🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA BISSIMILLAHI RAHAMSNIN RAHIM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI INA GODIYA GA ALLAH DAYA BAN DAMAN FARA WANAN LITTAFIN, UBAGIJI INA ROKON KA YADDA MUKA FARA A SA,A MU KARASA SHI CIKIN FARIN CIKI DA JIN DADIN JUNAN MU. YAN UWA MASOYANA HAR KULLUN INA MAI KARA BAKU HAKKURI DA KUYI HAKKURI DA ZAMAN TARE ZOMU ZAUNA ZOMU SABA DA FATAN ZAMU FAHINCI JUNA DAKU DON SAI KUN KARA HAKKURI DANI SAMA DA FARKO A YANZU KASANCEWA ZAN HADA TAURA BIYU A BAKI LOKACI GUDA. BADON KOWA BA NAI HAKA DON KUNE MASOYA NA MASU KAUNATA A KULLUN FARIN CIKIN KU SHINE NAMU DON DA BAZAN KU MUKE RAWA A KODA YAUSHE. FADA KARWAN DAKE CIKIN LABARIN NAN UBANGIJI YASA MU AN FANA DASHI AKAN MU DA YAYAYEN MU ALLAHUMA AMIN. DARI UKUNE HAR YANZU BAN KARA BA IDAN KINA SO SAI KU TUNTUBENI A LAYINA DON HAR YANZU DASHI NAKE AMFANI BUT ONLY TEXT DON DA WUYA KIRA YA SHIGO MIN A NAN YANZU. 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MTN KO EIRTEL NAGODE ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMIN SHI AMIN. A hankali take saukowa daga matakalan jirgin jirgin mai tambarin Nigeria Air way daya sauka a filin jirgin malam Aminu kano. Fuskanta yana saye da bakin glass din ido sai takunkumin dake saye a fuskan nata bayan ta yan samari biyu ne masu tsanin kama suna mara mata baya. Doguwar rigace baka a jikin ta sai gyalen shi data yafe har zuwa kanta takalman dake kafanta flat ne basu da wani tudu sosai . Sai handback din hannun ta data riko wanda ba wani babba bane sosai dan madaidaici dashi. Kallo daya zakai mata ka gane hamshakiyace ita din don siffan shigar da tayi kawai ya isa ya nunama hakan. Hjy Iyami ke nan matar tsohon Ambasardor din kasar America wanda ya wakilci Nigeria a 1986 zuwa 93 . A hankali ta runtse idanuwan ta kafin ta bude su ta kara kallon yanayin kasan nata na haihuwa wanda a yanzu ya zama mata abin kallo. Duk da dadewan da tayi bata a cikin kasan hakan bai hanata ganin wasu abubuwan da ta bari ba a tsawon shekarun data kwashe bata kasan. Da mamaki irin halin gwauntin kasan ta Nigeria a ranta taci gaba da saukowa a matakalan jirgin sannu a hankali duk da yanayin kasan nata hakan bai hanata son ganin ta dawo kasan ta na gado ta zauna tare da iyalan ta ba. Easy hajjajo daya daga cikin samarin dake bayan ta ya fada don ganin irin yadda take bin ko ina da kallon mamaki don rashin ganin wani cigaba da da kasan tayi sosai a zuwa nan lokacin data dawo. Don tun bayan barin mijin ta aiki sai take can da iyalinta dake kararu inda itama take aiki da wani company a can hakan ne ya dauke mata hankali da gida sosai. Sai yanzu take ganin dacewan dawowa gidan a cikin yan uwa da abokan arzikin su da suka bari badon komai ba sai don tarbiyan yaran ta da jikokin ta dake tasowa yanzu. Saboda yawan haramtatacen al,adan da yanzu ya mamaye duniya sai take ganin namu tarbiyan na malam bahaushen kamar daban yake da sauran tarbiyan wasu al,umman na duniya a yanzu . Don shi malam bahaushe yana mayar da al,ada ya zama addini sosai a gareshi balle kuma abinda addini din ya koyar damu. Duk da lalacewan duniya a yanzu malam bahaushe yayi kokari wurin ingata wasu tarbiyan da su koma kamar addini a garshi wanda yake taimakon al,umma a yanzu. Hakan yasa ta yanke shawara ba tare da zaunawa ta shawarci kowa daga cikin a halin nata ba a yanzu da take shugaba a gidan ga baki daya. Ba karamin tashin hankali ta fuskanta ba a gurin yaya da jikokin ta don jin zancen komawa sun gida Nigeria da sukayi. Wanda hakan yasa ta rufe ido taciwa kowa daga cikin su mutumci kan umurni ta bayar ba rokon su takeyi ba. Hajiya Iyami bata fada ma kowa ba saida komai ya gama kammala daga banhareta a yadda take son komai yazo mata daidai idan sun dawo. Gama daga gyaran gida zuwa company da sauran abubuwan rayuwa ta rigada ta kammala komai yadda zai tafi mata idan sun zo ba tare da sun sha wahalan komai ba tunda akwai kudin su ta fitar aka aiwatar masu da komai yadda take bukatan shi. Har zuwa yanzu da Allah ya nufa sun tataro sun dawo Nigerian da zama inda duk tawagan nata suke ransu a bace don suna ganin ta rabosu da rayuwan inda suka saba dashi yanzu ta kwasosu zuwa kasan da duhun kai da jahilci yayi katutu a ko ina. Alhamdullahi a bangaren hjy don ta isa da kowa na ahalin nata daga mazan su har matan su babu mai iya musa mata ga bukatan nata idan ta fada. Haka yasa abin ya kara zuwa mata da sauki sosai don bata samu tangarada a kowan su ba sai gun babban danta koshi ta daga mai kafa saboda irin aikin shi ne a can don shi tun gama karatun shi yake zaune a kasan chaina inda yake aiki tare dasu. Ta yarda da imanin shi dari bisa dari don ta auna shi taga yana da riko da addinin shi yana kan tarbiyan da suka bashi tun farko. Wanan dalilin yasa ta yarda ta barshi a can inda yake aikin wanda a yanzu zamuce shine dauke da nauyin komai da kowa na ahalin don iya sarrafa na,uran computer daya iya da wasu fasahana zamani kasan na chaina ta dauke shi yake aiki tare dasu dama wasu company na kere keren zamani. Motocine a jere a da suka zo daukan su wanda duk gaba daya nasu ne da aka saye da sunanyen kowa a gidan. Baya bo ba fallasa fuskan hjy iyami a dan sake tana farin cikin ganin yan uwanta dana mijin ta da sukazo filin jirgin don tarbon su. Aka dan gagaisa a gurguje inda kowa ke son nuna kulawan shi a garesu kamar dai yadda akeyi ga kowani mai hali a cikin zuria, Bayan shigar su motane inda sai a lokacin ta fata samun natsuwa a hankali ta runtse idanuwanta tana mai tuno da mijin ta marigayi Alh ma,azu ambasado. Wanda shine dalilin gatansu a yanzu har suka kai hakan ga Allah ya azurta yaran su da ma wasu dake zaune a karkashin inuwan su ta sanadiyar shi. Saidai ubangiji bai nufi yaga wanan baiwan ta yayan nasa ba a duniya don yanzu shekara kusan goma ke nan da Allah ya karbi rayuwan mijin nata. Duk da hakan suna zaune a can waje kamar yadda suke zaune tun farko da yake raye rasuwan shi bai sa sun dawo gida ba tun wanan lokacin saboda aikin ta dana yayan ta da sukeyi a can. Dan tafiya sukayi kasancew nisan kano da kaduna ba wani tazara mai tsawo bane sosai yasa basu kara wani wahala ba sosai. Duk hjy na cikin halin tunanen irin rayuwan da zasuyi a nan din yanzu cikin yan uwa da abokan arziki a haka suka shigo garin kadunan don ita bata ga wani nisan tafiyan da yaran nata keta faman jan tsukin nisan sa ba . A nan ma sun samu dandazom yan uwa na kusa da suka cika gidan suna murna da zuwan wanan family din. Anci ansha an gagaisa tare da tambayan bayan rabo inda yaran nata da duk mazane sai autar ta da matar danta dayayi aure saidai bata yarda ya auri yar can ba yar nan cikin dagi ta aura mashi aka kai mata ita can suke zaune lafiya da ita don iya zama da sarakuwar nata da ta iya. Tun wanan ranan rayuwa ta koma masu sabo a gidan ga yan uwa na nisa da kusa dasuke zuwa taron su da murnan dawowan su gida lafiya. Dawowan ta kasan yasa ta dauko diyan yan uwa mijin ta mata biyu ta hada da yarta suke zaune a tare. Saidai asali ba itace ta dauko su ba sudin ne dai sukaga wurin zama suka zauna a gidan tare dasu. Hajiya bata nuna komai ba illa kara jan su a jikin da tayi suka zauna a tare da sai yar sister daya suka cike su hudu yan mata a gidan. Rayuwa na jin dadi da sakewa sukeyi don hjy iyami na tsaye da saka ido ga motsin kowa a gidan. Saidai ta fanin karatu da jin dadin rayuwa a cikin gida duk abinda suke so a ransu tana ganin ta kawar masu da shi don kawai kada su gani ga wani har su saka rai sukai ga dauko mata magana. Ta farko itace salma yar gurin kanin mijin nata dake kula da duk wani al,amarin su daya shafi gida don shi suke sakawa a gaba tankar maigidan nata yana raye don mutumin yana da fahinta dakuma biyayya daya dace. Sai Rufaida diyar autar su maigidan nata dake aure a jos a can suke zaune da mijin ta da yaranta Rufaidace yarta ta biyu itama dawowan hjy nan kasan . Daga zuwa da sunan hutu tun lokacin bata koma ba take zaune tare dasu don jin dadin irin rayuwan da ake a gidan. Sai ta uku jamila ke nan diyar autan su hjy da ita kanta hjy ta dauko ta don ta sahalewa yar uwan nata nauyin yaran da suke a gaban ta zata debe mata wani kewan itama a matsayinta na yar yar, uwan haihuta. Tankar yar cikin ta take ganin ta a wurin ta don hakan ta daukesu gaba dayan su tankar diyan data haifa a cikin ta suma ba laifi a nasu bangaren hakan suke kokarin nuna mata kamar yadda itama din take kokarin nuna masu duk daya suke a wurin ta. ANCAU Tun a soron gidan nasu take jiyo muryan Asabe kakar su data haifi mahaufisun tana faman zazzaga bala,i. Dukda bata shiga gidan ba tasan bada kowa Asabe ke wanan fadan ba haka illa da mahaifiyar su. Don inda sabo aita saba da wanan hali na Asaben don tun bata da wayo da wanan hali ta bude idanuwanta a gidan. Kusan kullun fitinan Asabe ne ke tayar dasu daga barci na yau daban na gobe daban. Yau ma daga inda take take jiyo muryan Asaben tana fada akan iccen girki da innar tasu. A haka ta karasa ciki rai bace duk da gajiyan ranan data kwaso ga yunwa ga kishin ruwa don tun safe da ta fita bata karya ba . Hakan kuma ta juyo gida da kafa duk da nisan dake akwai daga makaranta zuwa gidan su. Shigowan Abu gidan bai hana Asabe fadin abinda take fadawa mahaifiyar tasu ba a lokacin. A daidai lokacin inna ke fadin adan maraice umma dama ba wani icce mai yawa bane dashi nayi koko da safe yanzu kuma na danyi muna danbun tsakin da akwai don yaran nan idan sun dawo su samu abinci. Duka bakin wutan baifi guda hudu da guntu indon ruwan dumine barin hada gawayin nan sai ruwan yayi dumi ki samu ki watsa din. Salman Abune yasa su juyowa gaba dayan su sai dai inna ce tayi karfin halin anwa a lokacin duk da tana cikin rudu da rikecewan bala,in Asaben. Asabe na fadin to sannu issasa mai diya ke kika san zafin diyan su kin iya kokarin nema masu abinda zasuci. Niko nawa dan dabai damu dani ba ai haka yasa kafa ya fita bai damu yasan da damuwata ba. Saukin abindai kema yaya matane a gaban ki, kinkin zuciya duk da gorin da kike sha a gari ki haifa mashi ko da naji dayane da zai taimaka mai idan karfin shi ya kare yasan yana da magaji. Ke kenan kullun dauksn ciki kina zuba mai diya mata a gida yau ace kitso gobe kumshi sai ko na omo. Ta yaya zai samu ya aje kullun laluran su yana kara yawa gareshi kullun yana fita nema ba matai maki sai Allah. Da maza kika haifa ai zai sa ran zasu taimaka mai a wani gurin ga wanan data saka kanta wani karatun boko da baida amfani a gurin ya mace. Abu dake kallon ta da mamaki tana cire takalmin makarantar dake kafanta wanda duk ya sude a titi saboda rana da yawan bin hanya ga ba kudi balle a saya mata sabo dole haka take maneji dashi. Saukin abin ma yanzu duk da karancin shekarun ta amma haka ta samu don kokarin ta ba,a taba mayar da ita baya ba har takai aji shida tana neman fitane yanzu. Duk irin matsin da Asabe kewa mahaifi su akan karatun nasu baida wani rana garesu kasancewar su na yaya mata gareshi. Don a cewar ta aure zata masu da zaran Abu ta cika shekara goma sha biyar da haihuwa a duniya don ko yanzu wasu daga cikin sa,annin ta sun riga da sunyi aure suna gidajen mazan su zaune daram. Muryan Asabene ya dawo da ita ciki tunanen da takeyi tana fadin ke kuma munafuka ki kura mi ido kuru kuru kina kallona dasu. Don rashin kunya rashin tarbiyan da baku samu ba tun farko ga uwar ku babba na magana yara suna kashe shi da ido don rashin kunyan da kuka gada a wurin uwar ku. Karya nake fada ba gaskiya na fada ba komai ya samo yana gurin ku keda yan uwan ki da makiran uwar ku ku gaku ga bawa na haifar maku ko ? Ice ma da mutum zai saka ruwan dumi ace an kona shi a gidan nan gaba daya wanan wani irin masifane yaron nan ya haifar min a gidan nan. Baki na turo gaba don jin irin cin zarafin da kullun Asabe ke muna muda mahaifiyar mu har wata rana takan tsaya sai baba ya saki inna ko kuma ya kara auren macen da zata zo ta dinga haifa mai diya maza a gidan mu. Da kyat Abba da wasu makwabta sukan iya shawo kan Asabe idan ta fara wanan bambamin nata lokacin. Inna dai tana duke a bakin murhu tana kokarin hura wuta da gawayi ne data dan kashe dazun sai faman fifita wutan take don ya kama. Daki na shiga na kwabe tufafin makaranta dake jikina don sanin bamu da clean din da zamu wanke a yau don gobe haka yasa na kwabe su na baza a dan gambun langa langan kwanon dake kofan dakin namu nafito. Wurin madafin namu na hara ina fadin inna kawo in hura kije ki huta hakana da ranan nasan tun safe baki huta ba. Barshi inna ta fada tana kokarin boye fuskanta gare ni don kada inga hawayen dake zubo mata a idanun ta a lokacin. Wanda nasan ba komai inna kewa hawaye ba sai gorin diya matan da Asabe ke mata don indan don fadan barana da Asabe ke fadin tanayi ne ta saba da wanan sai dai wana gorin ne inna bata iya shayewa a ranta sai ta nuna gazawan ta anan. Da kyar inna ta yarda ta bani maficin tana fadin kije ki huta yar mairo dan inna bata kiran sunana kasancewata yar fari a garesu. Ina tsugune bakin murhun Abba ya shigo gidan da kayan aikin shi idannun shi ya sauka a kaina yake fadin yar mairo kece har kika shiga girki daga dawowan ki haka? Dagowa nayi daga inda nake ina fadin Abba sannu da zuwa na nufo shi don amsar ledan dake hannun shi. Bayan na karba na juya don zuwa dakin su in aje Asabe ta fito tana fadin to to mai zaki tura daki daga kawowa yar nema data gaji kilibibi a gurin uwarta. Kai haba umma ba komai bane a ciki sai dan garin tuwo da kubewa ko za a samu a dan tuka da dare a samu naci . Don na fita dazun ban samu bada ko sisi ba a samu ko abin karyawa a gidan nan ina can na damu da tunane tun safe ina faman babu kwasta duk masu zuwa sai cewa suke ai masu bashi idan sun samu zasu kawo kudi. Kai Amma mutane sun lalace yanzu da son bashi facin ma shi kanshi bashi za ai masu shi kai Allah ya rabamu da fititinun duniyan nan . Sai lokacin Abba yakai kasa yana fadin barka da wuni umma mun wuni lafiya ya gidan kuma. Mun wuni lafiya ba lau ba dai tunda ko ruwan da zan dan samu in watsa a gidan nan ban kaiga samu ba har yanzu. Don kawai nace bazan iya wanka da farar safiya ba sai kawai a hana min ruwan ina kallo wanan matar taka ta hura wuta a gidan nan har ta gama abinda take saida taga icen ya kone ga baki daya . Amma yarinyar nan ta kasa saka min ruwan dumi in watsa don bakin ciki da rashin sanin muhinmancina a gidan nan. Daga inda Abba yake tsaye yana jin Asabe takai ayah yace kiyi hakkuri umma . Kin sa halin da nake ciki yanzu aikin ne nawa babu kasuwa ko ina ya rufe yau kwana uku sai ita saudatune ke dan dabara a cikin aljihun ta muna samu muna dan tabawa. Asabe tace da mamaki karara a fuskan ta take fadin haka ka koma ban sani ba dan nan ? Kai bakaji kunyar fadin wai ashe mace ke ciyar damu duk kwanakin nan a gidan nan ba. Mafarin abin gari ana yadamu da fadin talaucin mu yakai haka har mace ce take ciyar damu a gidan nan kai ka kasa. Kaga amfanin haihuwan da namijin da nake fadama ke nan da yanzu yarinyar nan namiji ne aida ta fara taimaka maka ta wani gurin. Inna ta fito dakin ta nufi wurin madafin danbun tsakin masaran data hadane ta shiga rabawa yayin da tsakar gidan namu yayi shiru kowa ya zuba idanu yana kallon inna. Na Asabe ta fara zubawa ta mike ta nufo ta tana fadin umma akai dakine ko a kawo maki nan aje anan in gani Asabe ta fada a hasale. Saida Inna ta kai kasa don girmamawa ta aje kwano a gaban ta inda take zaune saman kujera dan tsugunno. Bude kwanon samiran tayi tare da juya dan danbun dake cikin kwanon a yatsune tana tabe baki kafinta dago kai tana fadin. Saudatu wanan abincin fa kamar za,aba dan goye shi ta juya wurin Abba tana fadin ka duba dai ka gani da idanuwan ka yanzu dan abinda aka zubamin. Don kawai kace itace ke ciyar damu a gidan yanzu ai dole wullakanci ya shigo a bani abinda akaga dama don kawai rainin da kaja muna don kasawan ka yanzu da gidan. Umma ba hakana bane kiyi hakkuri tsakin ne baida yawa iyakarshi ke nan dan gyara don yaran nan dake. Nasan nida malam ba samu zamuyi bama a karshe tace duk da haka a kara min don wanan dai ba isane zaiyi ba ehhe. Kallin Asabe nayi lokacin da naji ta fadi hakan ina mamaki hali rashin tausayi irin nata duk da jin zancen inna din da tayi. Dakuwa ta jefo min da hannun tana hagu tana fadin daina kallo na yan nema mai kama da yanyawa. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL TA BANK KO KATIN WAYA DON TURAWA A BANK ZAKI IYA TURAWA A WANAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK ALLAH YA BADA IKON BIYA A CIKIN DAUKI AMIN Ki daure ki guji shiga hakkin wani abinda ka raina shike zama babba gareka don Allah yar uwa mu guji daukan hakkin a kan mu ki daure ki biya ki karanta don Allah. Hjy ce zaune a falon ta hannun ta rike da waya kaya take oder da za, a turo masu dan yanzu ba sai ka fita zuwa waje ba idan kasa hutar da kanka waya ya wadatar da komai ga kowa. Sallaman da akayi daga kofane ya dawo da ita cikin hankalinta ta dago kai tana kallon kofan shigowa falon nasu. Da fara,a a fuskanta tana aje wayan daga gefen kujera take fadin kune tafe sannun ku da zuwa a cikin fara,a kamaf yadda ta saba tarbon duk wani dan uwa da zaizo gidan musanman daga bangareta kona mijin ta . Yanzu ma yan uwan mijin tane su biyu sula shigo gidan barin abinda takeyi tayi ta tari bakin nata. Yau kan mun taki sa,a kina waje don zuwan mu biyu ana fada muna kina ciki bazamu ganki ba. A daidai lokacin ta sauke glass din dake idon ta tana fadin abako fada min zuwan ku ba gidan nan ko sau daya. Dayan tace yau dai aimun taka sa,a mun samu kina wajen dan dariya hjy iyami ta sakeyi tana fadin mun dade bamu haduba. Safiya ya bayan rabo wace ta kira da safiya tace wallahi haka al,amari yakan kasance ai rayuwa ke nan idan na tuna baya sai nakanji kamar abubuwan da su dawo sabo. Dariya sosai hjy iyami ta sake tare da fadin kin tuna zamanin kurciya ke nan dai ga wanan zancen naki. Safiya ta lumshe ido tana bin lafiyan kujera sanyin AC yana ratsa jikin ta a hankali tare da fadin bari matar yaya ai kowa tuna bara baiji dadin bana bane. Jin hakan hjy ta fahinci mai take nufi yasa tayi saurin kawar da zancen tana fadin bari a kawo muna abinci muci nima yanzu na dawo gidan . Yau na fita ziyarane har gidan su Ado da salihu nake don tun zuwa na garin ban leka kowa ba bako dadi mutum yana kulaka kai baka mayar da kara akace. Tana fadin hakan ta mayar da hankali kan wayanta dake gefe dauka tayi ta kira mai aiki tare da umartan a kawo masu abinci tana da baki a falo. Kai matar yaya wai wasu baki har yanzu dai wanan halin naki yana nan ashe ance idan kasan mutum ko shekara nawa ne kada ka tambayi halin sa. Murmushi hjy tayi tana fadin meye duniya sa,ade wanan duniyan har nawa yake ga bawan sa. Idan badon muzo mun gani da idanun mu bazamu taba yarda da kina nan a yadda kike ba a yanzu. Wai sa,ade ina da wa yanda sukafi min kune a rayuwa duk mace mai hankali da tasan ya kamata ai baki nata ba ko yaya yake kuwa. Don samun duniya sai idon ka ya rufe ka mata da goben ka ko makomar yayan ka yau fa in mune gobe bamu bane. Wani lokacin koda kana raye sai kaga anayi ba tare da kai haka abubuwan suke zuwa ai kinga gara mutum ya gyara tun duniya bata kisa ba. Mai aikin data kirane ta shigo dakin dauke da katon ture da manyan kuloli abinci saman shi dining ta nufa da zuman jerawa yadda ta saba. Sai hjy iyami take fadin ki kawo muna nan yau a kasa zamu zauna muci dan dariya suka kwasa tare da fadin za a tuna da baya ke nan dai. Lokacin da yaya yake aiki lagos muna gida tare dake ake zuba abinci a cikin katon ture mu taru munaci ana hiran arziki. Ai wanan abin duk shigowan sadiya ya kawar muna dashi tana fadin wai muna taruwa ana gulmanta bazan manta da zuwan wanan yar uwan hjyn mu datazo daga kauye take fadin kema ai saiki fito ayi gulman dake. Budan bakin sadiya sai cewa tayi ni ba zan shiga cikin su rainani ba ko ita wanan don diyan tallakawane ita bata san kanta ba. Dan murmushi hjy iyami ta sake don tuna wanan labarin da safiya ke fadi yanzu sa,ade tace yau ina arzikin nata dana gidan su datake tun kaho dashi din. Duniya ke nan alokacin tana dauka tafi kowa da komai bata san me gobe zai iya haifa ba a gare ta. Hjy ce ke fadin bissimilah ku muci abinci ko juyowa sukayi a lokaci guda suna kallo abincin da mai aiki ta hada masu gwanin ban sha,awa kai kace wani dinner aka hada hakan . Haka kamshin shi abin sone ga mutum balle ya kai ga baki yaji dandanon shi. Daidai hjy na zama a kasan take fadin ance yanzu koyarwa kikeyi safiya ke kuma sa,ade nursece asibiti ? Ashe kina da labarin mu ke nan har yanzu tana daukan cokali take fadin haba aiba zan taba mantawa da kuba a rayuwana . Adaidai lokacin data fara bude kulan tana mika masu plate a gaban su da spoon da fork ga kofuna da lemoka don sha aka tabardar masu. Nan kowa ya shiga dirkawa cikin sa abinci suna danci suna taba hira yayin da sanyin AC ya fara ratsa jikin su. Sai da anty safiya ta hadiye naman da take tauna a bakin ta na kaza take fadin a gaskiya mun gode daz bamu lokacin ki da nuna rashin kyama ko babbanci a garemu yadda ake nuna muna har yanzu a gidan mu. An mayar damu bare a cikin dangi duk kokarin da baba yayi yaga ya hada kan zurian shi kafin ya bar duniyan nan . Zan iya cewa daga ke sai mijin kine baku nuna muna wani bambanci a tsakanin sabanin sauran dake yawan nuna mu barene a cikin su ko yaushe wani abu idan ya taso na family din mu. Din kawai mu uwarmu kadai ta haifa a cikin su lokacin da yaya ke raye yana iya kokarin shi damu amma tun bayan rasuwan yaya din abubuwa suka kara lalace muna ga baki daya. Wani abin saidai mu tsunci labarin faruwan shi a gare bamuci arzikin da za,a fada muna ba mu. A hsnkali ta lumshe idanuwan ta tana maijin zafin yadda ake yawan nuna masu a cikin yan uwan su din. Tace ku dauka har yanzu ma yayan ku yana a raye ne safiya don ya barni ya bar zurian shi komai ke damun ku kofa a bude yake dakuzo da bukatan ku nan mudin dai abin baifi karfina ba agidan nan. Sallama yan matan hjy ne da suka dawo daga school saida su ukune kawai don farida yar wurin hjy ba a kaduna take karatun taba tun dawowan su suka sama bata gurbin karatu Abuja can take zaune tana karatun ta. Sai hutu take dawowa gidan haka yasa idan ba hutu akeyi ba zaka gansu su uku ne kawai a gidan. Kansu a sama suka gaidasu kamar basu sheda ko suwaye su din ba garesu don kawai raina masu arziki da sukeyi. Safiyace take fadin wai ba Rufaida bace da salma nan dan juyowa salma tana fadin nice daga haka tasa kai tana kokarin shigewa daki. Rufaida salma kuzo nan hjy ta fada a kausashe saiga su sun dawo da sauri suna fadin gamu mommy ta nuna su safiya da hannu tana fadin baku san wa yan nan bane halan ? Mun sansu mama gwaggo safiyace da gwaggo sa,a salma ta fada a dan yatsune kafin hjy tace duk da kun san su saidai kamar baku san yaya suke da mahaifan ku bako ? Nan kan shiru sukayi suna kokarin dukar da kawunan su kasa don sun fahinci mai hjy take nufi da fadan hakan. Karna kara ganin kunyiwa wani babba wanan gaisuwan koda basu din bane wai salma sai yaushe zaku gyara halin kune don Allah ta fada a dan hasale . We sorry mommy gajiyace dama ya hana mu tsaya dan Allah ku ban guri marasa ta ido kawai ta fada a dan hasale. Bayan shigewar su dakunan sune anty safiya ta sauke ajiyan zuciya tana fadin kindai gani yanzu ke nan ai. Wanan ba akidar kwarai bane ka nunawa yaro ga yadda kake da dan uwanka har abin yazo ya shafi naku yayan nan gaba. Mikewa sa,ade tayi tana fadin antyce ma dai ta damu da wa yan nan mutane, nina dade da zubar da duk wani wanda ya nuna baison wata alaka zumunci dani ai. Zancen ta baiwa hjy dadi ba ta fahinci akwai bacin rai a cikin halaiyan da yan uwa ke nuna masu kasancewar su su biyun yan uba ga yan uwan haihuwan nasu. Sallama sukaiwa hjy tare da mata godiya da nuna jin dadin su irin taron data nuna masu din bata nuna masu halin da yan uwa suke nuna masu a cikin su. Ita kanta bata samu mahaifiyar su a gidan raye ba saidai ga yadda take jin labari zamane akayi bana dadi ba a cikin gidan lokacin da mahaifan su suke a raye wanda itama ta dan ga wani abu a rayuwan datayi dasu gidan kafin Allah ya azurta mata mijin ta harsu bar gidan zuwa lagos karshe ma suka bar kasan ga baki daya. Lokacin ita kanta sarakuwanta tana yawan nuna mata tayi hankali da yaran don su din ba jinin taz bane diyane kawai na maigidan ta da aka haifa mai auren baya daya kara na karamar yarinya daya auro. Ga yadda take ji sarakuwar ta itace mata ta farko a guri mijin su saida sukai kusan shekara hamsim a tare ya auro mahaifiyar su safiya din. A cewar hjy ita ba a hadawa diyan ta yan uba don haka ta hana mijin nata kara wani aure daga baya . Surukin nasu yana sana,a a kauye har ya shigo birni ya fara sayar da kayan mata irin su dan kune da sarka da jakkuna. Daga baya kuma daya bun kasa ne ya fara sayar da gwala gwale wanan ne ya kawo mai tarin arziki mai yawa har ya tamfasawa iyalan shi katon gida da suke zaune a ciki. Bawai bokaye kawai ko asiri taga sarakuwar nata nbi ba saidai iri matan nan ne masu ji da izza da isa da gadara wanda take ganin yanzu diyan nata da jikoki suna koyi da wanan halin. Saidai daga bayane kariyan arziki ya afkawa mijin nasu bayan siyasan shehu shagari da mazajen arewa da dama suka samu wanan koma bayan a sanadiyar canji da gwaunatin soja mai a lokacin ta kawowa mutane yayi sanidiyar karewa wasu bayin Allah da dama a cikin su har da surukin nata ya samu wanan iftila,in tare dashi. ANCAU KADUNA STATE Kamar yadda Asabe ta sha alwashi akan Abban mu dole sai ya kara aure hakan ne ya faru don Asabe taje nema mashi auren yar wata mata da ta dade tana zawarci batai aure ba a kauyen mu. Tun innan mu bata san wanan zancen ba har yakai ta sani saboda bakin Asabe dake sake suratai barkatai na rashin ilimi da jahilci tare da kiyayya ga inna damu diyan ta. Da yake Allah yayi inna mu mace ce mai hakkuri da kawar da ido ga komai koda tasan kaine ke cuta mata din. Sai ma bata nuna tasan Asabe nayi ba a gidan don bata nuna damuwata ga abinda Asabe ke yawan fadi ba ko yaushe. Mu kan mu bamu tsira ba gurin Asabe don tana nuna muna tsana karara kamar ba jinta muke ba mudin . Daga zagi sai dungura dan abu kadan yanzu zata sauke muna bala,i a kanu komai mukayi bamuyi daidai ba. Ainihi Asabece mahaifiyar data haifi mahaifin mu ta hayayyafa da dama basa tsayawa da sun dan tasa an yayesu sai zazabi ya kama su su mutu. Sai ya kasance ga mahaifin mu ta samu ya fara tsayawa sai mace da muke kira da gwaggon birni don a birni take yanzu da mijin ta daya samu wani ubangida a can ya daukesu bayan aure ya mayar dasu a birnin. Sai ya kasance mahaifin mu yanzu kawai a gaban ta sai yan jikoki da take dashi ta tsatson shi wanda kiyayyan fitowan mu diya mata a duniya yasa bata kaunar mu har cikin ranta. Ni dana dan kawo wayau a cikin mu nasan halin da muke gidan na zaman Asabe da innar mu don su sauran yan uwana gorin inna bai taba tayar masu da hankali ba sai ma kawai ja baya da sukayi da al,amarin ta. Don yawan fada da zagi da take muna a gidan duk da Abba ya dan kewayewa Asabe gefen ta ma,ana ya dan raba tsakanin mu da ita sai dai hakan bai hana Asabe fitowa zaman sa ido ga inna damu. Wajen karfe dayan rana kasancewar yau asabar muna gida bamu zuwa boko mun dawo islamiya tun sha daya muna gida. Ina daki ln mu na yara don shigata ke nan na gama wanke tufafin mu da suka dan taru nayi wanka ina shafa mai. Naji muryan innar mu tana kwala min kira da yar mairo na amsa da Na,am inna daga dakin tare da saka hijjab a jikina na fito da sauri. Ina fadin gani inna tace yi maza ki dauku abincin nan ki kaiwa umma kada yayi sanyi nace tau inna tare da dukawa na dauki kwanon samiran abincin Asabe. Munace mata Asabe ne don dukka gari haka ake kiranta dashi in ka debe Abban mu da innar mu koshi Abba sai zuwan inna ne gidan ya canza mata suna dama da Asaben yake kiranta. Na isa kofan Asabe ina ta sallama bata karba min ba haka yass na kunna kai dakin na aje mata abincin a gefen kofan ta kadan ko waige banyi ba na fito daga dakin. Dawowa nayi na karasa shirina kafin mu zauna cin abinci tare da yan uwana don a tare mu hudu ake hada muna abinci don yana kawo dankon zumuci inji manya sukace. Muna gab da gamawa sai ga Asabe tun kan ta karaso wurin mu take kwalawa inna kira cikin tashin hankali. Gaba dayan mu hankalin mu ya koma gare ta muna duban hanyar kofanta tana zuwa take tambaya wa yakai min abinci a dakina ? Cikin sanyi murya irin na innar mu da kusan kowan mu ya gado hakan take tambayan Asabe wani abin ne inna ? A hasale asabe ke fadin tambaya nakeyi wa kika aika yakai min abincin don yanzu na aje dankali na fito bangani ba . Haka yasa nasan duk wanda yakai min abinci shine ya daukan min shi dama an dade ana min sata a daki ina hakkuri banda dama in aje yan kwabbaina sai in nema in rasa. Da sauri na furta Allah ya tsareni da daukan abin wani nina kai abinci kuma ko kallon dakin ki banyi ba na fito. Ke rufa min baki kwadayayya satan naku har yakai haka ban sani ba dole in kira mai gyara ya saka min kuba a kofana don watarana kada kuyi min wanda yafi wanan. Wani irin bakin cikine ya rufe ni a lokaci daya ina jin idona kamar zai rufemin a wurin don satan dankalin da Asabe ta laka min. Da ba don nasan itace ta haifi mahaifin mu da naja mata Allah ya isa a gurin duk da hakkurin inna saida tayi magana wanan karon. Haba umma a gabana yarinyar nan ta shiga takai maki abinci ta fito kuma ban ganta da komai ba a hannun ta. Ai dada goyon bayan ta zakiyi ta fara mugun abu tun a gida idan yayi karfi sai ta zauna maki a gida ai don babu mai kwasan barauniya yakai gidan shi. Abbane yayi sallama ya shigo ganin mu cirko cirko a tsaye bai hannashi fadin yanzu dankaline har yai yawa haka a gidan aka barwa Akuyan umma tana ci haka? Gaba dayan mu kallon Asabe mukayi don jin abinda baba ya fada nan kuma ta fara kame kame tana fadin . Hannu na dora akai na fasa wani uban ihu ina fadin Asabe mai nayi maki kika dafa min sata a gaban kowa. Ashe akuyan kice ta daukar maki dankalin ki kazo kina fadin nice na satar maki harda kudi nake shiga dakin ki in sata. Abba ya daka min tsawa tare da fadin ke ke meye haka kike fada da sauri kanwata Fatima dake bi mun take fadin Abba yanzu fa Asabe ta gama fadin wai Abuce ta sace mata dankalin ta a daki daga kawai takai mata abincin ta da innarmu taba takai mata. A wani irin yanayi na bacin rai da mamaki lokaci guda Abba ya juyo yana fadin sata kuma umma ? Ina yaran ne jinin kine umma koda itace ta daukar maki ai ba zaki kira hakan da sunan sata ba. Ta daka mashi tsawa tana fadin yi min shiru wanda baisan abinda yakeyi ba. Yau aka fara sata min abu a gidan nan bana magana don gudun irin haka in magana ku karyatani a gaban diyan ka da matan ka. Waya sani ko itace ma ta dauko din ganin za,a ganeta ta jefawa Akuyan nawa. Allah ya sauwaka Abba yace ya nufi hanyar dakin su bai shiga ba ya duka ya dauki buta zuwa ban daki. Asabe ma ta juya zuwa sashenta tana fada inda take shiga ba nan take fita ba wai Abba da innar mun suna lalatamu da gurbatacen tarbiyan da suke bamu. Inna kan daki ta shige tana kuka hankan yasa dole na tsayar da nawa hawayen don komai ya wuce a ran inna. Tun faruwan wanan abin na ja baya da lamarin Asabe ba ruwa na da tsabganta iya kana da ita gaisuwa ban yarda in shiga ko lungunta. Muna kallo idan jikokin ta na birni sukazo yadda take ji dasu take nuna kamar su kadaine ta haifi uwarsu sam mu bamu isa mu rabe ta ba. Shi yasa ake fadin kakanni sun fison jika na wurin diya mace don ni na tabbatar da wanan maganan gun kakantamu. Sannu sannu har lokacin Auren data nema wa Abban mu ya karaso buki ya tashi sosai Asabe ita tayi uwa tai makarbiya don Abba yace shi baida zarahin kara aure a yanzu. Ta saka aka tayar damu daga dakin da muke kwana munaji muna gani aka gyarashi tsab wace kullun take kukan bata da kudi sai gata ta fitar da kudi don kawai taga ta kuntatawa innar mu rai . Sai fadi take Allah dai ya kawo amaryan Abba tazo ta haifa masu magaji a gidan ko suma zasu shiga fagen zurian dake tun kaho da diya maza a gari. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL DON SAMUN SHI ZAKIYI TEXT A WANAN LAMBAN DON LAYIN BAYA KASAN A YANZU KO KI TURO KATI WAYA KO KI TURA BANK DA WANAN LAYIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK NAGODE DA KULAWAN KU GAREMU, , , , Ta dade zaune tana son mikewa zuwa daki don ta dauko takardan da take son turawa saidai jikin daya fara manyanta tana jin kiuya da nauyin tashi daga falon ta zuwa daki a lokacin. Wani wawan tsuki taja a ranta take raya ya kamata dai ta samu wanda zai dinga taimaka mata wanan dawainiyar yayi yawa a yanzu gareta. Wayan ta dake gefen tane ya dauki kira ta dauko tana kara jan tsuki sai dai ganin bakon lamba dake kiranta ne kuma ga layin special nomba ne ya bata mamaki. Taso share kiran don bata san mai layin wayan dake kiran nata ba a lokacin wayan yana gap da tsukewane ta samu ta daga. Muryan namijine yake mata sallama ta amsa da mamaki don har lokacin bata gane mai kiran nata ba dai. Bayan sun gama gaisawa ne mai magana ke fadin hjy nasan ba zaki sheda mai kiranki ba a yanzu don an dade bamu hadu ba tun muna US rabon damu gaisa. Sai mamaki hjy keyi a ranta tana fadin waye wanan kuma wanda ban gane ba dan tunane tayi kafin tace isma,il soba ko ? Dan dariya ya sake tare da fadin abin mamaki gaskiya kinyi kokarin sheda muryana is about 20 years yanzu da bamu hadu ba. Ai ba zan manta da muryan ka ba a duk inda naji shi ta fada tana daure fuska kamar wanda take wayan yana kusa a lokacin. Yace hjy sai naji kina kasan har kusan shekara daya da rabi abin ya ban mamaki matuka har ki shigo kasan nan muna jaha daya ban san da hakan ba. Yanzu ka sani ai wakila don bai zama dole irin ku su sanda dawowan nawa bane nan ta bashi amsa. Watau halin na nan a yadda nasan shi hjy baki barin ko ta kwana har yanzu ashe ? Jin tayi shiru ba amsa yace hjy dama naso muyi wani magana dake ne wanda ya shafi rayuwan ki sai dai naga kamar baki maraba da wayana a yanzu. Kai isma,il kafi kowa sanin halina don haka babu abinda ya shafi rayuwan ka dani a yanzu dama nasan don ka bata min rai ka nemi layina don haka ina maka warning da kada ka sake kirana. Dan murmushi taji ya sauke dama yasan za a rina idan hjy iyami ce don bata daukan maganin raini ko kadan. Shidin yasanta ta dalilin yin karatu a tare ne duk da ya girme mata sosai ga haihuwa amma haka suke shan fama da ita don akwaita da kwazo da basira a lokacin da sukai karatun tana goyon danta na uku ne . Kawar da zancen yayi ta hanyar tambayan ta yaran don sunayen su bai bace mai ba har wanan lokacin. Wanan tambayan yaran daya jefo mata yasa ta dan sasauta mashi tare da amsa mai da suna lafiya . Ance in kana son kama uwa rike yaranta yanzu zaka zama masoyi a gurin ta hakan ko ya faru da hjy har ta manta da fadan ta dashi take fada mai rayuwan yaran ta a yanzu. Karshe dai yace sai sun zo don bashi kadai ne zaizo ba akwai magana mai muhinmanci da zasu so suzo yi da ita. Nan ma saida hjy tayi korafi akai kafin ta kashe wayan tana kara jadda mai cewa idan yasan shirmene zai kawo shi kadama su zo din . Shi dai dariya yayi yana fadin sai idan sunzo din zataji sukai sallama ya kashe wayan. Kai hjy ta girgiza tana fadin mutane akwai tsegumi har suna daukan zancen abinda bai shafesu ba suna dangantawa da lamarin su. Mikewa tayi don dauko takardan datake so daki har lokacin tana maijin zafi a ranta na ba gaira ba dalili wata kila kuma har yanzu haushin wayan da abokin karatun ta yayi matane oho ? Kiuyan fitowa dakin tayi zuwa falon ta har akai kiran sallah ta samu ta mike don zuwa sallah. Yanzu idan akwai abinda hjy ta tsana shine rashin son motsa jikin ta don hutu yariga da ya gama ratsa ko ina nata ga yaran da take zaune dasu baka more ne gaba dayan su son jikin su yama so yafi na hjyn yanzu don gatan da ake nuna masu. Sai dai duk da hakan tana dan kokartawa tana sakasu wani abin can ba,a rasa ba sai dai zata sha mita da jini duk tana hakkuri da wanan. Wani lokaci kuma zata zage tayi masu fada sosai akan rashin son motsa jikin da basa yi dan abu kadan zasuce sun gaji. KAUYEN ANCAU An kawo amaryan Abba wata bakace gajera bata da tsayi saidai akwai mazauna irin na mata gareta. Ni dai banga abinda nagani gareta ba sai halin kiyayya kawai da Asabe ta dagwarawa mahaifiyar mu in bashi ba babu ta inda ta kama kafan innan mu. Zaman su ba yabo ba fallasa don inna bata shiga tsabganta ko yaushe tana kofanta ita kuma amarya tana lungun Asabe. Idan muna gida mune abokan hiran innar mu sai kuwa ranan da akace itace da girki ranan zan fara labe labe don ban yarda da tsarin Asabe ba . Na cewa mu dinga kwana dakin ta haka yasa na share dan karamin dakin da ake tara tarkace a gidan mu dakin ba wani girma ke gareshi ba asalima madafane Abba yayiwa innan mu don da dama tana wahalan girki a ruwan sama. Abba yayi fada har ya gaji don ko naje lungun Asabe da sunan kwana bana shiga dakin ta saidai in tsaya daga waje. Idan na faki idon Abba ya shige zan dawo wanan dan dakin in kwanta dama mu uku ne masu dan wayau da muke zuwa kwana dakin Asaben. Zakaji tunda asuba Asabe na fada wai an jawo mata kwanan wahala a daki yara sunzo sun hanata shakat daki suna damun ta da tusan dare ko tace wai an mata fitsari a daki. Ranan da tace fitsari kanwata dake bi mun tace itama daga ranan a inda nake kwana zata dinga kwana don sherin Asabe ya isheta. Sai lokacin Abba yasan ban kwana dakin dole yakawo ido yasa mun hakana muka mayar da dan dakin wurin zaman mu koda da rana ne a nan zamu zauna muyi tsabgogin mu. Wanan baiwa Asabe ba don ganin yadda mukan saka innan mu a cikin nishadi wani lokacin har mu zauna ana hira da dariya . Sai kuma hakan ya fara basu haushi suka kulla wani sherin a kaina wanda ya girgiza mu ga baki daya yan dakin mu. Ranan monday da safe muna ta shirin makaranta tunda naga Asabe ta fito daga lungunta zuciyana ke bani akwai wani abu da zai faru a gidan don daga dakin da muke ina jin muryan ta a tsakar gida tare da Lantana Amaryan Abba suna dan zance kasa kasa. Don ranan inna muce da girki a dan dakin mu muka kwana inna tunda ta fito ta dama kokon safe da zamu karya dashi kafin mu fita ta koma daki don ta shirya kananun da basu iya shirya kansu sai an taimaka masu. Na fito da sauri kada in makara kofan innar mu na isa ina fadin inna ni zan tafi kada in makara. Na juyo inda su Asabe suke da zuman in sallame su lokacin Abba daga daki yake fadin kin karyane Abu ? Na karya na bashi amsa daga waje don ban shiga dakin ba tunda na girma innan mu ta koya muna hakan idan Abba yana ckin dakin namu. Zoki karbi murtala ki rike ko fanke kya saya a hanya Abba ya fada daga dakin. Tsiyan banza dama nasan kai ke koya masu kashin kudi don baka gudun Abin kunya kai kan wa yan nan yaya matan naka. Karatun bokon dole duk yan uwanka wa kaga ya dage kan sai diya mace tayi boko haka ? Badani za, ayi wanan abin kunyan ba kuke nan ko yaushe ku dorawa ubanku wahala don kawai baisan ciwon kanshi ba. Gani kunan haihuwan yuyuyu da aka tara mai agida ace har mace bakwai ko daya ba kawar ba a cikin ku. Daku da uwarku kunki ku barshi ya ji da abinda zai ciyar daku da wanda zai tara yai maku aure nan gaba. Amma kullun in sata in maita sai ya lalube aljihun shi ya baku dan abinda ya kwana dashi ko kuma in bakuje makarantar ba uwar ku ta lalabe shi a daki. To hakan ba zai yuyu ba don baku da uwar ku kadai na haifarwa shi ba don haka daga yau na kashe wanan bokon naki. Aure zan maki shekara goma sha hudu ai kin isa aure har kina batun wuce munzali. Gwanda ki tafi dakin mijin ki yaji da sauran yan uwan ki da suka rage kafin suma a fitar dasu sai gidan ya koma hondaku . Bansan lokacin da Abba ya fito daga dakin inna ba don tunda ta fara magana na zuba mata ido ina kallon ta cikin al,ajabi da mamakinta. Muryan Abba naji yana fadin haba dai umma aure fa yanzu ga Abu haba wani irin aure kuma kamar yadda taken nan. Hae guda nawa Abu take da za ace za,ai mata aure a yanzu akaita gidan miji ? Wani tsawa ta dakawa Abba tana fadin yi min shiru shanyaye kawai wanda baisan ciwon kanshi ba. Dame su hansai da Adawiya suka fita ga shekaru da akai masu aure kuma suna zaune kalau a dakin mazan su har yanzu. Abba yace Allah ya huci zuciyar ki umma ni gani nayi har guda nawa Abun take ne da za a ce aure yanzu. To ai gaskiya umma ta fada inji lantana amaryan Abba ta fada aure ga ya mace shine wajibi. Ba wani karatun boko ba can da yanzu shike kara lalata yara yanzu haka idan ance ma yarinyar mnan tasan komai game da aure kada kayi musu. Ke lantana ahir dinki ga bata min diya da wanan kalamin naki sai Asabe tace kaji sauna yo ai gaskiya ta fada ko karya nakeyi Asabe ta tsatsareni da idanuwan ta na tsufa. Bansan lokacin da kuka yazo min ba na juya zuwa cikin dakin da na fito don jin sherin da ake kokarin lakaka min da farar safiya haka a gidan mu. Sauran magana ban jisu ba saboda kukan da nakeyi makarantar da ban tafi ba ke nan ranan don maganan Asabe tankar umurni ne ga Abba gama kowa a gidan. A karshe dai na fito yin alwala nake jin lantana na fadin toke umma tunda kowa yasan kyauta na dan maciciji ne babu masunsuni gareta. Ai baki kyale haka a zuba mata ido ba dadai kin nemi wani a cikin kauyen nan ki hadata dashi zaifi sai aji da sauran . Don muddin tana gaban ku haka ba wanda zai kula sauran duk sai ai masu daukan daya kinsan halin garin nan sarai. Duk wanan zance da sukeyi inna tana jin su bata ko nuna tasan ana zancen ba ta kawo ido ta sakawa kowa don nuna ka waici ga wasu mata na karkara. Har kwana hudu sati na batun shigewa ban shiga school ba na gaji da zama daki mu don ko tsakar gidan mu na daina fita idan ba wani abu zanyi wajen ba. Daki innar mu na shiga na saneta tana nade kayan data wanke na yara gaida ita nayi ta juyo tana amsawa fara nade kayan nayi sai inna tabar min nadin ta juya tana fadi. Saliha tazo tambayan kitso nace ta tafi ta dawo don nasan halin ki sarai dan ajiyan zuciya na sauke ina fadin. Ni inna banwa kowa kitso a barni inji da abinda yake damuna sai naga inna tayi murmushi tana kaiwa zaune gefen gadon famekan ta. Tace ai dama haka ake son a ganki cikin kuntatawa da damuwa sai bukatan lantana da umma ya biya idan sunga kina wanan takura dama abinda ake so ke nan damu. Shiru nayi ina nazarin maganan inna da bata kara dora wani lafazi ba bayan wanan data fada hawaye ne yadan biyo fuskana na share da sauri. Don nasan ran innan mu ba zaiyi dadi ba itama don ban taba jin ta furta komai cikin zancen hanani zuwa makarantar ba sai yau da tayi mi hannun ka mai sanda. Dan hira muke jefi jefi mukaji muryan saliha ta dawo tana tambayan kitson ina jin tana kwada sallama lantana na fadin wai waye haka ke damun mu da sallama ne. Fitowa nayi daga dakin inna ina amsawa tare da fadin saliha shigo dama yanzu inna ke gaya min kin zo ai ina barci. Saliha race wallahi nazo ko zan samu ki kwashe min kai zamu birni wurin bukin dan uwan maigidan mu ne. Nace bissimilah shigo bari na dauko tabarma na juya zuwa dakin innan mu na dauko mata tabarma muka zauna zaman kitson. Na koyi kitsone akan yan kanne na don yawan yawon neman kitso da kashin kudin da inna takeyi kan kitson mu. Wanan yasa har na koyi kitso ina zama in masu har na hannu na iya ba wevean ba kawai don ina dake son kitson hannu wanan kuma a kanta na koya. Yanzu kuma in muna makaranta nakan koyi kumshi a pepper har na fara zanawa kannena sai dai ba sosai na iya ba. Wasa wasa tun daga ranan da naiwa saliha kitso mutanen unguwan namu ke shigowa wurina yin kitso ko su turo yaran su in masu. Sai ya kasance har na fara mantawa da zancen hanani karatun da umma tayi yanzu. Ga kudi baya katse muna dan abinda zamu kashe a kauye baya buwayan inna yanzu. Don a wuni akalla muna dan rike dari biyu ko dari uku tundai idan akave weekend ne don ba wani kudi bane mai yawa kudin kitson kauye talati hamsim ne wani a kyauta zan mai ya tashi. Ga Abba abin kara lalacewa yayi mai tun shigowan Lantana gidan shi abinda zamuci ma yana batun gagaran mu a gidan. Don haka muke dan dora karamin tukunya mu dafa dan cimar da zamuci iyamu damu don Asabe ta fara a gaban mu zata dan dafa abu. Saidai muji tana kwalawa Lantana kira tazo ta karba idan lantana ta karbo a gaban mu zasu zauna suci har tana santi don muji haushi. Wani lokacin yan kannen mu sai su sa ido suna son ci sai inna ta doke su ko Asabe ta dinga fada ita ba zata iya ciyar da taron yan mata ba uwar mu data haifo mu ta nema ta bamu muci. Da ku mazane ai da bamu kai haka ba a gidan nan da yanzu kuna wurin nema kuna taimakawa mahaifin ku. IIrin wanan maganganun na kakar mu yasa muka dan fara dafa tukunyar gefe don kada kannen mu su koyi daukan ido ta wanan dalili. Ranan inawa wata makwaciyar mu kitso kanwa saratu tana dafa fate don shi zamu gyara muci don Abba bai kawo komai a gidan ba tun safe. Girkim ya dauko kamshi duk ya dume gidan da kamshi saratu na bakin murhu tana faman fita wuta don iccen baya ci sosai. Sai ga lantana ta fito lungun Asabe gurin kwata inda muke wanke wanke kakarin amai ta fara da karfe da yaji. Sai duk mukayi tsaye cirko cirko muna kallon ta da mamaki don bamu dade da jin dariyan su ba da asabe kamar ba sarakuwar ta bace lantana. Sai ga Asabe da sauri ta fito tana salati tare da fadin yau may zangani haka Lantana lafiya meya same ki ? Asabe ke tambayan ta a rude sai ga inna ta ma tafito daga dakin ta tana fadin Lantana meya faru. Ganin Lantana na nuna gurin da saratu ke girki da hannun ta alama dai warin girkin namu wai ya jawo mata aman a yanzu. Ja inna tayi baya don ta fahinci makircin da Lantana ke shiryawa a kan girkin da mukeyi din don muci tun safe bamu karya ba. Wani guda mukaji Asabe ta sake wanda bamu fahinci ko na menene ba sai da tace . Ahhaye nanaye Allah nagodema yau magaji ya bayana a gidana da yardan Allah. Ta juya wurin saratu tana fadin ke kashe wutan nan ki bar girkin nan kada kija min hasara a gida don ku ba damuwan ku bane tunda bata son kamshin dahuwan naku. Saratu ta mike tsaye ta fara buga kafa tana yaya zan kashe wuta kina ganin tun safe bamu karya ba. Kada ki kawo min diban albarka nace a kashe wutan ku mutu idan bakuci ba mana waya damu daku wanan matsalan uwarku ce. Wallahi bazan kashe ba tunda bai dahu ba saratu ta bata amsa saiga inna ta laiko daga daki tana fadin saratu jaye itace don Allah banson gardama da manya. Tamayi gardaman dani Asabe ta fada tana nufar wurin randan ruwan mu ta debo ruwa a roba tana zuwa ta lemawa itacen da garwashin wuta lokaci guda wutan ya mutu. Aiko saratu ta sake wani uban ihu tana fadin wallahi ban yarda Asabe tunda ba bamu abinda zamuci zakiyi ba tana magana ta nufi wurin murhun tana hawaye. Muryan innace ke fadin karkiyi barshi hakana kuci ko bai dahu ba idan zai ciyu. Wallahi inna bandade da zubawa ba tazo ta kashe wutan matar makwabtan mu da nakewa kitsone tace dauki dahuwan ki shiga gidan mu ki karasa girkin naki don Allah ku bar wanan magana. Saratu tana sharan hawaye take fadin wallahi Asabe saina rama don ba yarda zanyi ba kun dafa naku kunci zaki hanamu dafawa yanzu. Ranan dai sai gidan makwabciyan mu saratu ta karasa dafa abincin da zamuci ga Abba bai dawo ba har dare don haka da bafon faten ba haka zamu kwana da yunwa a ciki mu. Saida safe ne nake jin muryan Abba cikin jin dadi yana fadin masha Allah abu yayi kyau Allah ya raba lafiya. Ma,ana dai watau lantana ta samu ciki a gidan mu ke nan ni banji komai a raina ba a lokacin . Don ban gama mallakan hankalin kaina ba da zan gane may hakan ke nufi damu sai can naji muryan Abba nawa saratu fada don me tayiwa Asabe rashin kunya kamar Abba zai doki saratu din. Ban san ina Asabe ta tafi ba wai ashe ta fitane zuwa gidan wata mata mai bada magani ta ansowa lantana maganin baki kada innan mu ta zubar mata da cikin jikin ta. A daidai wanan lokacin saratu ta shige lungun Asabe ta fasa mata babban randan ruwanta ba wanda yasan da shigan ta har ta fito daga sashen. ZAINAB IDRI MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL GA MAI BUKATA TARE DA IMANI DA SANIN AKWAI HISABI GOBE KIYAMA. DON ALLAH YAN UWA MUJI TSORON ALLAH GA DAUKA HAKKI A KAN MU TA WANAN HANYAN SAYAR DA LITTAFI A ONLINE MUKE SAMUN CIGABA DA RUBUTUN DA MUKE MAKU KADA KIJI HASARAN BAMU HAKKIN MU KODA KADAN NE . Sai salatin Asabe mukaji a tsakar gida tana ta faman rabka salati da fada tare da zagi ga duk wanda yai mata wanan aikin. Babu wanda ya tanka a cikin mu har innan mu saiga Lantana ta fito tana fadin meya farune umma ? Meye ma bai faru ba randar ruwana tun tele tele na samu a fashe yau sai nasan wanda yai min wanan ta,asan a gidan nan ta fada tana zare ido. Lantana tace kema umma da wani zance kike ai wa zaiyi wanan banda yaran gidan nan ko Akuyar ki ta fada mata. Badai Akuya ba su din daine zasu aikata min haka saboda bakin ciki da mugun hali yau dai ai za,a yita ta kare ko a biyani randan ruwana ko kuma yasan inda zaiyi dasu nagaji wallahi . Ta karasa tare da juyawa wurin randan ta nufa tana hada guntayen sakainan da suke wurin a warwatse a kasa. Ranan wuni jininin wanan abin tayi babu wanda ya fito yace shi ya aikata hakan sai lantanane ke taya ta fadan. Abba na dawowa da wanan zancen aka tare shi kira ya kwalawa innan mu dake daki ta fito. Cikin yaran nan wayaiwa umma wanan barnan ya tambaya yana kallon fuskan ta. Malam ina zan sani tunda ba yawo nake dasu ba balle duk cikin su babu wanda ke yawan shiga wajen umma ko tana nan balle bata gidan yau tun safe. Asabe tayi caraf tana fadin waya sani ko ita dince tayi wanan abin don kawai tsaban bakin ciki dake cinnta. Aure daine na karawa dana ga kuma abin arziki har an samu saidai bakin ciki ya kashe mutum din sai anyi ma yayan ki dan uba a gidan nan. Wanan bai taba damuna ba umma kin sani in ma za a karo mai biyune rana guda su shigo su haihu a rana daya bai taba damun rayuwana. Kana dai jin wuyan matar ka yayi kauri har tana fada min bakar magana haka a gaban ka. To kisha kurmin ki wanan din ce dai guda na aura mai kuma baki so hakan ba dake da diya matan naki da suke tayaki kishin. Allah ya baku hakkuri umma randan ruwa ne dai ban san wanda ya kashe maki shiba . Makirci daine kiyi tayi aiga diya mata nan maki zube a gida har yau babu wanda ya sallama da sunan kiran su. Shiga dakin inna yayi daidai da soma fadan Abba Asabe na fadin in fito da miji cikin samarina Abba yace kwarai kuwa da gara dai in fara rage su nima zaifi min sauki tunda har sunyi wayau yin hakan yanzu. Idan ma bata da tsayayyene akwai wanda zan hada ta dashi ai shi a shirye yake ko yanzu idan har na bashi. Abba yace a, a umma gara dai a bari ta kawo din da kanta zaifi tunda kin ga yadda yar gidan muddi suka kare kan hakan yanzu. Gashi kullun maigari maganan shi ke nan a bar yara su zaba da kansu da ai masu dole. Ai ba dole bane tunda shidin wanda zan hadasu din yana son ta ai itama zata so shi tunda bata kaishi gata ba. Koma dai menene umma don Allah kada a soma hakan banda zarahin zuwa birni sharia tunda kinga can ake kai mutun kai tsaye. Jin hakan yasa Asabe tabe baki tana juyawa zuwa wurin ta tare da fadin ni banga ranan haihuwan diya mata ba a rayuwana ko kadan. Inna dake daki kuka take darza a hankali batare da fitar da sauti ba balle wani ya jita. Alwala nayi na nufi dakin ta sanin Abba ba dakin yake ba na samu inna zaune tayi tagumi a wurin data idar da nata sallah. Inna kada zancen su Asabe ya tayar maki da hankali har ki shiga damuwa tunda bake kika ba kanki diya mata ba ai. Meye laifina a cikin wanan zance yar mairo don kawai na haife a mata yasa umma ta dauko tsangwama ta dora min ni meye nawa a ciki. Su suke raina diya mata ina saboda in kin kula Asabe ba da bukatan ilimin addini ko kadan ne matar da ko alwala bata tsaya ta koya ba . Idan kuma za a gyara mata tace ina mutum ya fito ta kashe shi ai kinga fadin hakan daga bakinta ba abin mamaki bane jahilcine ke damunta daga ita har yar koran nata. Bashi yafi damuna ba yar mairo yadda yanzu mahaifin ku yake kokarin juya min baya tun lokacin zancen cikin matanshi da umma tayi. Ina kallo zai sayo mata abu a gaba zai bata idan nayi magana yace min tana da lalura dole a lalabata ai. Inna kema idan kina son abin ai sai ki fitar da kudi ki saya idan baifi karfin ki ba kiyi hakkuri ki saka masu ido Allah ba azzalumin kowa bane ai. Sallah nayi har na idar tana zaune tana faman tunane kafin ince niko inna sai nake ganin kamar saratu ne tayi wa randan ruwan Asabe ta,asa don abinda tai muna ranan . Don dazun naga sanda ta fita zuwa lungun Asabe bata dade ba ta dawo daki tana dariyan kyata. Amma idan itace ta aikata hakan sai na bata mata rai yau inna ta fada a hasale. Da sauri na tare inna ina fadin a, a inna idan kin doke ta zasu gane kiyi mata fada kawai don Allah idan ta shigo. Kwafa innayi ba tare da kara furta komai ba ta mike tsaye ta tada sallah don isha,i da ake kira lokacin. A daidai lokacin saratu ta shigo gida tana wakan ta mai kama da habaici a fakaice . Gamu munzo taron dangi, bama tsoro kugafar bama tsoro har zuwa karshen wanka tanayi tana rawa kafin sallama ta shigo dakin inna kai tsaye. Ganin muna sallah yasa itama ta juta ta suri buta ta shiga bandaki ta dade a ciki kafin ta fito tayi alwala lokacin har sauran sun shigo dakin ko suna sallah. Nice na fara idarwa don Inna ta tsaya dogon adduan da takeyi bayan sallah. Fatima ki tashi kuci abinci kada kiyi barci bakuci abinci ba cewa da yar karaman kanwar mu data kwanta tana shirin barci. Mikewa nayi don in raba muna abincin da mukayi tunda rana tuwo ina tayi muna da miyar ganye da gyada shine mukaci da rana sai koko da take cika roba ta aje don mai yara bata yarda ta rabu da koko a dakinta a kauye. Saratu na shigowa take fadin yanzu ma tuwon ne zamu kara ci nace idan kin tanadar muna wani abin ba sai kici ba. Sallah ta tayar har ta idar daga inda take fadin Abu bani abinci na zanci in kwanta ne yau barci nake ji. Ba zaki biya karatun ki ba ke nan yau barci zakiyi tace na gaji ne yau sosai na dibar muna abincin sai da muka faraci dakin hayi tsit a lokacin. Don inna ta horemu da hakan tun muna yara har muka gama kowa yaje ya wanke hannu muka dawo tana gyara wurin kwanciya inna tace. Saratu may yakaiki wurin inna har kika fasa mata randar ruwanta yau don kawai ki jawo min sabon masifa cikin gidan nan ina fama da kaina. Juyowa tayi inda nake ta dan kalleni kafin tace wani inna wallah, , , , bata karasa ba don tsawan da inna ta daka mata da rufe min baki tun kan na mareki wurin nan. Shiru tayi har inna ta kare mata fada bata sake magana ba don fada sosai inna tayi mata tana shiru har inna din ta gama. Ina jin tayi shiru nace ni inna gaskiya gobe zanyiwa Abba maganan karatuna gashi har zamu fara exam din shiga wani zango ban tafi ba. Idan kinga zaki iya ai gaki gashi nidai babu ruwa na tunda kikaji umma tace kin daina boko to ki barwan nan zacen a hakan. Har muka kwanta ba kara magana ba sai faman tunane nake a raina don ba abindake damu kamar rashin karatu da ban fita yanzu na riga da na kwallafa rai ga boko nace ni nurse zan zama idan na girma. Washe gari baba bai fito dakin lantana da wuri ba har kowa ya gama shiri ya fita don sauran suna zuwa makaranta basu fada kangin Asabe. Hankalina yana wurin fitowan baba daga daki lantana sai wuran goma ya fito tare da ita tana mai rakiya don kawai kada yace zai biya wurin innar mu su gaisa. Har yasha dan kwanan fita daga ciki gida na fito da sauri na same shi ina fadi Abba ina kwana. Ya tsaya tare da juyowa yana fafin yar mairo kun tashi lafiya ina kannen naki sun fita ko ke nan ? Nace a sanyayaye sun tafi baba sai na fara hawaye daga inda nake tsungune ina dan gogewa da gefen hijabi na. Me ya sameki kike kuka haka da safe Abba ya tambayeni cikin kullawa kasa bashi amsa nayi sai sharan hawayen da nakeyi a lokacin. Lantana dake tsaye gefen shi kamar bodyguard din shi ta tabe baki tana fadin ya wuce dai zancen auren ta da umma ke fadi. Kai haba lantana wani zancen aure kuma yanzu gun yar mairo adaiyi hakkuri ta karasa karatun nan datasa a gaba har kwana nawa yarage ta karasa idan muna raye. To ai naga kai umma take tausayawa a cikin zancen nan kamar rage maka nauyine umma ke kokarin yi ga hakan. Ya juyo wurina yana fadin kinga yar mairo kije kiyi hakkuri har in zauna da umma in fahintar da ita ko Allah zai bamu sa,a a kanta. Lantana dake jin mu ta karyar da kanta gefe tana fadin gamu gani ai indai umma ce a gidan nan. Na bude baki da kyar ina fadin don Allah Abba ka taimaka min na karasa karatuna ko iya secondary din ne in tsaya. Taysayinane ya kama Abba lokaci guda sanin yadda gun ina kankanuwa nake son boko har irin dagewan da nakeyi kan karatun a yanzu. Yayi karfin halin fadin kada ki damu yar mairo insha Allahu zaki karasa karatun ki har ki more a rayuwan ki, duk da lantana na fadin malam kasan fa ka makara kada kwastama su dinga mitan hakan. Haka yasa Abba ya wuce badon yaso ba don tausayina da yaji a lokaci guda ya rufe mashi zuciya. Bayan fitan baba lantana ta juyo ta dubeni a lalace tana fadin iska na wahal da mai kayan kara. Lantana wurin Asabe ta nufa ta fesa mata yadda mukayi da Abba tunda naga ta nufi can zuciyana ya raya min hakan. KADUNA GARIN GWAUNA Wanka tayi ta shiya a gurguje cikin shigar manyan mata da boko ya gama ratsa su. Fuskanta babu wani kwaliyan zama a tare da ita sai dan maikon mai data shafa sai man lebe data murza don yanayin garin. Gurin takalma ta nufa ta saka wanda yai shige da kayan jikinta da sauri ta fito daga dakin duk da sauri takeyi amma idan ka ganta sai ka dauka takon isa da iza takeyi saboda wayewa. Makullin mota ta dauka don bata bukatan driver a inda zata tafi yau don gidan safiya take son kaiwa ziyara da sa,a. Tana bude falo sukayi kicibis da bakin ta dake hawo steps din da zai sada mutum da kofan shiga gidan. Tsayawa sukayi suna kallon kallo a tsakanin su kafin hjy iyami ta fara fadin kune tafe banda labarin hakan. Sai lokacin Alh isma,il yayi dan murmushi yana kawar da abin kunyan dayaso yi lokaci guda don ganin hjy dayayi a yau bayan tsawon shekarun daya dauka basu hadu ba. Shima ya wayence da fadin af na manta da gidan bakar baturiya zamu ziyarta dole saida notice. Kai ta girgiza tare da kallon wanda suke tare tana fadin sannu da zuwa kaidai shi wanan har kullun baya tsufa halin shi na kurciya yana nan a yadda yake da zolaya. Ke kuma zolayan ne bakya so ba bissimillah ku mana ku shigo kasa na tsaya mun bar bako a waje. Bako ko baki don nima bokon ne tunda ban taba zuwa gidan ba ai kinga na zama bako. Hjy iyami tace kaidai ka sani tana ja dan gefe guda tare da nuna masu hanyar shiga don bata yarda su sakata gaba ba kasancewar su maza. Falon suke bi da kallon yadda ake tsara komai zakace a kasan turai gidan yake don tun a waje suke bin ginan gidan da kallon sha,awa. Zama sukayi saman kujerun alfarman dake falon kafin aka fara gaisawa tare da tambayan iyali. Alh isma,il yana tambayan samarin hajiya daya sani take fadin kai ai yanzu sun zama magidanta in ka debe shi na biyun da har yanzu baiyi aure ba yana chaina yana aiki dasu a yanzu. Kai masha Allahu Alh yace sai kuma yayi mata gausuwan rashin mijin ta don tun lokacin basu hadu ba dashi yace koda suka zo gaisuwa mata sunyi yawa basu shigo ba. A lokacin yanayin hjy yadan canza take fadin hakane saidai bamu dade ba muka koma don yara dake karatu a can. Bayan sun dan sha abin shanda aka cika masu gaba dashi yake fadin hjy dama kamar yadda nace dake magana ce tafe damu sai fuska da fuska zamuyi maganan . Hjy tace kwarai hakan kace yanzu ku nake saurare ai dayan mutumin ne ya karbe zancen da fadin hjy nasan baki sanni ba ni. To ni sunana Aliyu zaki kubau dan majalissan dake wakiltan nahiyar uku dake makwabtaka damu. Munzo nan ne da wani bukata ko shawara na duba a gareki wansn ba wani zance bane sai sunan ki da muke son mu bayar don zaman ki macen data cancanci wani mukami da muke son a samu a tamu nahiyar a cikjn gwaunatin nan. Ni kuma Alh har yaushe na dawo kasan nan da zan iya shiga wanan harkan na siyasan kasan nan yanzu. Bayan haka kuma ni yanzu duk wani mukami na gwaunati ko wani aiki ban ra, layin shi saboda hutu nake so a yanzu a cikin iyalina. Me nake nema a yanzu wanda Allah bai ban ba sai hamdala da shukura ga ubangijina ga yara sun kawo karfi suma Allah yana duba mana duk a yanzu. Mun san da hakan hjy sanin hakan ma yasa mukaga cancantan ki ga wanan matsayin don kece zaki tsaya muna badon kudi ba sai don tausayawa jama,an mu. Kada kace haka Alhaji don shi mukami da kake gani ba haka yake ba na rike na kuma san meke cikin sa sarau. Balle mukamin irin gwaunatin kasan nan sai a hankali don mutane ba gaskiya suke so ba a yanzu niko kasan a bisa tubalin mijina nake komai shine gaskiya. Don haka tun zancen baiyi nisa ba ina rokon ku da ku janye wanan magana a duba wata da ake ganin ta cancanci hakan a bata don Allah. May na fadama Alh isma,il ya fada yana kallon abokin nasa cikin dan murmushi nasan wanan matar ba zata canza ba ai a yadda na santa tun farko. Kaji ke nan ina nan a yadda nake har yanzu hjy iyami ta fada sai dayan mutumin yace hjy zamu baki lokaci kiyi shawara yadda ya dace don bamu son wanan daman ya kubbuce muna a yanzu. Don dama ne da hujja da muke dashi akan ki na mace mai ilimi da matsayi irin wanda ake nema a wanan nahiyar tamu a yanzu. Shiya sanni yasan ko wacece ni banda ra,ayin irin wanan mukamin ko a majalissan dunkin duniya danayi aiki dasu acan da ka fadi sunana sun san dani a wurin. Hjy ki dai kara shawara a duba abin kamar yadda nake fada maki a yanzu don wani abin ansan badon kudi mutum ke rike sa ba sai don al,umman nahiyan ka. Zatayi shara yanzu dai mun fada maki bukatan mu don Allah muna son kiyi duba ga wanan abin kafin mu sake dawowa muji shawarab da kika yanke akai. Hakana dai sukai sallama ba tare da sunga alaman yarda daga gurin hjy iyami ba shi dayan mutumin daya kira kanshi da Ali zaki kubau yana cike da mamakin hjy iyami din don bai dauka akwai irin matan nan a jaharsu ba haka. Unguwar da hjy bata fita ba ke nan a ranan don bayan tafiyan bakin ta sai taji kasalan fita ya kamata lokaci guda don tunanen maganan bakin nata da sukazo mata dashi. Tsuki taja tana gyara kafan ta saman kujera data dagwara don taji dadin zama da kyau tana fadin ina zaman zamana kuja min sabon zagi da tonon asiri da tsufana. Nikan dariya nayiwa hjy ina fadin hjy ina tsufan yake a nan saidai inda babu tsofin ko za a kiraki da tsohuwa ko dadtijuwa din. Don babu mai ganin ta a yanzu yace itace mahaifiyar wa yan nan yaran nata a yanzu. Sai data dan dade zaune ta tuna da zancen unguwar da zata tafi do yau taso ta ba su safiya mamaki ta ziyarci gidajen su su sanda suma yan uwane kamar kowa. Don kawai sun fito ba ciki daya da yan uwan su ba bai kamata ana ware su haka ba a cikin dangi don tasha alwashin ida nufin marigayin mijin ta duk akan yan uwanta idan tana raye a duniyan nan . Saidai muce Allah ubangiji ya ida nufi na alheri hjy da haka mata suke duka wurin raya zumucin da zumunci a yanzu bai tabarbare ba a duniyan nan. Shigowan yaran ta dake gida suna hutu ne ya dawo da hankalinta garesu gurinta suka nufo kamar yara kanana muhsin ya zauna a gefen ta tare da rankwafo kanshi saman wuyan ta yana fadin wallahi mami na gaji sosai. Kafin dayan ya zauna a makari kujera dayan gefeb yana fadin hajjaju zaman garin nan fa ya fara isata wallahi. Gashi ko a nan zaku zauna don ba zan yarda wani cikin ku ya kara niss dani ba kamar yadda kewan dan uwanku ke wahal dani a yanzu. Wai mami idan an tashi magana sai ki kawo zancen yaya jackson shifa ina jima yanzu ya manta da Nageria a ranshi. Dan duka takai mai ga kai tana fadin daga min ya daga da sauri yana fafin wassh Allah na yana shafan wurinda ta dukeshi din. Tana fadin har daku cikin batawa dan uwanku sunan shi na musulunci da kiranshi wai wani jackson cen ba dadin ji. Allah hajjaju idan ba kince haka ba a turai babu mai gane shi ake afadi don jackson din ko jack ya rufe sunan nasa a yanzu. Bai rufe ba ta fada a hayayyake shima idan yazo zan mashi magana kan hakan idan baso yake yaje lahira ana tayar dashi da wanan sunan kafiran ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAN UWA MASOYA ANNABI ALLAH YA KARAWA ANNABI DARAJA YABA MU IMANIN A MAI ANFANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , , DON SAMUN LITTAFI BA TARE DA DAUKAN HAKKI DA NAUYI A KANKI BA SAI KI TURA DARI UKU A BANK DINA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA TA WANAN LAYIN 08036959257 KO 09036 Tun bayan fitan Abban mu ban koma daki ba wankin dana tara na farayi muna kafin yan kitso su fara shigo min su hanani aikin komai. Ina shanya kayan ne nake jiyo zagin da Asabe ke durawa wanda ba sosai nake jiyo su ba daga inda nake har na samu na gama ruwa na diba naje nayi wanka. Ban kai ga karasawa aikai sallama ko ban leka ba nasan masi kitsonane suka fara shigowa lokacin . Makwabciyar mu hassana ce da yaranta yan mata biyu da zan wa kitso suka shigo fitowa nayi na dauko tabarman da innan mu ta bani don yan kitso din na shifinda tare da gaida ita. Dakin inna na shiga tana zaune tana gyaran sarkan kanwarmu daya katse nake fadin inna ko zan dora abinci ne kafin in zauna. Jekiyi tsabgan gaban ki gunda ga mata sun fara shigowa barni in gama in dafa muna fate da guntun tsakin daya saura muna shekaran jiya. Ko zai kaimu har dare tunda ba abinda zamu dafa da daren inna Allah zai bamu da yardan ubangiji tunda ga yan kitso nan sun fara shigo min yanzu sai a sayo ko taliyan hausa a dafa da daren. To kije ku zauna kada matar mutane ta dade a zaune inna ta fada na juya na fita raina babu dadi a lokacin don a yanzu kan ina iya fahintar halin da mahaifiyar namu ke ciki na mijinta da sauran mutanen gidan mu din. Daga kofan innan mu kadan nake zama muyi kitso don Asabe tace bata yarda ana sake masu gashin mata barkatai a gida ba kada azo a barbada masu tsiya a gida. Ina kitson ina tunanen halin da innar namu take ciki na bakin cikin rayuwa duk saboda kasancewan mu mata a gareta don kila badon mun fito a yaya mata ba da bata fuskanci duk wanan nakin cikin haka ba. Muryan lantanane ya dawo dani ga dogon tunanen dana lula ina rike da kan yar karamar yarinyar dana farawa kitson lokacin. Wai har an zauna wanan bakar sana,an da babu karuwa a kullun a cika muna gida da yan gulma da sunan kitso nikan malam ya dawo ya tare min wurina don wanan abin ya isheni hakana. Kai ke nan duk abinda kakeyi idon mace na kanka a zubama ido a fita dakai waje ana baradawa a cikin gari. Dagani har matan da nakewa kitso ba wanda ya tanka a cikin mu don idan da sabo sun saba da wanan halin na habaici idan sun zo kitson don kiri kiri ake nuna min hassada ga yin kitson kuma. Maimakon ta shiga dakin datayi niyar shiga da farko sai kuma ta juya ta koma lungun Asabe ta dade kafin ta fito. Lokacin har na gamawa yaran duka biyu na farayiwa uwar saura kadan mu karasa kitson namu tana yan wake waken ta na hausa mai kama da habaici. Naji matar da nakewa kitson tace uhumm wanan matar baban naki da jan magana take naga dai kullun nazo kitso gidan nan sai ta samu abindata fada a kanmu. Ina jin dadin yadda baki kulata kike aikin gaban ki ba tare dakin damu da ita ba don irin su saboda bakin ciki suke haka don tayi sanadin da zata saka a hanaki kitson ga baki daya tunda sun san kina samu a nan. Ba komai ai wata ran sai labari na fada mun gama ta dauko dari biyar sabuwa ta mika min na girgiza kai tare da fadin a, a wallahi ki ban dari ko dari da hamsin . Haba Abu kullun na turo yara a kyauta kike min kitson nan ki karba baban sune ya bamu mu kawo maki da nake fada mai alherin da kikewa yaran shi kullun. Dole na karbi kudin badon naso ba damun wanan kudin ya zama kamar buduwar hanyar alherina ranan don duk wa yanda sukazo kitso mun samu alheri sosai a wurin su. Bansan yaya Asabe sukayi da mahaifin mu ba ya dai bani hakkuri kan in hakkura da karatun nan kawai a yanxu. Ranan nayi kuka sosai kamar ba gobe tun innan mu na ban hakkuri har ta gaji ta kyaleni ta saka min ido. Saratu ne abinka da dan uwa data dawo innan muke fada mata wuni nayi ina kuka a daki yau don Abba yace ba zancen komawa makaranta a wurina. Tashi tayi ta sameni a dakin tana ban hakkuri tare da ban shawaran da muke ganin zai fitar dani daga kuncin da Asabe ds lantana ke shirin jefani s ciki. Fitowa nayi don taya innan aiki gitkin dare haka ma su sararu da sauran yan uwan mu suna debo ruwa daga rijiyan uguwar mu suna cika duk kayan dake gidan na ruwa. Har sun kusa cika na kofan lantana don sheri kawai lantana tace wai habiba ta saka hannu a ruwan don haka bata so sai dai su zubar su debo mata wani. Wanan ya kawo rikici a gidan mu sosai ranan don har inna takai ga tanka masu Abba kuma ya dawo ya hau innan mu da fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba. Wai inna ke goya muna baya muna iya shegen da mukaga dama a gidan ai lantana ma kamar uwa take a gurin su tunda tana auren shi. Saratu dai taki komawa diban ruwa kuma ta hana yan uwa zuwa su debo suka kada guga a riya karshe dai ruwan da ba,a deboba ke nan har Abba ya dawo hake wanan fadan . Kwala min kira yayi wai na kwashe ruwan randan innan mu guda in zubawa lantana a nata randan in yaso mu mu zauna ba ruwan tunda saratu ta zama abinda ta zama a yanzu duk gaba daya zai hadamu yai muna aure lokaci guda tunda ba finta nayi da wani girma ba. Inna kan bata da aiki sai kuka don hakane kowa ke kokarin takata yadda yaso a gidan don rashin maganan da bata yi idan suna mata abinda sukaga dama, mu a namu ganin ke nan. Hjy iyami abin duniya y isheta ga matsin da gwaunati da yan siyasa ke mata dole ta zauna da yaranta da yan uwanta kan maganan. Inda suka bata shawaran karban mukamin don taimakawa rayuwan tallakawa da sauran al,umman nahiyar su din. Haka yasa ta shedawa Alh Aliyu zaki kubau amincewan ta wanda ba karamin farin ciki yayi da jin hakan ba daga bakinta ,. Duk da yana hangen da wuya su iya tafiya a yadda suke so da ita don ra,ayin daya hango a tare da matar duk da ba laifi ko yaya ne ai wayau maza yafi na mata ya fada. Tawaga guda sukayo zuwa gidan sun dade suna tataunawa da ita kafin suyi mata godiya su tafi. Hakan yasa taji duk ta gaji ga ranan don yan aikin ta kawai bazasu iya mata abinda take so ba daidai a hakane safiya suka zo gidan suka same ta cikin gajiya. Bayan sun gaisane tare da mata murnan abin arzikin dake shirin faruwa da ita take fadin anya safiya zan iya wanan abin yanzu. Yau kawai duk nabi na gaji dan dawainiyar dana wuni inayi da jama,a agidan nan . Shiyasa nake son a samo min yarinya yar maidaidaciya da take da rikon Amana in zauna da ita don wa yan nan kinga su ba zama sukeyi ba ko ba school sai sun kirkuro fita sam basu zama a tare dani. Na rasa inda zan samu irin yarinyar da nake bukata na kusa wace zata dinga min hidima ko yaushe. Dan shiru safiya tayi kafin tace za a duba a gani indaya dace sai a samo maki yarinyar kamar yadda kika bukata. Zanje kauye in duba maki mai dama mu gani idan zata iya idan kuma ta gaza sai a mayar da ita a sake duba wata. Dakin mun hakan dana gode kuwa safiya shiyasa nake kara jin dadin ki wallahi na dade ina tunanen ta ina zan fara duba yarinyar data dace yadda nake so nan gari. Da wanan maganan suka rabu ranan inda safiyan ta koma gida da tunanen inda zata duba yarinyar data dace takawowa hjy a yanzu gashi tayi alkawarin hakan gare. Kafin gari ya waye ta yanke shawara a ranta zata duba ta gefen mahaifiyarsu ta gani idan hakan zai samu garesu. Don koma meye zata iyayiwa hjy iyami indai zata iya baifi karfinta ba don ko meye hjy ta cancin hakan garesu . Don ta nuna a duniya su yan uwan mijintane a yanzu don ko wani wuri zata tafi na alfarma suna daga cikin masu mata rakiya. Wanan abin yana ba mutane da dama haushi har suka fara fadin asiri sukai mata suka shiga zuciyan hjyn a lokaci guda. Daga hjy harsu suna jin ire iren wanan magana saidai ba abin mamaki bane hakan da mutane suke fadi don yanzu mutane basu dogara ga Allah sun manta da ba duga aka zama daya ba. ANCAU Tunda safe na samu masu kitso don haka na zauna muna kitson ga innan mu tana aikin girkin gida don yau Abba yayo cefane ana dafawa aci duka gida. Ditin mota mukaji a kofan gidan mu sai dai bamu dauki hakan wani abu ba don ba wanda zaizo gidan mu da mota ai. Haka yasa muke zaton ko makwabtan mu motar tazo yin wani abu sai can mukaji sallaman mata na shigowa gidan namu lokaci guda. Amsa masu sallama mukayi dani da matan da nakewa kitso sai inna ta dago dan ganin masu shigowa gidan lokacin. Tarbon su tayi tana fadin wa nake gani yau kamarsu hjy safiya garin namu ? Ba kama bane mune dai din kike gani don kasancewar su kamar tobasai tunda tana auren yaya a garsu. Dakinta ta kaisu don Asabe bata gidan lokacin ba laifi don dakin inna duk da yawan mu koda yaushe tsab yake don tsabtan ina yara basu hanata gyaran daki da tsakar gida har din muka koyi hakan. Don ko a kauye akwai masu hali irin na yan birni da zaka samu a talauci amma komai nasu yana tsab. Tabarma ta shimfida masu saman sumintin dakin dake sheki sai dan kamshin turaren wutan dake tashi ba wani mai kamshi ba amma duk da hakan ba laifi dai dakin don ba zakace dakin mai yara bane. Ruwa ta kawo masu a kofin silver tana fadin ga dai ruwan namu babu sanyi don har yanzu yayan naku baija wuta ba gidan nan. Ikon Allah duk wutan nan daya kewaye garin nan ba a ja maku wuta ba har yanzu inna dai bata ce komai ba kada zancen yayi nisa a hakan. Safiya ta dauka ta dan kurba kadan ta mikawa anty Sa, a kaita girgiza alaman ba zata sha ba ta aje kofin a gefen ta. Lokacin na sakewa matar kai nazo don in gaidasu da zuwa a dakin innar mu din . Saida nakai har kasa na fara gaida su da zuwa anty safiya na fadin wai kada dai ince wanan ce nan wa take da sunama don mantawa da sunana da tayi a ranta. Inna tace ki dai tuna don kinsan niba fada maki zanyi ba dai ta fada tana mikewa don barin dakin. A hankali nace Abu sunana gwaggo tace naji dayan da ake kira da anty sa, a tace min haba wani irin Abu kuma keda kanki kike batawa kanki suna haka? Zainab din ne kike kira da Abu wai kamar sunan wani abu can daban wanan ai suna tsofine nagani. Nidai na fita ina dan murmushi don jin may suke fada a gatin nan kan wa zai tsaya kirana da wani zainab can. Nakai kofa naji tana tambayana ina yan uwan ki suke nake fadin suna makaranta na fita daga dakin kai tsaye na koma inda nake kitso . Yaro inna ta nema ta tura a kira mata Asabe datace zata shiga makwabta tana jin lokacin da take fadawa Lantana hakan. Ba, a jima ba sai ga Asabe da dan saurin ta ta shigo tana fadin bakin daga birni su waye umma yayan kine su safiya inna tace. Sai lokacin na tuna dasu da suna yawan zuwa gidan muna kanana amma daga baya suka daina zuwa ban san dalilin hakan ba garesu. Suna ina Asabe ta tambaya inna ta nuna mata dakinta sai ta dan tabe baki ta nufi dakin inna din . Muryan lantana ne ya dakatar da ita shiga dakin lokacin lantana na fadin umma kin dawo ashe ? Na dawo yar nan yanzu yaro ya sameni wai nayi baki daga birni sai lantana tace au baki akayi ashe mu dake gidan ma bakin ciki ya hana a sanar damu. Dago kai nayi na kalli lantana da take maganan don nasan da innan mu take wanan maganan haka. Asabe ta shiga basu dade ba suka fito zuwa sashen ta tare da bakin sai lokacin lantana ta tafi gaida su. Don a nata nufin bazata shiga dakin innan mu ta gaida bakin da zuwa ba don innan mu bata kai mata can ba . Inna tana gama abinci ta zuba masu a kwano mai kyau ta dauka takai masu ta dawo ta debi ruwa ta sake kai masu a can. Abba ya shigo gidan yana fadin yanzu ake fadamin anga munyi baki a gidan yasa na garzayo in ga su waye suka zo. Can ya samesu a aurin Asabe suka zauna sun dan dade a tare kafin su fito suce zasu tafi sai da suka sake shiga dakin innan mu sukai mata alheri kafin su fito su tafi din. Bayan kwana biyu naji lantana na fadin duk kyau da bokon wasu ga aikatau zasu kare rayuwan su karshe ma su kare ga auren maigadin gida. Dagani har innan mu kallon juna mukayi lokaci guda don ba wanda ya fahinci may zancen ta ke nufi a lokacin. Share ta kowa yayi abu kadan yan kwanajkin nan zata ce kyau wasu ya kare ga banza tunda zasu tafiyin bauta a gidan wasu. Banga wanda ya isa ya tura min dana yawon bauta ba a gidan kamar banda kowa a duniya har dai ranan da dare muna zaune muna hira a dakin inna gaba dayan mu inna ke fadin. Nikan wanan zancen bautan da amaryan baban ke fadi na rasa gane inda maganan ta ya dosa da fadin haka ko yaushe . Wanan inna ai ita ko ba dalili kirkiro magana take ta yabawa mutane don kawai ayi fitina tunda bata son a zauna lafiya ita na fada. To dan wataga za,a tura yin bauta da take fadin haka inna karma magananta ya dameki don Allah saratu ta fada tana jan tsuki. Shiru mukayi kowa na nazari a cikin ranshi kan zancen don innan mu tafimu fahintan da akwai wani abinda zai faru da diyan ta don haka kawai bai saka lantana tayi ta gorin haka a tsakar gida. Aiko ranan da safe baba yai kiran mu nida innan mu yana lungun Asabe muka tafi don amsa kiran Abba din. A zaune muka same su a dakin kowa yai shiru saidai yanayin su ya nuna kowa na cikin bacin rai a lokacin. Wuri muka samu muka zauna nikan ina daga kofan dakin don ban shiga ba a lokacin inna tace gamu malam. Zuwan lantana yasa yayi shiru ya kasa maganan da zaiyi sai Asabe take fadin kayi magana ka tsaya kana wani kimbiya kumbiya kamar kana tsoron matar taka da yarka. Ke yahanasu bawani abu bane yake son fada maku ke da yarki sai zancen tafiyan yar ki birni da nace a turrata aikatau. Koba komai zai dan samu abinda zai rage saya mata kayan daki a nan tunda kunki bari ya aje komai gashi sun cika muna gida zagada zagada dasu. Aikatau kuma umma ina ta fada da mamaki karara a fuskan ta sai naji asabe tacd eh aikatau ko yar taki tafi karfin yin sikatau din ne. Ina ko tafi umma wanda yake nema ya samu duk wata za,a lalo mashi yaji dumus ai yafi zaman wanan kitson da takeyi kullun tana tara muna munafukai a gida lantana ta fada daga inda take. Koba zaki bari ta tafi bane Asabe ta fada a hasale tana duban inda inna take zaune. Abba yayi karfin halin fadin a barta suyi shawara da yarta umma don kinga daga sama sukaji wanan maganan yanzu. Shawaran me zasuyi wanda yafi wanda na fada yanzu a gaban ta kuma ko kuma sai abinda tace zamubi tunda itace ta ajemu bamu ba. Ai shike nan tunda kace haka dama ni kai nakejiwa nake tausaya maka tunda hakan ne kawai zatayi ma a matsayinta na ya mace ta taimakawa rayuwan ku na dan lokaci. Umma ai Allah daya bamu su yasan yadda zai iya mana dasu basai mun kaisu inda bamu san kowa ba don neman abin duniya. To mara kunya akan yar fadin ki kike kokarin musayan magana dani to kiji ki karaji zuwa birni babu fashi ga Abu. Idan ta samo kudin bakuso ku bani wani ya hana ki haifota a namiji halan birni daine kamar taje tagama yanzu haka na fada babu fashi ga zancena kuma. Inyaso idan ta tafi ta shiga duniya karewan rashin sanin kowa inds zata ke nan aikatau daine sai ta tafi. Wani kuka ne na fashe dashi lokaci guda don jin hukuncin da asabe ta yanke min yau a gidan mu. Ta hanani karatu don wani manufanta yanzu kuma zata turani birni yin aikatau do kawai a musgunawa innan mu. Daki inna ta sameni ina rusa kuka itama kukan ta shigo dashi a dakin muka taru muka rasa wanda zai ba wani hakkuri a cikin mu lokaci guda. Sai nice nayi karfin halin fadin inna kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zan tafi yin aikatau ba a birni. Yar mairo me nayiwa umma take min haka a raguwana ko yaushe take kokarin sai taga bakin cikina a rayuwan ta. Ita ya mace ba diya bace da za ai alfahari da ita cikkn zuria da wasu basu gane hakan. Ban taba bakin ciki da nadaman samun ku a diya matan da kukazo min ba don ban san kyautan da Allah yai min ba don haka bazan butulcewa Allah na ba. Amma umma kulun magana ya tashi a gidan maganan ta daya ne shine na cika masu gida da diya mata bafa san yadda zatayi da diya matan da nake haifo masu ba. Innan mu kiyi shiru ki barsu nasan munafuncine aka kula a turani yin bauta a gidan wasu. Koda Allah ya nufa zan tafi inna nayi maki alkawarin kula da kaina a duk inda na samu kaina din. Balld ba zaki tafi ba yar mairo muddin nina haifeki ba zaki tafi wanan bautan da umma ke nufin kije ba don kawai ta musgunawa rayuwan mu a gidan nan. Innan mu don Allah kada kice zakiyi wani abinda auren ki zai tamu gun Abba tunda shima ya nuna baison hakan a gaban mu amma asabe tace sai na tafi. Kiyi hakkuri ki bini da addua a duk inda zasu kaini ya zama kariya a gareni ko yaushe. Sai naji ta kara rushewa da wani kukan nima kukan na fara lokaci guds mun dauki lokaci a haka a dakin. Ranan da wanan bakin cikin gaba dayan mu muka kwana tare da tunanen ina za,a turani shine abinda ke damuna a raina . ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 6️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA LITTAFINA NA KUDINE DON DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA KI DAUKI HAKKIN HAKAN A KANKI SAI WACE TA BIYA TAKE DA ALHAKIN KARANTAWA A SAUWAKE NA FITAR DA HAKKIN KI NA FADA MAKI GASKIYA. Don Allah ki guji daukan alhaki akanki don gujewa fita ko yaushe abinda ka raina shike zama babba gareka wata rana. Ban gaskanta zancen tafiyana ba sai ranan da anty safiya ta dawo garin wanan karon ita kadai tazo ba tare da yar uwarta ba. Ina wa wata mata kitso kamar yadda na saba yiwa mata kitso a kullun aka tare ta cikin mutunci ta samu Asabe na gida a lokacin. Bata wani jima ba a dakin naji asabe ta kwalawa innan mu kira daga lungunta inna ta amsa taje sai Asaben ke fadi Abun ta shirya don anzo tafiya da itane yanzu kamar yadda na fada maku za a kaita birni aikatau. Cikin karfin hali inna tace basan da wanan zance ba tunda tun ranan na fada karatunta nake so ta karasa ai. Yahanasu ni kike fadawa hakan ko kinyatani kike son yi a bainar jama, a yanzu ki nuna min kina da iko kan yarki ko ? Tama nuna in bashi ba umma zaki bada umurni har ta tsaya tana gardama a kanshi don kawai ta nuna ta isa lantana ta fada. Eh ai naga alaman hakan kedai yar nan don kawai tana ganin an zuba mata ido dasu a gidan ko ? A,a umma anty safiya ta fada kin san fa irin wanan abin natsuwa yake so tun farko idan har baku sharwace ta bane ta hanyar daya dace gskiya ba,a kyauta wa matar yaya ba Anty safiya ke fadin hakan. Wani irin a fada mata ko yau kika zo daukan yarinyar nan nace na yarda ga abindana tsara ai in ita mai tunane ba zata tsaya jayaya dani ko ? Umma ni ba jayyaya nake dake ba gaskiya ta na fada don yatinyar ban diya mace ce kowa ko bs zaiso hakan ga nasa ba a dauki yarinya akai inda ban sani ba kamar bata ds gata. Eh lalai magana kike son daukowa kanki yahanasu umma tace tana kumfar baki ga innar mu wanda hakan yasa nayi shiru ina sauraren shiru na sauraren su daga inda nake zaune zaman kitso. Hawaye ne ya fara zubo min sannu a hankali don na fahinci akan me suke magana naga Abba ya shigo gidan da kyat na iya budan baki na fara gaidashi. Bai tsaya amsa min yadda ya saba ba ya nufi shiyan Asaben inda yake jin muryan Asabe yana tashi a can. Wai yaya ne meke faruwa kuma ya fada lokacin da yake shiga wurin Asabe din yana mai binsu da kallo gaba dayan su wurin. Wanan matar takace ke son ta raina min wayau yanzu wai bata sanda wanan zancen ba ita ba mai tafiya da yarta do ita keda abinta. Anty safiya tace a, a umma bata fadi hakana ba ta dai nuna bata san da zancen ba sai kuma ra,ayinta na son yarta taci gaba da karatun ta tace. Abba ya juya wurin inna yana fadin idan mugun wuri za a kai yarunyar nan ai ba za,a hada baki da safiya ko muba a kaita. Tunda umma tace a kaita din ke meye naki a ciki yanzu banda yiwa yarinya fatan alheri kawai. Amma dai malam kasan ba ai muna adalci ba idan akai muna haka ke nan bamu da inci daga har yaran sai yadda akayi damu ke nan. Gunma dai kaji da kunnuwan ka yanzu abinda take nufi ke nan tun dazun ita yar nan bata fahinci hakan ba da cewa anty safiya. Kinga ki kwantar da hankalin ki kada ki tayarwa yarinyar nan da nata hankalin taje can ta kasa tsayar da hankalin ta wuri daya. Inna batacewa anty safiya komai ba illa mikewa da tayi ta bar dakin muna jin Asabe na fadin in ba wanan ba wani taimakone ya mace zatayi a gidan nan dayafi wanan na dan lokaci. Dagani har matan da nakewa kitso a gurguje don inyi in gama mata ta tafi kada taji me gidan mu ke ciki batu yabi gari. Matar ke fadi wai rikicin me ake hakane nace maganar sune ta manyan gida kawai . Ina gama mata ta tafi na wanke hannu na na nufi dakin inna kuka na samu inna nayi wiwi zaune a dakin haka yasa nima na samu wuri na fara rera kukan kamar yadda innan mu takeyi. Muryan Abban mune ya leko falon yake fadin wai ina yar mairon takene ta fito su kama hanya kada a yi yamma a hanya. Kin tashi nayi sai gashi dakin ya shigo yana fadin bakiji me nace ba tashi ki shirya ku tafi Allah ya tsare hanya. Wani kuka mai karfi na sake tare da ambatan sunan Abba din ina fadin don Allah Abba kada ku kaini birni bauta. Har zai fita ya dawo ya tsaya yana fadin kinga kin saka yarinyar nan hankalin ta ya tashi ga tafiyan nan. Na rasa me kike nufi da hakan gaba daya yanzu kin canza a gidan nan kin dauko rayuwan banza kin sakawa kanki saboda bakin kishi dake cin ki. Ji Abba fa wai duk haklurin da inna keyi a yanzu Abban mu bai gani har yake fadin haka kai tsaye. Wani tsawa ya daka min tare da fadin zaki tashi a nan ko sai na makeki wurin nan maza ki tashi ku kama hanya. Ai gaskiyan umma data kawo sharan turaki birni aiki idan kin zauna nan uban me zaki tsinanawa mutane a nan in bada kullun ku saka uwarku a daki tana koya maku kilibibin baza. Mikewa nayi ba shiri na shiga daukan kayana a dakin inna ya juya ya fita ganin na fara tsuntar kayana. A cikin muryan kuka inna ke fadin yar mairo kiyi hakkuri da halin da muka riski kanmu a ciki ki tsare mutuncin ki ibadan ki da kima. Kije har kullun Allah yana tare da mai gaskiya komai wuya komai dadi ki kula da yin addua kinji sai kuma ta kasa karasa sauran zancen saboda kukan da yazo mata lokaci guda. Anty safiya ce tashigo dakin inna da kanta tana fadin na fahinci halin da kike ji yahanasu. Babu dadi ace ba,a fitar maki da hakkin ki ba su sanar dake ku sasanta kanku sai dai nayi maki alkawari insha Allahu wanan tafiyan nata zai zama alheri a gareku baki daya. Yanzu na kara fahintar rayuwan dake gudana a gidan nan naku na fahinci komai yan mintinan danayi daku a nan . Murmushin karfin hali inna tayi cikin kukan da takeyi take fadin na yarda dake safiya Allah ya iya muna ya tsare min ita aduk inda take . Ba komai kitafi da ita din tunda haka suka zabar mata insha Allahu tafiyan nan nata zai zama maku alheri tunda bada zuciya daya suka tura maki itaba. Ta bude jakka ta ciro kudi masu yawa tana fadin hjyn da zan kaitane ta bada wanan kudin aba iyayyen ta. Nayi niyar baiwa umma su sai na fahinci akwai kulli cikin harkan nan don haka ki karba kiyi maza ki boye albashin tama idan an bayar nasan yadda zan dinga maku dashi insha Allahu. Don sam ban dauka ita za a bamu ba nadai zowa umma da zancen muna son yarinya a garin nan idan da akwai yadda za a samu. Sai yau danazone naga ashe itace zamu tafi da ita ki dauka kamar tana gaban kine insha Allahu. Jin hakan da anty safiya ke fadi ya kara kwantarwa umma da hankali sosai muryan Asabe ne ke fadin . Wai ina safiyan take ne in kin soma ki bar bata bakin ki wurin lalashin ta ko ta yarda ko kada ta yarda tafiyan nan ba fashi . Muna ji muna gani haka muka kama hanya da yan kayana cikin ledan bacco don banda jakkana tafiya da zan saka kayan a ciki. Inama na taba zuwa hana rantsu daga makaranta mukazo zaria kuma ba a bari an kwana ranan muka koma gida wurin iyayyen mu. Har kofan gida wurin mota asabe ta biyo mu da lantana tana fadin atafi can a dandadi duniya aji yadda take. Kina nan zaune gida ba wanda ya taya balle a sallama muna da sunan kiranki zance. Umma wa zaiso ta a haka tana zama ko yaushe kamar kucaka gari kamar a kansu talauci ya kare a duniya. Allah yasa dai ta iya abinda taje yi din kar taje ta jawowa mutane abin kunya a can don dai sanin hakin kam. Kallon Abba nayi don jin abinda lantana ta fada sai naga Abba ya kawar da kanshi gefe daya na mayar da kallona kofan cikin gida namu ko Allah zaisa inga inna ta leko sai dai har motar ta daga banga inna din ba. KADUNA Hjy iyami zaune a dining din gidan bata da hutu a yanzu tun soma wanan zancen aikin data samu din koda yaushe tana makale da waya a kunnen ta. Yanzu ma wayan ta kare da wani lauyanta kan kammala mata duk wani takarda da take bukatan samu wanda za a tura abuja a tura zauren majalissa. Abincin dake gaban ta ta kalla tana dan jan tsuki kafin ta kai hannu ta sama warmer din abincin dake gaban ta. Budewa tayi sai ga tururin abincin dake cikin kulan yana tashi kamshi ya daki hancin ta tabe baki tadab yi don tasan ba lalai ne yayi dan danonon da take so ba. Plate ta jawo zuwa gaban ta ta fara diban abincin kadan ta tsakura don ba gwana bace wurin loda abinci a cikin taba. Lemo ta tsiya ta fara kaiwa a bakinta tana lumshe ido do sanyi da dandanon shi dake shiga cikin ta lokaci guda. Sallama akeyi a kofa ta amsa tana ba maishi umurnin ya shigo tafiya yake a cikin isa da izza har ya karaso inda take zaune. Daga tsayen da yake suka fara gaisawa dashi idon shi ya sauke kan abincin dake gaban ta kafin ya amsa mata gaisuwan nata. Bissimillah ka zauna take nuna mashi kujeran zama dake wurin yace ba zama nazo yi ba nazone in kara jin abinda kika yanke ga maganan mu. Alh Adamu ina dai yanzu kasan ba,a karskshin ku nake ba don mai rabawa ya raba tsakani da yayan ku ko. So banga wani abinda zaisa ka jefa kanka a cikin lamarin rayuwana ba kuma. Yara daine babu taulali a cikim su gaba dayan su sun kawo girma don haka ka barmu muyi rayuwan mu a cikin sallama don Allah. Jin abinda ta fada yasa ya dan sakd murmushi a fuskan shi yana jawo kujeran yakai zaune tare da fadin zaki iya fadin haka tunda baki so gaskiya. Kin sani sarai wanan abinda nake neman ki dashi ba haramttacen abu bane sunnan ma aiki zamu raya ta hakan. Wani kallo ta watso mai tare da fadin Alh Adamu na fada ma ka fita hanya da maganan banzan ne shin wai yin aure dolene ? Ya dan kara sake murmushi yana fadin amma kinsan aikin ladane ko na rasa meke damun ki kan hakan idan don ta matatace kinsan dai a yanzu kinfi karfin ta ta ko ina. Mikewa tayi a fusace tana nuna mai kofa tare da fadin fita min daga gida tunda kai bakasan abin arziki ba. Kai ko kunya bakaji kazo ka kalli idona kace wai aurena kake son yi don kawai kunga kasa ya fufewa mijjna ido. Yace shi kansh miijin maki ai da zai tasone a yanzu zaiyi alfari da abinda nake shirin aikatawa a yanzu. Eh na yarda lalai namiji baida kunya yau Adamu kaine da kanka wai kazo neman yardana akan in aureka don kasa ya gama rufe minin idon miji ko ? Har kamanta da irin tsana da kiyayyan da matarka ta saka min a gida lokacin da kuke ganin kowa a banza a idon ku shine yanzu don baka da kunya zaka dawo da wani zance a kaina. Matsalan ku ku mata ke nan dawo da abinda ya wuce baya kada ki hada wancan lokacin kurciya da yanzu garemu. Ni niyana na alheri ne gareki nasan ko yaran ki zasu farinciki da zaben dan uwan mahaifin su a matsayin mijin ki a yanzu. Ka fice min gida kafin in saka a fitar min dakai ta tsiya ya ce bazan gaji da tunkaran ki da wanan zancen ba har lokacin da zaki sauko don kanki. Yana fadab haka ya juya ya bar gidan bishi tayi da kallon takaici da kunan rai wanan yana daya daga cikin abinda ya hanata dawowa kasan tun rasuwan mijinta. Yana fita gidan wuri motar shi ya nufa kai tsaye yashiga ya dade a zaune yana karewa gidan kallo yata da motar ya tafi. Mun kawo lokacin yamma baiyi ba sosai don la, asar ya wuce a lokacin kai tsaye gidan anty safiya muka nufa. Gidane tsarare mai ban sha,awa gaskiya ba laifi gidan ya hadu ni dai a ganina ciki muka shiga yayin da muka zauna a falo. Tau zainab kinga gida yau dai don har umma bata san inda muke zaune ba duk zumuntan mu da ita yau sai gashi ke Allah ya kawo ki gidana. Mikewa tayi zuwa wurin fridge ta dauko min ruwa mai sanyi a fridge ta aje min tare da fadin sha ruwa kafin ki shiga ki watsa ruwa kiyi sallah sai ki fito muci abinci. Daukan ruwan nayi da zuman sha sai naji sanyin shi yayi min yawa a bakina ta yadda bazan iya sha ba. Mayar da kofin nayi na aje saman dan table din ta dawo tana fadin taso in nuna maki dakin da zaki zauna kafin in kai gidan da zaki aikin. Dakine da gado sai mirrow ta nufi wani kofa tana fadin nan bandakine ki shiga kiyi wanka da alwala ki fito. Tana fadin hakan ta juya ta fita daga dakin kayana na fara cire na nufi bandakin kamar wace za,a cewa na sheka na sheka da gudu. Ina shiga naja na tsaya wuri daya ina karewa wurin kallo da mamakin ban dakine haka a gyare tsab. Saida na gama karewa wurin kallo na nufi bakin famfon dake ciki badon na taba amfani dashi ba a fili amma dai nasan yadda ake kunnawa ruwa yazo. Don an koyamu a makaranta nagani wanka nayi a tsanake zuciyana fam da tunanen inna mu da yan uwana. Sai kuma tunanen Abban mu dasu Asabe irin maganganun batanci da sukeyi lokacin da zan baro gida don wai kawai ina ya mace suke min hakan. Sallah na tayar saman kafet din dakin ban tsaya neman sallaya ba don wurin tsab yake ni a ganina ina zaune a gurin bayan na idar da sallah. Sai ga anty safiya ta shigo dakin tana ganina kasa take fadin subbahanallahi zainab badai a kasa kiyi sallah ba sam na manta da na kawo maki abin sallah a dakin taso muje kici abinci ko ? Mikewa nayi na biyo ta zuwa falon na samu yaranta da sukaje islamiya sun dawo gida a lokacin. Ku gaida anty tace wa yaran da suke kallona da mamaki a fuskokin su suka fara gaidani din kamar yadda mahaifiyar nasu ta umurce su. Wuri ta nuna min na zauna tana fadin ki saki jiki ki nan kamar gidane a gare ki zainab. Nakai zaune ina murmushi abincin ta debo ta kawo min a gabana tana fadin ci abinci nasan rabon ki da abinci tun safe. Kallon abincin nayi dan shikafane da miya sai taliya da ganye da nama tsoka uku a sama. Dan tsakura nayi duk da ya zamo min bakon abincin daya dace inyi dsukin cin shi a lokacin tunda ban saba cin abinci haka ba. Sai gashi halin da zuciyana yake ciki ya hanani cin abincin sai tunanen yan uwana da innarmu nakeyi a raina. Gashi yan uwa basu gida aka wuto dani balle ko sallama in samu inyi dasu tunda bansan tsawon lokacin da zan dauka a wurin wanan bautan ba dabazo yi garin kaduna kamar yarda umma tace. Bansan mijin anty yana gidan ba saida naji yana magana da yaran shi na dago da sauri ina kallon shi. Gaidashi nayi hakan yasa ya dago yana kallona tare da amsa min gaisuwan da nayi mai yake cewa. Itace kuka zo din tare eh yar dan uwanane sukai min karamci suka ban ita kaga abin yazo min da sauki ke nan. To Allah yasa a dace sai ki ja mata kunne sosai don kin san zama a irin gidajen nan ba kowane zai iya rawayu dasu ba. Daki na mike zan koma anty ke fadin zaki shiga cikin ne kuma kifa sake jiki nan gidane na fada maki. Nace zan kwantane ina shiga naji mijin na anty na fadin wanan yar yarinyar suka turo ban san me yasa mutanen kauye suke da wanan akidar ba kan yaya mata. Yadda wanan rayuwa take a yanzu kosu masu dauko yarab dasun gane su dogara da shiga fadawa wani rikici sam duniyan nan cike yake da rudani daban daban. Sai dai daman ita wanan din da kika dauko ansan gidan su da kuma inda zaki kaita din in don haka ba gaskiya da zan baki shawara ki mayar masu da yarsu inda kika dauko ta. Nima kaina saida naje naji banji dadin ganin wanan yarince zasu ban ba don uwarta ba karamin rikici akayi da ita ba kafin ta yarda muzo nan din. Yace ke nan uwar tasan kanta da abinda take yi ga yarinya kallo daya zaikai mata kasan tana cikin wani yanayi. Zaka iya sani tunda aikin kune hakan ai don nuna fin karfi kawai aikai masu daga ita har mahaifiyar ta aka ban ita. Shine kuma kika dauko masu ya safiya baki tsoro abinda kaje ya dawo nan gaba kada faki lalata maku zumunci . Wallahi don dai hjy iyami ce kuma na riga da nayi mata alkawarin hakan kaga idan na saba mata ba zataji dadin hakan ba. Yace Allah ya sauwa ka saidai kija mata kunne sosai kafin ki kaita na fada maki zama irin gidan nan akwai kalubalin masu yawa ga wanda bai saba hakan ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 7️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA RAYUWA KE NAN YAN UWA MU FADI ALHERI KO MUYI SHIRU SHINE KOYI DA SUNNAN ANNABI SAW , , , , DON ALLAH YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON ALLAH KI GUJEWA KAYAN ALLAH YA ISA A KANKI 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 300 NE KACAL ZAKI TURA SABODA ALLAH SHINE HAKKINA GAREKU. Na dade kwance a dakin badon nayi barci ba tun ina jin karan tv da muryoyin su a falon har nazo na daina jin komai ina jin anty ta shigo tana ja min abin rufa sai naji sonta na yan uwan taka ya kara shiga raina sabanin dazun da nake jin haushinta ina ganin da hadin bakin ta wurin rabani da yan uwana da innan mu. Tambayan kaina na karayi karo na batkatai mai Asabe da lantana suke nufine a kaina. Mau ye lafin innar mu da bata ganin laifin Abba shi tunda ba inna kadai ta haifomu a mata ba. Meye laifin kasancewar yaya mata da asabe ke gani ga innan mu damu wanan halin shi a kowani gida da yaya mata sukafi biyu zuwa ukku kamar mu. Ba addinine yace a kyamaci diya mace ba wanan hain rayuwane na wasu mutane da hakan ya zama masu al,ada. A ganina duk da da aka haifa ta sunna walau mace ko namiji albarkan rayuwa ya kamata iyayye su newa yaro. Ni dai ba zan iya cewa nayi wayau naga inna da Asabe a cikin dadin raiba a gidan mu duk ko da irin biyayyan da ina ke mata sau da kafa. Ba zan manta a da can baya har talla asabe ta fara dora min idan na dawo boko zan dauki tallan goro ko gyada in fita dashi duk da ina kankanuwa a lokacin. Da kyat Abba ya samu ya hana wanan tallan ranan kan yasha fitina wurin Asabe ba Abba kawai ba har innan mu ba,a barta ba don cewa Asabe tayi inna ce ta zuga Abban mu don tana bakin ciki ina fita mata talle. Haka muke abu kamar marayu a gidan mu bawai don mun rasa uwa da uba a raye ba sai don kawai zama da fitinaniyar uwar miji da Allah ya hada inna da ita. Yanzu kuma tsanar yakai har Asabe ta turoni yin aikatau a birni ba tare da kowa ba gidan mu yasan inda za a kaini ba. A haka naci gaba da sake saken abinda zan tafi in taras gidan da Anty safiya zata kaini din. Juyawa nayi ina lumshe idanu tare da fadin Allah yasa hakan shine alherin mu gaba daya kamar yadda anty safiya ta fadawa inna da zamu zo. Har barci ya daukeni ban sani ba ga dai gadon laushi ga fanka a dakin na samu amma haka bai hanani barci a cikin damuwa ba. Karfe biyar da wani abu na falka kamar yadda inna ke tayar damu don sallah asuba idona bude nabi daki da kallo . Sai a lokacin na tuna da inda nake a yanzu da sauri na sauko saman gadon na fada bandakin dake dakin da nake ciki . Alwala nayi a gurguje na fito na tayar da sallah ina idarwa na dan zauna nayi addua kafin in mike na bude kofan a hankali na fito dakin. Duk da sauran duhun dare gari bai gama haskawa ba a lokacin amma na gane hanyan kitchen din anty safiya da jiya naga tana shiga tana fitowa da abinci. Wanke wanke na sama tare a kitchen din ban tsaya jiran komai ba na shiga wanke su a hankali don kada in tayar da mutanen gidan don har lokacin banji motsin kowa a gidan ba. Na gama na share kitchen din na fito zuwa falo na fara shara da kakabe kujeru da suka kewaye falon can naji motsi alaman wani na fitowa daga dayan dakunan su na kwana. A, a naji muryan anty safiya na fadi zainab kece a nan kuma har kin tashi ashe ban sani ba yau na gajine sosai dan tafiyan nan da mukayi jiya duk jikina ciwo yake min wallahi. Ban bata amsa ba sai kaiwa da nayi kasa ina gaida ita da kwana ta amsa min a gurguje tana shiga kitchen din ta. Sai kuma gata ta fito tana fadin ke yaushe kika tashi halan da kikayi wanan uban aikin haka zainab kin koyi barci da dare ko kin kasa barcine kina tunanen gida. Nace nayi barci dana tashi nayi sallahne na fito na wanke su tace ikon Allah toh sannu da kokari ashe tafiya zatayi kyau tunda baki da son jiki haka ? Abinci ta hadawa yaranta yayin da ni kuma na share ko ina na gidan sai gaidani da aiki takeyi tana fadin kinga idan har zakici gaba da hakan ina mai tabbatar maki zaki ji dadi sosai a wurin hjy. A raina nace watau ma wurin hjyce za a kaine kenan matar mai kudine tunda naji harda hjy anty ta kirata matar yanzu. Ni tace in shiga in shirya yaranta a wani daki nayi ta bin dakin da kallon mamaki a raina tana min bayanin abinda zan masu. Ta fita ta barni da yaran a dakin ina shirya su bayan nayi masu wanka da broshe tsab suka fito a tare muka fito daga dakin tace dani kinga koma ki gyaro min dakin nasu in karasa shirya su a nan. Dakin na koma na fara tattara kayan da suka watsar kafin in hau gadon dakin da gyara kafin wani lokaci sai ga dakin tsab dashi kamar bashi bane suka bata dazun da tarkace ko ina. Nan anty safiya ta yaba min sosai tana kara min bayanin kinga tun da safe idan kin tashi kinyi sallah. Kada ki tsaya sanyin jiki ki yi duk wani aikin da kika san naki ne a gidan tunda kina da kwazom tashi haka da safe. Don Allah zainab kada ki yarda ki bani kunya don inda zan kaiki nima gidan kunyanane can tayi bugun gaba ne dani tasa in samo mata yarinya natsatsiya mai kwazo da tsabta da amana. Idan kinga abu ba a baki ba kada ki yarda ki taba shi komai son da kikewa wanan abin a ranki. Na amsa da to anty tace zaki ga kudi kamar a banza mai yuyuwa zata gwada ki na dan lokaci taga idan kina da amanan hakan kafin ta yarda dake bandai sani ba. Zan fada mata gaskiya ke din yar uwatace ta jini don ba zan lamunci suyi maki wullakanci irin wanda akewa yan aiki ba ke kuma sai ki rike min amana sosai don Allah wanan abin taimakon kai da kai zamuyi tsakani nidake zainab. Insha Allahu anty na fada don idan ta kirani da zainab din nan yanzu sai inji kamar badani take magana ba. Wasa wasa na share sati daya gidan anty safiya banji zancen tafiya gidan da za a kaini din ba, nima kuma ban tambaya ba. Ashe hikimar ta na barina a gidan ta don dai in koyi wani abinda ta fahinci ban sani ba kada ta kaini a sha wuya a can . Gashi kullun cikin yi min bayani take da fahintar dani komai na rayuwa a birni wanda mu can kauye bama yin su. Har na dan fara sabawa da yaranta yanzu sosai ranan da dare muna zaune falo muna kallon wani shiri na yara naji anty ta ambaci sunana . Hakan yasa na juyo ina kallon ta cikin ladabi take fadin ina ganin gobe zan kaiki wajen hjy dazun muyi waya da ita take tambayana ke . Wani irin ba dadi naji a raina lokaci guda damuwa da fargaba ya dira min a zuciyana lokaci daya. Ganin canjin yanayina take fadin ki kwantar ds hankalin ki can ma nafada maki gidane a garemu ai tunda gidan babban yayan mu ne saidai shi a yanzu bai raye matarce kawai da yaran su a gidan kuma yaran ba yara kana bane sun girma kananan ma zaku zo yan sa,a daya dasu. Sai dai daga mazan har mata kada ki shiga tsabangan kowa duk abinda suka saki indai baya kaucewa idini bane wanda kuma ya shafi gaban kowa a cikjn gida kiyi. Na fahinci may anty ke nufi a nan ma, ana na kama mutuncina da kimata ga kowa a gidan dai. Haka na kwanta da tunane mai yawa sai kewan gida ya dawo min sabo sosai a raina don haka ban samu barci sosai a ranan saboda tunane. Karfe goma na safe muka bar unguwan su anty safiya wanda nake jin ana kira da barnawa muka doshi inda zasu kaini a motar mijin anty safiya din. Anty ta ban wani jakka nata na saka yan kayana wanda ta sai min kala hudu dana zo don tace nawa ba zasu tafi ko ina ba a haka. Sai bin garin nake da kallo yayin da anty suke gaba da mijinta zaune suna dan hiran su da ban san ko a kan wa suke zancen su ba. Kafin mu bar gidan anty safiya sai da sukai min nasiha sosai mjin anty safiya yace in kiyaye ibadana inyi hakkuri da duk yanayin da zangani a gidaba, ainyi biyayya ga wa yanda na sama a gidan. Shiga nan bullo nan har muka kawo unguwar mai kama da kasan waje muka fita ba jahata na kaduna ba. Uguwar kanshi abin kallo ne ba mutane sai motoci jefi jefi da suke wulgawa saman shimfudeden kwaltan da aka zuba a titin. Idan kaga wanan ginan sai kace shiyafi kyau sai kuma idan kaga wani kallo ya koma sabo. Wani katon gida daya tafi da imanina tundaga nisa mijin anty ya tsayar da motan shi yana danna horn. Kafin wani mutum daba tsoho ba ya fito yana dan lekowa naji anty na fadin bude get mune da mijina. Ya amsa yana washe baki tare da saurin komawa sai naga kofan na budewa kamar injin. Ya danna kan motar zuwa cikin gidan naji mutumin gidan yanayi masu sannu da zuwa da alama dai yasan anty din sosai . Saida mijinta ya tsayar da motar shi ne take fadin amma dai kasa yau zaka shiga ku gaisa da hjy ko ? Yace zan shiga kodon ta san yarinyar nan tana da muhinmaci sosai a garemu ai don ni dai da kinbi tanawa da ba, , , Please dear ina mun gama wanan zancen tun a gida sai kuma ta juya da harshen turanci tana magana. Ko ta dauka bokona baikai indanji abinda take fada bane oho do maganan da sukeyi da alama mijin nata yace a mayar danine kota rikeni tunda yar uwarta nake. Allah sarki nace a raina wanda ma suka haifeni suka san zafina sun kasa barina a gaban su balle anty da daga sama ta ganni haka. Don ina jin tana fada mai taso hakan amma kawo ni nan din shine mafita a gareta naji yace to shike nan Allah ya tsaya mata da hausa. Su suka fara fita daga motar kafin anty din ta zagayo ta bude min gefen da nake tana fadin in fito. Na fito sai bin gidan nake ko ina da kallon mamaki ina rayawa a raina wai yanzu mutane ne sukai wanan ginan haka da hannun su ?. Nidai ina bisu a baya ina karewa gidan kallo ta danna wani abu a bango ba, a dauki lokaci ba sai ga wata yar dattijuwa farace tafito tana fadin waye sai sukayi arba da anty dake tsaye a kofa. Hjy kece take cewa anty safiya nice kande ko hjyn tana ciki ta tambaye ta ? Tana nan yanzu ko tashiga daga cika ta fadi tana matsawa daga kofan da take tsaye. Shiga mukayi kai tsaye saida naja baya don abindana fara takawa ko ina na falon sai kyali yake da daukan ido. Zama sukayi a kujerun dake katon falon yayin da nakai kasa daga gefen anty din mijinta ya kalleni tare da fadin ki zauna saman kujera mana. Naji anty tace kasan ta ai da halin su na yan kauye barta kawai zata zo ta saba wata rana ai. Matar da naji anty ta kira da kande ne ta dawo falon dauke da tire da abin sha a ciki. Ga kan shin girki yana tashi a wani bangare na gidan duk da kamshi da falin keyi bai hana na girkin ziyaran hancina ba. Ga abin sha hjy kafin hjy ta fito, ta fada tana ajewa a gaban su bin abinda ta aje din nayi da kallo. Saida suka dan taba hira da mijin ta muna zaune ni dai sai bin hotunan dake tsaye a falon manya manya dasu kamar mutun ne tsaye a wurin nakeyi da kallo. Sai ga matar gidan ta fito da fara,a a fuskanta tana fadin ashe kuna tafe yanzun nan na shiga ciki. Tun safe yaran nan suka tayar dani da rigimar su na fito tarba na mutunci naga tana masu tana saki fuska da jiki dasu. Ta kalli mijin anty tana fadin yau baka fita aiki ba ke nan ta fada tana kallon shi. Ban fita daga nan zan wuce ya bata amsa da kara fadin yarinyar nan muka kawo dama. Ta juyo tana kallona tare da dan kuramin ido na dan lokaci tace masha Allah. Yarinya kamar kin shiga zuciyana kinga irin age din da nake so ta kasance min gashi ko kin samu ai anty safiya ta bata amsa. Menene sunan ki ta juyo tana tambayana kafin ince Abu naji anty safiya tace zainab ce sunanta. Kai zainab kice uwata ce ashe yarinya kin samu suna mai kyau kuwa tana kallona da kulawa. Aikuwa na manta sunan mama na unguwar rimi ke nan fa dacewa kanwar mahaifiyar hjyn . Mijin anty ne yake fadin ni zan tafi hjy don Allah sai a hada da hakkuri don kin san yarinyar akwai kurciya da kauyanci a tare da ita yanzu. No no no kada kuji komai wallahi muma ai kauyene asilin mu a da ko kowa ka gani daga kauye yake ai. Shigowa wasu yara kanana su biyu mace dana miji falon yasa zancena ya tsaya a nan suka juya magana kan yaran. Anty ke fadi a a ashe mutanena suna nan sai hjy tace wai yau hutu sukeyi basu je school ba sun shiga meet time break ne. Hannu anty safiya ta mika masu suki tare da make kafadun su suka nufi sirin kakan su kai tsaye. Tafiya ya fara yi tare da fadin to zainab a kulla kinji banda rashin ji anty safiya tace in tayi rashin ji ai zata gamu da nine sosai. Karfe nawa zaka dawo yace na fada maki sai yamma don haka idan kin gama ki koma gida don yara kada su dawo school bakya nan. Wai har yanzu motar bai tashi bane hjy ke tambayan anty motar ta kafin anty tace wanan motar ai sai wata yanzu gashi yaki ya saya min wata ina ta faman bin shi yana ja mi rai. Ki bar kanina ya huta safiya indon motace zan sa a duba maki idan ba zaki raina ba dai kai kai kai kice wanan zuwan takice ashe mijjn ta ya fada . Kasan ai safiya ta hannun damana ce sosai tafi danan a gurina in dai tana so. Ya tafi tare da ma hjy sallama nabishi da dan kallo kamar ince don Allah kada ya tafi ya barni. Anty ta mike tabi bayan shi bayan tafiyan tane falon ya danyi shiru tana ta danne danne a wayan ta sai ga anty safiya din ta dawo falon. Zama tayi sukaci gaba da hira a cikin hiran nasu ne take fada mata yadda muke da ita . A hiran na kara fahintar irin zumuntar dake tsakanin mu da ita din wai ashe mahaifiyar su da Asabe ce ya da kanwa. Asabece ya mahaifiyar su kanwarta tace kai kice min ita din ta gidace ashe eh ta gidace gaskiya sai dai gaskiya kin san yadda zumuncin zamanin nan yake ai. Koma dai yaya ne ai takice ita zan duba inga yadda zamu zauna sai ta kira wanan matar ta dazun data kawo ruwa tana fadin. Kande ga bakuwa ki bata daki wanan na kusa dani zaki bata don ni tazo gidan nan don kula da harkokina. Don haka zaku zauna tare sai dai kowa da aikin shi daban ke naki kula da kitchen ne da sauran ayukan da kika sa kinayi. Ita din dai ki barta dani sai zuwa gaba idan ta saba zan fara nuna mata aiyukan ta yadda ya dace. Sannu da zuwa kande tace min tana kokarin daukan jakkar kayana da anty ta shigo dashi ta aje a kuss dani. Kagin anty tace na karbs ni har na mike ina karba matar na fadin ai da ki barta bakuwace fa nace a a mama kawo in dauka. Jeki ta kaiki daki da zaki zauna kafin in shigo hjy ta fada tana dora kafanta saman dan table din dake kusa da ita. Muka nufi cikin gidan wanda bai isata da kallo matar na gaba ina binta har zuwa cikin dakin da akace ta kaini din. Dakin ta bude tana fadin bissimila shigo daga ciki nabi bayanta muka shiga. Wanan shine dakin ki sai ki zauna ki huta kafin girki ya sauka a wuta muci ni nawa dakin yana can daga waje kadan ta hanyar kitchen idan kina nemana. Daga haka ta juya ta barmin dakin ina tsaye sai bin dakin nakeyi d kallo nida ke santin gidan anty safiya sai gani a wanan dakin da fadin tsaruwan shi bata lokaci ne. Anty safiya bata bar gidan ba sai karfe dayan rana bata tafi ba saida ta shigo dakin ta kara min nasiha kan nayi biyayya ga kowa a gidan . Ta tafi ta barni cikkn kadaici da damuwa a gidan da ban san kowa a cikinsa ba ban ma san a inda nake ba dai. Wani irin kuka ne na rushe dashi ganin ta tafi ta barni daga ni sai halina sai wa yanda a yanzu zan zauna dasu din. Ganin kuka ba zai min bane yasa ni tashi na shiga bandaki dukda ba a nuna min ba dan zaman da nayi gidan anty na dan fahinci ya ginan birni yake yanzu. Alwala na dauro nazo na tayar da sallah ban daga ba na dade a wurin ina addua kafin na dan kai kwance sai ga barci ya daukeni a haka ba tade dana sani ba a wurin. Babu komai a raina sai tunanen halin da mahaifiyata take ciki a yanzu tare ds yan uwana a raina. Nasan innan mu zata kara shiga wani hali a yanzu don barina kusa da ita dan taimakon su daya ne wanan kudin da ban san ko nawa bane da anty ta bata da zamu zo. Irin wanan tunanen nakeyi sai hawaye yazo mi lokaci guda don tunanen hakin da inna zata shiga yanzu da ban kusa dasu dama da dan kudin kitson da nake muke tallafawa ake samun abinda akaci. Gashi yanzu lantana da Asabe sunyi makarkashiyan da aka raba tsakanina da mahaifiyata da yan uwa anya zan iya mantawa da wayan nan mutanen a raina kuwa , ? . ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 8️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA ALLAH KA SADA MU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN RANAN TA JUMMA,AT ALLAHUMA AMIN , , , , , , DOMIN SAYA SAI KI TURA KUDI TA WANAN ACCOUNT DON KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , , , Ni Abu ban taba tunanen zan gani a cikin irin wanan dakin ba ko a mafalki ban taba hango wanan irin gidan a malkina ba. Yau sai gani nayi barci na falka na ganin cikin wanan gidan ga sanyin AC da kande ta kunna kafin ta fita ya hade dana ties din dakin yana ratsa balgon jikina a hankali. Duk da sanyin yana damuna ban tashi a yadda nake kwance ba a kasan na dunkule a wuri daya sai faman tunane nakeyi na rayuwa. Muryan hjyn ce yasani dagawa daga inda nake kwance wanan karon ta sauya kayan dake jikin ta zuwa dogon riga mai laushi da daukan ido jikin shi wani dabbara dabbara ne kamar jikin zabra. Taci gaba da fadin ke zainab bakya gudun sanyin kasan nan ya ja maki illa kiyi ciwo fa. Da sauri na dago ina gaida ita dakin take bibda kallo ta sauke idon ta ga jakkan kayana tana fadin ga wardrobe nan ki saka kayan ki a ciki . Taci gaba da fadin ki dunga kula da kani ki kula da tsafta sai muyi zaman mu lafiya. Mu gaimaki juns tsakanin mu don kingani nan bana shiri da wanda baida tsafta sam. Iyakar sikin ki a gidan nan yanzu shine kula da sashina da komai wanda ya shafi rayuwana a cikin gidan nan. Yarana duka manya ne kuma duk zasu girme maki kinga kenan suna matsayin yayyin ki ne. Ni a yanzu yar kasuwace kuma mai rike da mukamin gwanatin kasan nan . Kinga ina da manyan hidimomi a tare dani wanda hakan yasa banda lokacin kaina shine dalilin da yasa nace a samo min yarinya da zata dinga taimakamin. Sai gashi ke Allah ya nufa a sama min na kuma yaba da irin yanayin dana ganki dashi na natsuwa . Ina fatan zaki zauna damu gaba daya gidan nan da zuciya daya cikin amana da yarda. A hankali na dago kai tare da fadin insha Allahu hjy nayi alkawarin hakan. Ban iddasa rufe bakina ba tace ba hjy nake a gurin ki ba mami nake don ni uwarkice a yanzu ki dauke ni yadda sauran yaran gidan nan suke daukana. Da fatan kin fahince ni tace ta fara tafiya don fita dakin tare da fadar ki fito kici abinci a falo yanzu idan kin gama saka kayan a ciki. Na amsa da to hjy da sauri nace mami tayi murmushi ta fita yayin da baki na yake dafe don katobaran dana farayi. A gurguje na jera kayan kamar yadda tace saidai saida nasha wahala wurin gane yadda zan bude wardrobe din. Falon na fito na dauka ita kadai ce kamar dazun sai dai naga sabanin hakan don sun kai su gama zaune wurin a ganina. Ja nayi na tsaya dan nisa kadan dasu ban karasa wurin da suke ba hjy ce ta dago tana fadin. Zainab zo ki zauna mana kici abincin tana kallon inda naja na tsaya dan nisa dasu kadan. Firgigit nayi daga sana,ata dana fara watau tunane don yanzu ya zama min abin yi ko yaushe. Sai lokacin sauran dake zaune suka farga da fitowana falon gaba dayan su juyowa sukayi suna kallona lokaci guda. Karaso mana kizo nan ga abinci nan ki diba ta kara fada sai naji sun kwashe da wani dariya. Wai mami sabuwar mai aikice kika dauko kuma take tambayan hjy tare da juyawa taji amsan da zata bayar. Haba dai mai aiki a haka kuma sai a rasa wace za a dauko aiki sai wanan yar kauyen haka irin yan kauyen nan fa wahalan sha,ani garesu kafin kansu ya waye don basu iya komai ba sai shirme da kauyanci wata yar farafara ta fada. Dayan ta yamutsa fuska tana fadin but she is dirty mami don Allah kada ta karaso nan inda muke. Ai kin san halin hajjajo da son mutane yanzu haka wani wurin ta kwasota itama ya fada yana mayar da kai ga abincin da yake ci. Yar uwan gwaggon Safiya ce kuga kenan kuma ta zama yar uwarku ai . Yanzu a nan gidan zata zauna damu ke nan ko dai tazo yin wani abune Rufaida ta tambaya a yatsune ? A haka mami zata zauna damu Nazifa ta fada tana kyabe baki tare da fadin ashe zamu sha kauyanci a gidan nan kuwa. Hjy tayi murmushi tana fadin in dai wanan da kuke ganine cikin kwana biyu zata goge ta zama yar birni tayi fes kamar kowa. Dariya suka sa gaba dayan su a lokaci guda nidai ina tsaye a inda nake ina kallon su kasa kasa ina jin cin mutuncin da suke min. Zainab kinja kinyi tsaye karaso mana ki dibi abinci kici hjy ta fada tana yafutoni da hannu. A, a mami don Allah dai karta matso nan ta bari idan mun gama sai ta zo ta diba amma ai haka raina mu zatayi ta dauka daya muke da ita. Tsawa hjy ta dakawa mai maganan tana fadin karna sake jin haka daga gareki ita din ba mutum bace kamar kowa nima a haka mahaifin ku ya daukoni ai. Shiru sukayi suna cigaba da cin abincin su yayin dana karaso inda hjy take na dan labe ina kaiwa kasa na fara gaida su. Ku duba yadda ta baku girma yanzu a cikin mutunci amma ku kuna kokarin zubar da darajan ku a idanunta, baku san cin fuska baida dadi ba. Shiru sukayi kowa na kai abinci ga bakin shi tashi ki dibi abinci hjy ta sake fada karo na barkatai. Plate wace batai magana ba ta jawo ta fara zuba min salma ke nan ta juyo tana fadin may za, a zuba maki ? Na nuna wanda ke cikin plate din dayan namijin dashima baiyi magana ba sai kallon banza da yake min. Dariya suka kwashe dashi ya dago kai yana tambayan menen suke cewa choice din ku daya da yarinyar nan abincin ka ta nunafa. Ware idanuwa yayi waje tare da fadin ke ni sa,arkice bakiga kowa ba a wurin nan saini halan. Yana fadin haka yai kwafa ya ture abincin ya tashi daga wurin sai suka kara fashe mai da dariya. Miko min abincin tayi na karba tare da dan rusunawa ina fadin nagode na juya zan bar wurin naji hjy na fadin ina kuma zaki tafi kici abincin ? Dan marairaicewa nayi ina fadin dakina hj, , mami ba zaki sake jikin ki ba har yanzu kina kewan gidane ko nidai na danyi murmushi na juya na tafi. Ina kallon abincin wai duka wanan naman da aka zuba a ciki nawane ni kadai kai yan birni kan suji dadin su. Wanan ai shine zamuci duka gidan mu da sallah idan yazo don sallah kadai muke cin nama sai ko idan rabo ya ratsa Abba ya sayo muna a ci. Gaba daya na cinye abincin tas na dauko plate din zuwa kitchen don na fahinci a nan kitchen din yake dazun da mama kande ta fito da abinci. Na canka daidai na samu baba larai tare da wata mata tana juya miyan da zasuci da dare miyan kaine saidai ban san ko kan me bane na daiga ya ciko tukunya sosai tana motsawa. Gaida su da aiki nayi kande ke fadi kin kamala ci yar nan ina jin marasa ta idon gidan nan dazun sunayi maki shakiyanci da suka iya. Ki fita batun su dan haka halin su yake da rainin wayau tsiya tundai in sun raina da kuran mutum sai suso su raina shi. Don ma hjy tana taka masu burki aida abin nasu yafi nan wallahi dayan matar ta fada. Inda wanke wanke suke na nufa na shiga hadawa da sauri kande tace yar nan me zakiyi nace wankewa zanyi mama. Rufa min asiri kada hjy tazo tagane ki tace na baki aikin da yafi karfin ki ko dazun saida ta kara jaddamin zance a kanki. Zan iya ai basu da yawa na fada ina kokarin hada kayan wa yanda sukaci abinci dasu da yamma. A gurguje na wanke kayan tas dayan matar da ake kira larai tana saka min albarka na kare tare da fadin aikwai wani aikin da zanyi kuma mama na tambaya ? Babu yar nan sai dai kizo muje dakin hjy na fara gwada maki aiyukan datace a nuna maki na bangaren ta. Hannu ta dauraye tana gaba ina binta baya muka nufi inda sashen hjy yake don gyarawa a kofa muka tsaya. Tana kwankwasawa kafin a bamu izinin shiga daga ciki hjy tana kwance kishingide saman wani kujera mai kaman gado a dakin. Ga wani abu babba kamar waya a gaban ta tana latsawa ta dago tana fadin kande baki bar yar nan ta huta ba yau yau da kawota. Ai sai taga aibun kan hakan to hjy nayi laifi wai gani nayi dai ta fara sani tun yanzu ai ba aikin zatayi ba a yanzu gani kawai zatayi ta koya. To shi ke nan hjy ta fada tana mayar da hankalin ta wurin abinda takeyi a lokacin. KAUYEN ANCAU Iska na wahal da mai kayan kara a gidan nan yarinyace dai ta tafi ba dawowa zatayi ba balle mutum ya shige daki yaki fitowa. Lantanace ke magana ita kadai a tsakar gida inna na daki tun bayan tafiyan mu har yara suka dawo boko suka tafi islamiya taki fitowa waje. Gashi sai tambayana suke inna ina yayar mu bamu ganta ba tun dazun tace dasu ta fita kawai daga haka kowa ya shiga harkan gaban shi. Sun tafi islamiya sun dawo sun samu inna a yarda suka barta haka yasa saratu mai dan wayau a cikin su sake tambayan inna. Inna wai lafiya kike yau kuwa ina yayan mu tajene tun dazun bata dawo ba kuma ban santa da zuwa unguwa haka ba ai. Hawayene ya fara zubawa inna da sauri saratu ta juya wurin jakkan kayana tana dubawa tare da fadin inna sun dauke yayan mu sun turata aikatau ke nan ? Wani irin kuka inna ta kara fashewa dashi lokaci guda saratu ma kukan ne yazo mata sai hakan ya jawo hankalin sauran yan uwan mu dake wasa kofan inna. Saratu ke fadin wayo yayan mu ki dawo kada kije aikatau don Allah an ce ana lalacewa wurin aikatau din nan. Haba dakin inna ya koma dandalin kuka da tashin hankali don kuka sosai yaran keyiwa inna. Da gudu lantana taje ta kira Asabe tana mayar mata da karya wai ga inna can ta tasa yara a gaba sai kuka sukeyi don tafiyana. Asabe ta fito babu ko dan kwali a kanta sai a hannu ta rike tana fadin bamu cikin abin kuka da yamman nan . Kuyi muna shiru masu mugun manufa da sheri don tafiyar yar uwarku zaki zauna ki dasa muna kuka ke da yara haka kamar anyi mutuwa a gidan. Asabe wallahi sai kin dawo muna da yayan mu ko zaman gidan nan ya gagareki keda munafukanki da cewa lantana. Mara kunyar banza da wofi koke can kika nufa idan naji dadin yar uwanki ana turo min kudi irin haka marasa hankali kawai. Da kuna zaune a gida kara zube ina zamu samu irin kudin da muka samu yau a gidan ba gashi har kun dawo kun samu anyi abinci ba yau. Kowan nan sai ya dandani wanan hanyar aini yanzu gaba haihuwan ku ya kaini tunda na samu mafita daku. Ana cikin hakane Abba ya shigo yana fadin yaya yayane tun a kofa nake jin muryan ki umma. Asabe tace barni da mutanen kawai din nan wai tafiyar yarinyar nan yahanasu ta saka yaran nan a gaba suka mayar muna da gida gidan makoki. Yahanasu kina da hankali kuwa ke yanzu idan kina da tunane ai wani nauyi aka rage maki Abba ya fada. Fada mata dai ko zata gane hakan ina nan gashi dan kudin da hajiya ta fara bayarwa kowa ya fara amfana dashi gidan nan ba gashi kunci shinkafa da wake ba yau a gidan. Umma kyale ta barin ganta ni yahanasu har mamaki take bani yanzu kan yarunyar nan babu nuna kawaici a kanta ko kadan. Idan ma bata nuna ba ita ta sani nidai na nuna mata nike da iko da abina daga diyan ko har kai a gidan nan ko wa yan nan na samu mai daukan su bayar dasu zanyi zuwa birni. Ba saki bada muba tunda ke kika haife mu cewan Saratu sai inna takai mata duga daidai Abba na shigowa dakin inna din. Bar dukan ta rabuwa da dan uwa nada zafi tundai irin wanan na yarsu nima dai ba haka naso tafiyan nataba kai tsaye so nayi muje tare inga wurin. Koma dai menene yanzu aikun nuna min kukeda yarku saidai ina son ku sani naji umma na fadin har wa yan nan za a tura min can birni aikatau. To wallahi hakan ba zai yuyuba wanan ya isa haka idan da hali dawo da yata zanyi gabana yafi mun kwanciyar hankali idan kasa mukeci mu kwaba muci tare. Toto to ya isa haka yana sa hannu ga aljihun shi ya ciro yan dubu guda biyu yana fadin ga wanan kya samu ko sabulun wanki ku saya. Da da nake saya kai kake ban kudi katafi da kudin Allah ya isan ka can kuci ku kadai ku gani. Kwadan ku ya fada kun raba ni da yata kun rabata da gatan ta da Allah yai mata don kawai tana diya mace. Shiru Abba yayi don inna bata taba tsayawa ta fada mai magana ba haka kai tsaye irun ranan. Kwafa yayi ya fita bayan ya mikawa saratu kudin yana fafin karbi ki aje mata idan ta sauko zata karba a wurinki. Yana fadin haka ya fita daga dakin don kada yayi laifi a gurin lantana dake tsaye ta rike kugunta tun shigan Abba dakin inna. Yana fitowa fuskanta ya fara kallo ta watsa mai wani harara ta juya zuwa dakin ta shima abba yasan sauran zancen ranan a guri lantana don haka wani dabara ya fado mai. Yana shiga dakin ta juyo zata fara fada yace me zakiwa fitina kin san dai ba zama nayi a can ba rufe mata baki nayi da dubu biyu ke kuma ga naki dubu biyar ki rike. Sai lokacin lantana ta dan saki murmushi tana fadin wallahi yau Allah yaso ka da kakoma can ka kwana surin tsohuwar matar ka Nina fara hakan gani da dalleliya kamar ki inje dakin da warin fitsari da kwamatse ya ciki. NEW G R A KADUNA A hankali mama kande take koyar dani komai duk wani abinda ya shafi mami da zirga zirgan ta na cikin gida nice mai mata hidinar shi.. Da na zauna zaki ta kirani da zeey zan amsa da na,am mami in zo da sauri don biya mata bukatun ta wanda ba wani aiki bane. Sai dauko min kaza jiki mayar da wanan a cikin wardrobe ko dauko min ruwa shine aikin nawa kawai dawai mami bata iyawa sai an dauko mai mata wanan hidimar da ban daukeshi a aikin komai ni. Sai gashi cikin sati daya kacal na gane komai na mami nasan lokacin tashin ta daga barci . Zan shiga dakin in gyara gado in wanko mata ban daki zan koma in hada mata ruwan wanka tana zaune tana lazumi don mami akwaita da yawan ibada sosai. Zan dawo dakina in jirata tana tashi zata kirani in dawo in share dakin duk da ba wani datti ke ga dakin ba amma kullun sai nayi gyaran shi sau biyu a wuni. Kafin ta fito wanka nagama hada komai sai in koma dakina can kuma idan ta fito zata kirani da zeey zan zo in je dining in hada mata tea wanda wani ruwa ne baki kawai sai dan sugar kadan bata shan madara da suga ita. Idan na gama zan koma dakina inyi wanka in shirya in dan huta kafin ai mi wani kiran kuma inzo. Kai masu kudi suna shagalin su banda abin aikin kudi wai wanan dinne aikin da aka raboni da gida do shi aikin da mutum zaiwa kansa ba sai ya nemi mataimaki ba. Amma hjy gashi tana ganin ina aiki sosai sai fadi take yarinyar akwai kwazo da sanin ya kamata. Do ita gani take yanzu komai na zuwa mata da sauki a nata bangare har zata samu tayi barci ta huta na dan lokaci. A bangaren yaran gidan hjy kuwa ba ruwab su da shiga tsabgata nima hakan ne dasu. Saidai su wani lokacin zasu sakani wani aiki a gidan wanda ya shafi rayuwan su suma ga tsana karara da ko wace ke nuna min. Dan gara salma da har yanzu ba zance tsanane ko tausayina ba a ranta don na kasa fahintar inda ta dosa dani a ranta. Wani lokaci inji sanyi a wurin ta wani lokaci kuma idan ta daka min tsawa sai na gigice don tsoro. Ita irin mutanen nan ne shiru shiru da mugun ta don surutu bai dameta ba ko kadan za a zauna wuri ba zakaji bakin ta ba sai wani lokaci ta furta idan ta furta daya kuma shike nan. Duk wanan abinda suke min bai damuna naka ma raya a raina idan naga sun dau wanka zasu tafi school nakan ce inama a ce nice a matsayin su haka. Nasan da ko Asabe ba zatayi gigin takani ba balle lantana dana tsana fiye da kowa a gidan mu yanzu. Ni dai na rasa dalilin da yasa yaran gidan hjy suka tsaneni a baki dayan su in ka debe hjy da mama kande da suke nuna min kulawa a gareni. Tun dai ace yan matan don a fili suke nuna min kin jini da kyama duk da yanzu nasan nima ina tsabta fiye dacan da nake Ancau din mu. Na kanyi tunane indon dun kauyancine da kazanta yazu duk na daina wanan a ganina do na canza nayi fes na kara zama shar kamar bani ba. Ga mai da turare na yan gagu da hjy taban tace in dinga shafawa idan nayi wanka gun kashe gari dana zo. Komai ina yi shi a taka tsamtsam a gidan ban yarda in ketare iya inda aka ajeni ga aikina dan dama wani lokaci idan zama ya isheni nakan shiga kitchen in taya su mama kande aiki do su basu da hutu kamarni. Ko yaushe a cikk girki suke dan hutun su kadan ne tundai idan yaran gidan suna gida wancan yace kaza yake so wana yace baya cin kaza yau. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 9️⃣ YAR UWA NOVEL DINA NA KUDINE KIJI TSORON ALLAH KI BAN HAKKINA KAFIN KI KARANTA DON GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , , 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI TURO KATIN WAYA DARI UKU NE KACAL BA YAWA, , , , Ina daki naji muryan hjy tana kwalla min kira daga dakin ta nima na amsa da karfi da Na,am mami. Fitowana daga wanka ke nan lokacin don haka na dauki riga a gurguje na saka a jikina don zuwa amsa kira hjy din. Na sameta zaune tana waya saman gadon da yasha gyara a wurina tunda safe nake gyaran dakin mami din don duk wani aiki da zata kai ga bude baki tace inyi kafin ma tace nayi din tunda yanzu nasan aikina a gidan. Bana jin kiuya ko kasala tunda na saba aikin daya fi wanan a kauye don hakane hjy bata samun matsala dani koda an samu din ma saidai gyaran dan abinda ba,a rasa ba kawai. Ganin tana waya yasa naja na tsaya daga nesa kadan ina jiran ta gama waya ta bani umurnin abinda zan mata lokacin. Wasu kaya data fitar ta nuna min da hannu alaman in dauko mata su ban tsaya ba na juya zuwa wurin kayan na fara dauko su ina ajewa a gaban ta. Sai waya take ta faman yi mai kama da fada da alama dai da danta ne ko wani kanin ta take waya yadda nake jin tana fitar da kalamai gareshi. Bayan na gama kwaso kayan ne naje gefe na tsaya don bata ban umurnin in tafi ba. Hango tawul din data fito wanka ta goge jiki nayi gefen gadon ta na juya zuwa wurin na dauke tare da nufar kofan ban daki na shiga na baza shi a dan karfen da ake bazawa. Unders din da suka taru a duk da na ranan dana daren jiya datai amfani dasu ne kamar rigan nono da buje da handkacin amfanin ta. Sai na tsaya na wanke tun ina jin muryan mami tana waya har nazo na daina ji da alaman ta dai gama wayan ne a lokacin. Nafito ta bini da kallo tana fadin wai dama kina cikin dakin nan zeey ? Ina ciki ina wanke under din da ke ajene tace min kai zee bakya hutu ko yaushe kina cikin aiki ai kiranki nayi kawai don ki miko min kayan nan in gani don jiya aka turo min su daga Dubai. Daga min su daya bayan daya nagani na duka na fara dauko kayan ina dagawa daya bayan daya tana daga kai idan na nuna mata. Amma sai naga kamar wanan yafisu tsaruwa zeey tana tambayana ta hanyar dago kanta taji me zan fada. Mami duk suna da kyau sai dai wanan din zai fi maki kyau gaskiya don kallan jikin ki. Ido ta kura min kamar tana nazarina kafin tace ashe kin iya zaben abu mai kyau kema ni dai murmushi nayi kawai ina kawar da kaina gefe. Sai dai ke har yanzu dadina dake kinki sake jiki a gidan nan ki nuna nina haifeki kamar kowa . Kullun kina abu kamar bakuwa a gidan nina rasa wanan halin naki kodai bakijin dadin zama da mune zainab ? Da sauri na dago kai ina fadin mami ina ji haka dai yanahina yake ko a gida nan ma aina sake ke nan . Sai tayi dan murmushi tare da fadin a hakan da kikeyi sai na dinga tunane ko bamu kyauta makine wani sa, an. Shigowan Rufaida dakin ne a daidai lokacin da nake kwashe kayan zuwa wardrobe din mami kamar yadda ta umurceni inyi. Rufaida tayi sallama ta shigo ina jin suna gaisawa da mami din take fadin kunga dama kun tashi ke nan yau weekend kun samu wuri kun kwanta kuna ta barci ina sauran mashiriritan suke basu tashi bako har yanzu ? Ban dubasu ba ta bata amsa gefen hjyn naga ta zauna ysyin da nazo wurin da niyar incewa hjy din akwai wani abinda zan matane ko in wuce. Kafin in furta Rufaida ta daka min wani uban tsawa malama may kikeyi kuma a nan bakin gama aikin ki ba ki fita magana nake son yiwa mami yanzu. No no no Rufaida na fada maku bana son wanan hattaran da kukewa yarinyar nan bari ganin tazo tana aiki a karkshin mu. Ku dauka hakan gazawa ne ko wani abu ni da kaina na rokota hannun iyayyen ta kuma aikaimin karamci aka ban ita don haka duk daya na dauke ku gareni don jinta nake kamar diyar cikina itama. Bana son wanan halin da kuke nuna mata a gidan nan to ai mami biyan ta akeyi bata daya damu ai. Na fada maku ban son hakan da kukeyi nan aikin ta yake tare dani dole kuma ta shigo dakin nan tunda abinda tazo yi ke nan a gidan nan. Baki Rufaida ta zunburo wai ita an mata fada ni dai ina tsaye ina sauraren su can nace mami da wani abinda zan maki yanzu ne wanka na fito dama ? Yamm yamm yamm don Allah fita kiba mutane wuri inda aikin ma zan karasa mata shi amebo kawai. Nidai na juya na fice daga dakin raina bai min dadin hakan ba ko kadan yadda yan matan nan suke min a gidan gashi naga duk da mami na tsawata masu sai dai bata son ransu ya baci ko kadan. Yanzun na gama waya da yayan ku yana son ya raina min wayau wai ba zai samu zuwa rantsar damu ba da za ayi. Abinda naji mami tana fada ke nan lokacin da zan fita daga dakin bayan korar da Rufaida tayi min. Dakina na koma na karasa shirina duk da ba wani shiri bane dan dongon rigar da anty safiya ta sai min sune nake sakawa yanzu saidai naji hjy tana wakan tana son a samu lokaci aje a sai min kaya don tana kunyar wanan kayan da nake sakawa haka. Ban sa raina ba sai na gani balle zumudin hakan ya hana zuciyana shakat da damuwa na fito na nufi kitchen don samawa cikina abin karyawa. Ruwan shayi da soyayyen dankalin turawa nagani a cikin kula shina diba na hada tea na dawo inda Larai ke gyara kayan miya na zauna kusa da ita na fara sha ke nan naji muryan Rufaida na kwala min kira da yar aikin hjy don sunan da suke kirana dashi ke nan dashi a gidan in ka debe hjy dake ce min zeey sai su mama kande da suke kirana da zainab. Amsawa nayi da na,am tana karyawa Larai ta fada yadda zata iya jiyo ta tana karyawa shine ba zata zo ba Rufaida ta fada. Dole na mike zuwa amsa mata kiran a tsakiyan falo na sameta tsaye ta rike kugu tana jirana a hasale. Ina zuwa take fadin ke don uban ki zan kiraki kice kina karyawa haba Rufaida wanan zagin fa haka ? Muryan Anty salma ce dake zaune wurun dinning tana karyawa lokacin ba dole in zage ta ba don daukan kanta take daya damu wanan yarinyar. Kin san dan kauye bai iya samun wuri ba dama idan yaga ya waye sai yake gani yafi kowa waye wa ki shige dakina kaya na nan na tara a bayi na ki wanke min ta fada tana juyowa inda nake tsaye ina kallon ta da idanuwa da suka ciko da hawaye don zagin da tayi min. Bazaki tafi yin abinda nasaki bane ta fada cikin tsawa da sauri na juya na nufi hanyar dakin nata don kwaso kayan datace din. Saurara ta fada naja na tsaya cak wuri guda ina saurarenta kada ki fara ki satar min wani abu a dakin nan don ranki zai baci sosai idan kinyi hakan. Haba haba hakan baida kyau fa Rufaida and kuma kinsan mami ba zataji dadi ba idan tasan da hakan anty salma tace. Mami kina nufin banda right din sakata aiki ko warning dinta akan kayana tana yar aiki gidan nan. Nidai na juya na wuce ina shara hawaye don abu biyu ga zagin dana samu ga kuma zargin sata yanzu. Dakin na shiga na same shi a ya mutse kamar ba mace ke kwana a cikin sa ba don daki babu gyara ko kadan yadda na ganshi. Bai da banbanci da dakin da nake bambancin su dai wanan mirrow shi cike yake tab da kayan shefe shafe sai manyan akwatuna dake gefe ajiya ga kuma tv bango babba. Duk a fakaice na kalli dakin nasan da hakan don wanan ne shigana na farko wani daki daya shifi gidan in kin debe na mami da kullun ina cikin sa. Mami bata taba ce min wani abu game da dakinta da zanga kudi ko agogo ko sarka da sauran su sai dai in dauka in mayar inda take aje sarka ko agogo kudi kuma zan daga filo in aje mata shi yadda suke. Ina shiga ban dakin idona ya fara arba da pant din ta saman kayan su rigan nono da bujen ciki kai kaya daine na unders da mace ke sakawa a jikin ta ta tara gudan masu yawa a wurin. Tattarawa nayi na a bucket din dana gani a bayin nafito tana tsaye tana kokarin cire rigan dake jikinta take fadin ki tsaya ki gyara min daki kafin kije wankin. Dole ba yadda na iya tunda nazo cin arziki ne gidan su na fara gyaran dakin ita kuma ta shige bayi don yin wanka kafin ma ta fito na gama na bar dakin. Can baya naje inda ake wanki da sauran aiyuka na wanke na shanya mata tunda wanan ba aiki bane a wurina. Na gama na dawo na samu ruwan tea di dana aje har yayi sanyi haka na dauka nakarasa shan shi da sanyi. Fitowa nayi da niyar komawa dakina na samu yan matan gidan zaune da kawayen su a falo zaune. Zuwa nayi zan wuce ba tare da nayi masu magana ba nakai tsakiyan naji muryan Nazifa na fadin amma wanan yarinyar bata kunya. Sai duk suka dawo da kallon su wurina wanan wacece yaushe tazo gidan nan cewar wata daga cikin bakin. Rufaida dake cin chewing gun ta tabe baki tana fadin a kauye mami ta dauko ta . A hakan mami ta dauko yar aiki wanan wani aiki zata iya kazama da ita haka ga ruwan kauyanci ko ina tare da ita. Gaba daya suka sa dariya lokaci guda ke zoki gaidasu ki shige salma ta fada a dake ba tare da tayi dariya ba ita. Nazo gaban su na tsuguna ina gaidasu basu amsa ba sai dayan ke fadin kina gani ta nan idan ta waye sai duk kun girgiza a gidan nan. Amma dai kin gama damu Laila wanan din ne zamu girgiza don tayi clean . Oh kina raina irin kauye ke nan ai barsu yadda kika gansu ba wani zancen clean gareta don tana clran aurin nan ba karamin taksici zakuci ba duk wanda ya zo kanta zai tsaya rabu da mutum ka barshi a ranan da yake kawai don idan kace zaka kaishi innuwa shiko yana turaka rana . Salma ta kalleni cikin takaici tace ba kingaida su ba me kike jira kuma a nan yanzu ? Sai ta gama jin abinda muke fada mana Rufaida tace tana watsa min harara na mike ba bar wurin ina jin bakin na fadin ke wanan ai idan tayi clean ko yaran gidan nan ba zasu barta ba tana hakama yaya aka kare da suranta duk mai hankali yasan anyi halitta a nan ai. Ire iren haka yasa nakan shige daki in zaune in dai ba mami ke gida ba dole ina falon don aike ko wani aiki da zan mata. Yan matan basu bar gidan ba har mami ta dawo daga unguwar data tafi tana shigowa ta samesu a falon gaisawa suka farayi bata ko amsa masu ba ta fara fadin ina wanan yarinyar zeey take ne ? Sai kawai ta shiga kwala min kira ina cikin daki na kulle kaina naci kuka har na gaji naji an bankado min kofan dakina da karfi . Haka yasa na dago kai ina kallon mai shigowa dakin lokacin ba kowa bane sai Nazifa ke kina nan zaune to mami tana kiran ki. Mikewa nayi da sauri ban ko tsaya share fuskana daya gama dan hawa ba saboda kukan da nasha. Mun iso falin daidai mami ta dauki ruwa zata kurba nake fadin sannu da dawowa mami ta dago kai ta kalleni sai ta furzo da ruwan lokaci guda daga bakin ta. Gaba daya hankalin kowa ya koma kanta don ganin me ya faru tana fadin zainab mamana kuka kikayi ne ? Kaina na girgiza mata kafin in ce a a ahankali ina wasa da yatsun hannuna haba bana son inganki cikin damuwa ko kadan. Shiru ta danyi ta mayar da hankalin ta ga wayan ta kafin tace kwashe kayan nab ki kai min daki. Na duka na dauki kayan zuwa dakinta kallo ta bini dashi tana fadin na rasa me yake samun wanan yarinyar taki ta sake jiki damu har yanzu. Cikin ko in kula salma tace mami tambayi yaran ki don su suka bata mata rai suka kirata da yar kauye a gaban ta dazu nasan shi takema kuka dai. Salma haka take bata shiga harkan kowa kuma bata boye gaskiya fadin shi takeyi komai dacin sa a cikin su. Amma na fada maku tun randa yarinyar nan tazo kan ku kiyayyeta a gidan nan ko ban fada ba ranan kan mami tayi masu tas a kaina a gaban kowa don sauran ma ashe ba baki bane duk yan gidane suma. Wanan fadan ne ya kara jawo mi bakin jini a gurin su sosai suka saka kafan wando daya dani dole idan mami bata gidan ina daki ko wurin kande. Haka kuma bai hanasu sakani aikin wahala da suke gani suna ban ba gashi mami bata zama gida yanzu don shirye shiryen da ake na zuwa rantsar dasu Abuja. Wanan ya dauke mata hankali daga komai dake faruwa a gidan ba wankin unders ba har tufafin su yanzu suke bani in wanke wai nafi mai wankin gidan iya wankin kaya sufita a cewar su don mugunta kawai. Ranan ina dakina kwance mami ta kirani kande aka aiko ta kirani nazo da sauri tare da wani na samesu ina zuwa ta nuna mashini tana fadin ka ganta nan duk ita zaka dinkawa kayan . Kallona tellan yayi yana fadin bari a aunata ke nan da sauri hjy tace tana daga mai hannu ina warning din ka da wanan awon da kukewa mata yana daga cikin aikata alfashan zama koda kuwa namijine dan uwanka ko mace yar uwar mace haramun ne yin hakan. Hjy za,a kiyaye ya fada yana dan sosa kai tare da dan jin kunyan abinda hjy ta fada mai sai kuma ta dago yana fadin kayab zasu matse ne ko a danyi mata su free ne. Kafin mami ta bashi amsa na karbe da fadin free nake so kada ya matseni don Allah. Ji mun yarinya kin san abinda yake nufi ke nan ko ni dai nayi dan murmushi kawai ina dukar da kaina kasa cikin kunya. Kudi masu yawa taba tella ya tafi yana mata sallama tare da godiya gareta wuri na samu sama kafet din dake tsakiya a daidai inda mami ta dora kafanta tana zauna cikin limtsetsen dogon kujeran falon. Hjy ta kalleni tayi murmushi kafin tace min wai zee yaushe zaki daina wanan hali naki ga kuja zaki wani zauna a kasa kamar marainiya. Dama ina son jin wani abu a dangane da rayuwan ki mahaifiyar ki tana da rai ? A bazata tambayan yazo min da sauri na dago kai na kalli hjy kafin ince tana da rai sai kuma tace mahaifin ki fa ? Shima yana nan na bata amsa kai tsaye kuma suna tare da babar ki kai na gyada mata wanan karon idanuna yana kawo hawaye. Yaya akayi suka barki zuwa inda basu sani ba kina matsayin kina ya mace zeey basu gudun ki fada mugun hannu ne ? Hawaye bakeyi sosai tare da fadin Asabe ne tace sai nazo birni suka hada kai da lantana aka turoni don innan mu na haihuwan yaya mata wai. Tace idan ba aikatau ba bamu da wani moriya nan gaba tunda aure zamuyi mu barsu gida. Tauuu ita Asaben ta fadi haka diya mace bata da amfani sai aikatau ta tambaya tana kallona. Kaina gyada mata alaman eh sai naga tayi wani dan murmushi iya fuska kawai. Wacece Asabe ta tambaye ni nace kakar mu ce wacce ta haifi Abban mu tare muke zaune gida daya . Mami tace kuma ita ta haifi Abban naki itace ta haifeshi shida gwaggon habiba subiyu ne yaranta kawai. Ina ita gwaggon naki take yanzu nace ance tana aure a zaria ne tace ikon Allah zarian nan dai tamu kaina gyada nan ma.. Bata san an kawoki gidan nan bane aiki daga garin ku nace nima ban sani ba mami don tana dadewa bata zo garin mu ba. Amma ai bata rasa samun labarin an kawo ki kaduna in har yar uwan haihuwan mahaifin kice ta hakika ya kamata acs suzo suga inda kike nawane kaduna da zaria . Sai ga hawaye nabin idona nace itama yanzu tunda Abba ya auri lantana ba ruwanta da innan mu kuma. Ikon Allah ita innan taku ina yan uwanta suke nace cikin ancau suke da zama saidai it inna iyayyen ta duk sun rasu kafin mu girma bamu sansu ba. Tace mahaifin ki kika kwaso da kama ko babar ki nace Asabe kullun in tana fada sai tace wai zubin innan mu kwaso sak. Kenan ita kika biyo da dirin jikin kin ga ai wata rana nasan zamu hadu da innar take idan ta kawo maki ziyara nan ko ? Yana da wuya inna tazo nan don Asabe ba zasu bari inna din tazo nan ba don ko zuwa za ayi sai dai Abba yazo kila. Kina da kanne da kuka fito ciki daya dasu nace mu bakwaine mata innar mu ta haifa shine Asabe ke mata gorin hakan. Ta auro lantana yanzu na barta da ciki wai za a haifawa Abban mu magajin gida tunda inna ta kasa haifa mai namiji. Innalillahi hjy ta fada tare da rike baki tana fadin har yanzu akwai irin jahilcin nan ashe ? Zata kara magana waya ta yai kara ta dauko haka yasa na mayar da hankalina ga tv dake aiki ga falon . Saiga yan jikokin ta su shigo do basu faye shigowa wurin kakar tasu ba uwarsu ma baifi sau uku na ganta a part din hjy ba. Daga bayane ma nasan a gida daya suke zaune da ita saidai ita tana nasu bangaren ne daban. Tunda nazo ban taba taka ko wurin get din gidan ba kullun ina cikin gida idan ma na fito iyakata backyard din gidan inda su mama kande kan zauna da yamma su sha iska. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 🔟 RAYUWA YANA FARUWA WUCEWA YAKE KAMAR BA, AYI BA ALLAH KABAMU IKON AIKATA ALHERI A KWANAKIN DA SUKA RAGEWA MUSULMI BAKI DAYA AMIN, , , , , 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU KACAL NE HAKKINA KAFIN KI KARANTA NAGODE, , , , Kamar yadda mami ke yawan jana a jiki yanzu na fara sake jiki a gidan mami saidai bada yan matan ta ba dan gara samarin ko a gaban mami zasu sakani wani aiki mami na fada tana komai zan masu shi. Hakama yau ya kasance kowa na gidan yana falo zaune ana hira ban dade da fitowa falon ba mami ta kirani in dauko mata wani takarda sunan shi kawai ta fada min nace nagane shi na juya da sauri zuwa dauko takardun. Rufaida ta kalleni tana fadin wanan akwai iya yin tsiya ko ina ta iya karatu balle ta san shi wai ta gane bari ta dauko shirme yau sai na mata tsiya a gidan nan kuwa. Yo aini tafi min ku kodai bata gane ba ai zata dauko din da kwatace ballema tunda tace ta gane ta gane din ne. Wani lokaci yarinyar tana bani mamaki sai in manta in mata magana cikin turanci sai kuma ta gane me na fada mata din. Hajjaju ko dai tayi karatu ne watakila ta danyi boko a can garin su fa yaya jalal ya fada yana dakilan wayar shi. Sai jamal yace boko for ware kana ganin yarinya yar tipical yar kauye da ita na maganan wani education nan. Sai gani da saurina nazo har gaban mami ina mika mata takardan mami ta karba tana fadin tau Rufaida dake da ita duk kun kuru yau a gidan nan . Lah mami ashe kin hakeni kimin tsiya idan na taba maki yar ki ke nan Rufaida ta fada tana dariya kafin ta juyo ta watsa min wani harara. Oh wellcome my boy jalal ke fada don shigowan jikokin hjy falon rike da takardun makarantar su yaron na zuwa ya fada jikin kanin mahaifin shi da sauri. Saiga uwarsu a bayan su itama ta shigo falon ashe tare suke tafe har yaran sun fara zuba mami tace oya great us cikin daure fuska. Take yaran suka fara bin kowa a falon suna gaida su har zasu gaidani Nazifa tayi saurin fadin she is not your aunt . Nazifa ki fice min a idona akan yarinyar nan kafin rayukan mu yakai ga baci a gidan nan don ba zan lamuci hakan ba. Jamal ya mike yana fadin ke stop interrupt your self akan wanan yar mami din a gaban ta don yanzu itace da mami baku ba. Ashe ka gane gaskiya bana son ana raina dan Adam a rayuwana idan ka sanni a da ban kokai zeey wayewa ba kuma a haka mahaifin ku yace sai ni. Duk aka kwashe da dariya falon wurin Rufaida yarinyar karama ta nufa tana fadin anty ki koya min assigment dina mommy tace bata iya ba. Karban littafin tayi tana dubawa kafin da namijin ya juyo zuwa gareta shima ta karba tana duba kafin tace wanan sai Nazifa kila don ban gane me ake nufi ba gaskiya. Wani subject ne Nazifa ta tambaya tace mathematics ne fa wanan ai sai ku Nazifa wace nazifan ta fada tana fadin su dai kaiwa salma ta duba. Salma dake zaune tana duban wayan ta tace kada ma su haroni don ban iyawa zanyi ba indai maths ne. Fuska yaran suka bata mami na fadin amma ko kunji kunya ta mika hannu yaran su kawo ta gani . Ban san lokacin da nace mami barin duba masu ko zan iya ba mami ba kowa dake falon dago kai yayi yana kallona da mamaki. Ke wanan fa ba tallan goro bane karatune na boko ake fada don kinji mami tace kina daidai da kowa zaki kawo muna rigima. Ban damu da abunda Nazifa ke fadi na karbi littafin tare da jawo yarinyar a jikina. Tsayawa nayi tare da nazarin abinda aka basu kafin in fara rubutu duk idanuwan su a kaina yake. Tiryan tiryan nakewa yarinyar bayani yadda zata gane har muka gama da nata na dago kai ina fadin namijin ya kawo nasa. Sai lokacin naga kallon mamakin da kowa ke min a falon lokaci guda mami tace dani kinyi boko ne mamana ? Nayi na bata amsa a hankali duk yan matan mami suka zaro ido waje kinyi boko kike haka kuma a aikatau ? Ban kulasu ba naci gaba da koyawa yaron assigment bamu dauki lokaci ba na karasa yaron ya dago yana murmushi. Mami ta mika hannu ta karba da wanda nayi mai musali ya kwashe ciki tana bin rubutu na da kallon mamaki. Wani maki kika tsaya a karatu ne zeey ta tambaya cikin kureni da idanu tana son jin amsa daga bakina. Ina ss3 Asabe ta fitar dani da banan nan zan gama karatu tace wai bata ga amfanin boko gun ya mace ba tunda ba namiji nake ba shine karshe ta turo ni nan. Kowa a falon shiru yayi yana kallon yadda hawaye ke zuba min a idanuna lokaci guda don maganan da nakeyi. Yanzu kina son karasa karatun ki ko aure zasuyi maki kauye kina da tsayayye acan . Kai na girgiza tare da fadin banda kowa sai Asabene tace wai zata sama min miji ta hadani dashi. Kai waiko wanan Asaben ita ta haifi mahaifin ku da cikin ta wanan abinda take gwada maku yayi yawa gaskiya. Karatun ma da zakiyi ki samu madogara a rayuwan ki saida ta hana kiyin shi gaskiya na tsani wanan matar damai irin halin ta. Muryan Nuriya matar yaya mubarak ke fadin mami ashe kuma an daga tafiyan ? Mami ta juyo tana ce mata sun daga kedai kin san abin gwaunatin kasan nan baida tabbas ai yanzu kuma sai dai sun kiramu kuma. Ai wa yan nan sun kwafsa muna wallahi don kila yaya Jafar ya fasa shigowa kasan nan ke nan sai wani jikon . Yasan an daga ne mami ta tambaya tana kallon jamal dayayi magana sai jamal din ya juya yana kallon jalal yana dariya. Kudai kuka sani da tsegumi kamar mata haba mami don mun fada mai an daga ranan shine tsegumi shifa ya tambaye mu muka fada mai gaskiya. Waya aike ku fada mai da ku barshi sai idan yazo yaji ai ba shike nan ba zai kirani ai zamu gamu dashi ta fada a hasale tana mayar da hankali kan sytem din ta data bude a gaban ta. Nice ta farkon mikewa a falin bayan Nuriya matar yaya mubarak data ja yaran ta suka koma part din su ba don yaran sun so haka ba don ko shigowan nan nasu don assigment din yaran tashigo har dasu. Dakina na shiga nabi gadona mai laushi na kwanta ga sanyin A C dana sake ya game dakin sai barci. Bada masaniya ba mami ta sama min makaranta don inci gaba da karatuna a wani college dake gaba da unguwaelr kadan. Ranan da dare take fadamin zancen ci gaba da karatun nawa lokacin nema kowa a gidan yasan da zancen cigaban karatuna yanzu. Wanan yasa yan matan nata kara jin haushina sosai banda daman bin motar su kamar yadda mami tace mu rika tafiya tare da safe idan zan tafi. Ganin haka ban fadawa mami ba nake takawa da kafa ina zuwa makaranta don nisan shi ai bai kai na kauyen mu dana baro. Zan tashi da asuba inyiwa mami duk wani abinda nasan nice mai mata shi kafin gari ya haska na karasa zan karya in taka da kafa inje school. Sam mami bata san da zancen tafiyana da kafa zuwa school ba sai wata rana zata unguwa da safe hakan yasa ta fito da wuri daga dakin ta. Yan matan ta samu zaune suna karyawa take tambayan ina nake nan suka fara kallon kallo a tsakanin sai salmace take fadin mami wayen garin nan banganta ba ai. Tafa tafi school Nazifa ta bada amsa sai mami tace usman ne ya kaita ya dawo ya dauke ku sai sukayi shiru don sun san da kafa nake tafiya school duk dadewan nan. Bana son irin haka sai kuyi kwanciyar ku a daki kuna sharan barci sai lokacin da yai maku dadi zaku fito . Alhalin kunsan da cewa ita nasu school din ana duka idan an makara ko shi malam usman din yayi ta zaman jiran fitowan ku. Fada sosai mami tayi masu kafin ta fita can ta hadu dani na kusan shiga school din mu ta tsaya tana tambayana yaya akayi na tako da kafa ? Nace mami bana sin in makara ana duka idan mun makarane maza shige mota in karasa dake ke baki tsoron wanan titin namu gashi shiru babu kowa a wanan lokacin. Har ta saukeni fada take min ta bude jakka ta zaro five hundred tana miko min tare da fadin karbi wanan kiyi break dashi don nasan baki tsaya karyawa ba kika fito. Lah mami wallahi na karya kafjn in fito ki bar kudin don mami bata ban kudi sai dai tace na karya kona dauki abinci inje dashi school din. Ina kallo ta wuce karfe biyu da yan mintoci na shigo gida har lokacin mami bata dawo daga unguwar da ta tafi ba. Haka yasa na samu daman samun dan barci rana bayan nayi sallah azahar ban sake fitowa ba duk da yunwan da nake ji don kudin da mami ta ban na kasa kashe su don ban saba da kashin kudi ba. Ban farka ba sai bayan la,asar wanka nayi lokacin ne naga fashin sallah yazo min don haka nayi wanka kawai na fito na dauki always na kimtsa jikina dashi. Abinci ya fito dani naga ashe yamma yayi sosai a lokacin haka yasa na gane na dade ina barcin rana yau. Don na samu har yan university sun dawo suna cin abinci mam kande ne ta dauko kuloli take fadin yau kan yar gidan hjy kin sha barcin rana. Ba dole tayi barci ba tunda taga arzikin banza wanan irun kune idan kun samu wuri kuke mayar da yan gida daga kofa. A a saidai tasan wanda zata mayar Nazifa tace tana amsawa Rufaida sai naji salma tace wai ku meye matsalan ku da yarinyar nan don Allah ? Rufaida tace I just hate her wallahi balle yanzu da take clean sai nake ganin gaskiyan maganan dasu Rubby suka fada ranan a kanta. Ashe bani kadai ke ganin canzawan yarinyar nan ba tundai wanan kayan da mami ta saka aka dinka mata suna fitar mata da suranta na asali waje. Zakace badaga kauye take ba har wani tafiyan sallo take tana yanga idan tana magana yanzu. Kai ku din nan kuna da wani magana wallahi koma dai yaya ta koma kunsan ba zata taba kaiku asali ba dai ko ? Sallama na fadan haka Nazifa tace yanzu waye ya damu da wani asalin mutum can zamanin nan boko ai mutane basu duban haka idan sunga abinda yai masu . Dariya sosai salma ta kwashe dashi don dama irin du baka ganin dariyan su sai ta baci ni dai ina diban abincin ina jin cinmutuncin da suke min kala ban tankasu ba. Saidai na kudurta duk ranan da wata daga cikin su ta kara zagan min uba bazan kyaleta ba sai inda karfina ya kare koda hakan na nufin inbar gidan ne na masan hjy ba zata yarda ba da hakan. Don takan fada min Zainab ina son in ga na taimakeki kin zama wani a rayuwa ki samu ki taimaki yan uwanki tunda dukan ku matane har ku bakwai . Shiyasa nake son ki dage ga karatun don wata rana ki taimakawa innan ki da yan uwan ki Asabe tasan diya mata ma diyane abin alfahari kuma. Ire iren wanan tunanen nakanyi inshanye wani abinda ake min a gidan don kawai manufar mami a kaina don kuma burina ya cika. Karatuna bai hanani yin abinda nazo yi gidan mami ba har na kai wata shida da zuwa gidan . Iyakata da anty safiya idan tazo in fito in gaida ita tare da tambayan yayan ta da mijin ta ta bani amsa da suna lafiya suna gaida ke. Sai kuma ta tambaya injin dai baki wani abin asha zainab kada ki manta da kinzo cin arziki ne a nan don haka kiyi biyayya sosai. Irin maganan da anty safiya takan min ke nan idan tazo gidan ina nan kafin ta tafi Gashi banji wani zancen kudin aikatauna ba ga bakin kowa nima kuma ba damuwa dana san komai a kan albashi na nayi ba. Mun samu hutu makaranta naji mami na fadin ya kamata in je in duba gida tunda su basu neme ni ba har yau. Don tasan yanzu inna na tacan cikin damuwan halin da nake ciki babu dai yadda zatayi ne ta sawa sarautan Allah ido. Ban san mami har ta saka ranan zuwana gida ba sai dai tace inje aimin kitso a makwabtan mu don akwai wata yar makarantar mu a gidan kusan tare muke dawowa da ita kullun. Itama takan zo gidan mu in mata nan yan gidan suka san na iya kitso sosai don har mami nakan wa kitso yanzu tunda ta gane na iya kitso sosai da yan matan ta. Sai dai bankan so yi masu kitso don muna kitson suna zagina har mu gama. Washe gari na shiga wurin mami in gaida ita da kwana sai na sameta zaune ta fitar da kayan data dawo daren jiya dasu don nice na kwaso zuwa dakin ta. Sallama nayi ta dago kai tana fadin yawa samu wuri ki zauna dama yanzu nake da niyar kiran ki sai gaki. Zama nayi kamar yadda ta umurce ni kafin ta fara fadin kinga wa yan nan turamen ta nuna min su da hannu nace eh mami. Tace yan uwanki zaki kaiwa su guda shiddane iri daya ne saidai nasa a bambanta kallar su wanan kuma na innan ki ne ta nuna min wasu uku a guri daya. Sai wanan kiba Sabe daya lantana daya wanan shaddan kuma ki ba mahaifin ki sai sabulai da omo kiba yan uwa da abokan arzikin ku . Kwana hudy zakiyi ki dawo driver daya kaiki zai dawo ya daukeki ranan ki gaiyar min da innan ki sai wanan ki ba mahaifiyar ki tana miko min wani abu a cikin leda wanan kuma mahaifin ki zaki ba albashin kine na watannin da kikayi a wurin mu na tara maki shine na raba biyu innar ki rabi mahaifin ki rabi. Kada ki manta ina gaida innar ku kwarai kice na gode sosai sai watarana idan mun hadu. Hawaye na fara yin a wurin ina tsugune sai mami tace ko kin fasa zuwa gidan ne in aika masu da sakon da sauri nace a, a mami na dai rasa godiyan da zan makine yanzu. To maza ki tashi ki shiya ga sabbin kayan kinan saman gado sai ki zabi wanda zaki dasu tsufin kuma duk ki hadasu ki kawai kannen ki su karasa su can . Ko mahaifiyar ki tana sa kwance ki zaba mata wa yan nan dana ware da za a kyautar . Da gudu nace tana sawa mana mami to jeki ki zabar mata kala biyar daga ciki da sauran tarkacen daya dace ki kai mata . Na mike don na rasa bakin da zanwa mami godiya don ta hanani yin hakan gareta. Kayane mai yawa har na rasa wanda zan cirewa inna sai da mami tace ki cire mata zannu da dogon riga zatafi son su ai. Haka muka dauki hanyar ANCAU da tsaraba taf a bayan mota da zankaiwa iyayyena koma in ce mahaifiyata don itace mai tsaraba da yawa ciki. Don hjy tafi son inna na fahinta sama da mahaifin mu Abba kodon tana mace yar uwantane ban sani ba. Malam Usman driver mami bai tsaya ko ina ba dani sai kofar gidan mu tun daga nesa na hango wata na suyar wani abu an baibaiye ta. Saida muka matso kuss ne na gane saratu ce kanwata ashe ganin mota ya nufo kofan gidan ya kuma ja ya tsaya. Duk wanda ke wurin ya kurawa motar ido don son ganin kowaye a motar ban fito ba saida na gama dauko kayan dana rike a hannu na fito daga motar. Saratu zoki kama min kayan nan kin tsaya kina kallona haka muryana kawai ta sheda yasa ta gane ni a lokacin. Ido ta waro waje tana kallona tare da fadin yayan mu maimakon ta yo wurina sai kawai ta kwasa da gudu tayi cikin gida tana fadin. Allah mun godema Allah mungodema yau ga yayar mu ta dawo garemu innan mu fito yau Allah ya dawo muna da yar uwarmu gida. Ashe ba sayar da ita akayi ba a birni ji abinda saratu ke fada yasa sayran kanne fitowa da gudu kafin su ja su tsaya suna ina take ta kwasa tayi hanyan fita suka bita da gudu. Mun hade dasu a kofan shiga gida sukayo kaina da murnan su da ihu suna jin dadin gani sai ihu sukeyi yayan mu ta dawo yayan mu ta dawo garemu yau. Jin ihun da yaran gidan suka dauka na murnan zuwana yasa Asabe fitowa daga shiyan ta dan kwali a hannu tana fadin. Shin Abu Abu kuke fadan tazo ina Abun take ne in ganta tana kokarin wuceni da yan uwana. Gani nan Asabe na fada ina kokari zuwa wurin ta sai taja baya tana dafe kirji tare da fadin Abuce haka ? Zonan na ganki na karasa wurin ta sai ta rungumeni tana kuka tana fadin yar nan ina kika shige haka babu duriyan ki har an fara zargina a gari na sayar dake ga yan birni. Ina gidan hajiyar da kuka kaini tun barina garin nan na da kwana bakwai gun anty kafin ta kaini gidan. A a ai dada kin dawo garemu ke nab dai yanzu ba komawa wanan birnin kuma dai ta fada tana share hawaye. Ni dai ban ce mata komai ba sai waige nake ko zanga innar mu ta fito banganta ba yasani sakin Asabe na nufi dakin mu da sauri ina sallama. Ina shiga da hango ina zaune saman dan gadon dake dakin tayi tagumi ns karasa gareta ta da sauri ina fadin inna gani nazo gare ku yau. Murmushi inna tayi kawai sai dayan kanwar mu data sawa kira daga dakin a daidai lokacin da yara suka fara shigo da kayana dakin. Irin surutun da yaran dake shigo da kayana gidane ya sa hankalin lantana dake daki bakin cikin dawowa ya hanata shakat tunda saratu tazo tana ihun na dawo wani tukukin bakin ciki ya sokar mata zuciya. Don Lantana sam bata so in dawo gidan ba a lokacin don so tayi ace ba bata da gaskiya kamar yadda ta kulla sherin haka har zance yabi gari gaba daya kowa ya dauka hakan ne. Inna eta bada kudi wai a sayo min ruwan leda nace basai an sayo min ba inna a dai sayawa driver hjy daya kawoni. Wai wanan mutumin driver ne yanzu saratu ta fada nace drivern gidan hjy ce shi ke kai yaran ta makaranta ya dauko su idan da aike kuma sai a aike shi. Bawada ya ankara da zuwan lantana daki namu tazo ta tsaya a kofan dakin ta tokare hannayen ta da katon kofan dukka gefe biyu. Saida ta gama saurarebn mu ta kalleni tsaba ta fara fadin eyya Abuce ta koma haka ? Gaba daya dakin muka juyo muna kallon ta lokaci guda taci gaba da fadin halan a cikin injin suka sakaki aka wankeki haka. An maidoki kamar wata karuwan birni koda yake wasan abinda kike a burnin wanan bude idon haka lokaci daya. Amarya ke nan ai inkiga mutum yayi abu yana da gadon shi ne ban gada ba babu dana da zai taba zina da yardan Allah inna ta bata amsa. Kinsan aikin mutum sai ya dauka shi kowa keyi ko ina ya samu kansa ni Allah ya tsare mi yata a birni don bata gaji watsar da kai ba. Kaina yana duke kasa ina tunanen wai yaushe inna ta fara magana haka sai naji lantana na fadin wa kike nufin ya gada to ? Wanda yasan ana haka har furtawa yata dashi nakeyi abu yaso zama rigima don har saratu taso shiga maganar inna ta kwabe ta. Andaiyi abin kunya ta fada tana batin kofan dakin don bata zaci innan mu zata bata amsar maganan taba. A kofa ta hadu da asabe da takawo min zogale data gyara tana shirin ci cewa lantana tayi muna ganin kilibibi a gidan nan. Ya tadawo yawo tazubar har ake wani riritata don kwadayin duniya muna jin ta a daki nace har yanzu wanan matar tana wanan haukan duk data haihu girma yazo mata yanzu. Ina girma a nan banda iya shegen data karo cin mutunci dai ne mutum ya guji karshen shi. Asabe ta shigo da sallaman ta tana aje min kwanon ganye a gaba tana fadin kici yar nan dan ganye na gyara sai gaki. Saratu takai hannu zata diba takaiwa saratu dundu a baya tana fadin mara kunya ba a ke nakawo ba bakuwa na kawowa. Sai dana huta nayi sallah kafin malam usman ya aiko wai zai tafi na samu inna ta dan dama fura ta aika mai kafin yayi sallah yasha ga awara da saratu ta cika mai leda dashi har kwan zabbi inna ta aika a nema cikin gari ba a samu dayawa ba hakan ma naji dadi yadda akai mai. Bayan mun dawo daga rakashi ne na bude kayan don saratu ta ta demeni da tambaya mena kawo masu ? Tundana fara bude kayan jikin kowa yayi sanyi kafin ma in farawa inna bayani kamar yadda mami tayi min. Nan dai na labartawa inna rayuwana a gidan hjy saidai na boye mata irin cin fuskan da yan matan hjy kemun a gidan. Don tsakanin mahaifa da diyan su sai Allah sararu ce ta dauki na Asabe da lantana takai masu nasan don fitina tace itace zata kai. Lantana ta fara kai ta karbi kayan a tsune tana fadin duk da ance kayan zina kamar kayi zinane kaima. Amma wanan zani ya shereni ba zan barshi ya tafi ga banza ba tunda a haka aka sameshi. Saratu tace dadai yafi tunda ba yau aka fara cin kayan zina ba don har na tsohuwa an saba ci cewa da uwar lantana din. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣1️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YA ALLAH KA KAWO MUNA TSARO A KASAR MUNA NIGERIA, KASAWA WANDA IF,TILLA,I YA FARU DASU HAKKURI DA SANIN KADDARA A RAYUWAN SU, , , , , , , DARI UKU NE NOVEL DINA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALLAMA YAR UWA DON TURA KUDI GA NOMBA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN KO EIRTEL NA DARI UKKU. Abba bai shigo gida ba sai gap da magariba ya dawo lokacin ina alwala a tsakar gidan mu dani ya fara arba. Ja yayi ya tsaya tare da fadin wa nake gani nan kamar Abu ya fada cikkn mamaki don bai san da zuwana ba ashe sai wanan shigowan da yayi ya ganni. Amsa na bashi ina mikewa a daidai lokacin ina kai dan ruwa a baki kamar yadda yin hakan ya zama min al,ada tun ina gida ba tafi kaduna har yanzu kuma ban daina yin hakan ba idan na idar da alwala don sallah. Abba nice na fada cikin dan murmushi Abu ina kika shiga haka babu labarin ki ga kowa ita din da tazo ta dauke ki bamu kara jin wani zance a gareta ba har wanan lokaci. Safiya bata kyauta muna ba ta barmu cikin zargi da fargaba don ba haka mukai alkwari da ita ba. Ayi hakkuri Abba kasa anty ma,aikaciya ba ko yaushe take da lokacin tafiya ba irin hakan. Yar mairo koma menene ai ya dace ta dan waiwayo musan halin da ake ciki dake a can . Yanzu kai ganin ta yasa ka tsaya nan kana zuba har ka mata irin bakin cikin data jefa ku a tafiyan ta . Lantana ce ke fadawa Abba hakan tare da mika hannu tana fadin ban ledan kafin ka shiga can a wawashe. Tana mika hannu ta fisgi ledan daga hannun Abba ta juya tana fada abin kunya yarinya taje gantali tsawon wani lokaci saida tagaji don kanta ta dawo har kuna wani jin dadin hakan. Abba yai tsaye kamar ba Abban dana sani ba yana bin inda tabi da kallo kafin ya juyo har na bar wurun ina kokarin shiga dakin innan mu ko. Da mamaki a raina yadda naga komai na gidan namu ya kara hargitsewa ga baki daya na tayar da sallah. Bayan na idar da sallah muka zauna da inna sai lokacin nayi mata bayanin komai a tsanake har sakon mami na dauko na bata na nuna mata na Abban mu da tace a bashi. Inna tace aidai bata don wanan yarinyar tana kyala ido a kansu sai taga bayan su a lokaci guda. Nace koma meye ai dai na isar da sako saidai inna nifa wasu abubuwa da nake gani a gidan suna daure min kai tun zuwana. Me kika gani daya daure maki kai ai dama shi ramin mugunta kurarene idan wanda akewa yayi hakuri. Bai wuce dai abinda kikaji ba tsakanin umma da lantana ko wanda kika gani yanzu tsakanin ta da mahaifin ki. Duk waya ja hakan sai umma gashi kuma tun ba,aje ko ina ba abin ya koma tsakanin su yanzu. Tana ji tana gani ganin danta yana batun gagaran ta a gidan nan tayi fada har ta gaji ta saka ido idan da can tayi mai aure ne don ni a gidan nan, yanzu bani kaida ke ganin bakin cikin ba harda ita. Shiru jayi ina tunane a raina tare da fadin mai yai zafi tsakanin Asabe da lantana kuma yanzu. Abba bai shigo dakin inna ba sai bayan sallah isha,i zama yayi muka gaisa na mike na dauko mai sakon shi kamar yadda mami tace in bashi. Duban kaya yayi yana juyawa tare da fadin ikon Allah duk wanan matar ta bayar a kawo min nace Abba ai mami mutumiyar arzikice. Zamanta mai kudi baisa ta raina tallaka ba nan dai na gutsura mai dan labarin mami din da aiyukan da nakeyi a gidan. Abba ya kalli takardan dake hannun shi yana juyawa a hankali kafin ya fara kokarin budewa kudi suka soma zubowa daga cikin takardan yan dubu daya sabbi fil dasu. Da mamaki yake fadin yahanasu kudine fa matar nan tayo muna sako a cikin takardan nan. Na amsa da fadin cewa tayi kudin aikina ne in kawo maka da zanzo duban kudin Abba yayi kafin ya juyo ya dubi inna da ko kallon inda yake batayi a lokacin. Wanan matar wani irin kudine gareta haka yar mairo ko harda wani sana,a kike mata bayan wanan ? Gaskiya matar kwarai Allah ya hadaki da ita a birni don ba kowa bane zai iya maka hakan . Mamaki kalaman Abba ya bani don na dauka zai tambaye fiye da hakan sai ga Abba ya buge da fadin in kara kwazo don gaba ta aiko da wanda yafi wanan din yana mikewa. Malam iya abinda zaka fada mata ke nan dan ka rike kudin da baka tabbatar daga ina suka fito ba kamar yadda matarka ke fadi kullun. Bana zargin tarbiyan diya na ko kadan don nasan tarbiyan da muka basu tun farko. Allah yasa a kanshi take don nina tsuke da sakon wanan matar gaba daya hankalina bai kwanta da hakan ba ko kadan. Abba yana kokarin tura kudin cikin aljihu yake fadin ance kudi kare magana ganin wanan kudin yanzu ya kara tabbatar min da gidan kwarai diyata take. Bayan fitan Abba a dakin ne yai shiru na dan lokaci kafin mu fara jiyo hayaniyar Abba da Lantana daga kofan ta. Lantana ba kunya take fadin yau sai dai a rabamu a gidan nan amma wallahi sai ka fada min abinda kajeyi dakin can ranan girkina. Kinji ko haka muke fama da fitinan su a gidan nan koda shi koda umma don ni ba shiga shirginta nakeyi ba sai ta koma yi da yara yanzu. Allah yasa har na tafi kada wani matsala ya faru tsakanin mu nace lokacin inna ke tambayan kwana nawa zanyi nace kwana hudu mami tace driver zai dawo ya daukeni. Ba zan yarda ki koma garin nan ba batare da wani ya biki yaga a inda kike ba koda malam ba zai tafi ba zan hada ki da kawun ki lawal kuje tare. Inna hakan yayi daidai don mami ma bataji dadin hakan da aka barni ba wanda ya biyo sawuna tunda naje garesu bayan anty safiya data kaini. Matar kirkine tunda tayi tunanen hakan duk wata uwa ta gari wanan tunane ne zaizo mata a rai. Yadda za a sake diya mace haka ba tare da wani nata yabi sawunta yaga inda take rayuwana. Nagodewa Allah daya karba min addua na danake kullun gare ku hankalina bai taba kwaci ba tun bayan tafiyan ki sai dana samu sakon safiya a boye tana min bayanin halin da kike ciki tare da kwantar min da hankalina. Tun wanan lokacin na falwala ma Allah al,amarin na kara dagewa da addua a gareku sosai. Mun sha hira ranan don bamuyi barci ba sai da inna ta labarta min abindaya faru tsakanin Asabe da lantana tun bayan haihuwan lantana gidan nan. Tunda lantana taga ta haifi namiji kamar yadda umma ke muradin haka a kanta shike nan take ganin ta gama da kowa a gidan nan shi kanshi malam gaba daya an rasa gane kanshi yana ganin itace hasken rayuwan shi ita da danta. Bata yarda kowa ya taba danta a gidan nan dama ga dan bai faye lafiya ba wai yana da ciwon numfashi. Subbahanallahi gaskiya banganshi ba tunda nazo ai ba zaki ganshi ba don ba barin shi gidan nan takeyi ba wai kada wani ya halaka matashi. Tunda an fada masu wurin biye biyen bokayen su cewa wai asiri akai mai yazo hakan ba lafiya. Jin hakan yasa na ra,ya a raina har na koma bazan taba yaron ba in Allah ya yarda . Me zai kai ki shiga shirmen wanan mara mutuncin barsu ya kare a kan su ranan dai mun dauki lokaci muna tataunawa da inna. Washe garin kukan yaron Lantana ne ya karade gidan dashi ina mamakin karfin halin inna data ki kulla al,amarin yaron. Na fito don gaida Asabe da Abba da lantana sai na samu Abba yana tsaye yana rarashin yaron a waje sai tsala ihu yakeyi uwar na shafa mai magani. Kasa nakai na gaida Abba na juya don gaida Lantana samu nayi tana hararana a wullakance. Ban damu da hakan ba na fara gaida ita da kwana kafin nnace Abba meke samun shi tun dare nake jin kukan shi. Kafin Abba ya furta Lantana ta karba da fadin kuka kan ai dole ne tunda an jefe shi bamu da hutu shi wahala ni a wahalce kullun idan dan ruwa ya tabeshi ko sanyi. An kaishi asibiti na tambaya ina kallon Abba don ban yarda na kalli lantana ba don yadda naji ta fara maganan ke nan zancen innan mu gaskiya ne da take fadin sune suka jefa mata da don ana bakin ciki dashi. Ina wanan tsohuwar gidan zata bari akaishi asibiti tace ina saka danta wahala ko yaushe yana kashe muna kudi. Tunda ni ban yarda ta juyani yadda ta saba ba ace uwar miji komai danta keyi da matar shi idon ta na a kai. Da dai Abba ka daure an kaishi asibitin birni bana kauyen nan ba aji mai zasu fada tunda yana wahala haka. Tab abu mai wuya ke nan yaya muka kare da asibitin mu ma na nan balle har nawani birni can tunda ansan abinda aka kulla a kai ai ba a bada shawaran haka ba. Koke don bakya nan ne ai da an sakaki a cikin wanan sherin don ni yanzu na san zamana da kowa a gidan nan ai. Allah ya sauwaka sannu kaji na fada ina kallon yarin kafin in juya in wuce zuwa lungun Asabe dana sama tana zuba ruwa a buta zata zagaya ban daki. Ban manta ba don ban yarda na shiga dakin ba a wajen na gaida ita na juyo na dawo dakin mu inda na samu kannena na shirin zuwa makaranta islamiy a lokacin don boko ana hutu. Na taimaka suka shirya saida suka fice bayan inna ta basu ashirin ashirin din cin masa idan sun tafi. Don ba ai abin karyawa ba alokacin lantana ce da girki kuma bata dora wanda za a ci din ba don yaron ta da ya kwana yana rigiman dare. Wanka nayi na shirya cikin wani dogon rigan atamfa dinkin shi mai kyau ya dan matseni kadan . Inna sai fadi takeyi mai za,a sayo min in karya dashi nake cewa ta bari a gyara dumame shi zanci don kada in takurawa rayuwan inna din. Sai ga Abba ma ya shigo gida da leda biyu ya tsaya daga tsakar gida yana sa min kira na amsa na fito ya miko min ledan ya tafi da daya dakin Lantana. Kosai ne da bread sai kayan shayi a ciki dana bude nake fadin inna ga kosai din ki diba ki karya da bread din don ni ba zan sha ba. Nace bazan sha shayi ba inna dan dama kosai din zanci sai inna tace daidai ki sha abin ki mu in da sabo mun saba da wanan ai a gidan nan. Inna tunda ga kudi a hannun ki me zai hana ku sai abinci rabi kuma sai ki juya shi kina dan sana,a dashi. Shawaran da nayi ke nan a zuciyana Allah ne ya dubemu ya jefoki a lokacin da muke cikin bukata hakan. Amma malam ya canza yanzu gaba daya a gaban kowa gari zai waye zai fita ya samowa matar shi abin karyawa muna kallo a gidan nan. Inna ki daina damuwa da wanan tunda ubangiji yana kawo maki mafita da zaki duba diyan ki ki basu abinda zasuci. Ire iren hiran da muke tayi ke nan a dakin inda na tillasawa innan mu sai data karya kafin yaran ta su dawo su hana taci tunda nasan tana son sha itama. Karfe goma suka dawo gida da shigowan su abinci suka fara nema a gida suka samu ba a gyara ba zasu ci shi hakana da sanyi na basu kudi suka sayo taliya saratu ta dafa kowa yaci. Na zaga wurin yan uwa da abokan arziki irin matan da nai sabo dasu ina masu kitso kafin tafiyana kaduna. Har ya saura kwana daya ya rage min duk da zaman gidan namu babu dadi amma nake ji kamar kada in koma kadunan kuma. Inna ta danyi kokatin ta sosai wurin yiwa hjy tsaraba irin na kauyen mu da zankai wasu mami din. Washe gari karfe goma driver yazo daukana inna taso muje tare da kawuna kaninta yaga inda nake saidai anyi rashin sa, a kawun nawa yana da uzuri a ranan don haka muka dauki hanya dagani sai malam usman driver gidan mami a motar.. Tunda muka tunda muka tun karo gifan naga wasu canji a cikin dan kwana hudun da nayi bana garin. Ni dai sai bin ko ina nake da kallon da mamaki a raina don ganin bakin fuskokin dake gidan namu tun daga get har zuwa cikin gidan. Na fito daga cikin motar tare da dora hijjabi da kyau a kaina na nufi hanya shiga gida don na tsaya daukan kayana malam usman yace za a shigo min dasu ciki. Da sallama a bakina na shigo falon sai dai abinda nayi arba dashi ne yasa gabana faduwa don ganin mutane a falon gidan kusan kowa na gidan yana falo ga bakin fuska. Wa nake gani kamar diyan mami haka muryan mami ya dawo dani daga tunanen dana fara a lokacin. Da dan gudu na karasa na fada jikin mami data ware min hannayen ta alaman inzo gare ta a lokacin. Kai kai kai mamana me innar taki ta baki haka cikin kwana biyu kika kara kiba haka kinyi wani fresh dake mami ke fadi. Tsuki yaya jamal yaja yana fadin ko dai ta kara kauyanci ji wanan bindata saka don Allah da cewa hijjab din jikina wai. No dan Allah malam usman bace muna da wanan kayan kazantan wurin nan ka shiga dashi wurin kande suna kice cewar Rufaida dake nufin a kauce masu da kayana a wurin. Malam usman dake shirin aje kayan ya dauka da sauri ya nufi hanyar kitchen dasu na dago ina fadin ban jakkana in kai daki bayan mun gama gaisawa da mami ban kalli kowa a falon ba. Jeki kai ki fito ki ci abinci wai ai kunsha tafiya don wurin bai kasa ba akwai dan nisa da kaduna. Shiyasa nace malam usman yayi sakko yaje ya dauko ki don ku dawo da wuri bana son tafiyan dare. Na dauki kayana zan shige naji muryar yaya jalal na fadin baki iya gaisuwa bane ke idan kin samu mutane ? Ke tafi ki aje kayan daki ki dawo mami tace haka yasa ban tsaya sauraren shi ba don bin umurnin mami din. Na kai kayan na dan dade ban fito ba azatona bakin zasu tafi kafin lokacin sai dai har na fito suna nan a inda suke sai lokacin na gaidasu sai dai sun ragewa a fLin don ko su yaya Jamal basa falon yanzu. Abinci na diba kamar yadda mami ta umurce ni na koma dakina ban kara fitowa ba sai dare bayan nayi sallah isha, . Don na kwanta ina tunanen gida ina tuna innar mu da na dan saba zama da ita a yan kwanakin danayi a can gida sai nake ji kewan su na damuna yanzu. Hjy na samu a falo kishigide saman kujera sai wani matashi dake zaune kasan kafet dake tsakiyan falo. Ya mike kafafuwan shi sambala sabala tare da dora daya saman daya kanshi yana daidai cinyar hajiya. Suna hira a cikin natsuwa su biyune kadai a falon, kowa yagan su zasu bashi sha, awa alokacin. Ni dai kallo daya na iya masu na kawar da idona garesu don kyawon mutumin da kwarjini ga zati da Allah yai mashi kamar shiyayi kanshi. Da ina ganin kyawon su yaya jamal kamar su sukai kansu gasu da iya kwalliya da tsabta shiyasa zaginsu gareni bai damuna da sukece min yar kauye amma sai ganin wanan ya dushe duk kyaun da suke dashi a idona yanzu. Zeey ga yayan ku yayan su jamal jiya yazo sai kanwarshi da tazo ranan da kika tafi. Sannu da zuwa yaya ya hanya nace mai ina dan rusunnawa don bashi girma da Allah ya bashi a kaina. Fuska a sake ya amsa min gaisuwa bazakace bakin shi na motsi ba yadda yake magana da hausarshi da baya fita da kyau. Daga haka na mike don barin wurin ina tafiya a harde don rudewa da nayi don ban taba ganin mutum yai min kwarjini irin haka ba a idona. Muryan mami naji tana fadin zeey dauko ma yayan ki abinci nan yaci yau a kasa yake so ci yace don kiuya. Taci gaba da fadin ki dauko har dani don nima din kiuyan nake ji sosai in samu inci in shige daki duk na gaji yau munyi yawo sosai yau. Kulolin abincin dana gani a jere sabbi fil dasu wanda ban taba ganin irin su ba a idona don kyau. Saida na dauko na karshe zan kawo naji karan bude kofa a part din mu wata matashiyan budurwace ta fito daga dakin dake kusa da nawa tana fadin. Mami na dauka baku dawo ba har yanzu naga yanzu is aftre eight ashe kun dawo sannun ku da zuwa ta fada fuska a sake. Mun dawo mami ta bata amsa lokacin da budurwan ke zama kusa da na zaune a kasa tana fadin bros yau kaga kd ke nan ashe ? Yamutsa fuska yayi yana fadin mami ta kaini gurin yan uwanta dana daddy har na gaji a cikin turanci suke maganan wanda ba ko wani abin nake ganewa ba saboda kwarewan su da yaren. Ina wuni nace mata da hausa ina durkushe kasa a lokacin lfy ta fada tana kallona kafin ta juya wurin mami tana fadin who is she mami ? Zainab ke nan da nake fada maki tayi tafiya yarinyar da nake zama da ita yanzu wace gwaggon safiya ta kawo min yar uwar safiya din ce. Oh itace she look quit ai ba kamar yadda su Rufaida ke fada ba a kanta mami tace rabu da yan rainin wayau kawai ban san me yarinyar nan ta tare masu ba gidan nan. Mami me za a zuba maki na tambaya sai ta dago tana fadin fara zuba mai shi da baison cin abinci sai shiririta ya saba da abincin su na shirme can. Lokacin ne na saci kallon shi na fara bude kulolin abincin ina son tambayan shi abinda zan zuba mai kuma ina jin tsoron ko bai iya hausa ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣2️⃣ ALHERIN ALLAH YA CIN MAKU MASOYA A DUK INDA KUKE A FADIN DUNIYAR NAN ALLAHUMA AMIN ALLAH. LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA DAUKAN NAUYIN HAKKIN WANI A KANKI BA. Nidai na kula tun dawowana kowa ke walwala ga yawan bakin dake ta zuwa gidan babu wanda zan dan tambaya ko meke faru a gidan haka. Naga kowa na gidan yazo ga kuma baki daketa zuwa daga ban garori daban daban sai gidan ya cika da baki sosai. Wurin kande naje ina tambayan ta abinda ke faruwa take fada min ai zancen hjy ne ya tabbata za, a tafi Abuja a rantsar dasu. Itace a jahar kaduna wace ta samu mukamin sai wasu daga sauran jahohin kasan nan kafin in furta wani abu larai take fadin. Wai mukamin me hjy ta samu hakane wanan cikar da akeyi gidan nan haka mama kande tace waya sani yar nan su dai suka san abinsu can. Shigowan anty safiya kitchen din tare da yar uwarta yasa muka katse hiran da mukeyi muka shiga gaidasu da zuwa. A, a ke yaushe kika dawo me tafiya babu sallama koda yake baki da laifin hjy ta fada min komai daga baya. Tana magana take karasawa cikin kitchen din tare da fadin kande zamu kawo maki wasu yan aikin da zasu kwana biyu suna aiki tare daku a gidan nan don aiki zai maku yawa ku biyun nan yanzu. Duk da dai maza da matane zasu zo din ba lalai bane ma ku taba masu aikin su sai dai idan suna nema wani abu zaku iya basu. Iyakar ku ke da larai shine zaku taimaka muna wurin bawa ko wani bako abinci idan an gama daga na karyawa har zuwa dare. Ta juya tana fadin ke naji hjy tana neman ki tun dazun ashe kina nan gurin su kande. Da sauri na mike zuwa wurin kiran da ake min na barsu kitchen din dasu kande tana masu bayani . Cikan da gidan yayi a lokacin yasa na fara dan rabe rabe har na isa wurin hjy din dake dakin ta tare da wasu jiga jigan mata farare tas kamar ta sai dai sunfi hjy jiki da tsayi sosai. Haka na rabasu har nakai wurin hjy nake fadin mami gani ance kina kirana ina kitchen wurin su mama kande ne. Tace yawa zee wanan kawar tawace ke son kitso sai kuma Autana da naji tana tambayana ke dazun din. Kallon matar data nuna min zanwa kitso nayi ina fadin yanzun zamuyi mama naji dayan race kai hjy wanan yar taki tayi min kyau wallahi. Kafin daya tace hjy maria ke nan kedai diya mata suna burgeki tace wallahi naso dai in haifi mace kamar yadda hjy iyami ta rufe da ya mace bayan maza amma ban samu ba. A raina nace duniya ke nan wasu na gudun mata wasu kuma suna son su kowa da irin bukatan shi duniyan nan. Nidai ganin dukkan su manyan matane yasa na juya da sauri na bar dakin tun kan ta bani amsa lokacin da zan mata kitso. Ina fita daga dakin mami dakin Anty Nuriya na shiga daga kofa na tsaya ina sallama kafin ta ban amsa in shigo. Dakin yana da dan duhu ba haske sosai a lokacin tana kwance saman gadon ta makale da waya a kunnen ta. Anty ina kwana na fada tare da dan rusunnawa kadan ta amsa min da fadin ina zuwa please taci gaba da wayan da takeyi abinta. A hankali na juya zan bar dakin don ganin ta shagala ga waya naji tana fadin ki dan jirani please kayan da zan tafi dasu Abuja nake son ki shirya min. A raina nace masu duniya ke nan kayan ma sai wani ya shirya mashi idan Allah ya ba wasu sai su manta kowa ma rai gare shi ai. Dole naja na tsaya din ta gama wayan ta juyo tana kallona tare da fadin yawa tun dazun nake neman ki ai mami tace kina cikin gida. Ina gun mama kande na bata amsa tace dama kayan da zan tafi dasu ne nake son ki shirya min su don ba wani dadewa zamuyi a can ba bai wuce ki saka min kala biyar ko hudu ba. Nuna min jakka da zan saka mata kayan nayi na nufi wurin tare da tambayanta a ina kayan suke ? Bude wanan drower suna ciki na zaba yadda tace hakan nayi na bude kayana daga sama har kasan wardrobe din. Kinga na tsakiya din nan sune ban taba amfani dasu ba a ciki so ki dinga daga min dinkin su ina gani ko zanga wanda yayi min. Bani da zabi sai yadda tace din na shiga daga mata kayan kamar yadda ta umurceni idan na daga wanda yai mata zatace muga wanan ta dan mike ta gwada a jikin ta idan kuma na dauko wani tace No bar wanan miko wancan da nake gani. A haka har muka zabi kalla hudu zuwa biyar na gyarasu na saka mata a dan karamin troler na tafiya mai masifan kyau. Na gyara sauran na juya don barin dakin take fadin kinga kwaso dagayen rigunan can mu gani. Sai naji raina ya baci don dai ba wani gitma na tayi ba kila amma ta kafeni da aiki haka ba wani aiki ba. Na nufi wirun kayan tare da kwaso mata ina dagawa take fadin aje wanan nan ko jefa wancan can har muka gama ta sake nuna min wanda zan mayar na nafe na marya inda suke. Na juyo in kwashi sauran don in mayar take fadin wa yanan ki kwasa ina ganin ai zasuyi maki wanda naje dasu school ne wanan time wani ma sau daya nayi amfani dashi. Ikon Allah ashe shi yasa ubangiji yace idan zakayi kayi don Allah idan zaka bari kabari don sa. Nagodewa Allah da ban nuna komai ba duk da raina ya baci amma na tsaya nayi mata abinda take so a dakin. Don kayana na yayan wani da wance masu tsada da kyau sun fi kalla goma wai duk ni kadai keda su tace min. Na juya kaina a sunkuye ina fadin nagodd tace kai haba dai da baki nan ma ai duk a nan zan barsu saida hjy ta bayar dasu ga wanda take so. Jin dadin kyautan yasa na ranan harda dakin ta na gyara mata da zuciya daya sai dai ta dawo ta samu dakin a gyara na gyara mata ko ina. Nayiwa kawar mami kitso haka yaja hankalin sauran matan suke ta kwadayin in masu suma sai naji mami tace su bari a dawo Abuja don tare dani zata tafi. Wani dadi naji sosai a raina jin mami tace dani za a tafi abuja din garin da nake jin labarin shi yau gani zan tafi cikin sa duk da nasan ba fita zanyi ko ina ba amma dai zan karasa ince ai na taba zuwa. Tun da naji na fara shiri nima duk da naji Nuriya ta fadi ba dadewa za ayi a can ba nima kaya kala biyar na zaba daga cikin wa yanda ta bani ranan. Naso sai na nunawa mami kafin inyi amfani dasu hakan bai samu ba don busy da mami take a ranan . Bata da lokacin kowa har kanta ma da tashigo zata fice daga gidan ko ace ana mata sallama. Sai ya kasance ina daki ko ina wurin su mama kande sai idan zanwa mami din wani abinda ya shafi rayuwan ta za a kirani. Dan taron da akayi a dan kwana biyun dana dawo kauyen mu a gidan mami yasa na koyi wasu abubuwa da dama a furin jama,an da suka cika gidan. Su kansu yan mata gidan mami suna ta kansu ne yanzu kowa na shirin tafiya saidai na kula cewa kamar ba wani shiri tsakanin su da yar mami din Nuriya don ban faye ganin su a tare ba. Ko banza duk tafisu aji da kyau sosai ga wayewa da tsari don ko maganan ta abin koyone. Washe garine za ai tafiyan inda wasu zasubi jirgi wasu kuma a mota zasu tafi inda ina cikin wa yanda zasubi mota da farko. Amma mami tana duba list din lokacin ina dakin take fadin ban yarda abar zeey nan ba idan mun isa can waye zai kula damu kafin su iso sai dai a cire sunan wani a sakata cikin tawagan da zamu tafi. Wayyo Allah na ashe in Allah yasoka tsuntuwa yake maga ko a dakin ka yau nice wai zan shiga jirgi tunda mami ta furta ai kamar na shiga ne in Allah ya nufa. Karfe shidda yai muna a filin jirgi ranan nasha zagi gun yan matan mami don tafiyan nan da mami tayi dani a jirgi tare da kawayen ta da yaranta dama wasu daga cikin dangin su. Koda muka isa can motoci muka samu sunzo daukan mu nidai basai na fada ba don bakauya na koma a cikin duk da dai kowa yana harkan gaban shine. Amma hakan bai hana tsaraguwa ba a cikin su da rakubewa a guri daya tunda ba wanda ya sanni ko nasan shi sai mami da yaran ta sukuma bata kaina sukeyi ba. Duk da akwai yan aiki irina kalian da wasu sukazo dasu daga wasu wurare sai dai hakan baisa na mamesu ba ina falo ko da yaushe don kada mami ta nemeni ban kusa kamar yadda naji ta fada kafin muzo. Haka komai ke tafiya a tsare kamar yadda suka tsara abinsu gwanin ban sha,awa sai kallon mamaki nakeyi maza da mata ana ta cudanya a guri daya ba wanda ya damu da hakan . Da kauyen mune ai da hakan ya zama abin magana a gurin mutana amma nan ba wanda ya damu da hakan . Wai washe garine za ayi rantsuwar su mami din tunda muka iso wasu maza sukazo gidan suka fita tare da mami da yaranta manyan mazan biyu. Haka yasa kadaicin rashin gabnin su mami a gidan ya dameni na dawo katon falon na zauna tare da wasu mata suna ta hiran su nidai sai sani lokaci nake dan jin hiran da sukeyi din. Ina kallon duk mai shiga da fita don na jawo kofan da muka sauka a cikin hikima na zare key din kofan ina ji daga inda naje zaune ana tambaya na kyalesu. Don ba wanda zai daukacewa nice na kulle kofan sai dai da mutum yazo ya murda yaji a rufe kofan yake ya juya inda ya fito. Har masu tafiya a mota suka iso gidan ya kara rikicewa da hayaniyar jamma, a haka yasa na fito daga cikin falon na dawo waje na zauna. Balle tun isowar ya matan suke aika min harara da warning ya karasa na gudo daka ciki na dawo wajen gidan. Nan ma motocine ke faman shige da fice tun ina aunawa a raina ince wanan yafi kyau a, a ta dazun tafi har na gaji na zubawa sarautan Allah ido. Can naga dawowan su mami hakan yasani mikewa tsaye daga inda nake zaune ina kallo na nufo wurin motar nasu. Sannu da zuwa mami na fada daga bayan ta hankalin ta naga daddy su siyama jikokin ta suna magana. Hakan bai hana mami dan juyowa tana amsa min gaisuwan ba ta juya taci gaba da maganan da sukeyi na juya zan bar wurin . Sai kuma ta juyo tana fadin zeey karbi jakkan nan nawa ki rike min nazo da sauri na karba na ja dan nisa dasu na tsaya. Sun dan gama magana ta fara tafiya yana biye da ita yana fadin amma mami sai naga kamar dai bayanin farkon nan shine shawaran bi koda yake barin gashi Jafar din duk da ban san inda ya shiga ba. Kuje kuyi shawara dai zan dan shiga inyi sallah kafin wani abu ya dauke min hankali kuma ta fada ta fara tafiya makarrabanta suka biyo bayan ta ruuuu dasu. Nima binsu nayi da kallo ina mamaki duk wanan taron haka don mami akayi shi haka ? Naji tace on Allah ku bari inyi sallah yanzu zan fito ta nufi kofan dakin da nake zaton shine nata wanda na riga dana rufe tunda na fahinci hakan. Mami ai kofan a rufe yake wata ke fadi daga gefenta lokacin da hjy ta murda kofan dakin da zuman shiga dakin.. Tun dazun ai dakin yana rufe an rasa inda key din yake da dan mamaki ta tsaya tana juyowa kafin na karso ina fadin ga key din mami a hannu nice na rufo kofan dazun. Ok zeey key din yana hannun ki ashe thank god wallahi yarinyar kirki shaf na manta da zan fita in rufo dakin. Da sauri na ciro a cikin aljihun dogon rigan dake jikina tunda ta dan jaye wurin na gane nufin ta na isa da sauri ina bude kofan. Juyawa mami tayi tana fadin don Allah a dan jirani in fito tasa kai tsshiga tana fadin zeey shigo ki hada min wanan maganin nabi bayan ta muna shiga tace don Allah rufo kofan nan in huta hakana. Ki duba akwai magani a cikin jakka ban samu shaba da safe na fita take fadi tana shiga bandakin. Maganin na dauko daga cikin jakkata don nasan shi na saba hada mata na balla daidai yadda take sha na dauko goran ruwa mara sanyi dake dakin na a je akusa. Daidai tana fitowa ne ake buga kofan taja tsuki tare da fadin mutanen nan idan nabita nasu bana samun sallah ko azahar ban samu yiba yau balle la,asar ga lokaci na shigewa. Dukan kofan da aka karayi da karfi take fadin wai waye zeey bude kofan idan maishi ya shigo yaga ina sallah dole yajira idan zai iya. Kofan na nufa na bude daga ciki aka turo ana fadin haba mami kin fita tun safe kin dawo kuma kin shige kin rufe kofa. Aisha yar mami ke magana tana shigowa dakin a cikin shagwaba idon ta ya sauka kan mami dake kabara sallah kafin ta juyo tana kallona tana fadin. Tare kuka fita ke nan da mami din kai na girgiza bakina kuma na fadin ina nan gida ina falo zaune na bata amsa. Wuri ta samu ta zauna tana maida hankalin ta furin wayan ta yayin da na shiga gyara dakin don wanan daman na samu a yanzu tun zuwan mu garin.. Har mami ta idar da sallolin dake kanta ta juyo tana fadi Esha ya akayi ne wai ma kunci abinci kuwa ? Zeey kinci abinci ita dai wanan din nasan halin ta balle yau taga wanan taron haka a gidan nan ? Kaina girgiza daga inda nake tsaye ba tare da nayi magana ba kina jiran me wanan yarinyar da gidanci kike wallahi ga abinci nan ki tambayi safiya mana tunda ta iso idan baki san wanda zaki tambaya anan. Waya ta dauko ta kira wani layi aka dauko ku kawo min abinci na mutum uku a hada komai a ciki ta fada. Tana kashe wayan tare da jan tsoki kafin Aisha ta ce mami gobe fa ni dinner kawai zan yi attending. Kina haukane gaba dayan ku da tan uwaki zamu tafi don duniya ta san ku ta fada sai yarinyar tace but mami kinsa, , , Hannu ta daga tare da fadin ban son korafi idan na fada kinsan iyakar maganata ke nan aka turo kofa wace ta kirane dauke da abincin wata hamshakiyar hajiya zakace ba zatai bara gidan kowa ba don bunkasanta sai gata itacs mai kasowa mami abincin . Bayan ta aje suka dan tsaya magana da mami nidai duk sai naji na takura a cikin su don Aisha ita tana dawainiya ne da wayanta bata ma saurareb su. Can mami ta juyo tana fadin zeey zuba muna abincin muci ko ? Matar ta juyo tana kallon daidai lokacin dana tashi tana fadin wanan yar ina kika samotane don ban santa ba gaskiya. Yata ce ta bata amsa kai tsaye tana jawo plate din abincin dana aje mata a gabanta inda ta idar da sallah. Kije ki lissafa min matan nan da suka zo da yamman nan za a kaisu masaukin su idan sunci abinci tafadawa matar. Yan kaduna ko na wani gari eh toh zaki iya lissafo min group group daga nan ki kiramin safiya tazo. An gama hjy ta fada tana fita daga dakin Esha aje wayan nan ki dauki abincin nan kici ta fadawa yarta. Ke kuma zuba naki idan kina zama da yunwa zaki jawa kanki matsala ba ruwana tana kai abinci a bakin ta. Zuba wanda nasan zai isheni nayi na dauka zan fita daga dakin take fadin ina kuma zaki dawo ki zauna muci a nan . Aka turo kofan yaya Mamud ne daddy su siyama ya shigo dakin da sallama ta karba mai tare da fadin har kun dawo ke nan yace . Eh mami an samu inda ya dace saidai kudin kusan duk dayana ne ma mamud kasan kudi ba matsala bane ai a dai samu inda ya kamata din shine abu yanzu. An samu mami kuma danki yace a tura mai ko nawa ne kudin zai biya munyi waya dashi ban samu ganin shi ba. Ai da ya barshi tunda akwai kudi a hannu na don gwaunati ta bamu dan kudi a hannun mu ai. Sun dade a dakin suna magana shigowan anty safiiya dakin yasa yafita ni dai ins zaune cikin su a tsawale. Bayan na gama na fito na barsu tare da anty safiya din suna magana kayan abincin na kwasa nakai kitchen inda ake tarawa. Nafito da zuman komawa falo in zauna muka hade da anty Rufaida wani irin shock naji lokaci guda saida na dan ja baya don tsoro. Yar iska masuwa mutane asiri kin dauka ba wanda yasan abinda kukewa mami daga ke har wace ta kawo kine gidan. Mu zuba dake a gidan nan ki gani idan zaki sha ruwa ya fada maki a ginan nan bakince kun iya mallake mutane ba ku. Duk da ban gama fahintar inda zancen ta ya nufa ba na dan gane wani bangare na zancen nata kadan. Tana fadin haka ta juya tabar wurin ba anty rufaida ba gaba dayan su yan kaduna dana sani a gidan wani kallo na kyamata suke bina dashi . Na kulla da hakan ne idan sun hangoni sai inga suna kallona ana gulmata ma,ana dai sun sani a baki sun tsargeni ke nan a yanzu. Wanda bansan wanan dalilin ba kuma banda wanda zaimin bayanin hakan sai kawai na fara kama kaina da kowa fiye da dacan baya dan dama anty salma idan mun hadu ba wanan kallon raini ko wullakanci sai dai idan na gaishe tace zeey din mami ke nan. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣3️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAN UWA FATAN ALHERI A GAREKU KO DA YAUSHE UBANGIJI YASA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA YA TSARE YA KARE MUNA IMANIN MU A DUK INDA MUKE AMIN. YAR UWA KADA KI DAUKI HAKKIN WANI KARAMIN ABUNE KI GUJI CIN HAKKIN DA DAUKAN ALHAKI WASU MAI IMANI A ZUCIYA TA GANE MAI NAKE NUFI NAN KIWA KAN KI DA KANKI HISSABIN IMANIN KI TUN A DUNIYA. DARI UKU NE NOVEL KI BIYA KI KARANTA CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA NAUYI KOWA BA A KANKI, , , , , Yau gidan ga baki daya ya kicime da shirin fita zuwa wurin taro duk da tun cikin dare an kwashe baki a gidan an kaisu hotel din da aka kamawa mutane. Hakan bai hana gidan cika ba da wa yanda suka kwana a gidan basu samu zuwa hotel ba din mutane sunzo da yawa sosai. Ban bar dakin mami ba tunda safe dana shiga don a falo na kwanta abina bayan na gama yiwa mami duk wani abinda zan mata a lokacin. Tunda asuba kuma na tashi na yi sallah ko alwala a famfon dana gani wajen gidan na fita nayi alwala duk wanda ya wuce a cikin mazan dake haraman zuwa sallah asuba sai ya dan kalleni. Nidai na gama na shigo ciki na shimfida dan kwalina nayi sallah daga gefen da mutane ke bi a lokacin. Na idar na dan dade zaune gurin ina kallon masu shige da fice ina dakon mami ta idar don nasan a lokacin tana saman salayan ta tana zikiri ga ubangjin talikai don wanan dabi,an mami ce hakan. Can na daidaici ta gama a lokacin na mike zuwa dakin don shine aikina kuma don shi akazo dani watau kula da al,amarin mami din. Sai kuma yanzu da nakan dan wa yarta wasu hidima a gidan don bata da damuwa ko ci fuska gata bata shiga lamarin kowa halin su yana yanayi dana anty salma itama saidai salman wani lokaci zumace ita ga zaki ga harbi idan halinta ya tashi. Da sallama na tura kofan na shiga sai dai nayi mamakin ganin su yaya mamud a dakin lokacin shida wanan bakon danta da yazo. Da gani wani maganan suri suke a tsakanin su a lokacin hakan yasa na juya da sauri zan bar dakin har su fita don ban san shigarsu ba lokacin sai ganin su nayi kawai a dakin. Muryan mami ke fadin shigo mana zeey ina kika shiga ne tun jiya da dare ban sakaki a ido ba na dauka nan zaki kwana ai tunda dakunan duk akwai mutane. Yaya mamud ya juyo yana kallo na shiko dayan ko dago kai baiyi ba ya kalli inda nake na fara takowa ina fadin. Falo na kwana mami na bata amsa kai tsaye kafin in karasa shiga dakin na durkusa har kasa gaban ta yadda na saba gaida ita kafi in jiyo i gaidasu daya bayan daya na mike. Kada ki sake kwana a falo baki gudun sanyi ya kamaki ne ko wani abu ya sameki nan. Nace mami akwai wa yanda muka kwana dasu ai koma dai menene amana kike a gareni ta fada ta juya tana fadin mamud kana da son gardama. Nikan nasa kai na shige ban daki don in fara gyara nan kafin su gama su fuce in gyara dakin ga baki daya. Har na gama da bandakin na fito suna cikin dakin basu fita ba haka yasa na koma falo na zauna har su fita . Ina nan zaune falon saiga Rufaida ta fito daga dakin da suka kwana tana ganina tace yauwa ke zo nan ki dibo muna ruwa a waje. Tashi nayi na karbi bucker din a hannun ta na nufi hanya tana fadin kiyi sauri don gaba daya dakin zaki debo muna ruwa muyi wanka. Ni dai na tafi bance komai ba na diba a mayawa na uku ne na samu masu aikin break fast suna wanke kayan miya dole na tsaya jiran su. Don gaba daya ruwan gidan ya tsaya ba,a san dalilin haka ba sai ga Rufaida ta fito tana fadi ke karamar yar iska ko ? Tun dazun ki debowa mutane ruwa kin tsaya iskanci dama ai tsiyan matsiyata ke nan basu iya samun arziki ba sai su ganshi a banza. Excuse me ya fada daga baya ta inda take tsaye da hannuwa saman west din ta sai masifa take dani ni kuma na juyo ina fadin nba tsayawa nayi ba wa yan nan na sama suna aiki wurin. Maza ki debowa mutane ruwa ko ranki ya baci shine taji ana ce mata excuse me ta dan juya don jin muryan wanda tayi a bayan ta. Da sauri ta jaye mai a hanyar da tai banga banga tana masifa dani daga saman step din. Wurin security din shi ya nufa yana saye da farar jallabiya kal mai sulbi a jikin sai kamshi ke tashi har inda muke saida kamshi yakai ga hancin mu. Jin ta gaida shi bai aksa ba ya wuce ina jin matan dake wurin na fadin wanan duk cikin diyan hjy yafisu kyau da kwarji saidai shi din miskilin karshe ne sosai. Sai lokacin na dago kai na dan saci kallon shi kafin in koma kallon Rufaida data suma a tsaye wurin da take kan kallon shi. Dauko ruwan da ta farga nayi harna zo gabanta ina jin tana sauke wani irin ajiyan zuciya na shige ta biyoni a baya. Daga ban dakin dana aje ruwan ina jin tana fadin kai yanzu naga hero a waje ashe fitan danayi bana banza bane tunda har na samu yai min magana yau. Wai me kike nufi Rufaida kin san dai alkawarin su daddy ai ko tace ina ruwana da wani alkawarin su can in dai na samu ya kyasa min. Da wanan cece kucen har na fito daga dakin suna kanyi na barsu nan dakin mami na nufa kai tsaye daga nan don in gyara. Ina shiga ranan ne karo na farko da mami tayi min fada kan aikinta don ina sallama tace zeey mena kawo kinan kiyi tun dazun kin shige ba a ganki kin san zan fita yau da wuri. Me ke damun ki yanzu ne tunda kikaje gida naga kina son ki sukurkuce min fa sai ayi ta neman ki kiyiwa mutum abu baki san kizo don kanki ba. Mami kiyi hakkuri ba wucewa nayi ba dama daga bayana naji ana fadin is OK mami tunda tazo din. Muryan ne ko mai maganan abin kallo na juya don ganin mai magana suka karaso tare da jamal, sai jamal ke fadin . Wata kila wani ne yasa ta aiki don naga tana diban ruwa a waje zuwa ciki cikin harshen turanci yake magana shidai tun maganan farko bai kara magana ba ya samu wuri ya zauna. Wa kike diban wa ruwa mami ta juyo tana tambayana tare da tsureni da idanuwan ta a kaina. Anty Rufaida ne tace in diban masu ruwan wanka dukka dakin shine na tsayayi dama na bata amsa. Wai mai Rufaida take nufi ne akan yar nan mami ta fada da hausa barta zamu hadu bari a watse gurin taron nan in mata tsiya. Kayan dake saman gadon na fara tatarawa ina nadewa na tara gefe guda sun dan dade dakin don maganace mai muhinmanci sukeyi a lokacin naga an aiki jamal mami na fadin don Allah kada ka tsaya don munyi waya dashi yanzu. Tare suka fita lokacin mami ta fara shiri tana fadin in miko mata wanan in bata wancan har ta shirya cikin wani rantsantsen lace da akai mata dinki ya sauko zuwa gwiwan ta. Ga wani sarka da na fitar a cikin wani gida mai kyau da dauka ido ta nuna min yadda zan saka mata shi. Ta tsaya a gaban mirrow dakin tana gyara kwalliyan ta da kyau da sauri na karasa gyaran dakin na share don ta fita zuwa falo. Dakin ya koma tsab na saka mai kamshi gadon yayi kamar ba a kwana saman shi ba lokacin. Gaba daya mami da yaranta har anty Aisha suka shigo dakin tare da ita sun sha ankon farar shada sai maiko jikin shadan da motsi yakeyi sun saka mami a tsakiya sai Aisha ce da wanab bakon da ban san dunan shi a baya suma magana sukeyi a cikin rada kamar Aisha zata shige mai jiki. Ganin yadda suka shigo suna magana haka yasa da sauri na zo fita sai muryan jalal ke fadin ke yarinyar hajjaju ana magana dake fa. Key ya mika mai yace ya bani shi jalal din ke min bayani wai inje in gyara mashi dakin shi yana bukatan gyara. Na rusunan na karbi key din harna juya sai kuma na juyo ina fadin ina dakin yake yaya ? Kwatance jamal ya fara min naji yaya mamud na fadin jeka nuna mata dakin mana har zan fita mami tace ki rike key din dakin nan guda tana nuna min kofa. Na tsaya na cire na tafi yana waje yana jirana har muka nufi wani part ya nuna min da hannu. Daga kofan shiga part din na hango wasu irin zaratan maza kartai dasu su shida kowa ya saka bakaken kaya a jikin shi. Tsoron sune ya kamani da fargaba na nufi wurin na gaidasu na sa key ina bude kofan kafin in tura da sallama in shiga. Bin ko ina na falon da nagani nayi da kallo komai yana a tsare ga wani kamshi yana tashi a dakin ta ko ina kada in tsaya kallo wani ya sameni haka yasa nasa kai zuwa kuryan dakin . Nan ma nasha kallon saidai ban yarda na tsaya ba ina kallo ina abinda ya kaini dakin ko ina sako da lungun dakin saida na sharo shi tasa na goge kafin in fito sha daya saura. Tun tun karowana part din da muka sauka naji gidan yai min tsit babu hayaniya har haraban wajen gidan babu wani motsi sosai kamar yadda na barshi . Babu kowa a part din sai motsin masu aiki da nake ji a kitchen din gidan tsayawa nayi ina tunanen sun tafi ke nan inda zasu ashe ? Ke nan na dade a dakin ina gyara ban sani ba har aka wuce akabarni sai kuma naba kaina amsa da fadin ke yar aiki wazai kaiki wurin taron manya haka. Wanka bake bukata don haka na nufi dakin mami tunda can kayana suke tunda mukazo ina shiga na rufo kofan dakin na shiga ban daki a gurguje da tsoro nayi wanka har na shirya na fito na rufe dakin. Kitchen din gidan na nufa don yunwa nakeji lokacin sosai gaida masu aikin dana sama nayi ina tambayan abinci. Daya daga cikin su mai hausar gwarawa take fadin abinci yanzu sun cinye komai nasu sun tafi ai sai ta hada da yaren su kuma naji daya na mata yare sai matar tace in tsaya ta debo min akwai wanda suka ajewa wasu basu zo ba. Suna ta yaren su har ta hado min na karba ina godiya tare da dawowa falo na zauna naci saida na koshi na kwashi kayan na mayar kitchen din da zuman in wanke da sauri matar tace ka bari wanan zaita wanke ai. Nikan na fito na barsu don jin abinda ta fada na zauna a falon ina kallon tv dake aiki ganin yadda aka bar falin na mike na gyaro ko ina na gidan ban samu kaina ba sai daya da wani abu. Alwala nake daidai lokacin dana fara jiyo hayaniyan dawowan mutanen gidan nayi alwalana na shige ciki a falon kamar yadda nayi da asuba ko wanan ma nan na tsaya nayi. Suka fara shigowa daya bayan daya kowa a gajiye sai shigowan anty Aisha na mike da dan sakin fuska nake gashe ta. Ta amsa min tare da fadin a, a yarinyar mami yaya bakije gurin taron bako kinje banganki bane tana fadin tana magana nidai nayi murmushi kawai. Har ta danyi nisa ta juyo tana fadin zo zo zo yarinyar mami tana miko min hannu na nufi gurun ta tare muka shiga dakin bayan ta bude ta fara yarda jakkan hannun ta saman gado na dauka nakai wurin filon na aje mata shi. Taje help me to remove dis cloth don Allah tun dazun duk na gaji dasu a jikina ja min zep please ko zanji dadi haba wanan wahalan yai yawa. Naja mata zip tana ta tsuki da fada bata tsaya komai ba ta kwabe kayan ina kawar da kaina gefe ta fada ban daki tare da barin kayan a watse. Tattara kayan na farayi ina nadewa kafin ta fito wanka na gyara ko ina na fito haka yayi daidai da shigowan mami gidan yan bambadanci suna bayan ta suna fadin saike hjy maryam mace mai kamar maza mata a gidan Alh ma,azu gin sun buga sun barki Allah dai yajikan maza maza sun kwanta. Ko yanzu yasan baiyi zaben banza ba yabar baya a duniya uwar zaratan maza kece uwar gwaunan gobe kece uwar shugaban kasa, . Wata ta karbe da fadin kece uwar manyan duniya ga gobe gaba sallama baya sallama yar manyan mutane. Nikan na suma wurin kallon yadda ake masu barin kudi kamar ba neman su akeyi ba. Zama mami tayi yayin da kawayen ta suka kewayeta ta ko ina ni sai lokacin ma naga wasu da ban gansu jiya ba. Take falon ya cika da jama, a ta ko ina babu masaka tsunke a gidan wuri ya kaule da ci dasha ina labe daga kofa ina kallon ikon Allah don ni ban taba ganin bukin manya ba irin haka. Wasu nacin abincin wasu na haraman sallah wasu kuma suna mayar da magana mai rabon abinci suna rabo kungiya kungiya. Nama girman shi yakai dunkulen hannun mutum don girma duk nau,in da kake so na abunci shi za a baka a wurin. Daga inda nake rakube naji mami ta fara kiran sunana da sauri na amsa da gani mami na isa guri ina gaida ita. Gaba daya mutanen dake gurin sun zuba min idanuwan su hannu mamu ta mika min na isa wurin ta da sauri tajawoni tana rada min in shiga daki in duba cikin turamen zanin dake zube gefe a kasa in dauko guda biyar in ba matan dake mata kirari . Na amsa ina gyada kai na matsu in bar wurin daki naje na bude na dauko kayan kamar yadda taimin bayani nazo dasu falon kowa ya saka min ido. Ina takowa da zannuwan a hannu na daya daga cikin matan da akace in kawowa tana kyala ido ta fara fadin kaga inda kyau asali yake farar mace alkyaban mata. Diyar hjy takawan ki lafiya dayan tace fari kun gadane ba ku ba shagon maida baka fara kaga jinin larabawa asali irin gado bana gada ba. Yarinya sai gidan gwauna ko minister minister ma mai fada aji irin uwarki ba muna minister ba akoma gefe ba office . Dayan ta karba da fadin haka yake don yau mun sheda mun gane bambamcin ayyah da tsakuwa a bainan jama, a. Nidai har jiri nake gani don idanun da aka watso min a falon na nufesu na mika masu zan juyo mukayi arba da yan matan Rufaida da Nazifa tare da wasu mata a zaune suna magana kasa kasa sai hararana sukeyi. Na raba na koma dakin mami na gyara wurin dana dauko kayan na fito har lokacin sai kirari sukewa mami din. Ance massadan ka fadawan ka a inda na tsaya idanun su ya rufe basu san ina wurin tsaye suke gulma akan mami. Wai haka duniya yake ai gashi bai gina kowa ba sai matarshi da diyan shi kawai ya inganta rayuwan su. Har mami tana daga kai dama ba,a san asalinta bane ko yar waye yar hakimin kauye kawai da ita yanzu ta samu duniya taba ganin kamar tafi kowa. Jifa kai duniya ina zaki damu kan hassada wai kuma sun zo ne har Abuja dalilin ta don tayata murna fa kuma suka koma gefe suna gulman ta. Kafin dayan ta dago kai mu hada ido ina kallo ta zuguri dayan matar dake magana ta dago mukai arba na watsa mata wani kallo don girman ta ya gama zubewa a idona ko tunda na shedata tana zuwa wurin mami ko a kaduna. Tun yamma nake ta kallon ana shiri muna idar da sallah mami tayi kirana muka shige dakin da wasu kawayen ta biyu. Shiga ta alfarma mami tayi ina ciki sai faman miko muna wancan mayar da wanan dauko muna wancan abin ko mami ta ce zee ina abu kaza din nan ? Haka dai har mami ta shirya wai dinner za, a tafi a wani katafaren hotel nan cikin garin Abuja. Mami kan hankalin ta ya dauke bata takan kowa a gidan don uzurin gaban ta yau data zauna za a kirata gefe da magana kus kus. Har aka fara tafiya gurin dinner din ina kallo su Nazifa da Rufaida da su Rubby suka fito sai wani shakiyanci sukeyi a tsakanin su. Wanan na fadin yau kan akwai babban kamu don bazan fito ba sai na sace zukatan mutane da yawa . Wanan ta daga tayi wani juyi tana gwada tafiya har suka gama iya shegen su suka fice gidan sai wani yauki da yanga suke yi nasan harda kari don inji haushi. Saboda ina jin Nazifa na fadawa wata tsohuwa da ban santa ba a cikin dangin su tsofi da mara gata su zauna gida ba, a zuwa daku taron manya don darajan wasu baikai can ba . Tsohuwar dai tayi mata dakuwa da hannu ta fita tana dariya ajiyan zuciya na sauke bayan fitan su falon ina wasa da yan yatsuna sai ga anty salma ma sun fito da wasu yan mata guda biyu ina ganin su nace anty salma sai kun dawo don dai tace inzo mu tafi. Tunda nayi dan kwalliyana a lokacin amma sai ta daga min hannu kawai suka fita na koma na zauna ina tunanw kala kala a raina. Can an dan dade sai ga anty Aisha ta fito tana tako daya daya tana waya na dago ina fadin anty Aisha sai kun dawo . Ta juyo tare da fadin yarinyar mami baki tafi bane daga haka ta sa kai ta fice a gidan bayan fitan ta naji gaba daya zaman wurin ya isheni. Don haka na yanke shawaran fita haraban gidan in sha iska duk da darene amma wajen kamar rana don hasken da ke akwai a wurin. Wuri na samu na zauna gefen flowers ni daya sai tunane barkata da kalle kalle nakeyi kafin kamshin turaren nan da tun rana dana aiki a dakin yake a jikina badon na cire kayan na daina jin shi a yanzu ba. Ta dan nisa kadan yazo ya wuce ni zuwa wurin motar shi lokacin ne na san da mutane a wurin sai ga bodyguard din nan nasa dana gani da rana sun taso zuwa wurin shi. Kallona ya koma can na samu abin gani da zagi a raina ganin yadda suke mai kamar ba mutum ba dan uwan su. Mota ya shiga suma suka shiga dayan motan bayan sun rufe mai suka tayar da motar hasken motar su ya haskani sosai inda nake nayi saurin dukar da kaina kasa. Shiru shiru motar bata tashi ba na dago kai da zuman in kalle su sai ganin mutum nayi a gabana yana fadin cikin harshen turanci boss yace ki zo. Na nuna kaina tare da fadin ni yace eh ya juya na mike na bi bayan shi zuwa wurin motar tun kan in karaso aka bude motar ina zuwa naji ance shiga mu tafi. Murna zanyi ko mamaki duk babu daman wanan saboda tsoron daya rufeni lokaci daya banda zabi na shiga gefen da aka bude min din. Wani sanyi da rabane ga kamshi ya dakeni lokaci daya sai dana zauna nake fadi ina wuni a cikin hausa ban sani ba ko ya amsa min don an rufe kofa a lokacin. Har muka kai wuri ba wanda yai magana a motar ga wurin da gidan akwai nisa sosai a nawa ganin. Wurin ya cika da motoci da ababen hawa ga jama, a wasu a wajen wurin sai security kala kala dana gani gani da tsoron yan sanda tun a kauyen mu. Motar ta samu wuri driver ya tsaya daga inda muke muna jin magana da kidan dake tashi a cikin wurin. Duk muna a cikin motar zaune nidai na kurawa sarautan Allah ido sai can aka bude motar duk da an bude ya dan dade bai fito daga cikin motar ba. Can ya sauko katan mazan nan suka wani zo suka tsaya wurin motar wani ke fadin in fito na fito da sauri har sunyi gaba na bi bayan su. Gap da zai shiga wayab shi yai kara ya tsaya a wurin yana amsa waya haka yasa na yanke shawaran fara shiga cikin inda ake taron. Sai masu tsaron get din wurin suka hanani shiga wai sai na nuna masu pass dina wanda mutum yafi a kirga sun shiga ni ina wurin tsaye. Har sojan dake kofan yana son ture da hannu biyu kyaleta tare muka zo ya bashi amsa bamu shiga ba saida akai muna bincike. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣4️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA JUMMA, AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA SADA MU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN MAI ALBARKA UBANGIJI YA YAFE MUNA KURAKUREN MU AMIN YA ALLAHU, , , , YAR UWA LITTAFIN KUDINE DON DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BANA FITAR MAKI DA HAKKIN RASHIN SANI NA FADA MAKI ALLAH YASA MU DACE AMIN, , , , , DARI UKU NE KUDIN SHI DON SHIGA GROUP ZAKI IYA TURA WA TA WANAN ACC 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN NA DARI UKU KACAL, , , , , Ina tsaye duk na kagu in shiga inga abinda ake a cikin dakin taron da nake ganin mutane kala kala suna shiga wasu ma ba mudulmai bane daga cikinsu.. Nayi kamar zan bi wani tawagan yan mata da naga zasu shiga sai sojan dake kofa ya kalleni yai warning dina da bulalan hannun shi . Dole naja baya na tsaya ina mazurai da idanuwa tare da dan bin ko ina da kallon mamaki a wurin don gaskiya ban taba zuwa irin wurin nan . Sojojin kofan na naganin shi ya gama waya bodyguard din shin sun sashi tsakiya suka fara jayewa a hanya suna girmama shi. Hannu ya daga masu yana kokati shiga nayi saurin shiga cikin su da saurina don kada su barni gurin ban san yaya zanyi ba gashi tunda nazo banga wani wanda na sani ba a wurin. Sojan ne yayi azaman riko ni sai ya juyo a hankali kamar mai rowan magana yace don't sojan yaja baya da sauri ya kame. Wani iri naji kaina ya amsa lokaci guda ganin irin taron mutanen dake wajen gasu zaune saman kujeru masu kyau kowa yayi kwalliya gwanin ban shawa,a. Ba zan iya sheda kowa a wurin ba idan ba karya zanyi ba saima ince kowa ya zubu muna idanune shigowan mu ashe ban sani ba mai magana ke sanar da shigowan dan mami dana biyo tawagan su. Biye nake dasu a baya kamar jela har aka nuna mashi wurin zama wani table babba yasha kayan ado dana ciye ciye saman shi. Da idanu yai nune sai wani ke ce min in zauna wai na dan kai zaune a hankali kamar yadda kowa ya zauna kaina na sade kasa. Ba mami ba duk wanda ke dakin taron hankalin shi ya dawo garemu ne ance yaro da kudi abokin manya. Wai ashe da Done nake zaune ban sani ba a wurin sai mamakin koni wacece wanda basu sanni ba suke yi. Wa yanda suka sanni kuma suna mamakine meye hadina dashi muka shigo tare ni yar aikin gida abinda ko yan gida basu samu gatan hakan ba sai karamar yar aiki kamana. Anci gaba da gudunar da shagalin da ake inda mawakan hausa dana sauran yare suke nuna bajintan su a wurin. Ga masu rabon gifts suna faman rabawa table table don komai a wurin a tsare ake yin shi tun ina kallo har gajiya ya fara kamani don zaman kurame muke a table din mu. Dan gara su dan motsi kadan zaiyi sai kaga daya daga cikin bodyguard din nan sun duka suna magana dashi a kunne. Har lokacin da muka tashi sai dai mutane suzo su gaisa dashi su wuce yana zaune bai daga ba sai da zasu tafi ne dayan ke min magana kamar rada yana fadin in tashi mu tafi. Haka na taso shike gaba sai ni a baya bodyguard din dun samu a tsakiya kusan ince shine farkon fita wurin da gani baison hayaniya don sai faman murza goshin shi da yake yi kadan kadan zai murza goshi har yakai ga mikewa muka fita. Kamar yadda mukazo haka muka koma ba wanda yai magana a motar har muka kai gida ni ban ma sani ba saida naga mota na shiga gidan nasan mun kawo. Aka bude motar zan fita na juyo inda yake zaune kamar ba zai fita ba nace na gode yaya don ban san sunan shi ba dan mami bako nake kiran shi dashi. Ina hawa steps din ne naji muryan dayan bodyguard din shi na fadin hjy ga wanan wai ki dauka inji boss wai ashe abinda aka rabane a wurin daya yakai a mota shine yanzu suka ban. Haka na shiga da jakkan niki niki don gifts din manya daban aka bada su ba irin wanda aka rabawa kowa bane wurin. Daki mami nakai jakkar har biyu mai kama data matafiya shake da kayan da ban san ko meye a ciki ba na aje. Hayaniya ne ya fara karde gidan lokacin har barci ya soma daukana don ban dauki hakan a komai a raina ni dai nasan ya taimaka min saboda halin kirki irin na uwarsa ya kaini naga buki haka na aje kawai a raina. Sabanin sauran jama,an wurin dake tunane kala kala yadda aka ganni dasu kowa da irin nashi fassaran a ran shi. Nikan ganin mami bata shigo ba yasa na kwanta kasa nayi filo da jakkunan kayan da nashigo dasu har barci ya daukeni hakana ban sanni ba a wurin. Ko da mami ta dawo ta samu ina barci a dakin ta a kasa na dunkule a wuri daya kallon tausayi tayi min yadda na kwanta a maraice a kasa. Sai taji komai da take son tambayana data dawo ya kawu a zuciyar ta bata tayar dani ba sai dai can hayaniyar suce ta tayar dani daga barcin. Da sauri na mike ina fadin mami sannuku da dawowa maki ina murzan ido . Sai mami ta juyo tana fadin tashi kikayi kuma koma ki kwanta nima a gajiye nake ai yanzu sallah zanyi in kwanta. Mami me zan maki yanzu na tambaya ta juyo tana fadin bakiji mena fada ba ki koma ki kwanta abin ki dare yayi yanzu sosai. Washe gari da safe na tashi kowa nata sallahfita nayi waje ca wurin famfo wajr inda na saba yin alwala nayi na dawo falo nayi sallah. Na dan zauna don jiran mami ta idar kafin in kwatanta in tashi zuwa dakin tana zaune suna magana dasu anty safiya da anty sa,a da wata mata. Gaidasu nayi na mike na shiga bandaki na fara wankewa kagin in hadawa mami ruwan zafi na fito yanzu sun karu a dakin yasa na fita na barsu a ciki na dawo falo saman kujera na takure a wuri daya . A yadda na lura wasu daga cikin bakin suna shirin komawane a ranan garuruwan da suka fito dan yiwa mami kara sai yanzu nasan mami mutumiyar mutane ne sosai. Yauwa zonan yar iska manya kawai mai mugun nufi dama nasan ba banza kika bar mami ba shegiya. Na dago kai ina duban dawa anty Rufaida ke wanan magana haka na fara waige waige ina duba sai naga tana nufo inda nake tana fadin . Bada ke nake ba kin tsaya kina kallon mutane yar iska nuna kaina nayi da hannu cikin mamaki ina fadin ban san dani kike ba ai anty na mike tsaye. Juyawa tayi haka yasa ba gane nufin ta nace anty mami zata nemeni yanzu don tace in bar nisa da ita jiya da kika sani diban ruwa tayi min fada. Ke ni kike fadawa wani mami tace kibar nisa da ita kizo dakin mu yanzu ina jiran ki idan baki zoba kuma kin san sauran. Juyawa nayi na kalli dakin mami kamar zanyi magana sai kuma na bi bayan Rufaida din zuwa dakin su. Ina shiga takai min mangara a kai da niyar kaimin mari saina dafe ta samu kaina kallon mamaki nake mata don ban san abinda nayi mata ba haka ? Ke yar iska yaya akayi kibi hero zuwa gurin jiya wai tana zare min idanuwanta waje tana son jin amsa daga bakina. Shiru nayi don bansan abinda take magana a kaiba lokacin ra kara maimaita tambayan ta nayi shiru Nazira tace idan ma ke manyace kici kanki kisha bakin ruwa don bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane. Sai wace akecewa rubby tace wanan ai na fada maku snake ce a ciki ku ga kyau ga daukan hankali ga duk wanda yasan abinda ake kira da matar manya. Don Allah rubby ki daina wanan maganan haka karta dauka ita din wata tsiyane can ta ban amsa kawai don jiya shegiya ta hanani barci da dadi duk na rufe ido yar iska nake gani a cikin su. Turo kofan da akayine ya dauki hankalin kowa a dakin ba kowa bane sai anty zulfa yar gurin kanin mahaifin su Rufaida tana fadin ke kina nan ga mami can na kira ki. Ban tsaya jin komai ba na mike na bar dakin da ssuri na nufi dakin mami na dauka zatayi min fadan haka sai naga sabanin hakan tana fadi yauwa zainab don Allah zauna ki hada min wanan kayan kafin in fito wanka zan tafi dasune in sallami mutanen yola don karfe tara jirgin su zai tashi. Na amsa da to mami tana fadin ki saka komai daya daya a cikin ko wani jakka tana fadin haka ta shige ban dakin. Zama nayi na saka kayan kamar yadda mami ta umurce ni inyi mata tana fitowa ta zauna shafan mai tana umartana dana bude jakkunan ta gani. Har ta gama shiri a gurguje tana fadin in kwasa zuwa cikin motar ta dake wajen gidan fake na na aje sai ga driver yazo yana fadin za a saka a cikin motar ne nace eh mami tace in kawo nan zata fito yanzu. Sai gata mun hangota suna tafe suna magana ta kawo inda nake tsaye take fadin idan kin gyara dakin zeey ki mayar min da sadkokin ida muka dauko su jiya. Sai kin dawo mami na bata amsa ina juyawa zusa cikin gidan kai tsaye dakin na shiga na samu mami ta barshi a bude. Gyara komai nayi tsab na shiga ban dakin a gurguje don nayi wanka sai dai kuma har lokacin ina tunanen abinda su Rufaida sukai min wanda bansan akan me suke magana ba akai. Mami ta dawo bayan bakin nata sun tafi nan kuma ta shiga sallaman masu tafiya a mota don komawa kaduna. Suma tana daki tare da su anty safiya da kannenta biyu suna kasafa abinda ake bawa masu tafiya. Zuwa karfe biyu gida ya koma sai mu kadai a cikin sa sai kuma kannen mami da basu tafi ba suna daki da anty salma wace sai yanzun na fahinci akwai mahaifiyarta a cikin su ashe don basu da kama sosai da uwar da mutum zaiyi saurin gane hakan. Mami ta tashi don yin sallah azahar saboda dan barcin daya dauketa a lokacin don gajiyan dake jikinta. Nima na danyi barci bayan gyara falon gidan danayi duk da girman falon amma hakan bai dameni ba na tsaya na gyara shi fes. Ina zaune ni kadai a katon falin sai tv dake aiki jefi jefi nake dan mayar da hankali wurin kallon abinda akeyi a ciki. Eyyeh zama ma kikayi saman kujara ke nan ke gaki mara ta ido ko a gidan ku akwai irin sane halan da zaki zaunawa mutane harda dora kafa sama. Ina sauke kafan naji muryan Anty Aisha na fadin me kuma tayi yanzu dan ta zauna kawai a kasa kike son ta zauna ke nan . Aisha baki san wanan munafukar yarinyar bane wallahi sai ta dinga yin abu simi simi kamar wata ta Allah can da ita nan ko munafukace ta gaske. Ku daina yin hakan mana yarinyar nan bata da wani aibun da za,ace kuna mata haka ai tana fitowa daga daki dauke da chip's tana ci a hankali ta nufo wurin mu. Wai kin san wanan bata aje kanta a kusa ba jifa jiya harda mannewa yaya J zuwa wuri dinner. Kin san yan kauyen nan da bakin shishigin tsiya ko ya akayi ma tabi bayan shi ko tsoro babu. Wanan she most go back to her village kafin rigiman ta ya fi nan don wallahi ni gaba daya nama tsaneta kwata kawata wallahi. Haba haba Aisha tace cikin muryan ta na sanyi irin nasu meye a cikin har kina fadin kin tsaneta haka yarinyar nan she is good and beside mami tana jin dadin zama da ita sosai so kima bar wanan magana kada ku hadu da mami. Ta mike tana fadin ashe na kusa barin gidan nan don ba zan iya zama da wanan yar iskan ba da take neman nuna ita watace a gidan nan. Har abi yakai can haba bai kamata ba kina fadin haka kan zainab don ba ruwan mu da ita don Allah kada hakan ya jawo wani matsala mai girma. Ina laifin wanan yarinyar a nan itace fa dazun ta gyara falon nan haka muna sharan barci a daki ita bata huta ba. Tace a fusace ni dai bana son ganin ta gidan nan ne tare damu I just hate d girl wallahi. Aisha tayi murmushi tare da daukan chip's din ta tasa a baki kafin tace ni banga wani aibunta ba wallahi. A gadarance tace tana wa mutane shishigi da yawa a gidan nan ko don tana ganin mami na kama matane oho ? Ru,faiidaaahta fada a wani irin yanayi kamar mai warning din ta sai kuma taci gaba da cin abinda ke hannun ta ba tare data furta komai ba kuma . Juyawa Rufaida tayi a fusace tabar falon ta bita da kallo tana girgiza kai kafin ta dago ta dubeni inda nake tsaye a rakube tace zauna. Ba bata lokaci nayi kokarin zama kasa don warning din da rufaida tayi min dazun kan kujeran da har ta zagi gidan mu. A, a kasa zaki zauna zauna a nan tana nuna min gefen da take zaune na girgiza kai tare da fadin akan hawa kujera yanzu anty Rufaida ta zageni. To ai yanzu ni nace ki zauna ko ta fada cikin rashin damuwa sai dana danyi jimm kafin in zauna a saman dayan kujaran a takure daga bakin kujeran don ban yarda na zauna ciki sosai ba kada kuma a kara zagan min iyayyena wanan karon. Kaina a kasa sai wasa nake da yan yatsun hannuna jin ta kira sunana yasani dago kai na dan kalleta kadan tare da kara sunkuyar da kaina a kasa. Sai naji ta dan sake murmushi tare da fadin feel free with me zee I am not like Rufaida OK. Na kula baki da walwala a gidan nan ko yaushe kamar a takure kike ina son sanin damuwan ki idan ba matsala. Jin tayi shiru yasa na dago kai na dan dubeta kadan ni take kallo a lokacin ganin na kalleta ta dan daga min kai tare da fadin ke nake saurare zainab. Ta sake fadin tell me meye matsalan ki ne meke damuwan ki ko yaushe kike a takure ? Ina son sanin menene sirin kin san ABU A CIKIN DUHU SIRINE, jin haka yasa na dago kai na dan kalle ta tare da fadin sirin me kuma Anty Aisha ? Sirin rashin jittuwan ki dasu mana nake son sani sai da dalilin ai hakan ke faruwa. Da kyat na bude bakina na nace banda matsala a komai sai dai su anty Rufaidane suke yawan takura min har tana zagina da iyayyana don kawai taga nazo yin aiki a gidan su. Zagi kuma zee koda yake koni yanzu naji yadda kukayi ko dukan ki zata iya ai a yadda ta nuna din . To wai me ya kawo hakan a tsakanin ku ne don na kula tunda na dawo hutu da abubuwan dake faruwa a gidan nan. Ko kina tunanen wani abune ya jawo hakan ke a tunanen ki zainab don naga dai ba shiga harkan su kikeyi ba ke a gidan nan. Idona ya kawo kwalla nace sai nake gani kamar don irin yadda mami take min ne sukewa haushin hakan don mami bata daukeni yar aiki ba kamar yarta ta daukeni ta jini. Sai suke ganin kamar ban cancanci hakan ba tunda nidin ba jinin ku bane da mami zata sakani a jikin ta. Umm, umm inda wanan da wanan gaskiya amma hakan ai ba zai jawo wanan tsanar haka ba a tsakanin ku tunda mami bata ragesu da komai ba su din ma tana nuna ita ta haifemu ga baki daya ai ga nawa ganin. Anyway koma dai meye ki kara nisa dasu duk da nasan kina hakan zangan su inyi warning din su ba tare da zancen yakai kunnen mami ba. Nagode Anty Aisha nace a sanyaye koba komai ta nuna min kaunarta a gareni ai tunda na samu kula a wurinta. Muryan tane ya katseni tana fadin ke din ce zeey da shegen kyau wallahi kila hakan sukewa kyashi kin san mu mata ai yadda muke. Nima kaina shigarki ta jiya saida naji kamar karna baki kayan nan don ban dauka haka suke da kyau ba. Saida nagan ki dashi a jiki nasan yadda sukewa mutum kyau ashe idan ya sakasu don jiyan nan gaskiya kin dauki hankalin mutane da yawa gaki kuma tare da big boss da yan mata da yawa a wurin suke son kasancewa tare dashi. Sai kawai aka ganki dashi by surprice kin ba kowa mamaki a wurin sosai don ba wanda ya zata hero zai tsaya duban wata mace ko wacece . Saidai bamu san sirin ba don abin ya bawa kowa dai mamaki gaskiya har mami kanta tayi maganan haka. Tausayina yaji shine kawai anty Aisha kin san irin ku irun tausayin na kasa dasune . Kafin tayi magana wayan ta yai kara ta dauka sai naji tana fadin gamu a falo tare da ita yasa nayi saurin dagowa ina duban ta. Kije mami na neman ki a daki ina jin haka na mike da sauri zuwa amsa kiran mami din yayin da Anty Aisha ta bini da kallo har na shige dan lungun da zai sada mutum da dakununin gidan. Zaune na samu mami tana duban wayan ta, na shigo da sallama ta dago tana fadin duba min ko masu girki sun gama a kawo min nan don bazan fita dakin nan yanzu ba hutu nake so yau. Da sauri na tashi zuwa kitchen din inda na samu anty Aisha tabar falin ita ma na shiga kitchen na fadawa madu aikin sakon mami din. Nan danan suka shiga hada hadan hada nata abincin cikin wani katon try na dauko na kawo mata . A dakin na samu anty Aisha tare da uwar suna magana shigowana sai sukai shiru mami na kula da tana bina da kallo kafin nace ga abinci mami. Yau ajeshi nan don har ruwa da drinks sun saka a ciki na juya zan fita take fadin zo nan zeey na dawo da sauri zuwa gareta. Nakai kasa take fadin yau zeey yaya akayi na ganki tare da jafar jiya a gurin buki ? Da sauri na dago kai ina fadin Jafar mami a, a bani bace nikan da yayan nan da yazo na tafi koshi an barni ni kadai a gida sai tsofi na fita waje na zauna shine da zasu wuce yace inzo mu tafi shine na bishi mami. Ok mami tace yayin da take saukowa saman gadon don wani lokaci mami a kasa take zama taci abincinta. Saida na tsaya na zuba mata ta fara ci tana fadin oya dauki wanan sauran kije kici don nasan bakico komai ba yanzu haka. Na dauka tare da fadin na gode mami na fita da ture din a hannu na ina murna zan sha ferfesun kai yau har in bari duk da ina ci sai dai diban tsoro nakanyi wa abinci wanan kuma an bani shine kai tsaye. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣5️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA IDAN NACE NA KUDINE INA NUFIN IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI KO ? Ranan nasha dadi don a dan lungun shiga dakin mami na zauna a kasa na kwashi garabasa na a wurin ina tsotson kanshi ne su yaya mamud suka shigo zasu shiga dakin mahaifiyar su su uku babu jamal a cikin su. Kunya ne ya kamani yadda suka sameni ina gwigwiyan kashin kafan saniya ina kuma tsotson ruwan miyan da ya lake a cikin sa don dadi. See dis village girl jalal ke fadi dubeki don Allah a kasa kika wani zauna kamar wata kazama can. Dan kallona yaya mamud yayi ya kawar da kanshi gefe daya yana fadin wai a ina mami ta samo wanan yarinyar ne ? Haka yayi daidai da shigar su dakin mami din inda direct wurin da mami ke zaune a kasa Jafar ya nufa ya zauna a kasa tare da karban cibi a hannun mami din. Kallo shi mami tayi kafi ta mayar da kallon ta ga mamud tana fadin me naji kana tambayane ? Sai jalal din yace dis your village girl mami kinga yadda tawani zauna a kasa tana cin abinci kamar wani zai daka mata tsawa ta sheka a wurin. Ina ruwan ka da ita mami tace tana kawar dakai zuwa kallon Jafar da yakai ruwan miya a bakin shi ya fara taunawa da kyat kamar an sashi ci dole. Yanzu haka nasan baka karya ba tun safe maimakon yai magana sai cikin shi ya shafa yana lumshe idanuwan shi a hankali. Yaya jalal zainab tana da gaskiyan ta ta fita falo kuma a zageta shiyasa ta labe nan nasan tana ci hankali kwance. Waye zai zage ta mami ta fada a hasale ciki ko in kulla kai tsaye tace your daughters don dazun nan na raba ta da Rufaida a falon . Wai kawai ta zauna a kan kujera in kaga yadda Rufaida kewa yarinyar nan abin ba kyau wallahi . Shine na zauna da zeey din ina tambayanta take fasin bata san abinda tayi masu ba suka tsane ta ita zagin ne ke ci mata rai dasu ai sosai. Wanan Rufaidan badon mahaifinta ba da nake jin nauyin shi a yanzu wallahi akan yarinyar na dana mata tsiya sosai a gidan nan ko ta koma gidan su. Mami akan wanan yarunyar har kike fadin haka yarinyar fa ba yar kowa bace balle har ki fadi haka nasan shi, , , , Karbi nan jalal mami ta jefa mai dakuwa da hannun ta tana fadin uwarka ma kaji ance ba yar kuwa bace face dagacin kauye. A haka kuma mahaifin ku ya aureni har muka haife ku ka san mai Allah zai mayar da ita gobe ita kanta Rufaida data sani da batai mata hakan ba don Allah yasan goben ta. Yaya mamud yace ni ban ma san yarinyar ba shine yanzu nake tambaya ko wacece ita ina dai yawan ganin ta gidan nan all d time idan na shigo. Ina zaka sani tunda ba a gida kake zaune ba itace yanzu mai koyawa diyan ka karatu a gida . Yace so tasan abu ke nan sosai ma mami ta fada tana budan baki ta karbi abincin da jafar ya debo ya bata. Ni dai bana son takurawan da su rufaida ke mata Allah mami yarinyar tana cikin damuwa haka sosai wallahi. Ido ya runtse kafun ya bude ya juyo yana fadin you are too talkative now kin fadi wanan maganan tun farko yake cewa Aisha. No mami ta tsawata masu su daina muzanta ta don yarinyar she is beautiful sosai sai dai tsiyar abin yar tallakawace ita. Mamud ya fada yana gyara zaman shi oh shi tallaka ba mutum bane ko don kawai tana tallaka sai akace a muzantata. Is OK mami ku bar zancen nan don Allah ya fada rai bace yana kai mata cibin abinci a bakin ta ta karba. Sai mamud ya kwashe da dariya yace mami ba fa nufina ke nan ba kin sani so iam sorry for dat ta dago tana hararan shi kawai. Hummm hummm in dai a kan wanan maganan ne mami zatayi fada da kowa ai a gidan nan na rasa me wanan yarinyar tazowa mami dashi haka. Anyway naji suna fadan wai sun asirce mami ne ita da , , , , Jalal getout bana son yawan zuba haka tin dazun nayi warning kan zancen nan kun kama magana kan abu daya haka. Yana gamawa ya mike tsaye zai bar dakin mami tace ina kuma zaka zansa a kawo maku abinci kunci yanzu a gabana. But mami , , , shiru yayi don hannun data daga alaman yai mata shiru dole ya dawo ya zauna waya ta daga ta kira wani layi tare da bayanin abinda za ai mata. Kafin wani lokaci an hada dining din tashi sukayi tana gaba suna biye a bayan ta a falon dai nake sai dai ba a zaune ba ina gutfane raben jikina na saman kujera hankalina yana gun kallon tv dake aiki tun safe a falon gashi ban iya canza chenal din ba, don haka nake kallon dole hakana. Zeey kina nan kina kallo mami ta fada saina dago da sauri don jin muryan ta danayi ina fadi cikin fara, a sannu da fitowa mami. Namike tsaye tace no koma abinki ki zauna don me baki zauna da kyau ba ta fada kamar bata san abinda ya faru ba tsakanina da Rufaida da rana ba. Dan murmushi nayi ta nuna min kujeran tana fadin zauna sama daga yau duk abinda kike son yi a gidan nan kiyi shi kamar kowa kinji abinda na fada ko ? Na gyada kai ina kaiwa zaune Nazifa dake fitowa daga kitchen a gaban ta mami ke min fada ta juya zuwa dakin su nasan zata fada masu abinda mami ta fada min ne yanzu. Mami basu bar wajen ba sai da magariba ya kawo jiki suka mike don zuwa sallah lokacin har na fita naje waje don yin alwalani. A wajen suka sameni sai dai ban samu gaidasu ba suma ba wanda ya kula dani kuma sun ganni din wurin ina alwalan. Na dawo na samu mami ta shige dakin ta nan falo na tayar da sallah sai da na idarne Rufaida ta fito tazo ta tsaya a kaina tana fadin. Sai kin bar gidan nan munafukar yarinya kawai don nayi maki fada kan hawa kujera dazun shine kika fadawa mami ko ? Da sauri na dago kai tare da fadin wani bamuyi wanan zancen da mami bani . Rufamin bakin nan naki mai warin tsiya zaki cikani da surutun tsiya to bari kiji tunda nan ba gidan ubanki bane sai kin barshi walla, , , , Ke menene haka me tayi maki keki zaginta haka kawai don cin zalin zaki saka yarinyar mutane da zaki haka. Yaya mamud ne tsaye daga bayan mu yake fada da Rufaida ta dan tabe baki tana fadin wallahi yaya yariny sai yace wanan ba daidai bane ya juya ya nufi dakin mami rai bace. Yana shiga yake fadin mami gaskiyan Aisha yaran nan sun matsawa yarinyar nan haka ashe yanzu na same su a falo rufaida na shirin dukan ta badan Allah ya kawoni ba data kai ga dukan nata ma kila. Innalillahi me yaran nan suke nufi newai kan yarunyar nan a to mami indai zamanta nan tare dasu zai zama matsala gara dai ki sallameta yace tare da mika mata ledan maganin daya sayo mata. Ranan ma a dakin mami na jena kwanta a kasa kamar yadda na kwana a jiya a takure don gani nake idan nayi dogon motsi zan dameta a dakin ta. Washe gari tunda na tashi nake jin kamar zazzabi a jikina hakana na daure nayi duk wani aikin da zanwa mami nayi shi cikin daurewa. Inda Allah ya taimakeni mami ta fita tun goma na safe na samu na shige dakinta na kwanta ba tare da nasha magani ba. Har lokacin da mami ta dawo daga unguwa data fita ta zauna falo bataji motsina ba kota ganni da ido sai tambayan mutane take suna fadin suma tun safe basu ga giccina ba. Aka kama fadin ina na shiga hankalin mami ya tashi ranta kuma ya baci dani sosai kan hakan don dai tasan ban san kowa ba a garin. Saida mami ta shigo dakine ta ganni a kwance na dunkule cikin hijjabina ina rawan sanyi. Ja tayi ta tsaya da mamaki tana fadin ke zeey lafiya ko kin shige daki kin kwanta kin tayarwa mutane da hankali. Jin muryan mami sama sama a kaina yasani bude ido da kyar na buda baki jikina na rawa zazzabi mai karfi nake fadin massarara nake ji mami tunda na tashi da safe. Jin haka yasa ta karaso inda nake kwance tana fadin saiki shige daki ba tare da kin fadawa kowa ba ki rufe kanki a ciki don rashin wayau ko me ? Da kin fada da an samu wanda ya baki magani ko a kaiki asibiti kinzo kin shige hijjab kina rawan sanyi haka kinki jan bargo saman gado ki rufe jikin ki dashi. Tana wanan fadan takai hannun ta a jikina tana tabawa taji zafi radau da sauri naga ta juya ta fita dakin. Sai gasu da jamal da Jafar sun shigo dakin da saurin su jamal ne ya kai hannun shi saman goshina yaji zafin da jikina yayi da sauri ya cire hannun shi yana fadin mami dis is serious fa jikin yayi zafi sosai. A hankali yaya jafar ya tako zuwa inda nake kwance saman rough shima ya taba jikin nawa wani irin shock ne ya ratsa jikina lokaci guda duk da yanayin zazzabin da nake ciki haka bai hanajin wani yanayi da ban san na meye ba lokacin. Idona na runtse daga inda nake kwance nunfashina har yana sarkewa yayin dashi har lokacin yana duke a kaina ya dago yana fadin les take her to the hospital dis is serious mom. Mamice ta dagani daga kwancen da nake sai na kasa tsayi tsaye da kyau jamal kamata da kyau a kaita wurin mota mami tace. No barta a kira wasu daga cikin yaran nan su taimaka su riketa zuwa motan ya fada yana juyawa ya fita daga dakin. Fita yayi ya tsaya yana fadin matar dayaga tana falo ta kira masa sisters din shi dakin su don baisan dakin da suke bama. Sai gasu sun zo suka same shi tsaye inda kowa sai mamakin kiranda yake masu sukeyi don da farko da matar tace shine basu yarda ba saida suka fito suka same shi a tsaye yana jiran su din. Bai tsaya kallon su ba ganin sun fito ya juya yana fadin help dis girl please kallon juna sukayi don basu gane wace yarinya yake magana a kanta ba lokacin. Ganin ya nufi dakin mami suka bi bayan shi sai ga mami ta fito tana ganin su tare dashi tace yawa don Allah wata ta taimakawa zainab zuwa wurin mota mu kaita asibiti. Jin an ambaci sunana yasa Nazira ta fara ja da baya Rufaida ko ko motsi batayi ba a inda take sai salma ne tace mami bata da lafiyane dama. Wallahi salma ki san yarinyar nan bata da hankali bata jin dadin jikinta ta shige daki ta kulle kanta a ciki haka. Salma ta matso tana dafani tare da fadin sannu zainab tana kokarin tayar dani zaune. Haka ta dan rikeni har zuwa wurin mota data ganshi tsaye shida jamal an bude kofar motar. Mamine tacewa salma shiga salma muje tare don Allah da sauri tace to mami ko mami ta dauka driver ne zai jamu sai ji tayi yace jamal shiga muje tare. Turkish hospital ya nufa damu da kwantace har ya gane wurin munyi sa, a akwai likitoci bamu dade ba muka shiga bayan yankar katin da jamal yayi baisan sunan baba na ba dole sunan mahaifin su yasa a katin don sauri. Tare da mami muka shiga ganin likitan ya dubani bayan yan tambayoyin da nake amsawa da kyat gareshi. Allura da maganguna aka ban sunso wai su dan kwantar dani mami tace aimin dai allura mu koma gida washe gari sai indawo in karbi sauran allura. Haka muka juyo muka dawo gida zuwa lokacin har na fara dan jin saukin jikina haka muka shigo gidan a falo muka samu wa yanda suke gidan a lokacin. Da ganin su akwai maganan da sukeyi a lokacin don yadda suke gaida mami da dawowa ba wanda ya tambayi yaya jikina daga cikin su. Dakin mami ta kaini ina jin anty salma na fadin ku baku iya gaida mara lafiya bane ? Ta fada tana shigewa dakin ta suka bita da fadin Amebo Olopopo suna hararan inda tabi zuwa dakin Nazifa tace waya sani. Ko taje ta daukowa mutane ciki ne a gida Rufaida tace ko cikin wa yan nan katan na waje wani ya taushe yar iska yafi karfin ta ba. No ku daina fadin haka don Allah Ruby dataki bin iyayyenta su tafi ta fada tace kun san fa wanan zargin abu mai girma idan kun zargeta da aikata zina alhalin batayi ba Allah na iya jarabtan ku kan hakan. Kawai dai mu barta da samun wuri don samun wuri kan yarinyar nan ta same shi har ta batun zarta mu a yanzu. Ku diba yadda guy din na ya fito a gigice dazun yana neman wai wanda zai taimaka ya kaita wurin mota. Kyale dan rainin wayon banza kawai yana wani abu kamar bakin baturen dake jin warin mutane nina rasa me wanan yarinyar tayi haka gaba dayan su suke ji da ita a gidan nan haka Nazifa ta fada tana jan tsuki a karshe. Ya kamata dai mu san mafita don wallahi garin kallon wuta kada kwado ya fada ciki muna nan zaune tazo ta samemu har tafimu kima a wurin su . To yanzu meye abinyi kawai Rufaida ta fada a cikin damuwa sai Ruby tace a abinyi shine mu san mafita . Don wata kila ladabin ta garesu ne yake ja mata kauna a wurin su kin san su don son girma kamar gyabo ai. Kai ba wanan bane gaskiya Rufaida tace ni kawai nasan shegiya asiri taje gida aka kara bankadawa mami dasu gaba dayan su. Ki duba ko jalal da jamal da muke zama tare duk a yanzu sun bari wallahi ke ni na tsani wanan yarinyar gaba daya sai na halakata ko inyi sanadin barinta gidan barni da yar iska kawai nasan abinda zan mata ai. Daga dakin shi inda yake zaune yake kallon su shida jamal da shi kanshi baisan gidan akwai cctv ba sai yau ya girgiza kai tare da fadin wasu irin yara mami ta aje haka a gida. Yaran nan ko mami ba zasu barta ba idan sun samu wuri ya fada yana mikewa zai shige daki sai kuma ya juyo yana fadin . Kada inji zancen tv din nan a bakin wani a gidan nan ko mami kafadawa dashi zamu samu matsala sosai dakai a rayuwan mu. Na dade ina zargin yara nan ba zaman banza sukeyi tare da mami ba tunda naji suna gidan nan zaune yanzu. Hannu jamal ya daga duka biyu yana fadin believe me yaya kowa ba zan fadawa wana magana ba ko jalal ne yace is better for you don ban son yawan magana. Nikan barci nayi sosai a dakin mami na samu gadon mami na haye ka laushi kamshi da sanyi na tashi yana shiga min hanci a hankali. Duk da halin rashi lafiyan da nake ciki bai hanani jin dadin kamahin dake shiga min hanci ba lokacin. Sai goma da rabi na dare na falka koshi mami ce da Aisha a dakin suke magana yasani bude idona sannu zee mami ta fada tana kallona tare da tambayana jikina. Me zakici yanzu Aisha ta tambaya tana kishingide saman gadon mamanta da waya a hannunta tana kallo. Mami ta kura mi ido tana so jin amsa da za bayar a hankali hannna ina share wayen dake kokarin zubo min a idona. Tambayan ki ake ba kuka akace kiwa mutane ba a na tun safe nasa bakici komai ba a cikin ki . Na amsa cikin karfin hali da fadin tea zan sha ina kokarin mikewa tsaye ina kuma zaki Aisha ta fada zanje inyi fitsarine na bata amsa. Ina koarin nufar kofan fita daga dakin don ba daman in kewaya mami tana dakin ta don haka nake kokatin fita ba tare da nasan inda zan nufa ba a lokacin. Sosai mami da yarta suka kula dani don sun nuna damuwan su a kaina sai anty salma da itama ba laifi don tana zuwa a kai akai tana gaidani da jikin. Har naji sauki na fara fitowa falon don in bawa mami dakin da ko yaushe a dan kwana biyun nan ina kwance. Ranan dana fara fitowa falon ne naga canji sosai wurin yan matan mami wanda hakan ya bani mamaki don fuska sosai suka sakarmin harda zolaya wai an taya naki sallamawa. Ni dai nayi murmushi tunda ba saba haka nayi dasu ba dama duk da yadda nake hakana mike na yi aikin da zanyi a ranan don sai naga aikin da akeyi kamar baya fita da kyau. Aiko mami na dawowa ta hauni da fada don ta gane nice nayi aikin cewa kawai nayi naji sauki mami. Tadaiyi min fada ta fara cire kayan jikinta na fita dakin don bata wuri ta shirya a tsanake kamar yadda muka sabayi. Sai data fito falo na koma dakin na gyara tare da nade kayan data cire a jikinta na wanko har bathroom din tas. Tun ina jiran inji ance gobe ko jibi zamu tafi sai naji shiru saidai kawai ranan da muka cika sati da zuwa ranan da dare mami ke fadin su Rufaida su shirya zasu koma kaduna do hutun su ya kare . Ina gurin jin haka yasa na kallo mami don banji tayi magana ba a ciki sai naji mami na fadin ina sane dake zainab ban manta da karatun ki ba ai. Wata kila nan karatun naki zai dawo yanzu do zaman mu zaifi yawa yanzu a nan sai dai na duba naga abinda ya dace mami ta fada. Basuji dadin yadda mami ta tsara ba don ba karamin dadi duke ji ga wanan zaman namu ba don ko yaushe suna fita shoping da yawo sun samu dakewa sosai don mami bata zana gida sai yamma take dawowa gida. Dole ba don sun so ba suka fara shirin komawa kaduna salmace kawai bata nuna damuwanta a fili akan hakan ba wucewab sune yasa mami bani daki na kaina inda zan zauna kamar yadda nake da dakina a kaduna gidan ta. Haka ba karamin dadi yai min ba sosai a raina don dama a takure nake saboda zama da mami da nakeyi daki daya. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣6️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAU DA GOBE NA ALLAH NE YAN UWA MU RIKA SHUKA ALHERI DON WATA RANA A FADE MU KO BAMA KUSA, UBANGIJI ALLAH KA KARA MUNA IMANI DA DOGARO DA KAI YA ALLAH, , , IDAN NACE KI BIYA INA NUFIN NA KUDINE YAR UWA KI GUJI SHIGA HAKKIN DABA NAKI BA DON ALLAH ALLAH YASA MU DACE . DARI UKU NE KACAL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA AMINCI. Zance tafiyan su rufaida baimun dadi ba don gidan ya kara komawa silent yanzu da suka tafi ashe dan mutum ko yaya kake dashi yana da rana a gareka. Yau na kara fahintar hakan wanda dama nasan da hakan tun barina gidan da har nakan ji kewan yan gidan mu ga baki daya har Asabe da lantana. Sai gashi dan sabon da nayi da zama da ukuban su Rufaidama yanzu ina kewan hakan gareni. Sai ya kasance in zauna ni kadai ina faman tunane a guri daya idan kowa ya fita zuwa nasa tsabgan sai in rage dagani sai gwarawan yan aikin nan dake gidan. Gashi ni ban saba dasu ba don ko yaushe a cikin yare suke su yau ma kamar kullun bayan fitan mami da Aisha data wuce school na gama gyaran dakin mami na koma dakina nayi wanka. Na shirya a cikin wani bakin dogon riga da Anty Aisha ta ban zuwan mu Abuja don ganina da yan kayana kala hudu dana dauko da zamuzo kullun. Dan kalin rigan na daura a kaina mai kawai na shafa a fuskana don ni ba gwanan kwaliya bace dama haka. Duk da hakan fuskana ya dan fito fayau falo na dawo na zauna ina karyawa ina kallon tv daya zama min abokin hira yanzu. Cibi biyu na kai ga bakina na orth din da nake sha muryan Nuriya matar yaya mamud ya ziyarci kunnena don ni nikan manta da itama a gidan tunda ita bata shiga mutane kuma bata barin yayan ta suna mamuwar kowa a gidan. Fadi take ke zeey ki zo ki gyara min part dina yayi datti da yawa yau ina son a gyara min shi don Abbani yai magana kan hakan da cewa yaya mamud kamar yadda take kiran da dashi. Yau kan na turza don bansan sanda bakina ya furta anty Nuriya yanzu nake karyawa idan na gama zanzo na bata amsa. Ke yaushe har raini ya shiga tsakanin ni dake haka ta fada niko a raina nace wata sabuwa kuma waini mena tarewa mutane haka kowa yake jin haushina dan abu kadan zai zama min matsala babba ga kowa. Maza ki tashi kije kiyi abindana sakaki kafin na bata maki rai ta fada a hasale tana mai tsureni da idon warning gareni. Kokarin aje cup din dake hannuna nake naji muryan Jamal na fadin ke dauki cup din ki ki karasa karyawan ki kafun ya juya wurinta yana fadin. Baki da tausayi wallahi yarinyar nan tun safe take tsaye sai yanzu ta samu kanta take karyawa zakice ta bar karyawa tazo maki aiki. Wani juyawa tayi tana masa wani kallo tare da fadin kai kuma fa dan rainin wayau da zakazo kaja min raini a wurin yar aiki haka. Aiki na sakata a part din mu kuma dole ta tashi ta tafi yanzu don yanzu nake bukatan ai min shi. Bazata ba sai ta gama karyawa ya kara bata amsa yana kallona tare da fadin koma ki zauna nace ki karya idan kin gama sai ki tafi. Ba abun mamaki bane don ka fadi haka jamal tunda kaganta haka kana da mugun nufi a kanta kamar yadda kuka saba yi a turai ai. Sheri zaki min ya fada a hasale yana nufota ni kan hannu na dora a kai ina shirin yin ihu don yadda ya nufota sai Allah zai gyara yau a tsakanin su. No no no jamal don Allah please kada ka tabata be a man kada ka karasa wurinta please. Nan dai hayaniya ya kaure a tsakanin su ta fadi ya fadi karshe dai ta juya tana fadin ke kuma karamar yar iska kada kizo ki min abindana saki kiga abinda zan maki yau gidan nan. Ba zatazo ba din kiyi duk abinda kikai niya a kanta jalal shima ya fada a hasale ta juyo tana fadin sai ku gayawa wanda baisan abinda kukeyi da ita ba a gidan nan. Innalillahi ai bansan lokacun dana dora hannu a kai na fara rusa kuka ba karyawan da banyi ba ranan ke nan. Don sukan tana wucewa suka tafi suna fadin yau zasu gamu a gidan nan dole sai ta fada abinda take nufi ko su casa ta son ransu nan suka barni tsaye ina kukan takaicin zargin da maman su Amir da Amirah tayi min kan tagwayen mami din. Banda yadda zanyi duk da sunce kada in tafi haka na aje abin karyawa na na nufi part din anty nuriya din da zuman mata aikin data sani. Gaskiyane part din kan yayi datti kamar ba mace a cikin sa da take rayuwa ko namiji yabar gutin shi haka za a iya kiranshi da kazamin namiji. Sai kaga mace fes a waje amma kaje muhalinta sai ka raina mata wayau kan rashin gyaran wurin zaman ta. Kayan dake saman kushin na duka na fara nadewa hankalina ya dauku ga abinda nakeyi kawai ba tsamani naji saukan mari a fuskana lokaci guda. Na dago dan gani waye yai min wanan aikin na kara jin wani a tsakiyan fuskana tana fadin gobe in kara saki aiki wani dan iska a gidan nan yace kada kiyi. Ke har kin isa me kika dauki kanki banda matsiyaciya kaskantatar yar aiki kawai kina nufin ni kyauki da wani halin ki can zai rudeni ne matsiyaciya mai zubin karuwai kawai. An walla, , , , kofan da aka bankadone yasa ta kasa karasa maganan da take son furta min ta juya tana kallon wanda ke tsaye a kofan nasu. Ni dai ina tsaye har lokacin zafin marin bai gama sauka min ba sai wani dishi dishi nake gani idan nayi yunkurin bude idanuna lokaci guda. Muryan Jalal ne yake fadin idan kika kara dukan ta yau sai kin raina kanki gidan nan wallahi kinji na fada maki. Jalal ya juya gareni yana fadin ke kuma fito part din nan tun kan ranki ya kai ga baci yayin da Nuriya ke kokari daukan waya don kiran mijin ta tana durawa jalal din zagi ta uwa ta uba. Bayan mun fita part din ne ta kira mijin ta fada mai karya da gaskiya shi kuma ya hau karfe uku duk suna gida gaba dayan su don mami tace su hadu a gida. Yayin da har lokacin ina daki tundana shige ban fito ba ga fuskana gefen idanuna ya hau ya rufe sosai har bana gani dashi. Sai faman tunane nake a raina duk kokarina wajen kaskantar da kaina a garesu don gujewa faruwan irin haka . Wanda mami da yaranta a kullun suke kokarin jana a jikin su suga dai na sake a cikin su wanda ni na kasa hakan don kada in shaga irin wanan matsalan a cikin su. Ina nan a kwancen da nake ina faman tunane muryan Anty Aisha ya daki kunnena tana fadin zainab mami na kiranki a falo. Na dago dan mata sannu da dawowa tana ganin fuskana tace ke meye haka fuskanki ya sauya lokaci daya ? Cikin dakewa da karfin hali nake fadin sannu da dawowa Anty Aisha yyawa me ya sameki haka ta kara fada. Ba komai anty na fada ina kokarin tashi daga saman gadon ta juya ta fita daga dakin. Ina tafe na sa gefen gyalen dake kaina na dafe idon dashi abu ga farin mutum lokaci daya fuskan nawa gaba daya ya canza kala ga alamun hannun Nuriya radau a fuskana. Gaba dayan su sun zuba min idanuwan su a kaina har na karaso inda suke zaune na kai kasa na fara gaida mami data kura min ido kamar ta suma da mamaki. Kafin in dan dago ina kare fuskana ina gaida yayan nata zeey meye wanan ya bata maki fuska haka mami ta fada tana kallona don jin abinda zan fada. Kowa falin ni yake kallo yayin da mami ta kara maimaita maganan ta gareni kafin in magana Nuriya tace nice na mareta. Har mijin ta saida ya juya yana kallon ta don abinda ta fada lokaci guda cikin rashin damuwan da hakan. Akan me kika duketa haka Nuriya mami take tambayan ta cikin mamaki har lokacin. Don me zan sakata aiki mami take zuwa lokacin dana umurceta tazo don kawai wanan dan rainin wayau yace kada taje tana nuna jamal a hasale. Shi dagowa yayi don yin magana sai lokacin Jafar ya dakatar dashi don tun zuwana kanshi na kasa yana dakilan wayan shi cikin ko in kula da wanda ke wurin gaba dayasu. Jamal me zaka fada tunda ta riga data fadi itace tai mata hakan da bakinta yanzu ta kuma fadi dalilin yin hakan gareta. Sai akace a duketa haka ko boyace na sayo ai ba za ai mata wanan dukan ba haka balle ba boya bace karbo ta nayi hannun iyayyen ta don kawai ta taimakawa rayuwana. Ban kawo don wani aiki ko aikin wani a gudan nan sai nawa bukatan ni kadai da take min kuma tana da kokatin wurun aiwatar min da komai tun kan na fada mata abinda zatayi min. Haba wanan dukan haka ai abin yayi muni komai tayi maki ai zaki bari in dawo ki fada min sai nayi mata fadan hakan . Koni dana karbota wurin iyayyen ta aiba zan taba mata wanan duka haka ba don itama mutum ce kamar kowa a gidan nan. Ok mami ke nan dai yanzu na fahinci da sa bakin ki yaran nan sukai min rashi mutunci ke nan wanan banzan yarinyar mara mutunci da asali ta fini yanzu a gidan nan. Nuriya mind your language bakin ki yasan abinda yake fada bayan kiyiwa yarinyar nan irin haka kuma zaki kirani ki fada min karya don kawai ki hadani fada da yan uwana. Dama nasan haka zai kasance ai don wanan yarinyar ba karya su Rufaida ke fada ba ta asirce kowa a cikin ku har mami din gaba dayan ku tasa an maku asiri a kanta. Enough enough Nuriya bakin ki yasan abin fada a nan kada ki kawo muna wanan shirmen naku ba banza yaya mamud ya kara fada a hasale. Tashi tayi tana fadin aida rama mata kayi zaifi da wanan hasalan da kakeyi don kawai na mari wanan . Mami ne ta daka masu tsawa tana fadin ya isa haka ki dawo ki zauna idan ki gama fadin abinda ke ranki. Kamar ba zata zauna di ba kome ta tuna sai ta kai zaune din tana kada kafa mami ta sauke ajiyan zuciya ta fara magana. Da farko ke Nuriya a kanki zan fara don ba zan tsaya kina fada min magana cikin rashin mutunci a gaban diyana ba haka. Don dan kuka shike jawa uwar shi jifa, sai dai kinci albarkacin darajan abu biyu da kike ci gareni har kullun a wurina. Shine auren dana da kuma kasancewar ki uwar jikokina a yanzu wanan damar kike ci har kullun a wurina don ba zan so saka matar dana a gaba idan ba haka ba ke kinsan wani abin ko ance kiyi min shi ba zakiyi shi ba duk da kudin da kike takama iyayyen Sai yaya mamud ya dukar da kanshi don ya gane me mami take nufi da maganan ta saboda halin Nuriya a ku)un magana ya taso itace bata da gaskiya. Mami taci gaba da fadin saidai zanso ki gane cewa ba zan lamunci aibanta mi diya ba ko zargi su a kan zina. Mami ni kar,a laka min abinda ban fada ba fa a nan don kawai ana jin zafina kowa ya taso sai yace banyi daidai ba . Don hakane nake nisantar kowa a gidan nan hakan baiyi ba har sai wani ya takaleni kuma inyi magana ace banyi daidai ba. Yanzun wanan mara galihun tafini daraja da kima a wurin ku ake nufi tunda itace mai gaskiya ke nan don kawai taimin ba daidai ba na hukuntata. Who are Nuriya who are you by the way har kina wani fadin tayi maki laifi kin hukuntata akanahi ke kika dauketa aiki a gidan nan ko wurin ki take. Ke ba zaki iya yin aiki ba ki zauna da masu aiki kuma kin hana hakan saboda bakin kishin dake damun ki. Mikewa tayi tana fadin na hana ka dauki yar aiki mamud don ban so kai din ban yarda da kaiba da har zan dauko wata yar aikican in aje wurina. Daga yau na hana kowa saka wanan yarinyar aiki ko taba lafiyan jikinta wallahi wallahi ko yaya nake da mutum a gidan nan ranan zai hadu da fushina. Wanan yazama na farko na karshe a gidan nan da wani zai kara taba lafiyan wani zainab yace kamar kowan ku nan dan haka a bani guri ban son wani magana kuma daga yau. Tana fadin haka ta mike zuwa dakin ta a fusace yayin da nake durkushe a gefe kujera tafiyan mami Nuriya ta mike tana fadin wallahi mu zuba da kowa a gidan nan kan wanan yar iskan kowa ya tabani tabashi zanyi. Binta da kallo sukayi kafin su dawo da kallon su gareni inda nake rakube ina hawaye don tashin hankali dana gani ranan. Da hannu ya nuna min hanya na mike simi simi na basu wuri yaya mamud ne ya kawar da shirun da fadin. Ni Nuriya zata watsawa kasa a ido haka kwata kwata banji dadin zaman mu da ita kullun a cikin fitina muke. Yau ma nasan haushi fadan da nayi mata na gyaran wuri ne ta sauke akan yar mutane haka. Bai bari dan uwan ya gama zancen shi ba ya mike zuwa dakin mahaifiyar su data shige ranta a bace ya sameta dakin. Shiko yaya mamud yaci gaba da fada da matar shi ranshi a bace yake fadin. Ya mike yana fadin nasan maganin yar iska ai bazata zan mata a gidan nan sai ta gane bata da wayau. Saidaya shige jalal ke fadin kamar da gaske din zai iya hakan yanzu kila hakkuri zaije ya bata. Suma mikewa sukayi zuwa dakin mahaifiyar tasu suka samesu a nan suna wani hira da dan lelen nata a gurin. Karfe biyar na bar dakina zuwa na mami don gyarawa ita kadai na samu a dakin da sallama na shigo dakin na duka har kasa ina gaida ita kafin in dago don fara aikin dakin. Kinsha maganin dana aika akai maki dazun take tambayana nasha mami na fada ina wasa da yan yatsun hannuna a hankali. Kamar zata sake magana sai kuma tayi shiru taci gaba da duban takardan dake hannun ta ko ina na dakin saidana gyara kafin in fito dakin kusa magariba yayi nan na samu matar da aka dauka don shara tazo ta fara aikin ta . Don faruwan avi mami tasa a kawo mata yar aiki wanan mai sharan bahaushiyace ita don ina gaida ita take amsawa naji hausanta na gane ita din bahauace ba kamar matan nan biyu gwarawa masu girki bane. Tun ranan shakuwa ya shiga tsakanin mu da matar da ake kira da hannatu yar ktsinawa irin matan nan ne da suka dade da fitowa bariki don har sigari take sha a boye. Nima dai rabon in gan tane a cikinyanayin yasa na rutsa da ita can bayan daki ta labe tana shan abinta na juya da sauri zan koma naji tana fadin a cikin kokarin kashe tabar da sauri yar hjy kamar yadda take kirana dashi. Ina nan ina wanan jarabar tsiyar da muka sawa kanmu ina dai ba zaki fadawa kowa ba halin da kika sameni wanan zancen. Da sauri na girgiza kai tare da fadin indai nice babu maijin wanan a abakina insha Allahu ina kokatin wucewa don natsani warin taba a rayuwana. Duk dan dakata min inzo har lokaci bata yarda dani don ta fahinci jikina yana rawa a lokacin. Ina kallo ta ballo goro daga haban zanin ta tura baki tana taunawa ta kakabe zanin inda ta zauna a kasa tana fadin wanan abin ya zama muna jaraba a rayuwa. Kinsan a zamani mu idan budurwa takai budurwa har bata shan sigari to bata cika wayayyan mace ba ke nan. Tun wanan lokacin mula koyi wanan cacan kashi kudin don ko nairan ka ta karshe ke nan sai ka fitar kaya zakaji dadi. Ni dai a kage nake na bar wurin nake fadin dama ban ganki bane a cikin gida sai nayi tunanen ko kina nan shine na biyo ki. Yo ai ina nan kedai jarabarce ta motso min shine nazo indan rage zafi kai. A tare muka jera zuwa cikin gidan idon ta mirsisi kamar bata sha komai ba taci gaba da sha,aninta Cikin sati daya kawai mun saba da hanne wace na lakawa mama hanne nake kiranta da hakan don girmamawa . Zama da mama hanne yasani cikin farin ciki da walwala sosai don zata zauna tayi hira dani kamar sa, anta nake gun ban iya bata amsa har yakai yazu ina bata zamu zauna tana ban labari ina kwasan dariya. Da sunan kwana hudu sai gashi mun share wata a abuja lokacin ne mami ta fara shirin ziyaran kaduna. Wanda gaba dayan mune zamu tafi gidan a yadda naji suna fada mahaifiyar mami ce bata da lafiya shine za a tafi gaida ita. Shiri sosai mami keyi don zuwa gida nikan nafi kowa murnan hakan kamar ance damun isa zan tafi ancau ne ranan. Ni kan na dauka yaya Jafar ya koma inda ya fito ne ashe wai tafiya sukayi tare da su jamal sai kwatsam gasu sun dawo ana saura kwana daya mu tafi kaduna. Mama hanne kan tunda tayi arba dashi tasha jinin jikin ta a zaton ta wai yanayin sa yai kama dana yasanda tunma dataga security din shi ta kara tsurewa da al,amadin shi. Take tambayana nake fada mata dan mami ne amma ni ban san aiki da yakeyi ba, ta sake fadan mutum.haka ba yar dariyan nan ko fara,a a fuskanshi. Dariya sosai nayi har ina dukawa a inda nake zaune sai kamshin turaren shi mukaji lokaci guda. Key din shi yake miko min ba tare da yayi magana ba, amma na gane me yake nufi dakin shi yake so a gyara mai ke nan. Yana miko min ya juya ya futa a cikin wani irin tako na mazan zamani da suka suka san ta kan duniya sosai yake tafiyan. Ban tsaya jiran komai ba na mike don cika umurni duk da mami ta hana inyiwa kowa wani aiki ita da kanta takan umurceni da inje in gyara mai dakin nasa. Tura kofan nayi na shiga dakin da sallama duk da nasan ba kowa a daKin hakan bai hanani inyi sallama ba. Idonane ya fara arba da wani kwalba dake aje saman table din dakin nasa ga abin cikin sa an zuba a kofi ansha an aje rabi. Da mamaki nake kallon abin don ban taba ganin kwalban abin sha irin sa ba nidai na fara kawar da takardun dana gani a saman wani table naji an turo kofa da karfi an shigo dakin. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣7️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YA ALLAH KA GAFARATA MUNA ZUNUBBAN KABA MU IKON AIKATA ALHERI A RAYUWAN MU DUNIYA DA LAHIRA AMIN. DO MIN SAMUN LITTAFIN NAN CIKKAKE ZAKI IYA TURA DARI UKU TA WANAN ACC 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN NA DARI UKU KACAL NAGODE UBANGIJI YA HORE YA BADA IKON BIYA ALLAHUMA AMIN ALLAH, , , , Idona a kan abin ina dan juyawa a cikin kofi naji wanan tsawan daya daka min sai da hanjin cikina ya kada don tsoro lokaci guda. Allah ya gyara ban sale cup din ba ya shigo ya karbi abinsa yana mai bina da wani kallo mai kamar na tsana. Wayace ki taba min wanan ya fada rai bace kamar da gangan na taba mashi abin bashi ya turoni dakin in gyara ba. Dan marairaicewa nayi ya karbi abin shi zuwa daki sai gashi ya fito da cup din ban san inda ya juye abin ba. Fita yayi daga dakin ba tare da yayi min magana ba hakan ya bani daman yin aikin a tsanake. A gurguje na gyara komai duk da hakan dakin ya gyaru da kyau na kulle masa na fito na kai key din dakin mami. Nikan don doki har na shirya kayana tafiya kawai nake jira washe gari na zata tun safe zamu wuce sai naga sabanin hakan. Saida yamma bayan la,asar muka bargidan zuwa filin jirgin ashe da jirgi zamuyi tafiyan kuma. Karfe shidda na yamma duk muna gida a lokacin har na bude dakin mami ina gyara don tun tafiyan ta dakin a rufe yake. Sai yau da muka dawone ta miko min key na bude duk da a gyare muka barshi da zamu tafi hakan bai hana yadan yi kuraba. Na gyara har bathroom na fito zuwa dakina shima na gyaro na shiga wanka dongon riga silk mai adon kamfala ne na dauko daga cikin kayab da anty Aisha ta bani na saka. Saida nayi sallah har isha,i na fito falon don yunwa da nake ji lokacin in samu abinda zanci a cikina. Suma mutanen gidan gaba daya a falo na same su saman dining suna cin abinci mami da yaranta maza su hudu sai yan matan mami din gaba dayan su har anty Aisha. Simi simi na fito na zo diban abincin wasun su suka kuro min ido hannuna rawa na dibi abincin ina jin mami tana waya tana fadin muna kaduna yanzun haka. Insha Allahu da safe zamu shigo Igabin naji tana fadi haka yasa na san zasuyi tafiya washe gari saidai ban san ko dani bane. Diban abincin na juya zan wuce naji muryan yaya Jafar na fadin ke saida hanjin cikina ya kada don jin muryan shi saidai ban tabbatar ba ko dani yake don kaina na duke na basu baya. Na kara takawa gabana na mumunan faduwa da ban san dalilin haka ba duk lokacin danaji muryan yaya jafar din duk da ina tsron kowa a gidan saidai nashi yafi yawa a zuciyana. Ko dan ganin kowa ma yana shakarshi ne a gidan don tsare gida irin nasa . Haka naci gaba da takawa cikin karfin halin zan tafi dakina inda na saba zama inci abinci hankali kwance zuciyana cike da addua nake tafiya. Ya sake fadin come and join us ina zaki da abinci ga kowa nan a zaune hakan yasa nasan lalai dani yake magana na juyo a hankali. Yana rike da cibin abinci da yake ci a hannun shi ya rike baikai a baki ba gabana na faduwa yace. Daga yau a nan zaki rika cin abinci tare da kowa kinji abindana fada maki yana nuna min kujera da hannun shi . Kai na gyada mai, tare da nufar gurin kujeran dake saiti da inda yake zaune babu kowa saman kujeran na zauna. Idanuwan yan matan gidan duk a kaina bama su kadai ba har mami dake waya a lokacin idonta yana kaina. Ko ban daga kaiba nasan akwai idon dake kallona a lokacin don jikina ya bani hakan ba ido daya ba ba biyu ba kodana dago kai duk idanuwan su na a kaina suna kai cibin abinci a bakin su. Tundana zauna ya maida hankali gun abincin dake gaban shi hankali kwance yake kai cibi a bakin shi a hankali . Daga mami har ya matan dama su jamal suka dago ido a sukwane suna kallon shi shiko ko a jikin shi. Sai juya cibin dake hannuna nakeyi na kasa sakin jiki inci abincin yadda ya kamata a wurin. Yadda kika san guba haka nake hadiyan abincin ba wai don baya da dadi ba don hadine na musanman akayi don zuwan su yau din su mama kande suka girka abincin mai rai da lafiya. Mikewa yayi tsam mami tace har ka gama cin abincin ke nan ko rabin plate fa baka ci ba ba tare daya juyo ba yace mami iam ok zanje na kwantane. Allah tashe mu lafiya mami tace yace amin yana tafiya sai jalal yace but yaya security dinka za a fada masu sutafi ke nan tunda ka shige ko ? Na sallamesu tunda muka fito massalaci dazun idan sun gama zasu tafi ya bashi amsa yana tafiya da dan sauri kamar mai uzuri. Mami ma bata dade ba wurin ta mike tabar falon sai mazan da suma suka mike lokaci daya falin ya rage mu kaida a ciki. Duk lokacin danayi yunkurin dago ido sai in samu ana aika min da wani irin mugun kallo da tsana dan dama salma da Aisha su ba kallon tsana bane saidai kallone mai kama dana mamaki lokacin. Amma dai yarinyar nan kina da sa, a yau kece yaya hero ke ba umurnin zama a saman table kici abinci tare da kowa a gidan nan. Ke ko ba dole ba tunda ta iya makirci kamar ta mutu ta mairaraice ita gata Allah ba dole ta bashi tausayi ba Nazira ta fada To kodai kin zauna a cikin mu ba a dai taba canza maki suna daga zainab yar aikin mami zuwa diyar gidan nan kamar kowa Rufaida a fada . A, a, za a yi kiranta ki da yar gida mana duba yarda yan kwanakin nan gaba daya tayi fresh da ita haka duk sai suka kalloni lokaci daya. Nagaji da cin fuska na mike don barin wurin, dama abincin ya fita min rai lokaci daya na dauki plate din zuwa kitchen. Ina ruwan ba saban ba yau har wanan ce zata bar abinci haka bataci don samun wuri. Ban kara fitowa dakin ba don na gamawa mami komai itama nasan ta gaji ta kwanta tunda akwai tafiya garesu washegari. Nasan da zancen tafiyan mami don naji tana waya kan tafiyan yasa na tashi da wuri na nufi dakin ta koda abinda zata sakani a lokacin. Aikuwa iba shiga dakin na samu ta fito daga wanka saida nayi mamakin hakan don bata ko tsaya jira inzo in wanke bandakin ba ta shiga. Gaisheta nayi na nufi bandakin har ta karasa shirinta na dawo na fara gyara don ko kadan ban kawo dani za a tafi tafiyan ba don banga alaman hakan ba. Hankali kwance nake aikina ina shiryawa maki kaya kamar yadda ta umurceni inyi mata anty Aisha ta shigo dakin tana gaida mahaifiyar nasu. Bayan dun gaisa mami ke fadin ina fatan kin shirya dai don banson bata lokaci ga tafiya kin sani dai. Mami wani shiri zanyi kauyefa zamu tafi banga abinda zan shirya bani ko haka zan iya tafiya ai ta fada cikin zolaya. Mami tace da ita ai kauye garine don akawai yan Adam a ciki na dauka dai daji zaki tafi ai ta kwashe da dariya don tasan ta tabo mami din . Gaba dayan mu zamu tafine mami ta tambaya tana kallon mahaiyar nata lokacin da ni kuma nake masu dan murshi don jin amsan da mami din ta bata. Naji mami tace eh dake da yan uwanki maza ba na fadawa kowa tunjiya don kada yau su kawo min wani zance na daban. Hae su Nazima ta sake tambayan mahaifiyar nata sai mami din tace haba dai Aisha ai ba zan sake zuwa dasu ba tunda da biyu suke zuwa Tun wancan zuwan da sukai min tsiya nasha alwashin ba zasu sake zuwa garin nan da yawuna ba. Mami samu,naka ne fa ba wani gari ba can Aisha ki fice mun a ido tun raki bai kai ga baci ba a dakin nan. Zainab jeki ki shirya kada ku bata min lokaci ta juyo inda nake tana fadi hakan yasa na gunde dariyan da nake masu jin an abamci sunana ga tafiyan nasu da za,ayi wanda ni banso hakan ba don sati biyu da komawan school ke nan mu. Dole na mike ba yadda na iya na koma dakina na fara dan shiryawa yan kayana kala uku a dan karakin jakkar da Aisha taban da zamu tafi kaduna. Karfe goma safe mun karya sai kaya ake ta fita dashi ana sakawa a mota yan matan sunso subita amma mami tace ba zata dasu ba tunda suna raina mata gari idan sunje. Ga motocin da za ai tafiyan dasu sai wani sheki suke ga hasken ranan daya fara gama gari suna daukan ido a ranan. Suna falo zaune na fito da kayan mami zuwa wurin mota kamar yarda ta umurceni indauko zuwa bakin mota jamal yana gurin zai nuna min inda za,a saka jakkar kayan nata. Wanan wau da ita za,a tafi halan Nazifa ta fada sai Rufaida take fadin kema ai kin sani itace yar miko min kawo min dole a tafi da banza. Maganan yai min zafi sosai saida ai aikina ne din hakan don sun fadi hakan bakomai bane gareni tunda kowa yasan abinda ya kawo ni gidan ai shine aikatau. Mota guda muka shiga nida mami da Anty Aisha sai driver nice a gaba zaune tare da driver suna baya a zaune su. Tun kan a baro gida banyi magana da kowa ba har mukai nisa ga tafiya naji Aisha tana fadin waiko mami lafiya yarki take ? Kodai abinda su Rufaida suka fadane ya bata maki rai kikai shiru tun dazun ? Mami tace ai kinsan ita din ba gwana bace wurin surutu barta da saurin aiki kan kamar inji mema suka fada matane daya bata mata rai haka ? No ba wani abu bane serious maganan su necan suke fadin wai ita dni ai dole aje da ita don yimin miko min . Kai wa yan nan yaran akwai tsegumi garesu bari Allah ya dawo damu lafiya sai na masu tsiya dai a kan yarinyar nan . Don banga abinda ta tare masu a gidan nan ba da suke matsa mata haka ko da yaushe. A raina nace kayya mami kullun haka dai kike fada kin kasa yin maganin su haryau su kuma basu barni ba da fitinan su. Wai mami yaya Jafar din ya yarda zai tafi gidan kawar taki ya duba yarinyar Aisha ta fada don a kawar da zancen . Don tsuki mami tayi tana dauko abu a cikin jakarta tana fadin ai kin san hali shi dai. Danayi mai magana dariya kawai yayi min ya mayar dani karamar yarinya sai na masa da gaske zai maida hankali wurin abinda nake son shi dashi ai. Mami da kin barshi ya zaba da kanshi nima ban goyi bayan wanan auren hadin ba kindai ga yadda na yaya mamud ya zama a karshe ai. Ni dai ina gaban mota ina faman tunane a raina har muka kai garin samu,naka din sai bin garin nake da kallon irin ni,imomin da Allah yai masu a garin. Wani gida motan mu ya tsaya duk da anyi gyaran gidan daga wajen shi amma mutum zai iya gane tshon ginane na mutanen da masu shi a lokacin akaiwa gyara. Tundai in ka shiga daga cikin gidan zaka samu part part gidane babba da ya kumshi jama, a masu yawa sosai a cikin sa. Sai tafiya muke ana faman yi muna sannu da zuwa har muka kai kofan wani part daya sha gyara sosai an masa irin ginan zamanin nan . Wasu mata biyu ne suka fito daga part din suna faman yi muna sannu da zuwa dukkan su na shedasu don sunje abuja na san su a lokacin. Da sallama muka shiga falin babba wanda yasha gyara da kujeru manya manya na zamani komai dai na bukata a kwashi a falon. Sai hoton wata dattijuwa dana gani tayi gwagoron irin daukan da akaiwa photon sai kuma photon mami da mijin ta duk da bantaba gani wanan photo ba amma na san fuskan marigayin mijin nata don akwai photunan manya a falin mami har gidan su na Abuja a saka a falon gidan. Mami bata zauna falon ba ta shiga daga cikin dakunan a ca nake jiyo muryan ta ni da Anty Aisha ne a falon zaune muka gaisa da sisters din mami din suna tambayan mu yaya hanya ? Can murya mami ke fadin ina kuke ne ku shigo ga hjyn a daki zaune kuzo ku gaisa kafin wa yancan su shigo. Mikewa mukayi zuwa dakin wata tshuwace a zaune saman gadon alfarama kamar ba dakin tsofi ba duk da tsohuwace matar hakan bai hanata kwaliya ba tana cikin atamfar supar a jikin ta. Aisha kan muna shiga gadon da take zaune ta haye tana fadin wanan ce mara lafiyan da mami ta tayar muna da hankali ga mutum na gani garau haka ba alaman ciwo. Tsohuwa mai barkwanci tana fadin ke kuma wanan shiga haka kamar matar limami chochi fa ? Duke nayiwa shi dan Allah dai udan zaki tafine ki tafi kiba mutane wuri kina dagawa iyayyen mu hankali haka. Daga inda nake zaune kafin taba Aisha amsa nace ina wuni mama sai ta mayar da hankalin ta a gurina tana fafin kedai yar albarka kunzo lafiya ? Yaya hanya ya kuka barsu a can nace lafiya yaya jikin mama Allah sa kafara ne ? Da alama taji dadin yadda muke gaisawa da ita din sai wasan baki take tana fadin amin yar albarka. Niko ko yar taki da ake fadi kin samu ke nan yarinya haka mai hankali Allah yasa ku raka tare. To mu da ba, awa addu,an a hana mu raka din kaji min tsohuwa daga ma kin samu anzo gaidake har da zaben yiwa mutane addu,a. Muryan yaya mamud ke fadin ni ina matar take gani nazo kada ki tafi muna son ki a hakan ko dan kwanciyan hankalun uwayen mu. Kaji ja,iri kice dasu kike tafe ashe yau ina da babban bako a garin nan mamuda yaushe ranon ka da garin nan tana kokarin mikewa tsaye da kyar. Aisha ta mayar da ita ta zauna mami takai mata duka tana fadin Aisha yo ga tsiya karki balla muna tsohuwa garin shashancin ki. Barta ai gani take kamar ta fini kwari a hankan yanzu sai in lankada maki dukan tsiya a wurin nan. Duk aka sa dariya sai ga daya sister din mami ta shigo tana fadin hjy yau fa kinyi baki harda Jafar akazo gaida ke. Mami tace har kwana kuwa zasuyi maki a nan sai ki shirya ke nan kedasu yau a gidan nan. Tana tafin dadi da murna ta samu ta mike da kyar tana lale marhabi da manyan bakina yau kuce amarya nake sai na zaba ashe tana fita daga uwar dakin nata din zuwa wurin su ta taresu. Zeey jeki dauko mi kayana ki shigo dashi dskin nan mami ta fada na mike saida tsohuwar ta gama fita na dan bi gefen ta na fito daga dakin. Suna zaune dukkan su tana masu lale marhabin cikin jin dadi har na fito kayan da mukazo dashine aketa faman shigowa dashi gidan. Jakkar mami dana Anty Aisha na dauko na shiga dashi daga cikin daki kafin i koma in dauko nawa sai kuma na rasa yadda zanyi da jakkar nawa. Na dan tsaya daga kofa ni ban shiga ba sai da dayan sister din mami takece min dan Allah shiga da ruwan nan mikawa su anty in gama da wayan nan. A lokacin na samu komawa dakin na samu mami ta kewaya ban daki Aisha kuma tana rashe rashe saman gadin tsohuwar tana waya. Ruwan na aje masu kafin in dan samu sakon gado na aje dan jekar kayana a wurin na juyo ina fadin anty Aisha ga ruwan . Da hannu tayi min alaman a, a na dai samu wuri na tsugunna duk da kishin ruwan da nakeji ban yarda nasha ba tun kan mami ta fito tasha. Ta fito tana fadin an shigo da kayan nan duka zeey don miyan nan kada a zubar dashi don Allah fadawa Ramatu ta kawar dashi kada a zubar. Don miyane mai yawa na zabbi dana kan saniya banda nama da mami ta saka a soya a zuba a babban ruba mai marfi kuma. Na mike da sauri duk da ban san wacece Ramatun ba a cikkn su sai dai nayi sa, a suna falon dukkan su nake fadin mama Ramatu mami tace akwai miya a waje akawar dashi kada a zubar. Ke wanan muryan wa zaisan kina magana a hanka yaya jalal ke fadi yana nunawa mama ramatun ni a lokacin. Na sake maimaita abindana fada da farko tana fadin aikuwa gara da aka fada muna bari yanzu a kawar dashi gurin. Umma ina key din dayan dakin yake akai kayan a ciki tana tambayan tsohuwar data mayar da hankalinta kan diyan mami da suka sakata tsakiya da hira. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣8️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU MASOYANA UBANGIJI YABA WUNI LAFIYA YA SADAMU DA RAHAMIMIN SA AMIN YA ALLAHU. KI BIYA HAKKIN MU KI KARANTA A CIKIN SALAM DA SAKEWA DARI UKUNE KACAL 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA NA DARI UKU. Ranan naga yadda ake nunawa jika so da kauna na gaskiya don tsohuwar kamar ta hade yaran su koma cikinta take ji basu kadai ba harni da nake bakuwa a cikin su bata nuna min bambancin hakan ba. Ga tawa kakar saboda wani dalilu nata na daban ta turoni bitnin yin aikatau badon Allah ya hadani da uwar daki ta Allah ba. Allah kadai yasan yadda rayuwata zata kasance a birni ba tare data damu da hakan ba ita nata butin dai shine ta samu kudi ta gareni kawai. Basu bar dakin ba nan kowa ke zuwa taron su suna gaisawa su yaya jamal ne suka mike don zaga gari zama wuri daya ya ishesu. Yaya mamud ya dade da fita daga dakin ya barsu yana fadin zai leka wani abokin shi ko yana nan suka bar yaya jafar dake faman aiki a cikin sytem din shi yamai da hankalin gaba daya ga abinda yakeyi din. Ina zaune takure wuri daya na kurawa tv dake aiki ido ana wani shiri a kscm kaduna hakab yasa hankalina ya dauku ga kallon. Ai bata jikaba tshohuwar ke fadi me take da suna tana murmushi take kallona nayi firgigit in dago kai sai naga ido shi a kaina. Bakiji me na fadaba yake tambayaba kai na girgiza mai ina tasowa daga inda nake ki dauke kayan nan da suka bari a nan ya kara fada. Sai lokacin nasan meya fada da farko na tashi da sauri na fara tattara kayan dake saman karamin table din. Waini kan dan gidan iyami yaushene zaka kawo muna sarakuwa tshohuwar ta fada tana kallon shi. Cikin basarwa da kalan maganan shi ba tare da ya dago kaiba yake fadin banga matar aure ba har yanzu. Allah na tuba duk matan daka baro kaduna har Abuja bakaga mata a cikin su ba don tsaban ruwan ido idan an fada uwarka ta tare maka. Ni yanzu nafi dason yaro yayi auren shi a cikin lokacin don wanan rayuwan baida tabbas dan rayuwan yanzu kadan ne. Ba sai ki nema min ba tunda ke kinga matan a ko ina birjit yo ko cikin yan uwanka ka nema mana ko wanan yar ta uwarku ai irice ta kwarai gata da hankali har naji dama ace ta shigo cikin zuria na. Ke kiji da kanki don Allah da wanan shirme da kikeyi an fada maki kowa irin kune halan ya fada yana zareww tshohuwar ido. Ta sake dariya tana fadin kaji min dan kawai ido ma zaka zare min don kawai na fadi gaskiya ko sai mun kaika mararaba mun ma wankane kafin a soka. Kinga idan kina matsa min da wanan magana idan na tashi na tafi ke nan ba zan dawowa ba ya fada kanshi duke. Nasan zaka iya dan nema mai zubin jan fata kai dama Allah yaga abinda ya gani ya kaika can cikin su da zama. Wanan karo kan tare dake zamu koma ai don naga kema dasu kikafi kama ai barni na mutu musulma tsohuwar ta fada. Saiga mami ta shigo falin tana fadin hjy dake dawa kike magana sai ta ganshi a zaune take fadin a a aboki kai kana ciki ashe na dauka tare kuka fita ai. Ina nan mami idan wanan tsohuwar bata daina damuwana ba zan bar garin nan yanzu ba sai anjima ba. Zaka iya na sani damuwar dai nasan fadan so kankane takema da baka son ai maka ko ? Kamar kin sani yar albarka daga zancen aure yake wanan halakon haka kamar an mashi maganar mutuwa shi. Wai shi baiga mata ba duk garin nan nakece mai ga wannan yar taki tun ba a kai ko ina ba don ni na yaba da halaiyar wanan yar taki. Da sauri mami ta juya inda nake ina daukan gorunan drinks a kasa take fadin haba dai hjy har abin nasa yakai haka kuma ? Ai ba zan barshi ya tafi ba sai ya tsayar da matar da zai aura in yaso sai ya koma idan bukin ya karaso ya dawo ayi buki nima zaman shi haka a can shi kadai ya dameni yanzu. Kaji maganar gaskiya don wanan da kike gani idan bakiyi da gaske ba baida niyar aure yanzu gashi ya fara zama magidanci. Wani kallo yaiwa tshohuwar tare da mikewa lokaci daya sai kuma naji ta koma rarashin shi tana fadin ai kasan bama haka dakai. Kada kasa mamuda yai muna dariya tun ba,aje ko ina ba yanzun fa na gama mashi tsiya a kanka yai fushi ya fita don nace kai nake so. Yanzu ma zan fada mai ya dawo nabar masa ke ya dauka bana so ni don kin faye jininini da yawa yanzu. Dawo dawo ka zauna na bar wanan jininin indai a kankane na isheka ni kadai ai dama ai baikai ciki ba zancen nawa ina ka taba ganin mutum ya dabawa cikin sa wuka ? Komawa yayi ya zauna sai abin ya bani dariya har bansan lokacin da sautin dariyan ya fito min fili ba. A, a a takwarana dariya kike min kuma don ina neman shiri da maigida a gaban ki ? Hararana yayi yasa na bar falon na koma daga wajen dakin na zauna saman dan dakalin dake wajen ina kallon mutanen gidan dake gittaya tako ina. Sai da ta fito da niyar zuwa sallah mami ta biyo shi suna magana dashi mami ke fadin zeey a nan kuma kika zauna ne ? Na juyo ina dan gaida ita take fadin shiga mana ciki koda yake ma anyi sallah azahar yanzu sai ki shiga wancan dakin dake gefe akwai bandaki a cikin sa a gyare dakin yake ku zauna keda Aisha. Jin haka yasa na mike ina kokarin shiga dakin don kallon da yai min mai kama dana warning a lokacin. Dakin da mami tayi min kwatance na shiga dakine gyarare da katon gado hade da mirrow din shi sai kujera three seater dake dakin gadon yasha gyara dakin yana ta kakahin turaren wuta. Ban dakin na nufa na samu ruwa a manyan robobi aje dashi nayi amfani na dauro alwala nafito na tayar da sallah saman salyan dake dakin. Ko dana idar ban zauna ba falon na fito na gyarashi tsab har waje duk suna cikin daki basu sani ba sai da mama habiba tazo fitane ta ganni take fadin yar nan kina nan kina aiki baki huta ba. Hjyn su mami ke tambaya wace yace kuma sai kuma ta tuna dani take fadin au yar iyami ko ? Wani aiki take kuma yarnan ki huta hakana mana ina hankalce da ke baki da son kazanta ta juya inda mami take kwance tana fadin. Kin samu ya sai ki rike tada amana don Allah yarinyar tana da shiga rai lokaci guda gata da ladabi. Sai naji ina kwadayin hada iri da ita don irice mai amfani ita din ba abin yarwa bane haka. Hjy nima yarinyar ta kwanta min a rai sosai ina kulla da ita tankar yar cikina don bata da kyashi ga sanin ya kamata kamar wata babba can. Tarbiyane idan kinga haka ta samu tun daga gida uwarta ta tarbiyartar da abinda yadda akeson ko wani da ya kasance sai ki kara himma wurin riko Allah ya taya ki rikasu. Don tafi min wa yan nan marasa moriyan sau dubu a wurina sai hjyn tasu tace tafisu kan gaskiya yaron da ba sai kace ya tashi yayi ba yake abu ai yana da dadin zama. Hjy kin san wancan zuwan da nayi da yaran nan iskancin da sukai min saida muka koma gida nake ji nayi masu tas wallahi. Kiyi hakkuri dasu tunda su suka kawo kansu gare ki inma sunyi maki don kansu kowa ma zai girbi tsiyar shi ai. Ke dai ki rike wanan bisa ga amana da yarda idan dai bata kauce bane don mutum mugun icce ne sai yaga ya ginu yace kaine makiyin sa daga baya Allah ya kare mami ta amsa da amin. Sai dare mazan suka sake shigowa ina daki naji hayaniyan su ban daga daga inda nake zaune ba naji muryan mami ta fito daga uwar daka tana fadin. Garin yai maku dadi ke nan ko kun shige cikin gari tun dazun ina shi aboki yake ne banganshi tare daku ba. Wanan friend naki saike mami yana masallaci mun barshi wai yanzu yake son sallam guards din shi su koma kaduna su kwana. Da daren nan tau haka dai yace don wai baiga inda zakaisu ba nan suwa ke nan tsohuwar ta tambaya. Security din da mijin ki ke tafiya dashi don tsaro yaya jamal ya bata amsa a takaice take fadin. Ikon Allah tafiyan ma sai anyi shi da masu tsaro ko may sai yaya mamud yace kin san su can hakan ai wani abu ne tundaga can aka hadu shi dasu aikin su sukeyi su. Duniya inda ranka kasha kallo yanzu shi wanan dan figegen aron ne harda wasu masu tsaron shi. Hjy mu a nanne ba a dauki tsaro da mahinmanci ba amma su can idan har kai wani abune dole kana da masu binka a baya ai massanman shi da sukeji da shi a can. Waini na kasa gane aikin yaton nan sai jalal yace bako zaki gane ba don shi bros telent ne sosai ilimin shi yaja masa hakan. Yanzu zai iya kera maki wani abu a wurin nan wanda sai kinyi mamaki don har abin yai tafiya da kafansa su ake kira da sciencetics mana masu fasahan kwakwalwa ikon Allah tace. Tare da fadin gaskiya yaki aure haka har yana batun rufe arbain fa don in ba zan manta ba tun mulkin shagari na farko aka haifeshi ai. Kai hjy wanan tashin tasgin haka kan friend dina yanzun dai ni abinda nake so kafin ya tura mutanen nan a cikin daren nan ai masu kokarin wurin kwana hjy. Tshohuwar ta tambaya su nawane akace hudu hudu ta fada da mamaki tana fadin har karte hudu ke yawo dashi wanan abindai da nake gani. Ikon Allah yafi gaban mamaki yau ace wai dannan ne Allah yaiwa bawa haka Allah ya ciyar daku baki daya suka amsa da amin. A daidai lokacin da dan bawan ke shigowa yana waya tsohuwar ke fadin gama yanan ya shigo dayani. Kai yanzu don baka da tausayi zaka tura yaran mutane da daren nan su koma kaduna don rashin imani. O lord wanan kuma wani zance take hakane da shigowan mutum ya fada yana kaiwa zaune yana aje wayan da yakeyi. Aboki wai yanzu da daren nan zaka tura security din nan su koma kaduna sai naga dare yayi ai. No sun fasa ai mami uncle bello ya sama masu wuri zama da zasu zauna suna can sun tafi suga wurin kafin su dawo su dauki abinci. Ko kaifa nace ko kai fa dan nan amma ka tura bayin Allah a cikin daren nan haka ai abin baiyi ba kamar dai ba mutane a nan. Enough dan Allah waiwa ya fadawa wanan mai wa,azin ta damu mutane da wa,azin nan nata a gurin nan. Kai rufamin baki aini yanzu nasan ba cikkaken namiji kake ba don a matsoraci nake kallon ka yanzu tunda sai an rakoka har karkaran mu matsoraci. Daidai lokacin nake fitowa daga dakin don kira da mami tayi na amsa daga ciki. Dariya ya bushe dashi bashi kadai ba duk wanda ke falon saida maganan ya bashi dariya yadda suke kwasa dashi din. Barin gani idan baki tsorona din da gaske ya fada yana mikewa ya harota ta juya tana neman abinda zata kare kanta kafin ya iso gareta . Tayi sa,a filo na kusa da ita ta dauka wai dashi zata kare kanta din tana kaimai duka yana dariya ya juyo a daidai lokacin na kawo wurin zan wuce sai ji nayi kumus nayi baya tangal tangal zan fadi. Mami tace zaka karya min da da wanan karfin naka haka kamar na doki shi kuma ya juyo yana fadin oh sorry . Tsohuwar nan kinga zaki saka in karyawa mami yarta don fitinan ki to yaushe rabo damuyi fitinan haka. Ai rabu a gana arzikine dan nan wata ran idan kunzo sai kun tunani da wanan wasan da mukeyi yau ina Alh ina mahaifin ku sun kare. Kowa yai wani iri a dakin don abinda tsohuwar ta fada wallahi hjy gashi yau muna kewan tsohon nan don da zaran zan shigo naga part din shi sai in tuna da lokacin da muke zuwa yana bamu mazzakwala muna sha yaya mamud ke fadi. Kai mukan bamu sanshi ba gaskiya sai dai a photo jalal ya fada ai old man din nan ya kware mu daya tafi bamu sanshi ba. Waike zeey kin debi abincin nan kuwa na juyo ina fadin ban diba ba mami yanzu na idar da sallah dama. Jeki ki dibi abinci da wanan halin naki ga abincin mu can ankai mana daki tun dazu wanan nasu sai na mutane yayan ku yacan sai a samu yaro yakai masu idan sun dawo. Juyawa nayi zan koma dakin don ban iya sake jiki suna wurin don haka na juya don na koma dakin hjyn su mami. Banji me yake fada ba yaya jamal yace ke wai kizo ki zuba mai abinci yar mami. Jin an ambaci sunana yasa na tsaya tare da juyowa na dawo zuwa inda abincin yake aje dan kallon yaya jamal nayi ina fadin wa zan zubawa. Yaya jackson ya fada hankalin shi naga wayan shi rasa abinda zan zuba mai nayi don kuloli ne gurin zasu kai biyar duk an cikasu da abincin alfarma har da fate da mami tace tana so yaji gyada a cikin sa. Fara bude masu kulan abincin nayi don ya zabi abinda ranshi ke so sai dai baya kallona hankalin shi naga waya yana rubutu. Yaya me zan zubama na tambaye shi ina dan gurfane a gaban shi don ba dining table falon tsohuwar kamar can gida kaduna. Ya dan dago kai yana fadin anything zaki iya zuba min Aisha ta fito daga dakin yaya mamud daya karbi plate din da mami ke shan fate yana dan sha yake fadin Essha kina gidan nan ashe tun zuwan mu ban ganki ba. Ina kwance ne yaya ta fada tare da ratsowa ta zauna a hannun kujera tsakiyan su shi da yaya Jafar din. Ke may kike a wurin nan ne haka ta tambayeni ya Jalal yace wai abinci akace ta zuba take tunane na dan kalleta ina fadi a hankali ban san may zan zubabane ai. Oh shine kike tsaye a gurin ya mamud yace ka duba ai tana da gaskiyar ta kada ta zubama abinda baka so ne. Wanan dai ina so inga matar shi kafin in mutu yaro da izza da isa kamar wani basarake dashi matar ka tana da hakkurin zama dakai haka. Hjy naga fa yau sai yar tsama kuke da yaya Jackson tunda muka zo Jalal ya fada don shi yafi yawan dan magana bisaga Jamal dake da zubin yanayi ya jafar din wasu halaiyan su suna da kama sosai. Aure nake son yayi hakana ya baku wuri kuma ku samu ku zaburo wanan gwauron ya tare maku wuri. Muka fada maki samarin suka fada tace to ai shike nan tunda baku son a matsa mai yayi aure. Wanan fa zata iya hada ma abincin nan duka tunda kace anything zata dauka kace tayima mix ne gaba daya Aisha ta fada tana kallona. Ke zuba min ki daga min nan don Allah ya fada tare dan dagowa yana kallona. Hasken kwan fitilan falon ya haskani gaba daya launina bada wani kala na daban ga mai kallona a lokacin. Na duka ina zuba mai kullan gabana wanda sakwara ne a ciki ashe sai na bude kulan miyan shi dake dauke da miyan ganye yaji egushi da manyan nama na zuba daida don nasan shi baya cin abinci da yawa. Mikewa nayi zan bar wurin ya kara fafin ruwan wanke hannu fa ba tare daya ko kallo inda nake bai yi ba yai magana. Har suka bar falon ban kara fitowa ba sai bayan danaji fitan su sunawa mami saida safe na dan kara mintina na fito. Kayan da sukaci abinci nake kwashewa yayin da nazo kan nasa naga spoon a ciki da alama dashi yaci. A raina nace bakin bature ke nan abincin ma da cibi zaici don sallo ai kakar nan tasuce maganin shi. Tas nayiwa falon kafin in shiga wurin mami ina tambayanta koda abinda zanyi mata kafin na kwanta. Zeey a kwashe kayan abincin nan da sukaci nace na kwashe mami ki duba min kayan barci na a cikin kayana ki ban shike nan sai kije ki kwanta. Har na kwanta a saman dogon kujera anty Aisha ta shigo tana fadin af namanta da charger na dakin tsohuwar nan dan Allah zeey dauko min. A kofa na tsaya nayi sallama kafin in shiga dakin yanayin dana samesu a ciki nagane wani magana sukeyi mai muhinmanci a tsakanin su su hudu. Tsohuwar da kuma kannen mami din duk suna zaune sunyi shiru da suka ganeni. Sai mami ke fadin bakiyi barci ba ashe zesy a, a nace nake fadi charger anty zan dauka ganin suna kallona duk sai na tsargu . Na dauka na fita da dan saurina daga dakin don ban son in dakatar masu da maganan da sukeyi din . Washe gari tunda safe dana tashi nayi sallah na fara gyaran falon har zuwa waje ina jin hayaniyar su dakin har na gama wanka na shiga don mami tana cikin dakin da yan uwanta. Sai kusan karfe goma suka fara shigowa falon ana gaisawa a tsakanin su babu muryan wanda nake jin tsoro don haka na fito na gaidasu da kwana ina jin mama Ramatu na fadin. Ga abinci nan tun safe aka aje masu shi basu shigo ba ina shi jafar din gana yan aikin shi nan suma . Bai fito ba jamal ya bata amsa tare da fadin mama kinsan shi baya fitowa da wuri haka ai sai idan ya gama abinda yake yi. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 1️⃣9️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAN UWA FATAN ALHERI HAR KULLUN A GARE KU UBANGJI YA GAFARTAWA MAGABATAN MU DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA ALLAHUMA AMIN. YAR UWA BA ZAN GAJI DA TUNATAR MAKU BIYA KAFIN KI KARANTA BA DON KAICEWA SHIGA HAKKI GA MASU IMANI ALLAH YASA MU DACE AMIN DARI UKU NE KACAL KI GUJI RAINA HAKKIN WANI A KANKI DON ALLAH. Saida gabana ya fadi don jin muryan dodona da ya shigo gidan bani kadai na gane ina tsoron shi ba don har salma, Rufaida da Nazifa. Idan ya shigo na kanga sun shiga taitayin su a gidan har jamal da jalal suna wanan rawan jikin da kama kai a gaban shi idan yana kusa . Nima hakan da nagani ya darsa min tsoron shi a lokaci guda duk da ban taba ganin wanda yaiwa cin fuska a gabana ba. Dagowa nayi a rikece ban ko debi abincin kwarai a platen din ba don in gudu in koma dakin mu. Na dai samu gaida shi da kwana na jakafata na shige dakin zama nayi don cin arish da kwai dana debo a falon . Nayi loma biyu ne naji mami na kwala min kira daga falon da sauri na mike na fito falon ina fadin mami gani. Tana can tana magana da mama Ramatu kanwarta a lokacin kafin ta juyo tana fadin . Yauwa zeey don Allah yi serving din yayan ku gashi nan ya shigo yanzu ni zan dan fitane yanzu zan dawo. Tana fadin haka ta mike sai naji yana fadin amma da mota zaku don akwai dan nisa daga nan gidan. Eh ai shine yasa nace Jalal ya sauke mu kada yaje nisa yana waje yana jiran fitowan mu ai. Amma mami jalal ne zai jaku ga driver suna waje sai shine zai jaku ban faye yarda da tukin yaran nan ba gaskiya yake fada da turanci. Sun saba jana a mota ko a kaduna don hakane ai na yarda da tukin motar nasu. Allah tsare yace yana mayar da kanshi ga wayan dake hannun shi aikin shi ke nan ko magana yake hankalin shi a kan waya ko sytem din shi shiya a raina nasa mashi mayen computer. Abincin na gama zubawa lokacin falon daga shi sai tsohuwar dake zaune itama kudi take kirgawa daga haban zanin ta nakai mai abincin gaban shi na aje. Ruwa na koma na dauko na aje mai cikin dan muryana nake fadin yaya ga abincin nan do gudun kada inyi laifi kuma gare shi. Jin abinda nace yasa shi dan juyawa saman lafiyayyen kujeran falon tsohuwar da zaka iya da kira dakin wata amaryace can don haduwa. Wayan ya aje daga gefe kafin yakai kallon shi ga abincin ya dago kai yana kallon tsohuwar kuma. Kai kai kai wanan tsohuwar ko fashi kika farane haka ina kika samo wanan kudin haka masu yawa ? Yanzun kuma bakiki kariba don baki da tausayi sai kuma kin karbewa mami dan kudin ta maimakon ki kara mata. Kafin tsohuwar ta dago kai tana fadin ja,iri da hausan ka kamar na mai koyo uwar taka mai tausayina ita take aiko min da kudin ai. Yau kuwa zance ta daina don ba kashewa kike yi ba boyewa kike yi idan an baki ashe. Ina wurin fridge ina daukan ruwa insha suke wanan barkwamcin da kakar tasu na dauko ruwan na juya zan wuce daki don da farko tsoron shigowan shi ya hanani daukan ruwan . Naji yace ke wanan uban abincin da kika zuba ni dawa zanci shi haka ? Tsayawa nayi wuri daya da goran ruwan a hannu na ya sake fadin sai kizo ki dauka ki cinye shi tas. Cikin karfin hali nake fadin na debi abinci yanzu yana daki na aje zanci kai wanan yaron da fitina kake wallahi ina laifin yar nan tana iya kokarin ta da kai. An fada maki kowa irin kine dake loda abinci a cikin sa yana kiba kamar za,a tafi gasan gwaji dashi halan ? To ba zataci ba idan zakaci kaci da yawan fitina har yaushe zaka zauna kana matsawa yarinya mutane haka. Yar nan ko karyawa bata samu tayi ba yanzun taga ba yan uwanka abin kalaci suka fita kai kuma kazo da naka tsurkun yanzu. Idan kayi fushi sai kaje kayi aure kowa ma ya huta mitar ka na tsiya kaji min yaro da jarabar tsiya haka. Hjy dama naga kin gaji dani ai ki huta min gori yau kaduna zan kwana idan Allah ya yarda idan ka tashi ka wuce jos zaifi ma sauki ai. Ina tsaye wuri daya ni ban gusa ba ina sauraren da bai karewa da tsohuwar ko da yaushe sai dai idan basu hadu ba idan kuma bata ganshi ba ta kafa mita ke nan ina ya shiga. Zo ki dauki abincin nan na fasa ci ya fada da dan karfi simi simi na tako zuwa gaban shi ina zuwa nakai kasa tare da fadin. Don Allah yaya kayi hakkuri na fada ina kaiwa kasa kamar zanyi kuka a gaban shi bace min dagani a nan na firgita sosai tare da kai hannu ina daukan plate din abincin. Na juya ya sake fadin zo nan na dawo baya da sauri zuwa gareshi hjy ko sai faman yi mai masifan hakan takeyi bai kullata ba. Baki da wasu kayane sai wanin black dress din da kullun kike sakawa ba kyau gani ? Kallon kayan na jikina nayi ina fadin anty Aishace ta bani sune sabbin kayana yanzu dasu kawai nazo garin nan. Fadan da kakan nasu takeyine ya hana taji me yake fada min don babu yadda zata jishi a yadda yake maganan. Tafi don Allah ya fada in deep voice na juya da sauri don in bar wurin kafin yakai ga makeni yadda naga ya hasala din nan. Tunda na shige ban kara fitowa ba shi kuma bai fita daga falon ba don ina jin muryan shi jefi jefi da hjy tsohuwa a falon. Har su mami suka kai ga dawowa gidan hakan yasani kwantawa na kirkiri ciwon karya don da Anty Aisha ta ganin kwance take tambayana nace kaina ke ciwo. Data fitane mami ke tambayan ina inane tace tana daki wai kanta ke ciwo tace . Yo ai dole kai yayi ciwo ko don fitinan wanan masifafen dan naki da kika barta dashi ta bashi kalaci ya aza mata fitina. Aiko ya Jackson baida fada hjy kece dai baki fahince shi ba Aisha ta fada tana kallin dan uwan nata. Murya mami tasa ta kirani daga falon kamar ince wayo don wani irin faduwan gabane ya zuyarci zuciyana lokaci guda . Saboda tsoracewa gashi yai min fadan jallabiya baka dana saka a jikina wanda har yanzu shine dai din a jikin nawa. Don gigicewa ban ko tsaya daukan dan kwalina ba kaina dake da kitso tsoro hudu da nayiwa kaina a daren da zamuzo sun kwanta suyi lub dasu ga bakin gashi na sai sheki yakeyi. Na fito nazo na zube a gaban mami din dake maganata da mahaifiyar ta kan rashin sake jikina a cikin su. Ban iya dago kai na kalli kowa a falon ba kaina yana sade a kasa ina jiran inji abinda zatace dani. Shiko ko kallon inda nake baimayi ba tunda nazo gaban mami din gashi a kusa dashi mami take zaune a daya kujeran dake gefen shi. Meke damun kine zeey mami ta fada tana duban yanayina kai na dan girgiza tare da fadi cikin karfin hali mami kaina ke ciwo dama tun kan muzo nan na kuma sha magani ya fada min don kada tace a kaini asibiti. Haka baida wuya a gurin mami dan abu kadan gare su yanzu asibiti ne za a ce akai mutum. Mami tace dawo nan ki zauna ki daina wanan yawan zama ke kadai da kikeyi a daki ko yaushe koshi yana ja maki ciwo. Banda zabi sai yadda mami tace dani dole haka ja mataciyan kafata da yai sanyi na hau saman kujeran data nuna min din. Yaya jafar da ke rubutu a cikin sytem shi cikin kwanciyan hankali sai lokacin dana kai zaune ya dago kanshi yana fadin . Ke meke damun kine wani irin magani kika sha nayi tsuru tsuru da ido don ban san me zance ba sai da mami ta kara tambayana nace. Mami dama wanda aka ban asibiti ne a abuja sauran daya rage na sha dazun. Sai naji yaja uban tsuki ya mike yana gyara dan riganshi daya takure don zaman daya dade a zaune. Zaka fitane kafin ya ba mami data tambayeshi amsa sai hjy tace yo ina zai fita tunda tsoron mutane yake ji a waje. Wurin ta ya nufa direct yana fadin zo muje ki rakani kada kada a saceni garin naku. Wai wace ke zaune a kauye ke fadin wani na tsoron mutane ke idan ba tsoron kikeyi ba meya hanaki komawa kaduna ki zauna da mami. Ja,iri ba zan tafi ba a dakin mijina zan mutu inda ya barni ba dakin wani ba ya fice yana dariyan maganan ta. Ya dan jima a waje ina nan zaune falin tare dasu mami daketa baki suna fita don zuwa gaida mami din sai faman basu alheri mami keyi. Nasan dai da yawan masu zuwa gaida ita yan uwantane saura kuma abokan arzikine. Yayi sallama ya shigo falon suka amsa mai inda nake ya nufo yana mika min magani nasa hannu biyu na karba a cikin ladabi. Mami ke tambaya maganin meye wanan din yace stress don kila aikine yai mata yawa yana mika min ya juya ya fita daga dakin. Haka ya ban dama tashi na hade maganin don dole duk da ban san maganin kome yake nufi ba aiko na fara jin jikina wasai. Ina sallah azahar sai barci ban tashi ba kuma ba wanda ya tayar dani din don sun dauka dai da gaske banda lafiya ne din sai bayan sallah la,asar na falka na tashi nayi sallah. Ina idar da sallah nayo falon part din tsit yake babu wani hayaniya acikin sa yasa na gane mami ta fitane a lokacin. Ko ina na gyara tunda aikinane nagama na hada kayan abincin da nagani ta nan na gane su yaya mamud sun dawo sunci abinci sun fita. Don da alama shi yasan garin sosai kilama yana da abokai a garin sabanin shi mai zaman gida ko yaushe. Salati naji a bayana mama Ramatu na fadin yanzu yarnan harda baki da lafiya baki kwanta kin huta ba ? Kina nan kina tikan aiki haka mama naji sauki na bata amsa ina dauraye kwanoni dana tara wanda na wanke. Kinga idan baki da lafiya bar matsawa kanki haka ai kowa yasan ciwo ko a daga maki kafa dashi. Ni dai na gama ban ce uffan ba sai dan murmyshin da nakeyi kawai dakin na koma na shiga wanka kafin magariba yayi. Iya kacin ganina da yaya Jafar ke nan tunda ya ban magani saida darene nake jin su mami na magana wai ashe fitan da yayi tunda ya kawo min magani kaduna suka nufa. Yana zuwa kaduna gida ya nufa don yana son yayi wanka abinka da goggagen dan boko mai ilimi ashe duk zaman garin ya ishe shi . Dan daurewa yayi kawai don ya farautawa mahaifiyar shi da kakan shi raine. Sai dai ya kasa kanne zama har kwana biyu ko ukun da mami tace zatayi da mahaifiyarta a tare dasu don suga yan uwa yan uwa su gansu. Tun daga kofan shiga yake jiyo hayaniyar yan matan a gida yake mamakin me suka samu hakane suke wanan hayaniya haka ? Rawa suke tika ga kida yana tashi kamar gidan club Nazira da Ruby suna wani irin rawa wanda bai dace ace sunyi ba. Ba wanda yasan da shigowan shi har ya tsaya yana kare masu kallo a wurin kafin kamshin shi dakewa mutum sallama ya daki hancin su. Duk suka juya suna kallon kofan salma na zaune tana shan milk a cup tana dan kurba a hankali itama daga inda take din zaune tayi arba dashi. Rudewa ko wacen su tayi ya tako a hankali zuwa part din shi dake gidan don wanka yake son yi da sauran abubuwan daya bari a nan. Da sauri Nazira taje kashe kidan baiko juyo ya kara kallon inda suke ba ya shige part din bayan ya bude tare da gwauro kofan da karfi. Duk yadda yake jin shi a da sai yaji komai ya gushe mashi bacin ran yaran nan ya mamaye zuciyar shi. Yes yasan da yana wasu abubuwa da suka kaucewa addini da tarbiyan shi amma tsani yaga diya mace tana kauce hanya. Zama yayi sama gado dakin tare da tokare hannaye shi ya kama haban shi yana tunanen zancen su da mami da take fadin. Ba zanso ka ketare gidan nan ba idan baka son yar hjy hindu sai ka zaba a cikin wa yan na yaran guda uku da ke gidan nan don nasan dukkan su babu wace ba zatayi makaba a cikin su. Tunda kai na fahinci baka da time din tsayawa dating da wata mace a yanzu tsuki yaja yana mikewa tsaye. Deep in thought yaya za ayi ya auri daya daga cikin yaran nan da idon su ya gama budewa haka wai. Dadai yaso bin ra,yin mami don shi ba wata macen da ta tsaya mai arai yanzu don hakane zaibi zaben mami din gareshi. Wani tsuki ya kara ja ya fara cire aninin gaban rigan dake jikin shi fara longsilve yana maijin tarin haushin su a ranshi. Wanka ya fada ya dan dauki lokaci kafin ya fito ya samu waya shi nata ringing ya nufi inda ya aje wayan yana dagawa. Yaya mamud ne a layin yai mai kira biyu bai daga ba gana ukune ya samu ya daga yake fadin ya jafar kana inane haka mami tana tambayan ka ta kira layin ka not reacheble. Ina gida yanzu haka ya bashi amsa kai tsaye gida yanzu na fito mami da hjy suna tambayan inda ka shiga yanzun hakan ina kofar gidan. Kaduna fa nake nufi ya bashi amsa kamar a hasale don har lokacin yana jin ranshi babu dadi ga abinda idon shi ya gane mashi din nasu Rufaida. Kokarin tayar da sallah dake kanshi yayi kafin ya gama ya shirya cikin wani jallabiya ya nufi gado ya fada. Saidai duk yadda yaso yayi barci hakan ya gagareshi don baison ya batawa mami rai ko kadan tunda yai mata alkawari ya zama dole ya cika mata burin ta.. Mami tunda yaya mamud ke fada mata ai Jackson ya koma kaduna taji rayuwanta ya baci dashi sosai don me zai nuna bai iya zama a mahaifan ta. Ko kuma yayi hakane don gujewa zancen auren data tasa shi gaba dashi don ko a daren jiya saida sukai mai tas itada yan uwanta da mahaifiyar su. Wanan zance ne na sama sunayi da anth Aisha ta aikoni daukan mata charger ashe a dakin tsohuwar da dare. Mami uwar zamanice don haka ba tare data furtawa kowa bacin ran da take ji a ranta ba ta nasa zata kyaleshi taga iya gudun shi yanzu. Don haka ta daure taci gaba da tsabgoginta ba tare da nunawa kowa komai ba kamar ranta bai baci ba. Haka kuma tasa a ranta wanan karon ba zata kirashi taji dalilin yin hakan dayayi ya barsu can ba tare data sani ba. Karshe ma shigewa tayi da sunan zatayi wanka harta shiga dakin ta juyo ta fito zuwa dakin mu ta sameni kwance na rufe idanuwa na sai jin muryan ta nayi a kaina. Da sauri na bude idanuwana cikin laushin murya nake gaida ita take fadin ya jikin naki yanzu ? Naci sauki na fada a yar siririyar murya ina kokarin mikewa zaune ta sake fadin badai inda kike ji a jikin naki yanzu don in sani tun dare baiyi ba. Zama tayi a gefen gafon dakin tana dan kale kale a dakin kamar tana nazarin dakin ne ko kuma wani tunane. Na dago kai a hankali sai naga tana kallona can take ce min ko dai zancen karatun kine kika saka a rai haka zeey har yaja maki ciwon kai ? Nace lah mami wallahi bashi bane mami dazun daine kan nawa ya fara ciwo kuma ai nasha magani yanzu naji sauki. Tana mikewa take fadin to shike nan ina ganin zan karbar maki transfer tunda yanzu zaman mu zaifi yawa a can. Don ba zan barki ba inda bana don ke din kamar amana kike ga hannu na ai. Mami duk yadda kika zantar a kaina daidaine tunda kece uwana yanzu ai mami banda wata uwar dana sani kuma. Tace to babu laifi na gode ga yadda kike nuna min nima sai dai ina tsoron watarana kar asabe ta rabani dake. Asabe yamzu bata da iko kamar yadda kike dashi a wurina mami don ba tare nake zaune dasu ba kuma. Sai tayi murmushi tana fadin kafin dai ki kwanta ki kara shan maganin da aboki ya sayo maki dazun don ina ganin har da gajiyan aiki din a ciki. ZAINAN IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣0️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA JUMMA,AT MUBARAK FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA KARBA IBADUN MU YA SADAMU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN RANAN YA GAFARTAWA MAGABATAN MUSULMI BAKI DAYA ALLAHUMA AMIN, , , , , , , YAU MA DAI INA MAKI TUNI AKAN HAKKI DA KWABON KU MUKE SAMUN CIGABAN RUBUTUN MU A DAURE A BADA HAKKI DON SAUKE NAYI A KAI, , , , Sai faman shiyawa muke tun dare ake shirin dawowan mu kaduna taaraba mai yawa aka hadawa mami irin abinda zata bukata a birni wanda babu shi sai a irin wanan gari. Gashi tare da wanan tsohuwar zamu koma don mami ta shawo kanta da kyar ta bari a kaita asibiti a dubata ta dan kwana mata biyu ta dawo koshi sai da wanan mami ya sa baki ta yarda da hakan. Tun a can mami ke fadin wanan bakuntar zeey ce da Aisha ce don dai nasan hjy ba shiryawa zatayi da sauran yaran nan ba cewa su anty salma dake gida. Bamu bar garin Samu,naka ba sai misalin sha dayan rana tafiyace maidan jayawa tsakanin kaduna da garin sai dai a gurin su yake haka nikan a wurina kamar unguwane hakan ai. Don ko banza naga gari da kauyokan da nake jin sunan su a bakin mutane a da can da nake gida. Allah ya kawo mu lafiya don wanan karon da motoci biyu muka juyo don mai tarin motocin ya juyo abinshi ya barmu can. Duk da nasan mami tana wayencewa kan barin ta can da yayi don kamar rashin da,a ya nuna mata ga hakan don naji suna magana da anty Aisha a dakin da muka sauka kan hakan. Aisha tana bata hakkuri da cewa mami ki dai bincika wata kila yana da wani uzurine yai haka don kinga ai daga baya jiya ya turo da sako a rabawa mutanen nan din. Mun samu su mama Kande sun gyara gida tsab suna koma kan aikin girkin da za a ci idan an iso, da yake aikin nada yawa yasa basu kare ba kafin isowan mu garin. Sun fito sun tari kowa da murna da farin ciki ina tsaye wurin mota babu wanda ya kulani a wurin nikan driver na fara fitar da kaya na fara dauka na shiga dashi cikin gidan da nakw ji yanzu kamar gidan mune. Tsohuwarce tafe a hankali tana saye da glass din ido a fuskan ta sai farin gyale kwato dage yafe a jikinta dake saye da atamfan super mai ruwan haki da dorawa a jikin shi da manyan zane. Da sauri na karasa ina kokarin karban ledan maganin data rike a hannun ta zata shigo gidan ga su Rufaida suna gefe suna mata tsiya. A cikin ladabi na mika hannu ina karban ledan tace ba kaji ba yar albarka kedai kinfi wa yan nan kirki da hankali. Barshi kinji ba wani kayan nauyi bane a cikin sa ai, aiko sukayo min caaaa a kai Rufaida na fadin wanan ai bakin iya yi ne da ita ga kowa saita nuna ita yar munafukaine ai. Kai haba wanan zagin haka kuma fa ku daina wanan dabi,an bai da kyau ko kadan zagi harda iyayye. Rufaida ta hasala ta watsa min harara nidai duk da tace baida nauyi bai hana in karbi ledan a hannunta ba. Zama tayi a falo bayan ta iso da kyar don yanayin tafiyan nata yadda take yinshi a hankali ga tsufa ga ciwo dake damunta a jiki. Nan falo gaba daya suka zube sai nuna kauna ga juna sukeyi ni dai ina tsaye da ledan nama shagala ban sani ba. Banji fitowan shi ba sai kamshin shi daya doki hancina lokaci daya tare da muryan shi yana fadin watau nan ma kin biyoni ke nan ko ? Na gudo na barki can bai maki ba saida kika biyosu kuka dawo tare yana magana tare da daure fuskan shi kamar gaske . Ja,iri to baka tsira ba ai don gani ko na biyo ka din don ba fasawa zanyi ba da magana ta sai kagaji kayi zuciya ka fito muna da mata mun gani idan shika guduwa dama. Mami yaya akayi kika zo muna da wanan yar matsalan tsohuwar gida yana magana yana kallon mami din data daure fuskanta tun fitowan shi kamar ba ita bace ke dariya yanzu . Saidai jin ya ambaci sunan ta fake fadin cikin daga mai hannu please live me alone don't metion my name again cikin kara daure fuskanta gare shi. Oh mami rely iam sorry for what i have done wanan tsohuwar ne ta dameni kuma nasan ba bari zakiyi in dawo ba idan na fada maki kai tsaye zanzo inyi wani abu a nan a ranan nima tafiyan ai da niyar in komane idan na gama sai gashi ban samu komawa ba. O hjy ce ma ta dameka har kana fadi a gabana forgive me mami iam sorry wlh wani abu nazo yi garin nan na lake a cikin sa. Alhalin tunda yazo yana gida bai fita ba yana daki yana ragewa kanshi zafi abindake tsunkularshi kwana da kwanaki. Is your on business koma meya baro ka da garin mu dai ai ba zaka hanamu yin kwanakin da mukai niyar yi ba a can. Ya dan laso bakinshi yana shafan kai don ya fahinci mami ta hau sosai dashi kan abinda yayi din na barin su can ya dawo nan shi kadai. Ke wai lafiya kin tsawa mutane saman kai haka kina bin mutane da kallo don rainin wayau Rufaida ke fadi a hasale. Keko gulma mana tana bin bakin kowa da kallon abinda ake fada kamar ba yar aiki ba ta dinga shiga cikin mutane tana kutsa kanta. Ikon Allah da alama yar nan dai bata jin dadi a wurin ku meye matsalanta don ta tsaya a cikin mu ita din ba mutum bace kamar ku ai dan mutum daraja gare shi tsohuwar ke fada tana kallo. Zo ki zauna a nan gaki tsaye kinyo tafiya baki zauna ba take fada tare da kallona tana nuna mi wurin zama. Nace dama ledan nan ne ban san dakin da zan kai maki ba shine na tsaya na fada a dan marairaice. To kuma ji da abinda ya tsayar da ita a gurin ba tsayin banza tayi ba ta mika hannu in miko mata ledan dake hannuna. Mami tace na rasa me yarinyar nan ta tare masu a gidan nan da basu bata salama sai hattara da tsana. A,a in kinga hakan wata kila dai sun hango wani abune a gareta sukewa kyashin sa ko don yanzu ta karbe masu fada gurin ki. Su dai daina haka don ban so banyi sharawa da kowa ba da zan kawo ta gidan nan do haka ba zan dauki hakan ba gareta tunda ban bari uta ta raina ku ba. Gaban mami bazo na tsuguna ina fadin mami bani key in bude daki zan gyara ne kafin ki shigo. Ga dai key din gyara ki bari sai anjima yanzu dai ki kwashe kayan mu kikai min daki hjy kuma nata dakin ki kai mata sai ki koma dakin Aisha da zama ke . A, a barmu mu zauna dakin ta a tare dama kawatace ki n ga ai ko tausa tayi min a dakin idan ina so naji kuma dumin mutum a kusa dani ai? Ko ba zaki zauna tare dani ba kawata tana tambayana cikin dan dariya tana kallon fuskana. Murmushi na sake wanda yasa fararen hakora dan baiya diple dina ya dan lutsa daga gefen fuskana ina fadin ina so sosai hjy . Ya daifi ni dama ba zan zauna da kowa a dakina ba Aisha ta fada tana mikewa tsaye mami tace hakan baidai taso bane . A nan na barsu ashe baya barina wurin Rufaida tayi fushi ta mike ta koma daki su waya ta jawo tana fadawa uwarta wai mami tana disgata kan yar aiki ita gida zata dawo don hakan da ake mata yana ci mata rai. Duk da mami tace kada na gyara dakin ba yarda na barshi hakan ba don sai dana kara gyarashi tas na dawo dakina na gyarawa hjy yadda ya dace na dauko wani zanin gado dakin mami mai kyau na shimfida mata. Falon na dawo inda na samu sun fara cin abinci har lokacin mami na zaune tare da yaran ta gaba dayan su a wurin sai salma da hjy ma kakarta ce don itace ta haifi uwarta a gurin tana nuna jin dadin ganinta. Yau zee kici abinci ki dauko zanin gado a daki ki shimfidawa hjycdakin ki . Nace na dauko na shimfida mami tun dazun ai tace kai zee na gode sa wanan karama hjy din da kike yi yamafi min ku zauna tare da zamanta da wanan mara moriya din tana nuna Aishan ta. Mami nice banda moriya bari ki gani har wanka zan dingawa hjy har ta bar gidan nan kuwa hannu mami ta watsowa Aisha tana fadin karbi naki nan ko uwarki Ramatu tayi kadan tayiwa hjy wanka yanzu ai. Abinci na diba na koma can gefe guda ina dan duban inda zan zauna mami ke fadin wanan abinci zai ishe ki ke nan zeey ? Ya isa mami na fada ina nufar can nisa dasu don in zauna tsohuwar take fadin wanan ya da dadin zama take wallahi. Wanan ba irin yarwa bace a cikin ahali yarinyar ta samu tarbiya a gun uwarta kada ki bar wa yan nan marasa ta ido su kore maki ita gidan nan. Ai ba zan barsu ba mami ta fada duk wanda bai iya zama da abindanake so yayi gaba hanya a bude yake mai ai. Baidai kai can ba kowa ya tsaya a matsayin sa tsohuwar ta fada mami ta nuna salma tana fadin sune ai marasa hankalin yarinya ta girmamasu sai sun zubar da mutuncin su gareta zasuji dadi. No mami ba salma a ciki zancen nan don da kanta zeey ke fada min tana jin dadin zama da anty salma sosai idan muna hira da ita. Salma tace mami ni ina ruwana da harkanta gidan nan tunda bata tare min komai ba ga kowa. Shine daidai hakan ai kinji itama tana yabon ki a bayan ki gashi yanzu yar uwan ki tana fadi kuwa kafin ta juya wurin yaya jafar tana fadin. Kai gwauro ba zakaci abincin bane kai ko sai yayi sanyi ka tsikara ka tashi tunda baka aje ba balle a dumama shi. Zaki fara tsokanarshi ko hjy yaya mamud ya fada yana mikewa sai tsohuwar tace gashi ko yanzu ya iya yaji saboda korafina ba kuma zan fasa ba idan baiyi abinda nake son yayi ba. Ya dago kai yana fadin me kike ci na baka na zuba hjy kwana zan fitar da mata kowa ya huta ina shike nan. Shike nan kuwa kaga an wuce wurin haba ko kai fa mutum kamar me jin warin mata a tare dashi. Barshi hjy rainawa mutane yake son yi wanan karin ko ba zan saurara mashi ba don naga wasa ya dauki zancen nan. Mami ai na fada maki kwanan zan fitar kowama ya huta sai mami take fadin yar gidan wanene yarinyar da zaka fitar din ? Mami ai ko yar waye zaki gani idan Allah ya kaimu ranan dinan ki sai naba kowa mamaki a gidan nan sosai. Mami ai kin san sai yar gwauna ko wani seneter don irin su yaya Jackson sai diyan manya a kasan nan ai Aisha ta fada tana kallon shi tana dariya. Shima murmushi yayiwa zancen Aisha din yace kedai bari zan yi surprise din kowa idan na tashi sai hjy tace kada dai kaiwa mutane zaben tumun dare garin ruwa idon kan nan. Ni makoho ne aka fada maki ai kece mai bani shawara ki bari ki gani idan ban zabo da kyau ba sai ki fadi hakan. Wayan shi da yai kara ya dauka yana duba kafin ya mike ya bar wurin yana wani magana kamar yare sai hjy ke fadin. Itace ta kiraka kake gudu kar muji me kuke fada dama ka zauna da wanan yaren naku baji muke ba mu. Daga inda nake ina dan murmushi wani tunane yazo min nake fadin a raina zanso nima inga wanan zabin na yaya jafar yadda yarinyar zata kasance. Nasan badai kyau da kudi ba kan kamar yadda yake da kyau din nan ga ilimi ga wayewa dole wace zai aura din itama ta kasance kamar ai. Ni daya ke faman tunane har naji abincin ma ya fita a raina ina tuna sukan sunji dadin su uwa kudi uba kudi haka. Suma gasu kudi wai ina mutanen nan zasu da wanan dukiya hakane idan da nice su ai ba zan nemi wani kudi ba zan zauna in hutane kwai inta jin dadi na a gida. Zeey zoki kwashe wanan kayan abincin nan wurin nan ki dawo ki kai hjy daki tayi sallah ta dan huta. Firgigit na dago kai tare da fadin to mami ina kokarin mikewa a inda nake zaune din. Sai dana gyara komai mami na zaune gurin tana waya da yayan ta da muka baro dazun garin su. Hjy muje in kaiki dakin azahar yayi tun dazun na fada a cikin ladabi ina kokarin daukan kayan ta gyale da ledan maganin ta dake gefenta aje. To yar nan har na fara gyangyadi ko a wurin ba tare dana sani ba tana mikewa tare da kokatin tattaro gyalen ta dake gefe. A hankali muke tafiya zuwa dakin har muka kai dakin yayi dan dumi sai kamshi ke tashi a cikin sa ledan na aje a gefen gadon kafin in nufi kofan ban dakin in bude mata shi. A, a kagani ba nan yayi min gara in zauna dake da in zauna da wanan mara moriyar Aisha wace ko kara ba zata iya kawar wa kanta ba balle wani. Bayan mun idar da sallah dukkan mu a nan kasan muka kwanta nabawa hjy filo tayi matashin kai dashi niko ko filon ban samu matashi dashi ba sai barci. Ban falka ba sai da hjy ta tashini don inyi sallah la,asar nasan yamma yayi saboda dadin barcin da nayi. Na idar na mike zuwa dakin mami bata dakin yasa na samu daman kara gyara dakin da yake ba wani datti a ciki dakin A falo mamice da yaya mamud suke magana haka yasa na juyo zan koma dakin mu indan gyara don ko ba komai da zan wa dakin ban dakin yana bukatan wanki koda yaushe. Na wanke na fito ina daukan filon data kwanta a kasa take fadin yar nan idan kin rage sai ki kaini falo in zauna don yamma tayi yanzu. Na amsa da to hjy muje mami ma tana falon zaune tare da yaya mamud . Wai ni iyalin shi mamud din suna inane don banji duriyan su ba tun dazun ina a nan gidan suke zaune ne suma. Suna Abuja an barsu a can da zamu dawo kaduna yar ta kifen tana nan dai da halin ta har yanzu bata canza zani ba ko ? Dan dariya mai sauti nayi ba tare da nayi magana ba don ban san abinda zance da ita ba. Falin muka fito tafiyan minti daya daga dakin mu zuwa falin saida muka biyar muna lalabawa kafin mukai saman kujeran ta zauna a hankali. Mami na fadin kun lalabo kun fitone hjy take fadin yar nannta lalabo dani ina dan jin dadin hakan yarnan akwai kirki sosai. Allah yasa kiga aurenta hjy amin ta juya tana fadin kada ki tsaya dogon bokon nan na zamanun nan dake batawa mutum lokaci sai a dauki lokaci yaro na zubar da irin sa duk wata. Yaran nan da kun gane ai da ku aurar da su don har sun wuce munzali aure a yanzu . Hjy kin san ai aure dan lokaci idan lokacin sa yayi koda shiri ko ba shiri sai ayishi a lokacin. Zaune yake saman farar kujeran roba a gurden din gidan mai dauke da dogayen itatuwan da ba wani zugun ganye suke dashi ba sai dai tarin tsayi a gasu. Babu wani abinda yakeyi duk da sytem din shi dake gaban shi a bude ya kasa aiwatar da komai sai faman tune a ranshi. Yakai hannu a hankali ya rufe sytem din ya dafe kan shi dashi yana ci gaba da tunanen shi ya rasa yaya zaiyi ne da wanan hukuncin da yake kokarin yakewa a ranshi. Allah ya gani bawai yana son yarinyar da mami ke son hadasu bane zai dai amincene don farin cikin mahaifiyar shi kawai. Don yadda mami dasu hjy suke nuna mai muhinmancin yin hakan gareshi saidai shi Allah ya gani bawai ya shiryawa aure a wanan shekarun nasa bane. Anya kuwa idan yayi gangancin yin aure a yanzu ba zai jawa kanshi matsala bane ga hakan. Kai ya girgiza shi kadai tare da fadin dole yai juriya da fin karfin zuciyar shi don ya samu su rabu lafiya da mahaifiyar su. Muryan Rufaida dake fadin ki tabbatar da kin wanke kayan nan tas wallahi kada inga jirwaye a jikin su banza kawai mun zuba ke nan dake a gidan nan. Ke gaki kin samu wuri zaki mike kafan ki kiji dadi ko to wanki har na tufafina duk ke zaki dinga wankin su a gidan nan daga wanan ranan. Nima ga nawa Nazira ta fada shegiya munafuka mumuke zamuyi maki a gidan nan ba tare da mami ta san da hakan ba ta jefo min unders din ta a fuska. A daidai lokacin daya karaso wurin don jin zagin da suke min din yayi yawa a lokacin. Yana tsaye hannun shi duka biyu zube cikin aljihun wandon shi kallon kayan yayi yayi saurin kawar da idon shi ga kayan. Ya dago yana kallona su kuma sai dan kame kame sukeyi suna fadin sannu da hutawa yaya J ke daga daga nan ki shige ciki ya fada yana kallona. Da sauri na bar wiein kayan na koma ciki dama wurin su mama kande nake zaune suka sameni suka ban wanan sikin wankin. Nan nabar masu kayan nasu na shige ina share hawaye babu mami a falin sai hjy dake zaune ita kadai ta kurawa tv ido tana sauraren malam daurawa dake wa,azi a tashan sunna tv. Na zauna take fadin yar nan akwai kura kuren da mukasha tabkawa a rayuwa sosai a baya wanda sai yanzu kake jin bayanai akan abubuwan da bamu sani ba a can baya. Jin tana magana ban bata amsa ba yasata dago kai tana fadin kinga kamar da can baya ai bamu sancewa ga lokacin da mutum ya dace yayi , , , , Ido ta kura mi don hawayen data ga ina sharewa a lokacin salati ta saka hankali tashe tana fadin . Waya tabaki me akai maki yar nan ki fada min wanda ya musguna maki yanzu don nasan ranki aka bata haka. Muryan mami ne ke fadin hjy lafiya wa aka batawa rai zeey lafiya me ya faru yanzun fa kika bar falin nan da raha da hjy . Mami ba komai ba komai kamat yaya ta fada tana kallona tana zama saman kujera takon kafab shine yana shigowa daga kofan baya yake fadin. Mami kiwa yaran nan iyaka da yarinyar nan abin is too much sun mayar da ita boya a gidan nan . Mami idan baki iya masu magana su daina don Allah ki mayar da yarinyar nan gaban iyayyenta haka cin fuskan yayi yawa. Ya kwashe komai da yaji yana fadawa mami rai bace yana gama fadi ya juya ya fita hjy ma tana masa magana bai tsaya sauraren ta ba ya fita don bai cikin dasin rai a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣1️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA TARE DA IMANI A ZUKATAN MU AMIN DON ALLAH KADA KI FITAR KARKI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA KI TUNA DA AKWAI RANAN HISSABI YANA NAN TAFE. Ki biya ki karanta a cikin salama yar uwa kan dari uku kada a tsayar dake ranan da kowa tashi ke fitar dashi sai abinda ka shuka. Yau tun safe Lantana da haibaici ta tashi a gidan don kawai Abban mu ya kwana a dakin innar mu kuma taga Abba ya fito ban daki da asuban farko. Saboda ta hana idon ta barci duk ranan da Abba ya shiga wurin innan mu haka take kwana leken tagar dakin ta don ganin halin da suke ciki. Wanan dalili ke sa Abba ko zai shiga dakin sai yaji wa,azi da nasiha abokan shi ko wani na kusa dashi akan yadda yake wofintar da innan mu har yan waje suka gane hakan. Hakan ba abin mamaki bane sanin ko wacece uwar lantana a garin dan zaman kanta takeyi tana sana,ar tuwo tuwo. Haka kuma take mu,amula da maza bata boye halinta har mutanen gari suka ki auren yarta data taso shine Asabe kakar mu taje ta kwasowa Abban mu ita. Don kswai a lokacin suna dan dasawa da mahaifiyar ta har suka hada wanan alakan cewa idan Abban mu yana son lantana yazo ya nemeta da aure ko za,a dace ta haifa mai diya maza a gidan. Bayan auren yanzu kuma ya fita a tsakanin su suka koma kamar annabi da kafiri tun bayan dataga ta haifi namiji din duk da dan ba lafiyayye bane yazo. Innan mu tana bakin murhu tana hura wuta ta fito ta zauna a kofan dakin ta tana fadi a fakace. Yau kuma su oo me aka samu da farar safiyan nan ake wanan duke a gaban murhu ko anyo aikene daga bariki za a sha dadi haka ? Inna dai yi tayi kamar bata jita ba taci gaba da fadin muna nan dai idan tayi wari maji ai . Gashi dama ko a gida a shedesu da dan hannu balle anje birni anga banza aita wawurowa ana kawowa gida. Hakan bai mata ba ta sake fadin wasu dai sunji takaici ya ko auren fari babu har ta shiga duniya yawon banza . Har azo anawa mutane feleke a gari a saka a canza duk da kayan zina to ai haka ba mamaki tunda tsohuwa ma ta tsufa bata san ta tsufa ba ka jaraba kullun ana makale da naji ana abu daya diya tayi da kaitai a birni uwa tayi nan da tsoho. Allah sarki dadin abun dai da tsohon sunna tsohuwar ke makale ba mazan wasu take ci ba a titi kamar macijiyar da bata ramin kanta. Sai dai anyi rami tayi shige ko tabi darnin makwabta ana dannan ta ana sukawa akanta saman titi da tsufanta diyata dana makwabta suna kallo. Innalillahi aikuwa dama inna takan tara mata na kwanaki kafin ta gaji ta bata amsa koshi sai idan taji ta tabo zancen diyan tane zata samu mai zafi daya ta fada mata taja bakinta tayi shiru ta barta tana haushi. Wani lokacin har makwabta sai sun shigo rabon ta akan tayi hakkuri ta daina idan kuma sun gaji sai tayi tayi sai ta gaji zata kyale don kanta. Wani lokaci kuma har uwarta takan tako gidan tazo taya ta fadan suyi harsu kare babu mai tankasu. Yau din ma da taga haka jin amsan da inna ta bata ta yafa gyalenta ta fita zuwa fadawa uwarta abinda ke faruwa harda karya da gaskiya ta kwasa ta fadamata. Sai gasu tare sun dawo ita haushi uwarta haushi Allah ya taimaka inna ta gama girka dan taliyan hausa da take dafawa yara su karya dashi din Abba yace kuntu billahi baida ko kwandala a hannun shi da zasu karya. Amma yana fita ya shiga dakin lantana data haushi da masifan ai ta ganshi ya shiga ban daki daga yau sai ka koma ka mannewa tsohuwar matar ka tunda duk kokarin da nake maka baka gani kai. Halin maza sai su nan Abba ya dan fara kame kame yana rarashinta har yakai ya dauko dan kudin daya kwana dashi hannun shi ya mika mata su gaba daya don kawai ya samu ya shawo kanta kada ta gujeshi kamar yadda ta fada din. Shine bayan fitan shi inna ta fito tana hura wuta ta ja inna da wanan masifan har yakai inna ta mayat mata da martanin da yai mata zafi shine uwarta ta shigo da masifa. Tana fadin sai tayi karan innan mu don kazafi wai inna tayi mata a cewan ta jin fitinan yayi yawa yasa Asabe fitowa don da farko batayi niyar fitowa ba. Ji datayi tace zata kai karan inna ga hukuma yasa ta fito tana fadin ke mai tuwo baki tunanen me yarki itama ta fada mata . Har ta bata wanan amsa itama don haka kawai ba zata fada mata ba ai don kawai an mayar da haulatu mai hakuri a gidan tana kawar da kai ga abinda yarki jeyi mata ko yaushe. To tsohuwar banza kin fito ki shigar matane ko me yanzy haulatun ce mutum a wurun ki tunda yarta na can birni tana bin maza tana zuwa maku nan da abin duniya yanzu sun koma abin son ki kuma ? Jin haka da innan mu tayi ta bude labulen kofan ta tana fadin saukin abindai kafin ta fara aikatau wasu sun tafi butnin sunyi har saudiya yin dandin kasa mai tsarki basu dawo da komai ba kasan nan sai tsaraban shegu. Idan kuma suna da uba yau a fito muna da uban su mu gani don haka kafin yata taje birni bin maza tsohuwar banza ta fara zuwa ta dawo muna garin nan da tsaraban annoba. Yau zaki san kin tabani garin nan yau zan nuna maki ko wacece ni a garin nan inna tace idan kin tashi kisa a rufeni dan makullin ya bace iyaka ke nan. Lokacin har yara da mata da muke makwabtaka dasu sun cika gidan suna kallo da saurare. In dai barikin ne ai iyawace don karshe sai an koro yar taki da ciki kowa ya gani a garin nan lantana ta fada cikin jin kunya da nauyin yaran dake ihu bayan fitar uwarta don halin su ya ishe mutanen unguwa dama. Har wurin aikin Abban mu lantana da uwarta suka sameshi suna fadin sai sunyi karan innar mu don tayi masu kazafi da cin mutuncin da ba a taba masu shiba yau. Abba ya shiga ba mahaifiyar lantana hakkuri yana fadin ta barshi da inna dama halin innan mu yakai mashi ko ina a gidan. Haka dai Abba ya samu ya lalaba su suka bar gidan bai dade ba shima a waje sai gashi ya shigo yana kwalawa inna dake bandaki kira . Bata amsa ba saida ta fito ta bayan shi take fadin gata ai tana sauraren shi. Ke don baki da mutunci yanzu har kika iya bude baki kika zagi uwar lantana a gaban ta karya suka fada wayasan inda yar taki take a birni dama. Allah sarki hakane dama ai na sani kaima yaran ba damuwan ka sukayi ba ai tunda tun lokacin daka mikata wurin yar uwarka har yau baka taba bin bayanta kaga inda take zaune ba don an hanaka zuwa gani don a samu abun fada min. To bari kaji malam idan ku dakai da uwar matan naka bakuyi karana ba yau ni zanyi naka a garin nan duk inda kakai min ya sai ka fito min da ita don wanan abin ya isheni. Ni ga Allah na dogara nasan irin tarbiyan dana ba diyana don bata gaji shashanci ba a gurina balle taje tayi shashanci a birni. Yanasu yau ke da bakin kike fadin zakiyi karana kan yar cikina a mata ya baci inna tace kwarai kuwa bello ta fadi sunan Abba ba sakaye kamar yadda take kiranshi da malam. Mamaki ya kara kashe abba jin abindata fada sunan shi gatsau haka babu sakaye data sabayi mai don gabadaya ta birkice masu a gidan. Wani kalon kalo suka watsawa juna kafin Abba ya kuta yana fita daga gidan inda lanta taji haushi cikin daga murya take fadin tunda har kika zageni dani da iyayyena ke kuwa sai yar taki tayo abin kunya birni an korota ta dawo maki maga ta tsiya. Nikan unda na shige daki nabar mami na fada a falo ban fito ba sai bayan sallah isha,i koshi din abinci na fito. A falo gaba dayan su suke in ka debe mazan da basu rigada sun shigo gidan bako a lokacin don ko hjy a falon tayi sallah bata shigo dakin tayi ba nasan saboda tafiyan ne yasa ta zauna a nan bata dawo dakin tayi sallah ba. Banda hara ba abindaya shiga tsakanina dasu Rufaida duk da na gashesu a cikin jam,i saidai su basu amsa min ba. Sai hjy ce ke fadin yarnan yanzu nake zancen ki a raina ina batun aje a dubo min ke a daki ko lafiya kika shige har wanan lokacin ? Ina zancen dai ai ya wuce tunda kinji uwar ku ta tsawata kan hakan suma kina ganin su da shegen son jiki suke ta yaya zaki dauki kayan kasan ki har kiba wata wanki can. Haba haba hjy a daina wanan zancen tunda mami tayi mana fada a kanshi dazu ba wanda zai kara bata irin wanan aikin acikkn mu ai tunda mami ta hana abata Aisha ke fadi. To uwata hanani in fadi tunda kun shuka rashin gaskiya wa yarinya baku son a fada kuma kai kuma dai kazamai ne wallahi. Ta fada rai a bace tana mai kawar da kanta ga kallon su sukai tsuru tsuru don mami na falon itama ta kafesu da idanu. Rufaida na shirin mikewa tabar falon don takai kololuwar cika tana batsewa wai akan yar aiki mami tana wullakantasu don kawai taga gidanta ne yanzu dan uwan mahaifin su ya rasu yasa ake masu hakan. Batakai ga tashi ba taji sallaman jalal yana washe baki ya shigo da ledoji niki niki a hannayen shi yakai gaban mami ya aje lodojin yana zama a kujera tare da fadin. Wassh Allah yau na gaji da yawa mami tace da kai me ke nan fa mami tunda aka fito daga sallah yaya jack , , , , Bai karasa fadi ba saboda hararan da mami ta watsa mai yasan me take hararan shi dashi yace a wani yanayi i am sorry mami na mantane kin hana mu kirasa hakan ni kuma bakina ya saba da hakan tun a can. Rufamin baki ku kun fada inagana waje jalal ka fita min a ido duk kuka bari wanan sunan ya shigo kasan nan raku saiya baci sosai. Yana dariya yace yanzu dai mami ba wanan ba kinga ledan nan wai duk na tsohuwar nan ne yaya ya ban kudi a hado mata wai kada taci abinci da dare sai wanan din shi ya dauka nan irin can ne da tsofi sukecin wanan dadin yana magana yana zamowa daga saman kujeran yana kokarin budan ledan. Wanan ya hana rufaida dake cika tana batsewa tashi don tun shigowan shi falon ya dume da kamahin suya irin na yan gayu ba suya na gida ba wanda yasha kayan hadin sanadarin zamani. Hannun shi mami ta buge ya jaye yana fadin wassh Allah mami zan bude ku gani ne ai ko ya fada yana dariya. Mikawa hjy abinta babu maici a cikin ku wurin sai idan ta gama ta baku ragowa idan zaku ci. Haba mami ta bamu ragowan ta kuma bayan ta gama zuba mai miyau da goro zamuci salma ta fada tana kallon mami din. Hjy da sai yanzu ta fahinci me ake nufi lokacin da mami ke kallon jalal tana fadin ya mikamata take fadin au me muka samu ne wai. Bakiji bane hjy wai Jafar ne yasa a sayo maki wanan shine syke son su saka maki rani a ciki don suna yan kwadai. Ja,irin miskili ya gama babautan nasa yana neman shiri danine kuma yanzu dazun fa ya gama fadin me na biyo ku yi nan nazo in sakawa mutane nauyina sai gashi shiya fara daukan nauyin kuma ? Haka kika fada ko bari ya dawo saina fada mai wai badan Allah ya saya maki ba neman shiri dake yake ya sayo maki. Kaji ja,ira zaki hadani fada da wanan mai kama da yan ruwa yazo ya hanani shanruwa a gidan nan ke nan. Ya jalal yaga sun tsaya surutu mami bata sab sanda ya jawo ledan ba yana fadin bari nidai na bude don inyai sanyi bana iya cinsa kuma. Yana bude ledan farko wani kanshi ne duk ya game wurin leda daya ya tura a gaban yan mata yana fadin ku ku dau wanan wanan kuma hjy wanan nasu ne idan sun shigo. Ya mike ya isa gaban tsohuwar tare da ledojin a hannun shi yana fadin hjy mu muci wanan ko tace kaidawa ke nan miko min nan dagani sai yar nan da take dawainiya dani zancisa. Kaji hjy kuma ya wuce ki bata fifike ne a ciki kilama bata taba cin suya irin wanan ba ai Nazira ta fada a daidai lokacin da suke shigowa gidan shida Jamal. Yau kan ya wanke kanshi a wurin tsohuwar da murna da lale marhabin ta tare shi tana fadin kaga mijin arziki wanda yasan zafin iyalin shi. Mami na masu dariya yazo gaban mami ya dan dukar da kanshi wanda kamar hakan al,adan yayan mami ne don har ya mamud haka yake mata da girman sa in zai fita ko ya shigo zai duka mami ta ahafa kansu tana saka masu albarka tare da fatan alheri a garesu. Don tun ina mamakin hakan har nagaji don na saba da ganin hakan wurin yayan gidan maza ko Aisha da take mace kamar zata koma cikin uwar wani lokaci idan abin ya motsa mata ko yanzu tana zaune tunda tai magana da farko bata kara magana ba a wurin kowan su nakan waya suna abu daya charting ko dawa soke yi oho ? My friend an dawo ke nan mami ta fada tana shafa kanshi tare da fadin ubangiji yayi maku albarka ya kare mun ku a duk inda kuka saka kafanku. Tashi yayi ya nufi wurin hjy ya zauna a kasan carpet tare da riko hannun da ta dauki cinyar kaza tana ci yakai a bakin shi ya gutsura kadan kafin ya kai mata itama a bakinta . Ni dai ina gefe zaune a kasa daga gefen hjyn ina kallon ikon Allah tare da mamin wai yan gidan mami suke kwadayin nama haka ? Wanda nama sai an mayar da saura kitchen don sunci ya ishesu wanan wani irin nama ne hakan don idan kaga mami ta sayo nama a waje to kilishi ne zata shigo dashi mai yawa kowa yaci har a ture saura su mama kande su dauka.. Dan albarka hjy ta fada tana hadiyan naman dayasa mata a bakinta ta gutsura kowa falon na busy suna cin naman suke gaidashi dashi. Dabi,an shine kyaluwa dan haka yi yayi kamar baiji su ba hjy ta juyo tana fadin taso mana yar nan ki diba kinyi zaune kina kallon kowa nacin abin arziki. Saiya dan juyo ya kalleni guri da nake zaune din ya kawar da kanshi kamar ba kowa a wurin . Na mike nazo gaban hjy din yana zaune har lokacin yayi rigingine a wurin kafanta idon shi a carpet nakai hannu zan diba Nazira tace Ke dakata don Allah menene haka zaki saka mata wanan hannun naki mai dauda a cikin abu haka kai tsaye ba tare da kin wanke hannu ba. Cak na tsaya daga daukan naman da nasoyi din ina kokarin mikewa a inda nake gurfane don barin wurin. Ke diba ki wuce ya fada batare daya dago kai ya kalli kowa a wurun ba ya fadi hakan sai jamal yake fadin haba Nazira ku daina irin hakan don Allah dai. Bazasu bari ba don da zasu bari ko ance suyi wani abu kan yarinyar nan ai basuyi ba kuma yadda nayi masu yau. Me ake mata idan ba iya yinta ba taga yan aiki a wurin nan ne ko taga su kande na zama a cikin mune haka su ? Nazira zan saba maki a gidan nan fiye da tsamanin ki to bari kiji zeey da kike gani daya kuke da ita a gidan nan yadda na daukeku dasu Aisha haka itama nake daukanta don ba wai aikin kudi aka kawota yiba yadda kuke tsammani. Rokota nayi gurin iyayyen ta suka taimaka min suka ban ita a cikin mutunci sau nawa wai kuke son in fada maku hakane wai ? Look akan yarinyar nan zan sabawa yarinya a cikin gidan nan ko wacece me yarinyar nan ta tsare makune wai haka kuke sakata a gaba ko yaushe ya fada a hasale cikin daga muryan shi dasai ranshi ya baci akejin shi irin hakan. May be don sunga ta fisu kyaune da tsari suke kyashin ta jalal sarkin barkwanci ya fada kai tsaye yana masu dariyan kyaita. Kai amma jalal din din don Allah kada tasa taji dadi har taji dadin raina mutane a gidan nan ta dauka wani kyaune da ita. Garin dauko naman saboda rawan da jikina keyi na dauko gefen fifiken kazan dayasha carbej da albasa dasu maggi curry da sauran hadi namike tsohuwar na fadin baki dauki abin kwarai ba nace wanan yayi min yanzu naci abinci na bar falon ga baki daya har lokacin jamal da jalal suna cacakan ya matan a kaina. Jalal ke fadin wanan kina ganita idan tayi clean gidan nan ma baya daukanta ke zeey fa idan ta waye ba karamar classic lady bace wurin nan. Dakin na shiga na aje naman don naji ya fita min a rai don disganin da nazira tayi wurin daukan naman a gaban kowa. Nima fa mutum ce kamar kowa da suke min haka don kawai ina yar kauye kuma diyar tallaka tallakama mai faci. Ina ban daki nake wanan fadan a raina na fito ban tsaya jiran komai ba na hau kujera na kwanta har barci ya daukeni ban sani ba don ban san lokacin da hjy ta shigo dakin ba bayan sun gama hiran su a falon don ko hidimar da nakewa mami ranan ban samu yimata shi ba. Koda mami ta rako hjy dakin ta samu ina barci bata tayar dani ba ta kyaleni hakana sai cikin dare dana falkone naga wutan dakin a kashe. Washe gari da safema motsin hjy ce ya falkar dani na tashi nima nayi sallah na idar na zauna a wurin hjy ta shafa tana fadin in koma in kwanta tunda ido akwai barci daga haka taci gaba dajan tasbahan ta. A daidai lokacin da nake shiga na gyarawa mami dakina falka kamar an tasheni har lokacin tsohuwar tana zaune a inda take. Mikewa nayi ba tare danayi magana ba na nufi dakin mami din ko a nan ma itama zaune take tana azzakar din safiya. Ban fito daga dakin ba saidana karasa komai na dawo na samu hjy ta dan kwanta a lokacin banyi dogon motsi ba wanka nayi tare da kara wanke ban dakin har na shirya a hankali duk tsohuwar tana barcin safe wanda nasan na gajiyane. Sai bayan goma da rabi ta falka lokacin mami tayi mayawa a dakin yakai sau uku tana duba mahaifiyar nata. Ruwan wanka na hada mata tayi wanka na taimaka mata data fito har ta shirya saiga abin karyawa an kawo mata har daki yaran gidan suna shigowa daya bayan daya suna gaida ita da kwana. Har suka dauke kafansu sai Aishace bata shigoba nasan bata tashi bane don ita sai wuraren sha biyun rana dama take tashi barcin safe ko ma zuwa dayan rana. Nan muka zauna muna hira da hjy don ban yarda na fita ba ko karyawa a cikin na tsohuwar na karya dashi take tambayana ni yar wani garine ? Nace ancau hjy tace ashema yar jaharnan ce ke na dauka ko yar shiyan jalingone ke ko bauchin don na ganki da zubin fulani. Nace innatace dai bafullata Abban kuma bazzagene shi yar nan da asalin ki haka har yaran nan suke maki wanan tsiyar haka ? ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣2️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU MASOYA UBANGIJI YA DAUKAKA MUSULUNCI A DUNIYA AMIN, , , , Banyi zaton akwai macen da zata kai sha shidda a yanzu ba wace bata san zata mutu ta koma wurin ubangijin ta ba da har za a hada da Allah da annabi ta rufe kunne da ido don rashin tunawa da Allah dayai mata rai da numfashi da take takama dashi a duniya wanda ubangiji zai iya karban abinsa duk sanda yaso . Yan uwa mu kulla da daraja da nauyin wanan sunan biyu idan ance Allah da annabi a zatona angama da musulmi ashe abin ba haka yake ba a wurin wasu. Allah kasa mufi karfin zukatan mu ya Allah ka bamu cikawa da imani amin kada ki karanta idan baki biya ba mai turawa na barki ga Allah shi yasan tsakanin mu dake. Sallama akayi daga kofan dakin yayin da mu kuma dariya ya dauke muna hankali a cikin dakin don tsohuwar dariyan labarina dana fara batane ina fadin garin mu ai kauyene kuma yan garin muma kauyawane a cikin sa don kaka hajiya bata kaiki tsufa ba amma bata wanka daga jumma, a sai jumma, a take wanka tunda wai bata da miji da zataiwa wanka. Sallama ya kara yi nice na karba a cikin raha da walwala don dan zaman mu da tsohuwar yasa na mance da duk wani bacin rai dana kwana dashi a gidan. Dan miko min wanan kawar da wanan gurin nan sai duba can ki miko min abu kaza dauki wanan kici hakan yasa na manta da komai dake a raina a lokacin. Wa,alaikum sallam na fada don hjy ita dariya yaci karfin ta a lokacin itama dai cikin dariyan take amsa mai haka yasa ya turo kofan gaba daya ya shigo. Saye yake a cikin farar jallabiya mai laushi sai wani maiko takeyi ashe jallabiyar ma suna suka tara sabanin da danake masu bugu daya don duk jallabiya da farko daya nake daukan su sai zuwa gidan mami ne na fara bambanta jallabiya yanzu. Yakaraso yana tako kamar wani balarabe dashi har zuwa kujaran da hjy take zaune sama a cikin hausan shi mai kama dana dan koyon hausa din. Yana fadin wanan dariya haka hjy kamar an gafarta maki yau fa don nidai badon nasan iyayyen su ba sai ince su din jinin labawan asaline . Don hasken jikin su yafi kama dana larabawa a gidan ga tsayi duk dadai shi yaya jafar din ya fisu tsayi sosai a cikin su sai jamal da jalal saidai basu kaishi tsayi ba su zan iya cewa su din kamar mahaifin su suka kwaso don ko ban sanshi a fili ba na san shi a manyan photunan shi dake falon gidan. Don shi mutum ne fari dogo ga tsayi ga kyau kamar shi yayi kansa wurin halitta duk da ya manyata a photunan lokacin dayayi su hakan bai hana kyau shi fita ba a fili. Hakan yasa nake kasa bambanta tsakanin su da dan nasa ko a cikin su wayafi kyau haka. Shi yaya mamud duk da farine sol baikai yan uwanshi tsayi ba yana dai da nasa gwargwado sai Aisha da ta biyo mami sak wurin kama. Don ba inda ta rage mahaifiyar tasu sai dai idan halin mahaifin su ne ta kwaso na rashin hayaniya dason motsa jiki don mami kan ita da alama ba mai yawan son jikibane ita don wani lokaci zan samu tanayin abu da kanta sai nazo in karbe ta. A cikin dariya hjy ke labarta mashi hiran mu tana kwasan dariya fuska a daure ya dan dago ya kalleni tare da kawar da kanshi duk lokaci guda. Ina tsugune nake gaidashi da kwana tare da mikewa don barin dakin duk da ina tunane a raina ina zan dosa idan na fita don gudun haduwa da yan matsalan gidan mami din yan kafi mai abu iko. Don ni sai daga bayane ma nasan ba mami ta haifesu ba a wurin anty Aisha yadda nazo gidan na samu sunayin abu a gadarance da yadda mami ke nuna kamar itace ta haifi abinta. Ina kuma zaki muna hiran mu kin dauko ban labari ina sauraren ki indon wanan ne ai shi nasan yanzu fita zaiyi a dakin don ba zama zaiyi ba ko kunya fada a gaban shi kikeyi. Dawo ki zauna muyi hiran mu kinji jikata ta kaina aini kin ganni nan ina son jin irin labarin nan sosai wallahi don nima kinga daga karkara na fito ai. Idon shi a waya kamar mayen waya ko computer dana sa mai yake fadin wani No kuyi hiran ku ni nawa nakeyi nan . Tace dada Asabe kowa kikace sunan ta nace a sanyayye don kasancewan shi wurin nake fadin Asabe ne. Ta nuna min bakin gado tana fadin zauna mana a tsaye zamuyi hiran haka na kai zaune a dan takure. Yanzu mahaifiyar ki dai tana tare da Abban ki ko ta tambaya take yanayi na yacanza a hankali nace suna tare da Abbanmu har yanzu. Saidai ba a cikin dadin raiba don Asabe tasa Abban mu yai wani auren wai don innan mu diya mata take haihuwa ita kuma bataga amfanin diya mace ba. Shima dalilin turoni birni wurin mami da Asabe da lantana sukayi wai nazo inyi aikatau a nan don hakane kawai za a morewa diya mace na karasa ina share hawaye. Kai ya dago ya kalleni a cikin mamakin jin abindana fada din na zancen Asabe ga innan mu da muka bude ido dashi a gidan kullun sai tayiwa inna gorin shi. Haba haba yar nan kada ki kuka mana nasan wanan zancen yana da ciwo sosai don baku ai kukayo kanku diya matan ba wasu ma nacan suna son diya matan kamar suyi hauka basu samu ba ita tasan baiwan da Allah yai maku dayayo ku diya mata a garesu. Abin mamaki sai naji ya saka muna baki a hiran mu yana tambayana ku nawane a wurin mahaifiyar ku da har take fadin hakan ? Mu bakwai ne nice babba a dakin mu sai kanne guda shidda dana bari tare da innar mu a gida. Babu ma wanda aka wanke a cikin ku ke nan tunda kece babba ashe kai wasu mutane da shishigin tsiya suke har da Allah sukewa izzigili. Shi mahaifin ki fa yaya ya tambaya sai na dago na kalleshi don ban fahinci mai tambayan shi ke nufi ba. Saidai na basu amsa da fadin yana nan kawai yace No ina nufin wani mataki ya dauka kan wanan zance Da Abba baya daukan zancen Asabe amma yanzu tunda ya auro lanta kuma ta haifi na miji sai ya sauyawa innar mu damu ga baki daya a gida yanzu ba ruwan Abba damu kamar da can baya na fada idanuwana suna kawo ruwan da ban iya controling din su a lokacin. Haba yar nan ki daina kuka kada nima ki sakani kukan don wanan labari naki akwaicin zuciya gaskiya. Do me bataga laifin danta ba dashi yake ba uwarki diya matan sai uwarku kadai zataga laifin su ta fada a hasale. Muryan mami ne data dawo take kwala min kira daga waje yasa na mike tsab na fita dakin da sauri na barsu a zaune da hjy. Duban hjy yayi yana fadin hjy ashe har yanzu akwai itin mutanen nan masu halin dabba a kasan nan yadda yanzu addini ya zagaye kasan nan. Yo jafari mai za a fasa a wurin kishin muna mata wasu matan fa kishi suke da matan diyan su kila irin hakane ya ke faruwa a gidan har wanan tsana ya shiga. Amma idan bashi ba menene laifin haihuwan diya mace a duniyan nan ni ba gani ba kai bani kadai ba har kowa ai yanzu moriyan diya mace mukeci kaf zuriam mu ga baki daya. Don uwarkuce tsaye da gidan ni kaina da kaganni nan na fuskanci itin wanan matsalan lokacin dana jera haihuwan iyayyen ku mata har su hudu a lokaci guda ban haifi namiji ba. Sai dai ni kishiyace ta goranta min hakan bawai uwar miji ko wani irun wanan zancen yana da shiga zuciyar bawa don yanzu Allah kadai yasan halin da uwar yarinyar nan take cikin dan bakin ciki kan tana ganin sa. Amma idan tayi hakkuri wataran sai labari yau ba gani danayi hakkuri na shanye hakan ba uwarku sai Allah ya daukaka muna ita ta zama muna zakara a cikin mazan. Yau zeey mami ta fada ki dauki wanan kikai dakin ku na hjy ne ki kula da bata tana ci lokaci lokaci kinji. Nace to mami ina daukan ledan da ban san ko na meye ba a cikin sa har na juya zan tafi take fadin zeey na juyo da na,am mami sai kuma ta kasa fadin abinda zata fada tana kallon fuskana da mamaki ta furta. Zeey kinyi kuka ko zancen jiyane har yanzu a ranki ko kuma wani ya kara tabaki gidan nan yanzu kuma ? Kai na girgiza da sauri alaman a, a tace to me akai maki fuskan a haka ko gida kika fara tunane kuma. Nace a a a sanyayye ina juyawa sai ta bini da kallo mikewa itama tayi ta biyoni baya ban san mami na bayana ba sai dana shiga dakin da sallama naji mami na fadin a a ashe kana nan tare da hjy ne yanzu fa nake shirin zeey ta kira min kai a waje na kira layin ka bakai picking ba. Yacs OK mami nabar wancan wayan daki da zan fito ai nazo gaida grany ce da kwana sai kuma na zauna muna hira. Wanan yarinyar na gani kamar tayi kuka ai shine na biyota in tambayeta ko wani abin kuma akai mata na ganta haka ? Ba wanda ya tabata tun safe muna dakin nan tare da ita nasan kukan da tayine kan labarin yan gidan su da take bani yanzu. Ta labarta maki jahilcin kakarta ke nan ko don shine damuwan ta a zuciya kullun Asabe ta tsani mahaifiyar su don kawai ta haifesu a diya mata. Shine fa yanzun nake mata musali dake kika kirata irin wanan mata da yawa suna haduwa dashi a rayuwan su in Allah ya hadasu zama da mace mara imani ga ubangiji har ma a cikin masu ilimin akwaisu sosai har gobe . Na fada mata ta kwantar da hankalinta muddin ina raye a duniyan nan sai tayi ilimin data tallafi gidan su insha Allah . Asabe zata gane diya mata ma mutane ne kamar kowa ba abin wullakantawa bane a gida. Mikawa hjy ledan dake hannuna nayi ina fadin mami ne tace in shigo maki dashi nan nakine na fada ina ajewa gaban hjyn nata a cikin ladabi. Me muka samu kuma nan ta fada tana kokatin budan ledan dake gaban ta lokaci daya ba komai bane sai goron ki da sauran tarkace dazaku bukata a nan dana san kina amfani dashi mami ta fada. Mami goro kuma ya kamata ace ta bar cin goron nan a yanzu fa don jikin tsufa daya kamata zai iya mata illa wanan goron haka. Ungo naka da zai mun illa da tuni yayi min tun kan a haifeka nake cin goro na a duniyan nan gani ko garau kana ganina. Allah baki hakkuri ya fada tare da mikewa tsaye yana gyara rigar shi hjy tace tafiya zakayi kuma muna zaune muna hiran mu ? Na gama hiran ai ku karasa hiran ku damani ai ba dani aka fara ba ya fada yana ficewa tace miskili kafi gaban gayya wanan wanan zan so naga macen da zata iya zama dashi haka. Mutum kuna zaune kalau ya birkice maka lokaci guda kuma ya hana ayi magana don tsaban miskilanci. Fita yayi daga dakin ba tare daya kara mata magana mami na gefe tana murmushi mama kande ne ta shigo dakin da sallamanta muka amsa take. Fadin mama ga abinci an gama na kawo maki da cewa hjy tana fadin sannu sanu yarnan sannu da kokari har kun kare na rana ban dade da cin na safeba ai. Ai kande akwai kokari shiyasa nake son daukesu mu koma Abuja don gwarawan nan sun isheni basu iya irin cimar muba nan sai kalar tasu abincin. Saidai kuma ina tunanen wanda zan bar yaran nan dasu a gidan nan don baka barin ya mace ita kadai a gida. Yo da kin fada tun bamu taso ba ai da anyiwa ladidi magana me take a gidan banda yawon bin makwata sai tazo ko ta zauna dasu nan kinga an rage mata ma wahala ai. Mami tace indai ya ladidin zata yarda hjy ai mata magana kafin mu wuce in sani don in tura su kande gida suyi sallama da mutanen su asan zasu tafi. Zan kira yayan ku in sheda mashi yai mata magana aji me zatace wanan ai ragewa ladidi nauyi ne babba. Kande ko baku zuwa mu koma Abuja mami ta tambaya sai kande din tace yo hjy ko ina kikace mu tafi aini mai bin umurnin ki ne. Yafi mun zama nan da yaran nan naki da basa jin magana na gara dai ina kusa dake yafi dadi ta fita tana murna tare da fatan Allah yasa a tafi da su din. Lokacin sallah yayi mami ta bar dakin aka barmu dagani sai hjy sai bayan mun idar ne muka zauna cin abincin rana lokacin ne kuma anty Aisha ta shigo gaida hjy da kwana. Tana wani daure fuska don tasan hjy zatai mata tsiya nan dai sukaita barkwancin su kafin Aishan ta juyo tana fadin . Zainab yanzu ba a ganin ki tunda hjy tazo na hadiye abincin dana saka a bakina ina fadin dazun na lekaki har sau biyu in gyara maki daki kina barci. To ai yanzu na tashi ta fada nace bari gama naje na gyara maki sai hjy tace ke arr ke kan anyi malalaciyar yarinya a nan sam baki biyo halin uwarki ba ke kan. Don Allah hjy ki rufa min asiri kafa mami ta shigo ta sakani gaba banda abinki don kawai ta gyara min daki shine wani abu. Yanzu ke haka za a kaiki aure ko gyaran daki baki iya ba kina haka tace wai hjy wa ya fada maki ban iya ba kawai dai ban samun lokacin hakane a tare dani. Haka rayuwan ke gudana yanzu zan iya cewa na samu sauki sosai iyakata in shiga dakin mami in gyara sai na anty Aisha sai bayan kwana biyu kuma a ce in gyarawa yaya dakin shi yayi datti. Su Rufaida iyaka ta dasu gaisuwa in suga dama su amsa in basuga dama ba su kyaleni sai ko idan na gilma idan ba mami kusa su sakar min magana mai zafi sai dai kawai in hadiye ban fadawa kowa kamar yadda mami tace in fada mata idan sun min wani abu. Ya safiya ma zuwanta biyu da muka zo tana wuni gidan a karshe kuma su kwasa da mami su fita don tunda mukazo da wuya mami ta zauna a gida. A bakin Aisha nake jin wai kafn mu tafi za a karrama mami nan jahar ta ita da wasu manyan jahar da suka samu mukamai shine dalilin ma da zamu kara sati daya nan gaba. Nikan naga sai manyan mutane ke shigowa suna fita gidan maza da mata suna ganawa da mami wani lokaci da yaya mamud don kome mami zatayi shine gaba wuri aiwatarwa a gidan sai dai shi baida daure fuska iri sauran fuskan shi a sake yake ko yaushe gayin ba,a da raha. Sai ince wanan shirin dinner kamar yafi wanda aka hada masu a abuja haduwa don irin shirin da naga anayi da kudin da ake fitarwa. Don kawai wana shagalin da za ai mata ake wanan barnar da kudin nake fadi a raina sai ga hjy itama tana fada kan hakan. Andace rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya har gashi ana gobe buki sai faman tanadar abinda zasu saka babba da yaro sukeyi a gidan. Ina kallo sai kiyasta abubuwa nake a raina idan naji suna ihun da shewa yasu yasun a falin har anty Aisha da yanzu kan wanan abin takan dan zauna tare dasu wani lokaci. Da farko hakan bai damuna abu ga mace kuma mai karancin shekaru irina a lokacin don haka na saka damuwa har na gaji na bakaina lafiya danayi wani tunanen cewa kilama badani za a tafi wurin dinner din ba kamar wancan na Abuja da yaya ya taimaka min ya tafi dani naga shagali kuma na samo abin bukin da har yau nake boyon su in kaiwa innar mu a gida idan zan tafi. Muna daki da hjy ta gama cewa in bata ledan goro taci na dauko mata na zauna ya shigo dakin suka fara gaisawa ni dai banyi gigin gaidashi ba don ko na gaidashi din ba amsawa yakeyi ba. Bai dade da zama ba sai ga Aisha dakin tana fadin hjy ni zan fita zuwa gyaran kai hjy tace shi jan ma har sai anje gun gyaran shi kamar wata kafira can dake ina dai irin gyaran kafirai din nan kike nufin zuwa. Kaji hjy kuma da wani zance bros ni zan tafi daga inda nake bansan lokacin danace anty Aisha nima zan tafi. Hjy ta jiyo inda nake tana fadin kema zaki tafi ai maki wanan banzan gyaran kanbna zamani yar nan a cikin mamaki take magana . Ballema ina zan tafi dake haka zainab don me ba zaki da ita ba ya fada fuska daure karbi nan kuje ai mata itama. Hjy tace balle yau daine da tayi sha,awan wanan abin ai, ina nan kuke ta sha,anin ku iyakarta ido ko dinkin nan bata samu albarkan ai mata shi ba gidan nan ina kallon hankalin iyami duk da aiyuka sun mata yawa. Har dai muka fita daga dakin bayan ya cikawa Aisha hannu da kudi masu yawa da suka sani mamaki a cikin raina. Aisha tayi mamaki kwarai lokacin da aka bude kaina da kullun yana cikin katon hulan da nake dunkule gashina a cikin sa ko kafi aula dubara baka taba ganin gashin kaina a gidan mami. Don haka ba wanda yasan wanan sirin dana barwa kaina sani ni kadai ba a gidan mami ba kwai ko a garin mu inna tace kan dunkula min a daki da dare. Aisha na kallon ikon Allah wayan ta yayi kara ta dauka ta kara a kunnen ta ni sai naji tana fadin to yaya daga nan din zamu wuce can insha Allah. Ashe ya Jafar ne ya kira ta ya umurce ta kaini wurun sayar da kaya a zaba min don hjy ta fada mashi ba a samu yu min dinkin fitar bukin bani don mami bata zauna ya kara da fasin kin san kuma tunda hjy ta fadi dole ayi basai mami ta sani ba tunda aiyuka sunyi mata yawa ranakun nan . Muna gamawa driver na waje na jiran mu don bata jan mota ita saboda mami bata yarda da hakan ba wai bata gama sanin garin ba. Ina mamaki idan ta dauko kayan yadda take gwadawa a jikinta kafin ta gwada a nawa jikin kayane masu kyau kala biyar babu na yarwa a cikin su. Ina kallo ta biya bayan ta hada da jakka da takalmi ko wani kayan muka dauki hanyan gida mami ko sai kira takeyi wai mun dade a waje ga hjy na fadan haka kuma. Dakin ta muka shiga da komai da muka sayo na wuce zuwa dakin mu ina shiga hjy fada sosai ta hau ni dashi wai na biyewa Aisha munyi dare a waje. Kala bance ba don ba dabi,a na bane babba na magana ina bashi amsa lokacin sai bayan mun idar da sallah magariba har isha i har lokacin na kasa sakin jiki a dakin har hjy ta kare abinda takeyi ta juyo inda nake tana fadin Yi hakkuri yar nan kin san garin kaduna ba kamar sauran garuruwa bane girma ga kuma yan daukan amarya a sasssan shi. Shine yasa kukaga hankali bai kwanta ba don Allah ku daina fita kukai yamma garin nan. Hjy kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zamu karan hakan ba tace ya wuce a cikin wani sauti dake nuna bacin ranta har lokacin. Ni dai nayi shiru gefe daya nasha jinin jikina nasan tunda hjy ta hasala haka damu na mami sai yafi nata zafi. Aikuwa ban gama tunane ba mami ta shigo dakin fada sosai mami tayi min a dakin kafin ta juya ta fita . Duk sai naji ba dadi a raina duk da nasan ba nice mai laifin ba amma kuma anga laifina a hakan ko sun mata da ni yar rakiyace kawai. Sai washe gari na samu hjy ta dan sake mun fuska muka koma daidai a dakin da ita har tana jana da hira tana fadin wanan gyaran kan danayi ya kara fitar min da suran fuskana a fili. Yar nan ashe haka kike da kyau kike munanta kanki baki gyara don Allah ki rika gyara kanki kina kwalliya kina fitar da suran ki waje. Ni dai sai dan murmushi nakeyi ina jin dadin yadda tsohuwar ke yabani koba komai dai na samu wace ta nuna min kauna nima kamar kowa. Hankalin kowa ya dauke gaba daya a gidan ma kuma cike yake da mutane don haka na makale daki tare da hjy sai jefi nake zuwa in leka dakin mami indanyi wani abin. Karfe bakwai kamar kowa jira yake yayi don dai shiga wanka akeyi ana shiryawa saiga anty Aisha ta shigo tana fadin ke zainab na manta da kayan nan ai da sauri na dago ina kallon kayan da take magana akai. Kayan jiyane dana rakata ta sayo take miko min da sauri na karba ina fadin Anty nikika sayawa dama ? No bani ba ya J ne ya bada kudi a saya maki jiya bayan fitar mu ai mantawa nayi na baki tun jiya wanan tsohuwar tasa mami na muna fada kawai kamar yara kanana ne mu. Nikan banbi ta nasu ba hankalina yana gurin kayan duk na rikice don murna har ta gama ta fita ba,a jima ba ta aiko kirana nazo. Da sauri na mike nabar hjy da muke kallon kayan a dakin mu tare na nufi dakin Aisha watace ke mata kwalliy a fuska ina shiga taks ce min zauna a gyara maki fuska ba tare data dubo in danake ba. Wurin na samu na zauna saiga mami ta leko tana fadin kin san fa tare dake zan fita ki shirya ku fito mu tafi haka yasa akaiwa anty Aisha a gurguje ta shirya ta fita ta barni a dakin da mai kwalliyan. Ina mamain yadda mai kwalliyan ta zauna ta shiryani kafin in fito gidan har ya koma shiru duk an watse zuwa wurin buki. Raina naji ya baci ina raya ni yanzu wa zanbi kuma tunda wayanda na sani sun wuce sun barni a gida ba tare da kowa ya kulani ba. Rigar da mai kwalliyan ta shirya ni aciki nake faman tatarawa don kada in fadi kasa don yayi min dan tsawo saidai tace dana saka takalma zai zauna daidai a jikina . Har tafiyan da zanyi da yadda zan rike jakka ta nuna min ni dai sai dariya take bami a raina ina fadin wa zai tsaya kallona a wurin balle yaga tafiyana. Takon takalma da kamshin shi ya dawo da hankalin mu surin da muke jiyo takon ya fito naji matar na fadin sir mun gama you can go now. Thank you yace da ita nikan na nufi dakin mu tunda naji sun fara magana ban tsaya ta kansu ba tunda naga mai tafiya dani yau ko bai amsawa zanyi kundun bala in daure in tambayeshi ya tafi dani. Sai gashi dakin yana sallama hjy ke fadin a,a miskili kafi gaban gaiya ba,a fita ba ashe yace sai yanzu hjy ko munyi sauri zuwa ba farawa zasuyi da wuri ba. Ke fito mu tafi ya fada fuska daure hjy tace dan albarka kamar ka sani yanzu ta shigo tana min korafin an tafi an barta har ina shirin kiran uwarku ta turo a dauke ta yanzu. Mun tafi sai mun dawo ya fada ba tare daya tsaya ya bata amsa ba don da alama sauri yake kada ya makara a wurin taron. