bukatar wani abu daganan ta watsar da Tunanin ta koma Bedroom dinta tana gyarawa ba Dadewa ta samu kira Daga Danmallam bayan ta Dauka sumgaisa kamar yadda suka Saba sai kuma yayi Shuru yana jin kunyar yayi mata mgana ta san Halinsa Tunda ita ta Haifesa. Yasa ta gyara Zama tana fadin"Dazu Aliyu abokin ka yazo..akan kai ka aikosa ya kawo ma Amina waya zaku yi mgana ko.? Dakyar ya iya amsa ma Hajiya gani yake kamar zata Fahimci abunda ya Faru Tsakaninsa da Aminar. Cikin Dattakonta ta cigaba da fadin"To nace yayi tafiyarsa Sabgoginsa ka taso mutum Tunda ga nisan Duniya Danmallam..! Ai sai ka Kirani muyi mgana ko ba Haka ba.? Kai tsaye yace mata"Kiyi hakuri Hajiya.. Cikin Ladabinsa bata Damu ba tace"Ni ba laifi kamin ba..gani nayi ka basa wahala..Daman ina ta so na kira ka nayi maka bayanin Dalilin Dayasa ban bana Amina wayar nan ba duk da ni nace ka siya mata mgana mukayi da mallam ya nuna min Rike waya ga Amina yayi sauri sannan Duba da har yanzu akwai kuruciya a tare da ita..hakan zai Dauke Hankalinta har ya Taba karatunta da muke Fata ta Samu,ya nuna min na bari sai zuwa gaba in kazo ka tafi da itan sai ka siya mata wayar Lokacin tana gabanka zaka kula da Motsinta yanzu kuma ya nuna min gaskiya a"a shiyasa kaji Shuru ban bata wayar ba tana nan na ijiyeta..! Cikin gamsuwa da mganar ta yace"Hakane Hajiya..! Hajiya tace"To kaji yadda mukayi da mallam da Dalilin dayasa kaji shuru..Sannan yace in kana son jin Lafiyarta ne ka kirani ko mallam din sai in ta na nan sai abata ku gaisa..! Danmallam yace"Shikenan Hajiya Allah ya kara girma..! Hajiya ta amsa da Ameen kafin tace"suna Hadda ammah ina ga bazasu Dade ba in sun Dawo zan kiraka sai na Hadaku..! Cikin Ladabinsa ya shiga Fadin"Allah yasa agama Lafiya Hajiya Allah ya kara Nisan kwana..! Ta amsa da Ameen suka rabu bayan ta Tambayi Iyalansa da ayyukansa. To sun ma gama wayar ba Dadewa wajen azahar sai ga su Aminan sun Dawo suna ta Murna an basu Hutun Sati ukun Dadinsu Daya gobe zasu fara Exam din second Semister a makarantar boko satin daya gabata Gabadaya Revision sukayi. Amina ke fadin Dama islamiya ma ta bata da Hutu ai da sun ji Dadi. Ba"a basu Sakamakon su ba sai Sun dawo Hutu sannan. Anan Shashen Hajiya sukayi sallah Sukaci abinci Hajiya na ciki bata san Amina da Hamida sun koma gida ba Tana zuci zucin ta Kirata sai ta Kira Danmallam din ta Hadasu ko da ta Fito sai Hanne kawai ta gani a Falo ita ke Fada mata Su Amina sun tafi gida kai Tsaye tace Hanne taje ta kira mata Aminar. Hanne ta mike ta saka Hijabi ta tafi tana zuwa ta iske su acikin Dakinsu har Amina ta kwanta bata ga mamanmu ba tana cikin Dakinta ta kwanta in ji Hamida jawaad ke ta wasa da Karamar kwallo a Tsakar gidan. Da Farko Amina Dataji Hanne na Tashinta kin tashi tayi sai da tace mata Hajiya ke kiranta sannan ta Mike tana fadin"Kice Wlh Hanne..! Hanne ta mike tana fadin"Au nace ma Wlh..!? To ki zauna kin ga tafiyata..! Amina ta mike tana fadin"Tsayani Hanne mu je..Fatana Allah yasa ba gida zata saka Idi ya kaini ba..! Hamida da Hanne suka kalli juna kafin Hanne tace"To in chan din ne fa..? Ai kince gidan mijinki ne..! Amina na saka Hijabi batayi mgana ba sai da ta gama sakawa sannan ta Dago Tana fadin"Ni yaushe na Fada..? Allah ya isa na, wuta bal bal in ban Fada ba..! Hamida na Dariya tace"Daman chan Allah ai ya ishi kowa Amina..! Harara ta balla musu kafin ta bangaje Hamida ta wuce fuu hamida da Hanne suka.bita da kallo Hanne tace"Kamar an kara mata bala"i wlh bayan auran nan..! Hamida tace"Kowa ma haka yake fadi..ya danmallam zai yi mganinta bari su koma Madina ki gani nan ta raina achan Ubanwa zata mawa .! Hanne na Dariya tace aifa Daganan ta bi bayan Amina zuwa gidansu. Koda Taje Amina da Hajiya na kuryan Daki Hanne na shiga Hajiya Data Kira Danmallam bai Dauka ba ta kalli Hanne ta nuna mata kofa Tana fadin"Jirata afalo..! Hanne ta Tura baki kafin ta fita Amina ta Fakaici idon Hajiya tayi ma Hanne gwalo ita azatonta wani abun Dadi Hajiya zata bata sai da wayar Hajiya ta shiga kidan larabawa taga Hajiyqn ta Dauka ta mika mata tana Fadin"Karbi Mijinki ke son mgana Dake..! Ta fada Lokaci Daya tana Ficewa Daga Dakin Harda Rufo mata kofar Bedroom din Amina gabanta ya Fadi tabi wayar da kallo ga sunan Danmallan nan baro baro na kan Layi sai jikinta ya fara rawa aranta tace na shiga uku ni Amina Allah yasa ba wani Abu akace mai nayi ba.. Jikinta a sanyaye ta kara wayar kunne Daidai Lokacin da Sanyayyiyar Muryansa ta Doketa Cikin Sallama da Hausansa daya Cakude da Larabci. Sai da ya kara maimaita Sallamar sannan ta amsa Bakin da jikinta na rawa Tun kafin ya gama rufe baki Tace"Ina yi..yini..! Ajiyar zuciyar daya sauke har sai da ta jisa a kunnenta Dayaji muryanta sai yaji Salama da natsuwa Cikin Taushinsa yace"AMINA...! sai taji kamar yafi kowa iya Fadar sunan nata jin yadda ya kirata ita bazata iya tuna ko yama taba kiran sunanta ba Haka ba, jin tayi shuru yasa ya kara cewa"Amina kina lafiya..? Cikin Sanyin Jiki tace"Na"am..eh lafiya kalau..!" "Ya jikin ki..? Ina fatan kin warke babu kuma inda ke miki ciwo..? Ya fada kai Tsaye domin baya Fatan ace wani abu kuma ya tashi bayan Tafiyarsa kunya ta kama Amina ta Dukar da kanta kamar yana ganinta ta kasa mgana sai gabansa ya Fadi da Sauri yace"Ko da wata matsala ne..? Da Sauri tace"A"a na warke..! Afili ta Furta"Alhamdulillah..! Kafin yace"Naji Dadin haka ina Fata kamar yadda kikamin alkawarin baki gayama kowa ba ko..? Sai da ta gyadamai kai kafin tace"Eh ban fadama kowa ba..! Cikin jin Dadi yace"Dakyau naji Dadin Haka..Ya karatu fata kina maida Hankali wajen karatu..?. Da Sauri tace"Eh yau ma mun yi Hutun Hadda..Gobe ma zamu Fara Jarabawa a boko..! Kai ya gyada kafin yace"Allah ya bada sa"a..ki rika maida hankali kinji ko..? Ta gyada kai ya cigaba da Fadin"Sannan ban da wasa ban da Fada ban da gujeguje ke yanzu ba yarinya bace kin tashi Daga su Hamida ke matar aure ce ba Daya kike Dasu ba kina jina ko..? Nan ma kai ta gyada mai yace"Baki da baki ne..! Ba nace ki daina min mgana Da kai ba .! Da Sauri tace"Naji insha Allahu..! Ajiyar rai ya Sauke kafin yace"Kina Bukatar wani abu..? Tace bakomai kai Tsaye yace"Ki rika gaida Sakina in kun hadu tana gaba Dake kinji ko..? Amina ta Tura baki kafin tace"Ni fa in na ganta batamin mgana sai tayi ta Hararana har zagina ma tanayi..! Cikin mamaki yace"Ita Sakinar..? Amina tace"Eh shiyasa nafi son zaman nan fiye da chan sannan achan ina jin Tsoro da Daddare bana iya barci don Allah ka Fadama Hajiya ta rika barina ina kwana anan in ka Dawo sai na koma achan..! Kawai sai ta sakamai kuka sai yaji Hankalinsa ya tashi meke Damun yarinyar nan ne Cikin Tausasa Murya yace"Naji ki daina kuka zan mata mgana..Daman baki daina Firgita cikin barci ba..? Tace mai eh sai da yayi shuru kafin yace"Ki samu mallam yau da Daddare in ya natsu ki Fadamai abunda kike jin in zaki Firgita kin ji ko..? Tace"Na Fadamai..? Yace"Eh ki Fadamai sannan mganar Zagin ki da Sakina ke yi kada ki Fadama kowa har su Hajiya zan mata Fada insha Allahu zata Daina ke dai in kin koma gidan kun Hadu ki rika gaisheta saboda ko bakomai Tana gaba Dake kuma a islamiya an koya muku yin biyayya ga na gaba da ku ko ba Haka ba..? Tace eh ya cigaba da fadin"To ki rika bata girmanta kin ji ko..?. Ta amsa da toh bai Tsawaita mganar ba yace"Zan ce ma Jafar a Cefanan wannan watan ya siya miki Goldenmorn da Cornfkles Saboda Saukaka miki Wahala sai ki Rika sha in zaki tafi makaranta..! Tace "To nagode..! Ya amsa ta da Fadin"Kada ki damu komai kike Bukata kada ki tambayi Hajiya ko mallan ki yi ma Jafar mgana ko kuma ki Dauki wayar Hajiya ki kirani kinji ko..! Nan ma tace mai da toh tagode Dagnan yace ta maida Hankali a karatunta ta amsa mai Daganan ya mata sallama ya kashe wayar. Tabi Wayar da kallo Tana Tura baki wai ta rika gaida Sakina Tab wannan mara mutumcin ne zata gaisheta.. Shi kuwa sai da sukayi mgana yaji Hankalinsa ya kwanta har ya natsu ya Cigaba da Duba Takardun Dalibansa da sukayi gwaji. Da suka gama wayar kunya ta Hana Anina fitowa sai da Hajiya ta Shigo Daukan abu ta ganta zaune tayi shuru tace"A a Mamah tunda kun gama wayar ki fito falo hanne na jiranki mana sai ki zauna ke kadai..! Jin haka yasa ta mike ta mikama Hajiya wayar, ta karba ta Fice da Sauri Hajiya ta bita da kallo tana Mirmishi a Cikin aranta tana Fatan addu"an su Allah ne ya karba na amitar da Ruhin Amina da Danmallam waje daya. Amina na fita Hanne ta taso tana Tambayanta da wa tayi waya Amina ta balla mata Harara kafin tace"Bansani ba..! Hanne na Dariya tace"Nasani Ya Danmallam ne..ko..? Amina ta mata wani kallo kafin tace"In ma shine sai na Fada miki..? Sirrin miji da mata..! Hanne ta saki Dariya kafin ta Ja Hijabinta tana fadin"Bari naje na gayama Hamida..Sabon Update..! Amina tayi Tsaki kafin tace"Ai ke Hanne mijinki ya shiga uku..duk wanda ya aureki ya auran ma kansa sai kin hada Fada a Family din mijinki Saboda munafuncinki..! Hanne bata bi ta kanta ba ta fice Amina tayi zamanta Falon Hajiya chan sai gasun dawo Tare Hamida sai kara maimaita abun da Hanne ta gayamata take yi Amina ta musu wani banzan kallo kafin tace"kusan dai ni yanzu ba Sa"arku bace ko..? Igiya uku ne akaina..Taimaka muku ma nake yi ina yawo da yara. ! Hanne da Hamida suka saki baki ganin haka yasa ta Musu gwalo tatashi da gudu ta Fada Dakin su Hanne Tana Dariya suka mara mata baya suna fadin yau sai ta gayamusu su waye yara..? Ranar dai anan suka wuni Shashen Hajiya suna abunda suka saba sai bayan sun dawo islamiya ne Hajiya ta saka aka maida Amina gida tana kunkuni Tana komai bata samu yima Baba mallam bayani ba sai washegari da suka dawo makaranta ta Fadamai ya Dade yana mamaki ya tambayeta yaushe ta fara tsorata tace tun tana karama ta dade mallam ya Dinga Fadin Sakacin mamanmu da Aba da Amina na Fama da wannan Laluran ammh bsu sani ba Hajiya ce ma ta Lallasheshi ya bar mganar da yace har Aba din sai ya kira da mamanmu ya musu Fada. Shi ya Rubuta mata addu"o'i ya bata yace ta Rika karantawa Duk Dare in zata kwanta Tare da Sauran addu"an barcin da Annabi ya koyar damu. Amina yadda Taga Mallam ya Dau abun ne yasa itama bata Dauka da wasa ba sannan Danmallam ma sun sake mgana da wayar Hajiya Data Fadamai yadda sukayi da mallam ya mata Fada kan ta Dage kada wasa ya Dauke mata Hankali ta rika kwanciya bata karanta su ba. Shiyasa ta Dake bata kwanciya sai ta karanta sai gashi kuma Cikin ikon Allah tunda ta Dage sai ta samu Saukin Firgita din sai abunda ba"a rasa ba Danmallam har da mallam sun yi mgana Mallam nata fada yana Fadin da Haka Umaima ta Fara gashi nan suna so su taba mata kwakwalwa Dannallam yana so ya Fadama Mallam bayan haka ma yana Zargin akwai wani abu Tattare da Amina sai dai kuma bai da Hujjan hakan ammh yana so sai in ya kara Dawowa ya Zauna ya Fahimci matsalanta Domin Ranar da abun nan ya Faru tsakaninsu da Washegarin nan da Safe yaga tana wasu abubuwan da Dole tana da wani abu a Tattare da ita. ******* Kwantashi ba wuya a wajen Allah su Amina har sun gama Jarabawarsu sun yi Hutu taso ta zauna anan tayi Hutunta Hajiya ta hanata sai ta Roki Baba mallan kan su Hanne su Bita ko Sati Daya su yi da Farko Hajiya ta Hana sai da Mallam ya saka baki Sannan ta amince suka Tattara suka koma chan da Niyar Sati Daya zasu yi Saboda islamiya basu yi Hutu ba. Mamanmu bata Damu ba da akace Hamida zata je gidan Amina Domin alokacin tana Tsakar Cin Duniyarta ne Domin komai tace Aba ya bata baya Gaddama Kudi yake sakar mata bana wasa ba ta zama Tauraruwa a wajen sa Mamanmu ta samu Cikar Burinta Fiye ma da yadda take fata shiyasa ta manta da kowa da komai ko Anty Amarya ta kirata bata ma kaunar Hakan gani take tana neman Takura mata Shiyasa Amina ma bata gabanta Ta barta da Anty Amarya chan itace Zatayi mganinta ita yanzu Sa"idu ne agabanta yanzu shawaran komai sai yayi da ita sai abunda tace koda yace Jafar yace kaza ya kamata ko Hajiya sai tasan yadda tayi ta Kushe mganarsu ta sauya da nata Shiga kawai take tana fita Daga kayan alfarma kamar wata Yarinya sannan Malaminsu tana sakarmai kudi sosai Domin ta yaba da aikinsa Anty Amarya kuma tana nan tana Jiran gawom Shanu domin ta yarda da aikin Malam ya sanar da ita Nasara tatace shiyasa bata Damu ba ta koma ta Zauna tana jiran tsammani kamar yadda ta basa duka yardanta Shiyasa ko Sakina ta kirata tana mata Korafi take mata Fadan bata da Hakuri aiki nawa suka basa kuma ya Biya musu Bukata..? To wannan ma ta Zauna ta Jira komai zai zama Daidai da yardan Allah abunda basu sani ba Daga wannan Lokacin aikin ya kuskure musu sannan zasu cigaba da jiran majirata ne Jiran da zai kai su ga Ranar Nadamar su da Tonon asirin su..! Ko Hutun da su hanne suka tafi Sakina kamar ta Haukace saboda Bala'i Amina Mahaukaciya take so ta maidata,gwara ma su Hanne suna dan jin mganarta banda Amina sai ta gama masifarta sun ba'ta mata Falo ko Kitchen Amina ta mata gwalo ko Ta mata Tsaki ta shige Daki abunta Sakina taci ji Yatsa kamar me..? Kamar yadda yace a Cefanan watan nan an kawo su Goldemorn su Amina an samu banza ana ta Wadaka madara kuma da kayan Tea kafin Sati sun kare saboda yadda suke barnan sa basa da aiki sai dan sululu ko Wainar Fulawa gashi Sakina bata son kazanta su kuma in suna aiki a Kitchen din sai sun yi kaca kaca dashi in tayi mgana Hanne da Hanida kadai ke Sauraranta banda Amina da take maidata ma mahaukaciya. Sakina abun ya isheta kullum sai ta Kira Danmallan ta kaimai karan Amina da kannensa shi har ma ya gaji Saboda bai isa ya kore su ba Amina Matarsa ce sannan su Hanne kannensa ne ko ba aure suna da Damar zama agidansa watarana da abun ya ishesa sai yace ta bama Amina wayar da an bata ya fara mata Fada sai ta saka kuka tace In ta gaishe da Sakina sai taki amsawa ta bita da Zagi sannan bata barin su suna shiga Kitchen sai tace suna mata kazanta Ayadda take mgana ne yasa Dole ma ayadda da ita sannan tace ga su hanne ma yaji ta bakinsu su hanne kuma basu taba kwaye ma Amina baya ba, sai su karantamai yadda Amina tace Daga karshe sai abun ya koma kan Sakina yayi mata Fadan itace babbar banza tana Biyema yara sun rainata sannan kada ta kara Hanasu shiga kitchen ta bar su dafa abunda suke so itama ta Dafa nata baya son Fitina. Tunda ga ranar ko Takai ma Korafin Amina ta mata kaza bai Sauraranta Anty ma Zaginta take yi tace ta Daina Danunta tunda ita Sakarya ce zata Zauna yara kanana su gagareta Alhalin basu san yadda yaran nan suka Sakata gaba bane barin ma Amina in ta fito falo ta gansu ta rika waka kenan tana cema mata agwagwa in ta yi mgana ta maidata mahaukaciya sannan ba Tsayawa ma take yi ba,ballatana ta Daketa ta huce. Su hanne wajen kwanansu goma Daga su Har Aminar basa zuwa makaranta da Hajiya tayi mgana ne Mallam yace ta rabu dasu Idi ya rika zuwa yana Daukosu yana kawo su makarantar Daganan,saboda dukkansu yara ne sannan nan gaba kadan In Aminar ta bar garin ina zasu ganta..? Sannan kuma suma watarana gidan auransu zasu watarana sai dai labari..da Haka ta kyalesu suka zauna achan sai dai Idi ke zuwa yana Daukosu da an tashi kuma ya maida su. Cin Duniyarsu da Tsinke suke yi ko ajikinsu Sakina ta koma zaman Daki bata Fitowa saboda su in tana son Tsira da Mutumcinta Ranar kwatsam sai ga Aliya matar Aliyu sun zo kawo Amarya wata Diyar kanwar mamanta ne shine tazo gidan ta iske Sakina cikin Daki Amina ta gagareta bata iya ma Fitowa sanda Sakina ke Fadamata tana kuka Sai taga Laifin Sakinar da ta Zauna yarinya karama ta gagareta. Taja Sakinar suka fito su Amina na Falo sunyi Daidai ga Filets nan da Kofuna da gorinan lemuka da suka gama dasu nan basu Dauke ba suna Hira Ita a Dole sai ta kwatan ma Sakina yancinta.. Haka ta Dinga surfama Amina Zagi tana kiranta kwaila kazama mara Tarbiya su hanne sukayi Tsuru Tsuru Amina ranta ya baci ta mike ta rama Zaginta da Aliya ke yi ita kuma tace Zata Daki Amina ai ko sun ga Hauka Amina ta Tsaya kikam idanuwanta sun juye ba baki sai Fari tace in Aliya ta isa ta tabata tagani Sakina ke jan Aliya tana ta bari kada ta tabata ta ja mata bala"in wajen su Hajiya. Ita kan Aliyan ta Tsorata bata Taba Aminar ba suka koma Daki tana Borin kunya Amina kuwa ba wani Abunda ya Sameta Zafin ranta ne ya taso mata Taso ta tabata ne Daga Sakinar har Aliyan sai sun raina kansu Wlh sai kuma Allah yaso su su Hanne na tabata Hakuri ta balla musu harara tace sun cika Tsoro ba wanda ya isa ya Takura musu acikin gidan nan. Aliya taso kwana ne ammh ganin yanayin Amina yasa taki kwana ta koma gidan Amarya ta kwana ko Washegari Datace zata dawo bata Dawo ba ko da Sakina ta Kirata tace mata gata a Hanya zata koma gida ammh Tana zuga Sakina kan Wlh in Amina ta kara mata rashin kunya ta kamata ta mata Dukan tsiya Sakina jinta kawai take ina ita ina taba wannan yar gold din ai sai Hajiya ta saka Umar ya Saketa. Allah ne ya taimaketa suka koma makaranta Hajiya tace su Dawo gida idi yazo ya Dauketa sai ta Samu Sauki Bata ma haduwa da Aminar sai ta bar gidan take Fitowa sannan Daga ranar jumma"a sai Lahadi take dawowa tana ganin Lokacin Dawowarta yayi zata shige Daki karfi da yaji Bala'in Amina da jindalinta ya Saka Sakina ta kasa Sakewa agidanta. Gashi Danmallam ya Daina Sauraranta indai kan Amina ne yace yana wata kasar ta daina tadamai da Hankali baya so in bazata kama girmanta ba bazai iya Hana Amina ta mata Rashin kunya ba abu goma da Ashirim ga rashin miji ga Fadan Anty Amarya Data Kirata sai tace laifinta ne sannan ga Amina ta Sakota gaba..! Ana cikin Haka Sadiya Diyar Anty Amarya ta Haihu bakwaini yarinyar tazo ba rai anan Dutse su Sakina ana ji sune gaba gaba ita da Hj.Nasara da Hajiya Babba suka tafi suka Duba Sadiya Dake asibiti domin ance ta Zubar da jini sosai achan suka Rabota Tunda Danmallan ya barta ita ta zauna da Sadiyan har aka sallamota Daga asibiti duk da ga yan"uwa ammh Anty Amarya tafi yarda Sakina ta Zauna da Sadiyan. Bayan sun Dawo gida ne Sakina ta Fara Zazzaabi har da su karin ruwa koda akaje asibiti akayi Test aka gano Tana da Shigar ciki kimanin wata Uku da kwanaki Ashe koda Danmallam ya Tafi ya jefa kwallinsa araga a maran Sakina basu sani ba. Murnan wajen Anty Amarya da Sakina ba"a mgana kamar an basu aljannah Hajiya da mallam ma Tare da shi kanshi gogan Danmallam Domin yana matukar son yaga kwansa a Duniya,Sannan da kansa ya Sanar da Sarood ta tayasa murna Har dai yanzu shuru ne ba wani cigaba ammh basu sare ba suna cigaba da shan mgani shi dai har yanzu ne bai yarda da Shawaran Aliyu na ya kira mallam ba yana tunanin al"amarin nasu ba Sihiri bane. Mamanmu dataji itama tayi murna sannan tasan yanzu tunda Cikin Sakina ya samu sai Madina ta barta taci Gumin Wahalarta ta Daina Damunta. Su ba Fatan cikin ya zauna suke yi ba kansu yayi girma suna ta Feleke Anty Amarya taso Sakina ta Dawo gabanta ta raini cikin mallam ya hana Saboda za"a bar Amina ita kadai Gidanta ta koma ammh sai Ta tafi da Sa"adatu tana kula da ita ana zuwa Daukansu Ita da Amina da ko mgana basa ma juna Amina taji zencen cikin Sakina ko ajikinta tunda ko"ina Zencen cikin ya Zaga. Haj uwani na gefe tana kallonsu aranta Dariya take musu domin tasan wannan karon ma ba zai zauna ba Haka kuwa akayi yana da wata Hudu watarana da Daddare Sakina ta tashi Cikin Jini Hankalin Sa"adatu ya tashi ta Kira Anty Amarya koda ta zo ita da Idi Direba suka tafi asibiti sai wankin Ciki akayi ma Sakina cikin jikinta ya Sake fita karo na Hudu. Abunda Haj.Uwani bata sani ba in na Sakina ya sake zubewa daman chan Allah bai yi Rayayye bane ammh wanda Allah zai rayasa yana nan har ya fara zama gudan jini batare da kowa ya Farga ba Hatta kuwa da wacce Cikin ke jikinta. *Janafty* *TFZB2012* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Wannan karon ba Anty Amarya kadai da Sakina suka shiga Tashin hankali ba harda mallam da Hajiya Tare da Uban gayyar Danmallam da kuma ilahirin Masoyansu sun tausaya musu bisa rasa wannan cikin ma a karo na hudu kamar sauran. Mallam shi ya saka ayi ma Sakina gwaje gwajen mahaifa domin a Fahimci inda matsalan take Dayake wani asibitin kudi dake cikin gari Anty Amarya ta kawo Sakina duk kudin da aka kashe mallam ya Dauki Nauyi sannan suna tsaye kan Sakina shi da Jafar da Nasir da ita kanta Hajiya da Aba din sakamakon Sakina ta Zubar da jini yasa sai da aka mata karin jini gabadaya yan"uwanta ne Anty Amarya ta kira tana kuka ta Fada musu wadanda ke kusa suka zo aka samu aka gwada jininsu sai Allah ya taimaka jinin kaninta wanda ke bimata yayi daidai shi aka diba aka sanya mata. Sakina sai da ta kwana ta wuni sannan ta farfado ko ba"a fada mata ba tasan ta rasa cikin ta ma a wannan karon domin haka take yin indai zata yi bari tayi ta zubar da jini sannan ta Fice Daga Hayyacinta na wani Lokaci. Sakina tayi kuka kamar ranta zai fita wannan karon Anty bata da bakin lallashinta domin ta Sare ta kuma kara yarda da Hasashenta na Tabbas akwai wanda ke lalata cikin Sakina akwai wanda ke neman shiga Tsakaninta da Cikar Burinta ko waye kuwa in ta ganosa sai ya gane bai da waye ita Madina bata fito ba sai da ta shirya. Anyi ma Sakina gwaje gwajen da Mallam yace an kuma tabbatar musu da komai lafiya harta mahaifanta Lafiyalau ita Hajiya har tana Fadin ko kila Sakinar tana da Raunin mahaifa ne ammh sai likita ya tabbatar musu da Komai lafiya Sanadin barin dai bai gano wani abu ba sai a bar shi da Allah ke ikonsa Domin shi ke kashewa ya kuma ya rayashi alokacin dayake so Sannan Haihuwa ta sa ce ga wanda yaga Dama yake bamawa Haka Mallam ya dinga fadama Sakina alokacin Dayake mata Nasiha a daran Data cika kwana Hudu asibitin Daya kara zuwa Dubata shi da Hajiya da Daddare. Hajiya ma ta kara da nata Nasihun Saboda duk mai imani in yaga yadda Sakina ta dawo sai ya Tsausayamata kuka kadai take yi,mganganunsu kwata kwata basu shiga kunnenta ba Hango kanta take a matsayin Bora duk Ranar da Haifarma Umar magaji ya kuskure kanta sannan ta Fara Sarewa da Tunanin Anty bazata iya ba Sannan wannan Burin nata bazai Taba cika ba Nasara kuma su daina Hasasota nan kusa tana da Nisa kafin su isketa bama domin haka ba itama Tana so ta Haihu sosai take son Taga ta Haihu sannan tafi so kowa Sanin yadda Umar ke son Haihuwa ya Fada mata ba Sau Daya ba sau Biyu ba,kawai yana da kawaici ne sannan addininsa yasa ya yarda da Allah ke yi alokacin da yaso shiyasa bai cika nuna Damuwarsa sosai ba.. Shiyasa har su mallam suka fita Sakina ma bata cikin Hayyacinta Anty ke kwana da ita tana kula da ita suna Fita Sakina ta Fashe da wani kuka mai karfi Daga karkashin ranta Anty Amarya ta taso zata riketa ta Daga mata Hannu tana fadin"Don Allah Anty kada ki hanani kuka ki bar ni nayi domin shine kadai zai sa naji Sanyin abunda ke damuna acikin Raina..! Tafada tana Dakatar da ita da Hannu Dole Anty ta koma baya ta Jinjina kai gabadaya bata cikin natsuwarta Saukinta Daya yadda mallam da Hajiya da yan"uwan Danmallam ke Tsaye kan sakina da shi kanshi Danmallam din,arana ya kira fiye da sau Biyar yana tambayan Lafiyan Sakina Sannan ya Turo abokinsa Aliyu dashi ake ta Zirga zirga in bai zo yau ba zai zo gobe har da matarsa Aliya yazo Abinci kuwa baya zuwa hannu Rabbana da kwalayen maltina da kayan maarmari saboda karin jini ga ita Sakinar Ta kira Dayyaba sun yi mgana gobe take so in kanwarta A"i tazo daga Dutse zata bar mata Sakina ta kula da ita zata koma wajen mallam tamai bayani so take ta gano wanda ke lalata mata aikin data wahala tayi shekaru tana Fata akansa in ko Zarginta ya Tabbata kan Uwani sai ta raina kanta sai ta Fahimci wacece madina ba marliya ba. Tana gani Sakina na gunjin kuka bata da karfin gwiwan hanata saboda ta gaza Duka alkawarin data mata ta kasa cikamata,maimakon ta Fahimci Talalar da Allah yayi musu ta kare ne suke ganin sabawa akan lamarinsu ammh ina idonsa ya rufe gani suke a koda yaushe nasara tasu ce. Suna Mota zasu koma gida Hajiya Dake gefen mallam ta kallesa tana Fadin"Mallam ka kira Danmallam ka yi mai Nasiha da Hakuri ko..? Domin jiya da mukayi mgana yace min yana gida kwance bayajin Dadi..kuma ko shakka babu abunda ya faru ne ya tabasa kamar yadda ya taba Sakina wannan karon..! Mallam ya muskuta kafin yace"Na kirasa da Safe munyi mgana..Sosai nayi masa nasihan na kuma tunasar dashi cikar imani shine yadda da kaddara mai kyau ko akasinta na horesa da yayi Hakuri ya jira kadan kila Tanadin da Allah yayi masa yana gaba ne Rashin hakurinsa sai ya bata komai..! Hajiya tace"Hakane kan mallam..Allah yasa mu dace Allah ya basa zuru"a Mai albarka..!. Mallam ya amsa mata cikin Damuwa a karkashin ransa yana jin Tsausayin Umaru ache kana neman rufe shekaru arba"in ko Haihuwan fari bakayi ba sa"o"insa ya tabbata Har da masu ya'ya goma wadanda sukayi aure da wuri ma kenan ga dai Amininsa Aliyu nan baya baya yayi aure ya"yansa Biyu tabbas yasan akwai Damuwa ammh bazai barsa ya nuna gazawarsa ba zai cigaba da Tunasar dashi Hakuri da Rayuwa a duk sanda tazo masa da kuma yanayin datazo maka sai ka saka Hannu Biyu ka karbeta. Kamar yadda Anty Amarya ta kwana da kuduri gari na waye saboda ma tana Sauri bata jira A"in tazo ba sun dai yi waya tana Hanya ta kusa shigowa ta bar Sakina tace mata zata je ta Dawo alokacin har Jafar da Nasir sun kawo breakfast Matan su suma suna kokari sunzo sun duba Sakina Daganan kowannen ya wuce wajen aikinsa. Batare da ko Sanin Mallam ba ta Dauki Hanyar Dutse tunda Gidan malamin nasu chan wani kauye ne kafin a shiga garin Dutse ne da wuri ta isa akwai layi ta jira kadan sannan aka bata izinin shiga tana shiga ko kafin tayi mgana ya Zayyana mata Duk abunda ya faru yace Garzali ya sanar dashi komai saboda haka ta Bada kudin da aljanu zasu sha jini kawai tayi tafiyarta nan da Sati Daya zai kirata abunda ke nan zai sanar da ita komai nan ta Bude bakin jaka ta Zazzage mai kudi da batasan ko nawa bane Kudi ne dai masu yawa har da wadanda Sakina ke samu a asibiti in anzo gaisheta sannan shekaranjiya Jafar ya kawo mata 30k yace in ji Danmallam yace ta rike a Hannunta koda wani abu zai taso ta saka a jaka Saboda komai na kudi mallam ke gudanarwa ko sisinsu basu kashe ba Har da su ta zubema Malamin nasu sannan ta kamo Hanyar Gumel Ranta na kuna ta kosa agano wacce ke neman shiga Tsakaninta da Burinta yadda zuciyarta ke azalzalanta Har taje ta Dawo ba wanda ya Sani daga ita sai Dayyaba sai Allah kawai yasan inda taje ko da tadawo Sakina ta samu barci kanwarta kuma ta zata Gida ta koma tayi wanka ta Huta Shiyasa bata Damu da Tambayarta ba. Sai da Sakina ta kwana goma asibiti sannan aka sallameta ta koma gida Saboda yanayinta yasa sai mallan ya yarda da Rokon Anty Amarya kan Dawo da Sakina gabanta har sai ta Warware,Daman Amina tunda akayi haka tana nan gidan Mallam bata koma chan ba mallan yace Tunda hakane dukkansu su zauna anan in Sakina ta kara jin Sauki sai su koma Tare abun yayi ma Amina Dadi daman ta Tsani zama agida chan sannan ta Tsani zama inda ba Hamida ba Hanne ita dai murnanta da Farincikinta ta gansu tare tana musu Jidalinta suna Dauka. Har ta da Amina duk kinta da Sakina sai da ta Tausayamata ganin ta yadda ta Rame sai katon kai,Dayake ranar da aka sallamo su suna makarata sannan bayan sun dawo islamiya suka tafi sai da suka Dawo ita da Hamida da Hanne Hajiya tace su shiga su gaisheta suka iske ta cikin Dakin sus Sa"adatu zaune ana bata abaya abaki sai ido zuru zuru kamar na mayu in ji Amina da suka fito. Hamida tace"Gaskiya ta bani Tausayi ji beta kamar ba ita ba duk ta rame..! Amina tace"Sai yanzu na kara ganin Gajartan ta ga Katom kai ashe ma dan jikinta na Rufa mata asiri..! Hamida tace"Amina ciwo dai na kan kowa..! Amina ta Harareta kafin tace"Ai ban ce bai kan kowa ba..In kin ji mgana na Tsausaya mata ne..! Hanne dai batace komai ba sai alokacin tace"Tasha Wahala inji Hajiya tace sosai.Sannan ta tada Hankalinta barinta na Hudu fa kenan har ya Danmallam naji hajiya namai Fada har ciwo sai da ya kwanta fa..! chan madina..! Hamida tace"Wayyo da Tsausayi kam..Allah ya basu rayayye..! Hanne ta amsa da Ameen banda Amina da Haka kurum taji ranta bai yi Dadi ba, wai har ciwo yayi saboda barin Cikin wanchan gajerar matar basu Fahimci yanayinta ba ta wuce Shashen Hajiya ta bar su nan Daman a Bakin Shashen Haj.Nasara suka Tsaya suna maida Zencen. Tun daga lokacin sai Kulawar Sakina ta koma karkashin Anty Amarya tunda ashashenta take sannan Hajiya ma har nan take zuwa tana Dubata ta saka su Ladidi su yi ma Sakina Fatan wake da ferfesun kayan ciki Saboda jininta ya Dawo sosai har Hajiya nasara ba barta a baya ba ita da Haj.Uwani Wacce Anty Amarya ke jin takaicin inda ta ganta ta rako Hajiya tana wani iyayi ita hakanan aranta taji bata yarda da ita ba.. Sannan Har mallam ma ya kan shigo ya Dubata Lokaci bayan Lokaci uwa uba kuma duka kannen Danmallam wadanda ke gidan auransu sun ji Labari sun kuma kira sun ma Sakina Sannu harta da Nazir da matarsa matan su Jafar kuma sun je asibiti sannan da suka Dawo ma sun zo sun Kara Dubata Ikram dake kusa tazo ita da Sadiya da Zulaihat sun zo sun kwana Daya sun Dubata sun koma Tunda Mamanmu ta Kirasu ta Fada musu har da goggo Husai Dake Jordan taji Labari ta kira tayi ma Sakina Ya jiki da jajen Abunda ya Faru haka su ya Jawahir suma sun kira harta Aba da basa wani Shiri da Anty Amarya Yaje assbiti bai san iyaka ba da suka Dawo gida ma sau biyu yana shiga Dubata ba saboda alherin kowa ba sai Saboda Danmallam In sakina ta fara kokenta Anty Amarya ta Dinga ce mata kenan"Ai kuka bai kamaceki ba Sakina..Godema Allah zaki yi..Ki kalli abunda ya faru Dake mijinki bai juya miki baya ba yana Tsaye kanki da lafiyarsa da Aljihunsa shi da Danginsa da yan"uwansa hajiya da mallam Sakina kullum suna tafe Shashen nan wajen Duba Lafiyarki wannan kadai ba matakin nasararmu bace.? Tabbas mun samu nasara domin ko bakomai Danmallam da Danginsa suna kimanta ki Sakina suna Darajaki Daraja mai yawa ban gane haka ba sai da wannan abun ya sake Faruwa..! Sakina cikin kuka take fadin"Na rasa Cikina a karo na hudu Anty..Na kara rasashi yaushe zan samu wani Cikin har ya zauna na Haihu..? Anty Amarya tace"Kada ki damu zaki Samu wani cikin..kuma da yardan Allah sai kin Haifar ma Umar Magaji in baki Haihu ba to sai dai ya Dauwama shima bai Haihu ba..Na Rantse da wanda Raina ke hannunsa in Zargina ya Tabbata sai na yi Fito na Fito da duk wanda ke Rusamin aikina ko waye shi kuwa..!. Tafada cikin kaushinta akoda yaushe kalamanta yanzu tuni sun Daina ma Sakina aiki a kanta ta fara Sarewa da al"amarin kwata kwata. Amina suna cigaba da zuwa makarantar su,Sannan tafi zama bangaren Hajiya har Hamida ma tare suke sai suyi sati basu kwana agidan Aba ba suna Shashen Hajiya saboda Hanne sannan ita kanta Mamanmu bata wani Damu ba Amina ba yanzu Duniya ta samu,Daga ita sai Aba ko Jawaad wani Lokacin Wajen su Amina yake kwana ashashen Hajiya Duniya ta samu yanzu Aba bai mata gaddama ko Hajiya da mallam tasha gabansu sai su gama mgana dasu yazo mamanmu na tambayansa zai kwashe ya Fadamata shawara kuma akomai da ita yake sai abunda tace shi yake yi ta kankane komai tana baza buraubanta yadda ta gama Dama shiyasa har Hamidan ba Damuwa da take yi da ita ba yanzu tasan dai lokacin auran su nayi za"a aurar dasu Amina kuma Daman sunan auranta gantali Ita kanta Aminar tasan Mamanmu ta Rage kula da ita kamar baya sai ta Danganta hakan da yanzu ba Yaya ba su ya Zeenatu Hidima tayi ma mamammu yawa tayi mata uzuri sosai,Su Hajiya kuma basu wani Lura ba saboda basu fiya saka ido ba ko da yaya nada rai Amina da Hamida yan Shashenta ne kowa ya sani shiyasa ko yanzu da suka Tare anan bama wanda ya Damu. Sannan in Allah zai ikonsa kan wani abu da karesa da kansa sai ya kaudar da Tunanin mutane akan hassashen wani abu to kamar hakane ya Faru da Amina cikin Lokaci kadan gabobinta suka fara girma kirjinta ya fara Cika har yazo ma yafi na Hanne yana neman fin na Hamida sannan Daga kasanta Hips dinta ya Bude ta fara Fashewa kibanta Daga sama ya Fara sai kuma ta Bude ta kasa sannan Fuskarta ta Ciko sosai yawancin kayanta ma sun mata kadan riguna sai da Hajiya ta saka aka kai aka Buda mata itama taga kiban da Amina tayi sai bata kawo komai ba azaton Cin abincin da Amina ke yi saboda cin abincinta ya ninka na baya har Cikin Dare ci take sannan ga shan Tea madara bata sati take karewa Amina hakanan take hambalamta har sata take yi tatafi da ita makaranta. Har su Hamida sai da suka ce Amina tayi kiba yanzu ko Hamida albarka. Ita kanta Aminar tana jin Canji Ajikinta ammh bata Damu ba Sai itama take Tunanin cin abincin datake yi shiyasa da kuma kila girman da batayi bane abaya sai yanzu take yi. Ranar ma suna shiri zasu makaranta da Safe Dakyar Amina ta iya saka Rigarta ta matseta duk da an kara Budeta. Ta saka tana Nishi kafin tace"ni dai girman nawa bai zo min da Dadi ba..Ku kalle har Tumbi fa na fara..! Suka bi Cikin nata da kallo kafin su saka Dariya Hamida tace"Kirjinki wlh sun fi nawa..Tumbi kuma wlh gashi nan Hanne..! Tafada tana Taba cikin Amina Daya Fara tasawaa taji Tauri ta cire Hannunta Tanacfadin"Sai Taurin bala"i..! Hanne tace"Ke kuwa wannan Abincin Datake narka ai ba Lafiya bane..Dole ta Ijiye Timbi taurinsa kuma Uban Madaran Dake sha ne wlh in baki Daina ba kikayi Kiba Ya Danmallam bazai je dake madina ba domin in kika Hau seleken awon Nauyi aka ga kin yi kiba bamai zuwa Dake..! Amina ta balla mata Harara tana Fadin"Dama wake son zuwa..? Dariya suke mata ita kuma tana masifan ita ba inda zata je Daganan suka shashantar da mganar. Aranar da sukaje gaida mallam kan su tafi makaranta da suka fita yana Tare da Hajiya ne sai da yayi mata mganar Kibar da Amina tayi hajiya tace kila gabobin girman nata basu bayyana ba sai yanzu Shima sai ya yarda da Haka. Duk wanda ya ganta bai kawo ma kansa wani Tunani sai Tunanin gobobin girma ne suka bayyanan mata Mamanmu kuma bata bi ta kan Amina ballatana ta iya ankarewa da wani abu na Faruwa Anty Amarya kuma sai tayi sati ma bata ga Amina ba in ma ba ta ganta ba, bata ma Tsayawa kare mata kallo balle ta zargi wani abi zai faru. Ana cikin haka aka fara Biyan kudin jarabawar fita ta su Akilu Hajiya tace a biyama Amina sai maallam yace da Aminar da sa"adatu da Hannatu da Hamida duk a Biya musu su zana a SS2 dinsu da hajiya ta nemi jin Dalili sai ya sanar da ita cewa in Umaru yazo ya tafi da Amina madina su hanne kewa zai musu yawa sannan sun ma isa auran suma da su zauna suna Damuwa da rashin Amina suma zai aurar dasu nan da wattani kadan zasu cigaba da zuwa hadda da islamiya kafin Mazajen nasu su bayyana Hajiya bata yi gaddama ba Tunda daman Jafar da Nasir sun fadamata cewa Karatun SS3 din duk maimaici ne da Reviosion shiyasa sai tayi na"am da mganarsa acikin Satin akaje aka biya musu su shida har da Akilu da Zubairu. Amina da taji murna kamar me baza"a rabata dasu hanne ba Sa"adatu ne bata so ba,tayi ta kuka Anty Amarya ko ta kanta bata bi ba, abunda ke gabanta yafi karfi wannan iskancin na Sa"adatu. Allah shi ke batar da Tunaninmu wani Lokaci ga abu a kusa damu sai mu Dade bamu Fahimcesa ba..! ******** Danmaallam achan madina Ko Sarood sai da ta Tausayamai yadda ya kwallafa rai akan cikin Sakina sannan yazo kuma ya tafi Ranar da Mallam ya kirasa ya fadamai da Zazzabi ya kwana,kwanansa biyu agida baya Fita Tana kula dashi,Ita kanta ta Damu sosai sai ta sakamai kuka ganin ya Daina Cin abinci sosai ballatana yawan mgana,da taimakon Mallam da Hajiya da Aliyu ya Dawo daidai da kuma Sarood itama tayi kokarin matuka wajen kula da shi Sosai take basa Tausayi tana da sanyin Hali kamarsa da kuma Hakuri shi kanshi yanzu ya Fara Tunanin mafitan da Aliyu yaso ya Nema tun farko yaki yarda da mganarsa ammh a yanzu yafi Sarood Damuwa Tsausayi take basa ita macece mai Rauni sannan kuma yaji yana Fatan in bai samu Haihuwa ta bangaran Sakina ba,me zai hana ya roki Allah ya basa ta bangaron Sarood Amina dai bai ma saka ta a Lissafinsa ba bai Taba kawo mata Daukan cikinsa nan kusa ba..!..abunda bai sani ba Daman Sau tari Allah yafi bamu abun da muke nema a inda bamu taba Zato ko Tsammani ba..! Washegari yana cikin makaranta ya kira Aliyu da niyar ya Tuntubesa da mganar sai gashi shima ya fara mai mganar bayan sun gaisa Aliyu ke tambayansa matsalansa da Sarood ya ake ciki..? Yace mai har yanzu ba Sauki domin ko ya jaraba jiya iyau ne. Aliyu ya kada baki yace"Shehi ni dai kaki jin Shawarata ne..Naso ka kira mallam ka sanar dashi matsalanka kila ya samo maka waraka Tunda yafimu sanin abubuwan da suka Shafi addini da irin wannan banace ka yarda wani yayi maka ba kasa aranka bamai yi sai Allah kuma wajensa kake neman waraka..! Umar yayi shuru kamar bazai yi mgana ba Jin haka yasa Aliyu yace"Tunda Sakina ga matsalan da ake Samu Shehi me zai hana ka Jaraba Sarood din itama mu gani..! Nasan fa kana son ya"ya bama kai da abun nan yake Faruwa Dakai ba ni kaina abokinka i feel ur pain Umar ina Fatan kai ma ka ka ijiye masu yi maka addu"a watarana..! Danmallam ya gyada,kai kamar Aliyu na ganinsa kafin yace"Shikenan Aliyu zan jaraba shawarka..bari na Kira mallam muyi mgana..! Aliyu yaji Dadi suka rabu bayan ya Bisa da addu"an Allah yasa adace a samu waraka kamar yadda suke fata.. Nan take ya kira mallam sai dai baya gida yace mai yana Jigawa sun zo Taro ne nasu na Da"awa ammh bazai Dade ba zai koma gida in ya koma zai kirasa. Dayake abun na ransa kuma ya Kudiri niyar fadama mallam komai yasa bayan awanni kadan ya Sake kiran mallam din Lokacin har ya koma gida Misalin goma na Dare anan madina Nageria kuma suna fitowa sallar mangariba. Mallam Shashensa ya koma abunda ba Dabi"arsa ba sai sun gama Sallar Isha"a yake shiga gida ammh ganinsa da waya yasa aka san uziri ne ya taso ma mallam din.Tabbas Uzuri ne domin yadda yaga Umaru ya Damu yasa yasan ba lafiya ba wani abu na Faruwa. Bayan ya Dauka sun gaisa da Tambayan gida da iyalai kamar kullum mallam yace"Umaru meke Faruwa ne.? Wannan kiran naka bana Lafiya bane ko..? Danmallam ya kaskastan da kansa Waje ma ya fito saboda ba ya so Sarood taji mganarsu cikin Ladabi yace"Eh ba Lafiyan ba mallam matsala ne dani tuntuni nayi iya bakin kokarina ta bangarena ammh abu ya ci Tura shiyasa na yanke Shawaran kiran ka na Sanar Dakai..! Mallam ya koma ya zauna gefen gadonsa domin kurya ya shige kada ma wani abu ya katsesa a yadda yaji Umarun yasan da wani abu. Cikin Dattakonsa yace"Ina jinka..Allah yasa Zan iya maka mganin matsalan ka Umaru..! Cikin Kunya kamar yana ganinsa ya farama mallam bayanin Tundaga Farkon matsalan har karshe da Mganin Shafan Aljanun da siya mata Tayi amfani dashi ammh matsalan kuma bata kare ba har alokacin..! Mallam yayi shuru yana jinsa har ya gama kansa ya Daure na wani Lokaci,daya sa ya kasa mgana Har sai da Umar ya Kira sunansa sannan ya amsa Cikin Alhininsa yace"Ta bangaranka da ita Sakinar lafiya kalau ko..? Duk da yasanni ammh so yake ya Tabbatar in da lafiya ai in ba lafiya ba ta Dinga samun ciki hartana barinsa ba. Danmallam ya amsa da Eh cikin kunya aransa yana addu"an Allah yasa kada mallan ya sako Amina Har ga Allah bai shirya fadamai ya haikema wannan yarinyar ba duk da ba Haramci yayi ba matarsace ta sunna. Sai Addu"arsa ta karbu mallam bai Tsawaita tambayarsa ba illah kai da ya Jinjina kafin yace"Umaru kana jina ko..? Ka bani nan da zuwa gobe zan yi Bincike na acikin littafan malaman musulunci sosai sunyi bayanai game da ira iran wadanan matsalolin naka..Insha Allahu zuwa gobe zan kiraka da kaina nayi maka bayanin komai..! Danmallam yace"Shikenan mallam..Allah ya kara girma Allah ya kara nisan kwana..! Mallam ya amsa da Ameen Ameen ya Cike da fadin"Kada ka damu da Yardan Allah zamu samu mafita..Domin Qur"ani waraka ne gamu bayin sa kaji ko..? Ya amsa cikin yakinin kamar ma ya Samu mafitan daganan sukayi sallama Mallam ya koma yayi jugum yana nazarin matsalan Umar.. Tabbas yana da zurfin ciki sannan yaga Hakurin ita Saratun,bazai ce ga matsalan ba kai Tsaye tunda Basir ko Sanyi na Haifar da haka ammh nasu sai dai Raunin gaban namiji ba ta ki yin amfani ba gabadaya sannan shi da Sakina lafiya lau ita Saratun ne matsalan. Lalle akwai wata mgana a kasa shi ba Malamin Duba bane ko na Shirka shi malamin sunna ne da Qur"ani in an kawo matsala ba kansa Tsaye yake yi ba yana Duba Littafan addini na malamai da kuma Qur"ani Domin neman mafita sannan akwai Irin irin matsalolin nan na Sihiri da malamai Dabam dabam sukayi littafai da Dadama Domin warware ma Mutane kai dasamun Mafita shima haka zai yi bazai yi zargin wani abu kai Tsaye ba sai ya bincika. Ana Idar da sallar isha"i ya Sake dawowa cikin gida yau ko Aba basu Tsawaita Hira ba sukayi sallama ya wuce Shashensa Ranar hajiya ke da Turaka ko da tazo ta iske malama nata Nazarin wasu littafai sama sama ma suka gaisa abinci ma sai da ta matsamai yaci kadan Abun bai bata mamaki ba taga ko barci bai kwanta ba tasan sa da son nazari wani Lokacin ammh bai hanasa kwanciya ammh sai gashi ya kasa barci data tambayasa yace yana wani Nazari mai muhimmaci ne,tayi kwanciyarta in ya gama zai zo ya sameta Dole ta shiga ta kwanta ta kyalesa. Shi kuma sai wajen biyu na Dare ya gama Bincikensa sannan bai kwanta ba ya Dauro alwala yayi nafilfilu da addu"o'i sannan ya kwanta wajen uku da Rabi Biyar na cika ya Farka ya Tada Hajiya ya fice zuwa masallaci. Sai Chan Safe ya Dawo Shashensa ya Tsaya masallaci sun yi meeting da Dattajan anguwannin kusa dasu. Wanka kawai yayi ya karya Lokacin Hajiya ta koma bangaranta ya Kira Umar bai Dauka ba sai da ta katse sannan ya Kirasa yana aji ne yana karatu yana ganin kiran maallam ya nemi lamini ya fita waje ya kirasa. Bayan gaisa kamar yadda suka saba Mallam ya fara mgana cikin Dattakonsa kamar haka. "Umaru ka yarda da Allah shine mai yi kuma mai hanawa..Sannan ka yarda da duk abunda ya samu bawa Daga garesa ne sannan kowata Lalura daga garesa ne sannan Waraka ma yana wajensa ko..? Danmallam ya amsa da eh Mallam ya Cigaba da nuna mai Duk abunda zai Faru da bawa koma ya faru kada ya Zargin kowa ya Dauka Daga Allah ne kuma garesa zai nemi waraka bai Fito ya mai bayanin Sihiri bane ammh Cikin Dattakonsa yace"Ka san Acikin Qur"ani akwai ayoyin da Allah ya Fadamana suna karya sihiri ko asiri ko .? Ai kasan su..? Cikin Sanyinsa yace"Eh mallam..! Maalllam yace"karantomin su naji..! Umar ya gyara Tsayuwa ya fara fadin"SURORIN AL'QUR'ANI GUDA SHIDA DAKE KARYA SIHIR KO ASIRI. 1. SURATUL TAUBA: AYATA 14. 2.SURATUL YUNUS :AYATA 57. 3.SURATUL NAHIL: AYATA 69. 4.SURATUL ISRA"I :AYATA 82. 5.SURATUL SHU'ARA :AYATA 78_82 6.SURATUL FUSILAT: AYATA 44. mallam ya jinjina kai kafin yace"Dakyau..To kamar yadda ka lissafasu ka samu ruwan zamzam ka karantasu duka ka tofe aciki ka rika Shafe al"auranka duk dare in zaka kwanta da jikinka gabadaya sannan ka rike addu"a da azkar domin koma menene Yana jikin ka ne ba jikin ita Saratun ba..! Danmallam ya jinjina kai yana Fadin"zanyi haka insha Allahu nagode mallam Allah ya kara girma..! Mallam ya amsa da Ameen yana fadin"Allah ya warware mana..Allah yasa adace Allah yasa asamu waraka..! Daga haka sukayi sallama Danmallam Ya Dade tsaye kafin ya koma cikin ajin sa ya cigaba da koyarwa karkashin Ransa kuma yana gasgasta mganar Aliyu koda mallam bai fito yace sihiri bane ammh Yanayin addu"o"in da ya basa na karya duk wani Sihiri ne ko asiri. Yana fitowa da ga ajin ya koma Office ya Kira Aliyu ya fadamai yadda sukayi da maallam Aliyu ya rike baki kafin yace"Kaji mganata ko..? To ka gaggauta fara abunda yace maka Fatan nasara Allah y bamu waraka..! Daga haka suka rabu Daga cikin makaranta gida ya wuce daman yanaa da Ruwan zamzam din Sarood bata nan tana makaranta sannan in ta Dawo Zata biya gida Mami Sara na Fama da Zazzabi. Alokacin ya samu Lokaci yayi Duk abunda mallam ya Umarcesa ya Tofesu acikin Ruwan zamzam din a kuma wannan Daran ya Fara amfani Dashi da yakinin Ciwonsa Daga Allah ne kuma waraka na wajensa..! Sannu sannu dai..Bata hana zuwa sai dai a Dade ba"a je ba..! Daga yanzu aikin nasu ya fara Lalacewa Alalan geronsu ya riga yayi Ruwan da bazasu taba iya Dauresa ba koda kuwa sun mai Cikon Gari acikinsa..! ***** Sati dayan da Malam ya Dibar ma Anty Amarya na cika ya Kirata a waya Daman kiransa take jira tana Lissafe da Ranakun. Sai dai yana fara bayanin Idanuwanta suka Rufe Daga sanda yace Wace ke Lalata Cikin Sakina tana cikin matan mallam sannan tafi kusa da Hajiya da kowa acikinsu sannan bama Take lalalata Cikin ba ko yau sakina ta kara Samun ciki bazai taba zama a mahaifanta ba akwai abunda aka bata Tacin ma cikinta wanda yake hana Cikin zama acikin maranta. ! Anty Amarya na Tsaye ne acikin Dakin su Sa"adatu in da su Sakina suke bata gama Sauraran mganar mallam ba ta yi wurigi da wayar sakina ta Tsorata tabi ta kallo ganin yadda ta fita a fusace. Haj.Uwani na gaban madubin bedromm dinta tana Saka dan kunne a kunnenta Kamar Daga sama taji an bango kofar lokaci Daya da shigowa Cikin mamaki ta juyo tana kallon ikon Allah.. Idonta fes a na Anty Amarya wacce ke kallonta Cikin Jajayen idanuwanta da suka rine da bacin rai da wani Bakinciki. Haj.Uwani Cikin mamaki tace"A"a Amarya Lafiya kika shigomin har Cikin kuryan Daki ba sallama..? Kawai sai Anty Amarya ta Nufeta ta Shako wuyanta idanuwanta sun firfoto waje cikin Karaji take fadin"Ke baki chanchanci sallaama ba..Baka mai bakar aniya muguwa azzaluma mai fuska Biyu da izinin Lahi Uwani sai kin ga sakamokon ki Tun aduniya muguwa macuciya azzaluma kaawai..! Haj.Uwani ta Fincike Wuyanta Cikin Wata irin kallo take bin Anty Amarya da shi kafin ta kece da wata irin Dariya tace"Azzalumai bakake masu bakar Aniya zaki ce Marliya sannan ki rika saka min jaye..Bazamu gama da Duniya Lafiya ba DA NI DA KE..tunda duk jirgi Daya ya kwasomu..! Tafada tana dariya lokaci Daya tana mata kallon Nasan ki, ni tuntuni ke kuma sai yanzu kika sanni..? *Janafty* *TFZB2013* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Anty Amarya ta dago tana kallonta cikin rawar baki dana jiki tace"Ban..ga ne ba..? Me kike nufi Uwani..? Haj.Uwani ta saki wani kayattacen Mirmishi mai hade da cin nasara tana kallon cikin Idanuwan Anty Amarya wacce ta fara tsorata da Lamarin Uwanin tace"Kina sane da abunda nake nufi marliya ko na kira ki da Madina ne..? Tafada cikin tsaida kallonta kan Anty Amarya wacce ta zaro ido jin Sunan da Uwani ta Kirata dashi Sunan da mutanen da suka santa dashi ba su da yawa suna ne da ta saka ma kanta Tun tuni domin cikar wani Buri nata. Haj.Uwani ta fara taku acikin Dakinta tana Zagaye Anty Amarya tana Sakin Dariya kasa kasa kafin ta nufi kofar Bedroom dinta ta kulle ta harda Murza key ta juyo tana Fadin"Komai na Bukatar sirri madina duk da bansan da wacce kike zo ba..? Anty Amarya da tagama Tsorata da mganganun Dake bakin Hj.Uwani baisa ta yi saurin karaya ba yasa cikin Gyara Tsayuwarta tace"Kina sane da duk abunda nazo dashi Uwani..Tunda ke kike aikata shi..Kashe rai fa kike yi fa Uwani..? Kina lalata duk cikin da Sakina take samu yanzu in wannan mganar ta fita kina Zaton zaki kara Minti Daya acikin gidan nan ne..? Tafada tana kallon Haj Uwani wacce ba karaya ko nadama ko kaadan a Tare da ita sai ma Zama da tayi gefen gadonta ta Dora kafa Daya kan Daya tabi Anty Amarya da kallo kafin tace"Ranar Biyan Bukata rai ba abakin komai yake ba Marliya a wajen ki na koyi wannan Tsarin sannan Da kike mganar in Labarin nan ya fita bazan kara ko minti Daya agidan nan ba..? To wayace miki zai fita yanzu..?. Ai ko zai fita sai na gama cika Burina Likacin na zama giwar mata ko mallam babu yadda ya iya dani marliya ballatana Hajiya da ban Dauketa wata Tsiya ba..Atafin Hannuna take kinsani..! Bama ita ba gabadayanku a nan dina kuke ba wacce bansan duka motsinta ba..! Ta karishe Fada tana Nunatafin hannunta cikin gadara Anty Amarya tayi wani mirmishin takaici kafin tace"Aiko kunyi kuskure Uwani..Wlh yadda kika yi sanadiyar Salwartar da Cikin Sakina sai nayi Sanadiyar da asirunki ya Tonu yau a idon Duniya..Yanzu ba sai anjuma ba, zan je na Sanar ma Hajiya komai domin ta gano Muguwar bakar Fusarki..! Tafada a fusace kafin ta juya zata fita ta tsinkayi muryan Haj.Uwani Cikin Gadara. "Bani kadai zaki tona ma asiri ba marliya Har da ke karan kanki..da wacce ta hada hannu Dake kuka KASHE YAYA..sannan kuma baya zatayi Zani marliya harta Danmallan zai gano cewa ba da Ra"ayinsa ya auri Sakina ba ke kika shiga kika fita hakan ta kasance..! Da wani irin mamaki da al"ajabi da Faduwar gaba Anty Amarya taci Burki ta kasa juyowa ta Fuskanci Hj.Uwani Domin tana faman kokuwa da Faduwar gabanta na yadda Uwani ta san wannan Boyayiyun sirrukan da ga ita sai balaraba sai Malaminsu suka san anyi haka sai gashi a bakin Uwani to garin ya akayi ta san duka sirrukan su haka su basu taba sani ba..? Tana wannan Tunanin taji Muryan Uwani a saitin kunnenta tana fadin"Kin yi mamakin ya akayi nasan Duka wadanan sirrukan naki ko nace naki keda Balaraba ko..? Anty Amarya ta kasa gaba ballatana baya ba inda jikinta baya rawa Haj.Uwani ta saki Dariyan nasara kafin ta fara Tafiya zuwa gaban madubin Dake Dakinta tana Fadin"Nayi mamakin da sai a yanzu malaminki ya gano miki ni marliya ai na Dade ina shirina kusan ma nace na Rigaki shirya komai..Ni tuni Mama ta Bincikomin komai naki da ke da wacce ke tayaki dukkan ku wani motsinku ko sirrinku yana Cikin Tafin Hanuna Marliya abunda baku sani ba Kuna aikin ne ni ina warware muku..Kamar yadda Sakina ke barin Cikinta haka in wannan balarabiyar ta samu ciki ita ma haka zatayi ta barinsa hakama Amina ita kanta ban kyaleta ba na shigo da ita cikin Tsarina..Tsarin da zai kai ni nan da Lokaci kadan na cika Burina..! Sai alokacin Anty Amarya ta Juyo tana kallon bayan Haj.Uwani Cikin Rawan baki tace"Wani irin Buri ne wannan da kika Zabi ni ki hanani Cikar nawa burin. A bar batun Rufa Rufa Uwani Tunda kinsan komai ba amfani na cigaba da Boye miki manufata ni in kinyi Hakuri ba mallam nake so na mallaka ba..Kawai Sakina nake so ta Zama Mowar mata wajen umar da Danginsa..Sannan ita kadai ce nayi ma alkawarin zata haifa ma Umar magaji ta kuma Haifa ma Hajiya da mallam jika mafi soyuwa bayan ita ban yarda wata tazo Daga baya ta fita ba..Sannan in hakan ta faru nasan nima zam zama Shalele a wajen mallam da Umaru tunda nice silar duk abubuwan da suka faru..! Ki fadamin meye naki burin da yasa ni kika ki bari nawa burin ya cika..? Ina so naji irin naki Burin akan mallam da zur"arsa..? Haj. Uwani ta juyo tana kallon Anty Amarya ido na cikin Ido kafin tace"Ko baki tambayeni ba zan fada miki..Boye boye ai ya kare. tunda malamin ki ya gano miki ni Marliya..Karkade kunnuwanki Ki sha Labari yanzu zan sanar Dake yadda naki Cikar Burin ke neman yayi min Cikas kan nawa Burin da nayi shekaru ina Wahala akansa..! Komawa tayi ta zauna ta kara Dora kafa Daya kan daya kafin ta fara Fadama Anty Amarya duka shirinta da nata tsarin da Burin datake dashi akan mallam da ahalinsa ta karishe da Fadin"In har na bar Sakina ta Haihu Da Umar kin batamin Tsarina marliya..shiyasa na hana faruwar haka sannan bama ita ba indai ina Raye Umar bazai ga kwansa a Duniya ba..Tunda na gano Mallam yana matukar son yaga jikokinsa ta bangaran sa na mike tsaye na shiga na Fita na hana faruwar hakan..Ya"yana kadai ne zasu haifama mallam jikoki kuma ya sosu ni kadai ce zan zama Tauraruwa ba Hajiya ba..In ta samu mallam a baya awannan gabar Lokacinta ya kusa karewa..! Nasan zaki ce ina Nazir da Nasir da na bari suka haihu.? Ai suma din ba gazawata bane Marliya Tsarin aikina ne..Daga ya"yan Nazir din har Nasir din wa kika gani mallam ya Damu dasu? Ai nasa mama ta Dakushe wannan Tasirin har Abada kuma bazasu yi shi a idanuwansa ba Nazeem ne kadai da Uzairu zasu haifa masa jikoki su zama Sanyin Idanuwan mallam bayan su kuma nayi alkawarin har Abada ba wanda zai haihafama mallam Jika Tun balle ma Danmallam da mallam ya fi so cikin ya'yansa shiyasa kika ga inayin Duk abunda nake so..! Niso nake nan gaba ya"yana su zama sune Hop din mallam gabadaya Sune komai nasa bashi da yarda zai yi sannan kuma alokacin ni zama giwar a cikin matansa ko yana so ko baya so..Ya'ya ne kan gaba a dukiyarsa sannan wajen haifa masa jikoki ma sune kan gaba Dole kauna da soyayya ta koma kaina da Ahalina gabadaya..Mganar Sa"idu bai gabana domin ke da Balaraba kun Rage min wannan aikin..Lokaci kadan nake jira na Aiwatar da Tsarina akansa kamar yadda na Tsara..! Ta karishe Fada tana kallon Anty Amarya wacce tayi mutuwar tsaye ta kasa ko motsi da jin wannan labarin lalle Haj.Uwani ta fi su zama Shedaniya,Su ashe bakomai ma sukeyi ba,Shekaruna nawa ta kwashe tana Wahala ammh Lokaci kadan Uwani tana neman Tsawartata to bazata bari ba,Bazata yi Saurin karaya ba,sai ta nuna mata in ita a Tsaye take ita a tafe ta kwana..! Ta kalli Uwani cikin Bakinciki kafin tace"meyasa Burinki ya yi kamanceceniya da nawa .? Meyasa sai dole kin Tsawartsani Uwani meyasa haka..? Haj.Uwani tayi kasa da Murya kafin tace"Ki yi kasa da muryanki mana marliya..Ai na riga na Fada miki Dalilina..Bake kadai na taba ba..Na Fada miki yadda na Raba Hajiya da ya"yanta a kusa da ita,Na maida Nasir mara amfani a wajen maallam na hanata ganin jikanta ta Tsatson babbar Danta ita meyasa batace ina so na Tsawartata ba sai ke da Duka Dagani har ke muna kan Turba Daya ne marliya..? Anty Amarya na Huci tace"To baki isa ba..wlh uwani karyan ki ta sha karya..! Haj.Uwani tayi Dariya kafin tace"Nama isa ai marliya..Kaawai ki yi Hakuri ki mara min baya Burina ya Cika in hakan ta faru nayi miki alkwarin Raba komai gida uku na Dauki Biyu na baki kashi Daya. ! Anty Amarya ta harareta kamar Idanuwanta zasu fado tace"Me kike nufi..? Haj.Uwani tayi Dariya kafin tace"Ki hakura da Sai Sakina ta Haihu marliya..! Anty Amarya ta Zumduma ashar kafin tace"Ina..Baki isa ba Uwani..Bazaki Hada baki dani ba..Kowa ya Tsaya da kafafunsa..Sannan kuma sai dai ki kare a muguntarki kina ji kina gani Sakina zata haifarma mallam da Hajiya jika sai dai bakin ciki ya kasheki. ! Tafada tana kumfar Baki Haj.Uwani ta tabe baki kafin ta Daga kaafadanta tace"Shikenan marliya..Kije ki cigaba da Wahala..Ammh ina mai kara gayamiki..in sau Dubu sakina zata samu Ciki sai ya Zube haka Sarood hakama Amina ke ko aure ya kara itana irin Tsarin dana Dora su itama akan shi Zan dora ta Marliya na Fada miki kan Cikar Burina zan iya aikata komai..! Anty Amarya taji wani abu ya Tsaya mata a wuya kawai sai tayi kukan kura ta kara shako Haj.Uwani cikin Hargagi take fadin"Me kika baa sakina tasha..? Ki Fadamin abunda kika Binne da kudin da kika kashe akan hana Sakina Haihuwa Uwani..? Kwace wuyanta tayi tana Hararan Anty Amarya Lokaci daya tana Fadin"Wlh in kika kara saka hannunki kika rikeni sai na Sharara miki mari marliya..! Ki kama kanki kafin Zuciya tajaki ki aikata abunda zaki zo kina Nadama..! Anty Amarya na Haki ta nuna Haj.Uwanu tana fadin"Wlh kin yi kadan..Nayi alkawarin sai nayi sillar Tona miki asiri..! Haj Uwani tace"To ai ban Hanaki ba..tunda baki min godiyar Taimakon ki da nayi ba akan Amina da Sarood ba, wato sakina kadai kike so ta Haihu ban da su ko..? To tunda baki ga Hallacin da nayi miki ba Shikenan jeki fadama wanda zaki Fadamawa ammh ki sani in asirin ya tashi Tonuwa naki sai yafi muni Marliya ni iya ka dai mallam ya Sakeni ko..? To in ya sakeni ai bai kare ba ina da Zaratan maza har uku ko da sun ji abunda ya faru basu isa su sauya ni a matsayin uwa ba marliya,Sannan kuma dole zasu neme ni kefa wa kike dashi..? Duka ya"yan ki mata ne baki da wani gata anan duniya iyayanki zasu yi Tir Dake ya"yan ki mata zaki bar musu abun kunya in ma bai taba auransu ba,Sannan Uwa uba kuma agaban idon ki Umar zai Saki Sakina kinga Daganan kin kare a Tutar babu..Wahalar ki tatashi a banza kenan kuma ke ahakan ma naki Tonuwar asirin mai kyau ne,akan na Balaraba ita wlh ko kaffara bazan yi ba kare sai ya fita Daraja in sirrin Boye ya fito Fili sai ta wulakanta ta Tozarta a wajen Sa"idu da Danginsa da kuma ya"yan Yaya da kukayi Sanadiyar barinta Duniya Saboda cikar naku burin..! In kin yarda da duka Faruwar wannan shikenan u can go..Ki je ki Fadama Hajiya sai mu shirya bankadewar siirikan namu dani da ke da balaraba alokaci Daya ko banza na San Dagani har ke bamu samu cikar Burukan namu ba..! Tafada tana wata yar Dariya Anty Amarya duk yadda taso kada ta nuna Rauninta sai da ta nuna Hawaye ya wanke mata Fuska ta nuna Haj.Uwani da yatsanta Cikin Kaushim murya mai Cike da karkawa tace"Ki Rubuta ki ijiye Uwani Indai ban samu abunda nake so ba..Na rantse ko Zan yi yawo Tsirara sai naga kema baki samu abunda kike so ba..In juran ki sammako ni madina a tafe na kwana mu Zuba mu gani..! haj.Uwani ta bata amsa da cewa"Shege ka fasa marliya..! Daga haka Anty Amarya ta murza key din ta Bude kofar ta Fice tana kuka Duk yadda taso ta shanye kukanta ta kasa bakinciki da Takaicin sun taimaka wajen Fitar Da ita daga natsuwarta uwa uba kuma da yadda Gabadaya sirrukansu yake tafin Hannun Haj.Uwani Hajiya ta fito kenan Daga Shashenta zata shashen Haj.Uwani suyi mganar wani Turaran wuta da suka je Bikin nan maiduguri tace tana so yagana ta kirata kan mganar ne yasa tace bari ta shiga ta fadamata.. Ta sawo kanta Falon kenan Anty Amarya na fita da gudu tana kuka Hajiya sai ta Rude hankalinta ya tashi ta rika fadin"Subhanallah Amarya Lafiyanki kuwa..? Ina ko jinta batayi ba batama ganta ba Domin kuncin datake ciki ya Rufe mata jinta da ganinta har ta fice Hajiya na Kallonta sai jikinta ya kama rawa tana Fatan Allah yasa ba wani abun ne ya Faru da Sakina ba kamar ta bi bayanta sai kuma ta fasa ta karisa Cikin Falon Haj.Uwani tana Fatan taji abunda ya faru Daga bakinta. Ita kuma Haj.Uwani Anty Amarya na fita ta yi shewa ta kara Sakin shewa kafin tace"Mu zuba mu gani marliya..Karki fara ja da Uwani Domin ni walkiya ce ban Fito ba sai da na shirya..! Haka take ta fada tana Dariya tasan Daman zatayi mamakin yadda tasan komai nasu Mama hatsabibiyar Bokanyance Dake Niger ita take Sanar da ita duka aikin marliya ita da Balaraba ita kanta da Farko ta Razana da jin sunan mamanmu domin bata taba Zaton matar mugun halinta yakai haka ba, sai dai batayi mamaki ba Sanin yadda Idon kowa yake Rufewa kan neman Duniya..sannan Ta kara jinjina ma wannan kalmar na rai ba abakin komai yake ba wajen Biyan Bukata Tunda Balaraba ta saka aka kashe yaya Matar data Zauna da ita Tsakani ga Allah ta bar mata gidanta da ya"yanta kawai saboda Cikar Burinta na mallakan sa"idu..! Tana wannan Tunanin kamar Daga Sama taji muryan Hajiya tana Sallama sai ta Rude ta mike da Sauri ta fito Tana kokarin Daidaita yanayinta Hajiya dake tsaye Tsakiyar Falon Uwani ko Zama ta kasa ta kalli Uwanin Yadda ta fito tana abu kamar wani abu dai ya faru yasa da Sauri tace"Wai ni Uwani me ya faru ne acikin gidan nan bansani ba..? Naga Amarya ta fita Daga shashen ki da Gudu tana kuka ina ta mgana bata jini ba kema mayi sallama kin Fito kamar kina ma a firgice ne Hankalina ya tashi muke Faruwa..? Haj Uwani na jin haka kawai sai ta Zube saman Cafet din Falonta ta Fashe da kuka yi take yi ba Saurarawa ta kara Tadama Hajiya da Hankali Cikin Rudewa tace"Ko Cikin yaran mu ne wata ta rasu kuke Boyemin..? Hajiya Uwani na jan majina da Hanci tace"Ai gwara ma Mutuwa da wannan Zargin da Amarya ke jifana dashi Hajiya..! Hajiya tace"Wani Zargi kuma Uwani..? Haj.Uwani na kara saka kuka tace"Hajiya wai ni Amarya tazo ta sama tamin zagin kare Dangi da Zargina wai ni nake asiri ina Zubar ma Sakina da cikinta..Fitar nan da kika ga tayi ni tazo ta kare ma Tanadi Hajiya..! Hajiya ta Zaro ido kafin ta saka Salati ganin haka yasa Haj.Uwani ta karkace baki ta Cigaba da fadin"wai malaminta ya mata Duba yace ci kin matan mallam ne..kawai hajiya sai tace ni ce..Nan tazo ina ta mata Rantsuwa taki yarda dani ina Fadamata kada tayi saurin yarda da irin mallaman nan na karya masu Hada Fada bata Saurareni ba Hajiya haka ta fita tana kukan da Ikirarin sai ta ga Baya na..! Hajiya nan da kika gani daman wajenki Zani Na fada miki abunda ke Faruwa naji Ciwon wannan abun sannan na Fadamiki bazan kyale Amarya ba sai ta san tayi min kazafi..! Ta karishe Fada tana kuka Wurjajan..hajiya kuwa sai Faman Salati take yi kafin tace"Kinga Uwani bar kuka..wannan mganar ba tawa bace..Bari naje na kira mallam na Sanar dashi abunda ke faruwa wannan mganar tayi muni da yawa Uwani..! Haj.Uwani na jan majina tace"Ko kin gayamai Hajiya ni bazan yafe ba..Sai an Bimin Hakkina akan kazafin da Amarya tamin..! Hajiya bata Saurareta ba ta Fice tana Jimamin wannnan abun aranta tana Jin Haushin Anty Amarya bata taba Zarginta da shiga malamai ba ammh jin abunda ta aikata sai taji duk ta Zube mata ina amfanin wannan aikin..?ta Biyema mallaman karya suna neman hada fada acikin gida. Hajiya na fita Haj Uwani ta mike ta Share Hawayenta ta yi Dariya kafin tace"Marliya tun a yau zaki san kin Hada Hanya da Uwani Diyar Hamza Tsafe..! Ta fada tana Dariya har ta Hango yadda Marliya zata gane bata da wayau a falon mallam Dakin da Umaima take ta leka barci take yi Domin yanzu ko Makarantar Haddar ta Daina zuwa saboda Ciwon nata ya tashi gadangadan ana ta dai fama da mgunguna ne. Hajiya ko na fita Bedroom dinta ta shige nan ta bar Hanne da Hamida afalo suna rike da Littafansu bata ma Bi ta kansu ba ta Shige Daki wayarta ta Dauko ta Kira mallam bai yi nisa ba yana gidan mai anguwa ya Kirasa kan Cases din Filin wasu marayu da aka kawo mai mganar to daman mai anguwa in wani abu irin haka ya Faru na bangaran addini yana kiran mallam Domin su Tattauna. Yana jin Hajiya tace yazo gida ba Lafiya yace mata suna ma kan Hanya. Lokacin ana gabda kiran Sallar La"asar ne yasa suna Dawowa yace bari ya Tsaya yayi sallah kafin ya shiga Cikin gidan Hajiya ta fito ranta a jagule sai yanzu ma ta lura bata ga Amina ba Tunda dazu da suka Dawo daga makaranta,yasa ta kalli Hanne da Hamida dake ta yin aikin da malamin Lissafinsu ya basu a makaranta tace"Ina Mamah yau. ? Hanne tace"Tana gidan baba Sa"idu dazu da muka shiga gaida mamanmu ta kwanta sai ta fara barci mu kuma da Zamu tahilo bamu tashe ta ba..! Hajiya bata ce komai ba ta kada kai kafin tace"ku tashi kuyi sallah Lokaci yayi..! Daga haka ta koma Cikin Bedroom dinta Ammh aranta sai da tayi Tunanin barcin Amina yayi yawa kamar kasa yanzu ko da asuba fa Dakyar ake tashinta wani Lokacin da Daddare kafin takwas Amina ta kwanta sannan in suka Dawo makaranta sai tayi barci ammh sai bata kawo wani Tunani ba tafi Barinsa a Saboda Basa Zama a zirga Zirgan makaranta da Sauransu. Hajiya ta idar da Sallah kenan Kiran mallam ya shigo mata yace gashi ya shigo Gidan Hajiya batayi kasa agwiwa ba ta saka lullubinta ta Biya Shashem Hajiya Uwani Dake zaman jiran Kiran mallam suka tafi Falon mallam suna zuwa Hajiya tace ta fara gayama Mallam yadda taga Anty Amarya sannan tace Uwani ta maimata abunda ta Fadaamata Haj.Uwani ta gyara Zama ta Fara Rattafama mallam yadda ta Fadama Hajiya ta karishe cikin kuka tana Fadin"Mallam abu dayane in na Tuna yake min ciwo..Da Amarya ta Zargeni da laifin kisa Mallam..? Ashe haka ta Tsaneni bansani ba..Ta rasa kazafin da Zatamin sai kazafin kashe gudun jini Tun kafin ya Fito Duniya..? Wannan in gaban yan Sanda za"a kai ai babban cases ne mallam..! Mallam da ransa ya gama baci ko mgana bai yi ba ya Daga wayarsa ya kira Anty Amarya wacce ke cikin Bedroom dinta tunda ta Dawo Daga Shashen Uwani ta shige ta rufe kanta tana kuka kukan rashin mafita da madafa kukan takaici da gazawa a karo na farko ko sallah bata tashi tayi ba sai ga Kiran Mallam sai da gabanta ya Fadi balle Dayace tazo ta same sa afalonsa a kausashe. Ai bata gama Sarewa ba sai da Sawo Hijabinta Fuskarta duk ta kode ta iso Falon mallam ganin Hajiya da Haj Uwani sai da yasa gabanta ya Fadi Jikinta ya fara rawa ta Tsaya Cak ta kasa gaba ballatana baya. Mallam cikin kaushinsa yace ta kariso ita ake jira,Jiki a sanyaye ta kariso ta Zauna gefen kafar Hajiya a kasa tana kallon Uwani dake mata Dariya a kasa kasa Daganan tasan wani makircin ta kulla mata.. Kanta ya Daure sanda Mallam yake karanta mata abunda Uwani tace ya Kalletaa Cikin bacin rai yana Fadin"Marliya ashe ban Dade ina muku nasihan yarda da malaman tsubbu ba..? Shine kika kai kanki bayan kin yarda dashi shine ya karanto miki karya kika zo kika Hadamin Fada acikin Ahalina alhalin na Dade ina gargadinku..? Anty Amarya ta Tsure hankalinta ya tashi ta kalli Haj.Uwani dake matsan kwallar karya ta maida kallonta kan mallam taga yana mata wani kallo Sai kuka ya taso mata ta Fashe da kuka Tana fadin"Wlh ma..! "Karki ce tak a nan wajen marliya..Baki da abunda zaki fadamin bana Kiraki Domin kimin karin bayani bane..na kiraki ne naja miki kunne Wlh Tallahi in na karajin mgana makammancin wannan sai na Saba miki in ma ban yanke Igiyan auran dake tsakanina Dake ba. domin ina kyamatar Zama Dake Marliya tunda kin zama Mushuruka mai bin malamai da yan Tsubbu makiya Allah..! Anty Amarya ta tsorata ta Duka gaban Hajiya ganin yadda mallam yake mgana tasan ransa ya baci Uwani tayi nasara akanta tace"Hajiya don Allah ki bama mallam Hakuri ba Laifina bane kuskure ne..da sharrin Shedan..! Sai kuma ta rike kafan Hajiya tana gunjun kuka Hajiya taji Tsausayinta ta Duka ta riketa tana fadin"Tashi ki Zauna marliya..! Komawa tayi ta zauna tana kallon Haj.uwani Dake matsar kwallah tana mata Dariya ba wanda ya Lura Hajiya ta kalli mallam kafin tace"Mallan kayi hakuri don Allah..Tace Sharrin shedan ne ayi mata uzuri..! Kema Amarya ki gyara wlh bazan Boye miki ba kimarki ta Zube awajena tunda naji kina daga Cikin masu Bin malaman karyan nan ammh Tunda kin bata Hakuri ya wuce..Mallam kai ma kamata Hakuri..!mallan cikin bacin rai yace"Bani zata bama Hakuri ba Uwani gatanan baiwar Allah da ta zargeta tana zaman zamanta zata bama Hakuri in kuma wlh bata yafe mata ba sai Allah ya kamata ! Yafada cikin nuna bacin ransa lokaci Daya yana Kauda kai baya son kallon Anty Amarya Hajiya ta juya tana kallon Anty Amarya tun kafin ma tayi mgana ta Zube gaban Uwani tana Fadin"Kiyi..hakuri sharrin shedan ne ki yafemin..! Haj.Uwani ta share Hawayenta kafin tace"Shikensn tunda Hajiya da mallam sun saka baki..Ammh wlh da naso ne sai na kai mganar nan gaba..Ammh Tunda kin bada Hakuri ya wuce sai ki kiyaye ki daina yarda da mganar makaryatan malama nan makiya Allah da addininsa..! Hajiya tace"Tabbas Allah ya Karemu gabadaya..! Haj.Uwani ta amsa da Ameen da karfi mallam ya mike yana Fadin"Sannan mgana ta karshe bayan mu Hudun nan kada naji wannan mganar abakin wani..Na kasheta Daga yau..! Daga haka ko mgana bai kara ba ya shige ciki bakincikinsa Daya yana tafe wa"azi akan mata masu Bin malamai ammh yau agidansa ma ake yi wannan aikin..? Tayaya ransa bazai baci ba..? Hajiya kuwa sai da ta kara yima Anty Amarya Nasiha sosai da nuna mata illah rashin yarda da Allah da kaddaran da Illah barin Shedan ya saka mutum wasi wasi da kuma illar Bin malaman karya na Tsubbu. Sannan ta sallame su Anty Amarya ta Mike kamar tana kan kaya ta Fice Haj.Uwani sai daga baya ta fito Hajiya kuma ta bi mallam ciki ta Rarrasosa..! Haj Uwani har takai shashenta tana Dariya Allah Allah take yi ta Kira Batula ta labatar mata abunda ya faru yau sai ta Kira ta bata Dauka ba Shiyasa ta bari sai an juma ta Sake nemanta kan kujera ta kame a falonta ta Dora kafa Daya kan Daya tana Mirmishin jin Dadi da Nishadi ko banza yau ta bama Marliya Daya daga Cikin Tsoronta..! Anty Amarya kuwa haka ta shiga Shashenta bata gani tana jin Sakina da Sa"adatu na kiran sunanta da suke Falo bata bi ta kansu ba ta shiga Daki ta Bame kofa da key jikinta na Rawa da Hannunta ta Dauki wayarta Dake kan madubi ta Dokama Balaraba kira. Mamanmu na cikin bedroom dinta bata Dade da tashi daga barci ba tayi sallah tana Zaune tana Tunanin irin girkin da zata Tsarama Aba da Daddaran nan Tunaninta ba kowa agidan Jawaad na Haraban gida yana Kwallo Su Hamida basa nan suna gidan mallam Domin bata Dauka Amina bata bisu ba dataji Fitansu ta Dauka gabadaya suka fita..shiyasa bata Damu data leka Dakin su Aminar ba da ba kowa acikinsa yanzu sannan Dazu da ta fita alwala taga kofar Dakin a Sakaye abunda bata sani ba Iska ne ta Dan Tura kofar Dakin Amina na ciki tana barci. Wayarta Dake gefenta ne ya katse mata tunani ita azaton ta Aba ne Domin yanzu ko yana wajen aiki haka suke cikin waya yana tambayanta ko ba wata matsala sai taga Madina ne ke kiran Wani katon Tsaki ta saki kafin tace"Kai madina bazata barni na Huta ba..ya kamata ta Hakura tunda ita dai kamar bata da sa"a ne..matsaww...! Sai da ta Daidaita kanta sannan ta Daga Kiran tana fadin lafiya"Madina Allah yasa lafiya kira da bayan la"asar haka..? Anty Amarya cikin kuka tace"Dayyaba mun kade mun gama yawo..Ashe duk abunda muke ciki siirinmu yana Bankadane bamu sani ba..Tabbas muna Shuka a idon makwarwa Dayyaba. ! Mamanmu ta ce cikin mamaki"Bangane ba madina..? Waye yasan sirrinmu..? Anty Amarya tace"Hajiya UWANI 'ce Dayyaba..A tsirara take kallonmu Duka Sirrukanmu dani Dake yana Tafin Hannunta ne. ! Mamanmu ta mike Dafe da Kirji Tana Fadin"Mun shiga uku Madina wani irin labari kike son ki Fadamin..? Anty Amarya ta share hawayenta tana Fadin"Ai bama uku muka shiga ba goma ne Dayyaba..! Nan ta fara gayamata komai da komai Tunda daga farko da zuwar da tayi ta Samu Haj Uwami da yadda suka kare da Sharrin data kulla mata ta karishe da Fadin" Kinga yadda take kuka afalon mallam kyce ta Allah ce Dayyaba..Wlh Uwani ta shirya yin Fito na fito damu kuma in muka yi wasa..Tana gabda Kware mana Zani a Tsakiyar kasuwa..! Mamanmu ta Mike Cikin wata irin Murya tace"Karya take yi madina..Uwani bata isa ba..In juranta Sammako mu mun Dade atafe..Bata isa ta zo ta lalatamana Aikin da mukayi wahala mukayi shekaru muna Wahala ba Haba Madina Hajiya Uwani muguwar matace bata da mutunci kuma bata da imani Tsakani ga Allah yadda Hajiya ta yarda da ita sai da ta Cutar da ita..? Sannan ina laifin in ta Hana Amina Haihuwa ko zama da Umar daman haka muke so auran yadda yake gantale ya kare a gantale itama wannan Balarabiyar ai in ta Hanata Haihuwa mu taimakon mu tayi ammh Sai ta Hado da Sakina..? Tasan shekara nawa kika kwashe kina Wahala kan Sakina ta Samu Ciki ta Haihuwa ta zama Mowar mata agidan Umar..? Ko kuwa tasan Shekara nawa ni na bata ina Zaune da Fuskar balaraba Domun cikar Burina..? Shekaru fin Talatin ina Kun san bakin Cikin Sa"idu da Matarsa YAYA shekaru talatin na kwaahe ina Bautama ya"yanta shekaru masu yawa na kwashe ina nuna ina son yarinyar nan Amina har saki sai da Tsinnanniyar tajamin sai acikin wannan shekarar ne na samu yadda nake so shima bayan kasa ta Shafe idon yaya..To bata isa ba ki Fadamata bata isa ba..Bazamu bari ta Rusa mana Shekarun da muka kwaashe muna Wahala na Samu Sa"idu Dakyar Madina saboda haka fa na Hada kai Dake domin cikar Burina ke kina komai Saboda Sakina ni kuma inayin komai saboda Sa"idu ne ko JAFAR daya so ya nuna taurin kansa nayi mganinsa yanzu..Duk da abaya ba AMINA NASO ta kangare ba..Ba ita naso ta zama mara kunya ba..Ba ita naso ta koma haka ba Jafar naso ya koma haka ammh duk da Haka ban Sare ba Madina lamarina ba ja da baya kuma ba Faduwa ballatana Na karaya kema bai kamata ki karaya ba Madina..! Ta karishe Cikin Hargagin ta na Daukan ita kadai ce agidan idonta ya Rufe bataji bata gani. Amina dake Tsaye Tsakiyar Falon Mamanmu sai da ta rike bango Sakamakon wani wawan jiri Daya kwasheta jin kalaman dake fitowa daga bakin mamammu wanda suke mata amsa kuwa acikin kunnuwanta tana Fatan yasa abunda taji ba gaskiya bane ba Mamanmu bace ke wannan mganar ba. Tasowarta Daga barci kenan ta fito tayi alwala ta Duba Bayinsu na Daki ba Ruwa sai taji kanar mgana Daga Dakin mamamu sama sama yasa ta fasa yin wajen famfo ta shigo Dakin da niyar kiran sunan mamanmu sai dai mganar data ji ne yasa ta tsaya sanda Taji kalaman mamanmu da suka kusa saka Zuciyarta ta Buga. Bata gama Dawowa daidai ba ta Sake jin muryan mamamu Cikin Fusata tana Fadin. "Ita din banza Madina da zata Tsorataki. me akayi akayi HAJIYA UWA..? Muka kauda YAYA har Lahira ballatana ita..? Karki manta Saboda Cikar Burina kika taimakamin muka saka Malam ya Kara mata gudu zuwa Lahira.kamar yadda nake kokarin taimaka miki auran AMINA DA UMAR ya kare ahakan sannan bazata taba Zama wata mai Daraja awajensa ba Sakina ce kadai zata haifasama D'a jikan mallam da Hajiya..Saboda haka ki kwantar da Hankalinki Rai fa ba abakin komai yake ba wajen Biyan Bukata AMARYA..! kai Amina ta Dafe saboda ya Fara juyamata Hannunta Duka Biyu ta saka ta Toshe kunnuuwanta Lokaci Daya tana girgiza kanta Hawayen da suka fito mata suka fara ambaliya saman Fuskarta kamar an Bude famfo..! *Janafty* *TFZB2014* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* To mu kawar da ita nace madina tunda zata kawo mana matsala mana..Nafa fada miki tun abaya wajen biyan bukata rai ba abakin komai yake ba ke kika kara tunatar dani hakan madina Lokacin da kikace mu Kawar da YAYA naki baki Dama ina ganin kamar a lokacin bai kamata ta mutu ba naso ne sai na kunsa mata kwatan kwacin bakincikin da ta kunsamin amamh da kika nuna min mutuwarta itace masalaha bagashi tatafi ta barmin Sa"idun ba kuma sai da ta kauce na samu abunda nake so to kamar hakane in dai Hajiya uwani zata zame miki matsala wajen cikar naki Burin Madina mu kawar da ita kawai..! Amina Tsabar Rudin data ke ciki yasa kafafunta suka kasa Daukanta bata san sanda ta sulale ta zube saman Cafet din dakin mamanmu Lokaci daya tana Saka Hannuwanta duka biyu ta toshe Bakinta saboda kuka ne ke son kwace mata ba taredata sani ba. Mamammu fa..?mamanmu Innalillahi wa"inna ilaihirraju"un ita ke fadi da bakinta ta kashe Yaya ta kashe yaya wannan mganar amsa kuwwa take mata sannan mganganun sun Haifar mata da juyawar kan data kasa gane wani yanayi take ciki abu daya ta sani Taji abunda Tunda take bata taba jin makancin sa ba taji abunda Hasashe ko zato ko Tsammani bata ba Zato zata jisa Daga Bakin data aminta dashi ba. Rarrafawa tayi kamar mai koyon Zama saboda ta kasa tashi ta Dage labulen Dakin mamammu na ciki ta gefe kadan so take ta Tabbatar da abunda taji domin gani take yi kamar ba Mamanmu din bace mai irin Muryanta ne sai gashi taga Fuskar mamanmu cikin yanayin da bata taba ganinta ba Tana Tsaye tana waya ta cigaba da mgana cikin Zaro ido tana Fadin"to maza ki kira mallam..Ayi mana mganinta mu koma gefe muna Cin Duniyarmu da tsinke a Matsayin Dayyaba da Madina chan gefe kuma muna Cigaba da yaudaran mutane da Salihan Fuskokin mu na Balaraba da Marliya..! Bata tsaya ma ta gama ji ba ta juya Cikin Rarrafen har ta fice Daga Falon batare da tayi wani motsi ba Hawaye kuwa kamar an bude Famfo haka wasu ke fita wasu na kara Bulbulowa Idanuwan mamanmu ya rufe shiyasa kwata kwata bata ji wata alaman akwai wani acikin gidan ba. Amina na fitowa Tsakar gida tayi tayi tatashi sai ta kasa Domin gabadaya jikinta ya Saki Lokaci Daya ta kasa gasgasta abunda taji kuma ta gani Mamanmu kadai kanta ke iya fadi da sunan yaya Anty Amarya bata wani bata mamaki ba jin sunanta Daman ita Tuni Tasan Halinta ammh acikin wannan yanayin ace Mamanmu ce ke da Alhakin Duka abubuwan da suke Faruwa ta yaya zuciya zata iya Daukan wannan Gaskiyan..? Dakyar ta iya mikewa sai da ta rike Karfen barandan su sannan gabadaya kanta juyamata yake Bata gani Dakyau wani irin Biji Biji take gani Allah ya taimaketa taga Hijabin Haddar Hamida kan igiya data wanke ta Taka Sannu sannu tana Nunfashi Sama sama ta Daukosa ta sakasa ko Takalmi babu a kafarta haka ta Fice Daga gidan Cikin wani yanayi duk Takun da Zatayi sai kalaman mamanmu sun mata amsa kuwwa acikin kunnuwanta Daki Daki Dayasa Cikinta ya Cure waje Daya Dakyar take iya taka kafarta a Haraban gidan taga Jawaad yana kwallo yana ganinta ya nufeta yana Kiran sunanta sai kawai Amina ta kallesa ta kara kallonsa Tabbas sai Allah ya Tsine ma balaraba ko da Hakkin Jawaad aka barta sai Rayuwarta ta D'aida'ice Rumgumesa kawai tana so ta Fashe da kuka ammh ta kasa acikin Kirjinta take jin wani zafi kamar zata mutu batare da tamai mgana ba taja Hannunsa suka fice domin gabadaya gidan ne yayi mata wani zafin Datake jinsa har acikin jikinta suna tafe yana Fadin"Ya Amina ina Takalmin ki. ? A islamiya an ce mana ba kyau tafiya ba Takalmi..! Bata ma Sauraransa ita dai kawai Jefa kafa take yi Allah ne ya kaita Falon Hajiya ba Domin tana ganin Hanya Dakyau ba suna shigowa Hamida da Hanne suka Dago suna kallonta gabansu ya fadi ganin Hawaye Kaca kaca a Fuskarta Hannun Jawaad ta Saki ko barayin bata kallah ba Ta nufi Dakin su Hanne tana jin ita da Hamida na Faman kiran sunanta suna tambayanta me ya faru take kuka ko Waigowa batayi ba a yanayin Datake Ciki ba kowa zai iya Fahintarta ta ba Tunda bata da Uwa a raye a Duniya to ta samu kadaicin da zata Zauna Tayi Tunanin makomar ta a wannan Duniyan da Rayuwar data ke cike da Tarin azzalumai maciya amana..! Tana shiga Dakin ta Ture kofar bata ma iya karisawa Kan gadon ba ta Sulale nan saman Cafet a kofar Dakin Tana Dafe Saitin zuciyarta Daya Dunkule waje daya ga cikinta Daya Cure waje Daya yana murdamata Sosai da sosai Hawaye da majina Har da Miyau haka suke kara kaina akan Fuskar Amina batare data Damu Data Share su ba. Achan Falo kuwa Hamida ta kalli Jawaad tana fadin"Wai me ya faru ne Amina ta shigo tana kuka..? Shima ya girgizamata kai kafin yace"Bansani ba nima ina kwallo na ne tazo tana kuka taja Hannuna muka zo nan..!. Hanne ta mike tana Fadin"Hamida muje mu gani..; Tare suka Dumguma suka Nufi Dakin suna Tura kofa suka kusa cin karo da Amina atare suka saki Salati Hanne ta Duka gaban Amina tana Fadin"Amina meke Faruwa ne..? Amina ta runtse ido sai wasu Hawayen ta Dafe saitin zuciyarta Dake mata Zafi bakinta yayi Nauyin da bazata iya mgana ba. Hamida ta kalli Hanne Cikin wani yanayi kafin tace"Ko zaki je ki kira Hajiya a shashen Baba mallam ne..? Hanne ta mike tana mai yarda da mganar Hamida da Sauri Amina ta Rike kasan Sikat dinta bata so ta Kira Hajiya domin in tazo bata san me Zata Fada mata ba, ta tabbata ita kanta ba Domin taji ta gani ba ko Duniya Zasu Taru su fadamata Bakaken Halayyar mamanmu bazata taba yarda ba shiyasa ta Dago Jajayen idanuwanta Dakyar tace"Kada ki kirata..! Hanne tace"To kuma kina ta kuka..! Amina ta Runtse ido kafin tace"Ba..bani da lafiya ne..! Hamida tace"Kan ki ke ciwo..? Daman tasan Amina da Raki ciwo kadan sai ta Fara kuka da Sauri Ta gyada kanta Hanne tace"To ki tashi kici abinci ki sha mgani sai ki kwanta..!. Saboda su kyaleta yasa tace musu tasha mgani agida Muryanta a Dakushe Hamida ne tace Hanne ta Taya ta su taimaka ma Amina ta koma kan gado tunda bata da Lafiya haka suka taimaka mata ta hau kan gado ta Dunkule ta Runte ido kamar mai barci har Hamida ta Lallube kafarta da Bargo suka fice bayan sun turo mata Kofar sai da suka fita ta Bude idanuwanta Allah Sarki Hamida mai kyakyawan zuciya tunda Take da Hamida bata taba ganin wani sharrinta ba sai Alheri ya zata ji in ta ji Halin Mahaifiyarta..? Kai Innalillahi Yaya ashe ashe kasheta sukayi Shiyasa ta kwanta Lafiya lau sai gawanta aka gani shin me yaya ta Tsare ma Mamanmu..? Ta bar mata ragamar gidanta ta bar mata Ragamar duka ya"yan data Haifa ace ko don haka mamanmu bazata Raga mata ba..? Tunda take bata taba ganin Aba yayi bambamci tsakanin Mamanmu da Yaya ba har tana Kwatantashi Cikin masu adalci Tsakanin matansa. Ashe ashe alheri yana komawa Sharri ashe ashe haka Duniya ta gada..! Sai yanzu ta Fahimci Bakin Zaren Ta Dade tana Tunanin da wa Anty Amarya take waya kwanaki tana ambaton sunanta da kokarin Hanata Tarewa a gidan ya Danmalam sai yau Sirrin Boye ya fito Filo ashe mamanmu da Anty Amarya Bakin su Daya..? Ita tanayin komai Saboda Aba ne ita kuma Anty Amarya saboda Sakina ne..? Ita fa Haj.uwa dataji suna ambatkn sunanta ita me ta ke aikatawa..?! Sannan domin wa take yin abunda take yi har suke Tunanin in zata basu matsala su kawar da ita..? Lalle Duniya ba abun yarda bace abunda ko a mafarki ko Finfinan India dana Hausa bata jiba ai ko a karance karancen datake yi bata taba Haduwa da makirci da mugunta irin wannan ba Shekaru Goma sha Shidda Mamanmu ta kwashe tana kassara Rayuwarta ko da da rana Daya bata taba bari ta rabu da Yaya tasan Dadi da Martaban uwa ba shekaru sha Shidda ta kwashe tana Gurgunta Rayuwarta sai alokacin abubuwa suka Dawo mata Daki Daki Tun Farko kovsau Daya mamanmu bata taba Zaunar da ita tayi mata Fada kan wani abu ba sai dai ta rika Fadin yarintace in ta girma Zata Daina Ammh ai Hamida bata mata Haka bama ita ba kaf ya"yanta tana Dorasu kan Hanyar mai kyau tun daga bangaran Tarbiya har bangaran Ayyukan gida da Sauraran abubuwa ashe da gangan ta Sangartata ta Shagwabata Duk cikin Lalata Rayuwarta ne bata sani ba Kaiconta ashe ashe duk wasu abubuwan datake yi ba yin kanta bane tasan wasu abubuwan na tadda Hali ammh wannan Rashin Tsoron da Zafin Zuciyar duk ba nata bane Mamanmu ne taso ta kassara Rayuwar ya Jafar sai abun ya Tsaya akanta ta Godema Allah da abun ya Tsaya kanta Domin daman karamin alhakin daka raina Watarana shi zai tsole maka ido. Tafara Tunanin yadda ta rika turata sai taje ta ce ma Hajiya ko mallam bazata tare ba batasan Dannallam sai yanzu ta Fahimci komai wato tana Taya Anty Amarya ne kamar yadda ta Taimaka mata ta kashe musu uwa anya Balaraba zata ga Annabi kuwa..? Idan ta Mutu kila kasa bazata taba karbanta ba ashe ashe bata son tarewarta da ya Danmallan ta Tabbata Auran ma Allah ne yaso da bazasu taba bari ba ta Tuna sanda take tusa mata ra"ayin tace ya saketa Tsoho ne bai dace da ita ba ta tuna yadda take Zaunar da ita tana Dukan ruwan cikinta in taje gidan Danmallan tayi Weekend ta Dawo tasha Turketa ta Tambayeta ko suna waya sai tace mata A"a data ga kuma kamar abun yayi musu yadda suke so ne ta fita Sabgarta ashe Duniyar ce ta Fara Samuwa ba shakka Taga Aba ya Rage damuwa da wasu al"muran sannan ko Jawad sai ya kwana wajen su a ashashen Hajiya Aba bai Damu ba abaya kuwa yana Dawowa sai ya nemi Jawaad inda ya Saka kafa nan yake sakawa shima sai da Mamanmu ta rabasu taji Dadi ashe ashe Sihiri ne ajikinta shiyasa take Fama da Zafin zuciya bata sani ba..! Sai ta Tuna Aminu sanda yake Fadamata watarana ga Mamanmu din ammh har Abada bazata Shafe mata matsayin UWA BA..ta yarda kuma ta amince a wannan Ranar kewar Uwa ne ya Taso mata da tana Raye da a kan kafadarta zata kwanta tayi wannan kukan ammh ina Duk da Lokacinta ne yayi domin mamanmu bata isa ta yi Ajalin yaya ba tunda ita ba Allah bace ta sani Daman chan kwanakin da suka Rage mata a Duniya kenan Mamanmu da izinin Lahi sai tayi mutuwar wulakanci sai tayi mutuwar kaskanci wannan Duniyar datake Fatan ta samu bazata taba cinta ba Har Abada tunda har tayi sakacin Datasan sirrinsu tayi alkawarin sai ta Daidaita Rayuwarsu daga ita har Anty Amarya kuma da yardan Allah zama da ya Danmallan yanzu ta fara Zama Daram Kuma Haihuwa da izinin Lahi indai Allah ke badawa sai ta Rokesa ya bata Ta Haifar masa dozin yan Bakinciki da mahasada sai dai su Fadi su mutu Allah Sarki bawan Allah yana chan yana aikinsa a nan an saka sa agaba Allah Sarki Hajiya da mallam kuna Zagaye da makirai da mugaye baku sani ba. Ita ne nan zata zama sillar Tonuwar asirinsu. An riga anyi walkiya ta gansu. Sannan an Dade ana ruwa kasa tana Shanyewa.. Ita nan Amina Aminene ikon Allah badai ta mutum ba sai ta Allah kainuwan Dashen Allah indan Rana ta fito Tafin Hannu bai isa ya kareta ba..Daya bayan Daya sai sun tsinci abunda suka shuka wannan alkwarinta ne..! Kukan da Amina bata samu tayi ba sai yanzu ya kwace mata sai da Filon Datake kwance akai ya jike da Hawaye kanta ciwo yake yi Idanuwanta sun mata nauyi ga Cikinta na murdamata Har da yunwa tana jin Hajiya ta shigo Dakin bayan ta Dawo daga Falon mallam sukace bata jin Dadi ta shigo ta Dubata ita kuma ta Tusa kanta cikin Hijabi tayi Luf kamar mai barci har ta fita tana fadin Ta samu barci. Duk tana kwance taji Su Hamida sun shigo sun yi sallar mangariba sai alokacin Hajiya ta leko tana Fadin"Hamida ku tada Mamah mangariba tayi..! Hamida ta mike ta isa wajen Amina tana tashinta kafarta tataba Taji Jikinta kamar wuta ta Dago tana Fadin"Zazzabi ya kamata jikinta Zafi..! Hajiya ta kariso Dakin tana Fadin"Asshsha..Mamah Daure ki tashi kiyi sallah sai kici wani abu ki sha mgani..! Dole Amina ta mike Hajiya sai da ta Tsorata da ta ga yadda idanuwanta suka koma Cikin wani yanayi tace"Amina meya faru kike kuka kinga idanuwanki yadda suka kumbura kuwa..? Amina ta mike Zaune tana fadin"Hajiya Yaya na tuna..Sai na fara kuka sai kirjina ya fara ciwo da kaina sai Zazzabi ya kamani..! Daganan kawai ta saki kuka Hajiya ta Dafa kanta Cikin Tsausaya tace"Addu"a zaki mata in kin Tuna ta kin ji ko mamah ba kuka ba..? Kai ta gyada tana kara sharan Hawayen wasu na ambaliya ita ta mike ta kama Aminar da Jikinta ke Rawa ta kaita Tiolet ta barota ta Fito tana kallon su Hanne da Jikinsu yayi sanyi tace"Zo ki kar ban mata magani ke kuma Hamida shiga kitchen ki zubo mata abinci ga Jawaad ma chan afalo ki zubamai yaci kafin yayi barci.! Da toh suka amsa mata ta fice suka bi bayanta Hamida tayi yarda Hajiya tace ta Zubama Jawad Jallop din Taliya da Miyar kifi ne ta Zubama Aminata kaimata ta iske tana Sallah a Zaune Hanne ma ta kawo mata mganin da Ruwa suka koma Falo suka barta kada su Dameta. Tana Idar da sallah ta zauna sai kuka take yi ta rasa addu"an ma da zatayi kawai sai ta Daga Hannu tana rokar ma Mamanmu tabewa da bala"in Duniya kala kala tanayi tana kuka Kafin ta kife kanta ta cigaba Tana wajen aka kira isha"i daga Zaunen ta yi sallar ko abincin bata kallah ba sai da taji kamar Hajiya zata shigo sannan ta Jawo Filet din ta fara ci Turawa kawai take yi ko Rabi bata ci ba Cikinta ya Cuse zuciyarta ta fara tashi ta Nufi Bayi a guje sai amai sai da ta Amayar dashi Duka sannan ta koma gefe tana maida numfashi koiya Fitowa batayi ba sai da Hamida tazo ta fito da ita ta iske Hajiya da Hanne afalon abincin tace a Dauke a Hado mata Tea mai kauri to shi ta dan samu ta sha ya Zauna ta hada da panadol Hajiya ta fice zuwa shashen mallam ta Sanar dashi cikin wani yanayi yace Allah ya Sauwake in ba sauki gobe sai Hajiya ta kaita asibiti tun abunda ya Faru ne Dazu Mallan bai Saki ba har yanzu..! Awannan Daran yadda Amina taga Rana haka taga Dare domin barci ko barawo bai Saceta ba ga kuncin zuciya ga Zazzabi Cikin Dare kaf Abunda ke Cikinta sai da ta amayar dashi kafin Safe Jikinta yayi zafi sai rawan sanyi take da Haduwar Hakora sallar asuba ma Dakyar ta iya yi tana neman Faduwa Hanne ta jira sai da Hajiya ta Dawo daga Shashen mallam ta Fada mata cewa tayi su sauya ma Amina Hijabi bari ta Fadama mallam ya ma Idi mgana yakai su asibiti. Mallam na jin jikin Amina yayi zafi Hankalinsa ya tashi ya Kira Idi a waya yace yazo ya kai Hajiya asibiti ba Dadewa sai gashi Lokacin Hajiya har ta Shirya Amina ko Tafiya bata iya yi Saboda yadda Jikinta yayi zafi Hanne da Hamida suka riketa har Bakin mota ta shiga Suka Bita da fatan samun Sauki Cike da Tsausayi mallam ma Sai da ya Tsausayamata ganin yadda ta koma Cikin kwana Daya yace su Hajiya su yi gaba komai kenan ta Kirasa. Kafin su tafi sai da Hajiya tace su Hanne su shirya su tafi makaranta Harda da Jawaad suka amsa mata da Toh suna masu Tsausayin Amina. Suka koma Shashen Hajiya suka yi wanka suka karya suka yi shirin tafiya makaranta Harda Jawaad sai da suka fito ne suka ga Aba suka gaisa sai Lokacin ya rike Jaawad yana Fadin ya yi musu yaji shi da balaraba ko Mallam na wajen yace to yaga su Hamida sun dawo ina zai zauna in da ba kowa abunda mallam bai sani ba in Aba baya ga Jawaad bane yanzu mancewa ma yake yi dashi. Hamida ta shiga gidansu ta gaida mamanmu ta sameta cikin kwalliya kamar wata yarinya ita abun ma sai ya bata mamaki sama sama suka gaisa ta shiga Dakinsu ta Dauki littafinta na Biology data manta Dashi bata ma samu Fadama Mamanmu Amina bata da lafiya ba Shidai Mallam ya sanar ma da Aba sai dai ba gida ya koma ba gidan gona ya wuce Shiyasa Mamanmu bata ji ba Sannan a matan mallam ba wacce ta Bude shashenta ma ballatana tasan abunda ke faruwa..! General Hospital tace Idi ya kai su suna zuwa ta Kira Nasir a waya ta Fadamai yace bai riga ya shigo asibitin ba ammh gashi nan kan Hanya ba Dadewa sai gashi ya iso ya Iske har Hajiya ta yanki kati suna bin layi Tunda gidan mallam bai Dauki wani Family Doctor ba ba ruwansa da wannan,Duk da ba bangaran yara bane A sanshi a asibitin shi ya karbi katin su Hajiya ya shiga wajen Likita yamai bayani ganin Dr.Isa ne abokinsa ne yamai bayanin Hajiyarsu ne ta kawo kanwarsu ba Lafiya jin haka yace su shigo kawai. Dole sai Nasir ne ya rike Amina Saboda tana mikewa jiri ya kwasheta ta kusa fadi Allah yasa yana kusa ya Tareta Hajiya bazata iya ba ita kadai Ganin yadda suka shigo da ita a rirrike yasa Dr Isa yace su shimfidar da ita kan gadon dayake ganin marasa Lafiya nan Nasir ya Dorata shi kanshi ya ji Tsausayin Amina jikinta kamar wuta Saboda Zafin Zazzabi. Likitan yazo ya Duba bayan ya cire mata Hijabin jikinta ya taba Temprature din jikinta ya gwale mata ido ya kuma Duba Tafin hannunta bayan ya kalleta na tsawon mintina goma kai ya girgiza kafin ya Dawo ya Zauna ya kalli hajiya da Nasir yana Fadin"Zamu dibi jininta za ayi Test..sannan akwai yunwa tare da ita zan kara mata drip da allurai wanda zasu taimaka mata ta Dawo Cikin hayyacinta..! Ba musu Hajiya tace"Ayi abunda ya kamata likita in ma gado zaka bamu ba Damuwa..! Yana Rubutu saman wata Takarda yace"A"a mama Ba gado bane zamu dai mu riketa na awa daya ko biyu zuwa uku mu saka mata Drip muyi mata allurai kafin Lokacin Sakamakon gwajin mu ya fito..! Wata Nurse ya kira tazo yace ta Dibi Jinin Amina aka kai lap yana son abun da Sauri ne Amina duk Tsoron Alluranta bataji ba yau ko Ihun batayi ba tana gama Diba ta fice  shikuma Nasir Likita ya bashi Takardan Daya Rubuta allurai da Driip yaje phamarcy cikin asibiti ya siyo ya kawo mai nan da nan ya saka Handgold ya Hada allura biyu ya yi mata ta Jijiya Biyun kuma tana Cikin Drip din Amina ahalin Datake ciki kuka ma Har ta gaji da yi ashe sai kana da ma natsuwa kake jin zafin wani abu ita ko Zafin Alluran ma yau bata ji ba.. Kamar almara ba Dadewa Amina sai barci ganin haka yasa Nasir ya tafi bangaransa inda yake aiki yace in da wani abu Hajiya ta Kirasa waje ta fita Tana jira domin Dr.Isa ya cigaba da ganin mara sa Lafiya kamar yadda aka saba..! Hajiya na babban Falo zaune tana jira sai ga Kiran mallam ta Dauka sukayi mgana tace mai Amina na ciki ta samu barci yace su dan jira na wani Lokaci Da haka sukayi sallama Idi bai koma ba yana nan yana jiransu. Awa Biyu da wani abu Hajiya ta kwashe Tana jira sannan wata Nurse tazo ta Kirata zuwa Office din Likita koda ta shiga har lokacin Amina barci take ammh Ruwan ya kare har an cire mata. Kujera yanuna ma Hajiya yace ta zauna, ta Zauna tana Sauraransa wata Farar Takarda Doguwa ya mika mata Hajiya ta karba Tana Fadin"Likita wannan Takardan fa..? Fadamin abunda ke faruwa kune yaran zamani yan Boko..! Mirmishi yayi kafin yace"Amina Sa"idu yarki ce Hajiya ko..? Hajiya ta Dagamai kai da Sauri kafin ya Cigaba da Fadin"Tana da aure ne..? Hajiya taji gabanta ya fadi sai ta basar kafim tace"Eh likita..! Ina fatan ba wata matsala ko..? Da Sauri yace"Babu Mama..Takardan Dake hannunki Sakaamakon gwajin da muka ma Amina ne..Sakamako ya nuna mana tana Dauke da Ciki kimanin Wata Hudu da kwana goma..! Hajiya sai taji kamar bata ji da kyau ba ta Zari ido kafin tace"bangane ba..Likita wani irin ciki..,? Dr Isa yace"Ciki dai na Haihuwa mama .! Hajiya taji jikinta ya Saki Cikin mamaki ta juya ta kalli Amina Dake Sharan barci kafin ta kalli Likitan tana Fadin"yanzu nan Likita Amina ciki gareta har na Tsawon wata Hudu da wani abu bamu taba ganin alamu ba..? Dariya Dr.Isa yayi kafin yace"hakan yana Faruwa sosai Mama...naga shekarar ta 17 ajikin katinta ko..? Hajiya ta gyada kai tana mamakin ikon Allah acikin ranta. Likita ya Cigaba da fadin"ba abun mamaki bane in baku gane ba..Tana da karancin shekaru sannan Cikin nata irinsa ne Hausawaa ke cema Kurman ciki bai cika bayyana kansa yana karami ba sai ya kusa fitowa Duniya..Sannan in kun lura Cikin yabi Jikinta ne ya kuma yazo Lokacin ta na age din kuruciyarta ne sannan tana da Tsawo sai ya shanye shi ajikinta inbamu masana abun ba, ba lalle ku iya gane tana da ciki ba..! Hajiya ta jinjina kai kafin tace"Ko fa Laulayi batayi ba Likita sai dai ta rika cin abinci sosai..da yawan barci..! Dr ya gyada kai kafin yace"Ba lalle sai tayi ba ai kowani Ciki da nasa Salon mama..Ita nata nacin abinci ne da yawan barci kila ko zatayi Laulayin sai nan gaba kadan..! Hajiya ta sake jinjina kai kafin tace"Sai jiya tayi ma amai sau Daya..! Dariya wannan karon yayi kafin yace"Normal ne..Mama kila ma Daga yanzu Lokaci bayan Lokaci in taci abund bai karbi Cikin ba Zata iya yin amansa.! Hajiya ta Damke Takardan Hannunta tana Fadin"Nagode likita yaushe Zamu tafi gida..? Yace"Yanzu da zarar ta farka..alluran barci nayi mata yanzu zata saketa..! Suna ma cikin mganar Amina ta Farka tana Kokarin tashi Hajiya ta karisa gabanta ta mata sannu Dr Isa ya taso ya kara Dubata ya tambayeta me take ji tace ba komai jikinta ya rage Zafi Zazzabin ya Sauka mganganuna ya Rubuta mata ya Sallamesu sai ga Amina na takawa da Kafarta har wajen mota sai alokacin hajya ta kare mata kallo Taga Cikin da Likita yace yabi Jikin Amina Allah mai iko Annabi mai Dumbin Daraja. Basu tafi ba sai da ta Kira Nasir yazo haraban asibitin ya same su koda ya Tambayi Hajiya me likita yace sai taki Fadamai ta dai basa Takardan mganin daya bata shi kuma yace ta Jira yaje ya siyo ba Dadewa sai gashi ya Dawo da Ledan mai Tambarin General Hospital Gumel. Shi Nasir bai wani tsaya duba takardan mganin ba shiyasa bai Fahimci ko na menene ba. Daganan sukayi sallama bayan ya leka Motar yayi ma Amina Sannu ta amsa tana Dagamai kai. Har suka kai gida Hajiya ta kasa gasgasta abunda taji Aranta kawai sai ta shiga wani Tunani Tsakanin miji da mata sai Allah bata Zargin Amina har ga Allah sai dai kuma likita yace Cikin Jikinta wata Hudu da kwana goma sannan in ta Lissafa dai dai Danmallan shima nada wajen wata hudu da sati Biyu in bai fi ba da komawa Madina,kenan kafin ya tafi ne in ma wani abun ne ya shiga Tsakaninsa da Amina Allah mai iko sai abun ya bata mamaki matuka. Sanda suka Dawo Mallam bai fita ba ammh yana Sauri zai je Fadar Sarki ana nemansa shiyasa bai Tsaya ma sun yi mgana da Hajiya ba ganin Amina Taji Sauki har gata ma tana Tafiya da kanta kuma cikin ikon Allah har suka kai Shashen Hajiya basu hadu da kowa ba. Suna shiga Hajiya bata Zauna ba ta Hado ma Amina tea mai kauri ta matsa mata tasha ta bata mgungunanta duk yawancin na karin Jini ne sai na Vitamin C da polic acid na masu Ciki sai kuma panadol sai da ta sha ta natsu Fatan ta kada tayi Amai sai kuma Allah yasa batayin ba. Hajiya ta rakata Dakin su Hanne ta kwantar da ita kan gado sannan ta Zauna gefenta tana kiran sunanta Aminaa na kokarim mikewa Zaune Hajiya tace ta koma ta kwanta. Hajiya ta kalleta Cikin ido kafin tace"Mama kinsan me Likita yace yana Damunki..? Amina ta girgixa kai kanta a kasa Hajiya ta gyara Zama kafin tace"Yace Kina CIKI har na Tsawon wata Hudu da kwana goma..! Dam!!! Gaban Amina ya fadi ta kalli Hajiya da Kumburarrun Idanuwanta ta maimaita Cikin mamaki "Ciki ...? Hajiya ta gyada mata ai sai acikin Ran Amina tayi wata Hamdala ta yi kabbara ta sake yin wata kabbara domin mganar mamanmu take Tunawa da tace bazata Haihu da Ya Danmallam ba sai Sakina sannan kuma auran haka zai kare ba Fa'ida Ashe ashe basu sani ba Allah ya Riga yayi ikonsa..! Ganin kamar bata wani Razana Sosai bane yasa Hajiya tace"ko kin san da shi ne Amina baki Fadamin ba..? Amina na sharan Hawayen data rasa ko na Dadi ne ko na Murnan Karshen mamanmu da Anty Amarya yazo ne. Bata sani ba cikin kukan tace"Wlh bansani ba Hajiya bansani ba..! Hajiya ta Dafa hannun Amina Kafin tace"Basai kin Rantse ba nima da naga Jiya naga yau ban gane ba sai ke yarinya karama Mamah..? Yi shurunki..! Hajiya ta fada tana Faman share ma Amina Hawaye Tsausayinta na kamata. Hajiya ta Dakata tana Fadin"Tambayarki zan yi Tsakaninki ga Allah Mamah..kada kiji nauyi na ina so na gasgata wani abu ne.. Shin Kafin tafiyar Danmallam wani abu ya shiga Tsakaninku ne..? Ai sai Amina taji kamar kasa ta Bude ta Shige sai ta juya baya ta Dunkule kanta tana mai jin kunyar Hajiya abunda ya faru Tskaninta da Danmallam yana Dawo mata kamar a jikin magiji. Hajiya ta Daga hannu tayi kabbara Tare da Hamdala ta mike tsaye ta Fice Tana Mai Farinciki wanda ya kasa Boyuwa a saman Fuskarta. Tana fita Direct Dakinta ta shiga waya ta Dauka ta Kira Danmallam bakinta kamar Gonar auduga saboda Murna Yana gida bai fita ba yaga Kiran Hajiya sai da gabansa ya fadi suna Falo Tare da Sarood ne ya barta ya shiga Cikin Bedroom dinsu,kafin ya Katse kiran yabi bayan kiran Hajiya Tana Dauka ko amsa sallamarsa batayi ba tace"Danmallam kana jina..? Cikin Wani yanayi yace"Ina jin ki Hajiya..! Ta cigaba da Fadin"Tambayarka zan yi kuma ina so ka fadamin gaskiya..! Zama yayi gefen gado yana fadin ina jinki Hajiya..! Hajiya tace"Wani abu na auratayya ya Shiga Tsakaninka da Amina ne kafin tafiyarka.? Ina kasa ta Tsage Danmallan ya shige ya kasa mgana gabadaya sai jikinsa ya Fara rawa kamar yana gaban Hajiya,Ya kasa mgana ma kamar ya kashe wayar haka yake ji meya kawo wannan mganar..? Badai wani abu ne kuma ya faru ba..? Jin yayi shuru yasa Hajiya tace"Amsar ka tana da muhimmanci Danmallam..! Muryansa a shake yace"Ehhh..! Hajiya tace"Allahu akbar Sarkin gagara Misali..UMAR  ka godema Allah..Amina nada ciki har na Tsawon wata Hudu da kwana goma cikin ka Umaru..! Haka yaji Hajiya tace kafin ta katse kiran sai ya fara Tunanin kodai bai ji Daidai bane..? Wata Aminar ke da Ciki..? Kwakwalwarsa ta Fara Hasko masa Amina ita ce ke Dauke da Cikinsa kuma ya Tabbata Hajiya bazata Kirasa tamai wasa ba..! Allahu akbar ya furta sau uku ashe Ashe Daman wannan kwan Hallitar yasa tafiyarsa bata yuyu ba aranar  Allah ya Kaddara mahaifan Amina Zata Dauki wannan hallitar shiyasa tafiyarsa bata samu ba sai da ya Dawo gida sannan cikin abunda bai Tsammani ba ya tara da Amina ashe ashe ya saka mata kwan haihuwa ashe ashe ya zama Daya da ita baisani ba..! Wannan shine ake kira Zanen kaddaran..? zakaran da Allah ya Nufa da Cara ki ana muzuru ana shaho sai yayi. Yau Cikin Farinciki suka tashi shi da Sarood na warkensa gabadaya jiya ya tabbata namiji ga Sarood ya maida ita mace shiyasa bai fita ba ya Zauna yana kula da ita Allah yayi gaskiya Qur"ani waraka ne bai san Sadda ya Durkushe a saman cafet din Dake Bedroom din ba ya Daidai ci gabas yayi Sujudul shukur Muryansa cikin Zaki da gardi yake fadin. "Alhamdulillah..Alhamdulillah..Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban Halittun duniya Annabi muhammadu Sallalahu alaihi wasallam.." *Janafty* *TFZB2015* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Hajiya na fita Daga Dakin Amina ta Dago kanta sai da ta tabbatar da Hajya ta shige Dakinta sannan ta Mike Zaune kan gadon ta yaye rigar kikinta Cikinta Daya fara tasowa kadan take kallo sai da ta kuramai ido sannan ta Fahimci ba"a sama yake ba yana kasan maranta ne dan tasawar da yayi ashe ashe ba Timbi bane kamar yadda suke Tunani ita dasu Hanne Ciki ne na Haihuwa..? Ita yau Amina ke da Ciki zata Haihu..? Yau ina yaya take..? Bata raye saboda haka bazata ga wannan ranar ba..? Mamanmu ta rabata da yaya Har gaban Abada mamanmu bazata ga Daidai a Rayuwarta ba Tana hawaye tana shafa Cikinta Daga jiya zuwa yau wanu Tsanar mamanmu ne ke yawo acikin ranta Tsanar da ko Anty Amarya bata yi ma irnsa ba Domin ta Cutar da Rayuwarta tundaga matakin Haihuwa har zuwa jiya da asirinta ya Tonu Shafan Cikinta take yi ta ke taji wani kaunarsa na mamaye aranta Dariya tayi acikin Ranta tana Hango Amina da y'a tab lalle za"a ga uwa anan wajen Sun so su hana ta Tarewa auran ma ba da son ransu bane sai dai In dan Rana ta fito tafin Hannu bai isa ya kareta ba Allah yace kuma ya isar da Cewarsa Hawayenta ta share wani kunci na Shiga aranta Tana Dafe da Cikinta tace"Allah ya kare min duk abunda ke Cikina..Allah ba ikona bane ko Dubarata ba ne da ka bani wannan kyautar ajikina kuma ka karesa batare da kowa yasan dashi ba Ya Allah ina Rokinka da kariyarka ka cigaba karesa har ya fito Duniya domin Fitowarsa Duniya ko bayyansa Shine Zai Taimakamin wajen Tona ma mugaye azzalumai asiri mara sa Tsoron Allah Kamar yadda suka ce na Ratso aikin su batare da sun sani ba nayi alkwarin Dawowa Amina Sa"idu gusai dina mai Biyayya da ladabi Mai Tsayawa ga Kafafunta nayi alkwarim Daga yau bazan kara kuka Domin na gaza ba sai domin imanin ka ya Allah ka Tsareni da Tsarewarka kabani Kwarin gwiwan da zan bankada Azzalumai dani suke zencen mu zuba mu gani shege kafasa Aminene nike kirarina badai ta mutum ba sai ta Allah..! Ta karishe fada Lokaci Daya wani karfin gwiwa na shiganta Tsoro yana barin ranta son Cikinta da son ta Rainesa ya fito Duniya ya Zauna aranta Abu Daya take son gani Tozartan Mamanmu da Sauran masu mugayen zuciya irin su Anty Amarya da Haj.Uwani yau gata da ciki in sun isa su hana Allah ya ikonsa ashe karyan Boka da mallam suke tunda suka kasa bankado musu wannan sirin Shashashan banza azzalumai Da Yardan Allah karshen ku yazo ku Fara Kirga Lokacin da zaku wulakanta. Hajiya ta rasa ina zata saka kanta Saboda Farinciki,Ta kasa zama ta kasa Tsayuwa waje daya ta Daga Hannunwanta duka biyu sama tanayima Allah kirari domin wannan shi ake kira tsammanin Abunda baka yi Tsammani ba. Hajiya ta rasa da wa zata ra ba wannan Farinciki na ganin Amina Dauke da cikin Danmallam ta Dade batayi farimciki irin na yau ba gashi mallam baya nan balle ta ruga ta Fadamai suyi wannan murnan tare yaya kuma bata Raye balle ta Ruga ta Fadamata Amina zata zama uwa nan bada Dadewa ba Amina zata koma yadda take so sai Bata a duniya lokacin da hakan ta faru sai dai tana Fatan Ta cikin samu salama acikin kabarinta har Abada. Haj.Uwani ta Fado mata arai itace tafi Kusa da ita in wani abu ya sameta bayan mallam da Sa"idu itace ta ukun Datake sani yasa ta kwashi Sauri zuwa Shashen nata bakinta kamar zai tsage Saboda murna. Koda ta shiga Falon ba kowa tsit tana Tunanin kila tana ciki ne yasa ta yi sallama sai dai ba"a amsa mata ba ta Bude baki zata sake wata sallama ne Taji Muryan Haj Uwani cikin shewa da Dariya tana Fadin"Batula naso kina wajen nan kiga idanuwan marliya gaban mallam da Hajiya..? Kinga yadda ta muzanta ba halin ta Fadi wata mgana na riga na gama Daureta da Jijuyoyin jikinta..sai uban kuka take yi mallam kuwa yayi mata Fata Fata Hajiya har da yar Nasihan kan Marliya ta Daina bin malamai wlh Batula naso kiga yadda marliya ta koma abun Tsausayi..! Shuru na wani Lokaci ya biyo baya Hajiya bata Fahimci kan zencen ba ganin kamar tana waya da Yar"uwanta Batula yasa Ta juya da niyyar Barin Falon AllaH barshi ta Dawo an juma ko in ita Uwanin ta shigo sai ta Sanar da ita sai dai tana Daga kafarta da niyar Fita taji Uwani na Fadin"Haba ni ce fa Batula kar kin manta ni..Ai marliya bazata kara kiran mai alewa bata da kudi ba..Alokacin da nake fadama Marliya Irin Tuggu na sai ta ga nata ai bakomai bane Batula na Fadamata zan yi shekaru aruru ina bin bayan Hajiya ne kamar wata Sakarya..? Na Fada mata na riga fara aiki akan biyan Bukata saboda haka sai da ta hakura da nata Cikar Burin ta barni na cika nawa in burina ya gama cika zan sallameta sai ta nuna Taurin kai cewa ita bazata yarda ba sai na Fadamata me nayi ma Sakina da yasa ta ke Barin duk cikin data samu. ? Nace mata ta kwantar da Hankalinta ba Sakina kadai ba, har ita Balarabiyat da ita kanta Aminar ko sau D'ari zasu samu Ciki sai yabi Rariya alkawari ne na Daukan ma kaina Nazir ya fara Haihuwan ma mallam Jikiko guda Biyu hakan ya Zama kuskure ammh yanzu bazan kara maimata kuskure na ba..Duk da Haka sai da nasa aka maida su mara sa amfani a wajen mallam kamar yadda aka maida Nasir yanzu abubuwa nawa akeyi agidan nan kafin kiji mallam ya kama sunansa an Dade..? Kamar yadda na saka Mama ta sa Nazir yayi nisa da Gumel din da har Abada bazai iya zama na Sati Daya acikinta ba na saka ta Lula kurciyar Danmallan madina yadda bazasu zauna ma agarin bama ballatana Mallam ya gansu ya ce zai Dorasu kan dukiyarsa Batula kin san yadda na sha Wahala shekaru aru aru kan ganin ya"yana akan gaba akomai agidan nan to Wahalata ta kusa zuwa karshe Nazeem sauran kadan ya karisa ya Dawo uzairu kuma yana Bautar kasa kafin ya gama Nazeem ya Dawo daganan zan Dora harshashen Burina ya fara cika ga Shamsu shima ya fara nasa karatun kina ganin zan bari marliya tazo ta rusamin Shirina na ne..? Shine na Tauna Tsakuwa domin aya taji Tsoro Batula na tabbata na Saka tsorona azuciyar Madina,bama ta da wayau ne ni da ya kamata ta godemin Batula..? Nan ta maida balarabiyar nan kamar Hoto wajen Umar kan Tariyan Amina kuwa babu abunda basu yi ba ita da mai tayata din saboda kar ta tare ammh sai da ta taren sai ni kuma na karisa musu aikin na Dorata kan Tsarin dana Dora Sauran..Domin na Riga na fadamata indai ina Numfashi Cikin matan Umar ba wacce ta isa ta Haihu ya"yana basu fara Haifama mallanm jikoki ba Domin Tunda Mama ta Fadamim mallam ya son ganin Ya"yan Umar tunda yafi soyuwa wajen ya'yansa ni kuma na mike Tsaye na hana Faruwar hakan sai dai ya Mutu bai taba Haihuwa ba batula. ! Hajiya tsabar mamaki da Rudewa sai da ta Bude baki kamar sau goma tana Rufewa Jikinta yayi wani irin sanyin mamaki da al"ajabin jin kalaman Dake Fitowa Daga Bakin Uwani Duniya Haka ta lalace bata sani ba..? Kana Zaune da Mutum Tsakani ga Allah shi kuma yana nan yana Cutarka ta karkashin kasa duk da bata Fahimci wasu mganganun ba ammh ta Fahimci Daga marliyan har Uwanin basu da zuciya mai kyau sannan Duk Jirgi Daya ya kwasosu sannan abunda ya Faru jiya wannan Tsakaninsu ne sannan Daga baya Uwani ta maida abun kan Marliya..? Ashe Uwani ke zubar da Cikin Sakina..? Ita tayi ma su Nazir kurciya kin zama a kusa da mallam..? Gabadaya sai taji kanta ya kulle ta kasa wani Tunani har zata tafi ta koma Shashenta sai ta fasa so take taga Idanuwan uwani taga ko zata iya Hada ido da ita Hajiya mace ce mai Juriya da Takwalli shiyasa koda taji haka Razanan Dake zuciyarta bai nuna a saman Fuskarta ba Murya ta Bude kadan ta kara yin wata sallaman tana Fadin"Uwani ko bakya Ciki ne..? Haj.Uwani Dake waya taji kamar mganar Hajiya afalo gabanta ya fadi ko sallama bata yima Batula ba ta Datse kiran ta fito falo da Sauri har Zaninta na neman Faduwa har ga Allah sai da gabanta ya fadi data ga Hajiya Cikin Daburcewa da kinganta kinsan bata da gaskiya ta washe baki Tana fadin"Hajiya ke ce daman..? Yaushe kika shigo. ? Hajiya ta kalleta na wani Lokaci ganin yadda take zufa yasa tayi wani Mirmishi aranta tace ruwa ai ya kare ma Dan kada kuma Uwani a Fili kuma cewa tayi"Eh shigowata kenan ina ta Sallama shuru..! Ajiyar zuciyar data saki sai da Hajiya ta jita ta sauke Numfashi tana Fadin"Eh wlh ina cikin Tiolet ne Fitowa ta kenan naji sallamanki..Sannu da zuwa hajiya.. Ki zauna mana kina Tsaye..? Hajiya ta kada kai kafin tace"A"a ba zama nazo yi ba..Naga duk yau baki Fito bane shine na leko naga ko lafiya.? Haj.uwani na sosa kanta tace"Lafiya lau barci ne a idona Hajiya jiya ban samu barci ba Umaima tatashi tana ta Kuka cikin Dare..! Hajiya ta kada kai kafin tace"Allah ya Sauwake ya bata lafiya..!. Uwani ta amsa da ameen Cikin Fuskar Tsausayi taso taja hajiyar da Hira sai hajiyar tace mata tana wani abun ne bari ta koma Shashenta sai ta shigo Suka Rabu da Uwanin akan zata shigo har da raka Hajiya tana fita ta kulle kofar Shashenta lokaci Daya tana Sauke Nunfashi Fatanta Daya Hajiya bataji wayar ta da batula ba ai da aikinta na Shekaru ya rushe alokaci Daya bata ma san meyasa ta bar Falon nata abude ba..! Hajiya har ta kai Shashenta mamakin Abunda taji Uwani na Fadi bai bar ranta ba ko iya karisawa Dakinta batayi ba ta samu saman kujera afalonta ta Zauna tayi Tagumi tunani take ko Tun Zamanta da uwani tun suna Gusai tataba Cutar da ita ne..? Balle itama ta rama ta Hanyar abunda take Fadin ta aikata..? Sai taga bata samu komai ba sai Mutuntawa da girmama juna da Tarin Alherinta ga Uwani ashe daman alheri na komawa sharri..? Allah Sarki Danmallam Uwani ta Curar dashi wajen salwantar mai da Cikinsa bama ita kadai ba tace har Amina in ta samu Ciki sai yabi Rariya..To ita Allah ne..? Ta isa da taja da abunda yace ne..? Sai jikinta ya fara rawa kada Uwani ta Farga da Cikin Amina shima ta ga bayansa Domin bata da Imani Allah Sarki Nasir bawan Allah har da shima bata barsa ba..? Ba ruwansa mai Sanyi da Hakuri Duniya ma bata Damesa ba duk Cikin ya"yanta shi kadai ne tabbas maallam bai wani Damu da lamuransa ba ashe da Dalili .? Ga Nazir da ya"yansa suma din badai kaji mallam na mganarsu ba duk da yake son ganin jikikinsa a gabansa shima ashe da Dalili..? Sai dai Uwani tayi kuskure tana Takama da Boka da mallam ne su kuma Allah suka Rike ko Daya abunda tama ya"yanta bai Dameta ba don sun yi nesa da ita bashi ke nuna sun manta da iyayensu ba Bata bakinciki da Haka Tunda suna chan suna neman na kansu ne kuma tana da yakinin addu"arta garesu shi ke Tsare dasu Duk kwanan duniya sai sun kirata sun gaisheta sannan haka mallam sannan Duk wata Daga Nazir har Danmallam suna aiko ma ta da kudi hakama mallam koda basu Cikin wahala ammh Basu manta cewa iyayensu dana Hakki akansu ba ko Nasir sai dai tace Allah ya biyasa da gidan Aljannah Shi da Jafaru ga Sa"idu wh Tallahi yau ko mutuwa Umaru da Naziru sukayi bazata ce tayi kukan maraici ba Domin sa"idu da ne kamar da goma sannan ga Nasir da Jafaru da bai Taba sakawa ta Ji zafin Rashin Zaman ya"yanta Biyu kusa da ita ba ga matansu Tsakaninsu sai mutumtawa da Martabawa har ta Matar Nazir Hidiya in bata kirata yau ba zata kirata gobe ta gaisheta kuma in suka zo garin bata Sauka a ko"ina sai shashenta sai in itace tace taje shashen Uwani ko Nasara tafi ma Darajata Fiye da Sakina domin kaf Cikin Surukanta bama wacce ta raina ta irin Sakina to me zai Dameta..? Ita Allah ta rike kuma dashi ta Dogara boka ko mallam basu isa su ja da Ikonsa ba..! Zata numa Uwani da dukkan mugaye irinta su Marliya da ma wasu Boyayyin wadanda Allah bai bayyanasu ba Domin ta tsorata Ta kasa ma yarda da kowa gani take Tunda Uwani ta Cutar da ita to wanda batayi Tunani ba shima zai iya Cutar da ita kafin Su farga da Cikin Amina ya kamata tayi wani abu a matsayinta na Uwa yau dai ta cire kawaici da kunya da nuna ikonta in takamar su boka da mallan ita ta rike Allah sannan bawa bai isa yayi ma Mutum abunda Allah bai masa ba. Zata kare Amina da abunda ke Cikinta Har sai ya bayyana Lokacin da Danzaki ya girma basu isa su ga karshensa ba Umaru zai haihu Tabbas zai ga kwansa Daga Tsatso mai Daraja Tsatson Sa"idu da Hadiza ta sani addu"arta ne Allah ya amsa ta Dade tana Fatan Ganin Zuru"a mai yawa ta bangaran Umar da Amina tun kafin mallam ya Hada wannan auran Burin haka ke ranta. Zata nuna musu ba su isa ba..Allah ya Fisu sannan suna Raye za"ayi komai Da yardan Allah sun fara ganin Rashin Nasara har abada acikin Rayuwarsu sannan burikansu bazasu taba Cika ba..! Tsam ta mike Amina ta leka taga ta Samu barci kafin ta kada kai ta Shiga Dakinta wayarta ta Sake Dauka ta Kira Dannallam har alokacin yana Cikin Daki bai fito farimcikin abunda Hajiya ta Fadamai ya kasa sakinsa Tsammamin abunda baka Taba Tsammani ba wajen wanda bakayi Tsammani ba..! Sarood na falo tana ta samu barci ya lekata ya gani shiyasa ya Dawo Daki ya Zauna kawai yana ta Tasbihi da yima Allah kirari Lokaci Daya soyayyar abunda ke Cikin Amina ya shiga ransa shiga ran da ko Sakina in ta Samu Ciki bai taba jiba Fata yake da Addu"am Allah ya bar masa wannan Ciki shi kadai yake tunanin Haihuwar Amina Zai faranta ran mallam da Hajiya da Baba Sa"idu fiye da Tunaninsa alokacin Kirjinsa ke Budewa Da sunan Amina da dukkan abunda ya Faru Tsakaninsu sai ga wani Kira Daga Hajiya gabansa ya fadi ya rika Allah Allah yasa ba cewa Zatayi wasa take mai sai da ta gama Ringing sannan yabi bayan kiran. Sai a wannan karon ne Hajiya ta bari suka gaisa Cikin Yanayinta na rashin Dadi tace"Ina fatan mganar da na Fadamaka baka Fadama kowa ba ko..? Kai tsaye ya amsa mata da Eh Hajiya ta gyara Zama tana fadin"To ka min alfarman bazaka fadama kowa ba Ciki kuwa har da matanka da Sa'idu da abokinka Aliyu ko yan"uwanka ban amince ka Sanar da kowa Amina dana Ciki ba .! Cikin mamaki yace"Hajiya har da mallam..? Hajiya tace"Ni zan sanar dashi Dakaina wannan..Ta bangaranka ka bar mganar nan asirri Umar..Ban yarda da kowa ba za"a iya Cutar da Abunda ke Cikin Amina nayi alkawarin da sunan Allah zan bata kariya saboda haka kayi shuru da bakinka ..! Cikin gamsuwa yace"Na Fahimta Hajiya..Allah ya saka da alheri..! Hajiya ta amsa da Ameen ta Cigaba da Fadin"Sannan zan Dauke Amina Daga idon mutane..Saboda wasu Dalilaina bana son bayan ni dakai da mallam wani yasan da mganar Cikinta da kuma inda zan kaita ajiya har zuwa Lokacin da Cikinta zai isa Haihuwa..! Cikin mamaki yace"Hajiya ina kenan..? Kai Tsaye tace"Abuja zan kaita Wajen Aisha..Chan zata Zauna na wani Lokaci kafin abubuwa su Daidaita..! Danmallam mamaki ya cikasa sai dai baya yima iyayensa gaddama yace"Shikenan Hajiya kiyi duk abunda ya kamata..! Ta jinjina kai kafin tace"Kada ka Damu zuwa Lokacin duk zaku san Dalilina na hakan sannan zan bata Wayar nan a hannunta in ta koma chan ku cigaba da mgana ta waya..! Cikin girmamawa ya amsa mata kafin Cikin wani yanayi yace"Tana Lafiya ko..? Hajiya tayi Mirmishi kafin tace"Lafiya kalau..jiya ne ta kwana da Zazzabi shine yau mukaje asibiti likita ya auna jininta sai ga Ciki kaji abun Allah ko..?ko ni Da nike Tare da ita Allah bai bani ikon gano hakan ba..Shiyasa na yarda akwai abunda Allah ya Boye kan cikin nan na Amina..Umaru ka Dage da addu"a don Allah azkar safe da yammah da Karatun Qur"ani na yarda Bawa bai isa yayima Mutum abunda Allah bai mai ba addau"armu gareku bazata taba Faduwa kasa banza ba duk Salolinka kada ka manta da Rokar ma Amina Tsarewar Allah da ita da Abunda ke Cikinta kaji ko..? Sai duk jikinsa yayi sanyi da kalaman Hajiya duk da tana yawan fada musu su dage da Addu"a ammh na yau na Dabam ne Cikin Sanyinsa ya amsa mata ta Dinga sakamai albarka kafin suyi sallama tace Zata kirasa in sun yi mgana da mallam zuwa gobe take son ta kai Amina Abujar bazata ba ta Lokaci ba. Bayan ta gama mgana da Danmallam Nazir ta kira suka gaisa shima abunda tace ma Danmallam tacemai shima sai yaji wani iri Hajiya kamar tana barin Wasiya suna gama waya ya Kira Danmmallam a chan madina yana Tambayansa ko sun yi waya da Hajiya yace eh sai yake tambayansa ko ta yimai nasiha da rokom ya Dage da addu"a yace eh sai nazir ya fara Tambayansa ko Hajiya bata da lafiya ne ya Tabbatar mai da lafiyanta kalau sun Dade suna tattaunawa kafin su rabu kan Shi Nazir din ranar Lahadi zai zo yaga Hajiya ya koma saboda Hajiya is d Best mother in d word. Bashi ba ko Hidiya na Fadin bata ga Uwa kamar Hajiya ba mai kirki mai kawaici sai ta kirata sau goma su gaisa bata kira dan data Haifa ba Tunda suke da Hajiya sai dai ta Bisu da addu"a bata taba Saka ido kan samun su ba bata taba tambayansu wani abu ba sai dai su Dauka su bata ta amsa tana godiya tana saka albarka ita da Mallam samun a iyaye is a Bleesing basu taba Dogara ga abun hannun ya"yansu ba sai dai su bisu da saka albarka da addu"an nasara. Hajiya kuma suna gama mgana da Nazir ta shiga wanka Saboda tana sauri suka Fita asibiti bata Tsaya yi ba tana fitowa taga wayarta na Haske tana Dubawa taga Mallan ke kiranta ta Dauka sukayi mgana yace mata ya Dawo tace mai gatanan zuwa Daman shi take jira,Mai ta shafa ta shirya Cikin wani sabon less din da Mijin Aisha ya Dinkamata suka aiko mata dashi har da mallam ma sun dinkamai shadda ganin Dattakon Mijin Aisha da kuma sanyin Aishan yasa ta Zabi ta kai mata Amina ta Zauna awajenta tasan zata kula da ita sannan kuma ba wanda zai san tana wajenta indai ba ita Hajiyan ta Fadama wani abu ita kuma tayi alkwarin bama Amina da abunda ke Cikin kariya da ikon Allah..! Kitchen din Shashenta ta shiga ta Dora ma Maallam Ruwwn Tea dinsa Datake dafamai na Sassaken mganungun Musulunci mganin sanyi ne sai da ya tafasa ta Juyemai a Fulas Ta Dauka da kofi saman wani katon Faranti ta fita zuwa Kitchen din Tsakar gida suka gaisa da su Lami taga Doya suka soya sai Miyar albasa da sukayi ta Diban ma mallam din ta Nufi Shashenta ahanya ta Hadu da Anty Amarya ta Dawo daga wajen mallam din Fuska kozai kozai kamar wacce tatashi Daga jinya sama sama Hajiyar ta Tsaya suka gaisa ta wuce Anty Amarya ita kanta sai da ta Bita da kallon mamaki ganin yanayin Hajiya na yau din da bata taba gani ba ,ko Sakina bata tambaya ba akwanakin nan kuwa ko bata shiga ba in suka Hadu sai ta tambayi Jikin Sakinar sai ta Danganta hakan da abunda ya Faru Jiya Uwani ai tatashi Wasa da ita yanzu ma mallam taje kara bama Hakuri har ya Sallameta bata samu wani kyakyawan kallo Daga garesa ba. Ta bi shawaran Dayyaba ta kira mallaminsu ta gayamai yayi mata mganin Uwa sannan ta sanar dashi ya Dakatar da Barin Cikin da Sakina take yi yace zai kirata nan da kwana uku ta Saurareshi,so take kafin Lokacin ta Samu mallam ya kalleta da kallon yafiya da kauna sai abun da yazo mata da Sauki ammh kalli fa mallam ko son ganinta bayayi ai Uwani ta gama Cutar da ita..! Hajiya koda ta shiga Falon mallam yana zaune yana nazarin Wani Littafin labarci ya amsa mata sallamanta ta shigo ta ijiye farantim Hannunta ta Zauna gefensa suka gaisa Ya tambayeta jikinn Amina tace da Sauki ya karya Tukunnah sai suyi mgana Littafin hannunsa ya ijinye ya Sauka kasa ya Tankwashe kafa ta Zubamai ya fara ci Hajiya na gefe tana kara Nazarin shawaran data yanke tana fatan Allah yasa mallam ya yarda da Tsarinta kada ya matsa sai yaji Dalili duk da awajensa ya"yansa suka Dauko Rashin son jim abunda ba"a so su ji ba Suma haka suke basu da yawan Tafiya ballatana Bin kwakkwafi. Sai da ya gama sannan ta tattara komai ta matsar gefe ita ko yunwar bata ji Cikinta ya Cushe da yanayin Data ke Ciki shima mallam din kallonta yake yi Cikin wani yanayi yace"Zainabu Fuskarki ta bayyana Damuwa..? Me yake Faruwa ne..? Hajiya ta Sauke Numfashi kafin ta mike tana fadin"Mganace dani mallam mu shiga ciki..! Yayi mamakin jin tace su shiga Ciki bai mata musu ba ya tashi yabi bayanta zuwa Cikin kuryan Dakinsa abunda ya basa mamaki suna shiga ta Sakayo kofa shidai yana binta da kallo ta Dawo ta Zauna agabansa asaman Katuwar Dardumar Dake Dakin. Cikin ajiyar rai tace"Mallam Munje asibiti likita ya Dibi Jinin Amina an aunata kuma yaga Ciki wanda yakai kimamin Wata Hudu da kwana goma ajikinta..! Mallam sai yayi mata kyar yana kallonta na tsawon Lokaci kafin kawai ya saki kabbara..! "Allahu akbar..! "Allahu akbar..! "Allahu akbar..! Sai da ya maimaita sau uku sannan Cikin Tsantsan Farinciki yace"Kin gani ko Hajiya..? Allah shi kadai yasan Lamarin Daya Boye kam Mamana da Umaru ...Kai wannan labarin Farinciki ne Hajiya Masha Allah ina mamar tawa fata Dai Likitan yace ba wata matsala ko..? Hajiya tace"Ba wata matsala..! Mallam na jinjina kai Cikin Farinciki yace"madallah..Allah ya inganta Allah ya Bata lafiya ya zaunar dashi Allah yasa ta Sauke lafiya..! Hajiya ta amsa da Ameen Mallam yaga yanayin ta wani a sanyaye yasa yace"Hajiya naga bakya murna ne..? Ko da wata matsala ne..? Sannan ya kamata a Fadama mijinta..! Hajiya tace"Na fadamai..! Cikin mamaki yace"kin fadamai fa kikace..!? Ta gyada kanta kafin tace"Eh mallam..Kuma na rokesa bayan ni da kai da shi ko Sa"idu bazai ji labarin Cikin nan na Amina ba mallam..! Mallam ya kalleta yana fadin"Bangane ba.? Hajiya ta gyara Zama tana fadin"Ina da Dalilina mallam..Bana son cikin nan na Amina ya fallasa..Daga ni sai kai sai Danmallam shima don yakamata ya sani ne tunda shine Uban cikin..Mallam kamin wannan alfarman cikin matanka ba wacce Zata sani ko Sa"idu kada yasani mallam Don Allah..! Mallam yayi shuru kafin yace"Duk naji Toh ammh meyasa kika ce haka..? Miye Dalilinki..? Hajiya tace"Zaka ji Dalilina ammh ba yanzu ba sai nan gaba Dalilin nawa zai bayyana kansa.. Mallam yayi shuru kafin yace"To sai yaushe Sa"idu zai sani..? Balaraba fa..?bai kamata ta sani ba makafin uwa take ga mamana fa..? Hajiya taji har Balaraban yanzu bata da yarda da ita ba yasa ta girgiza kai kafin tace"ya kamata ta sani..ammh a wannan gabar itama bai kamata ba mallam..Nidai kayi hakuri akwai Lokacin da zan fada maka Dalilaina nayin haka sannan zasu sani in lokacin su sani yayi..! Mallan ya tari numfashinta da Fadin"Yaushe kenan..? Hajiya ta kallesa Cikin ido kafin tace"Kafin abunda ke Cikinta ya Fito Duniya..! Ya kalleta yana mamakinta meyasa Hajiya tace haka sai kuma yaga bazai iya Ture alfarmanta ba. Yasa ya jinjinamata kai kafin yace"Shikenan..! Hajiya tace"Ba shikenan ba..Alkawarin zakamim ba wanda zai ji sannan kuma ina so na Fada maka zan Dauke Amina Daga gidan nan zan kaita inda zata yi Renon Cikinta har Zuwa Lokacin da zai bayyana kansa shima bayan ni da kai da Danmallam ba wanda zai san inda Amina take..! Mallam ya fara Tunanin da wani abu Cikin mamaki yace"Ina zaki kaita..!? Kai Tsaye tace"Gidan Aisha Abuja..! Mallam yace"Aishan ce zata iya kula da mai Ciki..? Nawa take ko itama ta Haihun ne bansani ba..? Hajiya tace"Ko Daya bansani ba ko tana da Ciki ammh ina da Dalilina na kaita Chan din ni na Haifi Aishan nasan Halinta Zata kula da Amina Sosai kuma ba ita kadai bace agidan yanzu akwai kakar megidanta da tadawo gidan da zama kaga kenan zata Tayata kula da Amina da abunda ke Cikinta..! Mallam ya kalli Hajiya ya kara kallonta kafin yace"Duk me ya kawo wannan..!? Sannan in tatafi karatunta fa kin san fa sun kusa fara jarabawar da kika matsa na Biya mata ita da yan"uwanta sannan mijinta ya kusa zuwa ya Dauketa kamar yadda kika basa Umarni..! Hajiya tace"yanzu ba lokacin karatu bane..Ta Haifi abunda ke Cikinta Lafiya sai komai ya Biyo baya mallam..! Zai yi mgana ta Riko hannayensa tana Fadin"Don Allah mallam.! Idonta sai ya ciko da kwallah gani take in tayi wani Sakaci Amina Zata Shiga wani Hali..ganin haka yasa ya Jinjina ma Hajiya kai kafin yace"Naji na amince mijinta fa..? Kinsan bazaki Dauke matarsa bai sani ba ko..? Sannan ita Aishar ai ba ita keda kanta ba An nemi izinin mijin nata..? Hajiya tace"Danmallam bai da matsala na Fadamai ya amince Megidan Aisha kuma Usman kai ne zaka kirasa kai mai mgana nasan ma bazai ce konai ba ni kuma zan kira Aishar na Fadamata komai zuwa gobe nake so mu tafi..Kada ka manta mallam iya ni dakai da Danmallam ko Sa"idu kar ya sani ballatana Sauran yaran don Allah..! Mallam bai da tacewa illah gyada kai kafin yace"Shikenan nayi alkawari..Zan kira Usman din muyi mgana..Allah yasa hakan shi yafi Zama alheri bazan ja da mganarki ba Domin baki taba aikata wani abu Sabanin Tarbiyan gidana ba na baki Dama ki kula da Mamana da abunda ke Cikinta Allah ya raba su lafiya..! Cikin jin Dadi Hajiya ta amsa da Ameen Ameen sannan ta mike tana Fadin"Nagode mallam..Ka taya mamarka da addu'ar Allah ya Tsareta ita da abunda ke Cikinta ya rabata da Sharrin mugum mutum da aljan..! Wannan karon bai boye mamakinsa ba sai da yace"Hajiya kodai wani abu ya Faru ne..? Da Sauri ta girgizamai kai kafin tace"Ko Daya..Kasan duniyar ne ta lalace..Ba kowa ke zaune dakai don Allah ba..Sannan ba kowa ke son ganin cigabanka ba. ! Daga haka ta Bude Dakin ta fice ya Bita da kalli yana kara nazarinta aransa yana Tunanin me ya faru..!? Hajiya bata Cika irin wannan mganar ba.? Tabbas wani abu ya faru sai dai bazai matsa mata sai yaji ba yasan ta bata aikata wani abu bata da Dalili mai karfi shiyaasa zai bata goyon baya insha Allahi zai kuma taya Amina da addu"a kamar yadda tace Duk da bai taba gazawa da mata addu"an shirya da Daidaituwa Tsakaninta da Umaru ba..! *Bakina yayi kadan wajen nuna godiyata ga masoyana..Nagode kwarai da gaske ina ganin Addu"o'in ku gareni Yadda kukemin Fatan Alheri nima ina bin ku dashi Godiya ta musamman ga Masoyan da suka siya wannan Littafin Allah ya rubanya muku da Alheri Allahu ya bar zumunci Ameen..* *Janafty* *TFZB2016* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* Hajiya Shashenta ta koma cikin wani yanayi,yanayin da take ciki tun Lokacin dataji wayar uwani da kanwarta,wani irin dakiya da kwarin gwiwa tare da yakinin babu wani mai yi sai Allah ne suka shigeta. Ta samu sukuni da sukayi mgana ta Fahimta da mallam yanzu zata jira har ya Kira shi Usman din mijin Aishar duk da tasan ba matsala Aisha kuma sai sun isa goben zata mata bayani haka kurum taji Hankalinta ya kwanta da Aishar saboda tana da bambamcin Hallayar da sauran sannan Halinta kamar Halin Danmallam ne, bata da Hayaniya ballatana yawan surutu. Ta yi ta leka Amina tagani ko tatashi bata tashi ba sai wajen sha biyun rana Data Sake lekata ta ga ta tashi Hajiya da kanta ta shiga Tiolet ta Hada mata Ruwan wanka ta taimaka mata ta shiga tayi wanka bayan ta fito ita ta Dauko mata wata Doguwar riga ta saka Duk ta rame ta wuya idanuwanta sun kumbura kadan Saboda kuka. Tea Hajiya ta sake hado mata da sauran Doyar da suka karya dashi da Safe,Kadan Amina taci Doyar Tea din ta Shanye duka domin cikin jikinta na son shan Tea musamman ma Dayake akwai madara aciki. Sai da Hajiya ta barta ta natsu sannan ta Dawo domin tayi mgana da ita Amina na Zaune Saman Cafet ta jingina da gadon Hanne tana maida numfashi Lokacin da Hajiya ta Sake shigowa Amina kuka take yi domin bata Zaman mintina goma bata tuna da Yaya ba da irin yadda mamanmu ta Dai'dai'ta Rayuwarsu. Tana ganin Hajiya sai tayi Dubara ta share Hawayenta,Bata sani ba Hajiyar ta gani ammh sai tayi Tunanin Sabida yanayin datake Ciki Domin abubuwa sun faru ne duka Tsammanin abunda basu yi Tsammani ba dukkansu. Gabanta Hajiya ta Zauna ta Tankwashe kafa Amina tana kokarin gyara Zamanta Hajiya ta Dakatar da ita da fadin"A"a mamah yi zamanki..! Kanta ta maida kasa domin kunyar Hajiya take ji. Hajiya ta kalli Amina Lokaci Daya ta Kira sunanta ta amsa jin muryan Hajiya Daga gani mganace a bakinta. Hajiya ta cigaba da fadin"Amina ina so kiyi hakuri ki kuma Dauki Rayuwa yadda tazo miki. domin bawa bai isa ya Zabama kansa wata Rayuwa ba illah wacce Allah ya Zaba masa..! Amina dai batace komai ba Hajiya ta kara Gyara Zamanta tacigaba da Fadin"Ina so na fada miki..Gobe zamu Tafi Abuja gidan Aisha chan zaki Zauna kiyi Renon Cikin ki Zuwa wani Lokacin..! Amina ta Dago da mamaki tana kallon Hajiya kafin tace"Hajiya gidan yaya Aisha..? Hajiya ta gyada kai kafin tace"Nan Amina nasan zaki yi ta mamakin meyasa haka..? Ina da Dalilina Amina akan hakan Dayasa bazaki zauna anan ba..Sannan bana so kowa yasan da mganar Cikin ki Mamah ko Hanne da Hamida ne kada ki Fadama kowa sannan shima Batun Tafiyarki ban ce ki sanar dasu ba..In na Dawo goben Daga kai ki Zan musu bayani bana son koken koken nan naku..! Kiyi hakuri Jarabawarki bazaki yi ta yanzu ba sai in kin haihu nayi miki alkawarin karatu zaki yi shi har sai kin gaji..Danmallam ma bazai taba Tauye miki Hakki ba..! Amina sai ta fara Tunanin ko Hajiya tasan wani abu ne kan mamanmu da Anty Amarya..? Sai dai bata ga wani alama ba,Ita yanzu zata iya yin komai Saboda Cikin jikinta sannan Zatayi komai Saboda Tonama mamanmu asiri da Anty Amarya kuma Cikin jikinta ne makami shiyasa bayanin Hajiya bai Dameta ba Hawaye suka kawo Idanuwanta in ta tuna Shekarun data kwashe bata san Dadi da muhimmancin Uwa ba,Gashi yanzu tana Cikin wani Siradi,Siradin da uwa ce kadai Zata tallafamata sai dai ina Mamanmu ta yanke wannan abun Saboda son zuciyrta da kuma Mugunta da zalunci. Ganin Tana Hawaye Yasa Hajiya tayi Tunanin Rabuwa da su hanne da karatunta yasa ta saka Hannu ta Rumgumo Amina kan kafadarta Tana Lallashinta Lokaci Daya tana Fadin"Kiyi hakuri Amina..ki daina kuka na dan Lokaci ne watarana sai Labari..! Amina na Shesshekan kuka tace"Hajiya ba ina kukan hukuncin ki bane.. Ina kukan rashin yaya ne..ayau bata a Duniya ina jin matukar kewarta..! Hajiya Tsausayinta ya kamata ta Dagota tana share mata Hawaye lokci Daya Tana fadin"In kin Tunata ki mata addu"a kin ji ko..?.Sannan in kin ji kewarta ki tuna Dani Domin tamkar Uwa nake gareki ina nan Saboda ke Amina ni ba Uwar Umar nake ba Har Abada ni ina matsayin mahaifiya gareki ne nayi kuma alkawarin Kareki da yardan Allah ke da abunda ke Cikin ki..! Tana Fada tana share mata Hawaye wasu na Bulbulowa Hajiya fadi take"ki daina kuka nasan zaki ji Dadin Zama da Aisha na dan Lokaci ne Zaki Dawo in Lokacin hakan yayi.! Amina ta gyada kai tana Fadin"Hajiya ke da mallam nasan har Abada bazaku kai ni inda Zan cutu ba..Sannan duk abunda kuka Zartan kan Rayuwata ina maraba dashi..Na yarda da Hukunci ku kuma Insha Allahu Zaki Sameni mai Bin Umarninki..! Hajiya taji Dadin haka ta Dinga shafa kan Amina ta saka mata albarka kafin ta mike tana fadin"Kayan ki duk suna gida ko..? Amina tace"Eh akwai wasu anan hajiya..! Hajiya tace"To ai ba kaya da yawa Zaki Diba ba nan gaba ma kadan zasu yi miki. Sai ta Dinka miki wasu achan kawai..! Har Hajiya ta Fice Daga Dakin Amina bata kara mgana ba,wani irin Dakiya ne da Taurin zuciya ke shiganta da kwarin gwiwan da bata san tana Dashi ba Duk da tasan zatayi kewar su hanne da makaranta ammh Gaskiyan Hajiya ne datace na dan Lokaci ne watarana sai labari. Daya da wani abu na rana su Hanne suka Dawo sun ji dadin ganin Amina taji Sauki basu damu da yanayinta ba sun Dauka saboda bata da Lafiya ne ita kuwa kallon su kawai take yi Tana Tunanin sai dai suga Hajiya ta Dawo ita kadai zasu yi kewarta kamar yadda itama Zatayi kewarsu Hamida kuma Tsausayinta take ji domin in ta kalletasa sai taji kuka ya taso mata ya Zataji in taji Abunda mahaifiyarta take aikatawa..? Bazasu iya Daukan wannan abun ba su take Tsausayi domin ba d'an da zai so uwarsa ta kasance bata gari ba abun akwai taba Zuciya ammh Dolen wata watarana Allah ya Tona musu asiri kamar yadda ya Fara Tona musu awajenta. Kamar sun san Amina zata koma wani wajen Ranar wuni sukayi tare ko Hamida bata ko leka gida ba suna Tare har Dare,Da mallam ya shigo har Shashen Hajiya ya Dubata ya Dafa kanta yana fadin"Allah yayi miki albarka..Allah ya Saukeki lafiya ya kareki mamana..! Ta amsa kanta na kasa kafin ya Sake fadin"Kina tsorata Cikin barcin ki har yanzu ko kin bari..? Amina tace"Yayi sauki baba..! Malam ya jin jina kai yana Fadin"Zai bari gabadaya ki Dage sosai ki Daina kwanciya ba alwala sannan ki Rike addu"o"in nan da yawaita karatun Qur"ani..! Amina ta amsa da toh ya Dade yana mata Nasiha kafin ya fita,Dakin Hajiya ya shiga sukayi mgana ya Fadamata ya Kira Usman mijin Aisha yace ba wata matsala sannan bayama gida yana Lagos,Daganan sukayi mgana sama sama kafin ya fice Daman shi da Aba suka shigo shima ya shiga ya gaida Amina bai Dade ba shima ya fita Amina bata Damu ba Sai ma wani Tsausayinsa Daya kamata Mace tatasa shi gaba da makircinta. Mallam nan ya bar Aba Hajiya tamai mganar Zata kai Amina gidan D'aya Daga Cikin yaran nan tadan koyi wasu abubuwa tunda ga yanayin yarintarta bata koyi wasu abubuwa ba sannan nan da Lokaci kadan Danmallan zai zo ya tafi da ita madina.. Aba bai Tambayi ina Za"a kai Amina ba Sai kawai yabi Hajiya da godiya yana komawa gida ya Fadama mamanmu yadda sukayi da Hajiya anan nema take jin Amina bata da lafiya Mamanmu dataji haka shewa ta Saki aranta tace auran da Zai kare a gantali ne za"a je koyon zama da Miji..!? Shiyasa kwata kwata bata Damu ba,ita Atunaninta Wahalar da kai kawai Hajiya take yi ammh Amina da Umar ai sai hange Daga nesa ammh a fili sai ta nuna Tasauyawanta da cewa da Safe zata shiga ta gaida Ameenan kafin su tafi ko aranta bata Damu da Sanin ina Hajiya zata kai Aminar ba wannan baya gabanta yanzu. Adaran Hajiya Ta kira Aisha tace gobe tana nan tafe Aisha taji mganar kamar Daga sama murna ta Cikata Dayake Usman din bai riga ya Kirata ya Fadamata ba Hajiya ta rigasa sai taga kamar ta zama mai sa"a domin Hajiya basa zuwa gidan mutum hakanan sai da babban Dalili ammh ita yau gata Hajiya Zata zo gidanta Murnan ta ya kasa Boyuwa suna gama mgana da Hajiya ta tafi Dakin kakar mijinta Dake zaune tare Dasu da suke Kira Yakaka ta sanar da ita Hajiyarsu na tafe gobe. Har gari ya waye su hanne basu san komai ba da Safen dai Hajiya tace ma Hanne zasu fita da Amina su shirya su tafi hadda sukace to basu yi wani tunani ba, sai sukayi Zaton Ko asibiti zasu koma basu damu ba. Ammh Sanda suke shirin tafiya Amina na kwance na kallon Hamida na shiryawa ta fito wanka aran Amina tana tunanin Hajiya zata zame ma Hamida uwa kamar yadda ta Zame mata uwa,Idonta ya kawo ruwa in ta Tuna zatayi nesa dasu saurin share Hawayenta tayi ta kira sunan Hamida bata Damu data waigo ba ta amsa mata. Amina tace"Hamida don Allah ki kula da Jawaad..! Hamida sai da ta saka Rigar wata atamfar dake jikinta sannan ta Juyo jin abunda Aminar tace da yanayinta yasa Cikin mamaki tace"Wasiya kika fara bari ne Aminene .!? Amina tayi Mirmishi tace"Eh mana kinsan Rayuwa haka ta gada..muna tafe ne bamu san muna tafiya da mutuwarmu ba .! Hamida ta fara Dariya tana Fadin"Lalle Amina ta fara Tunanin mutuwa..Hanne tazo kiji..Hanne. ! Ta shiga kwalama Hanne kira sai gata ta Dawo da Faratin kayan karinsu tana Fadin"Kiran me kike min hamida kamar kin bani ajiya..? Hamida na Dariya tace"Amina ce ta fara barin wasiyya..! Hanne ta ijiye abun hannunta saman Cafet tana kallon Amina Lokaci Daya tace"Topa ta fara Tunanin mutuwa ne..? Ko azara"ilu ta gani..? Ta fada tana yar Dariya Amina ta balla musu harara tana fadin"Bansani ba. kufa yan iska ne baku san abun arziki ba.! Hamida tace"Mu ko ke ne bamu san abun arziki ba..? Ke Amina uban wa ya kaiki maida abun arziki na fada ma. ! Hanne ta Zauna tana Fadin"Ki zauna mu karya hamida kada mu makara..Amina inaga asibiti zasu koma da Hajiya. ! Hamida tace"Shiyasa ta fara barin wasiyya kenan. ! Duk tana jinsu batace musu komai ba illah tasowa da tayi tace su karya Tare harda Jawaad daya shigo yanzu gabadayansu suka karya suna yi suna Hira Amina tana tunanin shine na karshe Zaman su tare Indomie ne sai soyayyan kwai da Tea Amina kwan taci ya taso mata da zuciya sai da tayi Amai ta koma ta kwanta tana maida Numfashi su Hanne na mata sannu da Zasu tafi haka taji kamar ta Bisu har suka fice tana musu bye bye suka fita Suna Dariyanta wai Amina ciwo yasa ta fara Tunanin mutuwa Basu san cewa Amina Zatayi nisa da su na wani dan Lokaci ba..suna fita ta Fashe da kuka sai da tagaji tatashi ta rarrafa tayi wanka sai a yanzu da aka Tabbatar tana da Ciki take jin wani Sauye Sauye ajikinta na masu juna Biyu. Ta shirya Cikin Riga da zani na kayan da Hajiya ta Dinka musu ita da Hanne da Hamida abunda yasa ma rigar tayi mata daman tun farko dinki yayi mata yawa saboda Sizes din Hamida aka mata kuma tun Lokacin ba"a rage kayan ba Ta yi shirinta da wuri ne Sabida Hajiya tace da wuri zasu tafi Tunda ita ayau din zata Dawo. Yan kayanta Dake nan kawai ta Hada kala uku sai Azakar da addu"o"in da mallam ya Rubuta mata' sai mangunanta,wasu kayan nata suna gidan Aba wasu kuma suna gidan ya Danmallam bata kwaso duka ba,Zama ta yi kawai tayi Tagumi tana Tunanin yadda Sabuwar rayuwa zata Bude mata ita da abunda ke Cikinta tana tunani tana Hawaye sai ga Hajiya ta shigo tayi saurin goge hawayenta saboda kada ta gani ashe ta gani sai bata nuna mata ba Kallonta tayi tana Fadin"Mamah kin gama shiryawan .? Amina kanta na kasa tace"Eh Hajiya ina kwana..? Hajiya ta amsa tana fadin"To kin kar ya kuwa..? Ta gyada mata kai tana Fadin"Eh hajiya..Tare da su hanne muka karya. ! Juyawa tayi ta Fice tana Fadin"To bari Idi ya dawo kai su makaranta sai mu wuce..! Fitan ta ba Dadewa ta Leko tace ma Amina ta fito Dogon Hijabinta ta Saka Jakar data Hada kayan nata Hajiya ta karba ta farayin gaba itama ta shirya Tsab da ita,Hajiya na gaba tana Binta abaya har falon Mallam suka gaisa ya kara mata Nasiha sai ga Idi ya Dawo Hajiya ta mike tace zasu tafi mallam yace"Ko in kira Sa"idu ne su yi sallama..? Hajiya tayi shuru kafin tace"kyalesa kawai ai na Fadamai jiya.. Mallam bai kara mgana ba shi ya rakosu har bakin mota sai ga Hajiya Nasara ta fito domin ita ke da Turakan mallam jiya ganin Hajiya da Amina yasa tace ko anguwa zasu je Hajiya tace eh ba Dadewa zasu yi ba mallam dai na gefe bai ce komai ba domin yayi alkwarin bazai ma Hajiya kaladan kan abunda ta Tsara ba ya yarda da ita fiye da duka matansa bazata taba aikata ba Daidai ba. Agaban idon Hajiya Nasara da Mallam Suka fita Daga gidan idi ke jan su a Motar mallam din prado baka suka Dauki Hanyar Abuja Amina na ta sharan kwallah Hajiya na kallonta batace komai ba Domin bazata hanata ta koka ba. Su hajiya basu yi nisa ba,Aba ya fito zai Tafi gidan gona mallam ke Fadamai su hajiya sun tafi yayi mata Fatan Dawowa lafiya bai Dade ba gaiswawa kawai sukayi da Mallam ya shiga Motarsa ya tafi bayan tafiyarsa sai ga mamanmu ta shigo gaida Amina da Haj.Nasara ta fara Cin karo ita ke shaida mata Hajiya sun fita da Amina mamanmu bata Damu ba aranta tace agayas ayasha ta gaida ayyah..! Shashen Anty Amarya ta shiga ta Duba Sakina sannan suka kule Daki suna Kulle kullensu da suka saba mamanmu ke fadama Anty Amarya Abunda Aba ya fadamata Hajiya ta Sanar dashi kan Amina da Tafiyar tasu yau. Anty Amarya ta tabe baki Tana Fadin"Ko shiyasa Daga jiya zuwa yau take wani Shan kamshi..ko Sakina ta Daina lekota su gaisa. ! Mamanmu tace"Yau she kuwa..? Tana chan tana shirin kaita inda Zata kwace miji..!. Anty Amarya tace"Aikin banza ne wannan..Ai Danmallan din yana Tafe nan da wata Biyu in ya Dauki Sakina suka koma ai sai naga karyan koyon kula da miji..! Wai ina ma Zata kaita..? Mamanmu tace"Oho ni dai yace min Gidan Da'ya Daga Cikin yaran mu..! Anty Amarya tace"Ni ba ma wannan ne agabana ba Dayyaba..Mallam nake jira ya Kirani so nake ayi ma Sakina mganin abunda uwani tayi mata Datake bari in aka gama da wannan bangaran mganinta bamai matsala bane..! Mamanmu tace"Ai Allah dai ya Tsine ma Uwani..! Anty Amarya tace"Amin matsiyaci ce..Ta gaban anuna ma jarida. ! Nan suka Cigaba da Tattauna yadda zasu Taru suyi mganin Uwani hankali kwance in sun gama da matsalan Sakina suna ganin Amina bata gabansu.Suna ganin ita karamar alhaki ce bata isa ba yanzu. Abunda basu sani ba wanda bai isan ba Allah yafi nuna isarsa akansa sannan alokacin da Uwani ta Dauke musu hankali Dan Zaki zai girma sannan Tsammanin abunda basu tsammani ba zai faru..!. ***** Abuja..! Misalin karfe Shadaya na rana suka isa gidan Aisha Dake maitama Abuja Kwatsam sai dai ta ga Hajiya abun Farincikin ma harda da Amina Aisha ta kasa Boye Murnanta ta Daka Tsalle ta Rumgume Hajiya sannan ta rumgume Amina Hajiya ta kalleta tana Fadin"Ki mata a hankali bata jin Dadi..! Sai alokacin Aisha ta Lura da yadda Amina tayi kiba Sannan Fuskarta ta Kumbura,haka ta jasu falonta Cikin murna tana da yar aiki wata yar matashiya ita ta cika gabansu da Kayan Taba ka Lashe,Amina sai Bin Gidan ya Aisha take da kallo mai kyau dashi. Aisha ta rasa ina Zata saka su Hajiya Saboda Murna Hajiya ta kalleta tana Fadin"Aisha to ki Zauna mana..!. Ta Zauna gefen Amina tana Fadin"Hajiya murna ce..Ga ki ga Amina. Hajiya ta yi mirmishi kafin tace"Yanzu dai ba wannan ba. ki sama ma Idi waje yaci abinci ya Huta kafin mu tafi..! Da azama ta mike tana amsa ma Hajiya yar aikinta mai suna Saude ta ma mgana taa shiga da Idi Dakin Baki na waje tazo takaimai ruwa da abinci. Tana Dawowa tace ma Hajiya"Hajiya Zaku gaisa da yakaka kakar Usman. ! Hajiya tace"Zan shiga mu gaisa Aisha kada ki damu..! Aisha ta koma ta Zauna kusa da Amina tana Fadin"Aminene ikon Allah Amaryan ya Danmallam ya naga kin yi Shuru ne bakya mgana..! Nice fa ya Aisha..? Ko bakin ya mutu ne basu Hamida..? Amina tayi Mirmishi ta gaisheta ta amsa tana Fadin"Amina kinyi Kiba Lokacin Bikin su Abida kina lange Langenki fa..! Hajiya tace"Na sanar Dake bata da Lafiya ne Dalilin zuwana ma kenan..! Aisha tace"Eh usman ya Fadamin sunyi mgana da mallam..Dama Amina ce Zata Zauna damu Hajiya..? Hajiya sai da ta gama shan ruwa sannan Ta gyada mata kai Aisha ta Zaro ido kafin tace"Hajiya ba ta tare gidan ya Danmallam ba..? Ko ansamu wata matsala ne .? Hajiya ta mike tana Fadin"Mu je Ciki mu yi mgana..Amina kici wani abu kafin mu gama. ! Ta daga ma Hajiya kai Aisha na gaba Hajiya na bayanta har bedroom dinta Gefen gado suka Zauna Aisha Duk ta Tsorata fatanta kada ace auran ne ya Lalace. Hajiya ta kalleta tana Fadin"Kada ki damu ba wata matsala bane..Auran su na nan sannan da sanin shi Danmallam din da Mallam kanshi na kawota wajenki. ! Sai alokacin Aisha ta ji sanyi Tace"Hajiya har gabana ya fadi na Zata ko wani abu ne ya samu auran nasu..! Hajiya tace"Ko Daya..Sai dai matakin dana Dauka duk saboda Kara Karfafa auran su ne Aisha..Ina mai Sanar Dake Amina na Dauke da Cikin yayanku har tsawon wata Hudu da kwanaki. ! Aisha ta zaro ido kafin tace"Ciki Hajiya..Aminar..? Kai ta gyada mata tana fadin"Kwarai kuwa baki ga alama ba ko..? Aisha ta washe baki tana Fadin"Bangani ba Hajiya sai kibar Data kara..Alhamdulillah na taya ya Danmallam Murna daman ga Sakina na ta samun bari Allah yasa na Amina ya Zauna ta sauka lafiya..! Hajiya ta amsa da Ameen kafin ta Kira Sunan Aisha ta amsa mata Cikin bada Hankalinta ganin yanayin Hajiyar. Hajiya tace"Aisha na yarda Dake kaf Cikin ya"yana shiyasa na Zabi Amina ta Zauna agidanki ki kula da ita ta Reni Cikinta na wani Lokaci Sannan na zabe ki saboda baki da Surutu achan gida dagani sa mallam sai Danmallam muka san da Amina nada Ciki sai ke yanzu sabida haka ina so ya Zama sirri Tsakanina Dake..Ban so wani yaji labarin Cikin jikinta ballatana labarin tana wajenki Shima ba wanda ya sani Harta ko da Sa"idu da su hanne basu san komai ba.ki kama Bakin ki koda tambayarki akayi kice baki sani ba Dani kadai zamu Dinga mgana in wani abu ya taso kina jina..? Aisha ta gyada kai Cikin mamaki Hajiya ta Cigaba da Fadin"Nasan Zaki yi mamakin meyasa nayi hakan..!? To ina da Dalilina ammh ba yanzu zaku sani ba sai nan gaba..Fatana ki kula da ita don Allah da abunda ke Cikinta sannan ki koyamata Girke girke da Sauran Kissa na mata Amina haka tataso Sakaka ba wani abunda ta iya Kinsan Tana da abokan zama dole sai ta kara wayewa kan wasu abubuwan..! Aisha tace"Insha Allahu Hajiya Zan yi Duk yadda kikace Sannan zan rike Amina kamar yadda Zan rike Hanne .! Hajiya taji Dadi ta Dinga saka mata albarka sannan tace tatashi ta Rakata Dakin kakar mijin nata su gaisa. Tare da Amina Hajiya tace suka shiga Dakin da Yakaka take Zaune Yar Dattijuwa kamar zata girme ma hajiya hutu ne da jin dadi suka boye girmanta ta amshe su da Fara"a tana Fadin bata son zuwansu ba,da ta fita sun gaisa Tana nan tunda ta idar da sallar walha bata matsa ba..Hajiya tace bakomai suka gaisa sai kallon Amina take yi Hajiya ta mata Bayanin kanwa take wajen Aisha tana da Ciki zata dan Zauna na wani Lokaci Tare dasu ta karishe da Fadin"Hajiya don Allah a kula..Daga Aishar har Aminan yara ne suna karkashin kulawarki Hajiya ga Amana nan..! Yakaka na kallon Amina tace"Insha Allahu Hajiya..Na karba zan kuma kula da ita..Allah Sarki gata yarinya karama Allah ya bata..To Allah ya Rabasu lafiya..! Su Hajiya suka amsa da Ameen Amina ta gaisheta ta amsa Cikin Sakewa tana da Sakin Fuska ga Fara"a nan da nan Hira ta barke tsakaninsu da Hajiya Har Aisha taja Amina suka fita ta nuna mata Dakin dake kusa da na yakaka nan takai mata kayanta Tace nan zata Zauna Daki ne babba mai katifa a kasa sai Cafet da Tiolet aciki Dakin ya Hadu sosai. Nan Aisha ta bar Amina ta shiga wanka ta fito Cikin Farinciki zata Zauna da Amina sannan gefe Daya tana Tunanin yadda zata inganta Rayuwar Aminene jidali ZUWA Aminene mai aji da Haiba. Taya Saude tayi suka yima su Hajiya girki ta Dibarma Idi da megadi ta Dibar ma Amina ta mika mata na Hajiya kuma da yakaka Saude ta mika musu Dakinsu. Aisha tare da Amina sukaci abinci tana yi tana janta da Hira Farar shinkafa ce da wake mai miya Amina kadan taci sai Amai Aisha ta Tsausayama Amina ganin yadda ta wahala wajen amai sannan gata da karancin Shekaru Allah ya bata wannan kyautar ita da tana son Cikin ammh har yau ko bari bata taba yi ba Allah bai kawo ba. ! Ita ta Wanke inda tayi aman a Cikin Tiolet ta kamo Aminar suka tafi tana Tambayanta me zataci tace Tea shi ta Hado mata ta samu ta sha ya Tsaya Daganan Aisha ta barta ta koma Dakin Yakaka ta iske su Hajiya sai Hirar garinsu Bama suke da yakaka nan Hajiya ke fadamata ai su ma sun a zauna a bama su yakaka asalinsu yan Maiduguri ne a bama da labari ya yi Labari Hajiya ta san har gidan su yakaka anan bama kafin yan Boko Haram su Tarwatsa su kowa yayi ta kansa.. Daman ai Yakaka ba ruwanta akwai Hira tare suka ci abinci da Hajiya tayi Sallarta anan wajen Uku saura tayi Shirin Tafiya suka rabu da Yakaka Cikin Aminci kafin su tafi Hajiya ta Damka ma Amima wayar nan da Jafar ya taba kawo mata. Ta bata ta Sanar da ita Tuntuni mijinta ya aiko da ita sai dai a wanchan Lokacin bata bata ita bane Saboda wasu Dalilai ammh yanzu gata nan zata Fadama Danmallam Saboda ya rika kira yana jin Lafiyarta Sannan tama Aisha bayanin Da Amina Zata Zana jarabawa ammh Dalilin haka yasa zata fasa sai wani Lokacin in ta Haihu. Amina sai da taga Hajiya Zata tafin da gaske sannan ta riketa tana ta kuka Hajiya tana llashinta tace zasu yi mgana ta waya tana ji tana gani Hajiya ta tafi ta barta sai kuka Aisha ce ta Zauna ta na bata baki Saukinta Daya ma akwai ya Aishar duk da ba kamar su hanne ba ammh da Sauki akwai wanda ka sani a kusa Dakai.... Sai da tayi sallar La"sar barci ya Dauketa Yakaka kuma na jin ance Amina ta kwanta tace maza Aisha ta Tasheta ba kyau barcin yammah Sannan gata da Ciki Dole ta tasheta ita yakakan tazo Dakin Aminan ta Zauna da ita tana janta da Hira ai Tun Amina bata Saki ba har ta Saki jikinta Saboda Yakaka akwai ban Dariya da barkwanci haka ta Dage tana bama Amina labarin Lokacin suna bama farkon hareharen yan Boko haram yadda suka ringa Gudun ceton ransu sai ga Amina na Dariya harda kyatatawa Aisha taji Dadi sosai domin yakaka uwace kamar Hajiya yadda take Daukanta kamar yarta Shiyasa ta matsa sai da Usman ya Daukota daga kaduna wajen kaninsa ya dawo da ita wajensu tasan Amina Zataji Dadin ZaMa da ita sannan zata Dauki darasin wasu abubuwan..! Hajiya sai Dare ta Kira tace sun isa lafiya har sukayi mgana da Amina ta bata Labarin yadda su hanne suka Dinga kuka ta Fada musu Ta kaita wani waje bazata Dawo ba yanzu Amina itama taji kamar tayi kuka Hajiya ta kara Lallashinta da Fadin kada ta saka Damuwa har ya shafi abunda ke Cikinta To in batayi hakuri ba ya Zatayi..? Ai hakuri ya Zama Dole tunda haka Allah yayi da ita daga wannan sai wannan..! *Janafty* *TFZB2017* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488* _A WEEK LATER._ Bayan Sati Daya da Tafiyar Amina Abuja acikin Satin Dayan data yi a garin Abuja karo na farko tun da take ta fita garin gumel taje wani waje da sunan Zama na wani dan lokaci. Alokacin da Hajiya ta mata mganar zuwanta Abuja ta shiga Damuwa,Da kuma Tunanin zatayi zaman kadaici ba hanne ba Hamida sannan inda bata Saba ba sai gashi kuma Cikin kwanaki da zuwanta Abuja ta Saki jikinta sosai da garin Musamman ma da Yakaka data kasance mai kirki da Dattako Sannan Aisha ma na iya Bakin kokarinta sosai akan Amina abaya Amina tasan ya Aisha bata da Hayaniya sosai da yawan mgana ammh yanzu haka zata zauna tayi ta jan ta da hira suna tuna irin Rashin ji da su kayi ita dasu hanne Tana bama Yakaka Labari itama Dayake sunan Amina gareta ake ce mata Yakaka tace ai masu suna Amina haka suke yarintarsu an sha kwallo sannan haka suke basu Daukan raini su taru da Amina su yita yabon masu sunansu Nan da nan Amina ta Saki jikinta Dakin Yakaka ma take kwana yanzu Saboda bata son kwana ita kadai yakaka tace ta dawo Dakinta su Zauna tare itama ta samu abokin zama. Haka kuwa akayi sai da ya Aisha taga Amina ta kwashe kayanta takai Dakin Yakaka suna Zamansu lafiya batayi mgana ba saboda ko bakomai yakaka Zata kula da ita sannan ga Ciki ajikinta tana Bukatar wani a kusa da ita. Usman mijinta ya Dawo ya ga Amina har sun gaisa saboda yasanta abakin ya Aisha lokacin tana amarya in kewar gida ya isheta sai ta Zauna ta rika basa labarin kannenta Amina da Hamida da Hanne sannan yasan mganar auranta da ya Danmallam din Tunda sukan yi mgana da shi Lokaci bayan Lokaci haka Itama Aminar tasan Usman sun taba ganinsa Sanda yazo wajen ya Aisha kafin auran sannan sun gansa ranar Daurin auran shiyasa dukkansu basu Tarbi juna abaki ba.. Achan gumel kuwa Hanne da Hamida sun gaji da tambayar Hajiya ina takai Amina..! Sun kyaleta saboda bata gayamusu sai dai tace Amina na nan Dawowa insha Allahu sun Damu Matuka,Ammh kuma Dole suka hakura sai dai kana ganinsu kasan sun rage walwala Sannan a makaranta ko an tambayi Amina cewa suke yi tayi tafiya,Hamida har mamanmu tama mgana ko tasan inda Hajiya takai Amina..? Mamanmu tace bata sani ba tadai san Hajiya tace ma Aba bata wuce Tsakanin gidajen yaran gidan nan ko na gidan mallam ba,ita duk a Tsammaninta bata wuce Tsakanin gidan Jawahir ko Jalela ba tafi ma Tunanin Jalela saboda tayi mgana da yan Gusai kuma bataji Labarin Zuwan Amina ko Hajiya abakinsu ba ita bama wannan ne agabanta ba shiyasa bata Damu da tasan Inda take ba,Saboda kada azargeta da rashin kula da Jawad yasa ta jawosa ajiki ganin yana neman yaki Zama wajenta ya koma wajen Hajiya Hamida kuma ganin ba Amina sai ta Dawo kwana agidansu tana kula da kanta da jawaad tunda Daman Amina ta bar mata Amanarsa to shima ganinta yasa bai Damu ba Duk da shima ya gaji da tambayar ina ya Amina..? Sai dai Hamida tace mai tayi tafiya ammh ta kusa Dawowa.. Sun kusa fara jarabawar Fita nan da Sati uku hanne da Hamida suna Zaton Amina Zata dawo kafin su fara jarabawa Tunda Hajiya bata sanar dasu komai ba. Sakina ta koma gidanta mallam yace Tunda taji Sauki ta koma Gidanta ta Jira Mijinta Dole ta tattara tatafi ammh Sai da ta roki mallam ya bata Sa"adatu tatafi da ita sai yace sai dai Tatafi da Sabeeha tunda ta gama primary zata shiga Jss1 kafin a sakata to da Sabeehan ta koma bayan mallaminsu ya Kira Anty Amarya ta koma wajensa ta Zubaimai kudi ya bata wani kullin mgani yace Sakina ta sha da Ruwan Zafi duk abunda Uwani ta bata taci ko ta sha Zatayi amansa ko Tayi kashinsa Domin ya tabbatar ma da Anty Amarya wani abu ne Aka bama Sakina taci acikinta.. Haka kuwa akayi ranar data sha mganin kwana tayi tana Zagayawa har safe ta Kira Anty ta Sanar da ita Tana jin haka Cikin farimciki tace in Sha Allahu nasara tasu ce. Tsakaninta da Haj Uwa kuma ko mgana basa yi sai agaban idon da bai san tsakaninsu ba kamar mallam da Hajiya da Suke Dauka bata san boyayyin Fuskokinsu ba..Ammh in suka hadu su Biyu su harari juna sannan kuma kowacce ta wuce tana ikirarin sai taga bayan yar"uwanta. ***** Achan Madina kuwa Danmallam dai da Sarood balarabiya suna ta gwangwajen amarcin su sosai fa ya Saki jiki yana Morewa Saboda ai ya Dade Rabonsa da mace tun Kan Amina wannan kuma ai ya Daukesa a matsayin Rabo ne shiyasa daya samu wannan Damar yake ta amfana da ita Domin Daman Daurewa kawai yake yi Yana fama da azumin Litini da alhamis saboda kariya da Tsare kansan. Ita kanta Sarood din sai alokacin tasan ta yi aure sai kuma ayanzu tasan tana kishin Mijinta ada kamar bata Damu da kishin Sakina ba ammh yanzu da tasan waye Umar sai taji har Sakina ma tana matsanancin kishi da ita ballatana Amina datafi Tsayamata arai ganin itace yarinya sannan kuma Amarya. Sosai take ta shagwabanta shi kuma yana lallabata Dalilin haka ne ma yasa har yau bai kira Amina ba Saboda ai sun yi mgana da Hajiya washegarin Ranar data koma Gumel a wayar Nazir Saboda ya cika alkwari yaje ya kwana Daya Ranar Litini da Safe ya hau Jirgi ya koma hankalinsa ya kwanta daya ga Hajiya lafiyanta kalau Cikin koshin Lafiya. Da farko kafin Bullowan Cikin jikin Amina har ya fara Cuku cukun nema mata Takardan Zama madina sannan har sun yi shawara da Aliyu kan zai shigar da Takardan kan zai karbi Gidan malamai na makaranta Saboda gidansa yayi musu kadan sai ya saka Amina ana Cikin makaranta,Sai kuma ga wannan al"amarin da hajiya tace ya Dakatar da komai Shiyasa ya dan Samu Sauki ya fara shirin Tahowa saboda Sakina sannan uwa uba Amina yana son yazo ya ganta Tunda ya tafi bai fi sau hudu sukayi mgana ta waya ba sannan Sakina duk sanda sukayi mgana ta Dinga mai kuka keman tana fadin yazo ya tafi da ita Tsausayinta yake ji ganin halin Datake Ciki yasa yayi mata alkawarin zai zo nan da wata Biyu zai zo sai su koma Tare Umra yake so yayi shiyasa ya Dakata da Tafiyar Sannan Sarood ma tayi Damara sai taje kuma in yace bazai je da ita yayi rashin adalci ko Iyayanta sai sun ga rashin adalcinsa...! Tunda suka yi mgana da Hajiya tace kada ya sanar ma kowa ko Aliyu bai Fadama komai ba yadai Fadamai laluran nan tasa Allah ya basa waraka da Taimakon shawarwarin mallam Daganan kuma sun ma Dade basu yi mgana ba daya kirasa sai ya Fara mai Tsiyan ya barsa ne yaci amarcinsa da yar Balarabiyarsa Danmallam Tsaki kawai yake yi da Dariya domin ba karya yana fa shan amarci. Sai da Amina tayi kwana Goma A Abuja sannan ya nemi wayarta da lambar da Jafar ya Dade da Turomai sai kuma ya kara jin wayar a kashe bai ji Dadi ba in yace Amina bata aransa yayi karya abubuwa ne suka sha mai kai sannan da Tazaran Dake Tsakaninsa da ita da rashin shakuwa da kuma Basu wani saba da juna ba. Aisha ya kira kawai saboda ko ya Kira Hajiya bata kusa da Amina. Daman duka kannensa suna kiransa awaya suna gaisheshi lokaci bayan Lokaci Haka suke basu yar da tarbiyan gidan mallam ba ko da yayyinsu basa kusa dashi suna Kiransu a waya suna Zumunci dasu Lokacin Ba'rin Sakina sun ta Kiransa suna mai Jaje. Lokacin da yake tambayan Aisha mganar yaji wayar Amina akashe ya Aisha tace bata sani ba ammh Zata tambayi Aminar taji tunda ita tama manta da mganar wayar sannan batama Taba ganin Aminar da wayar ba. Yace to ta fadama Amina yana son mgana da ita ta kuna wayarta Ya Aisha ta amsa da insha Allahu zata Fada mata ya tambayeta ya jikin Aminar..? Ta sanar dashi lafiyanta kalau sai godiya Zazzabin Dare dai take fama dashi sai amai sannan bata iya cin kowani abinci sai Tea sai Kuma wainar Fulawa,Komai Taci baya Zama sai ta Amayar dashi sai yaji Tausayinta gata yarinya ga shi ya Dora mata nauyi sun yi mgana da ya Aisha sosai ya sanar da ita suje asibiti tace eh Usman ne yace ta bari ya Dawo yaje Kaduna wani aiki Da haka suka rabu.. Suna gama wayar Aisha ta nufi Dakin Yakaka tana shiga ta iske Amina Zaune saman Cafet tayi Daidai tana cin wainar Fulamai mai manja da Saude mai aikinta tayi mata Tun Safe bata ci komai ba Tea din ma yau taki sha ita sai Wainar Fulawa Shine Yakaka tace Saude tayi mata Wainar Fulawan har Sauden tana Dakin ne suna ta Hira Yakaka na basu labarin Cikin kakan su Usman har ta Haihu kanwa ne abincinta sai da bakinta ya Lashe saboda Cin kanwa tana Fadama Amina ta godema Allah tayi ma Ciki mai kyau tunda batayi mugun laulayi ba sannan ta iya shan Tea da Cin wainar Fulawar tayi kyan ma Laulayi. Amina sai cin abunta take yi tana Dangwala yaji tana Sanye Cikin Bakar Doguwar riga cikin kayan ya Aisha ne da ta bata take sakawa tunda kayanta sun Daina Shigarta Cikin fa Kiba kawai da Budewa yake saka Amina ta bari ne Usman ya dawo su je asibiti da kasuwa ta siyo ma Aminar Dogayen Riguna tunda duk ta bata na wajen nata sannan sun ma Aminar karanci. Shiga Dakin tayi da Sallama Suka amsa mata,Saude tama mgana tace taje Kitchen ta Dora Girkin Rana Ta amsa da Toh ta fice sai da ta fita sannan ya Aisha ta kalli yakaka tana Fadin"Yakaka sannu da Hira..! Tana Dariya tace"Yauwa Sannu Aisha..Hala har kin kwanta Hirarmu ta, tada ke..? Aisha tace"A"a Wlh ina ta gyare gyare ne ma Yakaka ban ji ma Hirarku ba..! Yakaka tace"Au ho..Ai ina nan ina ma Takwarata Tsiya ina fadin ta godema Allah tayi Ciki mai kyau ba laulayi sannan ta na cin abincin Zamaninmu ni lokacin da nayi Cikin Gaddafi har na Haihu kanwa ce abincina..! Ya Aisha ta jinjina kai tana fadin"Kanwa..? Taba..Yakaka kin sha wahala..! Ta yi Dariya kafin tace"Ai Darajan Uwa ta Daban ce Aisha..Allah dai ya bama kowa nashi kema ina miki addu"an Allah ya baki naki Aisha ita Aminatu ai tana mai kyau ma Kinga banda aman da take yi to sai Zazzabin Daren dana ce miki tana Faama dashi..! Ya Aisha tace"Eh zamu je asibiti taga Likita ma yakaka in Usman ya Dawo..! Ta jinjina kai kafin tace"Hakan yana Dakyau..Allah ya Dawo dashi lafiya..! Suka amsa da Ameen harda Amina Data gama ci ta Kora da ruwa ta koma Tana Sauke Numfashi. Ya Aisha ta kalleta tana Fadin"Amina ina wayar da Hajiya ta baki da Zata tafi..? Amina ta Dafe Cikinta daya Fara Fitowa ta yamutsa Fuska kafin tace"To ina na sani..? Tunda ta bani chan Dakin na wurgar da ita..! Ya Aisha ta hararrta tana Fadin"To daman don ki ijiye Aka baki wayar..? Kefa kina da sarkaci bayan ma jidalinki wani Lokaci..! Amina ta kalleta kafin ta Tura baki ya Aisha tace"Tashi muje ki Daukomin ita na saka miki chaji tunda Daman Hajiya tace Sabuwa ce..Mijin ki ya Kirani yace yana son mgana Dake in fada miki ki kunna wayar hannunki..! Amina ta kalleta Shekeke kafin tace"Mijina kuma..? Ya Aisha tace"Eh ko ba mijin naki bane..? Amina ta Hura Hanci kafin tace"Ina Laifin kice yaya danmallan..? Ya Aisha tace"Ni yayana ne ke kuma Mijin ki ne..karyan iskanci kike yi bakin ki ya Bude yanzu ko..? Amina ta Yi fari da ido kafin ta bata rai Lokaci Daya tana Fadin"To ni yaushe rabon daya nemeni? Ko tawayar Hajiya yaushe da Rabon Daya Kira yace abani..! Tafada tana bata rai saboda Tsakani ga Allah tana jin takaicin hakan wato bai Damu da ita ba..? Ya Aisha ta rike baki Tana Fadin"Au Daman kina jiran sai ya nemeki ne..? tab kina da aiki kada ki manta wata matar garesa achan sannan anan ma yana da Sakina mu masu mu kadai muna Kula da Mazajenmu ballatana ke mai Kishiyoyi har biyu.? To ki rage wannan Sakarcin naki ko ba Haka ba Yakaka..? Yakaka ta gyara Zama Tana Fadin"Au to gayamata dai ai ni nan Tunda naji yarinyar nan da Zama da kishiyoyi har Biyu nace Zama bai ganni ba..Tana Haihuwa Gyaran yan maiduguri zan Mata wanda ba su biyu ko su Uku ne itace ta Hudu sai ta fita Zakka..Ai mu masu sunan mu ba Borori bane..Muna da Tasiri sannan wlh badai mutum ba Sai ta Allah.. Amina na Dariya Ita da ya Aisha wacce tace"To ai Kirarin ta kenan Yakaka Aminene badai ta Mutum ba sai ta Allah..! Yakaka tace"Ai Gaskiya ne..Ke kwantar da Hankalin ki yar nan har nan Zai zo yana mana yar murna sai mun Wahalar dashi ammh dai kafin nan tashi maza ki Dauko wayar ajonata in ta Cika sai ki kirasa ai mune akasansa ba komai in min nemesa muma watarana Zai nememu ko don Darajan wannan abun da ke Tare Dake in ya manta Dake don Kaniyarsa ai bazai manta da wannan aikin Daya kunsamiki ba..! Amina sai ta kasa mgana kunya ya kamata ya Aisha kuma ta Fice sum sum tana Dariya Dole Amina ta mike tabi bayanta suka shiga Dakin atare ta Dauko wayar nan Gefen katifa inda ta Watsar da ita Aisha ta karba ta Bude ta a kwali ta jona mata achaji Tana ta mata Fada fadi take"Wlh ijiye wannan Jidalin naki Zaki yi agefe wajen bautar aure ba wannan ake Bukata ba..ki iya Kissa da Kisisinan rike miji..Ni ban ma jin balarabiyar nan Sakinar ce mai ido a Tsakar ka..Kema ki Samu ki Zama mace awajensa..! Amina dai batace komai ba aranta Tace ai so ma suke ya Sakeni baki sani ba. Afili kuma batayi mgana ba Saboda abun ya fado mata arai duk da Tana kokarin Cire abun aranta ammh kuma har Abada bazai taba Fita ba.. Har ya Aisha ta gama fadanta ta fita batace komai gefen katifa ta koma ta Zauna tayi tagumi in ta Tuna kalaman mamanmu na kashe mata uwa sai taji ta tsaneta kamar tayi tsuntsuwa ta ganta agabanta ta Chaka mata wuka har sai  ta Daina Numfashi. Sannan ga kewar yaya aranta ga kuma Rashin samun wanda Zata Fadamawa baalle ta samu sauki ta kwanta akan jikinsa tayi kukan abunda ke ranta. Haka ta Dinga kuka ita kadai ta Share Hawayenta ta sulale nan saman katifar ta kwanta ta na maida Numfashi har barci ya kwasheta bata Sani ba sai Wajen Biyu na rana ta Farka shima Ya Aisha ce ta tada ita tayi sallah Sai da tayi wanka tayi salla Ta maida Doguwar rigar jikinta ta koma Dakin yakaka ta Haye gadon ta kwanta tana jin yakaka Dake zaune a saman Cafet tana goga goranta tana Korafin ta rage yawan barci mai Ciki da zirga Zirga aka santa tana jinta ta kara Dunkule kanta Cikin Filo aranta tana fadin Yakaka ba kisan irin barcin dana ke ji bane ita dai sama sama ta dinga jin yakaka dagachan kuma barci ya sake Daukanta la"sar nayi yakaka tatasheta tace ta tashi tayi salla ta Daina kuma barcin la"asar. Fadi take"Ke bake kadai ba..Ki rika barci har yamma tayi in kina son Lafiyanki da abunda ke Cikin ki sai kin kiyaye wasu abubuwan ku yaran yanzu komai Cikin gata kuke yi mu alokacin da in kina da Ciki ko barcin sai kin Ragesa har na Dare bama na yammah ba..! Amina dai batace komai ba ta Fada Tiolet ta Dauro alwala tazo tayi sallar tayi addu"a domin ta daina Sakaci da addu",an kamar baya da kuruciya yake Dauke mata hankali. Tana Idarwa ta Dauko Sauran wainar Fulawanta ta Sake ci tana ci tana jan yaji Yakaka na kallinta tana Girgiza kai fadi take"Ki Sautata ma kanki Cin yaji nan wajen haihuwa nake jiyemiki basir ya taso miki..! Amina tace"Au daman yana Tasowa ne..!? Yakaka tace"Zaki sani ne in kika shiga Dakim Haihuwa..! Amina Dariya kawai tayi sai ga Ya Aisha ta shigo tana Fadin"Amina wayar ta Cika na kunna miki..Rike ta Hannunki na Fadama ya Danmallam Zai kiraki yace..! Ta Fada tana mika mata wayar ta karba tana Tura baki ya Aisha ta Dunguremata kai Tana Fadin"Kinsan Allah ki fita Daga idonaa Amina na Rufe..! Zamu zo mu Tsara abubuwan da Zaki rika koya fanni girki da gayu dasauran abubuwa sannan har karatu Zamu rika yi,ga yakaka nan na san ban da matsala zata koya miki Dubarun Zaman duniya..! Yakaka tace"Ai ita Duniya basai an koya maka Dubarunta ba..Ita ke koya maka yin Hankali da ita..barni da ita ai muna Tare har Madina in tayi ba Daidai ba tasha rankwashi..! Amina tace"Tab wazai bisa madinan..? Ya Aisha tace"Yakaka kina jinta ko..!? Tace"Yi tafiyarki barni da yar nema..! Bata lambar mijin nata ta Kirasa da kanta..! Ya Aisha tace"Munyi mgana yanzu yace zai kirata..! Yakaka ta amsa da Toh fita Aisha tayi ta barta da yakaka sai Fada take mata ta shiga bata labarin irin yadda tayi gwagwamarya agidan kakan su Usman Cikin mata Biyu har sai mijinsu ya rasu ana ta Kishi da ita Amina dai tayi bakam tana jinta kafin tace"Yakaka in ka hadu da masu asiri fa suna zuwa gidan Boka..? Yakaka tace"To Sai me..,? Ai akwai su duniya ta lalace sai ka koma gefe ka rike Allah ka sa aranka Bawa bai isa yayi maka abunda Allah bai maka ba..yar nan rike gaskiya ki rike Allah ko min Dadewa gaskiyanki Zata bayyana sannan Allah baya barin Azzalumi da sannnu hakki zai bayyana .! Kai ta jinjina domin ta gamsu da mganar Yakaka suna Cikin hirar ne Taji karar wayar dake gefenta da Farko ta Firgita sai da Yakaka tace mata wayar tace sannan hankalinta ya kwanta Mikewa yakaka tayi da Go ranta ta fice tana Fadin"Mgana mai Dadi kuma ban da Tura masa wannan bakin..Ki ce sabuwar amaryansa tana gaishesa .! Ta fice ta bar Amina da waya a Hannunta sai da ta Katse sai kuma ya Sake kira tabi jerin lambobin da kallo bata Nigeria bane,Daukan wayar tayi Domin sak irin ta yaya ce tasan yanayinta tana Daga Kiran taji Sanyayyar Muryansa yana mata sallama sai taji kamar an kwara mata Ruwan sanyi ko"ina na jikinta yayi Sanyi har Bakinta ma yayi nauyi ta kasa amsa mai sai da ya maimaita sannan ta iya amsa murya shake Cikin Haibansa yace"Amina ya jikin ki..? Tura baki tayi kamar yana ganinta kafin tace"Ni ai lafiyata kalau..! Gemunsa ya sosa kujeran Office dinsa tana Dan juyawa dashi,yace"To ko ya nauyin jiki zan ce..? Amina sai taji kunya ta kasa mgana cikin wani yanayi yace"Nayi ta Kiranki ban samu ba tunda Hajiya tace min ta baki wayar..! Uhm kawai tace ya Cigaba da Fadin"Amina kinga lamarin Ubangiji ko..? Wannan rabon Dake Tsakanin mu shine silar Faruwar duk abunda ya Faru..! Amina tayi shuru batayi mgana ba shims shurun yayi kafin yace"Ba inda ke miki ciwo ko..? Amima sai taji wani Rauni ya shigeta kafin tace"Eh..! Cikin Rudewa yace"Eh kuma..? To ina ke miki ciwo..? Amina kai Tsaye tace"Menene mgani in an yi ma mutun sihiri sannan ta wata hanya Zai gane an yi masa..? Umar yaji mamakin mganarta Cikin mamakin yace"Amina waye akayi ma Sihiri..? Cikin wani yanayi Amina tace"Ni ce..! Baki ya Bude kamar tana ganinsa Cikin mamaki yace"Ke kuma..? Ta ce"Eh..! Sai kuma kawai ta Fashemai da kuka Har da Sheshsheka Saboda Dacin abun na taso mata lokaci Daya Rauninta na bayanna. Danmallan jikinsa yayi sanyi Cikin wani yanayi yake fadin"Kinga Amina..bar kuka nan yimin bayani yadda zan gane..! Ina ko jinsa batayi sai faman kuka take yi Dagacin kukan datake yi Daga karkashin Zuciyarta ne kansa ya Dafe Cikin wani yanayi duk da yasan yarinyar akwai kukan banza har da na siyarwa sai dai jin kalamanta da wannan kukan datake yi tabbatar wani ya faru wanda kedamunta acikinta kuma ta kasa fadamawa kowa..! Cikin sigar lallashi yake fadin"kiyi hakuri ki daina kuka sanar dani abunda ke faruwa..! Sai taji muryansa kamar wani waraka ne ga matsalanta yasa tace mai cikin kuka"ban taba Fada ma kowa ba sai kai..Wlh duk abunda Zan fada maka ba karya bane ya Dannallam..! Da Sauri yace"Eh naji bazan Fada ma kowa ba taimakeni kibar wannan kukan saboda yanayin Dakike Ciki..! Amina ta share Hawaye tana jan majina tace"Yaya..Yaya. ! Ta fada sai kuma ta kara sakamai kuka Umar ya shiga wani yanayin Tashin hankali da jin kukanta Cikin mamaki yace"Yaya. ? Amina tace"Eh yaya ba mutuwa tayi ba Kasheta MAMANMU tayi..! Ta fada tana matse bakinta kada kukanta ya kara fitowa yana Zaune ne sai da ya mike Cikin wani yanayi a Muryansa yace"Yaya ba mutuwa tayi ba kuma..? Mamanmu ta kasheta..? Amina ta amsa mai da Eh Cikin kuka Umar ya katseta Cikin Muryansa da kaifi yace"Ki bar wannan kukan yimin bayani sosai yadda Zan gane..! Amina sai kawai taji ta yarda Data Fadama Danmallam abunda taji ko zai Daina Damunta aranta ko Zata Samu Saukin abunda take ji.. Cikin kuka ta fara Fadamai komai Tun farkon wayar da taji Anty Amarya nayi a ranar da Hajiya tace zata tare da kuma Ranar da Ta kama mamanmu tana mgana da duka mganganunta,Sai dai ta Boye sunan Hajiya Uwa tunda bata san meye Tsakaninsu ba.. Amina ta sharbe hawaye tana Fadin"Da kunbina naji suna waya ya Danmallan..Da kunnina naji mamanmu na Fadin malaminta ta saka ya kashe mana uwa Saboda ta Samu Aba yadda take so Sannan da kunnena naji tana Fadamin Ba ni taso na ZAMA haka ba ya Jafar taso ya lalace da kunnina naji Tana Fadin Bazan haihu Dakai ba Sai Sakina sannan sukace har Abada sai dai aurena Dakai ya kare a gantali..Zuciyata tana min Zafi tun Ranar da naji haka..nayi kukan rashin Uwa Ya Danmallam bansan Dadinta ba Duka Mamanmu ta nesanta dashi ya Zanyi..? Abun na Damuna Zuciyata zafi take min kamar Zan mutu. ! Ta karishe fada Cikin kuka Danmallam Zufa kawai yake yi kansa na juyawa Mamaki da Dimuwa da al"ajabi sun kamasa ya kame awaje daya salati kawai yake maimaitawa acikin Ransa kafin ya samu yar natsuwa Cikin Wani irin Sauti yace"AMINA..!Kin tabbatar da mganar da kika Fadamin..? Amina ta kara fashewa da kuka Tana Fadin"Wlh in nayi maka karya Allah ya..! Da Sauri ya Katseta da Fadin"Amina ba kyau irin wannan rantsuwan ba kyau..! Sai yaji yama kasa mgana Saboda mamakin abunda yaji,Amina kuka ta Cigaba da yi kamar ranta zai Fita yana jinta ya kasa mgana sai chan yace"Kin Sanar da Hajiya ne..? Saboda yana tunanin kodai Hajiya ta sani ne Data Dauki wannan matakin sai Amina tace bata Fadama kowa ba...kansa ya Daure Tunaninsa ba Lokaci Daya bane yana Bukatar natsuwa Cikin lallashi yace"Ki daina kuka..Sannan ki cire damuwa aranki..Zan yi Bincike a barayina in dai mganar ki gaskiya ne akwai yuyuwar kowa yaji labarin nan,Alkawari Zaki min zaki Daina Tunani da Damuwa bakin gayamin ba .? Da yardan Allah komai zai zama Daidai kada ki damu..! Amina ta koma sheshshekan kuka tana Fadin"Haka mamanmu ZAta kashe mana uwa a banza kenan ya Danmallam..? Kai ya girgiza kafin yace"Ai hakkin Rai ma bazai barta ba Amina..In ma da Gaske ne Allah bazai barta ba sai ya Wulakantata aduniya..Sannan ai Allah ya nuna musu basu isa ba..Suna nasu ne Allah shi kuma yayi nashi..Amina Kina da juna Biyu wannan kadai ya isa kisan Allah ne Kadai mai yi alokacin da yaso a kuma Sanda yaso..! Amina taji jikinta yayi sanyi ammh bata bar kuka ba shi kuma ya tattaro Jarumtarsa yana ta bata baki da lallashinta Shima kenan datake da shekaru ya shiga wannan Halin balle ita mai karancin shekaru kamar Amina..? Dakyar ya samu Amina ta bar kuka shi Tunaninsa ma kada Damuwar ta Haifar da Matsala ga abunda ke Cikinta sai da ya tabbatar da ya lallasheta tare da alkawarin komai zai zama Daidai ya karishe da Fadin"Zan zo Gida watan gobe..In nazo sai mu Sake zama muyi mganar musan yadda zamu bullo ma lamarin ni dai ki daina Damuwa Sannan kada ki Fadamawa kowa..! Amina ta gyada kai kafin tace"Zaka zo nan ne..? Wajena..? Yace"Eh zan zo na ganki naga yadda Kika koma in kuma ga yadda Cikina ya zauna ajikinki ! Sai kunya ta kama Amina ta kasa mgana shi ma bai wani Damu ba,baya Cikin natsuwarsa Daganan ya mata sallama ya katse kiran. Zagayen office dinsa ya farayi kansa ya Dafe ya shiga Tunanin mganganun Amina bai san mamanmu a boye ba sai dan Zahirinta Daya sani kadan ana Fadin Kirkinta,ko abakin yaya yasha jin haka Sannan shi bai da wani Sakewa da ita iyakarsa su gaisa sannan ita kanta Anty Amarya gaisuwa ce Tsakaninsu har gwara itama sukan yi Doguwar mgana Sanadin Sakina Sai dai kuma ya fara jiyo kamshin gaskiya kan mganar Amina Duba da Yaya ance Lafiyalau ta kwanta sai gawa duk da ita Mutuwa ko da Ciwo ko ba Ciwo sai an tafi..! Ammh Amina yarinya ce ba yadda Zata Zauna ta Tsara mgana haka in ba ji tayi ba Sannan ya tuna yadda Sakina tada hankalinta kan Auran sa da Amina da kuma Matsalan data Faru tsakaninsa da Sarood Aliyu ya fara Hangomai Lamarin a matsayin Shihiri ammh bai yarda ba sai da Mallam ya sanar dashi Cikin Hikima har ga Allah bai zargi Sakina ba ammh kuma yanzu Dayaji wannan mganar sai ya shiga kokonta ya tuna Bakin kishi Sakina da Burinta ita ta Samu Ciki ta Haihu har wani Lokacin ya Dinga mata Fadan ta roki mafi alheri.. Bawai ya yarda da mganar Amina Duka bane sai dai kuma ya shiga Rudi da kokwanto agidansu ake wannan Tsantsan jahilcin da mugunta har da kashe rai..! Indai ko gaskiya ne Anty Amarya da mamanmu Allah bazai barsu ba sannan sai ya nuna musu basu isa su raba auran da Allah ya kulla da kansa ba. Cikin tashin Hankali ya kira jafar a waya yana Tambayansa Amina na karya?.. tunda sun fisa sanin yarintar ta shi ba mazauni banw baisan komai kan Rayuwarsu ba. Ya jafar ya fara fada yana Fadin"Hala iskancinta ta maka..? Ai Amina sai Allah..Wlh ya Danmallan ka daina Sake mata ne. ! Cikin haushinsa yace"Tambayata zaka bani amsa ko zaka Tsaya kana gayamin abunda zan yi da matata ne..? Saj jafar ya rike baki yana yar Dariya kafin yace"Amina bata da Halin karya..Bata da kumbiya kumbiya ita Free take abunta bata da Tsoro sannan tana da kafiya da Taurin kai yadda kasan zuciyan kafuran farko bantaba ganin wanda duka baya Sata tayi Laushi ba sai Amina..Ko zaka kasheta sai tayi mgana sannan abunda yake gaskiya take fada Bansanta da karya ba gaskiya..Sai dai Rashin kunya da tsiwa da Tonen fada da Yawon tsiya..! Danmallam ya jinjina kai alamun gamsuwa kafin ya Datse kiransa ya jafar afili yace"Ko son Amina ya Danmallam ya fara ne..? Dariya yayi kafin yace"Tab..bai Fada hannu na gari ba..Amina ai jidali ce..! Danmallam kuwa suna gama mgana ya saki Huci Amina tana da gaskiya wani abu na Faruwa sannan ya Fara ZArgin Hajiya tasan wani abu shiyasa ta hana Amina ta zauna a gumel sannan kuma ta hana kowa yasan da Cikin jikinta tabbas ya hasaso wani abu.. Sai dai koma menene ya kamata yaje Negaria yaga Amina su yi mgana sosai sannan yaga ta ina zai Bullo ma al"amarin da ke faruwa agidansu karkashin Tarbiyan mallam..? Lalle ana Zaton wuta a makera sai aka sameta a masaka..Zuciyarsa ne taji ta Bude da duka mganar Amina da Tsausayinta da bai taba jiba ba..Dole ya tafi gida cikin watanan mai Shiga abubuwa Dadama suna Bukatar yaje ya gabatar dasu tukunnah..! *Janafty* *TFZB2018* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488* Tun daga ranar Danmallam bai taba kwana batare daya Kira Amina ya lallasheta ba ganin da gaske fa abun na cinta aranta Fatansa Allah yasa kada Damuwar ta haifarma da abunda ke cikin wata matsala sannan bayaso ta fadama kowa abunda ta Fadamai mganar tana Bukatar Bincike da Lura sannan ba kowa bane zai iya Daukan mgar har ya Fahimceta sannan yayi tunanin mafita Shiyasa yake kokarin kiran Aminar yana amfani da Hikimarsa wajen kara Lallashinta da bata Baki. Wani Lokacin yafi Kiranta in yaje Wajen aiki ko in ya bar gida Zashi masallacin Madina ammh in yana Gida baya Kiranta Daga ita har Sakinar saboda Gudun matsala Ga Sarood kamar ta goyasa haka take ji Dashi bazai so yayi abunda zai ci mata Fuska ba shiyasa yake kiyaye wasu abubuwan sannan nauyi ne akansa ya kwatanta adalci Tsakanin mtansa. Abunda Amina ta Fadamai na nan aransa kamar ya Tuntubi Hajiya da mganar sai kuma ya fasa yana Tunanin ta ina Zai fara duk da fa yana da Zargin Hajiya tasan wani abu Shiyasa ta Boye Amina da Cikin Dake jikinta,Mallam ma kamar Zai mai mgana sai kuma yaga ai bai da wata Sheda itama Aminar ji tayi bata Nadi murya ba Tunkarar wani da wannan mganar ma a yanzu bai taso ba,Sannan abu ne na Kashe rai duk da daman kowa yasan Mutuwa ta Allah ce sai dai mutum ya Zama Sanadinta. Bangaran Sakina kuma ai ya Dade da Fahimtar mganar Amina Hakane kodaga yadda bata taba mai mganar Amina ba Ranar Dayake so  ji ta  Bakinta suna waya sai Rigima take mai kan yaushe zai zo ya Dauketa..? Ita ta gaji da Zama agarin nan baya nan sannan ta yi bari tana son maida Cikinta,Mirmishi kawai yayi kenan mganar Amina ta fito su Burinsu kawai Sakina ta Samu Ciki ta Haihu..? Saboda ya jarabata yasa yace mata Bata taba Tambaynsa ina Amina ba..? Sai Sakina tayi Tsaki kafin tace"To ni ina Ruwana..Tunda ta bar min gidan mijina ban damu ba..Ba"an ce hajiya takai ta wani waje ba..? Yana jinta ammh Daganan bai kara mata mganar Amina ba Itama Sakinan bata Damu ba,ita kamar ma Dadi Take ji tunda ta bar mata gidanta ai taje koma ina ne bata Damu ba Allah ya raka taki gona..! Allah duk ya shafe musu Tunanin Mezai sa rana Tsaka a Dauke Amina Daga Gumel..? Duk basu yi wannan Tunanin ba Idonsu ya Rufe da nasu Cikar Burin dukkansu. ****** Usman mijin Aisha ya Dawo washegari suka kai Amina asibiti shi da Aisha speacialist  Hop suka kaita Inda Aisha ke zuwa in Bukatar Hakan tataso,anyi mata Scan cikin Amina Har ya shiga wata na Biyar sannan jininta yana sama kadan Saboda Tana saka Damuwa sannan kuma Sugar masu Ciki na son kamata ammh ita da Abunda ke Cikinta suna Cikin koshin Lafiyan an bata mganin karin jini su Vitamin c da sauransu sai kuma  na cin abinci tunda Aisha Tayi Korafin batacin abinci Likitan yace Normal ne indai tana cin abunda Cikin yake so ba wata Damuwa...! Ya sanar dasu zata fara zuwa awo Duk bayan Sati Hudu sannan in yayi  shiga wata shidda za"a sake mata wani Scan din Basu Dade a asibitin ba suka Dawo Gida suka ijiye Amina suka kara Fita kasuwa suka shiga Aisha ta Zabo ma Amina Dogayen Riguna guda Biyar da Wanduna plazo sai ruguna masu yalwar wadanda zasu mata Saboda ta kara kiba kaya wanda tazo dasu sun mata kadan sannan nata bazasu wadaceta ba. Data kawo ma Amina taji Dadi sosai kamar ta goya ya Aisha tana Daga rigunan adakin Yakaka take fadin"Yakaka kalli Rigar nan bata miki kyau ba .? Tana zaune saman Cafet tana Gogan goranta tace"Sosai ma ai sai ma kin sakata Ajikin ki takwarata ai mu duk kayan da muka saka sai ya karbemu..! Ya Aisha na Dariya ta Fice tana Fadin"Ki fito kiyi ma Darling godiya yana Falo..! Amina in Aisha ta Kira mijinta Da Darling mamaki take bata,agida shuru shuru kamar bazata aikata ba kamar ma batasan komai ba. Kwashe kayan tayi ta maida a leda ta Saka Hijabinta ta fita falo ta Durkusa tama Usman godiya ya amsa mata yana Fadin"Bakomai Matar yayanmu..Kin dai ji abunda Likita yace ko..? Ta gyada mai kai kanta na kasa tana jin kunya ya cigaba da Fadin"To sai ki yaye in kina Bukatar wani abu ga Sweety nan ga kuma Yakaka Dukkansu They are Their for u..! Kanta na kasa ta amsamai Lokaci Daya damai godiya kafin tatashi ta koma Dakin yakaka tana Santin kayanta ta gwada wannan ta gwada wannan tana nuna ma yakaka ita kuma tana yabonta Amina ta gwada wata Riga Mai yalwa ta juya ta Sake juyawa kafin tace"Sai yanzu najini Daidai...Ammh wacce ya Aisha ta bani jan nan tamin kadan fa yakaka..! Yakaka tace"To Daman ai irin wannan ne Daidai dake..Daga gani ba wani Girman Ciki Zaki yi duk a kiba Zai tsaya .! Amina ta bata rai kafin tace"Wai sai nama kara Kiba yanxu..? Yakaka na cin soyayyan gyadan da su Aisha suka siyomata a kasuwa tace"Af ai sai kin ninka kibanki na yanzu.. Ai sai Amina ta Zauna akasa ta Fashe da kuka Yakaka ta saki baki tana kallonta Kafin ta tabe baki tana Fadin"Yarinyar nan kin samu waje..Ki bari Balaraban Madina yazo sai ki mai wannan shagwabar..! Amina Ta tura baki Batayi mgana ba Yakaka tayi Dariya kafin tace"Tsoro kike ji kada su kwace shi..? Amina tace"Tab..Allah ya Tsareni ni bana tsoron su har ita gajeran ma..! Yakaka tayi Dariya kafin tace"yauwa haka nake son naji Tsoro ai ba namu bane..kada ki Damu kina Haihuwa Zaki Dawo silandiyan dinki..! Amina ta washe baki Tana Fadin"Da Gaske kike yakaka..? Yakaka tace"sosai ma ai mu ko da kiban mu muka je mune agaba bazamu taba komawa baya ba. ! Amina ta amsa da wlh kuwa Daganan ta warware suka Cigaba hirarsu Daman kukan Aminar na Tabara ne da jidalinta. Hajiya suna waya da Amina ta wayar Amina Tunda Aisha ta Tura mata lambar Aminar koda yaushe sukayi mgana sai Amina tace ina su hanne abasu su gaisa sai Hajiya tace ba yanzu ba ko Aba bata yarda ta Kira ba sai Mallam kawai ta Turo mata Lambarsa ta Kirasa suka gaaisa ya Dinga mata nasiha da Saka albarka yaji Dadin jin tana Lafiya kalau.. Amina tana jin kewar su Hanne sosai Kamar yadda suma suke kewarta Tunda suka ga sun fara Jarabawar Fita Amina bata Dawo ba suka Sare Hanne tace da sun san ba tare da Amina zasu zana Jarabawar Fita da Mallam ya bar su sun gama SS3 Kamar kowa sai dai ina bakin alkalami ai ya Riga ya bushe. Duk damuwarsu basu kai Sa"adatu ba wanda hakan da mallam yayi yanuna cewa bazasu Dade agida ba suma zai aurar dasu Shine tashin hankalinta su kuma su Hanne Amina ce Damuwarsu Saboda rayuwar ba Dadi ba ta abaya ashe ba Rashi sukayi ba Tunda Amina na kusa dasu yanzu kuma da basu da tabbas din ina take sai Damuwar tafi ta baya,Sun gaji da Tambayar Hajiya sun kare har Mallam sun tambaya yace su tambayi Hajiya Hamida data tambayi Aba shima yace Hajiya bata Fadamai ba. Ganin Hamida ta Damu ne yasa Mamanmu ta Kikkira su Jaleela ta tambayesu ko wajen su Hajiya ta kawo Amina ammh har Jordan ta Kira amsar Daya ne A"a sai ta fara Dawowa Hankalinta ta fara Tunanin ina Hajiya takai Amina..? Har su Zulaihat ta Kira suma suka ce mata bata wajensu kuma kowacce ta Kira sai ta nemi karin bayanin ina Aminar ba"a ganta bane..? Sai Mamanmu tace wayasani Hajiya dai tace Zata kaita Gidanjenku gashi Wajen Wata Daya da wani abu ba Labari sannan Hajiyar taki Fadan inda take in sukaji basa Damuwa cewa suke ai Hajiya bazata kai Amina inda Za"a Cutar da ita kada ma mamanmu ta Damu Hajiya Zata Dawo da Amina kamar yadda ta tafi da ita. Mamanmu ta fara Tunanin kodai da wani abu ne..? Sai kuma ta Tuna ance Dubaran Zaman aure za"a koyamata tuna haka yasa ta watsar da mganar Amina aranta tana ma Hajiya Dariya Tana Wahalar da kanta ne saboda auran Amina da Danmallan ai haka zai kare agantale. Da sukayi waya da Anty Amarya ma sai da ta mata batun Anty Amarya ta Saki Tsaki Tana Fadin"Nace miki ki daina mana wannan mganar mun gama da wannan shafin..Ba inda Zata kaita Daya wuce maiduguri garinsu tana da inda yafi chan ne..? Mamanmu tayi Dariya kafin tace"Ai Tunanina bai kawo nan ba..To Allah ya raka Taki gona ya mganar Sakinan..? Madina ina son kema naga Burinki ya Cika kamar yadda nawa Burin ya Cika .! Anty Amarya tace"kada ki Damu Saura kadan..Cikin watan nan Danmallan zai zo ya tafi da Sakina kinga in ya tafi da ita shikenan sai naji da Hajiya uwani kuma..! Mamanmu tace"Ai Hajiya Uwani matsiyaciyace..! Anty Amarya tace"Babba ma kuwa sai kin ga yadda take shigema Hajiya..Kamar ta Allah..! Abunda basu sani ba ai Daman in Dubunka Zata cika rasa Dubara kake yi Hajiya gefe ta koma tayi bakam tana karban kowa yadda yazo mata Sannan tana Daina yarda da kowa ta gama Sarewa da lamarin duniya sannan Haj.uwani bata san wani abu ba ita adole tana shigema hajiya tasan wasu sirrukan ai ta Dade da Cin Taliyar karshe tunda Hajiya ta ganota ta DAina bata labarin abunda ya Shafeta da ya"yanta.. Har Falonta tazo tana bin bakin jin ina Amina take taki Fadamata Saboda Sai Daga baya tasan ma Aminar bata bata nan shima abakin Haj Nasara taji Data Tambayi mallam yace hakane ita mamakinta Daya meyasa Hajiya ta Kauda Amina Daga gabanta..? Ko madinar Aka Turata sai dai tana Tunanin ba Haka bane Tunda taji ana mganar Dawowar Danmallan din Cikin wannan watan.. Sai Hajiya ta bangarar da Tunanin Haj.Uwani da cewa Amina ba Nisa tayi ba Jarabawa take yi a inda take in ta gama Zata Dawo to ganin suma su Hanne sun fara sai ta yarda da mganar Hajiya aranta tace ita wannan auran ai su Amarya da Balaraba sun gama gantallar dashi. Dayake itama ba Aminar ne agabanta ba Sai ta Watsar da mganar ta Ita yanzu babu abunda ke gabanta sai Shirye shiryen dawowar Nazeem gabadaya Cikin Sati mai Shiga yace mata Zai dawo gabadaya in ya Dawo kuma aikin da zata karisa ai kadan ne har ta Fara hango kanta ta Cika Burinta mganar Anty Amarya kuma bata gabanta tasan ko giyan wake tasha bazata fasa mganar nan har wani yaji ba..Kuma tasan Mama ta sha gaban Bokansu har Mganin Data Karbo ma Sakina sai da mama ta labartamata Dariya kawai tayi in su suna zaune ita ai ta Dade da kwana atsaye kan Cikar Burinta ko kofa bata taba badawa ba ballatana a samu matsala..! Ashe ashe bata sani ba shi Allah ba"a masa Dubara sannan a lokacin Daka ke Tunanin ka Rufe kofar gefenka ta kofar da bakayi Tunani ba sai Allah ya Wangale taa asirinka ya gama Tonuwa a idon Jama"a. ******* Kamar yadda Aisha tayi ma Hajiya alkwarin ta kuma ta gayama Amina bata  sauya Shawara ba Haka take tasa keyar Amina Kitchen in suna Girki da Saude ta rika gani tana koya mata Saukakkun girke girke,Tun Amina na Tura baki tana kunkunin tana barcinta ya Aisha na takura mata har tazo ta saki ta Fara maida hankali To Saboda ko ta koma Daki Yakaka ke Fatattako ta dole ta Dage tana maida Hankali ballema ya Aisha data koyi Fada tunda tayi aure. Haka Zata Zaunar da Amina tana koyamata yar shagwaban nan da yadda zata rika ma ya Danmallam mgana da karaiyaya Amina sai ta Dinga Dariya aranta tana Fadin a ina ya Aisha ta san wasu abubuwan agidan kamar in ka samata Hannu abaki bazata Cija ba Kamar ya Aishan tasan abunda take Tunani ta Dunkure mata kai tana fadin"Ban son iskanci ana koya miki yadda zaki zama Tauraruwa wajen ya Danmallan kina Iskanci ko..? Nasan kina mamakin ina duk nasan wadanan abubuwan ko..? To ai gidan aure makaranta ne Amina sannan tunda ya siyamin babbar waya nake dan shige shige ina koyan wasu abubuwa sannan Addini ma ai ya koyamana yadda zamu yi mu"amala da kowa har da gidan auranmu..! Amina ta jinjina kai Domin tana ganin  yadda ya Aisha ke yi in ya Usman yana gari kwalliya da salon mgana da kwarkwasa duk tana gani kuma tana Dauka Domin a Zahirin gaskiya itama tana so ta zama mace sannan tunda ga inda kaddara ta kaita ai sai ta Dage Uwa uba kuma taci Uban Sakina ta nuna mata nasu ba irin nata bane Sannan bazatace ta fara son ya Danmallam ba ammh sun fara Shakuwa da juna tunda koyaushe suna Tare a waya kullum Cikin Tambayar baki da wani Damuwa ko.? Yau da gobe bata bar komai ba sannan ita ai Zuciya tana son mai kyautata mata Amina tana da Budaddiyar zuciya ne shiyasa nan da nan mutum ke Shiga ranta abunda bata sani ba shi ya Danmallam ai jinin jikinta ne shi da take Dauke da Kwansa acikin jikinta,Sannan kuma ba kamar Soyayyarsu da Aminu bane,da ba Sakewa Cikin Tsoro da Fargaba tayi ta wannan kuwa a sake take sannan in suna waya sai tarika jin wannan fa ai mijinta ne wani abu ke shiga ranta batare data sani ba. Sannan abunda ya Faru Tsakaninsu ya Haifar da wani bond mai karfi wanda Bawa bai isa ya hasaso farkonsa ba ballatana karshensa ba abu Daya ta saani tana jinsa aranta sannan tana Kishi da Sakina daman chan tana jin haushinta balle yanzu da suka Hada miji ko sunanta taji sai ranta ya baci bata ma Damu da balarabiyar nan yadda ta Damu da Sakina ba. Ko kwana Daya yayi bai kirata ba ta Dinga fushi kenan tana Tura baki in ya Kira taki Dauka Sai Yakaka ta mata Fada da cewa"Tsiya na Dake Sarkaci Takwara..Haka ake karban miji a Hannun kishiya..? Amina na hura Hanci tace"To bashi bane Jiya fa bai kirani ba..! Yakaka ta aika mata da Dakuwa tana Fadin"Kin ga naki nan..? Don bai Kiraki ba sai me..? Ai kinsan yana da uzuri ko..? Kada ki Dauka sai ki barma ita balarabiyar ki koma baya ke ko yan Dubaran nan na yaran Zamani da suka iya su Tadama Mazajensu hankalinsu in suna nesa saboda su zo wajensu da wuri baki iya ba,Sai Sakarci da Kunkuni kadai kika iya..! In yakaka ta fara fadanta bar mata Dakin Amina ke yi abunta ranar kuwa sai taja mai aji Zata Daga kiransa in kuma ta Dauka yana mgana ta basar dashi yasan Laifinsa sai yayi mirmishi yace"Amina kiyi hakuri..! Sai ya fara fadamata Uzirinsa sannan Zata Hakuri koda yaushe Cikin Tambayanta lafiyanta yake yi tana Bashi amsa ba wata matsala bawani Hira suke ba na ma"aurata ba sai dai suna Hirar abunda ya shafi mganar da Amina ta Fadamai koda yaushe sai tace mai yaushe zai taho Ranar dai yace mata"Cikin karshen watanan..Sannan yana so yazo da Sarood su yi Sati Biyu sai su koma Tare da Sakina..! Ai Har suka gama wayar Amina bata kara Dariya ba wani Tukikin Takaici take ji wato zai zo da wannan balarabiyar sannan ya koma da Sakina ita ko Oho..? Sai kuka da Ya Aisha tazo ta ganta Tana kuka Har Hankalinta ya tashi ta Zata ko jikin ta ne take jin wani abu..? Sai Amina na kukan ba Hawaye tsabar Takaici tace"ba ba..ya Danmallan bane yace wai zai zo da balarabiyar matarsa ba..Sannan in sun tashi tafiya su koma da wannan gajerar matar tasa..! Galala Aisha ta Saki baki tana kallon mgana kafin ta Tsintsire da Dariya Amina ganin haka yasa ta kara bare Baki ya Aisha ta buge bakin tana Fadin"Kefa ko ya'ya Dubu Zaki haifa na tabbata wannan iskancin naki bazai barki ba..Miye na bare min baki kmar na yankaki Salon yakaka Dake Daki Taji tace nayi miki wani abu..! Amina ta hura Hanci kafin tace"To bake bace ina gayamiki mgana kina min Dariya ba .! Ya Aisha ta matso ta kama Hannunta tana Fadin"to na bari kanwata gayamin yaki keso ayi..? Amina tace"To ni kada ya tafi da Sakinar nan gaskiya..ni fa kadai zai bari anan kuma sai ya Dade kafin ya Dawo. ! Ya Aisha tace"Yanzu waya isa ya hansa tafiya da matarsa Amina..? Ai bamu isa ba matarsace kuma kinga Daman achan take sannan duk keki keda matsala ina nan ina Koya miki irin  kissar da zai saka Miji yazo gareka bai sani ba kin ki Dauka nace miki watarana ki sakamai kuka kice cikin ana Miki motsi ke zaki mutu ki Tadamai hankali yayi lallashi ki kinyi Shuru Da gudu zai taho ma Lokacin Tafiyarsa bai yi ba ammh sai ki kalleni kina Dariya..,! Amina tace"To ai kunya nake ji..Kuma kuma..! Ya Aisha tace"Kuma me..? Amina tace"to ai naga shi babba ne. ! Dariya ya Aisha tayi kafin tace"to ai ke kin ji Dadi ma baki san sirrin auran irin su ya Danmallan ba..? Gaki da kuruciyarki Amina da Shagwaba da Yarintarki zaki sacemai Zuciya shi kuma ya lalace akanki Wlh irin ku an fi sonku kiyi ta Jidalinki yana lallabaki shiyasa na Fada miki shima wannan Jidalin naki aikwai Inda ZAI miki amfani balle nasan shima ya Danmallam din ai yana son soyayya..! Amina tayi Dariya "To kuwa matarsa bata iya ba..bandai sani ba ko wannan Sarood din..! Ya Aisha tace"Ke ya akayi kikasan bata iya ba..? Amina tace'Tab ai na Zauna da su..! Aisha tace"ai bata iya komai ba sai Fadin rai ita kuma wannan Sarood din naga kamar ta Biye mata sun maida ta wata wawiya ma..! Amina tace"ai kamar ma wawiyar ce..! Dunkure mata kai ya Aisha tayi tana Dariya tana Fadin"Tunda ke kin iya sai ki Dage ki rikitamana yayanmu.! Amina taji kunya ta kasa mgana. Tundaga ranar ta Bude kunne tana kwasan Abubuwa awajen ya Aisha Da gaske take yi duk sai ta nuna ma su Sakina basu iya komai ba Aminene ai Ta musu Zarra. Bangaran karatu kam sai da ya Aisha tasha mamakin Amina ba inda baza"a bude mata a Qur"ani ta karanta ba Hadisi kuwa tunda ga na farko har na bakwai suna kanta sannan ta haddace Arba"una Hadith sira ma haka Tajwid wasu Littafan Ya Aisha mamakin Amina ya isheta sai da ta Furta mata tace"Yanzu daman Amina kin iya wannan duk abubuwan kike iskanci a makarantar islamiya da Haddda..? Amina Dariya kawai tayi tana Fadin"ai ya Aisha ba kowani Hali muke sani na mutanen da muke Tare dasu ba..Muna sanin wanda suka bayyana mana ne..! Ya Aisha ta jinjina kai tace ba Shakka ko bangaran Boko sai da ta Kusa raina kanta sun yi kunsan mintinaa Talatin suna hira da Usman Cikin Harshen Turanci Amina bata kage ba sannan ba Turancin yan koyo ba Turancin ya Zauna abakinta sosai har Usman sai da yayi mamaki yace mata"Amina fa tana da kwakwalwa..In ta samu cigaba da makaranta sosai zata Zama wani abu watarana. ! Ya Aisha ta jinjina kai tana Fadin"Agida ko sai kace bata gane komai..Bama Damuwa tayi da karatun bafa..! Dariya yayi yace"ai irin su sun fi raina ma mutane hankali da basa ganewa nan kuwa sun fi kowa Dauke komai Lokaci Daya..Muma lokacin muna Secodary sch muna da wani Dan ajin mu haka mai suna yahaya kamar wawa fa ana karatu yana wasa wlh a Exam shine Overoll..! Ya Aisha tace"irin Aminace..A aji Dakikiya a Result sai kaga ta Doke kowa ko su hanne Dake maida hankali Tana gabansu..! Usman yace"Da yawam irin masu baiwar nan basa samun masu Courage dinsu ne in ana kushe su ana cewa basa yi sai su boye baiwarsu sun fi bayyanasa wajen wanda ya yarda suna da ita kanta baiwar..! Ya Aisha ta jinjina kai domin tagamsu da hakan yanzu sannan baba mallam koda yaushe Cikin Fada yake Uwata yar baiwace nan gaba sai mun baku mamaki aiko gashi ta bata yau wlh Bata Taba jin Amina tayi Turanci ba Duk azatonta batajin komai sai Tsinta tsinta. Daman haka Lamarin Allah yake Tsammanin Abunda baka Tsammani ba..! ******* Bayan kwana Shida..! Nazeem ya Diro gumel Ranar wata Laraba da yammah tun Safe Haj.Uwani ta kasa zama ayi chan ayi nan tasa su Baba lami sun shiryamai kayattacen abincin daya fi so Priderice da soyayyan kaza an yi pepe dinta da kunin aya,Tasa su Akilu sun Share masa Dakinsa an gyara an goge an Baza Turaran wuta Duk ta kasa Zaune sai da ya Shigo gidan Abunda yafara bata mata rai duk yadda Taci Burin Dawowarsa sai da ya Fara Shiga Shashen Hajiya suka gaisa ya Dade ma suna Hira sannan ya kariso wajenta ammh Dayake yar Duniya ce sai bata nuna mai ba ta karbesa Cikin maraba da lalenta kamar ko yaushe. Ya Duka yana gaisheta ta amsa Cikin Sakewa tana Fadin"An gama karatu gabadaya Nazeem an dawo gida..? Daman ance kowa ya bar gida..Gida ya barsa..! Yana Dariya kansa a kasa yace"Hakane Mommy..Mun dawo sai Fatan mu samu aiki atayamu da addu"a..! Tana Dariya cin nasara tace"ai kama samu aiki ka gama Nazeem..kai fai tashi ka karisa Dakinka kayi wanka ga abincinka nan tafe. ! Ya mike yana mata godiya har ya fara Tafiya tana Binsa da kallon alfahari ganin ya kara girma sam bai yi kama da ita ba yafi kama da Mallam ne kuma suna bala"in kama da Danmallan. Juyowa yayi yana Fadin"Mommy ina Umai..? Ya jikinta..?haj.uwani tace"Taji Sauki har ta koma ma islamiya da Hadda. Kai ya jinjina ya fice yana fadin Allah ya bata lafiya.. Yana fita itama ta fita Kitchen din Tsakar gida tace su kaimai abincinsa da komai da komai tana Tsaye sai da Taga an Dauka an kai ta koma Shashenta ta Kira Batula ta Fadamata Dawowar Nazeem. Batula tace"Dakyau..To gobe zan yi Sammakon zuwa Minna in samu mama na mata bayani yadda ake Ciki Zaki ji..! Haj Uwani tace"Nagode batula..Kada kiyi sanya..Kinsan wani Lokacin jinkiri ma yana batamana aiki. ! Da sauri Batula tace"Haba a baya ma ban yi sanya ba..Ballatana da yanzu da muke gabda Cikar Burinmu..? Kedai sai kin jini.. Daga haka suka sauke wayar Haj.Uwani Bakinta har kunne sauran matan ma su Anty Amarya sai Da Daddare suka san Nazeem ya Dawo da suka gansa Falon Mallan har suka gaisa Mallam yaji Dadin Dawowarsa Saboda Nazeem akwai natsuwa ga Hnkali yana ta mai fatan alheri da fatan samun aiki mai kyau. Ranar Hajiya Uwani bata Samu kebewa da Danta ba washegari ma Tare da yan"uwansa Nasir da Jafar suka shigo mata ranta ya sosu sai bata nuna ba ta barsa sai da ya kwana Biyu da ya shigo gaisheta da Safe tana Dakinta taji suna gaisawa da Umaima da Jikin nata yayi sauki yanzu har tana Fitowa falo ta Zauna. Daman jiransa take yi yana shigowa bayan sun gaisa ta sako mai mganar Dake ranta Cikin Dakiyarta tace"Tunda ka Dawo gida..sai ka fara bin Baban ku sa"idu gidan gona kana Duba wasu abubuwan tunda kaima Harkan kasuwancin nan ka karanta..Wani abun gwara ku masu Dukiyar kuna kusa zaku fi ku kula dasahi Dakyau akan bare..! Ya Dade yana mamakin kalamanta kafin yace"Mommy ai baba Sa"idu kuwa ba bare bane kema kinsani..Kada ma ki Fada baba yajiki bazaki ji Dadi ba sannan shekaru aruru yana kula da kasuwancin Baba ko Da rana Daya bamu taba jin kansu ba..Sannan infact ma ni bana Sha"awar aiki a karkashin Mahaifina gwara na samu aiki na tara gumina..Na ma yi interview da wani kamfanin Sarrafa fata dake Lagos sun ce xasu neme ni Albashi 100k sukace zasu rika Biyana Duk wata..! Kafin ya gama mgana ya sha Harara nan ta Rufesa da Fada tana Fadin"Inda Uzairu ya fika kenan shi Burinsa ya gama karatu yazo ya taimaka ma mahaifinku kai kuma Shashaha kana wani mganar kamfani Dubu Darin banza..? Kasan iya adadin Dukiyar mallam ne..? To ahir dinka..ba inda zaka yi aiki sai karkashin mallam kuna chan sake da Baki wasu dagachan nesa suna amfana da abunda yake watarana mallakin ku ne. Gargadi na shine in mallam yamaka mgana ka amsa mai wlh ka kunyatani sai na sabamaka..! Har ya fice yana mamakin me yasamu mommy ne take irin wannan mganganu ? Washegari Batula ta kirata tace Mama tace yau da Daddare ta tunkari mallam da mganar bazai mata gaddama ba. Cikin jin Dadi da Nasarar ta Ta tunkari mallam adaran Daman ita keda Turaka yana cin abinci ta lamkwashe kafa agabansa tana Fadin"Mallan nace tunda Nazeem ya gama karatun nan ya Dawo gida kafin aiki ya samu kasan kasar tamu yadda takkoma sai Kana da wani asama..Sai naga Tunda shima bangaran Kasuwanci ya karanta mai zai hana ya fara Bin Sa"idu gidan gona yana ganin waau abubuwan yana taimakai ko wajen Rubuce rubuce ne tunda naga Jafar ke taimakamai shima kuma kaga ga aikinsa..! Har ta Sare da ba nasara taji mallam yace"Hakane..Zan m Sa"aidun mgana sai ya fara Binsa yana da kyau hakan Zai taimakamai..! Haj.Uwani taji kamar ta goya Mallam Dole ta karama Mama kudi haka ta shiga yi ma mallam godiya sai da ya ji mamakinta. Abunda bata sani ba wani abun yana Tarda Sa"a ne mallam yayi la"akari da nazeem ya Dawo gida Zaman banza zai yi kafin ya samu aiki daman kuma yana da wannan Tunanin shiyasa bai mata gaddama ba. Da Safe da Aba yazo su gaisa ya Sanar dashi yaji Dadi Sosai,suna ma Cikin Tattaunar ne sai ga Nazeem ya shigo gaida mallam nan ya sanar dashi bai iya cewa komai bs tunda Haj.Uwani tace in yayi gaddama sai ta sabamai. Shi dai zai bi umarninta dana mallam ne ammh yana samun aiki bazai Zauna ba. Aranar suka fara tafiya gidan gona shi kanshi a wuni Daya kawai da yayi aikin Lissafi kadai ya yi sai da ya Jinjina Dukiyar baba mallam Aba na Fadamai a duk sati ana Fita da kwai Fin na miliyan Daya sai da ya Rike baki ya dai san gidan gonar babbane ammuh bai Taba maidakai akai ba. Da Daddare suka Dawo Haj.Uwani daya Shigo Falonta Tana jansa da Hira anan nema ya gayamata tana jin Uban kudi ta zare ido tana Fadin"kaji ko..? To ban da na gonakinsa kila in kaji abunda yake samu a shekara sai kanka ya Kasa Dauka..! Sai jin Dadi take yi tana Mirmishi shi dai wannan baya gabansa dukiyar Mallam bazata Burgesa ba Tunda ba nasa bace. Kwana Hudu da Fara zuwan Nazeem gidan gona da Sakar masa ragamar Wasu abubuwan da Aba yayi Mamammu taji labari shima suna Tare ne taji yana waya da Nazeem da ya gama ta tambayeshi yake fadamata Tare suke kasuwancim mallam yanzu yana taimakamai sosai da Umarnin mallam din. Mamanmu jiki na rawa ta koma Daki ta kwalama Anty Amarya Kira ta Sanar da ita abunda Aba ya Fadamata. Anty Amarya ta lailayo ashar ta maka kafin tace"Ammh Uwani dai an yi bakar Tsinanniya..Allah dai ya Tsine mata albarka.. Mamanmu ta amsa da Ameen madina da gaske take yi fa..! Anty Amarya tace"Ai na rigata..Nasha gabanta wlh..! *Janafty* *TFZB2019* *Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488* Mamanmu tace"To yanzu menene mafita..? So nake ki nuna ma Hajiya Uwani ita din banza da wofi..bata isa ba kuma bata kai ba wlh.. Anty Amarya tayi kwafa kafin tace"Ki kyaleni da ita Dayyaba..Ni yanzu abu Daya ke gabana Umar yazo ya tafi da Sakina Madina,kuma Hakan na gabda Faruwa saboda Cikin sati nan mai shiga yana tafe sakinar ma ke fadamin jirgin yawo zai fara yo gaba da kayansu..Kinga suna komawa shikenan hankalina ya kwanta Sai na Fuskanceta na nuna mata bata isa ba Daga ita har Sa"idun sai sun Dawo karkashin cewata ai Fara Bin sa gidan gona ba shi ne Mallam ya sakar mai komai ba Tukunnah dai Dayyaba akwai sauran rina akaba..! Mamanmu gabadaya yanayinta ya Sauya jin kalaman madina har suka gama wayar sama sama take amsata tana faman mata gatsine,Har dai ita mamanmu tagaji ta katse kiran lokaci daya tana bin wayar da Harara tana fadin"Haka kurum na kiraki da kudina da wayata ki Zauna kina neman gayamin mgana ina Dalili..! Dukiyar ai bataki bace Ko shi mallam din Daya tara bai Damu da ita ba sai ku kuna ta neman halaka kanku Saboda ita har kina Fadin har sa"idun sai ya Dawo karkashin cewarki..? Haka kurum ba kara sai ki maidamin Miji kamar kwallo ki dinga garasa yadda kika ga Dama to wlh madina Baki isa ba kan Sa"idu zan iya yin komai Ciki har da Raba Hanya Dake sai kowa yayi ta kansa kan mene ina Dalili wannan Bakinciki ina jin Dadi na Samu yadda nake so aikuwa Allah ne ya Hada mallam da Sa"idu ban ga mai rabasu ba haka kurum Madina ke wata mganar banza..! Surutun ma tana yi ne bata san tanayi ba Aba ne ya fito zai shiga bayi yaji tashin mganarta har ya shiga ya fita tana mganganunta shiyasa ya Leka Dakin nata yana Fadin"Balaraba ke da waye kike ta fada haka..? Tun dazu nake jin tashin mganarki nama Zata ko da hamida kike ne sai na Leka Dakinsu naga sun kwanta ita da Jawaad. Sai alokacin mamanmu ta Dawo Cikin Hayyacinta ta fara inda inda tana Fadin"Ni da masu yarenan ne yan iskan sai su kira ka suna maka gwaranci ko kai basa kiranka..?. Ya saki labulen yana Fadin"To da kin ji sune ai sai ki kashe wayar ki ni ai bani da Lokacin Sauraran irin su. ! Da haka ya koma Dakinsa Mamanmu ta Sauke ajiyar zuciya ta biyosa tana Fadin"Shikenan kuwa haka zan dinga yi musu sai mu rabu lafiya. ! Aranta sai taji salama da Aba bai Tsinkayi wasu daga cikin magnganunta ba. Ai data shiga goma ba uku ba. Acikin Satin kamar yadda Danmallam ya Tsara jirgi ya fara yo gaba da kayansu saboda yayi ma iyayansa da matansa siyayya musamman ma Amina Komai ya gani sai yace zai ma masu Ciki kyau harda kayan jarirai masu kyau duk ya siya ammh bai bari Sarood ta gani ba sannan yazo da Ruwan Zam zam mai yawa saboda mallam yamai mgana yana so da Dabinio sai sauran abunda ba"a rasa ba kuma bai sanar da kowa shi da Sarood zai taho ba sai dai agansu kawai. Kwana Biyu Tsakani kayan suka iso Jafar da Nasir suka je Filin jirgin Kano suka karbo kayan Direct Gidan mallan akayo da kayan Dakin Hajiya Daman kowa yasan in irin wannan ya faru kayan da komai Shashen Hajiya ake ijiyesu kafin ya Danmallam din ya sauka. Sakina ana chan ana shiri miji zai Dawo tayi gyaran kai tayi kunshi Sannan tayi gyaran jiki da na chan Shawaran Aliya ne ita ta Hadata da mai kayan matan ta siya awajenta. Miji kawai take jira ta riga ta gama Shiryawanta. Ko Amina in sukayi mgana in ta tambayeshi yaushe zai dawo sai yace ya kusa bai saka mata rana ba,yaki gayamata ranar da zai dawo so yake ya bata mamaki sai dai ta ga ya Kirata da Layinsa na Nageria. Haka kuwa akayi Ranar laraba suka sauka da karfe sha biyun Dare,kwana Biyar da sau kan kayansu suka iso a kano jirgi ya saukesu saboda Dare ne yasa bai kira kowa ba suka samu Tashar Mota shi da Sarood sai jakar kayansu suka nufo gumel sai wajen Biyu da wani abu na Dare suka iso gidansa ya wuce kai Tsaye sai dai Sakina taga Bakin Dare sai murnanta ta koma Ciki ganin Sarood sai da ta nuna afuskantar duk yadda taso ta boye hakan Sarood ko Cikin Murna taje ta Rumgume Sakina Tana Murnan ganinta.... Sakina tayi yake kawai tana Tunanin yadda Umar ya maidata banza ai bai gayamata kafarsa kafar matarsa ba Tana jin dadi ta gagari Amina Zama agumel shine zai jajibomata wannan Sakaryan. Dakin da aka bama Amina ta Zauna Sarood ta shiga sai dai yanayin Dakin da sauran kayan Amina Data gani yasa tasan an zauna adakin Saboda Gajiyan Hanya da kuma Dare yasa sai da Safe ta ma Sakina Zencen tunda suna Dawowa Umar Dakinsa ya nufa yayi wanka ya kwanta Sai barci sai da Safen suna kari Sarood ke tambayan sakina kayan waye tagani adakin ta..? Sakina Cikin kissa ta ke sanar da ita kayan Amaryan sa ne Amina nan ta Zauna Sarood ta kallesa sai dai batace komai ba ammh ranta ya baci meyasa Sai Dakinta baga Dakinsa ba..? Sannan wato ita aka raina meyasa bai ce ta Zauna Dakin Sakina ba..? Kwafa tayi har suka gama karyawa batace komai ba Sakina sai jin Dadi take yi ranta Fes domin da asuba sai da ta ribaci Umar yayi wani abu da ita kuma taga Chanji Sosai yadda ya rikice mata sannan karin jin Dadinta yadda ta zuga Sarood Cikin Ruwan Sanyi batare data gane ba Tunda ita Sakaryace shi kuma Danmallan kunu yasha baisan wata mgana yasan Nufin Sakina tunda ba yau ta saba raina ma Sarood din hankali ba. Ganin yadda ya Hade rai ne yasa Sarood din bata yi mganar ba Sai dai Daga yanayin ta sha ka matuka da Kishi Sosai. Suna gama karyawan suka shirya suka suka nufo Gidan Mallam Jafar ya Kira yazo da mota ya Daukesu daman Tun shekaranjiya an san sun iso Gida ya Rude da Murnan dawowarsa Gabadayansu har da Matan nasa duka Shashen Hajiya suka fara Sauka Har Sakinar domin ba hanyar da zata fara wucewa Shashen Anty Amarya ganin yadda ya Tsare gida.. Gabadaya matan mallam har da Anty Amarya nan shashen Hajiyar sukazo musu maraba su Hajiya Uwani kada aji labari sai barin jiki take yi Danmallan kallon Anty Amarya kawai yake yi yana Tuna labarin da Amina ta sanar dashi bai san Dalili ba sai yaji bai yarda da ita ba Tun balle ma ganin yadda take ta Kiftama Sakina Ido tana so su kebe suyi mgana ganin wannan balarabiyar da bata san da Zencen zuwa da ita ba, yana ganin su yayi kamar bai gani ba. Nan ya barsu ya tafi falon mallam shi da Nazeem suka hadu da Aba suka gaisa basu Dade ba suka tafi gidan gona ya Dade shashen mallam suna kara Tataunawa . Fitarsa ne ya bama Sakina Daman sulalewa ta koma Shashen Anty Amarya suka kebe Anty Amarya Cikin Bacin rai tace"Sai naga kuma wannan Sakaryan. ? Sakina ta tabe baki kafin tace"Nima yadda kika ganta haka na ganta..Ashe da ita zai taho..! Anty Amarya tace"To me kika fahimta da Zamansu tana nan a Hotonka ko kin Fahimci sauyi. !? Sakina tace"Anya..?nidai ban Fahimci komai ba..! Anty Amarya tace"To ki saka musu ido duk nasan aikin mallam na Dadewa yana Tasiri..! Da toh sakina ta amsa mata suka Ciga da Kulle kullen su tana bata Labarin Tambayar da Sarood tayi na wacce ta Zauna Adakinta da abunda Sakinar tace mata Anty Amarya na Dariya tace"Gwara da kika fadamata haka..Sakaryan sai ta bisa da tsiya..Ai Amina ba zaman gidanki ba ma Mijin da garin gumel gabadaya ne ya gagareta. waya gayamata Barno gabas take..! Sakina Tayi dariya kafin tace"Wlh kamar fa anyi ruwa an Dauke ko mganar fa bayayi..!. Anty Amarya tace"Ai bazai yi ba..Wayama sani ko auran ya Dade da Mutuwa fasawa ne ba"ayi ba kada aji kunya su Hajiya an yi Zani an yi Riga. ! Sakina tace"Zai iya yuyu wlh Anty..! Allah ma yasa hakan ne..!. Ta amsa mata da Ameen suna Dariya Ranar dai suna gidan har Dare wannan karon Sarood Shashen Hajiya ta Zauna tare da su Hanne tunda suna gida basu da Jarabawa wannan karon Sakina taji Haushin zuwa da ita da akayi yasa bata jata ajiki kamar baya ba Sai Dare suka koma gida,Washegari shi kadai yazo su suna gida Shashen Hajiya ya yada Zango aka Bude kaya ya bama Hajiya Tsarabanta na Turaren da Hijabin larabawa na mata sai Dogayen riguna guda Biyu masu kyau da Tsada da takalmi haka ma Anty Amarya da Haj.Nasara da Haj.Uwa dogayen riguna da Turare,Wannan karon har Hanne da Hamida yama Tsaraba domin bazai manta da kaunar da Amina ke musu ba, waya goma sai ta ambace su shiyasa daya siyo mata suma ya siyo musu Ya kuma nuna mata tsaraban Amina da Siyayyan kayan Jariran Da yayi,Hajiya Taji dadi sosai ta dinga yabawa sai dai Bata ga Tsaraban Mamanmu ba Tunda Har Aba ya yoma Tsaraba Sai alokacin ya tuna ma da ita Har ga Allah bai yi niyyar bata bane kawai Saboda tundaga Labarin da Amina ta basa yaji matar bata kwanta masa ba sai bai nuna ma Hajiya ba yace ya manta ne sai Hajiya tace bari ta bata Cikin nata. Sai ta hada mata da Ruwan Zam zam da Dabino. Hajiya ta aika ma su Haj.Nasara da Tsaraban Danmallan suna ta godiya haka su Hanne suka yi ta Tsallen murna,Ganin har dasu a Tsaraban Hamida da Hannen ma suka kai ma Mamanmu nata ta karba tana ta godiya da Santi tana auna kanta in tayi ma Aba kwaliya da ita.. Mallam dai Turarensa ne na Arab sai Zam zam da Dabino. Tsaraban sakina gida yakai mata nata Sai jin Dadi take yi ganin har da takalma ga kayan masu kyau da Tsada Na Amina kuma wajen Hajiya ya barsu su hanne kuwa tunda suka ga basu ga Amina ba kwana uku da Dawowar ya Danmallam ba labarin Dawowar Amina sai suka cire rai da Mganar Hajiya da kullum take sanar dasu Amina zata dawo nan kusa sai suka Sare.. Gashi har sun yi nisa a jarabarwarsu suna gabda gamawa gabadaya sai basa jin Dadin zama,ba Amina suma sun yi ahuru kamar basu agidan da ko da Amina ke nan wlh sai su shiga gidan mallam sau goma gidan Aba ma haka Rashin jinsu kawai yasa Dole ma asan dasu ammh yanzu sai a kwana awuni ba ba"aji ko motsinsu ba. Islamiya da Boko ma an gaji da Cigiyar Amina Daga baya ma su Hanne cewa kawai sukayi an cireta Daga mkaranta bata agarin harta mariya abokiyar fadanta da malaman makarantarsu Mallam Datti da kansa ya Kira mallam ya tambayesa Amina Mallam yace mai Amina bata gari ne shiyasa..! Kwana hudu da dawowarsa Ranar yazo Gidan da Safe Ya shiga shashen Hajiya suka gaisa da sauran matan Sannan ya koma wajen mallam to basu Dade da Mallam ba aka kirasa agidan mai anguwa Idi ya tafi kaisa Aba kuma baya nan sai ya tafi Dakin Nazeem ya dan kwanta ya Huta Sarood Tun abunda Sakina ta Fadamata take shamai kamshi sai bai Biye mata ba Sakina kuma kamar rana Daya zai mata Ciki takuranta ne ya Ishesa,yake barin mata gidan ita da Sarood din su ci kansu. Amina kuma tun washegarin ranar daya sauka daya Kirata bayan ya saka Layinsa na nan ya fadamata ya Dawo suka gaisa har take fadamai sun je asibiti ta fara awo sannan an mata Scan,basu wani jima suna mgana ba yace zai sake kiranta,kuma bai Samu Lokaci ba,Basu zauna sun yi mgana da Hajiya bane yana so yaje ya ganta kafin ya koma tunda ba wani Dadewa zai yi ba Sati Biyu ne zasu yi,zasu koma. Yana kwance har ya fara barci yaji sallama kamar daga sama yana Bude idanuwansa ya ci karo da Hanne da Hamida suna rabe raben shigowa Hanne na Tura hamida itama tana Turata mikewa Zaune yayi Daga kan gadon yana fadin"Ku shigo mana..! Jin haka yasa suka shigo Dakin kansu na kasa kamar wasu marayu duk suna Sanye da manya Hijabi har kasa mamakin ganinsu yayi gabansa suka Duka kamar masu neman gafara gaishesa sukayi ya amsa yana Dan Nazarinsa dazu a falon Hajiya yaga Hanne sun gaisa hamidan ne dai bai gani ba. ! Hamida kuma hanne ce taje ta jawota kan suzo su tambayi Ya Danmallam Tunda Hajiya taki fadamusu inda Amina take kila shi zai fadamusu shine suka zo a bakin Hajiya sukaji yana Dakin ya Nazeem Shine suka zo sun kuma kasa mgana saboda ba Sakewa Tsakaninsu sannan yana musu kwarjini. Shine yaga suna Sunkuye sunkuye kai da taba juna yayi mirmishi kafin yace"Lafiya..? Baku je makaranta bane yau..? Hanne tace"ai jarabawa muke yi yau bamu dashi sai monday..! Ya gyada kai sai yanzu ya tuna da Tsarin Tun farko,tunda Hajiya ta sanar dashi yadai manta ne,Cikin Sanyinsa yace"Kuyi mgana ina Fatan dai lafiya ko..? Hamida ta sanda kanta kasa tana Fadin"Dama..Dama..Muna so mu tambayeka ne ya Danmaallan..! Zama ya gyara yana Fadin"Allah yasa na sani..! Hanne ta zungura ita kuma sai ta kara kasa da Murya tana Fadin"Dama kan mganar Amina ne yaya.. Kai Tsaye yace"Amina..? Me ya faru da Aminar.? Hanne tace"Bakomai tunda Hajiya ta tafi da ita har yanzu bata Dawo ba..Muna ta tambayanta ina take taki gayamana gashi har mun fara jarabawa ba Amina muna kewarta ne Hajiya sai tayi ta ce mana zata Dawo Zata Dawo ammh shuru..Shine mukace bari muzo mu tambayeka muji ko kasan inda take..? Wlh kuma bamajin Dadin Zama ba Amina..! Hanne ta karbe da cewa"Kawayen mu sai tambayan mu ita suke yi..Kowa sai yace ina Amina.? Mu kan mu muna son sanin inda take..! Sai da suka gama Mgana yana kallonsu kafin ya saki Mirmishi ya tuna sanda ya kira Amina yace ya Dawo abunda ta fara tambayansa yaga Hamida da Hanne..? Don Allah ya gaishesu yace tana missing dinsu.ai shi shaida ne Saboda Rabin wayarsu mganar Hanne da Hamida ne ya Dade yana jinjina wannan kaunar Dake Tsakaninsu Amina tana matukar ji da Hanne da Hamida in tana Hiransu haka Zakaji Farinciki da Murna acikin muryanta Shi bai wani zauna dasu ba ammh yasan dai tare suke su uku ammh baisan Rayuwarsu ba gaskiya. Gyaran Murya yayi kafin yace"Kada ku Damu Amina na Cikin koshin Lafiya..Itama tace na gaisheku sosai tana kewarku..! Suka kallesa kafin su koma su kalli juna sai Hawaye duk ya Cicciko Idanuwansu Hanne tace"Muma muna kewarta don Allah tana ina..? Kuma yaushe zata Dawo..? Kai Tsaye yace"kuyi hakuri bazan iya Fada muku inda take ba..Ammh tana Cikin Koshin lafiya..Sannan zata Dawi kowani Lokaci itama bata manta daku ba koda yaushe Cikin Zencen ku take yi..! Kawai sai suka fara mai sharan kwallah ya kallesu baki bude bai yi mamaki ba in ya Tuna yadda suka rika uban kuka Ranar da zai tafi da Amina gidansa. Gyara zama yayi kallesu yana Fadin"ku share hawayenku..Ku Zauna Dakyau yau labarin Amina zaku bani Tundaga Farko har karshe..! Yau ina so naji nima..! Hama kurum yake son jin Labarin Amina,batare da yasan Dalili ba. Jin haka yasa suka gyara zama suka Fara bashi Labarin Amina da yarintarsu Hanne tayi in ta gaji Hamida ta karbe in suka fadamai wani abu baya sanin ma yana Dariya jin jina Jidalin Amina kawai yake yi aransa ashe haka tayi nisa bai sani ba ? Kirarinta ke basa Dariya in ya Tuna wai Aminene ikon Allah badai ta Mutum ba sai ta Allah lalle yarinyar nan sai Allah taci kuma kirarinta.. Hanne ta Karbe da Fadin"Wlh ya Danmallam Amina tana da kirki sai wanda ya Zauna da ita ya sani...Tana da son yan"uwanta sai dai akwai abu Daya Amina tana da riko in ta Tsaneka sai Alllah sannan tana da Fada da Tsiwa kuma bata Laushi ko bata da gaskiya sannan ga son jin gulma,Amina fada ko ba nata bane siyanta take yi a makarantar boko da Islamiya ba malami ko Dalibin da baisan Jidalin Amina ba,ba wanda ta Kyale tana da Fara"a sai dai bata Daukan Reni bata kuma son arainata kan Hamida da hanne Amina Zata iya yin komai tasha Fada saboda mu kuma duk wani abu da ake yi Amina ce gand leader din mu. Ya Danmallam ga ni Amina wata Hudu ta bani Hamida kuma wata uku ta bata ammh nuna wa take kamar ta Girmemu Amina bata san Faduwa ba bata nuna gazawarta Wlh ko su ya Abida ban shaku dasu yadda na shaku da Amina ba tunda muka taso bamu taba Rabuwa ko na kwana Daya ba,Shiyasa Rashinta ya ke sakamu cikin Wani hali komai baya mana Dadi..! Hamida ta karbe da Mirmishi tace"kuma ba"a zaman minti goma da ita ba"ayi fada da ita ba..tafi Fada dani Fiye da Hanne saboda ni bana gani na kyale Hanne kuma bata da yawan mgana,Mu yi fada mu Shirya hakanan muke zaune duk duniya ba wanda yakaimu sanin Amina sannan mun san Halinta sai muka ci Mganin zama da ita, jidalin Amina ni da Hanne kadai muke iya Daukan ta, ko Ciwo tayi kowa sai yaji wani iri saboda Amina mai Fara"a ce sannan tana da Dadin zama ga wanda ya santa sai dai kawai Fada da Zafin rai sannan bata Daukan Reni Haka Aminene take bata da tsoro bata Shakka Kirarinta badai ta mutum ba sai Allah..! Ko abunda ya faru na Aminu Tsausayi ne wlh ba Halin Amina bane nan ta shiga bashi labarin soyayyar ta da Aminu tundaga farko Har karshe da abun da ya Faru Hamida ta kareshe da Rantsuwan wlh tallahi ya Danmallam Tsautsayi ne ammh wannan ba Halin Amina bane barta da Jidalanta ammh Namiji baya gabanta soyayyarta da Aminu kaddara ne ta Ubangiji..! Da Dukkan Hankalinsa yake sauraranasu duka labaransu suna shiga kansa wasu labaran na Amina abun Dariya ne wasu kuma ya Dauki wasu abubuwa da mganar Data Fadamai akwai kamshin gaskiya ko wani yaro akawai irin yarintarsa ammh na Amina yayi yawa wannan Rashin Tsoro da rashin jinta yayi yawa ba nata bane ita kadai da gaske an kara mata ne duk da abun ya Tarda Halinta ne ya gasgasta mganar ta Dalilai da dama sannan ga abunda ya Lura dashi a wajenta lokacin da ya kusanceta din nan ya Fahimci akwai matsala sannan ga mgangan su Hamida sosai yaji tsausayin Amina da wani Kaunarta na shiga ransa bai sani ba.. Mganar Aminu kuma mallam yadan Fadamai kadan Daga Cikin abun da ya faru Lokacin bai wani mai da kai ba kan mganar tunda alokacin yana ganin Aaminar kamar ta riga ta gagarane aransa kuma sai yaji ya baci da jin Labarin yadda su Jafar suka Dinga Dukan mai mata gaskiya ransa ya baci da Yana Kasar sai ya hanasu ai wannan abun yayi yawa kamar sun sanu jaka su bazasu Fahimci wani abu kan Amina ba..? Yayi mamakin da ko mallam bai Taba kaawo wani abu acikin Ransa ba sai dai kila wani abu Allah bai Cika bayyanasa da wuri ba sai Tafiya tayi tafiya mganar Aminu kuma bai Damu ba yasan ba son shi Amima ke yi ba yarinta ne da kuma kaddaran auransa da Amina shi kamar ma taimakonsa yayi sannan da kuma karfin rabon dake Tsakaninsa da ita Mirmishi yayi har Hakoransa suka bayyana kafin yace"Wato Aminene dai ikon Allah ce badai ta mutum ba sai ta Allah..! Hamida da Hanne sukayi Dariya suka Dukar dakai shima Dariya yayi yana tuna wai tace ma malamar corper dinsu tana warin maza kawai sai yaji wani abu mai gardi da Zumudi kan Amina na kara mamaye ransa To ai a jidalin nata zata zama uwa..! Lalle akwai kallo sannan Jidalin akwaishi kam Nan ya samu ya lallaba su hanne yace zai hadasu suyi mgana da Amina ammh bai sanar dasu inda take ba sun ji Dadi da sanyi tunda Amina dai tana Lafiya sannan tunda yace zai hadasu susan bazai musu karya ba sannan yace kada su fadama ko Hajiya mganar da sukayi. Adaran yayi ma Hajiya mganar zuwa Abuja Hajiya tace ko da yaushe ya shirya yaje mana ya ganta.. Kansa na kasa yace zai sanar da Mallam jibi sai ya tafi gobe zai je Dutse shi da su Sarood su gaida Aliya matar Aliyu tana asibiti Ciki na bata Wahala... Hajiya ta jajanta kai Tsaye tace ma Danmallam ya Dauki Aliyu ya rakasa Abujan mana. Cikin mamaki yace"Hajiya kin manta kin ce ko shi kada yasan komai..? Hajiya tace"Ka sanar dashi nasan shima bazai sanar da kowa ba..Bai kyautu kaje kai kadai bane..! Ko Jiya sai da nayi ma Sa"idu Tsiya kawaicinsa yayi yawa bai Taba Tambayana ina Amina ba ko ina na kaita ba.? Anya akwai Uba irin Sa'idu kuwa..? Cemin yake yarda da nayi Dake Hajiya yarda kika rikeni Tsakani ga Allah na Tabbata duk inda Zaki kai Amina Za"a kula da ita kuma bazaki kaita inda Za"a Cutar da ita ba .! Danmallam mirmishi kawai yayi bai ce komai ba Tsakanin Baba Sa"idu da Hajiya ko mallam baisan Tsakaninsu ba ballatana shi da ba mazauni ba sun Dade suna Hira da Hajiya kafin ya mata sallama Shashen falon ya koma sukayi mganar Tafiyarsu Dutse gobe da zuwansu Abuja shi da Aliyu mallam yace yana da kyau hakan Aliyu ai Aminini sosai sannan ya bada Sakon gaisuwarsa ga Mamarsa Amina. Daya fito daga wajen Mallam shi da Nazeem suka yi hira sai after 10 ya koma gida Sarood ta kwanta Sakina dai na Zaman jiransa ya riga yaci abinci shashen mallam shiyasa bai ci wanda suka shiryamai ba yasan Daman abunda take mawa shi har mamaki take basa zafin nema na kawo samu ne..! Tunda ya Dawo bata barsa ya Huta ba koda yaushe abu Daya ce mata akayi haka ake samun Ciki..? Koda yake duba da Cikar Burinsu ai yasa tama Fita daga hankalinta Kada ya Danne mata Hakkinta yasa ya Biye mata kuma duk Shawaran Anty Amarya ne Ta Dake ta maida Cikinta Datayi barinsa. Washegari karfe tara na Safe suka Dauki Hanyar Dutse shi ke Driving din Sakina na gidan gaba Sarood na baya sun isa da wuri Ajiyan aka Sallami Aliyan tana gidan chan suka wuce Direct bayan sun ci abinci sun huta sai mazan suka shiga Cikin gari suka bar matan agida Sakina da Aliya suna mgana da Hausa suna Yamutsan fuska suna zunden Sarood, ita kuma tana kallon su tana washe baki batajin me suke Fadi Daga baya ma tashi sukayi suka shige Ciki suka barta ita kadai afalo kamar mayya su kuma sai bayan La"asar suka Dawo abokansu suka ziyarta da sukayi makaranta tare da aiki ya kawosu Dutse da zasu dawo suna Hanya Danmallan yace gobe da Safe ya zo zai rakasa Abuja Aliyu bai kawo komai ba Tunaninsa wani abun zai kai Umar din Abuja. Yasa bai matsamai da Tambaya ba ya amsa masa da toh Allah ya kaimu. Bayan La"asar suka Dauki Hanya bayan su Aliyu sun rakosu da Fatan isa Lafiya da suka Dawo gidan mallam suka Sauka sai aranar suka shiga gidan Baba Sa"idu suka gaisa da mamanmu shima adaran ya shiga shida Aba suka gaisa da ita sai kallonta yake yi yana Nazarinta haka kurum daman shi tun Farko kirkirta bai mai ba sai kuma ta kara Dora kanta azargi da Aba ya shiga Shashensa ta fara tambayansa Amina harda sharan kwallarta na karya wai Hajiya taki sanar ma kowa inda takai Amina.. Mirmishin yayi kafin yace mata shima bata Fadamai ba sai ta fara sallallanmi tana Fadin Allah yasa to dai lafiya. Har ya mata sallama ya fita yana Auna mganganunta Biri dai yaso yayi kama da mutum a kaunar datake ma Amina in har na gaskiya ne Amina Bazata kai wannan wattanin bata nan ba bata wani damu ba gaskiya bai yarda da ita ba daman mutum ya cika Kirki wani Lokacin mugu ne. Sai dare ya kwashi matansa suka koma gida adaran ya Fada musu gobe zai je Abuja wani aiki zai kaisa ba su Damu ba ita kanta Sakina bata kawo komai aranta ba ta Dauka dai aikin zai kaisa kamar yadda yace. Washegari kuwa agidan mallam suka Hadu da Aliyu bayan ya gaida su Hajiya suka Dauki Hanya,Hajiya ta bata Goriba da su Rama da zogale da kulu su gauta da yalo da Daffafiyar gurjiya akaima Amina sun yi mgana da Aisha ta fada mata abincin zamani Amina bataci sai na gargajiya. Danmallan ya taho da Tsaraban Amina tare da Ruwan zam zam din daya riga ya karanta mata duka ayoyin dake karya sihiri aciki sannan da Sauran addu"o"in Tsari Domin ya yardan ma kansa Amina ba ita kadai bace. A motar Aliyu sukayi tafiyar dayake sun tafi da wuri sha Biyu suka shigo Abuja Usman mijin Aisha Danmallam ya Kira yayi musu kwatance cikin Lokaci sai gasu a anguwan maitama Dayake gidajen akawai lamba sai gasu agidan Usman ya Fito ya tarbesu daman yana gida ya samu dan break yana Hutawa kuma shima sai da Safen nan Ya Dannallam ya kirasa ya fadamai suna tafe kuma yace kada ya Fada su Aisha..! Sai da suka iso gidan ne Aliyu yaga Usman sanna ya kalli Umar yana Fadin"Daman gidan Aisha zamu zo..? Ko wannan ba mijinta bane..? Lokacin Usman din yayi gaba suna Binsa abaya zuwa Cikin gidan. Danmallam yace"Eh ammh ba wajenta nazo ba..! Aliyu Cikin mamaki yace"To wajen wa kazo..? Ai naga har sako Hajiya ta baka ka kawo mata. ! Kamar bazai yi mgana ba sai kuma yace"Zaka ganta ita wacce nazo Dominta..! daidai suna shiga kayattacen Falon na gidan Aisha. *Janafty*