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣3️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA UBANGIJI ALLAH KA SADAMU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN RANAN KA KAREMU DAGA DUK WANI ABIN CUTARWA DUNIYA DA LAHIRA AMIN. Ba a karanta min labari idan baki bani dan na saka data ba don posting idan kin karanta na biki bashi zaki biya. Gabana ya fadi don jin abinda ya fada ba shiri na mike nabi bayan shi saida hjy tace takalman fa na dawo na saka na dauki dan jakkar hannun na rike. Tsaye yake a falo na zata zan gansu da wanan mai kwalliyan sai naga babu ita babu labarinta wurin. Sai shi kadai yana kallon kofan fitowa jin takona tafe ya fara tafiya saida ya fita daga kofan falon yaja ya tsaya wuri daya. A nan na same shi ba tare daya kalleni ba ya fara magana kamar haka ki kama kanki ki natsu fiye da yadda kowa ya kama kanshi a wurin banda kauyanci da kalle kale duk abinda nayi maki ban son musu ko gardama so be cool kamar yadda na umurce ki. Duk da hausa yakeyi wai saidai kamal turanci yayi yawa ga maganan shi amma ba laifi ga dan turancin dana iya ina fahintar shi hakana. Ma,ana dai akwai abinda ke shirin faruwa a wurin yake min indirect akai wanda na kasa fahintar hakan a raina. Har ya fara tafiya naga yaja ya tsaya sai na tashi karo dashi wani wawan tsuki yaja yana fadin idan kikai min wanan wautar taki wurin nan tun acan zan balbalaki. Saboda haka kada ki bari in kara wuceki tunda ba dodo nake ba kuma ba sauri nakeyi ba. Ya takalman kafanane ban iya tafiya dashi don ban taba saka irin shi ba kallon kafan nawa yayi ya kawar da kai don gaba daya shigar tawa ya tsorata shi wurin sai take ganin bani bace a gaban shi. Kamar yadda yace hakan muka jero gabana sai faduwa yake min kamshin shi kamar a hancin na aka zuba turaren. Security din shi suna hango mu mun fito sukayo kan mu suna gaidashi tare dani tunda sun gani tare dashi. Umurni naji ya basu cikin turancin da baikai can ba suka amsa da yes boss da sauri wani daga ciki ke bude motar maimakon ya shiga sai kawai naji ya riko min hannu sai da gabana ya fadi uku uku don tsoro da bazatan da yai min lokacin . Kofan da zan zauna ya nufa ya bude min na shiga ya ya rufo a hankali sai ya juya ya nufi dayan bangaren da daya daga cikin security din ke rike da kofan yana shiga aka rufe motar suma suka shiga nasu. Mami dake zaune cikin taron duk rashin ganin shi hankalinta bai kwanta ba duk da ga sauran yan uwansa a gurin. Table daya aka ware mata daga ita sai diyan ta sai anty Nuriya da ban san da zuwan taba a gurin, kujera biyu ya rage shine kujeran da Jafar zai zauna tare da matar dayace wa mami yau zai nunawa kowa a gurin wanda mami ta rigada ta gama sanarwa MC ya fada tun dazun kuma yake faman sanar da yau dan mami din nan matashi da duniya ke ji dashi saboda ilimi da nagartan iya sarrafa computer zai bayanawa kowa abin kaunar shi. Haka yasa mami zaran ido kadan kadan ta kalli hanyar shigowa don ganin bai karaso ba yau dai tana son ganin wanan yar mai sa, a haka a duniya da har ta iya sace zuciyar danta dake gudun mata. Wanda har ta fara zargin kodai aljannu ne suka aure shi bata farga ba don duk yar data nuna mai sai yace batai mashi ba shi. A lokacin kuma shima yana faman tunane a ranshi ne yadda mutane zasu dubi zabin nasa yadda aka kwallafa rai da cewa diyar wani kusa zai kawo ko diyar wani hamshakin mai kudi a kasan . Yes yasan ba mami ba kowa ma a wurin zai iya ganin rashin dacewan su to saboda me ita din ba mace bace kamar kowa tunda mami ita ta matsa mai sai yayi aure . Wanan itace kadai zai zaba ya zauna lafiya a rayuwan shi don zabin mami sam yasan ba zasuyi daidai. Lumshe ido yayi yana gyara zama kodai ya fasa wanan shirmen da yake shirin aikatawa ne idan hakan zai kawo masu matsala da mami. Shin meye laifin shi har in ya gabatar da wanan yarinyar a yau a matsayin macen da zai aura. Itace yaji rashin ya kwanta da ita a matsayin abokiyar rayuwa kamar yadda mami ke shan fada mashi kullun idan tana masa nasiha yayi aure. Shi gaba daya ya yarda da hakan har zuciyar shi da gangan jikin shi ya amince da wanan zabin nasa matukar zasu zauna lafiya. Yasan yarinyar is pretty shi ba wanan yabi ba nashi tsarin ne a hakan aure dai akace yayi kuma ita din zai aura yasan ta hanyan shi yarinyar itama zata zama wani abu a duniya muddin dai tana tare dashi. Ya dan muskuta kadan tare da gyara zaman shi yaci gaba da tunane yace a ransa yasan ko bai samu goyon nayan kowa ba zai samu na hjy matukar ba mamice ta zugata ba funda itace ta fara kawo mai wanan idea din a falonta. Yasan amsan da zai ba duk wanda ya tun kareshi da rashin yardan wanan zabin nasa duk na kowa bai damesa kamar na mami ba. Ko ita din a yanzu ya tanadi hujjojin da zai bata idan idan har ta nuna bata yarda ya auri yar nan nata ba. Ido ya kara lumshewa a hankali yasan dole akwai aiki ja a gaban shi ba shi kadai ba yanzu har wanan yarinyar ya jefata a cikin dabon tashin hankali don dole ta fuskaci kalubali daga mutane da dama daga yau . A yanzu kan yayi niyar hakan bayajin kiran kowa ko dakatarwan wani bai damu da duk abinda wani zai furta akan hakan da zaiyi ba. Ya shirya daukan duk wani rigiman da zai taso na barazana a kan mu duk yadda mutane zasu kalli abinda zai aikata din shi a shirye yake . Wurin ya hadu da manya da yara da masu ruwa da tsaki a gwaunati tarone na yan boko da suka amsa sunan boko a wurin. Haka motar ta danno kai a cikin get din wurin inda hankalin yan sa ido ya dawo garta akwai daya a gaban mu sai wace muke ciki a tsakiya dayana bayan mu ma,ana dai sun saka mu a tsakiya ke nan. A daidai lokacin da motar ta tsayane driver ya fita da sauri sai ya rage dagani sai shi a motar . Ya dan ja lokaci ba tare da yai magana ba sai can ya danyi gyaran murya yana fadin ke ina son ki kara saurarena da kyau kiji me zan fada maki. Na dan daga kai a cikin tsoro kamar kadangaruwa ya furzu wani iska kamar abinda zai fada ansashi ya fada dole ne lokacin. Ya fara magana a cikin muryan nan nasa mai fidda wani irin amon sauti ya fara ratsa kunnuwana. Na fada maki tun gida wanan wuri akwai yan uwan mahaifina akwai na mahaifiyan mu kin sa wasu wasu baki sansu ba. Don haka duk abinda wani ko wata zasu fada maki iyakarsu dake murmushi kada ki yarda ki wani abinda zai ba dani a gurin duk yadda nace dake haka zakiyi. Zanso idan mun zauna zandan rika jan ki da hira ke kuma kina murmushi a cikin wayewa kada ki yarda ki nuna min kauyancin ki a nan. Idan kinyi abinda nake so kin taimaki rayuwan ki har na yan uwanki nan gaba sai duniya tasan da diya mace ma yace kamar kowa. Yana fadin haka ya dan yun kura kamar zai tashi daga wurin dai kuma ya dawo ya zauna tare da fadin nasan mami zata bincikeki idan mun dawo gida kice da ita ni kike so idan kuma kin ki ruwan ki wanan duk abinda mami zatayi ki nuna mata ni kike so. Yana fadin haka ya juya ya bude motar ya jefa kafanshi daya waje tare da juyowa hana fadin ki dakata an fito in bude maki motar aikin ki ya fara daga yanzu ke nan. A zuciya na amsa cikin damuwa da tsoron me haka ke nufi ke nan ga yanayi ya canza a lokaci guda duk murna da daukin da nakeyi in shiga wurin bukin inga irin kallon da su Rufaida zasu min sai naneme shi na rasa don yadda nake jina kamar wata mara lafiya dani. Daga haka ya fita a motar ya bani gabana na faduwa don har lokacin na kasa hada maganan shi wuri daya in gane me yake nufi da hakan. Kayan jikin shi kawai abin kallone don ina kulla yana sha,awan fararen kaya don duk kyau tufafi farin kala zai saka a jikin shi. Yau ma rigace da wando da ban san ko na wani yarene ba sai yar karamar hula fara mai zagaye a kanshi rigar tana da aninaiya a gaba manya dasu har uku sai wani adon zaiba na manyan zane da akaiwa jikin rigar. Idan nace wurin taron nan gaba daya ba wanda yakai haduwa banyi karya ba don yadda kyaushi da kayan jikin shi suka kara haska wurin. Don yayi matukar kyau yau fiye dama kullun ko dan yau adon buki yayi ya kara haskawa haka oho sai na nemi nawa kwalliyan na raina kaina a wurin. A hankali na fito daga motar tsikar jikina yana wani tashi yarrr daga kaina har zuwa kafana dole badan naso ba muka jera har muna hada kafada a yadda muke tafiyan. Da sauri na dan jada baya don yadda muka manne mind your self OK ya fada ba tare dako na bayan mu sunji yai magana ba. Buki bidiri birede wurin ya cika ya batse don tun daga ganin haraban kai ma kasan yau babu kama hannun yaro sai dai muce Allah sa a watse lafiya. Saida muka dan tsaya a wajen na yan mintina kafin a bude mu shiga kamar an bada sanarwa shigan mu don idanuwan da sukayo kan mu can. Masha Allah mai sanarwa ya fada kunsan kaduna da izala ko dan gala yana izala kaduna kowa sunna Allah yasa muga Annabi Allahuma amin. Kamar in shige kasa in nutse dan kunyan abinda mc din ke fada a kanmu da shigowan mu hakan ya kara jawo hankalin kowa gare mu. Tafiya muke guda guda wanda zai nuna muna inda zamu zauna yana gaba security din shi suna daga bayan mu. Kwalliyan da gyaran da mai kwalliyan tayi min yasa basuyi saurin gane nice ba kunsan yadda kwaliya yanzu ke canza siffan mutum lokaci daya tundai in an hadu da wace ta iya tsarawa. Haka muke ta tafiya kafada da kafada har zuwa wanan table da aka tana da don mami da iyalin ta a wurin. Tunda naga yan gidan na soma kokarin sunkuyar da kaina kasa don nauyi da kunyan su daya kamani lokaci daya saboda kallon mamakin da suke muna gaba dayan su. A, a, a ya J yau yar mami ne haka ka, , , , hannun daya daga mai yasa jalal ya kasa karasa abinda yai niyar fada sai ya zagaya ya ja min kujera tare da dan nuna min in zauna. Nakai zaune a hankali godiyana yau ga Allah da baiyini mai garaje ba sai sanyin jikin nawa a yau yaba da kala a wurin. Saidana zauna ya zagaya ya zauna a dayan kujeran a daidai lokacin da mc ke fadin yanzu dai kujeran hjy iyami ya gama haduwa tare da sanar da shigowa ya Jafar da bayanin ko waye shi da kuma inda yake aikin sa sai kuma ya kara da fadin. Sai bride to be insha Allah kamar yadda kuke ganin wa yan nan masoya sun shigo muna da haske mai haska gidan kowa a wurin nan. Ya jafar ya dan rankwafo inda nake yana fadin kinji me mc din nan ya fada game damu ko ? A dan razane na dan sake murmushi yake na bude bakina da mai kwaliyan nan ta fesa min wasu abubuwa tare da wani sweet na tsotse tun a gida sai hakan yasa bakina fitar da wani kamshi mai ma,ana har yana jin shi a hancin shi lokacin. Sai ka dauka kai dake kallon mu kaga masoya na asali a wurin yadda muke mami kan imani ya hanata magana da kawar da kai daga garemu. Ba mami ba har yaran ta da muke zaune gaba dayan su sun kasa boye mamakin su a wurin ; Hakama sauran kujerun dake kusa dana mami din inda yan uwane da abokan arziki suke zagaye damu a wurin kowa imanin ganin hakan. Rufaida tunda salma tace waike baki ganeta bane zee ce yar mami fa yarinyar mami dai da muka bari a gida. Ai bata san lokacin data mike tsaye ba tana fadin kutumar uban nan zeey zeey dai zeey yar aikin mami dai. Amma wai yaya hakan ya faru dama yarin yar nan haka take ashe ? Shike nan dama Ruby ta fadi hakan gashiko yanzu hakan ya tabbata muna nan shekara da shekaru muna dakon wahala ashe ? Yau ga wata yar kauye mara asali da tushe tazo ga banza ta sameshi a saukake a wanan lokacin muka danyi wanan magana Rubby tace ku duba ku gani wallahi soyayya sukeyi ki duba yadda suke nuna kauna a gaban mami. Kai haba ina wallahi sam sam wallahi ina hakan ba zai taba yuyuwa ba muna zaune wata banza kamar zee tazo ta kwace muna shi. Tunda kowa wurin nan cikin ku zaman jiran ya zabeta takeyi haka kawai zamu kyale muna kallo wanan yarinyar kauyen ta rushe muna plain din mu. Humm yazu na yarda da zancen ki Rufaida yarinyar nan matsafiya ce ta sace zuciyar mami yanzun kuma ga wanda ko a zato bamu taba kawo hakan ba a ran mu wai yaya J zai kali wanan banzan yarinyar yar aiki ya kyasa. Wallahi da sake sam hakan ba zai taba yuyuwa ba kan sai dai inda wata manufa yazo da ita wuri nan wanan kan na yarda kai koma dashine wanan yarinyar ta gama shammatan mu yau. Da hannu aka kira Nazira daga table din da iyayyen su mata ke zaune ciki harda uwar nazira din dake zaune da matan yayyun ta a wurin. Tana zuwa ta dan duka dafata matar tayi tana fadin wai wanan yar yar gidan waye a garin ko kuma a kasan nan ? Wanan mama baki ganeta bane zeey ce yar mami mawa mami hidimar nan muma abinda mukewa magana yanzu ke nan a can. Mami tace Jafar wai me nake ganine nan haka meke shirin faruwa ne wai haka ta tabaya tana tsure shi da idanu babu ko kakautawa a wurin. Please mami kada kiyi wani motsi a nan idan mutane yana a kan ku yanzu don Allah mami kibar komai har a koma gida. Jafar din baiyi magana ba sai murmushi yakeyi yana fadin surprise mami aina fada maki zan baki mamakine da zabina a yau ko ? Please ya J gaji me ya mamud ya fada ai so a daina wana maganan a nan please Aisha ta fada kanta na duke kamar ba itace ke magana ba. Daga inda Nuriya ke zaune kusa da mijin ta take fadin wai mamaki a nan kuma aka kare gun yar , , , , Hannu mami ta daga mata yasa tayi shiru bata karasa maganan da zata fada ba lokacin taja bakinta tayi shiru. Koda aka kira mami tashi tayi friends din ta suka mara mata baya sai da ya bari an dan rage muka tashi zuwa wuri mami tayi niyar juyawa tabar wurin kafin mu iso saida wata kawarta ta dan rada mata kada tayi hakan don Allah. Kudin daya saka min a yar jakan hannuna nima na bude jakkan ina likawa mami din ya dan rada min zakace mudin wasu masoyane na gaske sai ji mami tayi mun rungumeta a lokaci guda. Masu photo suka shiga daukan mu a cikin karfin hali mami ta rungumomu a jikin ta don kawai ta kawar da hankalin kowa ga zargi komai a wurin kanmu baki daya. Saidai na ciki na ciki a zuciyar mami don in ma wasa jafar yai mata haka dani wasan yayi yawa haka don hankalinta ba karamin tashi yayi ba da ganin hakan. Tsoron ya Allah shine kada wanan abin ya zama gaskiya ga jafar don zuwa yazun bataga alaman wasa a idanun dan nata ba yau. Daga inda nake na dan dago ido na saci kallon mami din dake tsaye suna magana da wata kallon da taimin yasani jin wani irin ba dadi a raina. Haka yasa na fara shan jinin jikina gabana sai faduwa yake uku uku riko hannuna naji anyi daga bayana yasa na dago da sauri yayane dan rankwafo yana rada min zaki gaisa da abokainane gasu can . A haka muka bar wurin yana rike da hannu na har inda ya barsu kai maginet wanan irin zabin naka a ina kashiga kasan nan ka samon wanan pretty girl din. Suka shiga wasa shi duk su ukun yana tsaye kimkam ko murmushi baiyi kamar an tsayar dashi a wurin dole. Muryan wani daga cikin su ke fadin dole mc ya bamu fili mu gwadawa duniya farin cikin mu da zabin ka. Bai tsaya jirab komai ba ya nufi wurin mc tun kan ma ya dawo inda muke mc yasa muna wakan tare da sanarwa zamu fito fili abokan JM nason su nuna mai farin cikin su da wanan ranan. Ance ana buki da dollars ranan koda bansan darajan kudin ba nasan masu daraja ne wanan kudin yadda wurin ya dauki ihu ga baki daya ya jafar yana rike dani da hannu daya. Dayan hannun kuma yana cikin aljihun wandonshi muke takawa a hankali sai photuna ake zuba mana babu kama hannun yaro. Sai daya gaji yaja hannuna ko ya fahinci ina gab da bashi kunyane don kiris ya rage in duka in cire takalmin dake kafana kada in fadi. Daurewa kawai nakeyi a hakan sai gashi yaja hannuna mu fita daga hilin wasa bama nan ba kawai gaba daya dakin taron muka bari lokaci guda security dinshi na biye damu duk inda muka saka kafan mu a wurin. Maroka suka sakashi gaba yana rike da hannu na har muka fice daga dakin yayin da suka dan sarara muna ke nan. Wani iska mai sanyi naji ya dokeni sai da nayi wani irin ajiyan zuciya kamar an gafarta min a wurin. Mota muka shiga ba wanda yai magana a cikin to nima me zance nida nawa umurni kuma in aiwatar don dole na. Sai da muka shigo unguwar ne ko ina yayi tsit alaman dai dare yayi sosai a lokacin duk mutane sun shige gidajen su. Mota na tsaye kofan gidan mami din ana jiran maigadi da akewa horn ya bude get din gidan naji yana fadin kin taka matakin farko a cikin shirin mu. Yanzu saiki shirya mataki na gaba shine amsa tambayan mami a gareki kaina na fada maki abu daya nake so dake shine. Idan mami ta tambaye ki a kaina ki fada mata nine nace ina son ki nasan zata tambayeki ke kina sona ko bakya sona ? Kada ki manta da amsan dana fada maki dazun ki basu idan sun maki wanan tambayan. Kai na gyada don ba bakin bashi amsa don duk a cikkn fargaban abinda zai faru idan mami ta dawo nake yi. A kofan shiga gidan ma mun dan jima ana buga kofan kafin lami ta bude mana daga ciki don su aka bari jiran gida dakuma hjy dake dakina. Har dakin ya kaini tsohuwar na zaune saman sallaya taji shigowan mu take fadin a, a har kun dawo ke nan eeh gatanan na dawo maki da ita ya fada yana wucewa bai yarda ya tsaya a dakin ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣4️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA UBANGIJI ALLAH KA KAREMU DAGA SABA MAKA TAKO WANI HANYA A RAYUWAN MU ALLAHUMA AMIN, , , , Gaba na faduwa ina tsaye ban iya gusawa a inda nake ba tunda ya bar dakin jin muryan hjy ce data juyo gareni tana fadin. Yar nan lafiya kuwa hawaye ne yazo min lokaci daya nayi karfin halin girgiza mata kai ina daga kafa da kyat nace ba komai hjy. A cikin karfin hali na karasa cikin dakin ina kokarin aje jakkar dake hannuna da naji ya kara min nauyi a wurin. Bandaki na nufa tukun na fara sake fitsarin tsoro daya taru mi a mara na dan dade tsugune ina sake shi kamar ba zai tsaya ba lokacin. Na dade a zaune ina tunane kafin in samu inyi tsarki in fito daga bandakin duk jikina a sabule har lokacin yau kan nasan na taro mach a gidan mami wanda mai fitar dani sai Allah. Ni da wani ido zan kalli mami dashi wai yau ni zainab yar aikin ta ke ikirarin zama sarakuwar mami a duniya. Ni zainabu wani hali da rikici na jefa kaina a ciki aikin dana sani daga baya ke nan yake zuwa don nayi dana sanin yarjewa yaya Jafar bukatan shi yafi sau dubu a wurin. A gurguje na shiga dakin mami a cikin daren nan don daya saura na dare a lokacin na gyara ko ina na dakin ban tsaya ba don kada mami ta riskeni a ciki na jawo kofan ina dawo na haye kujera dama na cire kayan jikina tun kan in shiga dakin mami din. Tundana kwanta ba dunkule a cikin hijabina ban yarda nayi ko motsiba wurin. Ina jin hjy na magana tana fadin su a can zasu kwanane har wanan lokacin basu dawo ba haka. Shiru nayi kamar ina barci haka yasa ta kyaleni sai can na fara jin hayaniyan mutane a gidan alaman an fara dawowa ke nan daga dinner din. Can aka turo kofan dakin da karfi ana kiran sunana muryan Aisha ce sai naji hjy na fadin yau naga sha shanci a gidan nan. Zaki turo kofa haka babu sallama to boyar taku tayi barci tunda yaron nan ya dawo da ita don da alaman a gajiye takema ko da ta shigo. Mami ke kiran ta yanzun nan a dakin ta ta fada a cikin wani murya da ban santa dashi ba sai ranan. Kada ki soma ki tada yar nan daga barcin nan kije ki fadawa uwar taku tayi barci tun dazun inji ni haba kowa fa rai gare shi kamar kowa ace mutum ba zai huta ba haka dare ai mahutane ta fada cikin bacin rai. Ina jin lokacin data rufo kofan hakan yasa nasan ta tafi na sauke wani iri ajiyan zuciya daga kwancen hjy taci gaba da fada ita kadai a dakin. Sai muryan sallaman mami tana fadin hjy ashe baki barci ba ina zanyi barci kuna waje har wanan lokacin iyami. Ki duba lokaci fa karfe nawa yanzu zaku biyewa shedanu kukai lokacin nan a waje dare fa mahutun muminine don a daren yake raya rayuwan shi walau ta hanyar barci ko na samun ganawa da ubangijin shi a natse. Wallahi hjy taron ne ba, a fara da wuri ba tana magana hankalinta na inda nake kwance zata tayar dani . Yar nan tayi barci tun dazun haba ku rika sauwaka mata hakana tana iya kokarin ta gidan nan yanzu sha shan yarki ta shigo tayar da ita. Koma me zatayi ita Aishan tai maki mana baku bari yaron ya samu albarka a wurin ku saboda karyan zamani har yaushe kamar Aisha za ace ba zata iya aikin da wanan yar zata iya maki ba. Ba aiki zatai min ba hjy dama dai tambayan ta nake son yi kawai mami ta fada sai hjyn tace. Koma menene tunda tayi barci ai sai a kyaleta har safe a tambaye ta itama fa mutum ce kamar kowa a cikin ku. Hjyce ta ceceni a ranan don mami fita tayi a dakin ba tare data tasheni ba kamar yadda mahaifiyar ta ta hana. Ranan idan nayi barci barawo ne ya sace ni don haka na kwana ina sake sake bani kadai ba har wanda duk abin ya shafa banda ya jafar dashi ko a jikin shima hakan. Aiko gari na wayewa sai ga sakon mami inzo gabana na duka uku uku na mike daga inda nake zaune a takure na nufi dakin mami din. Addu,a kan nasha shi yafi cikkn kwando ranan da sallama na shigo dakin daga ita sai Aisha da mama Ramatu. Mami tayi tagumi tana zaune kasa a inda ta idarda sallah asuba ta rasa abinda ke mata dadi a rai so kawai take taji na bakina abindake wakana a tsakanina da danta. Nayi sallama na shiga sai mama Ramatu ne ta amsa min a lalace koshi Aisha ko tana bina da wani irin kallon mai kama da mamakina a fuskanta. Kasa nakai cikin karfin hali ina fadin ina kwana mami ban jira amsawan ta ba na juya airin mama ramatu itama na gaida ita na juya gun anty Aisha itama hakan ne. Shiru dakin yayi na dan lokaci ina tsugune kafin inyi yunkurin mikewa don shiga ban daki in wako yaddana saba yi. Dakata zainab komaki zauna mami tace dani na koma da sauri inda na tashi ta dan dago kai ta kalleni kafin tace zeey ban saki da karya ba ko wani abu makamancin hakan. Balle boye magana don baki taba min shi ba tun zuwan ki gidan nan wurina. Kaina dan gyada a hankali yayin da gabana yaci gaba da faduwa sosai jiya tare da wa na ganki zeey ? Kai na dan dago da sauri na dan saci satan kallon mami na samu ta kafeni da ido tana son amsa daga gareni. Shiru na danyi tare da dukar da kaina kasa ina kallon carpet din da nake saman shi. Bakiji me aka tambaye ki bane mama Ramatu ta fada daga inda take zaune din da dan karfi hakan yasa na dan zabura tare da dago kaina ina fadin babu komai mami. Babu komai kuke haka jiya tare dashi a gaban kowa Aisha ta fada a dan hasale tana watso min harara. Ni ban san komai ba tun bayan da kikace mai kwaliya ta shiryani yadda ya kama kika fita kika barni da ita mun gama na fito na samu duk kun tafi babu kowa da zanbi sai gashi shi yace nazo mu tafi. Wani ajiya zuciya mami ta sauke har ina jinta daga inda nake Aisha ko na kokarin fadin wai kina nufin ni No wallahi mami ban san komai ba a kai kawai dai ya ban kudi a gyara mata kai daga can kuma ya kara turo kudi waina saya mata kaya expensive one don kin manta ki saya maya yanzu hjy ke fada mai. Jeki zan kara nema ki mami ta fada tana kallon mama Ramatu da itama din ita take kallo don jin abinda ta fada. Kai mami ta gyada mata alaman ta bari in fita daga dakin tukun suci gaba da magana zan shiga ban daki tace barshi anjima ki dawo idan mun fita. Na juya na fita nan na barsu a dakin sai da na fita ta juya tana kallon Aisha dake zaune tana fadin duk abinda aka kitsa tare dake aka shirya hakan ashe kika boye muna. Wani mami wallahi ban san komai a kai nima iya abindana sani ke nan na ta fada yanzu dana sani ai dana fada maki komai tuni. Daki na koma na takure a wuri daya ina faman funane a raina don na kara daure kaina again ban san da wani ido zai kalleni ba kuma nasa bangare ga mami bawai ta yarda dani bane tunda har tayi mi abinda bata taba min ba yau shine. Wai in fita idan sun gama na dawo in gyara dakin kenan da sauran maganan da zasuyi a kaina ke nan a dakin. Shirun da nayi yasa hjy dake magana still kan daren dasu mami sukayi jiya a waje taji nayi shiru hakan yasata jutowa gareni. Hawayen da ban san yana zubane daga fuskana ta ganin haka ta fara sake salati tana tafa hannu tare da fadin yarnan an maki wani abi ne ko kiranda iyami ke maki jiya na hana a tasheki tai maki fada a kansa yanzu don naga bata so hakan ba dama. Saboda shine ta bata maki tunda farar safiyan nan ko da sauri na girgiza kai don nasan baida wuya yanzu ta sauke wa mami bala,i akai ta kara jamin wani tsana. Kofan dakin aka turo Aisha ce tsaye a kofan tana fadin zainab mami na kira daidai lokacin da hjy ke fadin. Ke kan yar nan arr da halin nan naki ace dan musulmi bai iya sallama idan zai shiga guri gara dai da uwarku ta raboku da kasan kafiran nan tun kan kufi haka ai. Sai kuma jin abinda ta fada ta sake fadin wai wani laifi tayi maku haka baku bari yarnan ta hutane wai ? Ba laifi tayi ba naji Aishan ta fada a daidai lokacin da zan fita daga dakin bayan fitana asheta fada mata komai dake faru tun daren jiya din a bayana. Sai da tsohuwar ta gama ji take fadin meye laifi a cikin zancen nan idan shi jafarin yace itace zabin sa ai baiyi zabin banza ba nake gani ko ? Haba hjy yar aiki ce fa wanan yarinyar da bata waye bane zai dauka a matsayin matarshi yadda ya J yake wayayye dan boko mai ilimi din nan dashi. Yo wani waye akwai wanda yafi wani a gurin Allah ne idan ba Annabin rahama ba shi kadai zai fadi haka sai ko wa yanda sukai zamani dashi aka tabbatar masu da aljanna . Kai don Allah hjy ki daina danganta wanan da yayan mu please ai abin kunyane ace wai wanan ce zabinsa haba dai. Kaji min ya da wani maganan banza meye laifin zabin nasa har idan da gaske yakeyi ba wasa ba uwarku da ubanku ya aureta takai wanan din wayewa ne a lokacin. Aida ba yanzu bane Aisha ta bata amsa tana fita tace kinci gidan ku nace kinci gidan ku yarnan da wanan maganan banza kece zaki zauna mashi da ita koshi zai zauna da abinsa. Fita tayi ta kyale tsohuwar tana jin zancen ta na kara mata takaici a ranta sai ta dauki zancen tsohuwar ga tsufane kawai ke damun ta ba wani abuba don da tasan abinda takeyi da bata fadi hakan ba ai. Ina shiga dakin mami ba tare data kalleni ba tana jin sallamana take fadin jeki ki wanke muna bandakin nan idan kin gama ki daukowa hjy abin karyawanta a kitchen. Don mami ta dauki zugin mama Ramatu da wata kawarta da tun jiya ta zugeta a kaina baki daya don haka ta kudurta canza min daga wanan lokacin tun ban dauko mata magana ba a cikin diyan ta. Wanan zugin kan mami ta haushi ta zauna akai sosai har yakai ta fara ganin aibuna a gareta yanzu. Kafin in fito har ta shirya zata fita ta gaisa da mutane take fadin yi ki karasa ki fufo min dakina na amsa da toh kawai a cikin sanyin jiki ga canjin da nagani gareta. Dakin mu tashiga gaida mahaifiyar ta inda ta samu hjy har lokacin tana mitan zancen ita kadai a dakin. Koda mami ta shiga amsa sallama dai tsohuwar tai mata babu sakin fuska suka gaisa tayi mata ya jiki ? Mami bata tsaya ba ta juya tana fadin bari ta leka yan uwa a dakin in dawo tana fadar haka ta fice daga dakin. Har na gama gyaran dakin na jawa kamar yadda ta umurceni in mata da dakin na wuce kitchen na karbowa hjy abincin. Ban daki na shiga nayi wanka na fito na shirya a cikin wani atamfa da Aisha ta bani dinkin buje da riga bujen dai bai matseni sosai ba yadda ita yakan matse jikinta idan ta saka a jikinta kafinta bani . Ban zauna a dakin ba na nufi kofan fita daga dakin ina zuwa kawata hjy ta fada zan je in karbo abincine a kitchen na bata amsa. Yau kuma ba a nan mukeci tare ba dake mazaki dawo ki dibi abincin nan kici karna saba maki. Ko ta fahinci tsoron mami nake sai tace kowa yasan tare dake nake cin abinci sai yaune zasu kawo min wani zance. Dole na dawo na rakube a gefe ba tare dana yi yadda na saba muna wasa da dariya a gurin ci ba haka hjy ta sakani gaba dole na debe abinci mai yawa tana kara ina ya isheni haka ta kyaleni. Na fara ci ke nan mami ta shigo dakin tana magana sai ta dagata da maganan tana fadin ke kuma meye haka ? Me tayi hjy ta tambaya tana kallonta da mamaki hjy don me zata zo ta zauna tare dake a nan tana cin maki abinci ? Yau din kuma iyami ina har ke muna zama da ita ana aci abinci baki taba fadan wani magana sai yau ? Daga yau din ban son in kara ganin hakan ta koma can wurun yan aiki ta dinga ci tare dasu kande da lami. A, a iyami bana son irin haka wanan ba halinki bane hakan ban san kuma yaushe kika fara hakan ba. Hjy na canza tsarinane yanzu a gidan nan don a fara bambamta yan aiki da yan gidan nan iyami dakata hakana hjy ta fada tare da juyawa inda nake tana kallona kafin tace dani kinga kawata. Jeki falo kici abincin ki ki bamu wuri zamuyi magana da uwar ki ina jin hakan na mike da sauri don barin dakin. A daidai lokacin mami ta kai zaune a kusa da mahaifiyar ta saidai ita saman kujeran ta zauna ba a kasa ba inda hjy take zaune. Ko dana fita ban nufi cikin falon inda nake jin dan dararakun mutane na zauna dan filin da zai sadaka da falon da gefen dakunan mu din. Ina kallon abincin ba tare danayi ko yunkurin cin cibi daya daga abincin ba sai idon dana zuba mai kawai. Iyami kada ki bari shedan ya rudeki kiyi yunkurin yaki da ubangijin ki kan abinda Allah shida kanshi ya halasta hakan. Yarki dazun ta fada min komai dake faruwa daku tun jiya wanda na hango kina kokarin fita daga ilimin ki da irin tarbiyan ki dana sanki na girmama dan adam a duk yadda yake. Hjy ba hakana bane ni yaran nan zasu kunyata a cikin taron jama, an arzikina wai yaron nan ya nemi ya raina min wayau ya hada baki da yar nan a kunyatani hjy ? Akunyataki kamar yaya hjy ta tambaya shi auren ne kunya ko yarinyar ce kunya a gareki yau kuma kina kunyan a santa da ahakin ki kika ajeta a gidan ki har kika jata a jikin ki kamar kece kika haifi abinki. Wani irin shedani ne yayi saurin tasiri haka a jikin ki har kika manta da bayan ki ke ? Da sauri ta dago kai ta kalli tsohuwar hjy tace eh kin manta da naki bayan kina son ki maimaita tarihi a kanki yau. Hjy bawai hakana bane ni abinne yai bala,in bata min rai kawaion su wullakantani har jafa, , , , , Hannun da tsohuwar ta daga matane ya dakatar daga karasa maganan ta datayi niyar fadi a kanmu. Iyami na haneki tun wuri da wanan halin abinda zai kawo dana sani daga baya wanda zai zama keya gareki. Yaya zaki idan Allah ya nufa wanan abin mai yuyuwane garesu ko kina son in kin matsa da jayayya da ubangiji ya dauki ranki ayi a bayan ki. To ina baki shawara ki natsu ki shiga hankalinki tun wanan abin bai fita waje an dawo ana maki dariya ba daga bayan ki. Ina yar nan ke kika kawota gidan nan har danki ya ganta ya nuna sha, awan shi gareta duk ko da yadda take ba yar kowa ba kamar yadda ku kuke gani. Shin iyami kin manta da yadda akayi lokacin auren ki da mahaifin yaran nan sam ban taba zaton zaki manta da hakan ba har ace yau ke da kanki kike kokarin yin wanan halin da ba, a san musulmin kwarai dashi ba. Ina wanan abin ke kanki kamar darasine a gareki ban taba zaton har zaki yada kiyi ko maka mancin hakaba a yanzu. Daga inda nake zaune naji takon tafiya haka yasa na dago kai da sauri ina kallon mai zuwa a lokacin ya Jafar ne da yaya mamud suna tafe suna magana a tsakanin su. Saidai ganina a wurin yasa sukaja suka tsaya suna kallona da sauri na gyara zaman da nayi da farko ina gaidasu. Duk kallon mamakin ganina a wurin sukeyi sai ya mamud ke fadin lafiya kanwata kika zauna a nan haka a kasa baki je dinning kin zauna ba. Wani kallo ya Jafar ke min ba tare dayayi magana ba sai hannayen shi daya zuba a cikin aljihun wandon shi bakin wandon jeans dake ciki ya dan fito waje ya wani kara haske ko kallon tsoro nayi masa oho. Badake ake magana ba ya jafar din ya fada na dan dago kai na kallesu sai nayi saurin dukar da kaina don duk idon su yana a kaina. Ganin ina kokarin mikewa yasa ya mamud ya fara tafiya shima ya mara masa baya zuwa dakin dana baro su mami din da hjy. Da sallama suka shiga dakin saidai ganin yadda daga hjyn har mami suke sai yasa suka dan tsaya daga kofa basu karaso ba sai ya mamud ke tambaya lafiya dai mami ko wani abinne ya faru ? Shike nan ma hjy ta fada ga magani ga ciwo Allah ya kawo ki tambayi dan ki a gaban mu yanzu aji idan da gaske yakeyi ko wasan da kike tsamani kika tsani yar mutane haka ba gaira ba dalili lokaci guda . Kin hana yar mutane tun jiya kwanciyan hankali duk kunbi kun rikita yarinya ga baki daya ni bani son irin haka wallahi abu baikai abin daga hankali ba zaku sakawa mutane rigima a gida. Kallon mami yayi ya karaso inda take yana kaiwa zaune ta gefen gujeran tare da kamo hannun mami din yana fadin wani abu ya farune mami ? Bai faru ba zai dai faru ka gaya muna meke tsakanin ka da Abu dana ganku jiya a gurin taro har kana nuna muna wai surprise din ka ke nan garemu ta fada rai a bace. Abu mami ? Waye hakana mami ban gane wa kike nufi ba hannun ta dake rike a nashi ta fisge tana fadin zeey yar aikina nake nufi ba wani ba. Kai ya girgiza tare da dukar da kanshi kasa can ya dago yana fadin mami ba ke kikace na fito da yarinyar data kwanta min a kasan nan ko diyar waye ba ? ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUKU 🦅 2️⃣5️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YA ALLAH MUNA ROKON RAHAMANKA DA KARIYAN DAGA DUK WANI ABIN CUTARWA A GAREMU ALLAHUMA AMIN, , , , , To ka samo din ta tambaye shi a cikin gatse ? Eh na soma mana mami kuma ai a karkashin ikon ki take itama yarkice kamar su Aisha. Wa ke nan ya mamuda ya tambaya wanan yatinyar taki da kika dauko a kauye mana ga zahiri kun gani jiya tunda kun gamu tare. Mami kan yake tayi wanda yafi kuka ciwo kafin ta tattaro natsuwa don hjy dake wurin a zaune bata da halin furta mai wani abu a lokacin. Saidai duk da hakan sai da mami tayi bajintar fadin wai zeey dai kake nufi ai zee din kasan a matsayin dana daukota kuma bayan haka karatu take a yanzu. Mami nasan da hakan saidai ai takai munzalin aure a yanzu don haka aurena da ita ba zai hanata karatun ta ba. Ko kin manta kin fada muna kema kina karatun secondry daddy ya ganki ya aure ki lokacin. Look jafar bana son shirmen banza mata nace ka fito da ita in maka aure at dis stage bawai ka tsaya kana min wanan shirmen ba haka. Zainab na fadama karatu take kuma bata cikin zabin matan da nake son ka aura don tayi kankanta gare ka yanzu. Hjy dai da yaya mamud na gefe zaune suna sauraren draman uwa da danta sai murmushi suke masu kawai. Mami to aini ita din ce chooice dina sai ta karasa girman ta a gurina don ni a hakan da take yayi min daidai. Jafar kada ka mayar dani abokiyar wasan ka idan kai tayi mani ba, , , ya mamud ne yace mami please. Ki barshi ya zabi abinda yake so a rayuwan shi tunda shine zai zauna da ita bake ba kada a tillasta mai yayi abinda baiso a dawo ana dana sani daga baya kuma. Hjy tacs fada mata dai dan nan ko kai zataji maganan ka tunda ni ban kai matsayin da zan tsawata mata ta saurare ni ba Hjy bawai haka bane na lura yaron nan rainawa mutane wayau yake son yiwa mutane tunda mun tursasashi yayi aure bari ya zabo wace bata yuyuwa a gareshi yanzu ya rama abinda mukai masa ko ? Wallahi mami tunane baikai ga hankan ba itace dai din naga tana daidai da rayuwana ita kuma din nake so a matsayin a bokiyar rayuwana. To ban yarda bami ta fada a hasale tana mikewa hjy tace iyami dawo ki zauna mu kai karshen wanan maganan a nan tun wani bai kaiga ji ba. Shiko jafar jikin shi ne yayi sanyi lakwas don bai taba tunanen mami zata dauki abin da zafi haka ba. Ya mamud ne ya kawar da duk wata magana ta hanyar fadin tunda ita ka zaba din ba laifi ga hakan saidai yana da kyau itama muji ta bakinta ai idan tana son ka shike nan aurene mami ba wani abuba ai. Mai yuyuwa kai itace zabinka ka ganta kana sonta a haka karamar ta ita kuma yarinyar ba kai mata ba a ranta . Kaga ba zamuyi mata dole ba a kanka a matsayin na yar amana a wurin mami din don haka sai muji ta bakin ita yarinyat kuma. Ban gane abinda kake nufi ba mamud mami ta fada tana kallon yaya mamud din taci gaba da fadin kaima kasan tunda ya tursasa mata ai bazatace batayi ba tunda duk mace ko banza neman irinsa takeyi. Mata ma masu aji da ilimi da wayewa suna binsa su sameshi yana gudu sai akan wanan yar kauyen yarinyar idon ka zai sauka sai dai idan kana da wani manufane a kan hakan dai. Banda manufar kome mami ita din ce nagani nake kuma so a hankan don banga wani matsalan da zaisa a hanani aurenta ba a tare da ita. Mtss mami taja wani matsiyacin tsuki tana fadin Jafar kana son bacin raina da jefa yarinyar nan ga fushi wallahi. Mami kiyi hakkuri yanzun nan zan kira ita yarinyar a gaban sa muji ta bakinta idan tace ta yarda dashi shike nan mami sai ki masu fatan alheri a rayuwan su. Me zata fada tunda tana son shi mamud karka mata fa yar kauyece dama nema tafito yi a birni kuma ta samu a yanzu. Gashi ta samu wanda darajan ta da kimarta baikai ta samu ba a yanzu, abinda bata taba tsamanin samun shi ba sai tace maka a a kuma ? Mami please ayi hakkuri aji ta bakin ta idan ta amince ai masu fatan alheri shiyafi yanzu. Mamud na fada maku yarinyarce bana son ya aura gaba daya don haka abar wanan na zancen tambayan ta please mamud. But mami ni kuma ita din nake don banga wata da hankalina ya kwanta da ita ba bayan wanan din. Jafar idan ma tausayinta ne yakaika fadin kana son ta ai ba sai ka furta kalman aure a tsakanin ku ba kana iya taimaka mata ta hanya da dama basai wanan hanyar ba daka fito dashi wai auren ta zakayi. Jafar dake ta faman latsan wayan hannun shi tankar ba da shi ake zancen ba sai lokacin ya dago kai yana fadin. Mami bawai taimakonta kawai nakeson yi ba ni kawai dai auren ta nakeso nayi dan tayi min a raina yana magana a cikin daure fuskan shi. Daga inda hjy take zaune tace da kyau na mijin duniya kai mamuda kira muna yarinyar muji na bakinta yanzu. Na bar gurin da suka sameni zaune don abincin ya gagara ci gareni don haka na dauka na kai kitchen. Daga nan ne na tsaya don yin wanke wanken kayan da akaci abincin safe gasu nan an tara birjit don bakin da akayi gidan. Maganan da mami tayi nake son in fara kiyayyewa da tace in dinga zama a cikin su lami da kande sune yan aiki irina. Ina tsaye na fara tara kayan ne lami na faman sakamin albarka don haka suke min duk lokacin da nashigo zan tayasu wani aiki daya shafesu. Muryan yaya mamud ne a kofan kitchen din yake fadin ke zainab zo mami na magana dake a dakin hjy. Yana tsaye ya tokare hannayen shi a kofan shigowa kitchen din yayin daya zubamin idanuwan shi sai tausayin yadda ya sameni ya kamshi. Juyawa yayi ya fara tafiya haka yasa na dauraye hannaye da sauri nabi bayan yaya mamud din ina jin wa yanda ke falo zaune na fadin. Yar iska yarinya yau zakici uban ki gidan nan don yarinya kin tarowa kanki bala,i da hannun ki. Idona ne ya kawo kwalla don ban kaunan abinda zakai a zagi iyayyena ko kadan saboda sanin daranjan su da nakeyi suko yan gida mami zagi a wurin su ba bakin komai bane a wurin su. Zaune suke su hudu a dakin mami hjy ya mamud dashi gabana ne ya fadi don ganin su har lokacin a dakin . Sallama nayi cikin yar siririyar murya hjy da ya mamud suka amsa min mami kan kai ta dago ta dan kalleni tare da kawar da kanta ga kallona. Zauna a nan ya mamud yace dani yana nuna min wuri daga gefen kofa da nake tsaye saina kai rusunne da sauri ba tare dana zauna ba kamar yadda ya bukaci inyi din ba. Kaina kasa ya mamud naji ya kira suna sai na dago kai a hankali na kalleshi yace mun kirakine muji ta bakin ki a kan wani maganan daba musan dashi ba tsakanin ki da jafar gashi zaune. Ya nuna min shi da hannu sai lokacin na dan saci kallon Jafar din da idonshi sun kada a lokacin da gani shima yana cikin bacin rai ke nan. Jafar ga yanan ya gabatar muna dake a matsayin wace zai aura kamar yadda mami ta bukaci da yakawo mata, matar da zai aura a yanzu. Da sauri na sake dago kai nakai kallona ga Jafar din da shima a yanzu nice yake kallo da idanuwan da suka kade mai lokaci guda. Don haka muke son jin ko kin amince da wanan ra,ayin nasa kema kin shirya da zaki aure shi kamar yadda ya bukata dake. Dukar da kaina nayi kasa don ban san amsan daya dace in bada ba a wurin ga gardadin dayai min tun daren jiyan a mota ina tunane. Ga mami dana hango tsanata saboda wanan zancen daya taso tsakanina dashi mami ta canza min gaba daya daga dare zuwa wanan lokacin kamar ba mami bace a gabana. Don ba wanan yanayin na tausayina data min yau a gare ta ko kadan illa tsana karara da take nuna min a fuskanta. Kiyi magana ke muke saurare ya mamud ya fada yana kallona don jin amsan da zan basu a lokacin. Kai na fara girgizawa a hankali na samu na bude baki da kyat ina fadin ban san da maganan bani koma na sani ya jafar ba sa, an aurena bans shi don matsayina dana iyayyena baikai ko na yaron shi ba yaya. Tunda na fara magana ido kowa ya zuba min sai mami dake fadin nikan nayi mamaki ina hankalin zeey da yatafi har take shirin tafkamin wanan kuskuren duk, , , , Dakata iyami ke a matsayin ki na uwa kin taba ganin inda aka tsiye yarinya haka wai ana tambayanta zabinta kai tsaye. Kiwa Allah kiwa yaran nan adalci iyami tunda ni yanzu ba magana ta kike ji ba ban isa ba ko dan nima din banda mutuncine tunda nima daga kauyen nake ko ? Yarasulu hjy me ya kawo wanan zance kuma har kina danganta kanki da hakan Allah ya gani ni ba manufa ke nan ba ta fada tana kallona az cikin yanayin daba zan iya fassarashi ba a lokacin. Ke tashi ki tafi ya jafar ya fada a tsawace kuma ranshi bace ga wasu jijiyoyin kai da suka mai jasur a goshi abu fa farar fata sai suka mike sukai wani layi layi a saman goshin shi kamar mai tsananin ciwon kai a lokacin. Da gani hankalin shi gaba daya a tashe yake mai a lokacin zainab jeki abinki ya mamud ya sake fada da sauri na mike nabar dakin. Don dama a kage nake dana bar aurin saboda rikicin da nake hangowa a idanuwan su wurin. Ina barin dakin kitchen na nufa har ina hadawa da tuntube don sauri saboda gaba daya na gama tsoracewa da lamarin nasu ga baki dayan su. A daki kan hjy ta tubure tana fadin ya mamud yazo ya mayar da ita dakin ta ba zata zauna inda ba,a san darajan ta ba. Hankalin mami ya tashi tsohuwar taci gaba da fadin yaron nan yace ga zabin shi ta yaya bayan kun gama tsorata yarjnya tun safe yanzu za a kirata ace ta fadi ra, ayinta a gaban kowa ? Ke lokacin da akai maki aure haka mukai maki mami tace hjy kina dai son ganin laifina ne yanzu. Wanan shawaran yaran nan sukazo da shirmen su a gaban kifa akai komai yanzu don Allah hjy kada kija zancen nan inda bai kai ba. Yarinya dai tace ba zatayi dashi ba final Allahu akabar don kuma hankalin ki ya bata yanzu sai kikaji dadin hakan ke. Allah na tuba ashe gaskiyane mace komai tsufanta wayau ta ragagge ne. Ke yanzu har kina murna yar da kika raina kike gani ba a bakin komai ba ta iya budan baki a gaban idon ki yau tace maki batayi da dan naki da kike dauka wani kayan gabas a wurin ki. Niyi tir da wanan hukuncin da kika bari yaron nan ya yanke a gaba me zan zauna inyi tunda banda sauran kima a idon ki. Gidan ki nazo zaki iya min duk wani rashin da, a don yanzu kina ganin ke kin isarwa kanki a komai sai dai da badon jafari ba da sai ince yarinyar nan zainabu ta burgeni sosai . To jinin ka jinin kane banji dadin yadda ta watsawa jafarin kasa a ido ba a gaban kowa don kawai tsoron idon ki data gani a daure kin sakar mata na mujiya . Wanan maganan kuma sai yasa mami ta ji daci a zuciyar ta da kyat dai ta samu ta shawo kan yar tsohuwar ta fasa tafiya saidai mami bataji dadin yadda tsohuwar ta dauki zafi da ita ba haka. Ya jafarko tunda ya fita ya bar mami da su ya mamud a dakin ya bar gidan tun mami bata damu da rashin ganin shi ba har dare yasa ta tambaya ko ina ya shiga haka bai dawo gida ba don hakan ba dabi a shi bane yin dare a waje . Har yakai ta fara tambayan duk wanda ya shigo gidan a cikin mazan dake gidan amsa dayane dai daga shi har security din shi fun safe basa gidan. Ta kira wayan shi yafi a kirga wayan ba ya shiga kwata kwata ba, a samun shi gaba gaba daya ranan. Tunane kala kala mami tayishi ga zafin yarinyar daya mamaye mata rai gaba daya taji ta tsani yarinyar tana dana sanin daukoni dayi ta jefa a cikkn iyalin ta. Gashi kuma hjy ma a nata ban garen haka ya jawo masu matsala da ita don tana matukar son mahaifiyar nata sosai. Gaba daya gidan sai yai min zafi a yan kwanaki biyun nan babu wurin wanda nake dafawa inji sanyi kowa tsanata yake a gidan ga baki daya. Sai gurin hjy kawai ita kuma yanzu ba zama muke sosai ba idan na shiga dakin sai zanyi wani abu don ina gudun mami tashigo ta sameni a ciki zaune yasa na koma kitchen wurin yan aikin da dukkan mu kawomu akayi gidan don aiki. Hjy tayi fadan hakan har ta gaji ta saka min ido ta kyale ga yadda lamarin ya juye muna. Ga zagi da nake sha a gun yan matan gidan a yanzu yayi yawa har takai ranan Rufaida tayi min mari biyu masu kyau. Saida anty Aisha tayi mata fadan hakan kan su dan sasautamin don Allah tunda ba laifina bane shine ya ganni yace yana sona ai. Ba nice na leke mashi ba kuma yanzu ba wanan zancen budan bakin Rufaida sai cewa tayi Aisha kece baki san halin yan kauyen nan ba. Mudake tare dasu muka san halin su basu shigowa gari sai sun shirya an asirce su yadda duk namijin daya gansu ba zai iya kawar da idon shi a kansu ba meye ba a yi yanzu halan. Gasu da sihiri mai dafi da kaifi wanda in basu ba kainan dan birni kace ai maka saidai aci kudin mu ga banza. Tace au hakane nima fa abin yaban mamaki ace wai duk wanan baiwa da jin kan na ya jafar ga ilimi da wayewa amma ace wai zee yake so shi . Wanan to zarcin da suke min ne yasa hankalina ya kara dagawa sosai a gidan naji ina son komawa kauyen mu baki alaikum ba tare dana fadawa kowa ba. Sai dai kuma ina jin tsoro don ban san kan garin ba kada in fita ni kadai a ganni ba kauya a saceni. Tunda na fara jin ana fadin jibine tafiya Abuja na fara funane a raina don nagama yankewa kaina hukunci . Gara kawai in gudu in koma gida ko ta kan anty safiya data kawoni da itama tazo tayi min tas kan wanan zancen a gaban mami ta wanke tas wanda nasan hakan tayi shine don kawai ta wanke kanta a wurin mami din. Saida na bari hjy tayi barci na mike na fara hada kayana a cikin jakkata inayi ina juyowa ina kallon ta kada ta tashi ta ganni. Aiko ban tsira ba don ashe idon ta biyu tun dana fara take kallon abinda nakeyi. Juyowan da zanyi sai ganin ta nayi zaund ta kura min ido kaduwa nayi don ban zaci hakan ba na dauka tayi nisan barci a lokacin. Ikon Allah yar nan me kike kokarin yine karda ace guduwa kike son yi daga gidan nan sai kawai na durkushe a wurin ina kuka ina fadin hjy gida zan tafi. Babu mai sona a gidan nan mami ma fushi take dani har su anty Aisha da nake dan dafawa naji sanyi yanzu itama bata sona suncewa asiri nakeyiwa mutane suke sona. Sai naga tsohuwar ta danyi murmushi can kuma tace kai yaro dai yarone ke in banda abinki dama ai duk wanda Allah ya mayar sani abu a duniya saiya fuskaci kalubali mai tsanani kafin ya taka nasaran shi. Ba wanda ya tsamaci haka gareki sai gashi kwatsam Allah ya doraki a kan kowa dake gaban ki ga yanzu sun san da sani ke din yar bawaice kinga dole ko su nuna hassadan hakan gareki Yanzu kinga mayar da kayan nan kafin gari ya waye wani ya shigo dakin nan yasan abinda kikai kokarin aikatawa har makiyan naki suji suyi maki dariya. Hjy Abujan ne da za a koma ban son zuwa gara dai in tafi tun muna nan kusa da gida. Yar nan ashe haka kike da gardaman banza ko dai kin san inda Jafarin din yake ne ? Hakan data fada yasani fadi wallahi hjy babu komai a tsakanin mu ban san komai ba game dashi. To wanan tafiyan da zakiyi ne zai sa a kara zargin ki a dauka kun hada baki dashine kan ki gudu hakan kuma na iya jefa iyayyen ki dake a cikin wani mawuyaci hali. Kallon ta nayi da mamaki tace kwarai kin dai san iyami na da halin da zata sa a daure kowa naki a kasan nan ko. Tsoron maganan da hjy ta fada ya kamani sai na kara fashewa da wani irin kuka tace kinga ki shiru kin san yanzu darene kada wani yajiyo mu a waje. Na maki alkawari muddin ina raye zan tsaya maku har burin ku yaci ka duk da naga kin sare kin ji tsoron barazanan uwar taku har kina fadin shine ya tsara hakan. Da sauri nace wallahi hjy ban san komai ba a kan zancen nan ni dai kawai komai da yace nayi a wurin nayi. Da haka har ta shawo kaina muna dan hira kafin ta mike ta shiga ban daki ta dauro alwala tana fitowa nima na shiga don cewa da tayi min in yawaita yawan ibada in roki ubangiji sauki. Naji dadin wanan shawaran da tsohuwar ta bani sosai don duk kunci dake zuciyana sai na nemeshi na rasa washe gari naji na tashi raina ya sake duk da mutanen gidan basu daina halin da suke min sai dai ko dunyima hakan bai damuwa na yanzu don shawaran dana samu daga tsohuwar. Ga kuma iyayyena da nakejin tsoron lefin da basuji ba basu gani ba yazo ya shafesu ya zama dole a gareni in daure ga duk abinda zan gani don yakin nawa ni kadai kamar yadda hjy din ta fada min kar in yarda in kada iyayyena ga tashin hankali. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 ZAINAB IDRIS MAKAWA JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI FATAN ALHERI GA MUSUMAI DUNIYA BAKI DAYA AMIN, , , , , Yar uwa ban son ki da shiga hakkin wani ko wata don Allah kiyi kokari ki biya kafin ki karanta kada ki raina hakkin wani a kanki gara ace kece mai bi da abiki. Allah ubangiji ya bamu ikon aikata alheri da fin karfin zukatan mu Allah ka sadamu da rahamomin sa amin. Mami ta shigo dakin wurin hjy a lokacin ina zaune ina gyarawa hjy kayan ta da aka wanke don da ta cire kaya zan dauka in hada danawa in wanke tas. Shine hjy ta tsayar dani in gyara mata jakkar kayanta muna dan hira ina dariya don gareta kadai nake jin dadi a gidan bayan ita sai dan dama anty Aisha duk da yanzu itama akwai sauyi sosai a fuskanta gareni. Mami na shigowa dakin saidana kadu dan fargaban daya ziyarci zuciyana lokaci guda don yanzu ina tsoron ta sameni a dakin tare da hjy saboda kada ta yi min cin mutunci. Don haka nake iya kokarina wajen kaskantar da kaina a garesu kamar yadda suke nufi da zancen su gareni. Ba wai suna takuramin ga hakan bane saidai ko sakin fuska ance rahamane to babu wanan yanzu tsakani da kowa a gidan sai hjy sai ko yan samarin mami jalal da jamal da basu taba nuna min wani canji ba a fuskokin su. Kamar yadda muka saba hakan ne har yanzu a wurin su do shi jalal sarkin wasa har yakan min ba, a da fadin amaryan mu. A cikin wasa hakan yasa yanzuma dana fito daga dakin hjy na sameshi zaune tare da yan matan gidan yana cin abinci suna hira nazo zan wuce zuwa kitchen wurin su mama kande. Muryan shi naji yana fadin a, a ke kuma armaryan mu yau ko dan gaisuwan ban samu ko dai har kin fara amarcin ne mu fara kawo gaisuwa don yanzu ke dan kin zama key a gurin mu sai an murdaki za a bude, Kai kai haba jalal wanan irin maganan kesa kuna kara hurawa yarinyar nan kai amaryan wa kuma wanan yar kauyen yar aikin kakewa irin wanan maganan. Sai ta dauka kamar daidai take da kowa a gidan nan yanzu don dan kauye bai iya samun wuri ba. Wuce daidai yanzu tunda har ta iya halbo zuciyar ya J aiko tafi kowa ke nan dai a yanzu tunda ta doke duk yan matan dake garin nan kai bama garin nan kadai ba duk kasan nan zance. Ya jamal naci karo dashi da sauri na dan duka ina gaidashi da kwana yadda na saba na shige kitchen haka yasa ban ji sauran maganganun su ba a wurin. Ashe a bayana har zancen yaso koma masu fada don Rufaida ta dauki zancen da zafi har gaban mami saida maganan ya kaisu. Mami kan jalal taiwa fada sosai a wurin jamal yace haba mami kina wanan maganan haka gaban kowa bayan yarinyar nan kin sanda cewa itace dai ya jafar ya tsayar zai aure kice kika sanda wanan zancen a yanzu. Amma shi ya J din ai ya dade da nuna yana kaunar zeey din ki tun muna abuja da kika fara ganin su wurin dinner rantsar daku . Dalilin kine fa har ya J ya fara kula yarinyar nan yanzu kuma kina fadan wanan irin maganan a kanshi idan bakya son wanan abin ki mayar da yarinyar hannun iyayyenta kowa ya huta idan yana so sai yaje can gurin iyayyenta ya nemeta. Kai jamal ka rufa min baki da wanan bakar maganan da kake fadi duk yan matan dake garin nan ace baiga wace tayi mashi sai wanan zeey din da bata da asali yar kauye. Meye to aciki mami ya tambaya da mamaki yana kallon ta tare da fadin itace fa zabinsa mami don me kike kokarin kawo matsala a cikin zancen nan yanzu ? Jamal ta fada a cikin tsawa tare da fadin ka fita a idona tun kan ranka yakai ga baci dama halin ku daya da Jafar ai don baku san ciwon kanku ba. Mami don kawai na fadi gaskiya ki barshi mana yayi abinda yake so zaifi ace kin takura kanki akan wanan magana. Yana fadin hakan ban tsaya sauraren me zata fadaba ya juya wurin jalal yana fadin kai ya mutafi ko ? Jalal din dakewa mamin su kallon mamakine ya mike yana fadin mami zamu tafi wurin ticket din don a samu da wuri sai dai bamu san na mutum nawa za,a saya ba idan munje. Ajiyan zuciya mami ta sauke don yanda ranta ya baci da zancen yaran da safen nan tana fadin naku sainawa da hajiya da Aisha Nuriya da yaran tunda shi mamud din ya tafi tun jiya. Mami zeey din bada ita za, a tafi bane wanan karon ko a nan za a barta ne wanan karon kinsan fa basu haduwa dasu Rufaida a wuri daya ko banza. Ya za a barta a nan jamal ya fada dole ai da ita za a tafi ko dan taimakawa hjy wa zai iya da lalurar ta idan ba ita ba. Jin wanan zancen yasa mami ta danyi tunane kafin tace da ita zamu tafi amma mota zatabi wanan karin ita dasu kande da lami da drivobi. Haba mami ai hakan ba girman ki bane yarinyar nan meye laifin ta dankine fa duk yaja mata koma meye a wurin ku zeey din nan tana da halin kirki gun kowa. Kallon data watsa masune yasa su fita daga dakin da sauri har suka kai wurin sayar da ticket din suka sayo jamal yace su hada da nawa su saya koma me mami zatace dai sun saya ai. Hjy kawai zamu fadawa da mun koma gidan zai fi suna wanan maganan ne wayan ya jamal yayi kara ya dauka da mamaki yake kallon wayan daya nuna lamban kasar South Africa. Waye kuma ya kirani daga south africa ya fada yana nunawa dan uwan nasa dayake tuki a lokacin. May be wani friend din kane ko ya fada shima yana kallon lamban kafin ya mayar da hankalin shi ga tukin da yakeyi din. Jamal kuma ya dauki wayan da hello muryan dan uwan shi jafar yaji yana fadin kai jamal ya kuna lafiya ya mami. Ya Jackson kaine kayi nisa fa ka daga hankalin mami sosai don har yanzu bata koma daidai ba rashin jin inda ka shiga. No ball kawai nazo kallo don in samu natsuwa a tare dani ya kana gidane ko waje ya tambayi dan uwan nasa. Wallahi ya gamu nan munzo yankar ticket gobe zamu koma Abuja mami zasu fara aiki monday din nan mai zuwa. Wanan yarinyar fa ya tambaya sai jamal din yace yanzun haka zancen ta muke a mota don mami tace wai kada mu yanki ticket da ita a mota zasu tafi ita da sauran yan aiki kamar ta. Yanzun fa ya tambaya No mun yanko da ita zamu hada da hjy saitawa mami magana fine idan ka koma gida kayi flashing layin nan zan yi magana da ita ok ya nagode take care. Sun dan biya wani guri kafin su dawo sai bayan sallah azahar suka dawo gidan a dakin hjy suka sameta ita kadai a dakin sun gaisa take fadin yau bata gansu ba tun safe. Jalal yace dazun na shigo da niyar idan nagama karyawa in shigo mu gaisa sai wa yanan yan rainin hankalin suka so raina min wayau suka ja har mami tayi min fada kan yarinyar nan zainab. Nan dai yake fada mata komai har zancen sayo ticket din da sukayi dani take fadin sun mata daidai don daba haka ba ko ita ba zata tafi ba idan ba wanan yarinyar cikin su don ko taje wa zai kula da ita a can kamarta. Karbi waya wani ke son magana dake ya fada a dake sai ta watso mai wani irin kallo tana fadin wani wa ka samomin da yake son magana dani. Wayan ya kara mata a kunne jafar din yana jin rikicin da sukeyi a dakin yana murmushi kafin yace ke tsohuwa kanki nake so nawa zaki sayar min a turo maki kudi gobe nazo na sare. Dan nema mai muryan turawa ka dauka ba zan sheda muryan ka bane halan ? Jafari ina ka shige kabar mutane a cikin damuaa haka kan dan magana kankani ka yankewa kanka wanan hukucin. Ashe kai baka cika jarumi ba kaja fadan da baka iyawa da uwarka na dauka kai cikkaken jarumi ne ashe ba haka ba. Matsoraci kawai yace lailai tsohuwar nan kin gama sani yau zan ko gwada maku ni jadumine da bai magana biyu. Ni baka da bakin fadar komai yanzu a gabana tunda kaja fada kabar yar mutane nan da yaki ita kadai. Hjy wa ya isa ya yakar min mata ban gama dashi ba ai ita mami ta sani tasan bana magana biyu yasa na bata wuri ta sauko daga fushin data dauka. Yanzun dai ba wanan ba wallahi tafiya ne ya kamani gani nan a kasan africa ta kudu nazo wani abu zan dawo da yardan Allah nan zuwa jibi idan Allah ya kaimu. Nikan daka ban mamaki sai ince wanan jarumin nawa bai cika jarumin maza ba ashe a duniya. Yanzu dai hjy ina yarinyar take don nasan nabar sarkin yaki a gida yasa ban daga hankaliba ga zancen. Yarinya kan na nan tana fuskantar matsi da tsangwama don har tayi niyar guduwa wallahi na dakatar da ita daga hakan. Kallon juna jamal da dan uwanshi sukayi shikuma yana fadin hjy don Allah kada ki bari ta gudu daga gidan nan idan na dawo zan sake zama na karshe da mami akan zancen. Bazata ko ina ba a yanzu kan sai dai ban sanarwa gaba ba idan ka kasa shawo kan uwartaka kan zancen. Ba jamal waya yace jamal din ya karba yake fadin idan mami ta tambaya ka fada mata nine nace a saya da ita. An gama yaya ya fada yana dariya suka danyi maganan su kafin yace jamal din ya ban wayan. Ina kitchen abinci lami ke kwasa ina mika mata ledan da take saka tuwon data tuke a cikin sa naji muryan ya jalal na fadin ke zeey karbi waya ana magana dake a bayana.. Sai da gabana ya fadi kanfin in juyo ina fuskanta shi bai tsaya jiran komai ba kawai ya ban wayan na karba. Tare da karawa a kunnena gami da sallama duk da bansan mai magana ba a lokacin amma sai da nayi sallaman dan koyi da sunan ma,aiki S A W . Ajiyan zuciya naji an sauke wanda hakan ya tabbatar min dashi ne a layin duk da ban tabbatar da hakan ba lokacin. Ido lumshi yana maijin wani iri a zuciyar shi ya amsa sallaman tare da fadin ya kike kina lafiya ko kina nan kina aikin kuka da tunane ? Ko baki maganane ya fada kamar bashine jafar din mami mai yawan daure fuska ga kowa na gidan ba in badon ina yawan zama da hjy ba ina ganin yadda yake sakin jiki a gaban tsohuwar zan iya rantsaewa da baya dariya tunda yake don yawan daure fuskanshi koda yan uwan shi maza. Sai yau gashi shike min magana mai kama da ba,a a kunnena haka ina jin shi. Sake maimaita abinda ya fada yayi yana fadin ko bakiji mena fada ba kina nan kin saka kanki a damuwa ko ? Aa,a na samu kaina da fadi a cikin sanyin murya ina mai girgiza kai kamar yana gabana a lokacin. To ki daina damuwa don banga laifin ki ba ko kadan a ranan don na gama fahintar dama ke matsoraciyace sosai. Ko kin fasa taimakawa yan uwar ki da innan kine in sani don in kyaleki in neme wata. Daga inda nake na dan runtse idanuwa don da ace shidin sa,a nace da zan so haka ya kasance ko dan kyaushi da wayewan shi saidai nasan shirme nakeyi don wutsiyan rakumi yayi nisa da kasa. Shi din ba ajin irin mu bane yayan talakawa kamar yadda mami ta fada muryan shine ya katse min tunane yana fadin. Da kun koma abuja zakici gaba da karatun ki don nayiwa mamud magana yanzu ma abinda ya kaishi Abuja ke nan zancen karatun ki don zanfi son sai kin kamala secondary kafin in aure ki mu tafi. Nagode yaya na fada a dan kunyace danaji zancen karatu Allah yasa dai kina da kokaerin karatun kamar yadda nake zafo ya fada. Gane bazanyi magana kamar yadda yakeso ba yasa shi fadin ni zan kashe tunda har da magana a hanaki yi dani yanzu. Sai an jima nace a kage don na matsu ya kashe wayan in huta da wanan bugun zuciyar danake ji a lokacin. Maimakon naji ya kashe din sai ji nayi yana fadin kingaji dajin muryana ne to idan kin gaji ni ban gaji ba zan iya barin wayan a haka har lokacin dana gama sauran bugun zuciyarki da numfashin ki tunda naga a tsorace kike. Ban kaiga sani anmsar da zan bashi ba sai muryan Nazira ke fadin ji min yar iska ana aiki kinzo nan kin labe kina waya da maza ko ? Uban wama ya baki wanan wayan dake hannun ki haka ko sato wayan mutane kikayi kina waya dashi yar iska muga wayan har sata kika fara a gidan nan ashe yau Allah ya tona maki asiri magen banza mai kwanciyar kwanto ayi sake tayi wuf da abin mutum. Duk abinda take fada a cikin kunnen ya Jafar yana ji bata farga ba don bata kai ga karban wayan ba tana shirin tara min mutane a wurin. Shigeya yar kauye mara gata da asali watau ke kinzo birni kinsha jan miya har kina kokarin sace zuciyar dan masu gida da kissan ki na yan kauye ko ? Ki rasa wanda zaki likewa kamar chewing gun sai ya J da kowan mu a nan take zaman jiran shi mutumin da ko ganin shi tsadane a wurin mu. Ke amma dan bakin tsafin ki da maitar ki har kika iya sanin yadda kika ja hankalinki gareshi yasan da zaman ki gidan nan maza ban wayan naga ko wayan waye kika sace. Idona ya riga daya ciko da ruwan hawaye a cikin karfin hali nake fadin ni ba barauniya bace kuma bana maita waya kuma ba satan shi nayi ba ya jalal ne ya kawo min shi yanzu da kansa. Lami daga gefena take fadin haba Naziran hjy yanzu fa jalal ya kawo mata wayan nan muna tsaka da aiki ya miko mata shi. Karyane wallahi satoshi tayi yar iska watau ke zaki goya mata baya ta dinga muna barna a gidan nan wallahi yau sai kowa yaji sata ta fara muna don kowa ya kankanta kayan shi tunda muna tare da barauniya. Wallahi ni ba sata nayi ba na fada don ni ko tsinken wani ban taba tabawa a gidan nan na samu kaina da fada cikin sheshekar kuka sai ga Rufaida da salma dake falo sun shigo suna tambaya take fada masu. Wallahi yarinyar nan na kama ta sato waya tana magana dashi a nan Allah ya kawoni da maishi yau yayi hasara iphone ce kamar ta jamal salma ke fada. Ba sata nayi ba anty salma yanzu ya jalal ya kawo min wayan inyi magana karya take Nazifa da Rufaida suka hada baki wurin fada. Satan shi kikayi ke har kina da darajan da zasu baki wayan su shegiya yau Allah ya tona maki asiri don dole sai kin bar gidan nan yau. Hasken da wayan yayi daga hannuna yasa salma fadin dawa kike waya yar mami a hankali na dago kai na kalleta kafin in mayar da kaina a kasa ba tare dana bata amsa ba. Dawa ko zatai waya banda munafukan iyayyen tan nan dake mata tsafi a gida. Nazifa kin san koda ya J take waya kike fadan wanan maganan haka don duk abinda kike fada yana jin ki tun dazun don wayan sai yanzu aka kashe ta. Sai jikin ta yai sanyi ta juya tana fadin ke ki bari don Allah dama wayan a kunne take ashe salma tace wallahi shi yasa nake fada maki ku fita harkan yarinyar nan ku kyaleta ba kuji. Zeey yar mami kin gama wayan ki miko min muryan ya jalal ne daya dawo yake fadan haka daga kofa sai kuma yai shiru yana binsu da kallo lokaci guda. Ina sharan hawaye nake miko mai wayan tare da fadin nagode duk suna tsaye suna kallon mu a wajen lami tace haka kawai kinzo kin dafawa yar mutane sata ba gaira ba dalili kina neman tara mata mutane ki kunyata ta. Na fada maki shi ya kawo mata wayan yanzu muna aiki a wurin nan amma bakiji ba. Ba dole in zargeta ba ta fada tana watso min wani kallon tsana daga inda take tsaye Rufaida kuma wani irin kallo mai nuna matukar tsana gareni take jifana dashi kafin tace. Ya J din kike waya dashi a boye ashe shigiya mai bakin sihiri kin rantse sai kin sace mai zuciya a gidan nan ko to tsaya kiji . Ya J ba sa, an yin ki bane gaja irin ki yar kauye idan ko ba aikin asiriba me ya gani a jikin ki yake wanan haukan haka akanki . Jeki ki tambaye sa ai dan uwan ki ne don me zaku ga laifin yar mutane a banza ga mailefin daya nace mata hjy tsohuwa ta fada daga bayan su don layin jalal daya kira yake fada masu hankali tashe abinda suke min a kitchen din. Hjy bashi keda laifi ba wanan dince mai laifin ita da batar aika mai da asiri ba ke rufaida ki shiga hankalin ki dani kada ki kawo min diban albarka a gaba wurin nan. Ba kunya har kike maganan asiri haka a gabana yaushe kika san wani aikin asiri can idan ma shi kuke tunane ai da asiri tai masa daba hakan ba. Da sauri ta dago ido tana kallon hjy din tace eh da idan ya zare a gidan nan baijin assh a kanta wanan ake kira da asiri. Wanan ko kauna zallasa so da kaunane nata yaja hankalin shi har don sa ya rufe ya gama mutuwa a kanta ta yadda bai iya jin kiran kowa a yanzu. Mami dake kwance salma ta kirata ta fito da dan saurin ta zuwa kitchen din ta samu hjy na yanka sababi a kofan shiga kitchen din. Tsaye take bata san abinda ke mata dadi a wurin ba sai faman tunane take a ranta ita kan ta daukowa kanta jidali da hannun ta. Ita kan dame wanan abin yai kama me jafar dinta ya gani gun wanan yar haka ya mace a kanta ya hanata sakat a zuciyar ta yan kwanakin nan kan wanan magana. Wai me ya kawo wanan zace mami ta fada daga bayan mahaifiyar nata inda take tsaye. Mami wanan munafukan ne na kama a kitchen yanzu da wayan su jalal a hannun ta shine na zata satowa tayi take waya dashi nake mata magana hjy ta taso. Dawa kike waya zeey ya akayi wayan su ma yazo hannun ki har kike waya dashi. Diyan ki zaki tambaya wanan don su suka bata wayam ba sata tayi ba a gurin su hjy ta fada a hasale ta juya wurina tana fadin fito mu tafi daki ba zan barki a nan ba tunda basu da imani. Daga mami har yan matan dake tsaye su biyu suka dago ido suka kalli junan su . Ina tsaye rakube a jikin bango ban ko motsaba don tsoro naji mami tace ba dake ake magana bane kinyiwa mutane tsaye haka. Na dago matacciyar kafata daya gama sanyi da sarewa na fara dan tafiya nazo na ratsa tsakiyan su na fice daga kitchen din ina jin wani iri a zuciyata sosai. Nazo wucewa gaban mami dake tsaye a kofan naji tana fadin ku fito daga kitchen din nan kuma da tada zaune tsaye kuke wallahi ina ruwan ku tunda ba wayan ku ta dauka ba. Da kyat naga dakin don nisan da yai min lokacin ina shiga na zauna daga kofa na fara rera kuka a fili hjy na shigowa dakin tana mitan zancen. Nace hjy don Allah don so da kikewa Annabi ki roki mami ta mayar dani gidan mu hannun iyayyena . Ba sai ta rokeni ba ma zeey nima wanan abjn ya fara isata hakana don haka ki shirya gobe a mayar dake gida. Mudai shirya a maidamu gida zaki fada don ba yar nan kadai zata tafi a gobe har dani yar kauyen uwar yan kauye zamu tafi kafanta kafana a gidan nan goben, har gaban iyayyen ta zan kaita in yaso dan naki yaje gurin iyayyen ta ya nemeta idan yafi maki sauki. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣7️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GARE KU YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN, , , , , Jin abinda hjy ke fadi yasa dole na daina kuka don ba zanso nayi sanadin mami da mahaifiyar ta arayuwana ba don na samesu cikin so da kauna iri ta da mahaifi a tsakanin su. Ni na bar shiri sai ga tsohuwar ita tana hada kayan ta wai ita gida zata bata kara kwana gidan mami. Hakan ya tayar da hankalin kowa a gidan don mami har kasa take tana ba hjy hakkuri hjy ko sai fada take tana fadin. Sam bazan zauna inga wanan cin fuskan da yaran ki kewa yar mutane ba haka idan ke kin kasa da ita ni zan tafi da ita can kauyen mu in yaso shi Jafari yazo gurina ya nemi auren ta. Kin dauko amana dadi dadi kina riko tsakani da Allah ashe rikon naki ga yar baikai ciki ba da har dan ki zaiji shawan hada iri da ita ki fito kina fadin baki yarda ba don ita din ba diyar kowa bane a kasan nan. Gasu nan birjit a gari dan naki yaje ya zabi daidai dashi a kadarta yau Aisha ce dan tallakawa ya fito nema ashe ba zaki iya bada aurenta ba ga wanda take so ? Don kawai yanzu kudi ya bude maki ido kowa kuna kallon shi a mutumin banza koko samun abokai yan duniya dakikayi ne yanzu ya sauya maki yanayi. Idan ma hakan ne sai kije ki aura mashi wacce duk kike son aure mai din ita kuma wanan din zan tafi da ita gurina in sakata karatu idan ina raye wata ran sai kince ba ita bace a gidan nan. Kuma ki sani koda danki zai mutu ne idan yazo ba zan bashi yar nan ba muddin na bar gidan nan da ita. Inda nake ta kalla tana fadin tashi muje yar nan nasan dai ko ban san kowa a garin nan bazan kwana a waje ba yau zan samu na Allah da zasu duba tsufana su tausaya min. Tana kokarin sungumar jakkan kayan ta daga saman gado inda yake ajiye mami tayi saurin dafe jakkar tana fadin hjy don Allah ki rufa min asiri a garin nan kada kije ko ina gwiwa biyu nakai kasa tare da daga hannaye biyu sama ina fadin. Hjy don girman Allah kiwa mami hakkuri karki fushi da mami ba laifin ta bane laifin zuciyane. Da yau danta bai bijiro da wanan zancen ba da mami batai fushi dani ba har gobe mami uwace a gareni mai mutunci da kima a idona. Bazan taba mance mutuncinta a gareni ba don Allah kiyi hakkuri ni in tafi ko mami da yaran ta zasu zauna lafiya. Hjy ba zan biki ba zan koma gidan ubana in zauna duk abinda Allah yayi min mai kyaune a rayuwata Allah ne shedata wani kalami na soyayya bai taba hadani dasu yaya ba a gidan nan wanan yana daga cikin kaddaran rayuwata. Don Allah hjy kiyi hakkuri ki zauna a cikin gatan ki kada ki fushi da mami sabodani kada laifin hakan nima yazo ya shafeni watarana. Ina fadin hakan na fashe da wani irin kuka mai tsanani na mike tare da nufar wardrobe inda kayana yake cikin jakka a jere ina kokarin daukan jakkar. Takwara ina yanzun kika gama bani hakkuri akan uwarki idan nayi hakkuri ke kuma ina zaki a cikin daren nan . Ko so kike in fasa hakkuri da uwar taku mu tafi tare kafata kafarki mubar gidan nan a yau din nan basai gobe ba. Hjy ba Anchau zan tafi yau din ba zanyi kokari in kai kaina gidan anty safiya har kashe gari ta sakani mota in koma gida nufina ke nan muddin barina gidan mami zaisa ta samu sallama tsakanin ta daku. Ba zaki bar gidan nan ba koda bana raye sai idan aure ya rabaku da uwarki kamar yadda aure zai rabata da yarta Indo. Muryan mami ke fadin ke zeey mayar da kayan nan ki fice daga nan ki ban wuri da hjy kije gun su kande ko dakin Aisha ki jirani. Mami ta bani umurni da hakan da sauri na juya na bar dakin nan na barsu tare da mahaifiyar ta na nufi gurin su mama kande na zauna. Sun dade da mami da hjy a dakin har bayan magariba san nan salma tace dani hjy tana kirana a daki. Na mike na tafi ina addu,a a raina Allah yasa sun yake hukuncin in koma gidane gaban iyayyena zaifi min wanan zaman rashin yancin kai da banda shi a gidan mami yau har ni zainab Nazifa ta dafawa satan waya. Hajiya ta idar da sallah har isha,i ina shiga da sallama fuskan tar a kaina tana son ta fahinci halinda nake ciki take tambayana da nayi sallah na bata amsa da nayi tun dazun hjy. Zauna ki zuba muna abinci ta fada kai tsaye dai umurni ta bani babu daman yin mussu gareta ke nan. Itama ba wani cika mata nayi sosai ba na dai zuba kadan kadan sai dai nawa din yafi zama kadan don nasan ba zan iya cinye wanda ma na zuba din ba. Sai faman cakulan abincin nakeyi cikin sanyin jiki itama dai hjyn haka dai take kokari tura abincin a bakin ta can naji tace kada ki yarda in hada nawa baki karasa cinye wanan dan abincin da kika zuba ba kamar za,abawa yaron goye. Dole na fara tura abincin da sauri ds kyat nake hadeshi gaba daya raina babu dadi a lokacin har na samu na gama kamar yadda ta umurceni dayi. Ba zancen hira garemu sai kowa yayi shiru a dakin dan dama hjy ma takan dan jefo min magana jefi jefi. Washegari aka tashi da shirin tafiya kamar in dora hannu akai ince wayo ni Allah don banson inyi nisa da gida kuma. Dan dama nan na rike sunan unguwar da muke dana su anty safiya don bam manta da sunan unguwar ba har yanzu a raina. Ina ji ina gani har aka fara fadin a fito da kayan da za a wuce dashi a mota don masu mota zasu rigamu tafiya nake gani. Jakkunan kayan mu gaba daya an labta su a mota hakan yasa naji raina ya kara baki nasan yanzu kan zuwa ba fashi gareni. Hjy ta aikeni dakin mami don in tuna mata zancen maganin ta da za a saya mata nan kaduna. Ina gab da shiga dakin nake jin muryan mami na fadin saida nace kada ku sayo ticket da zeey mota zatabi ita dasu kande baku maganata ba sai da kuka sayo. Ba laifin mu bane mami ya J yasa mu saya mata kinga ko ba zamu ce masa a a ba tunda kudin sane. Gulman ku zai ciku daku har jafar din in dai akan wanan yarinyar ne ido na zuba dani da jafar din a gidan nan za,aga waye zai sare a karshe. Jikina ya sake yaraf kamar kayan wanki inaji kamar in juya kada in shiga dakin a lokacin sai dai na ba zuciyata sanyi na fada dakin da sallama. Duk suka juyo suna amsa min shigowana ya basu daman sulalewa daga dakin suka bar mami tare dani ina fada mata sakon da hjy ta aikoni. Naji ki fada mata za a saye na daga don barin dakin sai naji ta dakatar dani ta hanyar kiran sunana. Da sauri na koma na tsuguna a inda nake tare da dukar da kaina kasa ina sauraren abinda zata fada min a lokacin. Mami ta dan dade tana kallona na dan wani lokaci kafin ta bude baki ta soma magana dani. Zeey ina son ki saurareni dakyau kiji abinda zan fada maki kaina gyada ina wasa da yan yatsun hannuna dana hade a wuri daya ina saurenta. Ba zan taba bari ki bar gidan nan ba koda hjy bata nuna hakan ba don in taimakeki ki taimakeni na raboki da iyayyen ki zuwa nan. Saidai zanso kiyi nisa da duk wani dana bawai jafar ba kwai a a ina nufin gaba dayan su muddin kina son mu zauna lafiya dake a zaman mu. Zancen karatu kuma da mun koma abuja zan sa a nema maki wani makaranta gwaunati ki karasa karafun naki a nan. Saboda haka in kinyi abinda na fada maki kiji dadina idan kuma kinki to ina mai fada maki zeey zaki kwammace dama baki sanni ba a duniyan nan. Na riga nagiwa jafar mata amma saboda ke yana kokarin ya bijire min kan umurni na don kawai ya nuna min shi dan zamani ne. Mami kiyi hakkuri in Allah ya yarda zan kiye ni ban taba magana dashi ba kuma bazan taba ko a bayan ki mami. Shike nan zeey zaki iya tafiya mami ta fada ba sakin fuska a tare da ita zuwa gareni a yanzu haka na mike na fita daga dakin. Karfe biyun rana muka fito mami tana makale da yan matan ta dake mata sallama mu kuma muna guri daya dasu ya jalal da hjy sai Aisha dake daga gefen mu tsaye tana sana,an ta da waya. Ba wanda ya kula da yai min sallama kamar yadda suke sallaman su hjy da su jalal dan dama salma dace zeey za a tafi ke nan na danyi dariyan yake ina fadin sai mun dawo anty salma tace ko sai munzo ba. Haka motar mu ya daga kamar su jawoni su fidani daga cikin motar yadda suke watsa min harara daga sama har kasa kuma kowa ya kula da hakan. Karfe hudu duk muna cikin gidan mami na Abuja da farko mami taso raba muna daki ni da hjy don tace naje daki daya zamu zauna dasu kande a nan. Sai hjy tace ni kuma na zauna dawa idan kin kaita can kinsan ko a gida da yaran yayan ki nake zama ai. Don haka barmin ita mu zauna tare kawatace ko banza tare muke kashewa mu bisa a dakin mu daga ni sai ita. Haka yasa na koma da zama a dakina dana bari da farko kafin mu wuce kaduna don yanzun ma a nan zamu zauna da hjy din. Mami bata da lokacin zama gida tare da mu karfe taran safe baya mata a gida don hakane nake tashi da sassafe nai mata aiyukan dana saba mata a dakin ta harta shirya ta tafi. Kamar yadda mami ta canza min hakan nima nake canza don a gurguje zan karasa aikina kafin ta fita na bar mata dakin sai idan ta gama zata rufo dakin ta kawo makulli gurin hjyn ta ta fice. Satin mu daya da zuwa wani yammaci muna zaune da dare a falon dukan mu ya mamud ya shigo muka shiga gaida shi da dawo yana amsa muna. Ina zaune kusa da kafan hjy naji yana fadin mami monday fa yarki zata fara shiga school don na samo mata makaranta a nan garin. Da bakin wa kayin wanan mami ta fada a daidai lokacin da nake murnan hakan ina kuma gode masu a raina sai naji wanan furcin nata a bazata. Gabana ya yanke ya fadi lokaci guda naji taci gaba da fadin ko akwai wanda ya kawo min ita gidan nan ne a cikin ku da kuke nuna min gaba gadi game da yarinyar nan. Meye gaba gadi cikin wana zancen iyami ina taimaka maki yayi kan abinda baki samu lokacin yin sa ba kuma nautin kine kiyi hakan. Ko haka yar taki zata zauna a gida ita bata karatu ta taimaki rayuwan ta nan gaba tunda a zamanin nan kome ka zama idan ba wanan karatun baka cika cikkaken mutum ba a idon jama,a.. Hjy kikan so tarewa yaran nan fada a kan gaskiyata da zai tafi nema mata ai sai ya nemi shawarata yaji abinda na yanke a kanta. Fada muna yanzu ai gashi zaune me kika yanke a kan yar nan a yanzu tunda an hutar dake baki ga hakan ba. Iyami bansan yaushe hali ki ya sauya ya zama na mutanen zamanin nan wajen , , , Hjy ba nufina ke nan ba bandai jin dadin yadda yaran nan suke min abu gaba gadi haka kamar banda daraja a gunsu kamata yayi yazo ya fada min kafin ya samo mata din. Sai kawai yazo yanzu yana fada min magana haka kai tsaye wai mondaya zata fara tafiya wani makarantar ma ka samo mata din. Mami inda yaran nan suke zuwa a nan na sama mata itama sai su dinga zuwa tare duk da ita a secondary section zata zauna. What har nawa za a dinga kashewa a kanta ke nan ina kosu yaran nan kana min korafin yayi yawa da farko saidana haneka. Mami indai zatayi kararun ai karuwan kowa ne nan gaba don haka kiyi hakkuri nayi kuskure ya fada yana dukkar da kanshi kasa alaman ban hakkuri a gareta. Allah ya kyau hjy ta fada tare da dafani tana fadin yar nan nayi maki murna ubangiji yasa a shiga da kafan dama nace. Yaya na gode Allah ya karawa arziki albarka yace ba komai ki dai dage da karatu sunce idan sun gwada ki kinyi nasara zasu iya barin ki inda kike a can kaduna. Allah yasa hjy ta fada tana tattara takardun dake gaban ta alaman zata bar falon ke nan nayi saurin mikewa ina karban kayan daga hannun ta. Sai naji tana fadin wa zai dinga sauke su a school din kai ko driver zai kaiku ya amsa da fadin. Dama ai nike saukesu kafin in shiga office yanzun ma nidin dai ne zan dinga sauke su idan zan fita . Ka nema masu driver daga yanzu da zai dinga sauke su kai ka wuce office din ka kaji abindana fada ta juya wurin hjy tana fadin hjy zan shiga in karasa aiki a daki. Ni dai na aje kayan na fito daga dakin don babu wani abinda zan mata a lokacin don haka na dawo falon na samu hjy da yaya mamud suna hira Aisha ta shige dakinta ko lokacin. Har kasa nakai na kara mai godiya yacs Jafar ne ya saka in sama maki nan don haka shi zaki godewa idan ya dawo. Sai ki mai da hankali ki samu abinda kikaje mema banda wasa ko wani hali na banza don Allah. Nagode yaya na kara fada kaina yana kasa nake fadin hakan don gabana na faduwa tun lkkacin daya ambaci sunan ya Jafar din. Suna ta hiran su da hjy ni kuma ina faman tunanen gargadin hjy a raina a wani bangare kuma ina Allah Allah in ga na fara zuwa makaranta ranan monday din. Rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya hausa suka fada don yau gani a class tare da diya manyan mutane don an gwadani na ketare da kyat don su ba wani gata da zaka nuna masu su yarda su kaika gaba saidai idan kokarin kane ya kaika. Na mayar da hankalina sosai ga karatuna banyi kawa ko aboki ba kamar yadda naga wasu sunayi a school din koda yaushe ni kadai zaka sama a class din ina bitar takarduna da akai mana darasi. Ranan kwatsan mun dawo daga school tun a haraban gidan idona yayi tozali da bodyguard din shi suna tsatsaye waje suna mazurai da idanu don motan mu daya danno kai gidan. Gabana ya shiga faduwa haka na daure na shiga cikin part din mu da sanda nayi arziki babu kowa a falon sai tv dake aiki a falon shi kadai babu mai kallo. Da sauri na shige dakin mu inda na samu hjy zaune ta idar da sallah la,asar a gurin tana zaune. A gurguje na tube uniform din jikina na fada bandaki ban fito ba saidana shirya a cikin wani dogon riga duk kayan da Aisha ta ban ne nake sakawa a jikinao. Na fito na o da sallah nacewa hjy zan leka kitchen in fito daga can na zauna abina ina taya su mama kande aiki har muka karasa na dawo don yin sallah lokacin har mami ta dawo tana dakin ta . Tunda na tun karo wuein kamshin turaren shi ya daki hancina na tsaya na dan saurara ko yana dakin in koma kitchen in zauna har ya fita. Naji banji wani hayaniya a dakin ba na shiga hjy ne zaune ita kade tana ganina take fadin wai ina kika shiga haka daga barin je in dawo naji shiru sai yanzu. Har yaron nan ya dawo daga balaguron da yayi yana tambayan ki bai dade da fita daga dakin nan ba. Wa ke nan na tambaya kamar ban fahince ta ba tace wanan bayahuden mana jafari ai ya dawo tun dazun da ranan nan wai wata kasa yaje kallon ball kawai don barnan kudi. Shiru nayi don ban san me zan fada ba sai kuma hakan yaiwa hjy zafi take fadin anya yar nan kinko damu da yaron nan kamar yadda ya damu dake. Don shi da zuwan shi ke ya fara tambayana na fada mai kindan fita sai gashi shiru shiru baki leko ba dakin nan sai yanzu daya fita. Ko uwar taku tayi nasara a kanki ne tun yanzu nace hjy dan Allah ki daina zancen shi dani kada mami taji ta riga da tayi min kashedi a kanshi tun a kaduna hjy. Ita iyami din hjy ta fada nace hjy kada kiyi mata magana ko dan karatun nan da yanzu nakeyi kada in rasa sa,ata ta wanan dalilin. Wai maryama kanta daya kuwa gaba daya yarinyar nan ta rikice min lokaci guda na kasa gane inda ta dosa kan zancen nan. Haka mukai ta shan bambam dashi ban yarda mun hadu ko sau daya ba a gidan tundaya dawo garin. Ran ba makaranta ina zaune inawa kaina kitso muna hira da hjy ya fado dakin namu daga sallaman shi ya kutso kai ciki. Ba daman in gudu in shige koda bathroom ns don ya riga daya ganni ko dole na daure na gaida shi tare damai an dawo lafiya. Shima yadda ya amsa min naji dadin hakan don ba yabo ba fallasa gareni sai na mike zan bar masu dakin don dai kawai in kaucewa warning din mami gareni. Ki zauna fita zanyi na leko hjy ya fada daga inda yake tsaye yana magana da hjy gashi ya kara haske sosao yayi wani kyau dashi bakin gashin kanshi yayi lub kwace a kanshi sai sheki yakeyi ga wani saje daya bari a fuska tasa wanda bai saba bari shi a fuska ba. Yana gama magana ya sa kai ya fita ya bar dakin gabana sai faduwa yakeyi min don abinda idona ya gane min din duk da ban kalleshi sosai ba ma ke nan. Tun daga wanan rana ban yarda mun kara haduwa dashi ba a gidan don ina ganin shima bai faye zama a gidan ba sosai sai jefi jefi. Ranan zan fito daki ke nan don hjy na falo mami tafita gurin aiki bata dawo ba ina ganin shi na ruga da gudu na koma daki a zatona ko bai ganni ba ne. Saida ya dan dade a zaune kafin ya mike ya nufi dakin namu hjy dai tana zaune tana kallon shi tare da tausayi mu a ranta. Ya tsaya daga bakin kofa dakin bai karasa shigowa dakin ba sai hannun daman shi dayayi amfani dashi wurin rike labulen dakin dashi. Wa kike gudu haka ya fada a cikin muryan nan nasa mai fida sauti mai dadin saurara kunnuwa suka jiyo min hakan. A razane na juyo ina kallon shi yana tsaye a kofan yadda yake a wurin wani irin tsoro da damuwane suka ziyarci zuciya sosai take jikina ya fara kyarna ta yadda har ya fahinci hakan. Hannun ya sauke daya tokare kofa dashi yana gyara suit din dayake sagale a hannun nasa karya fadi. Takowa naga ya fara yi zuwa inda nake haka yasa gana ya tsananta da faduwa sosai a haka ya iso inda nake rakube ga bango ginan dakin. Wani abu naji yana taso min wanda yasa na duntse idona a hankali kafin ya kara tako ya cin min a gurin. Jin kamshin turaren jikin shi gab dani yasa na bude idona na dube shi kadan babu sauran tako a tsakanin mu ko daya a yadda muke tsaye a dakin. Kokarin ja nayi baya sai dai babu inda zan daga don gaba daya ya tare wurin ya tokare hannayen shi a ginan dakin. Shiru ya ratsa dakin ba wanda yai magana a cikkn mu kamar babu kowa a dakin lokacin. Inan tsakiyan hannayen shi har lokacin idanuwa na a rutse kamar naga dodo a gabana. Ga ba hanyar da zanbi in gudu daga wajen don ya hana hakan gareni ya kankame ko wane gefe da zan iya guduwa mashi. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣8️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE DON TURA KUDI ZAKI TURO GA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU NE KACAL KATIN WAYA KI TURA GA WANAN LAYIN 08036959257 YAR UWA DON ALLAH KI DAURE KINA BIYAN HAKKIN MUTANE DON ABIN BAN YAFE BA KALMACE MAI NAUYI GA MUSULMI NAGODE. Har lokacin idanuwana suna a rufe ga numfashinsa ina jin saukan su a kunnuwana idon na kara budewa don jin shirun da yai yawa na dauka nike haukana a lokacin shi baya ko wurin. Yana nan tsaye a yadda yaken haka yasa na soma kokarin sunkuyawa ta kasan hannun shi in samu in wuce don tserar da rayuwata ga mami dashi. Ji nayi ya kamoni ya kankame ni a jikin shi tare da mamaye ni cikin wasu irin abubuwan da ban taba tsintar kaina a cikin ba ko a mafalki ban san da wanan nau,in abinba. Haka kuma ban taba sanin ana wanan abin ba na dauka sai kafiran turawa da nake ganin haka a film danazo gidan mami. Suma din kuma idan sunayi kawar da ido nakeyi koma na tashi na bar wurin ga baki daya. Can kasan makogorna na iya furta innalillahi don Allah ya jafar ka bari kada kayi min sanadin da mami zata koreni gidan nan. Bai kula da abinda nake fadi din ba yaci gaba da abinda yake min kamar ma zancena ya kara mashi kaimi ne . Babu inda baya karkarawa a jikinsa don abinda yake min din nikan na sadakar sai hawayen da ke zubomin kamar an sake famfo na barwa Allah lamarin sa duk abinda Allah ya kaddara min mai kyaune. Muryan shi naji a kunne kamar mai rada yana fadin mami kike tsoro yasa har kika fara guduna kina boyewa ? Idan mami din ta sakaki ki min hakan ko ta hana ki aure ni kamar yadda na bukata ai ba zata hanani wanan bako ? Abinda mami taji ke nan a karshe wurin da take tsaye ta mutu a tsaye don mamakin ganin halin data same mu a ciki a dakin. Da sauri mami ta juya kafin ko wanin mu ya ankara mu farga tana gidan a lokacin ta nufi dakin ta da sauri duk maganan da hajiya ke mata a falon bata jita ba. Karan sakin kofan da mami tayi ne ya farga damu don dai kawai tsoron dake yawa a zuciyana ne daya rufemin ido ban farga da ita ba tun shigowan ta dakin. Yanzu kan sheshekan kuka na fara mai don na kula in dai ba mami ba hjy tsohuwa ce ta rutsamu a halin da muke ciki. Ya jafar don girman Allah don ya rasulillahi ka, , , , , shhh yace tare da fufe min baki da hannun sa na kasa karasa abinda nake nufin fadi karshe. I boldly care da duk wanda zai shigo ya same mu a haka dake dakin nan idan su basu san soyayya yada yake ba wanan ni bai taba damuna tunda sun hana min abinda nake so. Naji yaya ba zaka taba damuwa ba don kai nan gidan kune bayan hakan kuma kai na miji ne dama mace itace da kunya ai. Idan mami ne ta bar wurin nan na tabar da yau ban kwana a gidan nan don ta riga da tayi warning dina tun kan muzo garin nan a kanka. Babu inda zaki tafi matukar ina raye a gidan nan doIn ko kin tafi dawowa zakiyi ita mami tasan halina idan ke baki sani ba. Ban taba cewa ina son abu har in sashi a raina ban in rasa samu wanan abin don haka ba zan soma shi a kanki ba. Naji amma don Allah ka barni in bar gidan nan yanzu tun mami bataji wanan maganan ba yau ta kasheni gidan nan. Don girman Allah ka daga, daga nan in fice na fada cikin wani irin kuka daya zo min mai karfi. Maimakon ya daga daga wurin saima naji yana kokarin kara matseni a jikin shi. Kayi ma Allah kaimun alfama na hadaka da girman iyayyen ka ka daina rike ni haka kana hadani da fushin ubangijin mu. Ka rabu dani ya jafar ka kyale rayuwana hakana ya huta da wanan ukuban daka sakani a cikin sa yanzu. Ka taimakeni ka taimaki rayuwana da kake shirin rusa min yau karatuna shike nan na rasa shi tunda mami kauye zata mayat dani ina gap da gamawa. Nima ki taimake ni zainab don ke kadai zan aura a kasan nan in zauna lafiya dake bani na sawa kaina son ki ba Allah ne ya zaba min ke don hakkurin ki da tarbiyan ki. Abu daya nake so dake shine ki daina cewa zaki bar gidan nan ko karatun ki zai tsaya ba wanda zai faru daga insha Allahu. A razane na dago kai na kalle shi kafin in mayar da kan kasa don kwarji da nauyin da yai min ga kallon shi. Ya daga min gira yana fadin nasan mami zata yarda da bukata na idan na kafe a kanki a cikin sauki. Don farin cikin ta shine nawa itama nawa shine nata bata taba hanani abu nayi shi ba a duniyan sai wanan karon kinga ko zatayi min adalci a nan. So da sannu mami zata fahinta ta yarde mana muyi aure in dauki mu tafi can inda zaki karatu sai kince kin gaji da karatu a rayuwan ki. Wani irin takaicin sa da tsanar sa yake tokare min zuciya ga tausayin kaina danakeji nida kaina kamar in dora hannu aka in ta kurma mai ihun a dakin sai anzo an ceceni. Sai da ya fahinci ya gama hada min zafi akaina don kansa ya janye min daga banga bangan dayi da farko ya tare ko ina da zan iya sulalewa in gudu daga tsayin dayayi a gaba. Kamar jira nake ya nuna min kofa in gudu aiko yana nunawa na sheka da gudu ina kuka mukai karo da hjy a kofa da tazo shiga kamar. Duk da nayi murnan ganin ta amma naji haushin da sai yanzu ta zo dakin duk dadewa da mukayi a tsaye tare dashi zuwan ta yai min kama da zuwan yan sandan indiya da sai an gama cin gari suke isowa. Fadawa nayi a jikin ta ina kuka take ta rude a wurin tana fadin a rikice maikai mata jafari na fadama kabi yarinyar nan a sannu akwai kurciya a tare da ita yanzu sai ka lalabata tukunna. Ask her idan nai mata wani abin just magana nayi mata kan guduna da takeyi kawai. Ba dole ta gujeka ba kaida uwar ka kun saka yar mutane a gaba haka wanan hattaran yai wa yar nan yawa a gidan nan. Ai saika tashi kaje don uwar taku ta dawo har ta leko nan baka sani ba kana nan kana gyara kanka a wurin mace. Hjy kefa kikace sai na jata a hankali zata fahinceni na fara hakan kuma laifine yanzu hjy ? Laifine kan indai zaka dinga sakata kuka haka ko wani lokaci murmushi ya sake mai laushi yana kada kai tare da fadin well i know what to do next barin leka mami ya fada yana mikewa har lokacin ina a jikin hjy ina dan sheshekan kuka. Yana fita daga dakin na dago kai ina fadin shike nan hjy yau zamana ya kare karatun da nakewa murna ya tafi daga gareno don mami korata zatayi yau gidan nan. Saboda kawai kun kebe dashi a nan zata kore ki hauka tayi kome daga haka sai kora kawai. Hjy mami tayi warning dina tun a kaduna kada in yarda in tsaya da danta don ta riga da tayi mai mata ko. Ita iyamin ta fada maki hakan na gyada mata kai kawai ba baki idan ma har ta fadin hakan ai yanzu bake kika bishi ba shi ya biyo ki ko sai tayiwa danta fada shida ke binki. Dakin mami ya nufa direct ba tare da jin komai a zuciyar shi ba duk da hjy ta fada mai mami ta leko dakin mu yana ciki yasan kuma ta ga halin da muke ciki a lokacin. Da sallama ya leka dakin ba,a ansa ba haka yasa kai ya shiga dakin mami ya hango a zaune gefeb gado tayi tagumi da hannayen ta dukka biyu kamar wacce ke cikin tsananin damuwa. Ta rasa abinda ke mata dadi a duniya yaron nan wani abin kunya haka yake son jawo mata ne duk ita a zaton ta ya bar wanan zance ashe shi yanzu yakema ga zancen wata namiji dai sai a barshi ga abinda yake so ya kwallafa rai kuma. Kallon mamaki yake mata har ya karasa bakin gadon da take zaune a kai yace mami lafiya kuwa na ganki a haka ? Wani abu ya faru ne ko wani abin kike tunane haka ke kadai a daki kinyi tagumi. Ido mami ta dago ta gallamai harara da idanuwan ta da suka kade sukai ja tankar zasu fado. Ji take kamar ta wanka mai mari da tana iyawa a yanzu so yake ya tozarta ta ya kunyata ta a idon kawayen ta tozarta. Maganan hjy da take tunawa guda biyu shike taka mata burki ga koran yarinyar nan ta koma kauye. Saidai idan ta tuna da kalamin hjy da take fadin idan ta kori yarnan a gidan ta sai danta yaje gun iyayyen ta a bashi ita ya aure muddin yaje da waliyan shi makusanta ita kuma a barta tana hargowa a gida. Ga kuma barazan hjy data ita kuma idan ta matsa sai ta dauke yar ta koma da ita wurinta ta inganta rayuwan ta fiye da tsamanin ta to me hjyn ke nufi da hakan. Hannun ta ya riko don yaga ko a yanzu da take kallon shi hankalinta na ga tunanen da takeyi a lokacin. Riko hannunta yayi yana fadin haba mami meye zai sakaki irin wanan damuwan haka kinsan fa yanzu aiki na maki ya, , , , Baiyi aune ba yaji saukan mari a lafiyayyen fuskan shi lokaci guda ya dago kai da mamaki yana kallonta da kyar ya iya furta mami you slap me ? Ko zaka ramane tunda yanzu ka girma har bakajin umurnina kake ganin kaika isa har yanzu kake mamakin na mareka ko ? Allah yasa yanzu da idona na gama ganin ku da kazaman yarinyar nan a dakin hjy ba wani ya tsegunta min hakan ba. Yanzun kai bakaji kunya ba ace kamarka jafar kamar kafa kamar kake rugumar wanan kazaman yarinyar zainab yarinyar da wani lokaci ma tsami takeyi da wari. Da sauri ya dago kai a karo na farko tun bayan marin data kwasheshi dashi ya dukar da kanshi bai daga ba yana dafe da wurin cikin mamaki. Wari mami wari fa kikace yarinyar nan tanayi ban taba jin haka ba a tare da ita asalima ni yau wani kamshin ma naji a wurin ta. Mami nifa kome takeyi ina sonta hakana da don itace zabina a duk yadda take ya fada yana kokarin mikewa tsaye. Jikin mami ya sake yaraf kaman ruwan sanyi a gabanta yau jafar ke wanan magana kan mace macen ma wai yar aikin gidan ta wanan wani irin lalacewa ne ya kama dan nata haka? Ganin ya soma batrin dakin don tafiya don marin ma datayi mai shiko a jikinshi ya yadda nunata take ta soma magana tana fadin. Yau da uban ka yana raye jafar zakai min haka ince ga wace nake son ka aura kace kai ba hakan ba yaushe ka fara wanan halin banzan na kafi ban sani ba ? Mami daddy , aiko daddy yana raye ba zai hanani zaban abinda hankalina ya kwanta gareshi don dama daddy yana raye aida yanzun akaiga matsaya ga zancen nan don shi daddy ban taba ganin ya kyamaci wani a rayuwan shi ba And mami kin san koda daddy yake da rai mun fi shakuwa dake fiye da daddyn mu Mami kin kasa fahintana ne kin kasa tausa zuciyar ki akan yarinyar nan why mami zaki hanani abinda nake so. Ba zaka aure ta ba nace bazaka aureta ba ko dole zakai matane mu gani idan zaka iya No mami ba dole amma nasan itama tana sona don naga alaman hakan tare da ita. Tsoron warning dinki gareta ne take amma ba matsala zan gwada sa, a ta tunda kinban dama a yanzu. JAFAR mami ta fada da karfi ya fice dakin ba tare daya juyo ya kalleta ba tunda mami take da danta haka bai taba faruwa a tsakanin su ba sai akan wanan dalili. Me yaron nan yake nufi dani da wanan kalamin nasa tursasa yarinyar nan zaiyi taso shi tunda a yadda ta samemu a dakin da alaman tsoro shi a fuskana don kuka ta samu ina masa. Ma,ana dai shi jafar din ne ke bibiyan ta a dole meya gani ajikina har ya mace ga son yar nan haka. Yarinyar da saida tazo nan ma tadan yi wanan clean din da yake rudin shi ta runtse idanunta tana mai fadin kada Allah yasa so ya rudi yaron na ya aikata wani abinda zaija mata kunya ga idon mutane. Ya zama dole ta jashi a jiki tasan hanyar data bi ta lalashi da lalama ya janye kudirin shi akan yarinyar na don koranta gidanta baida wani fa,ida a yanzu idan tayi amfani da maganan hjy. Zeey bata da laifi ta sani amma wanan dalilin ya jawo mata tsanar yarinyar ba gara ba dalili taji yarinyar ta fita mata rai ga baki daya ta wanan dalilin. A dakin mu hjy ta samu ta lalabe ina kwance lamo sai faman ajiyan zuciya nakeyi ga tunanen abinda ya faru tsakanin mu yaki fita a rai. Duk motsi nayi sai inga kamar a lokacin abin ke faruwa dani uwa uba ga kamshin turaren jikin shi daya dameni a hancina yana kokarin saukar min da kasala a jikina. Mikewa nayi zubur hjy dake zaune ta kalloni tare da fadin ina zaki ban daki zan shiga inyi fitsari na fada. Na shiga ta bini da kallon tausayi tana gyada kai Allah kadai yasan yadda take ji a zuciyar ta kan yaranan a yanzu. Na dan jima a ciki kafin in fito rike da digana dana cire ina daure da tawul a jikina wanda nake kewayawa dashi don a dakin muka same shi wani babba haka dashi fari mai kyau da yan flawer a jikin shi kanana a gefe. Dogon rigar yar katin da anty safiya ta saya min da zanzo gidan mami na jawo na zauna saman kujera ina dan shafawa jikina mai don kada in bushe. Au yar nan wanka kikayi gabanin magariban nan kudai yaran yanzu baku da tadan lokacin yin abu. Hjy na magana tana kallon gashina da har lokacin yana tuke babu kitso a kaina sai fibon dana daure gashin dashi ta bayan kaina. Kafin ta mayar da kallonta da kyau a inda nake tanaci gaba da fadin yadda kike nan da tsari irin hakane mutanen boye ke so su shige jikin mutum a sauke. Mutanen boye kuma hjy na fada ina juyowa gareta tace kwarai kuwa yar nan ai su abinda sukw so ke nan urin wanan sakacin da kukeyi a yanzu take sun shigeka suyi maka illa. Kinga mu a zamanin mu duk irin wa yan nan abubuwan musanshi iyayyen mu na fada muna mukiyaye don tsaron lafiyan mu. Hjy daga yau na daina ba zan sake kewaya a wanan lokacin ba in Allah ya yarda tace dadai yafi maki kam. Waini meya hadaki da mutumin naki ne dazun kike ta wanan kuka ina saka riga a jikina da sauri don maganan da tayi naji wanan maganan. Juyowa nayi da a daidai ina karasa saka rigan na dauki hulan dana dora saman gado na dawo kusa da ita na zauna tare da dan marairaicewa nace hjy ki taimake ni ya jafar yafita daga tsabgata a gidan nan don Allah idan ba haka ba mami zata koreni ta fada. Kin taba ganin inda aka cirewa mutum rai ga abinda yake so farat daya wanab sai uwarku da take ganin tana iya hakan. Wai yau dai ki fada min yar nan shin kina son jafarin nan ko bakya son shi inji da sauri na dago kai na kalli tsohuwar sai kuma na dukar da kaina kasa don bansan amsan da zan bata ba. Ince ina son sa in kaishi ina ko ince banson jinin ta kiri kiri haka a gabanta anya zataci gaba da sona nima duk da nasan tun kan haduwan mu da jafar din tsohuwar take nuna min kauna sahihi. Sai kuma yanzu da take nuna min kauna tankar itace ta haifi iyayyena ta san zafina fiye da kowa ta yaya zan iya bude baki ince banson jikanta mafi soyuwa a gareta ido da ido haka. Nasan wani abu yanzu ma saboda shine ta tsaya min take tsare min komai a gidan yadda ya dace. Murmushi naji tayi tana fadin to ai abu yayi kyau takwara shiya nake kara sonki saboda halin nan naki na alkunya ga kuma girmama mutum saidai iyami taki gane hakan . Ke din wani baiwace a garesu takwara naso iyami ta gane hakan amma idonta ya rufe ta kasa hangon hakan da kanta. Nidai har ta gama maganan daidai ana kiran magariba ga agogon dake dakin namu ta mike da sauri zuwa bandaki do bata wasa da ibanda ta kiran sallah kawai ta kan jira ta mike ko wani lokaci. Bayan kowa ya kammala komai aka fito cin abincin dare kamar yadda aka saba da kyat hjy ta shawo kaina na yarda na fito daga dakin. Mun samu mami a falon har ta fito tana zaune tunda muka tun karo wurin ta dago kallo daya tayi min ta kawar da idon ta gareni tana fadin hjy kin fito yanzu nake zancen ko lafiya yau baki fito da wuri ba haka. Muna daki nida mutumiyar ina bata labari mutanen da can yadda suke rayuwan su ga wuri hjy ki zauna tana fadawa mahaifiyar nata cikin girmamawa gareta. Kafin ta dago kai inda nake tana fadin cikin bada umurni ke jeki aka hijabi a jikin ki baki ganin gidan nan akwai samari ne kike fitow haka dake. Ya ilahi nikan ko me zanyi mami a yanzu bata ganin haske na na juya naji hjy na fadin zancen banza ke nan yo ai shigarta yafi naki dana yarki mutuntuwa bakiwa wanan mai zama kamar arniya a gida ba haka kai babu hula ko dan kwali sai wanan da jikkn ta yake a suturce. Hjy mu muharamin si ne ita fa irin shigar da ta dauko yi ke nan har yaro nan ya jefa kanshi a tarkon ta. Ita yar nan din tasan ta danawa wani tarko da ace hakan take da baki fada ba da bakinki yanzu don da kin gane kabewa ruwane. Tsohuwar ta juyo gareni tana fadi jeki ki saka hijabin ki dawo muci abinci nikan ina shiga dakin ban kara fitowa ba na neme wuri na kwanta ina sharan kwalla. Abuja ba kaduna bane don ko sunan uguwanin su ban gama sani ba sabanin kaduna da tun ban shigo shi ba nake jin sunaye unguwanin cikin shi a bakunan mutanen kauyen mu. Ina barin wurin mami ta mike ta nufi dakin dan lelen ta a karo na farko tun dawowa shi Nigeria don ba dabi,an ta bane zagaya dakin samari nata. Kofan dakin yana rufe ta murda taji shi a ruwa saidai karan tv dake aiki ana wasan kwallo tana dan iya jiyo hayaniya daga inda take tsaye. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 2️⃣9️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA YAR UWA DON TURA KUDINSA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN DARI UKU KACAL A WANAN LAYIN 08036959257 NAGODE GA WANDA YASAN ZAFIN ABINDA NA FADA. Da mamaki ta juya don a zaton ta yana cikin dakin sai dai bataji alaman mutum a part din ba haka ta dawo dakin ta ta nufa direct . Har ta zauna ta bude system dinta da niyar tayi aiki a cikin sa sai zuciyar ta ba zai barta tayi abinda take so ba a lokacin. Har dare duk wanda ya shigo gaida ita tana tambaya idan ya dawo sai suce basuga shigowan shi ba kuma security din shi basa nan saidai ga wayan shi na shiga kuma karshe taji wayan a kashe. Washegari wanan dalilin ya hana mami fita aiki da wuri ni dai nagama mata komai tana bandaki kafin ta fito na karasa na fita daga dakin shiryawa nayi a gurguje kar driver dake kaimu school ya jirani. Mami ta gane me nake nufi don ta fahinci tun jiyan ina gudinta don ban fito ba ita kuma bata tambaya ba duk ta san banda laifin kan hakan amma zuciyar ta ya kasa daina jin haushina. Zazzabi mai karfe gaske yake ji a jikin shi tunda ya falka da safe da kyat ya iya shiga bandaki yai wanka ya fito yayi sallah asuba ya koma ya kwanta. Mami ta fito daga dakinta ta samu hjy zaune a falo ita kadai tana kallo wa,azi da takance kafin mu kai mata kafin mu fita da safe. Mami ke fadin hjy tun jiya banga shigowan jafar ba ko kinga fitan shi da safen nan da mamaki hjy ke fadin yanzun nake maganan shi a raina ni kadai. Ko tafiyan yayi babu salma kuma wanan karo ma mami ta dan yi tunanw tare da fadin anya don bai dade da dawowa ba da wuya ya sake fita. Part din shi ta nufa tana fadin bari in dubashi ko yana ciki har yanzu idan ba fita yayi ba. Murda kofan tayi taji kofan a bude yake haka ya bata daman shiga dakin kai tsaye tsab falon yake kamar kullun sai kamshin dake tashi a cikin sa. Cups har biyu ta gani aje saman dan table din glass din dake gaban kujera sai fararen takardu dasu laptop a gefen kujera aje. Kai tsaye ta nufi dakin kwanan shi ta fara kwankwasa kofan ta fara kwankwasawa sai gana ukune ya amsa da kyar ya iya yin magana ya tambaya da waye ? Nice ta bashi amsa a gadarance ba tare da ta kara furta wani abuba a kai. Kofan a bude yake ya fada yana kokarin cire bargon dake jikin shi rufe mami ta tura kofan ta shiga daga cikin dakin. Ta hango shi yadda yake kwance saman gado ya dan rufe rabin jikin shi da bargon. Lafiya kake kwance haka a rufe tun dare baka leko muba baka kuma shigo da safen nan ba mami ta fada tana karasawa bakin gadon nasa tana zama. Sai daya dan dago daga kwancen cikin yanayin yamutsa fuskan shi yace yau bana jin dadi ne amma yanzun nake son in shiga. Baka jin dadi shine zaka kwanta a daki kai kadai haka ba wanda ya sani kamar karamin yaro mami ta karasa fadan nata da tambayan wai meke damuwan kane. Cikin dauriya yai magana da kyat yana dafe kirjin shi mami ina jin kirjina na ciwo da zazzabi. Wani kallo tayi mashi kafin tace dashi ai saika tashi kaje likita ya dubaka ko ? Mami ba sai naje asibiti ba nasha magani dazun da zan kwanta tace ka karya ne da kasha maganin ? Baida matsala mami yanzun zan fito ya fada yana maida kanshi ga filon da ya dago akai. Ido mami ta dan kura mai kafin tace zaka jawa kanka matsala akan wanan yarinyar har da kwanciya ciwo don kawai na fadama gaskiya. Murmushi kawai ya danyi tare da lumshe idanun shi ba tare daya iya mata magana ba ta mike tana fadin idan ba zaka iya fitowa insa lami ta kawo ma abin karyawan ka nan ka tashi ka karya ko zakaji saukin jikin. Sai lokacin ya iya magana yace ba sai ta kawo min ba mami zan fito da kaina ai ya sake lumshe idon shi a hankali. Mami a cikin dakewa take da karfin hali a lokacin don gaba daya hankalinta ya tashi ga halin data samu dan nata a ciki wanda take tunanen maganan su najiyane yaja masa wanan kwanciyar haka. Hjy na zaune falo tana dakon fitowan hjy sai gata tun kan ta karaso take tambaya kin same shi a ciki ? Yana nan hjy wai ashe baya jin dadin jikin sane yakw kwance daki shi kadai bai fadawa kowa ba. Subbahanallahi me ya sameshi haka har yaron nan yake kwance bamu sani a cikin gidan nan. Ciwo yake son jawa kanshi kawai hjy don nayi masa fada jiya shine yake wanan ciwon don batacin zaijawa kanshi ciwo ya halaka kansa akan abinda baikai ya kawo ba. Hjy bata ba mami amsa ba sai mikewan da tayi tana fadin bari na leka shi inga halinda yake ciki tabar mami na kiran lami daga falon. Dakin shi hjy ta nufa daga kofa ta tsaya tana kwala sallama daga can ya jiyo muryanta ya yunkura da kyar ya taso zuwa falon. Da kyat ya iso yana kokarin zama saman dogon kujeran tare da fadin hjy kin tasone yanzun nake son tashi in shiga mu gaisa dake ai. Kai da baka da lafiya aikai ya kamata azo a duba koda yake uwarka tace kaine kajawa kanka ciwon bansan dalilin ta na fadin hakan ba. Hankalinshi yaji ya kara tashi lokaci guda idon shi suka kada sukai jawur gashi abinda yake ji a zuciyar shi kamar ya fita a lokacin ya aikata saidai baison ya biyowa mami ta wanan hanyan da yake ganin ranta zai mugun baci a karshe. Gashi hundred pacent ya amin a zuciyar shi da zabinshi yasan da farko ba son yarinyar yakeyi har cikin ranshi ba. Illa tausayinta da taimakon kanshi ya zauna lafiya a rayuwan shi don itace kawai fufin asirin shi a rayuwan shi. Zai iya samunta da sauki fiye da wace mami ke shirin aura mai yasan ko wacece indai yaran ire iren kawayen mamine dole idanun yarinyar a bude yake itama. Sai dai kuma daga jiyan da mami ke kara ikirari akan ya janyewa yarinyar nan zeey abinda ya faru tsakanin su yasa yana jin wani irin feeling yana matukar jin yarinyar a ranshi. Fiye da yadda bai taba tsanmanin faruwan haka ba a tsakanin su tunda yake mu,amulan shi da mata a rayuwan shi badai wani abune ke shiga tsakani su ba sai dai hugging da dan kiss a tsakanin su kawai. Hannun shi yakai a kai yana dan shafan kanshi tare da jin wani wutan son yarinyar na kara ruwa akansa. Tankar yadda wutan kara yake kamawa gadan gadan yana saurin yaduwa a duk lokacin daya kama a cikin jeji. Jafari ka sassauta zuciyar ka kabi lamarin nan a sannu kamar yadda na fada ma da farko kada kajawa kanka ciwo idan har iyami bata yarda da bukatan ka a cikin lalama ai tana da magabata ko, wa yanda zaka iya gani bayan ita. Saida ya sanye harshen shi ya lashi labbansa da suka bushe masa yana cike da takaici da kunan ran wanan lamarin da mami ta bijiro masa. Kafin yace hjy mami bata sani ba idan har tace a yanzu ba zata yarda da zabina ba sai dai in fasa auren duk wata yarinya da take fadin zata hadani da ita a kasan nan. Ni namiji ne fa ina da daman da zan zabawa kaina abinda nake son rayuwana dashi don ba wani ne zai zauna da ita ba saini. Ta bangarena ranan dai naje school ne amma babu abindana iya tsinta a cikin abinda akai muna don tune biyu daya tsaya min a rai. Na farko shine mami yadda take min din nan abin ya fara tsoratani sosai duk a kan danta take nuna min wanan kyamar dana kasa gane dalilin ta nayin hakan gareni idan nayi dubaiya ga yadda muke da, da ita. Amma sanadiyar bullowan wanan maganan gaba daya mami ta sauya min ga sabon halin disgani ko agaban waye data dauko yi min yanzu wanda hakan ya fara taba min zuciya duk da ina yarinya. Sai nabiyu abinda ya jafar yai min a jiyan ya tsoratani matuka gaba daya ya dasa min tsoron shi a zuciyana. Haka muka dawo gida ina a cikin damu tun daga ranan na daina fitowa falo idan ina gidan har ma in na fito sai idan zan shiga kitchen dauko abinci ko wurin su mama kande mudan taba hira. Gashi tun ranan ban kara saka yaya a idona ba saidai nasan yana gidan ba tafiya yayi ba don ina ganin security din shi da safe idan zamu tafi makaranta. Ta hakan na gane yana gidan bamu dai haduwane dashi ko kuma mami ta shawo kanshine ya yarda zabinta gareshi. Yanzu ya gane niba ajin sa bace ya wuce ajina ga aure saidai diyan manya irin su can irin wanda mami keson ya aure har hakan ya jawo matsaloli a tsakanin mu. Na fito ina tafiya kamar yadda na saba zakace ko ina tsoron kasa ne yadda nake takona, ga uniform din jikina sun karbeni sosai. Kamar ance in daga kai in kalle saitin dakin ya jafar daga inda nake tsaye jikin mota ina jiran fitowan yaran yaya mamud mu kama hanya. Caraf idona ya hadu da nasa daga inda yake tsaye jikin aindon shi yana sanye da bathrobe a jikin shi ya bude gaban rigar yadda zaka iya hango six pack din shi na kiran maza a waje. Yana rike da cup din farin glass a hannun shi idanun shi a kaina da sauri na juya na bashi baya daga kallon shi da gujewa nashi ganin kuma. Kai ya girgiza cikin dan murmushi yana mai jin dadin yanayin danayi din don shi abin nawa ma dariya yake basa ko yaushe a yadda nake nuna tsoro idan na ganshi. Yasan bayin kaina bane hakan mami ce ta riga da ta dasa min tsoronta a raina akan shi don hakan dole inyi hakan don tserar da mutuncina a furin mami din. Har muka shiga mota yana tsaye a gurin yana dan kurban abinda yake sha a hankali a cikin cup din. Sai da motar mu ta daga na sauke wani irin nauyayyan ajiyan zuciya a fili tare da lumshe idona a hankali ina mai jin wani iri a raina. Haka shima ya jafar din bai daga, daga wurin ba saida yaga motar tamu ta bace ga ganin shi ya sauke wani irin ajiyan zuciya lokaci guda tare da juyawa yabar wurin da sauri. Mami na zaune dakin ta tana shiryawa adaidai lokacin yayi sallama ya shigo dakin direct inda take ya nufa ya danyi hugging din ta. Tare da fadin morning mami kanshi ta shafa tare da fadin dan albarka ka tashi lafiya lafiya kalau mami ya fada ya koma bakin gadon ya dan kidinshida tare da daga kafan shi daya yana duban wayan shi. Friend wai gaba daya ka sauya dabi,un ka yanzu har abincin dare ka daina zama dani muci ka kuma san wanan time din ne kawai nake dashi danake dan kebewa daku. Tunda ba fitowa kake da safe ba kafin in wuce wurin aiki balle in ganka shiru yayi bai bata amsa ba sai ta dauka hankalin shi yaga wayan hannun shine hakan yasa ta juyo tana kallon shi. Saidai ganin sabanin hakan garshi lokacin data juyo din yana kallon wani wurin na daban tare da yanayin tunane a fuskan shi. Friend wai me yake damun kane haka ina magana ka lula wani duniyan tunane me kake tunane hakane wanan kwailar yarinyar zeey ka saka a zuciyar ka ko ? Kan shi ya dago a hankali ya dubi mami tare da fadin babu komai mami me kika gani halan. Kai ta girgiza tare da juyowa gareshi gaba daya tana fadin babu yadda za ayi kace babu komai duk mutum mai hankali da zarar ya dubeka yasan kana cikin yanayi na damuwa. Amma dai tunda ba zaka fada kuma ni nasan zancen yarinyar nan ne har yanzu ka saka a ranka kamar yar wani da wata. Kai yanzu kana ganin kafanka ya kama kasa ban isa kai min abinda nake so kayi a matsayina na mahaifiyar ka balle har kace ba zaka fada min abinda ke tsoce ka ba sai dan dogon wuya kake ajewa kanka. Mami na fada maki bani tare da wata matsala kirjinane kawai har yanzu bana jin dadin sa zancen zeey kuma aini na fita wanan zancen yanzu, don shirin komawama nakeyi tunda an fasa zancen auren kince bakyayi da zabina sai a fasa auren a yanzu sai na laluba wata kuma. Mikewa mami tayi tana fadin kaima kasan hakan ai ba zai yuyu ba ka koma ba tare da aje iyali ba . To mami ki bari in auri zabina don shine rufin asirin daki dani daku ga baki daya ba ko wace mace bane zabin namiji ko wani namiji da kalar macen da yake so a rayuwan shi. Haka kace ke nan ni bansan abinda zuciyar ka keso ba ke nan na zaba maka nawa ra,yin ko to tashi ka ban wuri . Ga mamakin mami sai taga ya mike don barin dakin kamar yadda ta umurceshi ya bari din. Har ya fice daga dakin mami tana binshi da kallon mamaki da tsoron abindaya fada yanzu a gabanta wanda ta kasa gane me hakan da yaron nn ke fadi yake nufi ne ? Ya dan jima tare da hjy a falo suna fira inda yake fada mata zai koma bakin aikin shi bada dadewan nan ba. Hjy ta dago kai tana fadin har tafiyan ya karaso ke nan yaya zancen auren naka don idan ka koma a yanzu wayasan ran dawowan ka wanan kasar jafari ? Hjy zan dawo a daidai lokacin daya dace sai dai wanan sirine tsakanina dake ki kula min da yarinyar nan yadda ya dace zan dan barta ta kara wayau da sanin kanta. Yanzu zan nunawa mami ni yarinyar bata gaba sai daidai da lokacin daya dace in dawo gareku da wanan zancen zan dawo da nuna mata gaskiyata. Ban fahinci maganar kaba jafari tsohuwar ta fada yacs zaki fahinta hjy don koma a bayane zaizo maku hjy. Mikewa tsaye yayi yana kallon agogon hannun shi tare da fadin zai soma tafiya a rude tsohuwar ke fadin don Allah dan son manzon tsira ka saurareni kada ka je ka dan dakata mu kara fuskantar iyami na dan lokaci. Shu,umin murmushi shi kawai ya sakar ma tsohuwar ba tare da ya tsaya ya furta wani abuba akai yai mata Allah bamu wuni lafiya yasa kai ya fita daga gidan. Ashe hjy ta samu mami ta yi mata tas akan ya jafar tare da lurar da ita halinda take son jefa danta a ciki takare da fadin idan kin kashe shi ko kika bari ya tafi yabar kasan nan kan wani dalili naki can baku fuskanci juna ba kanki zaki tarawa bakin ciki. Shi auren gatan da kike fada bashi bane kukaiwa mamud yanzu ki fada min dadin da kukaji a cikin wanan hadin na mamuda din. Ke kanki ba dadin yarinyar nan kike ji ba ina gani sai taga dama take shigowa nan koshi sai da wani dalili mai kwari shi mamudan basai ya fada ba da ganin sa kasan a tauye yake da ita duk dai saboda ku a gidan nan. Iyami da zaki gane abinda nake nufi a nan da sai ince ki kyale yaron nan ya auri zabinsa tunda dai hakan ba haramun bane. In kin hanashi auren wacce kika san halinta ai zai kwaso maki fitsarariya da zata zo ta wargaza maki gidan ki. Kindai ji ikirarin da yaron nan keyi a gaban ki ko yaushe da yarinyar nan itace daidai dashi kinsan abinda hakan ke nufi a zuciyar shi ke baki kwantawa ki auna me hakan da yake fada ko yaushene yake nufi. Maza fa ba ayi masu dole ba kamar mata suke ba su ki barshi da zabin sa abinda yagani da idon sa yace yana so. Ai gara wanan din ma daya zaba kinsanta kinsan ta kinsan halinta ciki da bai kina yi tankwasa ta aduk yadda kike son ta ba kamar wanan ta wurin mamudan ba. Sannan har idan itama yarinyar nan ta kamu da son yaron fa kinga kin zalunce su tunda itama a karkashin ki take. Har in kina gudun tayar da alkawari ne ga iyayyen wacan da kika nema masa ki barsu dashi shida kanshi zai nuna masu halinshi ita din ba zabinsa bane amma ina amfanin ayi abu adawo ana danasani akansa haka. Iyami ki rabu da dan yau idan ya furta baison abu to ki kyaleshi yai wanda yake so matukar ba abinda zai sabawa mahaliccin shi bane abin. Gaba daya jikin mami yayi sanyi lokaci guda hankalinta da natsuwa suka zo mat lokaci guda ta bude baki tace hjy ni kaina kalamin yaron nan yana sakani a duhu ko yaushe idan na zauna nayi tunane mai kalman nan da yake yawan fada min haka yake nufine gareni . To kin gani ABU A CIKIN DUHU SIRINE shi yasan me hakan ke nufi ya kuma barwa kanshi sirin abin a zuciyar shi maza ba kamar mu mata suke ba yaron nan shi yasan me yagani gun yarinyat nan ya dahe mata har baijin kwabon ki a yanzu. Hjy zan ga iyayyen yarinyar mu zanta zancen dasu in Allah ya yarda hjy tace ba sai na shiga zancen ba ke nan yanzu. Hjy basai kin kara magana ba in Allah ya yarda zan zauna da yan uwana muyi duba dakyau ki barmu da kaina zan gyara kurakurena zan shirya komai. Hjy tace koke fa Iyami Allah yayi maki albarka ya daukaka maki zurian ki ya kare ku daga sherin makiya da mahassada. Naji dadi kwarai da kika fahinci mai nake nufi kafin wani abinda ba a so yazo ya faru kan maganan nan yanzu. Duniya yanzu idan zaka biyewa mutanen cikin ta ba zaka taba aikata daidai ba a rayuwan ka sai a baka gurguwan shawara idan ta kwabe adawo ana zunden ka a baya. Sai yarinyar nan ya zama dole yanzu ki gyara mu,amulan ku da ita tunda kin riga da kin bata komai a tsakanin ku don dai yarinyar ma mai hakkurice da sanin yakamata. Ba kowa bane za a nunawa hakan ya iya shanyeshi a zuciyar shi ki gyara tsakanin ku kada yazo ta rike abin a ranta ki nuna mata mu ba butulai bane kuskure aka samu a baya hakan ya faru. Nayi mamaki sanin kankine aurene fa yarin ga yace yana so da yar nan taki don yarinyar ta zama yarki halal malal sanan aure sunnan ma,akin Allah ne. Bai kamata kiyi shishigi da nuna iko a cikin lamarin aure ba hakan nan kizo ki mutu akuma yi wanan auren idan da rabo a tsakanin su azo ana fadan da baki mutu ba ba za,ayi wanan auren ba. Idan ma baki mutum ba ayi ba acikin yardan ki ba kikuma gansu a tare da babu yadda zakiyi da hukuncin ubangijin ki a kansu. Wani hawayen bakin cikine ya zubu a idon mami lokaci guda tace wallahi nima hjy na rasa me yasa bana son wanan auren ko nayi niyar barin shi yayi abinsa. Don zeey har ga Allah abin asone a gida dubaga irin hakkurin yarinyar da sanin yakamatan ta kamar ba karamar yarinya ba da ita. Gata abin tausayi to hjy na rigada nayiwa hjy saude alkawari akan yar ta duba da yadda muka dade da ita muna amintaka yau ace naki hadin da take so a tsakanin mu. Hjy tace ai itama ta haifa tana dasu ba zataki abinda danta zaiso ba har in son gaskiya take maki bazata taba ganin laifin ki kan zancen nan ba. Tunda ba kece maiyin auren ba wanda zaiyi yace yarta batai mashi ba sai dai tayi hakkuri yanzu kan. Tana fadan haka ta mike tana fadin ni zanje inyi alwala inyi nafila lokaci na kure min. Nan tabar mami zaune da dinbin tunane a ranta na yadda zata bullowa wanan al,amarin da yaronta ya bijiro mata dashi a yanzu. Don ko ita dadin tane ta sani nan gaba don samun yarinyar garesu ba karamin alheri ba wurin jafar sai dai kawai ace babu good backgraund gareta ne na iyayyen da suka isa gare ta shine kawai abin duba. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣0️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA BARKA DA WARHAKA SHI KO KINSAN LITTAFIN NAN NA KUDINE DON ALLAH DON KAUNAN ANNABI IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KASADAN KARANTA SHI DON KINSAN BAKI BAN HAKKINA BA UBANGIJI ALLAH YASA TUNANEN KI NA ALHERI YA RINJAYI SHEDANI DAKE TARE DAKE KODA YAUSHE ALLAHUMA AMIN ALLAH 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA 08036959257 ALLAH YA BADA IKON BIYA ALLAHUMA AMIN, , , , , , Tiryan tiryan hjy ke mayar mai da yadda sukayi da mami zaune yake kawai yana sauraren hjy din ba tare da yai magana idon shi na kan wayan hannun shi. Sai idan ta fadi wani abin tambaya ta dago kao tayi magana ya danyi murmushi kawai ta gefen fuska. Bai bari ta gama fadin labarin duka ba ya mike yana fadin hjy zan dan fita akwai ida nake son zuwa kafin rana yayi sosai don gobe kaduna zamu akwai abinda nake sonyi a can. Kace gobe gida kayi ke nan ni likitan bai gama dubana ba ai da nabika mun tafi tare zaman garin nan wuri daya ya fara isata yanzu. Wa zai tafi dake ya fada yana kallon fuskanta tace bandai tashi ba yaro idan na tashi ai dole kaje dani. Hannun rigan shi yake gyarawa tare da fadin wa ni in jera dake ki zama min matsala sai wurin fita jirgi kice min naki san hakan ba. Dakuwa tayi mai da hannu tana fadin wani munafukin ne ya fada ma dama yaran nan biyu akwai bakin gulma ko kuma Indo ce don dai takwarana ba zata taba fadin wanan labarin ba. Kinyi ke nan ya fada yana fita daga dakin tace miskilin banza nagama ma yaki a wurin uwarka, yanzu ka dawo zakai min sheri kuma. Yana fita ya daga wayan shi dake ringing da security din shi yai magana na minti daya bai karasa fitowa ba har sun kawo mai mota bakin kofan shiga gidan. Ya fito kamar mai kare rana fatar jikin shi yayi sumul dashi kamar jikin larabawa don farin shi na daban ne . Bai tsaya jiran komai ba ya fada mota suka rufe a hankalin motar tafita daga tangamemen get din gidan mami din a hankali ya lumshe idanun shi yana tuna kalaman hjy data gama rabtabo mashi yanzu. Wani shu,umin dariya ya sauke yasan waye mami don mahaifiyarshi ce ya kuma san halinta don ita hjy sanin da can baya tana karama taiwa mami din. Lalai da akwai wani plan da mami ke kullawa tayiwa hjy wanan dadin bakin har yar tsohuwar tayi saurin yarda da maganan ta. Gyara zaman shi yayi yana gyara lumshe idanuwan shi tare da fadin mami sai dai kiyi hakkuri dani don tun ranan dana fara dora idona kan yarinyar nan tausayinta ya rikede ya zama soyayya a zuciyar danki. Shi kanshi yasan akwai kyawan mata dasukafi wanan yarinyar da idan yau yace a aura mai aure dasu zai yuyu. Sai dai shikan ubangiji ya dagwara mai tausayin ta da sonta a yanzu don bai taba fadawa tarkon son wata mace ba irin wanan yar abin da mami ke rainawa. Shiya idan mami na korafinta a kaina bai iya furta komai a yanzu don son da yakewa yarinyar baki ba zai iya furta shi ba har abin yakan bashi mamaki. A wani babban shago motar ta tsaya ya dan dade kafin ya fito motae ya shiga shagon biyu daga cikin security din shi na bayan shi duk inda ya bi sai binshi ake da kallo. Sayayya yayi sosai a shagon saga turare sabulun wanka manshafi da sauran kayan gyaran jikin mata ya biya suka fito daga shagon daga nan ya shiga wani shago na sayar da redmed nan ma ya duba ya zabo ya fito. Bai dawo gida ba don ya wuce kallon ball sai bayan sallah isha,i ya shigo gidan ga security din shi har biyu da kaya niki niki a bayan shi suna biye dashi. Daga mami Aisha da hjy duk suna falon sai ya jalal suna zaune a dining suna cin abinci suma. Welcome ya J suke fada yana amsawa a cikin basar ya nufi kujera ya zauna security din suka shiga gaida mami da hjy. Suna tsaye saitin inda yake zaune a bayan kujeran tsaye da ledojin da suka shigo dashi a hannun su. Ya kalli Aisha yana fadin a cikin turanci karbi kayan nan ki shigawa yarinyar nan dasu dakin su. Ba Aisha ba har mami saida ta dago kai a cikin mamaki tana kallon shi, shiko fuska a daure ya kara bata umurni yana fadin ki karbi kayan nan ki kaiwa zainab daki nace. Ta mike simi simi don bata hango sassauci a fuskan shi ba lokacin idan taki tasan kwanan wasan a wurin shi. Meye a cikin mami ta tambaya a hasale ba wani abu bane ya fada yana mayar da kanshi saman kujera tare da fadin john kuna iya tafiya yanzu and make sure by six kun fito don bakwai jirgin mu zai tashi zuwa kaduna. Aisha dawo da kayan nan, nan mugani mami na fada maki ba wani abu bane a ciki perfume ne da kayan body odor da kikace tana wari na saya mata . Ido waje mami ke kallon shi waje don jin abunda ya fada don ita har ta manta da tayi wanan maganan a cikin fada ashe shi yana rike da zancen a ranshi. Wari kuma wake wari a gidan nan hjy ta tambaya a cikin mamaki saida ya mike tsaye bayan ya tabatar da shigan Aisha dakin namu yake fadin. Tare da duban hjy har lokacin fuska a daure yace wai yarinyar nan zainab shine na sayo mata kayan kamshi. Jafar zaka fice min a ido tun kan na feto ka ko sai kayi min rashin kunya a nan na fada bata warin ne ko wani oud take shafawa daba za aji warinta ba. Ok fine mami shine ai na saya mata yanzu don ta dinga kamshi kamar kowa ya dan juyo ya kalli hjy yana fadin ya kike hope ba wani matsala dai ko ? Ba matsala dan duniya hjy ta fada tana dariyan draman shi da mami din don ita abin ma dariya ya bata kuma. Mami kan binshi tayi da kallon mamaki har ya bacewa gani ta ta juyo da kallonta wurin hjyn ta . Iyami na fada maki kibi zancen yaron nan a sannu yanzu ina dadin wanan zancen da yaron nan ya fada koda yarinyar na wurin shi fada zaiyi abinsa namijine bai damu ba. Hjy gaba daya yaron nan ya sauya akan yarnan don wanan ba halin shi bane musaya min magana ta. Amma yanzu kan zeey yake kokarin saba min tun kan aje ko ina inaga ya riketa ta zama tasa ke nan. Don nace zeey din tana da body odor shine ya nuna min shi yasan hanyar gyaranta ko ? Wanda yaki jin bari ai bayaki gani ba dan zamani ne fa kike jayayya dashi iyami tunda baki jin zance ai yanzu sai ku zuba dashi namu ido. A karshe idan an zugaki kin ma dan naki baki ya lalace sai ki dawo ku zauna a gidan ina shike nan dai tunda haka kike so. Daga haka ta juya ta mayar da hankalinta gun tv dake aiki duk daba fahintar abinda ake ciki takeyi ba. Daga hakan kowa yayi shiru a falon ba wanda ya kara magana sai Aisha data dawo tana zuburan baki take fadin gaskiya ya J ya jamin raini mami nice zankaiwa zeey sayayyan daya yo mata daki. Ni wallahi dana sani da ban zauna falon nan ba yanzu ke enough kada ki cikamu da surutun banza a nan dan Allah mami ta fada a hasale. Kafanta ta dauka ta dora saman dan karamin table din dake gaban ta tana karkadawa a hankali kafin ta juyo wurin zeey din tana fadin. Jeki kira min zeey din tazo nan da kayan da kika kai mata dakin mu gani ikon Allah iyami yaushe kika zama haka. Ashe bawa yakan canza rayuwan sa yanzu wani zubar da mutunci zai sa ki karbi kayan toshin yarinyar nan don baki data ido. Daga yau ba zan kara saka maku baki a cikin zancen nan ba na fada tundazun karki dauka wasa nakeyi a zancen nan . Hjy kiyi hakkuri yaran nan ne da abin bacin rai bawai karban kayab zanyi ba ai dubawa kawai zanyi idan babu na assha a cikin sa. Barwa yar nan kayan ta a hannun ta koma meye a ciki ina kinfi karfin shi a yanzu hakan kamar zubar da kimar kine a idon ta ai. Koda Aisha tazo daki ina zaune ina assgment na baje saman gado hakalina ya dauku ga abinda nakeyi. Naji shigowan mutum dakin haka yasa na dago da sauri don jin karan ledan dake motsi a hannun ta don nasan ba hjy bace wanan mai karfine ya shigo. Anty Aisha na fada ina niyar gayar da ita take fadin ke dan raini nine zan kawo maki kaya kallonta nake da mamaki don jin abinda take fada daga kofa ta dangwara min kayan tana fadin you will pay for this. Kiyi hakkuri Anty na fada tare da fadin ba kayana bane don a zatona bata tayi dasu. Ke dan Allah ja can ya J yace a kawo maki wai kazama kawai ta fada tana juyawa don barin dakin. In kalli inda kayan suke aje a kasa in kalli bayan anty Aisha dake fita daga dakin ina mamakin kalaminta a fili. Ni zainab na fada na tare da sake biron dake hannuna na kurawa ledan kayan idanu kamar mai nazari. Da kyar na iya furta na shiga uku ni zainab me wanan bawan Allah yakeso danine a duniyan nan koso yake sai rayuwana ya salwantane ? Shiru nayi cikin dakin na kasa cigaba da assigment din da nakeyi sai tunane da nakeyi barkatai a dakin. Nasan sai tara hjy zata bar falon mikewa nayi na dauki kayan na nufi dakin mami dasu a hannuna bata dakin yasa na aje nafito ba tare dana bude ledan don ganin abinda ke ciki ba. Gaba na faduwa na fito sai muka hade da mami saidana kadu don tsoron mami da nakeji yanzu a raina . Gaida ita nayi ta amsa min da kyat na zata zatayi min magana me na tafi nema a dakin nata sai naga ta wuce ta shiga dakin. Hjy na hango a falo na nufi wurin ta don tsoron zama dakin ma nake ni kadai don ban san abinda mami zata fada idan taga kayan dana kai mata dakin. Yauwa yar albarka kin zo a lokacin daya dace yanzun nake shirin tashi yau sun watse sun barmu ki kama min kofin nan zuwa daki na amsa da to hjy na dauki kofin da sauri muka jera zuwa dakin. Ina tsaye saidata zauna na aje mata kofi a gefenta na nufi bandaki don a tsure nake lokacin ina sauraren kiran mami a lokacin duk cikin tsoro nake don bansan abinda zata fadamin ba kan kayan da bansan dalilin su ba. Na fito na dauke littafina dana bari saman gadon na koma sama kujera na zauna hjy na dan dube dube a cikin aljihu bujen yadi dake jikinta. Don ko yaushe a cikin kidayan kudi take kamar wani na taba maga gashi idan ina kusa nice mai lissafa mata su kullun. Duk da babu abinda take saye da kudin ta a gidan komai takeso saidai mami ta sayo mata ko daya daga cikin yaran mami din. Yauma lissafin muka fara don anyi baki sun bawa hjy kudi da bana nan shi take son mu lissafa da ita. Mamine ta tsaya daga kofa tana kwala min kira ke zeey na amsa da sauri ina fadin na,am mami tare da mikewa lokaci guda. Nasamu tako daki ko duk saurin danayi na amsa kiran don naso kada mu kauce a gaban hjy lokacin. Ina shiga ta zauna a bakin gadon ta kafunta a harde mami gani na fada bayan na shiga dakin da sallamana. Wanan kayan fa da kika kawo min nan tana nuna kayan take tambayana ba tare data dago kai ta kalli inda nake ba. Shiru nayi saidata sake fadin kayan nan fa me sukeyi a nan tafada a cikin dan tsawa. Mami nima yanzu anty Aisha ta shigo dashi dakin mu wai ya J ne ya ce ta kawo nan . Zeey ta fada tana dago kai ni sa,arki ce ita Aisha data kawo maki bata fada maki naki bane dauke min kayan nan a na tun kan ranki yabaci. Da sauri na duka na dauki kayan ina kiciniya da ledojin saboda nauyin ledan su yi yawa sosai bazan iya dauka ba . Hakana ja su zuwa dakin mu na ajesu da kyat ina nishi hjy dake zaune har lokacin tana lissafi ta dago tana kallona tare da fadin. Ina kayan nan suka fito kuma a cikin mamaki take tambayana na aje a gabanta na koma na zauna tare da tin tagumi don fargaban abinda zaije ya dawo gareni kan kayan nan yadda naga mami ta dau zafi a lokacin. Yaushe aka kai kayan nan can ko can dakin Indo takai maki don bakin ciki yaron nan fa ya yo maki toshi dazun a gabab kowa ya bada kayan a kawo maki nan dakin. Hjy don Allah kice ya daina min hakan kada mami tayi min fadan haka sai ta dauko koni ke rokon su abu. Ina roko anan takwara kayan nan fa keya sayowa su don kansa kuma a gaban uwar taku ya bayar a kawo maki ai. Maza tashi ki bude muga abinda ya sayo a cikin ledan mai nacin tsiya shine ai daidai da uwar taku . Kamar ba zan tashi ba ta kara fadi na mike badon nasoba na fara fitar da kayan ledan da man shafa suke su turare da kayan shafe shafen jiki dana wankin kai wasu ban san su ba. Ja,iri hjy ta fada so yake yakai uwar taku kul idan tace katobara ta iya a gaban yara dayan na jawo na fara budewa dogayen rugana ne masu kyau da daukan ido. Sai kamahin sabontaka suke duk wanda na daga ko anty Aisha ban taba gani da irin su ba dukda ko irin su take sakawa. Dayan ledan kuma karami ina dagashi saida nakai zaune don photon waya danagani a jikin kwalin haka ya tabbatar min da cewa wayane a cikin kwalin ko ledan shi ba a cire ba saidai andan yaga gefe da alama a dan budeshine an duba. Komawa nayi na kai zaune tare da kurawa kayan ido ina tunane kala kala a raina karshe dai tasa na tattara kayan zuwa drower kayana naje. Har hjy taga ba anta ban samu bakin magana ba don tsoron da fargaban ganin ran mami yana a bace sai na dauka akan yaya jafar din take cikin yanayin dana sameta din. Washe gari ana public holiday don haka kowa na gida bamu fita zuwa school ba ina idar da sallah na koma na kwanta saman gado don hjy tana zaune a gurin sallah har lokacin. Muryan shine a kofan yana sallama ta amsa mai daga inda take zaune din saiya shigo daga cikin dakin . Kafito ke nan hjy ta fada a daidai lokacin daya karasa shigowa dakin idon shi na akaina yadda nake kwamce nayi tub da ciki saman gadon. Wanan barci takeyi ne ya fada daidai yana zama saman kujeran dakin inda nakan kwana wani lokaci. Yanzu dai ta idar da sallah ta kara kwanci kafin gari ya waye tafi aikinta. Wai hjy aikin nan ba a neman wata ta dinga yinsane a barta haka da aikin nan don Allah. Fadawa uwarku nima na dade ina shawaran hakan a raina duba ga irin sakkon da takeyi na zuwa makaranta tunda safe. Amma hjy yakamata iyanzu ace ta daina hakana kuna, , , , , ina kwana yaya na fada a daidai lokacin dana dan mike zaune saman gadon. Lafiya ya fada tare da kawar da kanshi daga kallona ko ya fahinci fita nake sonyi daga dakin ne oho ? Zauna abinki yanzun fita zanyi ni hjy nazo sallama dama ana jirana a waje ya fada. Dan satan kallon shi nayi yayi wanka fes yana saye cikin suit baka ga farar riganshi ta ciki ta dan fito waje don aninaiyan su a bude yabarshi. Zan tafi hjy sai na dawo ya fada tare da mikewa zuwa inda take zaune ya aje mata kudi a gabanta ta shiga jero mai adduan kariya a gareshi kwando kwando. Har yakai kofa nace da sauri nagode yaya naga sako jiya Allah ya karawa dukiya albarka. Kisa wayan a caji ya fada daga haka yasa kai ya tafi hjy da har lokacin sai albarka take zuka mai tace tashi ki saka wayan caji yadda yace. Hjy mami batace min komai akan kayan ba kuma ni naga kamar ranta a bace yake dani . Yaushe zaki tsaya jiran cewar ta ki saka waya a caji kada kija hasara kuma kudi daine ya riga ya kashesu sai dai tayi hakkuri. KADUNA Gidab ya nufa kai tsaye saida yadda ya samu gidane ransa bai masa dadi ba sai sha biyu yake da meeting din dayazo yi anan kaduna. Yadda ya samu falon kamar ba mutane a gidan musanman ma mata ko ina ga kayanan ajiye sun baza. Part din shi ya nufa ya bude da niyar ya dan huta a ciki saidai yaga kuran dakin da kyankyami kasancewar shi mai tsabta sosai. Fitowa yayi don ya duba mai aiki sukai kicibis da Nazifa ta fito falin sannu da zuwa ya J ta fada cikin nuna kulawa ba taee daya amsa ba yace ke dauko tsintsiya ki share part din nan. Wa ni ya jafar ta fada tana wani turo baki gaba bake ba wancan zaki bace min kiyi abinda nace tunkan ranki ya baci wurin nan. Ta juya tana gunguni zuwa kitchen yana tsaye har ta fito abinka da wanda bai saba aiki ba ji rakeyi kamar ta kurma hannu akai tayi ihu a lokacin. Wajen gidan ya koma ya tsaya harta karasa can ya dawo ya samu wai ta gama kamar bata taba komai ba a dakin dakin na nan yadda yake. Fita yayi da sauri yana kiran sunan ta da dan karfi ta fito ya balla mata harara yace common shara ma ba zaki iya ba. Yayani fa bana shara wanan ma ai nayi kokarin yin sa yanzu kawai ba a sa yan aiki irin su , , , Ji kake fauuu ya wanke mata fuskan ta da mari da sauri ta kurma wani uban ihu daya fito da sauran daga daki. Ta durkushe a wurin tare da dafe kuncinta da dukka hanayen ta biyu ta durkushe a wurin. Saiga salma da Rufaida sun fito daga dakin da sauri suna ganin shi suka rikice sai sannu da zuwa suke mashi. Kai ku fito ku gyara ko ina na gidan nan yanzu kafin indawo ko kuma ku samu naku hukuncin zaku zauna kubar gida haka a kazance kamar babu mutane a gidan. Ya J mai sharan ne bata zo ba wai danta baida lafiya ku ba mata bane aikin me kukeyi a gidan ku ? Ya j ba aikin mu bane shara fa yace oho relly ku din ba mata bane oya ban son in dawo gidan nan in sameshi a haka ya juya fita ya barsu nan tsaye nazifa na dafe da kumatunta tana hawaye. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣1️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAR UWA BARKAN MU DA WARHAKA DA FATAN ALHERI GAREMU BAKI DAYA ALLAHUMA AMIN. LITTAFIN NAN NAN NA KUDINE DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA YAR UWA DON KAUCEWA SHIGA HAKKIN WANI. DON TURA KUDINSA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA 08036959257 UBANGIJI ALLAH YA HORE ABIN SAYA ALLAHUMA AMIN, , , , , , Daga inda nake kwance nake tajin dan kida na tashi a dakin sai dai dayake ba waya gareni ba yasa ban damu da in dago don ganin inda wayan ke kuka don a zatona ko wanine zai shigo dakin wurin hjy. Don yanzu dakin bai rasa masu shigowa lokaci lokaci mussanman jikokin hjyn diyan mami ko wasu baki. Haka yasa ko yaushe nake cikin gyaran dakin don kada a samu dakin yadda bai dace ba. Wayan ne ya kara kira daga inda nake kwance rub da ciki don wanan dabi,a nane idan ina karatu in kwanta hakan duk da ance hakan baida kyau a musulunce. Makan da hjy takai min a baya yasani dagowa a firgice tare da juyowa lokaci guda ina mamakin hakan take fadin sabon shiga wayan taki ce ke kida haka yana damun mu. Kallon hjy nayi tace jeki ki dauka kada ya katse hjy kila ba kira bane wata kila alam ne wa nake dashi da zai kirani ni ? Waya saya maki wayan idan bashi zai kira wanan lokacin ba ta fada a dan shagwabe da ban ma san nayi ba don ance ido wa ka raina yace wanda nake gani kullun idan ba hjyn ba wa zan tsaya yiwa wani shagwaba haka a gidan sai dai idan su mama kande da lami dan dama dama. Jeki mana tun dazin waya na kara baki daga ba ta dan fada a cikin yanayin bani umurni don ba wasa a idon ta ko kadan a lokacin. Dauka nayi sai kuma na tsaya ina kallon wayan don ban san yadda zan danata ba in amsa kiran. Can dai na tuna da yadda anty Aisha ke daukan nata na daga tare da kara wayan a kunne na shiru babu sallama babu hello. Yasa na sauke wayan ina kallon screen din wayan da sai lokacin ma na fara ganin yanayin ta na mayar da sauri na sake karawa a kunne na. Jin har lokacin ba magana yasa na mayar da wayan kasa inda take canji na kara jona ta na juyo zan koma inda nake kwancene wayan ya kara daukan kara. Na kara dauka na danna dauka a cikin siririyar murya nayi sallama badon naso ba sai naji sauke ajiyan zuciyar shi a hankali tare da fadin. Barka da dare kuna lafiya saida na lumshe idona don jin muryan shi tar a kunne na da kuma abinda ya fada. Da kyar na iya budan baki na amsa da lafiya kawai ban kara furta komai ba shima a nasa bangaren shiru yayi bai kara magana ba sai can yake fadin . Wayar tayi maki ke nan ko ya fada don yarasa me zai fada, don jin muryana yasa shi jin kamar numfashin shi zai dauke a lokacin. Dan murmushi nayi wanda bansan sautin shi zai fita waje ba har ya iya jina a cikin wayan. Ashe kina murmushi da alama dai kina son waya a rayuwan ki tunda yau har waya ya sakaki yi min murmushi duk da bangani a fili ba nasan hakan yai maki dadi sosai. Yaya sai anjima na fada don jin abinda yake fadi wanda kunnena ba zai jure daukan sautin muryan shi don yanayin dana soma ji a tare dani lokacin. Ke ina wasa dakene zan kira kice zaki kashe min waya kina jina ya karasa magana dashi. Kayi hakkuri yaya na fada a dan maraice kin kyautawa kanki da kika zamo mai saurin bada hakkuri don ni mutum ne da bai son raini ko a cikin abokaina. Gabana ne ya fadi don jin abindaya fada tare da tambayan kaina yanzu wani raini nayi mai daga fadin sai anjima kawai. Hjy fa tana ina naji yana fada donni har na shiga tunane a raina na manta da waya a hannu na lokacin. Gata kusa dani na fada yace a bata wayan da sauri na mikawa hjy wayan ta karba naji sun fara gaisawa dashi. Ka isa lafiya ya ka samesu nan yace hjy banje gidan kowa ba ina gida kwance tundana dawo. Tace badai kana lafiya ba ko kadai kula da kanka ka dinga cin abinci don nasan halin ka jafari baka son cin abinci akan lokaci. Allah sarki hjy zan kula kinsan ba komai nake ci ba hakana nagode da kulawan ki garemu kema ki kula da kanki ki dinga kashe kudin ki ba sai mami ta saya maki ba . Idan na kashe zaka ban wasune ta fada a cikin zolaya kada ki damu hjy idan kudine baki da matsala su ko yanzu idan kina so zan turo maki. A,a Allah dai ya karawa arziki albarka ta fada hjy wanan adduan muke bukata a wurin ku ko yaushe. Addua kan muna yi ko yaushe ana kanyin tane Allah ya tsare ya kare ya kawo sauki a rayuwa. Ya saki ajiyan zuciya tare da fadin shiyasa muma muke addua Allah ya barmuna ke a tare damu hjy don ki kula damu. Kaida ka kara hakkuri kayiwa uwar ka biyayya a tafi a yadda take so don wuyan sha,ani kega uwar taku rayuwan turai ya bata ku ga baki daya yanzu. Hjy turai basu da wanan halin ni kaina ina mamakin canzawan mami yanzu tun daeowan ta kasan nan komai nata ya canza a yanzu kamar ba mamin mu ba. Ku daiyi hakkuri hjy nasan mami zata sauko da kanta idan ta gane gaskiya don mamud ma complain din da yake min ke nan ya rasa gane kan mami yanzu. Kuci gaba da mata biyayya dukkan ku wataran zata gane gaskiya ta gyara da kanta Allah yace aiwa iyayye biyayya koda basu raye wasu nasu suna nan. A hankali yace Allah ya bamu ikomn yi hjy nagode sukai sallama ya kashe wayan shi don yasan ba zan kara dauka ba. Wayan ta miko min na karba take fadin kinga yanzu ai kwaji sauki ki daina wanan guje gujen da kike masa kamar kinga dodo. Murmushi mai kama da yake na sake kasan fuskana tare da daukan takarduna na hada a jakkan makarantana. Dan hira muka taba kafin barci ya fara daukana itakan sai dare da na falko fitsari na samu tana ibadan ta a zaune. Idan na samu tana hakan watarana nakan yo alwalan inyi raka, a biyu in koma in kwanta idan an kira sallah zata tayar dani nayi sallah asuba zaman da banyi da kakana Asabe a gidan mu shi nakeyi da wanan tsohuwar don yadda ta daukeni take kuma sake min fuskanta tankar itace ta haifi mahaifana a cikin ta. Barci ne ya daukeni ban sani ba bayan na idar da sallah sama sama naji muryan mami a dakin mu suna magana da hjy. Bayan sun gaisane take fadin hjy kinji shirmen da yaron nan yaje yayi a kaduna wai jafar nason mu gama lafiya dashi kuwa hjy ? Me kuma yayi kibi a sannu koma meye don yana da hankali ko me zai aiwatar. Ina hankalin yake nan hjy yanzu aka kirani ake fada min wai yaje ya daki yaran nan har Nazifa da Rufaida sun kwana a gidajen su. Yanzun kanwar daddy su ta kirani tana fada kan abinda yaiwa yar nata assha ita hjy ta fada tun kan mami ta karasa magana. Wanan yar bata da tunane don jafari ya duki yar ta har zata kira ki ta fada maki ina wanta ne yana da ikon hukuntata idan tayi mai ba daidai ba. Hjy meya kawo duka yanzu kamar jafar zai tsaya yana duka mace ina yaran nan yanzu dai sun wuce duka sai tsawatawa. Ki dai yi bincike abinda ya hadasu fada aji haka kawai tunda ba hauka yayi ba, haka kawai ba zai farmasu da duka ba ai. Wani abin dai sukai mai har hakan yakai ga faru a tsakanin su don haka ki binkita karki hau danki da mumunan zato har ki yanke hukuncin da bai dace ba a kanshi. Hjy koma meye ba zaiyi hakkuri dasu wanan kawai wani sallon jan magana ne a guna yanzu kinji ita Binta tana fadin wai akan wanan yarinyar zeey ce ya daki yarta. Wace yar tana nan ina suka ganta wai meyasa mutane basa son a zauna lafiya ne. Kawai su dorawa yar nan bakin jini don kawai suna daukanta mara gata shi rashin gata rashin ubane halan ? Yar nan fa ba shegiya bace don da ubanta don Allah ya nufa zataci daga tsatson su duk wani maganan bantanci sai ya kare akanta yanzu ? Don kawai suna takana da iskanci irin tasu da basu san darajan dan Adam ba ina koke haka kikai ta fama da korafin su a lokacin saida Allah yai maki tsaye a kansu. Hjy shine dalilina kan yaron don nasan ko bai samu matsala da kowa ba zai samu da yan uwan uban shi kan abinda yake son yi a yanzu. Don daga sama,ila har ita binta din duk suna da bukatan ya auri diyan su kinga kuma ba abinda zai yuyu bane gareni. Shiyasa nafi son ya fita can nesa yaje yai auren shi zaifi mun kwanciyan hankali tunda dai ba ganin su zasuyi ba idan yai auren sai dai idan yazo da tashi matar irin haka. Duk ina kwance na lafe ina jin duk abinda ke wakana a tsakanin su zancen sukaci gaba dayi inda yanzu zancen ya koma akan hiran auren mami da mijinta . Mikewa nayi daga inda nake kwance na sauko a hankali tare da kaiwa kasa na gaida mami da kwana ban tsaya dakin ba nafita zuwa dakin mami din na fara gyara mata. Ga kudi nan a watse ko ina saman gadon kamar lissafin su take ta fita daga dakin da wayoyin ta aje saman gadon. Ni dai na hadasu wuri daya na daga filo na saka karshin filon na gyara gado ta hanyar cire zanin gadon na shimfida wani don wanan kwanan shi biyu da shimfidawa ke nan. Har na gama da dakin nata, tana dakin mu da hjy suna hira don haka na nufi kitchen kai tsaye don mu gaisa dasu mama kande da kwana. Ina kitchen din suka hada abincin hjy na dauko na nufo dakin mu dashi inda na samu mami din tafice daga dakin. Ina kika shiga ne tun dazun nake zancen ki a araina wankin tufafina da suka dan hadu nake son a kaiwa mai wankin can ya wanke min. Ina kitchen wurin su mama kande kina aikin ko kindaiji abinda sahibin naki ya fada ki daina aiki a gidan nan gashi uwar taku yanzu nake fada mata abinda yace tace bashi ya dauko mata ke ba ai. Kinsan iyami hutsuwace idan ba ita taso abu ba balle wanan da kamar jira takeyi ya zanta akai. Hjy nidai don Allah ai masa magana ya daina kulani kada mami tazo tana ganin laifina a banza . Yar nan aikin san yadda so yake ke idan kika fara kaunarsa ai duk abinda uwar taku zata fada ba zai taba damun ki ba gidan nan. Hjy ni na fada da mamaki ni ina zan kai dangaye kamar yaya a kauyen mu ai sai suce yawon barikin na fita da gaske. Kai yaro man kaza ke yanzu wazai samu tsalelen saurayi kamar jafari nidai hjy don Allah ki masa magana ya daina kulani kada su anty Rufaida su sakani gaba kuma ina zaune kalau. A kul, akul na sake jin kiyi wanan zancen wata rufaibaida can dagasu har iyayyen nasu suma ba so suke ayi dasu ba. Nasan wanan ba yanzu ba ina kula dasu a gidan nan duk take taken su ina karantasu a idona kece din dai da suka raina Allah ya makalawa son ki a ranshi. Dukda suna ganin ki ba a bakin komai ba a gidan nan ba sai gashi Allah yana shirin daukakaki a cikin su shine suke neman hanyar da zasu bataki ga kowa yanzu. Ni jafarin yayi min daidai daya gargadasu ya kora min yan banzan yaran nan suka bar gidan nan yara babu abinda suka iya sai munufi da iya shege a tsakanin manya. To ba suna son shi ba su yaso su mana tunda sune yan uwan shi masu kudi nikan ya rabu dani hjy. Yar nan kina data ido kuwa jafarin ne bakya so ko Allah zakiwa butulci da baiwan da yai maki na samun shi ta fada ranta a bace. Bakina bude da zumar bata hakkuri don na fahinci jikan nata baya laifi a wurin ta amma sai ta dakatar dani tana cewa. Ke matsoraciya ce ko mai zurfin ciki ke ko irin kishin nan ma bakya nunawa akan mai son ki sai faman gudun shi kike kamar kinga dodo. Bance komai ba donni maganan tsohuwar ya fara wuce sanina don ni a ganina ko anty Aisha banjin tana maganan samari balle har aje ga magana na a gidan meyasa wanan bawan Allah keson ya takurawa rauwana hakane yanzu gashi ya saka tsohuwar nan ta hau zancen ta zauna a kai ba wanda ya isa ya furta wani kalami kan zancen shi. Ganin yadda take magana rai bace bil,hakki yasa muryana rawa nace hjy don Allah kiyi hakkuri ban san ranki zai baci haka ba don na fadi ra,ayina. Tsaki taja tana kawar dakai daga gefen tare da fadin ana baki kina roko idan uwar taku taji kina fadan haka ta samu inda zata fito masa ke nan ai akan cewa ya rabu mata dake tunda bakyason shi. Fita nayi daga dakin tare da kayan wankin ta dana kwasa ban yarda na dawo dakin ba na zauna wurin su kande ko abinci ranan ban samu ciba don dan damuwan dana shiga najin wai akaina wani abu na shirin faruwa a family su kuma yanzu. Ina jin su kande da lami suna hiran su wanda yawanci akan aiki dake masu yawa na yaran mamine wanan yace wanan yakeso a dafa mai wanan kuma yace baya son wanan dole sai sun kara dafawa. Ga Nuriya matar yaya mamud da nata azzalzalan don ita din girkin daban suke mata dole don tace ba zataci na yawa ba da ake dafawa a gidan duk da haduwan shi ga dadi. Ban tsika a zancen su ba kuma din sun san ba zan fadawa kowa wanan zancen ba a gidan. Lamice ta kalloni tana fadin yau kan ke kamar wani abuna damun rayuwan ki gidan nan tunda safe nake ganin ki a haka. Gida nake son komawa bakina ya furta kai tsaye gida yar nan kina nan kina rufawa kanki asiri da iyayyen ki zaki zabi zuwa kauye a yanzu. Ke kuwa idan kinji zomo yaje kasuwa ai ba a banza bane dole saida dalili yar nan ina kula da ita akwai abinda ke cin zuciyar ta na kula matsalan nan ya kwana biyu a tsakanin ta da uwar dakin mu don yanzu dai tau Allah dai ya sauwaka. Da gaske kande ke fadi zainabu lami ta jiyo tana fuskantata don son jin amsan da zan bata. Taci gaba da fadin ina fatan dai ba wani abin kikai mata wanda bai dace ba har hakan ya faru ?. Banjin hakan ne don ni dai nan hjy da kanta ta ban aikin sakawa zainabu ido sai dai ban yarda na taba fada mata komai ba yo mema zan fada tunda bangani ba. Kallon kande nayi da mamaki lami kuma tana fadin akan me haka kande ? Dan duban kofan kitchen din tayi kamar mai gudun wani yaji me take fadi kafin tace akan me kuwa sai mugun hali irin na wasu tunda mu masu aiki an dauke marasa galihu ma. Sun manta su din ba rawa sukaiwa Allah da ya ba basu arzikin ba kai zai iya azurtaka a duk lokacin da yaso hakan. Idan ba hakan ba dame wanan yan matan da hjy take kokarin hada danta dasu sukafi yar nan da Allah zai bata daulan itama sai kaga tafi dadin kallo da ma,ana. Amma dayake shi ubangiji maiyin komai yadda yaso ne sai kaga yayo maikyau a gidan tallaka mumuna a gidan mai arziki kuma kowa a yadda ya tsunci kansa yake tawakkali ga ubagijin sa. Amma da zaran anga tallaka yau yana kokarin tsallakewa talaucin sa yanzune zakaji an fara suka da sara akan sa duk da muma tallakawan muna da namu laifin a wani bangare don wani baya iya boye zalaman sa ga mai kudi. Irin hakan shike kawo kaga masu arzikin suna kyamar tallakan ya shiga jikin su a dama dashi. Saidai ba kowani tallaka ne yake zama butulu ba amma kaman wanan yar ai nata matsalan ma sai nace banga abin ki a cikin sa ba. Waini kande tun dazun kina wanan bayanin nina kasa gane inda zanceki ya dosa tun dazun. Cikin kashe murya ta dan duka tana fadin kinsan dan hjy ya turburewa uwarshi sai yar nan ita kuma uwar tace basu dace ba da wanan. Cikin kashe murya lami tace wa ke nan a cikin su wanan dai dake zaune a turai dayazo shike da wanan maganan. Ita hjyn da kanta yo ai idan ya samu yarnan yayi dace a rayuwan shi wanan son kowa kin wanda ya rasa ai itace daidai da irin su yarinya kin shigo birni a sa, a. Saidai abinne kan da kamar wuya don masu kudin nan sai kansu suka sani sai yar wani da wance iyasu, , , , Ke mekike anan hjy nacan tana neman ki a daki ta aikeki kin dawo nan kin zauna Aisha ta fada a tsiwace. Zeey din nan kin soma canza halin ki don kinga kamar kowa daidai yake dake yanzu ko ? Mikewa nayi ina fadin ba zaunawa nayi ba aiki nake kama masu a nan tunda ban komai a ciki. Kurban lemon dake hannun ta tayi tare da dan watsa min harara take fadin ni dan Allah wuce mu tafi mami ma tana kiran ki a ciki . Da sauri nakarasa dakin wurin hjy na samu mami kamar suna magana na gaidasu lokacin Aisha ta shigo dakin mami ke fadin tana ina tundazun. A kitchen na sameta zaune dasu kande suna hira da sauri na dago ina fadin ba hira mukeyi ba aiki muke tare. Waya sakaki aiki hjy ta tambaya hjy aikin ne harsai an sakata yi nina bata umurni ta dinga zuwa idan bata zuwa school suna aikin a tare. Tafada tare da fadin ke ina kudin dana aje dazun a daki gaba daya suka sako min ido don jin abinda zan fada a lokacin. Kudi nace a cikin mamaki eh kudi dana zube saman gado dazun dana shigo wurin hjy da safe . Da sauri na dago kai ina fadin sunan a dakin mami da zan canza zanin gado na saka maki cikin wardrobe. Jeki ki kwaso min mami ta fada na juya da sauri don in dauko naji hjy na fadin na fada maki ba halin yar nan bane kada ki soma zargin ta da haka. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣2️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM WAHAMATULLAH YAR UWA BARKA DA WARHAKA FATAN ALHERI GAREKU YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI YA TAIMAKI MUSULMI A DUK INDA YAKE AMIN, , , , LITTAFIN DAI NA SAYARWANE DON ALLAHU MU SAHILEWA JUNA DANI DAKE KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON KI SANI NA FADA IN FITAR DA HAKKIN HAKA GAREKI, , , Gaba na faduwa na nufi wurin kayan saidai ganin yadda na gyara komai ba haka na samesu ba yasa faduwan gaban nawa tsananta sosai. Kaf na bincike kayan basa wajen haka ya kara tayar min da hankali muryan mami ne naji tana kwalla min kira dakin hjy yasa na fito ba tare dana gama bincika ba. Ina shiga dakin da sallama a daidai lokacin da nake fadin mami gani ita kuma take fadin fadin ina kudin tare da kallona. Na duba inda na aje ban gansuba mami na fada a dan firgice don a rude nake lokacin dan rashin ganin kudin da banyi ba. Kamar ya baki gani ba dazun nan fa da zan fita na barsu saman gado dama na fitarne akai lami kasuwa ta sayo cefane. Mami basa nan inda na aje asalima kayan ba,a jere suke ba yadda na barsu wani ya taba wurin kayan. Wa kike nufin zai shiga dakin mami ya taba wani abu a gidan nan baya ke saiko mami din dake da dakinta. Ni ai tasan ko kaya zan dauka itace mai miko min ban damu da daukan wani abuba ciki ba. May ta canza haline ta fara dan hali yanzu tunda taga kudin kamar banza a gidan Aisha ta fada a cikin wani irin yanayi tana dukar da kanta kan wayan ta. Wallahi mami ban dauka ba a nan na saka yanzu kuma ban samesu wurin ba an canza masu wuri. Ke zeey kada ki kawo min rainin hankali wani yarona kikaga ya shiga dakina balle ya kai har cikin wardrobe dina bayan ke ? Haba haba yar nan yau kuke da ita a gidan nan meya kawo wanan zance haka babu dadin ji sam wanan zance bai dace ba ai haba dai ku dinga tunane kafin ku furta magana man. Wanan tsohuwar haka kike fa ga magana ta gaskiya zaki daurewa karya gindi ke hjyn nan sai sakawa mutane baki ga zance baki san abinda ke faruwa ba. Ke yar nan nizaki kawowa diban albarka yan zamani dubani da kyau banyi kama da tsofin banza ba da jika zai iya kawowa rainin wayau yan zamani. Ko uwarki kyaleta nayi take min yadda takeso a gidanta nazo kinga ko a karkashinta nake yanzu. Idan bashi ba ita ta sanni sarai tasan binta nake kafin in kai ga juya mata baya ga duk iya shigen da kuke zubawa a gidan nan. Hjy kiyi hakkuri Aisha wani lokaci haka take abindaba wasa ba sai ta mayar dashi abin wasa a wurin ta. Iyami wanan ne zancen wasa kina zaune tana kokarin dorawa yar mutane halin daba nata ba yau yar nan take gidan nan tare daku. Ada can batai maku haka ba sai yanzu ne zaku dora mata halinda ba nataba don kawai a bata mata suna . Shin ko kin mata ne da wanan watarana itama wani gidan zata idan an wa yarki wanan sherin yaya zakiji a zuciyar ki ko ince yaya zamuji a zukatan mu. Yar nan amana take a wurin mu da duk kowa naki don karbota akayi a hannun iyayyen ta Allah ma,aiki yanzu kuma a binta da wanan barnan sunan haka. Kuka nake wiwi mara sauti don hawaye ke tsiyaya a idona ina maijin dacin satan da mami da yarta ke kokarin dora min. Nagodewa Allah nagodewa wanan tsohuwar datayi min tsaye ta hana kowa ci gaba da abinda ake shirin min don dai na fahinci kamar sheri ake kokarin min a gidan kan kudin. Muryan mami ne ya katse min tunanena tana fadin hjy bafa wani abu bane kudin ne kawai akeson sanin ina ta zubasu don a kiramin lami su tafi kasuwan wanan kuma ta tsaya nata shirmen. Jeki ki kara dubawa da kyau ko ina a dakin ko kin manta da inda kika sakane. Na amsa da to da sauri na barsu a dakin na nufi dakin mami ko ina nake dubawa banga kudin ba na rasa yadda zanyi in fadawa mami ban gani ba a dakin ko ina na duba babu kudin a inda na ajesu. Da kuka na dawo dakin daga kofa na dan tsaya ina fadin mami bangani ba na duba a wurin gaba daya kayan basa wurin. Jeki Allah ya sauwaka ta fada a cikin wani daure fuska tare da fadin jeki ki kiramin lami a kitchen a bata wani kudin tunda wacan kan an kwashe ke nan sai dai ba zan kara lamintan hakan ba gaskiya. Allah ya kyauta hjy ta fada tare da fadin nidai nasan ba yar nan ta dauki kudin nan ba tunda ba yau take daku a gidan nan ba komai bai taba faruwa ba irin haka. Idan da yarnan tana dauke dauke da tuni ansan da hakan kadafa a maidani tsofuwar banza don nagane abinda ake kokarin kullawa yar nan kuma ba zan taba yarda haka ya faru ba. So ai da laifine, laifin namu ya kamata mu gani domin shine ya nuna yana sonta ba wai yarinyarce ta nuna tana son shi ba balle mu dauki laifi mu dorawa yar mutane ga banza. Don haka iyami ina shawartan ki ki dauki yar nan ki maida ita hannun iyayyenta tun kan shedan ya zugaki ki aikata abinda ba daidai ba. Amma idan har yar nan tana zaune gidan nan tare daku kuna kokarin dora mata laifin daba nata ba. Hjy nima naso hakan tun farko saidai ina tunanen maganan ki kan yaron nan kada ta koma gaban iyayyenta ya bita can ba tare da sanina ba wani abu yazo ya faru a tsakanin su. Ko tana nan a gaban ki idan Allah ya nufa akwai aure a tsakanin ku sai angi iyami. Kada ki manta a kullun ina tuna maki baya ki daure yadda Allah ya turo yarinyar nan a karkashin ku har danki yaganta ya nuna yana ra,ayin ta. Shin me zai hana ki daina hattaran yar nan ki sanya ido ga danki shida ke faman bibiyar rayuwar mutane haka. Ita metayi za aga laifinta waya take masa ko binshi takeyi, ko kulashi take tana bibiyan shi inda duk ya saka kafa ? Daki iyami shike wa yarinyar nan duk wanan abinda na lissafo maki a gidan nan kullun yar nan a tashin hankali take gidan nan . Don haka ina gargadin ki karo na karshe da ki takawa danki burki ya rabu da yar mutane tunda dai baki aminta da wanan abin ba. Don iyayyen yarinyar nan suna can suna fadin kina nan kin rike amanan yarsu da hannu bibiyu basu san ba haka ba yarsu na nan cikin ukubar ki don kawai danki yace yana ra,ayin ta. Hjy kin san halin dan yau shi jafar na rasa gane kansa kan wanan abinda yanace sai zeey ni fa bawai niki zeey din nan bane don ina kyamarta ko wani abu. A, a ba hakana bane zabin nasane ni sam bai kwanta mun raiba don idan har ilimi ko kyau ko wayewa ko arziki yaron nan nasan duk zai iya samo macen data tara wanan abin gaba daya da kansa. Amma wai hjy sai ace yau yaron nan ya kafe shi sai zeey a cikin kasan nan abinnne da ban haushi da ban mamaki don yi iya tunane na rasa gane dalilin shi na wanan kafiyan tsiyar ta kare tare da jan tsuki mai nuna takaici. Koda ta dago kai sai duk ta tsargu da irin kallon da hjy kemata don haka ta dukar da kanta. Mikewa tayi don barin dakin iyami hjy ta kira ta fuska a daure cikin murya mai kaushi mami ta amsa da na,am hjy cikin girmamawa. Tace wai me yake damun ki ne iyami zaman turai fa ba hauka bane mami tayi shiru tana sauraren yar uwan nata. Hjy ta sake daga murya cikin bacin rai tana fadin kul naji wanan maganan batar kudin nan ya karde gidan nan har yawuce iyamu nan rayuka zasu baci fiye da tsamani. Don ina da tabbacin yarinyar nan bata taba maki komai naki a gidan nan don da tana tabawa da tuni an gama gane ta. A, a hjy aini na gama maganan don ya, , , , sallaman lamine a kofan yasa su yin shiru gabaki dayan su tace lami muje falo in baki sakon a can. Na dade a inda nake ina hawaye saida naga mami ta koma daki sun gama da lami naja kafata da yai min nauyi zuwa dakin namu. Ina shiga tsohuwar ke fadin kina ina tun dazun acikin yanayin damuwa na iya budan bakina da kyar ina fadin waje na zauna. Kinga sake ranki idan kin so nasan bazaki taba wanan halin banzan daba a sanki dashi ba tun farko. Hawaye masu dumi naji sun fara saukomin a idanu hjy ta nuna min matukar tausayawan ta gareni tana ta bani hakkuri. Hakan daya farune yasa ranan gaba daya na wuni sukuku dani a gidan ban ko leka falo ba ina kwance a daki zazzabi yana neman rufeni sosai. Panadol hjy taban nasha sai barci koda mami tasa murya ta kirani sai hjyn ce ta amsa tana fadin banjin dadin jikina na kwanta. Kamar mami zatayi magana sai kuma tayi shiru don tasan idan tayima yanzu hjy zata kareni gareta ne. Karfe takwas ya kira wayan ina barci ba wanda ya daga wayan har saida y kara kiran hjy ta dauka zuwa falo don wani ya karba min . Aisha ce da hjy zaune saman doguwar kujera suna zaune sama a guri daya ta mika mata wayan tana fadi karba min wanan wayan don Allah yar nan tasha magani ta kara kwanci. Wayar waye wanan ta fada tana karban wayan a hannun hjy din mami ta dan juyo ta kalli wayan tare da kawar da kanta gefe. Receive din wayan tasa tare da kara wayan a kunnen ta sweety rowan daukan wayan ma kike min kuma tun dazun ina kira ba a daga ba . Ehhy, , , ya J to ba ita bace yace Aisha yah kuna lafiya lafiya ya mami na kira bata daga ba gata nan tana kokarin karawa mami wayan a kunnen ta. Don't dear touch me with dis dirty phone mami ta fada a dan hasale Aisha sorry mami a dan shagwabe. Ta mayar da wayan a kunnen ta yace bar mami nasan akan yaran nan marasa tarbiya take fushi dani haka. Where is my baby girl ya fada cikin katse Aisha din tace who ya J ? Yace the owner of the phone wai wanan stupid girl din zeey tana daki tana fushin banza after she steel mami money . What, ya fada dan karfi kamar a fili yake kusa dasu ba a waya ba yace it can't. Wani irin wasane wanan da sata kuma satan kuma na kudi hjy dake gefe tana fadin kai amma keko an daiyi yarinyar kawai a gurin nan. Ban wayan mara mutunci ina saidana gargade uwarki kar zancen nan ya fita har yakai kunnen yaron nan. Hjy why are you always abusing me bata dauki kudin nan bane ko me kina wani kareta can mami dake daga gefenta take wani tunane yazo mata lokaci guda. Take fadin Aisha meyasa kika fara yawan surutu ne yanzu sai kuma ta juya harshe a cikin turanci tana fadin kinsan hjy akwai tsufa a tare da ita ki daina biye mata kuna haka mana bana jin dadi haka nima lalaba abina nake ta karasa fadi ki bata hakkuri please. Hjy yi hakkuri bansan kin fadi haka ba ai ta fada a cikin fushi hjy da ranta ya gama baci take fadin yanzu ai kanku ake ji yar nan . Duk abinda ake waya a kunne take har lokacin a hannun hjy data fisge gun Aisha yana sauraren duk abinda ke faruwa lokacin. Idanun shi ya runtse a cikin takaici da bacin rai why mami zata tsani yar mutane haka har su dora mata mugun tabo mai zafi hakan nan. Ga kalman da baffan shi ya fada dazun cewa don zeey ya kama masu yara yai masu wullakanci don kawai yana takama shi mai arzikine ko yafi kowane yake gani. Ya dade a zaune inda yake duk da dare ya soma sai yaji sam ba zai iya kwana bai fadawa wani daga cikin mutanen nan wanda baida wani aboki ko shakiki da sukafi mai yanuwan shi na jini. Baida aboki ko wani amini a kasan daya wuce mai yan uwan haihuwan shi kasancewan shi wanda bai tashi a kasan shi na ainihi ba Nageria. Haka yasa komai da zaiyi anan ya mamud ne mutum na farko da yake nema ga shawaran shi kamar yadda shima ya mamud din bai wasa da lamarin kanin sa don yana masa biyayya yadda ya dace ga kyautatawa ko yaushe a tsakanin su. Sai kuma yan kannen shi biyu jamal da jalal sumafi dinkewa da jamal don halin su da yazo kusan daya sosai. Bayan su akwai Bukar dan kanin mahaifinsu wanda kusan akwai dan shakuwa sosai shima don zai iya cewa shine mutum na farko ds ya yarda dashi bayan yan uwan nasa. Don tun suna yara bukar din yake nuna ra,ayin shi akansu har wanan lokacin da suka kai hakan bai daina kula dan uwan nasa ba duk da yasan shi din mutum ne da baida saurin sabo lokaci daya. Ya mamud dake shirin kwanciya tare da matarshi Nuriya yajo kiran dan uwan nasa ya shigo mai don yasa ba halin shi bane kira a cikin dare. Furta suna shi da yayi ne yasa Nuriya dake gefen shi dan dagowa da sauri tana kallon shi da mamaki don ita a nata rayuwan ta tsani duk wani dan uwa mijin nata. Tundai shi da take ganin yafi mijinta da komai a rayuwa kamar mijin nata, yana son mayar da kanshi a karkashin shi yanzu wanda ita kuma irun matan nan ne da basu son hakan. Jafar ya akayine ya mamud ya fada lokacin daya dauki kiran na dan uwannasa normal ya fada saidai ina so zuwa safe ka bincika min meke faruwa a gidan nan don Aisha was telling that that girl ta saci kudin mami wanda nasan sheri ne wanan suke kokarin mata. What sata kuma ya mamud ya fada da dan karfi wanda hakan yasa Nuriya dago kai ta dan kalleshi cikin mamaki don jin abinda ya fada. No nima nasan da hakan wanan yarinyar ba zata taba haka ba jafar saidai idan wani sheri kuma ake kokari kulla mata yanzu which is bad . Yanzu dare yayi sun rufe muma nan muna shirin kwanciyane da safe zan binciki hjy in fara jin abindaya faru. Ya samu ya lalaba dan uwan nasa suka kashe wayan Nuriya take fadin wanan yarinyar ce tayi sata kowa ? Ba sata ba kan yau take gidan nan tare dasu wani dai abinne kila yake faruwa a tsakanin su har haka ya faru. Dama nasan haka zaka fada don har kai ina zargi akan wanan yarinyar da farko don kawai dan uwanka ya rigaka furta mata sone kaima nasan da hakan zakayi. Da mamaki ya dago yana kallon ta tace eh na sani don yarinyar macijiyace babu namijin da zai ganta farat daya baiji yana sonta ba sai dai bakin tabo ya yanke mata kadari ai. Don warin talauci da yake binta ita din kaskantatace a idon kowa don bakin talaucin iyayyenta har kasa riketa sukayi suka turota aikatau a birni. What noses talking kike fada haka me yarinyar nan tayi maki haka wai kika tsaneta kema ina yanzu kika gama fadar dan uwana ke sonta da bakin ki . Bazan taba lamunta hakan ba yarinyar nan abin tausayine bata da matsala da kowa a gidan nan ki duba yadda take kula yaran nan tankar ciki daya suka fito dasu duk da tasan ke baki son hakan da takeyi masu din. Bai bata wani kafa da zata fadi wani abuba akai dole tayi shiru ba don taso ba ta kyale zancen a ranta. Washegari na tashi da zazzabi mai karfi wanda har ya tayar da hankalin hjy a dakin ta nufi gurin mami tana fadin yar nan fa iyami zancen nan har zazzabi ya saukar mata jiya bamuyi barci da dadi ba. Budan bakin mami sai cewa tayi wanan kuma ai matsalantane tunda nida taiwa laifin ban dauki wani mataki ba a kai balle ta zauna tanawa mutane ciwon banza a gida. Anya ! Iyami kina da tausayi yanzu kuwa hjy abinne da ban haushi tun jiya nake ganin take taken yarinyar nan ita a dole gata mai zuciya ko. Mikewa mami tayi ta ballo magani tana fadin ta sha wanan zai sauka idan na fito zan shigo in dubata. Hjy dai ta karbo maganin cikin sanyin jiki dajin kuna a ranta yadda gaba daya yar nata ta sauya akidarta ga baki daya har yakai tsohuwar tana zargi a ranta kodai wani abu ya shiga kan mami din ne. Nasha magani cikin ikon Allah naji daman jikin nawa gashi ina son zuwa inyi aikina a daki mami kuma ina jin tsoron shiga dakin yanzu. Babu yadda na iya haka yasa na sauko daga kan gadon a hankali na dan zauna a bakin gado hjy data fitowa ban daki ta dauro alwala ta ganni a zaune take fadin. Alhamdullahi sauki ya samu ke nan nace eh hjy ya fada min ina kokari tashi tsaye take fadin ina kuma zaki tafi yanzu. Zan tafi in gyarawa mami dakine na bata amsa koma ki kwanta babu inda zaki yanzu kina jin jikin nan yarta ta gyara mata idan ta matsu. Ban iya furta komai ba dole na koma na kwanta don bazan iya mussawa tsohuwar ba don nasan wanan tsakanin sune da mami kuma don nasan baida wuya hakan ya zama wani matsala kuma. Kara rufa nayi har barci ya soma daukata naji hjy na fadin in tashi in kara karyawa kafin barci ya daukeki. Zan tashi na fada ina gyara kwanciyana ya mamud yayi sallama a dakin ta amsa mashi suka gaisa ya samu wuri ya zauna. Ina daga kwance ina jin hiran su a cikin ba, a kafin yace wanan da take rufe haka meya sameta ne kuma ? Zazzabi ke damunta tunjiya gata nan a kwance yace subbahanallahi shine ba a kaita asibiti ba take kwance a gida haka. Uwarku ta bata magani shine ta dan samu saukin nan Allah ya kara sauki ya fada kafin yace jiya da dare jafar ya kirani yake fada min wani zance mara dadin ji wai Aisha ta fada mai yarinyar nan ta satarwa mami kudi yaya zancen yakene hajiya ? Dama nasan za a rina saidana gargadi uwarku kan zancen nan amma ta bari zancen nan yakai kunnen yaron nan. Nawane kudin yaya jafar ya tambaya zaka biya mata ne mami ke fada daga kofan No mami ba wai zan biya bane kawai dai tambaya nakeyi don in sani. Ka koma ka fadawa wanda ya aikoka cewa dubu dari ukune ina jiran inji alernt ta fada a cikin gatse ta juya inda nake kwance ina hawaye tana fadin ke zeey jikin bai saki bane ki gyaro min daki ni fita zanyi. Nice nan na hanata zuwa don kowa yasan da ciwo a dakin shi ai don haka sai idan taji sauki. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 ZAINAB IDRIS MAKAWA 3️⃣3️⃣ BARKA DA WARHAKA YAR UWA UBANGIJI YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN. Tana tafe a fusace don ranta daya riga ya baci da yaranta a dakin hjy data shiga sallama da ita ta samu ya mamud suna zancen da hjynta ta ballashi ta fito da fushi ranta a bace cike da tunane. Tun kan ta iso bakin motan security din ta suka mike tsaye tare da bude motar suna jiran isowan ta wurin. Tsayawa tayi gaisawa da masu gadi da wanki da mai kulla da komai dake gudana a gidan massege ne yashigo wayan ta tayi niyar shiga mota ta diba sai kuma ta dakata a yadda take tsaye. Kafatan daya na a motan yayin da dayan kafan nata yake waje ta dafa motan ta bude sakon da mamakin ko sakon meye ya shigo mata a wanan lokaci. What ta fada da dan karfi, bayan ta karanta sakon dake a fuskan wayan nata a fusace ta juya zuwa cikin gidan tana shiga a kofa suka hadu da ya mamud. Gaba daya yanayin fuskanta duk ya sauya ranta ya gama baci tanajin zuciyan ta bakikirin a lokacin. Wani sakon ne ya sake shigowa a lokacin a hasale take duba sakon take idon ta ya kara kankancewa ga baki daya. Mamud da suka hadu a lokacin ganin yanayinta mami lafiya ya ya fada a dan razane ? Wani kallo tayi mai kafinta ce biyoni muje ciki kawai ta fada tana gaba yana biye da ita a baya. Dakin namu suka shiga wurin hjy da sallama cikin wani irin yanayi hjy dake zaune take fadin lafiya dai ko iyami ? Hjy yaron nan me yake nufine, me yake tunanen ya taka da har zai rainani ko ince su rainani. Wai me ke faruwane haka iyami ya mamud daya karasa shigowa yake fadin . Wai mami wani abune kuma akayi yanzu rufa min baki ta fada a cikin tsawa wallahi ka zama babban banza a gurin kannen ka mamud. Wani kallon mamaki ya jefowa uwar don baisan dalilin wanan fada ba a sanyayye ya furta a cikin mamaki mami ni kuma me nayi yanzu kuma ? Hjy wai ki duba yaron nan dan baida wayau kullun shi dan maganan nan danayi yanzun nan yaron nan ya kwashe ya fadawa dan uwansa. Wai sai gashi jafar ya turo min kudi masu yawa haka har yana fada min ga kudin aikina nan tun lokacin dana dauko zainab a gidan ya biya. Shike nan ta faru ta kare dan nan ya fashi yarinyar nan a gidan nan yanzun kuma sai ki samo wata. Hjy me kike fada haka kuma sanda na dauko yarinyar nan nayi shawara da shine ko yasan su waye iyayyen ta? Wallahi wallahi mami ga hjy nan idan nayi magana da Jafar a yanzu kan na fita dakin nan wurin ta ya mamud ya fada rai bace hankali a tashe. Hjy tayi wani shu,umin murmushi a fuskanta kafin takai zaune cikin tagumi tana karkada kafan ta a cikin mamaki. Hannu takai ta cire glass din dake sanye a idon ta na fadin ni jafar zai nunawa yanzu wuyan shi ya isa yanka. Har zai turo min miliyoyin kudi waishi a dole ya fanshi zeey a hannu na to dashi da kudin nasa duk sun, , , , , Kai kai kai iyami karki soma furta wani zance mara dadi ga danki dan yau ne fa ke kuma uwar zamani kinga kuna kamanceceniya a wurin hali. Ba yadda banyi dake ba a gidan nan tun kan zancen nan ya kainan na baki shawara da ki zuba masu ido ki kyalesu suyi soyayyan su. Wasan gobe banda Allah iyami Allah kadai yasan meya tsara ga hakan kince ba hakan ba kin tsaya kina jayayya da hukuncin ubangiji. Iyami ina ji maki tsoron irin abinda zaije ya dawo baya a kan wanan jayayyan da kikeyi a yanzu. Yaron nan idan dai ba alhakinshi zaki dauka ba a banza wallahi baiyi waya da dan uwansa ba a dakin nan yanzun nan ya fita. Hjy dan Allah bari lokacin da zai aikata hakan kina ina zai iya tura mai sako. Mami baki yarda da rantsuwana ba kenan ya fada a dan mairaice yana maijin wani iri a ransa ba dadi duk yana jin mami ta muzantashi a lokacin. Ya dubi mami fuska a daure yana fadin ki kira jafar din yanzu aji wanda ya fada mai don ni wanan abin gaba daya mami kin jefani a cikin zargi . Idan bakai bane waye ko yarinyar nan ne zeey gata kuma a kwance tun dazun sai dai idan daga kwancen ta kulla wanan sherin ba abin mamaki bane kuma. Haba mami ji wanan don Allah bai dace ba meye laifin yarinyar nan a yanzu kuma don Allah ? Kai ke na ka fadamai saka fito fili kafada sukaji muryan Jafar na fadin hi bro ya akayi ne ka fito ke nan naji duk abinda mami ke fadi a waya dazun so na tura mata da kudin sai tai set din yarinyar free by now. A samo wata daga yau ta dinga wanan aiki ita kuma tayi facing din karatun ta final. Eehhee mara kunya beran tankwa nayi shawara da kaine da zan karbo ta yaji muryan mami tana fada a cikin tsawa. No mami bakiyi ba saidai tunda abin har yakai wanan irin zargin yana shiga tsakanin ku let her set free by now tayi karatunta kawai. Mami yanzun kin daina zargina a wanan zancen me zaisa na fadawa jafar wanan magana tunda nasan a cikin fushi kika fade shi. Ni kuma ba zan so inga wani abu na tashi hankali haka ya faruwa a tsakanin kuba ko yaushe Jafar fa dankine mami. Yau yace ga abinda yake so a rayuwan shi mami ya kamata ki sasauta zuciyan ki don in kin kula jafar yayi nisa a wanan zan, , , , Kaga dai yanzu na gane yadda zancen yake don haka katafi kawai kada ka makara a wurin aikin ka ta fada kuma a dan hasale. Toh mami na gode ni zan tafi ya fada yana mikewa daga bakin gadon da ya zauna da farko a gigice. Yama manta a kusa dani ya kai zaune a lokavin don haka bai kara waigowa ba ya fice daga dakin. Idona biyu duk zancen da sukeyi yana a kunne na ina sauraren su ban yarda na motsa ko kadan ba don kar mami ta gane a falke nake duk da bana tantama da tasan a falke din nake a lokacin. Mami naji ta mike tsaye tana fadin ni zan tafi hjy sai dai idan na dawo shi kuma ai zai dawo gidan nan zamu hadu dashine ai ni zai nunawa kudi har yaushe yai kudin nasa shi . Ko yau din nan yayi dai ya wuce raini a garesa da kayan sa hjy ta bata amsa murmushin karfin hali mami ta sauke a fuskan nata ta fice daga dakin. Nasan idon ki biyu yar nan bayan wuya sai dadi insha Allahu wata rana idan an daure sai labari. Dagowa nayi ido shabe shabe da hawayen wahala ga ciwo ga tashin hankali a lokaci daya ya dameni. Don ranan gaba daya wanan zancen ya hanani shakat a rayuwana don ko makarantar ban samu zuwa ba a ranan ke nan. Kamar yadda hjy ta fada na mike tsaye da kyat na nufi bandaki ruwan zafin dana samu a heater na kunna ya dan taru na wasa a jikina. Na fito na shirya a cikin wani blue din dongon rigan English wear mai adon stonen fari a gaban shi. Fuskana ya koma fayau a dan lokaci guda bana jin karfin jikina ko kadan zama nagi gaban abincin karyawan dake gaban hjy na zuba ido . Kici abincin mana ta fada a daidai lokacin na dago fuskana dake zubo hawayen dana kasa tare su a lokacin. A bazata naji muryan hjy na fadin ki daina kuka nima wanan abin ya fara firgitani a gidan nan ki shiya kayan ki kaf zuwa gobe ki koma gaban iyayyen ki kowa ya huta. Kada azo matsalan yazo yafi wanan abu ya taru ya rikice a lokaci guda ta yadda ba za a iya gyaran sa ba har idan kina da rana a gareta zata gani nan gaba. Shi kuma ya tafi ya nemi wace uwarshi ke son ya aura din mu gani yanzu kici abinci ba a ciwo da rashin ci ko kadan ne. Hakana na daure ba don ina so ba na tsakuri a bincin zuciyana yana cike da damuwa kala kala don a gaskiya naso duk wani cin fuskan su mami gareni in daure in karbi kwalin karatuna. In yaso daga baya in nuna ni gida nake bukatan komawa gaban iyayyena yafi mun kwanciyan hankali. Sai dai a yanzu kan banda sauran zabi fiye da barin gidan mami din gara in hakkura da karatun nan tunda abin har yakai ga dafa min sata abinda ban taba yi ba a rayuwana. Gobe kafarki kafata a garin nan ba zan haifi da da cikina in zauna dashi ba tare da yaji magana ta ba duk ko abinda yazama. Nabi iyami a sannu ne inga iya gudun ta gareni saida har yanzu shedan yayi shimfida a zuciyar ta ita bata bi magana ta ba ta yaya yayan ta take son subi nata don wani manufa nata can na daban. Idan anyi magana ta farawa mutane kame kame akan zancen ta mata ita ba haka muka dorata ba ina mahaifin yaran nan da halin shi ta aure shi lokacin shima ba matsiyaci ta sameshi ba ba a cin arziki taci ita a rayuwanta. Hjy ce ke fadan wanan maganan a cikin bacin rai ban yarda na tsuka mata ba sai faman tunanen da nake a cikin raina a lokacin. Mikewa tayi don yin sallah walha haka ya ban daman gyara kayana kamar yadda ta umurce ni inyi har ta idan a daidai lokacin dana gama komai duk da yar jakar kayan da aka ban bai isheni hada yan tsumakarana ba don yanzu Alhamdullahi ina da yan waddatatun kayan da Aisha dashi jafar din suka waddatar dani dasu. Falo ta tursasa min da mu fito ko jikin nawa zai kara ake min a kwance nake na dunkule saman kujera a daidai lokacin da mukaji takon tafiyan mutum yana shigowa falon mami din. Ban dago kaina don ganin kowaye ba a lokacin ina kwance a yadda nake. Muryanta ne ya sheda min da Nuriya ce matar ya mamud tana gaida hjy dake zaune saman kujera ban dago don gaishe ta ba don kowa na gidan ina kallon shi a makiyina. Idan ka debe mazan gidan gaba dayan su da suke nuna min iya kulawan su idan sun shigo. Tsiyata da dan kauye gadara ke me kika taka da bazaki gaida mutane ba dadin abin dai dan halin bera ke ga mutum bai gani ya kauda idon sa saiya dauka. To ai sai ya gani yake dauka ko wani ko ai ko bai gani ba dauka yakeyi don abin yanzu ba sai dan kauye ba don har wanda baka zata ba sai kaji ya yaudari mutane mutanen ma mijin shi na sunna don kawai ya tara ya kaiwa tsofin sa gida. Hjy kina nufin dani kike wanan zancen au kema da wani ke zancen ke nan ke kalleni da kyau banyi maki kama da tsofin banza ba da zaki kawo wa diban albarka ba. Kin taba aje abu a gidan nan ta daukar maki ko wani naki ko dan gidan abinsa ya taba bata toyo dama shi ya kawo ki shiyan nan takalan magana ko me ? Girman mahaukaci karamin mai wayau sai ya fishi ke abinda kikeyi a gidan nan ai ko kare baya ja . Mayafi kayan dake jikin ta ta cire ta mayar a kafadan ta taja wani uban tsuki tare da fadin hjy tsohuwa ba mamaki dai kema an gama dake gun malam na kauye yanzu. Idan bashi ba yanzu dai magana ta nake a wurin nan ba tare da ambatar sunan kowa ba shine har kike kokarin bata min suna haka ? Bari shi mamud di ya dawo da uwarsa Inji wanda ya fada maki haka a cikin su don ba zan taba lamuntan wanan zancen ya tafi a banza ba gidan nan. Allah dai ya dawo dasu din lafiya hjy tace tana nuna bajin tsoro a cikin zancen ta ko kadan tafito mata hjy zainabu Abun tana asali. Wanan abin ya kara saukar min da hawayen bakin ciki masu dumi da kunan zuciya a lokaci guda sai me kuma ? Ba hjy sai ta juyo gareni a zafafe ta hauni da fada a cikin takaici tana fadin ke yar da wanan bakin kukan naki dayaki ci yaki cinyewa gareki. Wa yan nan ba mutuncine dasu ba zai ruwan jikin ki ya kare a banza basu san kina yi ba maza ki gyagije ki shiga tsabganki hankali kwance kamar Allah ya aiko ki. Shi ai sheri ga dan wani takine babba ga wanda yayi shi ni dai nasan harga Allah ba shedun zurba baki daukan masu kwandala a gidan nan ba in har sun yayada wanan zancen haka suyiwa kansu sheri don min sai ya tambaye su. Hjy nikan na yafe masu kada Allah ya jarabi kowa a cikin su da wanan abinda nake ji a yanzu don akwai zafi da ciwo a zuciya. Kaji ya mai hankali nima bawai ina nufin hakan ya samesu bane ai ina dai fadin yadda abin yake ne don idan sheri ko hairan ka kuddurata wa dan uwan ka sai kwantankwancin hakan ya sameka kaima. Kiran sallah azahar ya tayar damu a gurin sallah muka idar a daidai lokacin da lami ta shigo dauke da kayan abincin hjy dakin na gaida ita da aiki. Take fadin yar hjy ance yau bakiji dadin jikin naki ba Allah ya karo sauki na amsa da amin kawai don yanayina babu dadi cikin sa ko kadan a lokacin. Fitar lami dakin yayi daidai da shigowan shi da sallama a dakin kamar daga sama muka ganshi ya fado dakin a wanan lokacin. Jafari ka dawone ashe yau zaka dawo garin hjy dake zaune saman sallaya tana jan tasbaha ta fada a cikin fara, a da kulawa. Eh mun dawo hjy mun sameku lafiya ya gida ya tsufa da jinya ya fada fuskan shi a kaina na dukar da kaina gabana na faduwa tunda yayi sallama dakin kamar an aiko min da mutuwa nakeji. Ya jikin naki ya fada a lokacin daya karaso yana zama a kujera kusa da inda nake zaune daga ni sai ni don na nade hijjabin danayi sallah. Dagani sai dogon rigan dake jikina a lokacin sai duk na tsargu da kaina don ban so ya sameni hakan ba a daki. Sannu da dawowa ya na fada can ciki ciki ya kara fadin ya jikin kunje asibitin hjy ya fada yana kallon hjy din don son jin abinda zata fada. Asibiti ai sai yan gata ita ina taga gatan da iyami zata kaita asibiti yanzu tunda kajawa yar bakin jini ga kowa a gidan nan wai ace wanan zancen yakai har ga kunnen matar mamuda a gidan nan. Zata zo ta nemi karawa mutane zafi akai ina fama da uwarku sai gata dazun gabanin azahar din nan wai tazo yiwa yar fade tayiwa uwarku sata a gabana don yarinyar nan bata data ido a gabana fa jafari don iyami ta mayar da yarinyar nan sabban gida yanzu. Murmushin takaici kawai ya sake a fuskan shi tare da mikewa tsaye lokaci guda yana fadin zan shiga ciki hjy in watsa ruwa. Naso hjy ta barshi ys fice a lokacin amma sai gashi tana ta janshi da fira daga tsayen da yake yana amsa mata da eh ko a, a da kuma Allah sarki. Har ya samu ya fita bansan lokacin dana sauke wani irin gwarou nufashi da har ya fito fili ba a lokacin. Ki daina tsoron shi kwana nawa ne kun zama daya yar nan ki duba saboda ke ya bar abinda yakeyi ya dawo garin nan yanzu bana ko tantama donke ya dawo a wanan lokaci. Hjy don ni kuma na fada a cikin yar murya da mutum zai dauka a shagwabe nake magana na tace. Don ke mana yar nan ya kamata ki fara nuna mashi yadda ake nuna mai yadda yake nuna maki kulawa haka nan. Munci abincin na kwashe kaya don mayarwa kitchen din a can su kande suka tsareni da tambayan meya hada hjy tsohuwa da matar mamud dazun ? Ke fadin ina barci ban san meya hadasu ba mama bata da kunya bata data ido sam wanan yar kowa sai kokarin takashi take a gidan nan haka take muna sai bayan mun karasa hada mata abinci tasa a dawo muna dashi wai baiyi ba. Nidai ban tofa ba na bar kitchen din ina jin daci da kunci a tare dani dakin na dawo na kwanta a gefen hjy don jinta nake kamar kakata data haifeni da kanta. A dakin shi bayan ya fito daga wanka yayi sallah har la,asar yakai zaune a inda yake bai daga daga kasan ba sai murzan kai da goshin shi da yake yana ji yanayin da yake wani iri. Baison yayi komai a lokacin don yana jiran dawowan mami ne a lokacin yasan zasu hau sama da ita a yadda ta hasala dashi din a waya. Don kawai yace ta yi set din yarinyar free shi bai dauka hakan ai lefi bane a gurin shi tunda ya biya abinda mami ke tunanen ta kashe wa yarinyar. Waya ya karba hakan ne ya dauke mai hankali don suna neman shi kan wani ma,aikata da za a gina suna bukatan shi ya tsara masu wasu na,urori a cikin tsarin ginan wanda saishi ne yasan yadda abin zaiyi daidai yadda suke son shi a ginan don bayanin da yakewa sauran ma,aikatar su basu gamsu dashi ba. Wanan dalilin yasa shi dole ya koma a bakin aikin shi sai dai zaiso kafin ya koma maganan shi da yarinyar nan ya tsaya kada ya bar baya da kura idan ya tafi. Anyi magariba duk bai fito ba mami kuma tasan ya dawo yana gidan bata nemeshi yadda ta saba ba idan yai hakan. Ba wai baison fitowa bane gurinta saidai abinda zai faru a tsakanin sune nai shirya mai ba alokacin. Mami da ta gama fusata da lanarin da hjy ta bata tsakanin ta da Nuriya yasa ranta baci don abinda tayiwa mahaifiyar nata din don bata kaunar abinda zai taba mutuncin hjyn balle ta bangaren ta. Sallama yayi kofan mami ya shiga dakin kai tsaye tana zaune a bakin gado a cikin rigar bacin ta sai farin tabarau da zai kare mata haske a idon ta na karatu ta duban wani takarda a hannunnta. Ba tare data dago ta kalleshi ba ta amsa mai sallama a ciki ciki tana mai cigaba da kallon takardan. Gefen ta yakai zaune yana fadi a dan shagwabe mami iam tearyed ubana ka dawo ta fada ya riko hannun ta yana fadin kasan nan akwai matsala mami. Bazan iya abinda suke son nayi masu ba don ba zasu iya fitar da kudi ayi aikin kwarai ba mami nasan ba zaka iya dasu ba dama kada dai suga sun gaiyace ka baka amsa su bane kawai. Duk maganan da take bata dago ido ta kalleshi ba taci gaba da fadin dana san haka zai faru da zuwan ka garin nan da ban bari ka tafi ba. Dasun baffan ku ya kara kirana kan zancen ka har yana ikirarin ya baka wata daya ka fitar d mata a cikin yan uwan ka daga Rufaida Nazifa da su Rubby. What mami me zanyi da yaran nan godforbid mami wanan meye a cikin su banda zalla rashin kunya a tare dasu. Wa yaja kansa da har ya samu kafan wanan maganan dama ai na dade da sani nufin su kanka ko su jalal niko yarana ba wanda zanwa aure a gida . Mami ku fitar dani a wanan zancen don wanan shirme na dauke shi gareni na riga dana fada maku matata don haka yanzu ku nake saurare. Zaka fadi haka jafar tunda ka sayeta a hannuna kake gani kana da kudin da kai zaka ban ni maryam har zaka turowa kudi jafar ? No mami ba haka nake nufi ba don Allah ina son tayi facing din studies din ta a yanzu ne idan haka ya bata maki rai kiyi hakkuri mami ki nemi wata. Bazan nema ba ta fada tana juyowa gareshi kaje gaka ga yarinyar nan sai dai kasan inda zaka kaita yanzu kuma baida ma matsala hakan mami ya fada tare da mikewa ya bar dakin. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅ABU CIKIN DUHU SIRI NE🦅 3️⃣4️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Bayan kwana biyu da dawowan shi garin na girshesu dakin mu na fito daga kitchen na nufo dakin da sauri na in fadawa hjy aiken da tayi min wurin kande a kitchen. Da sauri na koma baya na kasa shiga dakin a cikin tsoro da fargaba don Nuriya dana samu a dakin tana kuka wiwi a tsakiyan su. Kitchen na koma cikin fargaba tare da tunanen ko akan akainane ko kan waye sukayi wanan haduwan haka. Na dade a kitchen din kafin in koma dakin bayan fitan su daga dakin wurin hjy duk dako sun dan dade a dakin suna tataunawa a lokacin. Hjy tana zaune ita kade a dakin bayan dul sun watse daga dakin tana zaune da kullin abu a farar leda tana kallo. Na shigo take fadin kina kitchen wurin kande ne nace eh na shigo dakin nasame ku a ciki na koma . Muna nan da mara kunyar sarakuwar gidan nan yau tajimu a gidan nan don jarumina yai mata tas a dakin nan a gaban kowa ya tashi taka ta saida uwarku taja mashi burki. Wanan dan maganan da tayi ne ya sani tunane tare da jin tsanar da nake mai a wautana gani shine ya jawo min duk wani tsagwama da akemin yanzun a gidan mami. Sai naji ya dan ragu a raina don yadda hjy tayi min bayani sai naji tausayin shi ya dan tsirga min a zuciya tunda duk a kaina shima yake samun wanan matsalan da kowa haka a gidan yanzu. Ban kai ga gama tunane ba sai ga yaran Nuriya din sun shigo da littafi a hannun su sun zo nayi masu assignment din su. Kwasan su nayi muka koma waje kada mu damu hjy a dakin can lambun gidan muka je muka zauna na fara koya masu sosai nakan ji dadin zama da yaran don sukan sakani a cikin nishadi sosai idan muna tare da su. Hakan ne ya kasance a wanan lokacin da muke tare da yaran a lambo na shagala sosai ga dariyan yarinyar dake shirin kuka don kawai bata gane me nake tambayan ta ba. Daga can bangare daya ba tare da sanin mu ba ya jafar ne da zaman daki ya isheshi ya fito don ya sha iska a wajen. Daga inda muke zaune yake kallon mu don mun masifan burgeshi da dauke mai hankalin don ya kula da abinda ke faruwa a wurin. Ga yaran duk gaba daya suna zaune ne a saman jikina a hakan nake koyar dasu sai in basu takardan su kwashe akarshe. Yakai minti biyar a gurin tsaye hankalin shi a garemu yana tunane shi kadai a wurin yana kallon mu ko kyafta idanuwan shi baiyi. Ganin yarinyar ta tubure da kuka a lokaci guda yasa shi saki zafaffan ajiyan zuciya ya fara takowa zuwa inda muke. Baiso ya karaso inda muken ba amma sai ya tsunci kanshi da takowa zuwa garemu din gadan gadan zuciyar shi na cike da jin tausayin yar dan uwan shi dayaga tana kuka akan karatu. Kamar daga sama na tsinkayi muryan ya jafar yana fadin meya sa kuka sakata kuka haka zainab ? A dan firgice na waigo baya ta inda nake jin muryan shi din yana tsaye ya zura hanayen shi a cikin aljihun wandon shi gami da zubo min idanuwan shi akaina yana son jin amsan da zan bashi. Ganin yadda na dan dirance da ganin shi a wurin a bazata yasa shi fadin kuyi hakkuri don min naga kamar har yanzu bata gane me kike nufi bane. Malaman kuma kina ganina kin firgice da ganina yanzu yana fadin hakan ya duka ya dauki yarinyar ya dora a cinyar shi tare da kaiwa zaune a dayan kujeran dake gefen mu, muna fuskantar juna dashi. Da sauri na janye kaina gefe daya tare da kurawa kasan wurin ido ina jin yadda yake lalashi yarinyar dake jikin nasa. Ina zaune a cikin tsarguwa sai kace wata gunki a wurin ko kwakwaran motsi ban yarda na karayi ba wurin tunda ya zauna din. Da kyar ya iya budan bakin shi tare da dago kai yana kallona yace kiyi hakkuri ki kara fahintar da ita yadda zata gane me kike nufi da wanan lissafi din. Bai tsaya yaji abinda zan fada ba ya jawo kujeran tare da dan matsowa kadan a inda nake zaune. Na cira kai da sauri na dubeshi babu wasa a fuskan shi don shima ni yake kallo a lokacin. Tsoro da mamakin shi yadda ya zauna a gurin kuma yake son in koyar da yarinyar tasu ya kamani sai naji ya sake fadin yi mata bayani yadda zata fahinta a yanzu man. A firgice nace nayi mata tace bata gane bane yaya kiyi mata yanzu zata gane din insha Allahu. Ba yadda zanyi dashi haka na fara nunawa yarinyar yadda zata gane takuma fahinci abinda nake nufi a cijin lissafin tiryan tiryan nake mata bayanin komai ba tare da na dago kai na dubi inda yake zaune rike da yarinyar ba . Duk da ban dago kai na kalleshi ba jikina ya bani yana kallona a lokacin har lokacin da yarinyar ta nuna ta fahinta ya saketa tare da umartan ta data rubuta din a nata littafin na karatu. Hankalin yaran gaba daya ya dauku ga abinda suke rubutawa a lokacin don hankalin su baya kanmu ga baki daya muryan shi ya diro min a kunnuwa na yana fadin. Zainab tun ranan dana fara jin labarinki nakuma gankii a gidan nan Allah ya jarabce da tausayin ki dakuma kaunar na tallafawa rayuwan ki a cikin harshen turanci yai maganan da kamar bashi yayi shi ba. Da sauri na dubeshi don maganan nashi tazo min a bazata don ban zata zaimin wani magana makamancin wanan hakan a wanan lokacin ba. A dab firgice saida na kalli kofan fitowa daga cikin gidan nace a harshen hausa yaya ka rufa min asiri ka barni don Allah hakan da kake nuna min yana jamin matsala a furin mami da sauran mutanen gidan nan. Ya dan gyara zaman shi sosai ta hanyar yin balanced a saman kujeran da yake zaune akai kafin yace. Idan na dauke kiki daga gidan nan zaki daina jin tsoron kowa a gidan nan kinga sai ki zauna ke kadai sai wanda kike tare dashi ya fada kai tsaye. Hannuna na hade guri daya tare da kaiwa kasa a lokaci daya gwiwa bibiyu idanuwana suka kawo ruwa lokaci guda yanayina ya canza a lokaci guda. Na bude baki a cikin kyarma ina fadin yaya don Allah ka rufa min asiri ka taimaki rayuwana ka tallafamin ina son karatuna ka barni in samu nasaran karasa karatun secondary dina kada mami tayi fushi dani ta koreni a gidan nan. Sai naga ya mike tsaye zubur jikin shi ya dau kyarma yace look nasan ko waye shiyasa na shirya hakan a kanki. Ban fito da zancen nan ba saidana gama shirya komai a kanki koda ace ke din baki shirya hakan ba a zuciyar ki ni a shirye nake na shaye duk wani barazanan da wani zai kawo min a wanan zancen. Na kara fadi cikin razana don Allah yaya ka taimakeni ka rufa min asiri ka rufawa iyayyena da suka turoni don rufin asirin su. Yai wani murmushi mai dauke da takaici kafin ya sake daure fuskan shi murtuk kamar bai taba murmushi ba a rayuwan shi. Ya gyara tsayuwan shi tare da tura hannayen shi cikin aljihunshi yai min wani kallo da ba zan iya fassara ko na kiyayya ko na tsana. Yadubeni da kyau ya kada kai a cikin alaman tambayoyi a fuskan shi tare da kara kallona kafin fadin . Nima a lokacin tsoro ko shakkun shi ya fita min a rai don abinda naji ya fada na rabani da gidan ya kaini wani wuri da ban sani ba. Don haka na tsura mai manyan idanuwana da suke min a firgice ina sauraren abinda zai fada min a yadda yayi min nuni a lokacin. Shima da kyar ya iya tattara courage din shi ya kalleni ya bude bakin nasa yace dani yace haka na tsarawa rayuwan mu hakan kuma zai kasance damu. Yaya wallahi ban yarda ba ni ban amince ba bana so kuma bantaba yin wani soba ka kyaleni ka barni a yadda ka ganni in samu in kammala karatuna. Ya kada idanuwan shi tare da rausayasu yana fadin wanan kuma ruwan kine ko ki yarda ko kada ki yarda ba ra,ayin ki nake son ji ba a yanzu so take care as from now. A hanzarce ya juya ya fara tafiya ya nufi hanyar shiga cikin gidan ta inda muka fito ya shige ya barni rusunne a wurin ina rusa kuka. Takon Nuriya data fito ina wurin a durkushe take fadin tsiyar banza za a kawo min yara nan azo ana koya masu abinda bai dace ba a rayuwa don tsaban iya iskancin tsiya don ba kwabo ko tsawatawa gare ku. Wani sabon kuka na kara barkewa dashi lokaci daya ina fadi a cikin kuka ni kan ba yar iska bace bani kuma naje na kira yaran ki zuwa inda nake ba. Don haka ki daina aibantani da bata min rayuwa don kawai Allah ya kawoni a karkashin ku in zauna zaki ta min kallon wullakantantar matum ko yaushe. Ta juyo ta kalleni tare da jefamin wani irin wullakantacen kallo mai tattare da tsana da takaicina taja hannun yaranta suka shige ciki. Nan suka barni a yashe kasa karshe na dora hannuna a saman kai naja kafana daya gama yimin sanyi a lokacin zuwa cikin gidan ina rusa kuka. Sam ban san yana dakin ba yasa na fada da kuka wiwi sai ganin sa nayi zaune a dakin ya mike kafa suna magana da hjy a dakin. Lafiya hjy ta fada hankali a tashe tana kallona kokarin juyawa in fita daga dakin nayi don ganin shi a zaune dakin. Yace ina zaki ba karata kika kawo mata ba a yanzu gani zaune ai saiki fada mata tayi min hukunci a yanzu. Hjy taja wani dogon tsaki daga inda take zaune kuryan dakin tace yanzu a kan dan wanan maganan yarinyar nan kike wanan kukan haka ? Kyaleta tayi hjy do ni a shirye nake na jure da duk wani barazana da wullakancin da zaki iya min a yanzu. Hjy ki rokeshi ya barni hakan hakan ya isa hjy yanzu anty nuriya ta gama kirana da yar iska a kanshi nazo zan iskanta mata diya a gabansu muke iskanci don mu lalata masu yaransu. A zabure ya fadi what da karfi saida na dan razana na dan ja da baya a daidai lokacin da ya mike tsaye a firgice zai bar dakin. Yaka zonan kada ka fita dan nan dawo ka zauna wanan yarinyar babu abinda ke damun ta yadda na kula sai kyashi da hassada da bakin ciki a rayuwanta. Kyashin me hjy ina ruwanta da yarinyar nan tunda ba mijin ta zai zauna da ita ba. Kai dai ka barta a hakan kamar yadda na fada watarana zakace nace hakan koda bana raye kuwa. Nasan kai a shirye kake da ka dauki duk wani cin fuska da zaka gani a gidan nan don haka ya saura gareki yanzu ki daure ki amshi zancen yaron nan da hannu bibiyu. Hjy ba zan iya ba bazan iya jure wanan abinba a barni a yadda Allah ya ajeni tun kan sunana ya kara tashi ga barauniya zuwa yar iska. Yadda nake magana a wurin ba hjy ba har shi kanshi a lokacin mamakina suke yadda nake fitar da lafazi a bakina babu shayin kowa a wurin. Duk da suna min kallon mai dauke da ma,anoni a zukatan su hakan baisa na fasa fadan abinda ke a bakina a lokacin ba garesu. Hjy sai kallon mamaki take watso min tare da tuhumar kodai wanan zancen ya taba min kwakwalwane har na hadu da wani lalura da damuwa ya jawo min. Idan ba na samu tabuwa ba ko kurciya ta yaya Allah zai ban wanan daman inyi wanan sakarcin da nakeyi haka. Ya mike duk da hjy ta hane shi da fita daga dakin ya kalleni tare da sakarmin wani malalacin murmushi mai wuyan fassarawa a fuskan shi kafin ya juya ya kalli hjy yana fadin. Ya kirayi sunan hjy yana fadin ki kyaleta akwai kurciya a tare da ita duk wanan haukan a yanzu baya damuna ko kadan don wata rana bazata so ta tuna hakan ba. Yana gama fadin hakan yayi hanzarin juyawa ya bar dakin ko juyowa bai karayi ba a lokacin. Hjy ta bishi da kallo har ya bace mata da gani kafin ta juyo ta mayar da kallon ta gareni a cikin takaici tana fadin kaicon ki yarinya kurciya zai kaiki ga aikata abinda zai dawo ya dame ki a rayuwa da baya. Tana fadan hakan itama ta juya ta bani baya ba tare data kara kulluni ba taci gaba da harkokin ta a dakin ita kadai ta barni a zaune a guri daya ina zaune a takure a gurin a cikin damuwa. Ni da kaina sai na tsargu a wurin na shiga tunane da nazari ina neman mafita a kaina da rayuna. Cikin kankanin lokaci saina tsunci kaina a cikin matsanancin tashin hankali mara misaltuwa ba tare da wani bata lokaci ba na gama yankewa kaina shawaran abinda zan aiwatar a zuciyana. Don kwakwalwata ya fara hasko min abinda hjy dashi yaya jafar din suke nufi a gareni don rayuwana. A sannu na fara hasko manufarsu a kaina kan son in amince da zancen da yadda rayuwana dana yan uwana zasu daukaka kamar yadda kullun suke shan fada min. Tabas nasan ko basu fada aurena dashi kamar yadda yake fada alheri zai zamo min dagani har iyayyena nan gaba din. To amma duk da hakan zuciyana ta kasa yarda da cewa wai shi yaya jafar so Allah da Annabi ne yake min har kasan zuciyar shi hakan. Dole sai idan dai yana da wata manufane a zuciyae a kaina idan ba hakan ba ni nasan babu abinda zai kawo ya jafar din wurina da wanan zancen. Duba da irin rayuwan su da kuma irin yan matan dake hariyar shi a rayuwan shi sam ni din babu ta inda na dace dashi duba da cewa. Ko hausa sun fadi wutsiyar rakumi tayi nisa da doron kasa don ni din ba sa,an auren shi bace don nasan ya fini ga komai daga kudi ilimi kyau da wayewa. Tun lokacin da na kula hjy ta fita zance na a gidan sai kuma hakan ya saukar min da damuwa a zuciyana . Don nasan ni kaina nayiwa tsohuwar cin fuskan da baidace ba duk da kokarin da take min amma a gabanta na bude baki nake fada mata bana kaunar jikanta jinin ta. Sai bayan sallah magariba ban yarda har lokacin na fito daga dakin ba daga sallah sai kwanci da nakeyi ina faman tunane barkatai a raina . Ina zaune a cikkn muzanta bani baya da hjy tayi tun safe har dare ba tare data kara kulani ba har abin yana son ya zama min ciwo a zuciyana. Saida na bari ta idar da sallah ta zauna cin abinci na taso daga inda nake nazo mannin ta na dan tsuguna tare da kiran sunan ta da hjy. Ta dago kai fuska ba yabo ba fallasa ta dubeni kafin ta mayar da hankalinta ga abinda takeyi tace ina sauraren ki. Sai kuma yadda tayi min din ya kara sani muzanta a gurin a dan maraice nake fadin kiyi hakkuri ki yafe min idan na bata maki ba zan kara maki hakan ba idan Allah ya yarda zaki sameni da maki biyayya a koyau. Ban yarda ba hjy ta fada har lokacin bata dago kai ta kalleni ba taci gaba da cin abincin ta hankali kwance kamar bana a wurin. Kiyi hakkuri hjy na sake fada hawaye na zubo min a cikin muryan kuka da nadama lokaci guda don na gama fahinta da tsohuwar ta hau sama dani a zuciyar ta. Kinga jeki ya wuce a gareni duk da ta sallameni na dade a gurfane gefen kafin in daga na koma na rakube gefe daya a cikin damuwa. Washe gari ma har na fita zuwa makaranta muna a halin da muke ciki da hjy babu wani sakin jiki a tsakanin mu dakin. Kwana biyu da faruwan hakan ina dari dari da kowa a gidan ko me hjy ta gani ranan ina zaune nayi shiru saman kujera . Naji hjy na fadin me ke faruwa ne dake haka kwanan nan yar nan kina kokarin susuta kanki a banza lokaci guda ina hankalce dake ko abinci baki son ci a gidan nan. Na girgiza kaina cikin mamaki nake fadin banu komai hjy. Hjy tace ban yarda ba ta yaya zakice dani babu komai bayan ina kallin ki a cikin damuwa haka ? Ai duk mahalunkin mamalaki daya dubi yanayin ki da fuskan ki a yan kwanakin nan yasan akwai damuwa a tare dake sai dai idan boyewa kike son min. Hjy ba komai saidai banjin dadin yadda kema kike fushi kamar yadda mami keyi dani akan laifin daba ni na kawo hakan ba akaina. Baki daukan shawara ne yarnan a rayuwana nafi son mutum ya tsaya a inda na ajeshi kina ganin da tsufana za a hada kai dani a cuce ki idan ban tallafa maki ba. Da sauri na girgiza kaina ina fadin hjy ba hakan a cikin zuciyana ko kadan nasan kina hakane garemu dan raimakawa rayuwan mu ga baki daya na fada a sanyayye cikin muryan dake shirin kuka. Kinga wanan kukan ya isa haka yanzu taki kwantar da hankalin ki mu masu taimakon kine ba masu cutar dake ba. Na tsaya inga wanan abin ya tabbata a tsakanin ku don ni nan na tsukayi wani abinda sai kece zaki iya hakkurin jure irin sa. Wanda uwarshi ta kasa hango komai ga nufin yaron nan ya fada ba sau daya ba a gabanta da cewa din karinya da wani manufa ya zabi hakan a gareshi. Da sauri na dago kai na kalli hjy daga inda nake tace kwarai jikata yaudai zan fada maki gaskiya a gidan nan. Duk wani abinda iyami zatai maki ki daure ki fitar da mu akan wanan sarkakken abin da yake a cikin duhu wanda wani sirine dake rufe a duhu wanda Allah kadai yasan dalilin hakan a gareku. Sai dai zan shawarceki duk ritsi duk wahala kada ki yarda ki fitar da wana zancen don idan zaka sadaukar da rayuwan ka ga wani ba sai maishi yasan da haka ba. Don wanan abinda kike shirin yi zakiyi ne akan Iyakin da yanzu take wanan haukan a kanku don, , , , Sallaman wata mace ce da ta shigo dakin da abinci ta ta dire a gaban hjy ya hanata yin magana naji hjy na fadin wani abincin aka sakw girkawa ko me ? Wanan ba abinci ba ta fada a cikin wani hausa dayasa saida na dago kai na sakw duban matan don na fahinci ita din yar garin abujane irin gwarawan nasu. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣5️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA YAR UWA BA TARE DA SHIGA HAKKIN WANI BA AKAN DARI UKU KACAL 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA, , , , , , , Zan iya cewa komai na tafiya kusan daidai tun wanan ranan sai dai abindake damuna shine hanani aikin da mami tayi a lokacin. Don wanan bakuwar fuskan dana gani a gidan ranan yanzu itace keyiwa mami aiyukan da nakeyi a gidan . Saidai can ba a rasa bane mami kan kwala min kira nazo nayi mata dan gyaran a wardrobe din ta ko in boye mata wani abin koshi ba kullun ba sai can ba a rasa ba. Saidai wanan dan fadan da mami kan min abu ba abu ba zakaji mami ta falfalni da fada kamar ba mami dake kauna na da farko ba a gidan. Wanan abin yana damuna sosai har ya jawo mi zama gurin su kande koda yaushe idan mami tana gidan. Sai dai idan bata gidane zan zauna da hjy a dakin duk da ita hjyn tana fadan hakan ko yaushe saidai a gareni hakan shine mafita a gurina. Sannu sannu har yakai na saba da hakan yayin da su kande suke jin dadin zama tare dani muna yan aiyukan gida a tare. Daga wanan hutun damuke idan mun koma zamu zana jerabawan karshe hakan ya kara daukan min hankali ga komai. Wanan matar ne ta sameni inda nake zaune ina karatu lami tana gyara kayan miya da zasuyi girkin dare dashi. Naji muryan ta gatsau tana fadi da harshen hausan su zainab ana kira a dakin hjy tsofuwa jin hakan yasani dago kai na dan kalleta kafin na nade takarduna a guri daya na mike tsaye. Dakinmu na nufa da sallama na shiga sai kuma na dan ja baya don ya mamud dana sama a zaune dakin suna magana da hjy. Da sauri na dan ja da baya don ganin shi girshi da nayi a dakin lokaci guda don ban zata yana ciki ba a lokacin. Daga kofa na dan tsaya kuma na juyo ina gaida shi ya amsa ba tare da komai ba yake fadin dama nina ce a kira min ke. Ina jin hakan da sauri na durkusa kasa a inda nake tsaye don jin abinda zai fada min a lokacin ki fada muna sunan garin ku da yadda zamu samu iyayyen ki idan anje garin ku. Kaina dake duke kasa na dago da sauri don jin abinda ya fada a lokacin kafin in kara dago kai nakai kallona gurin hjy dake zaune a kasa ta mike kafafuwan ta tana daga zaune. Anchau ne garin mu na fada a sanyayye sunan mahaifin ki fa ma,ana yadda za,ayi saurin gane shi a garin. A hankali na dago kai da yan yatsuna dake a harde guri daya ina wasa da yan yatsun hannun nawa nace. Unguwar sarkin harbi muke da anje akace Habu mai faci dan gidan Asabe za a nunawa mutum gidan. Dago kai sukayi suka kalli juna da hjy kafin yace dani ida an fadi hakan kawai za a gane nace eh ko ace gidan su Asaben sarkin harbi marigayi. Yace shike nan jeki bayan yayi dan rubutu a wayan dake hannun shi ya juya wurin hjy yana fadin hjy zan tafi ina da inda zan tafi wanan ne ya dawo dani dama. Sai bayan danaga fitan shi na dawo dakin na samu hjy tana kokarin diban abinci da kanta taci nasan ta gaji da kirana ko yaushe tunda ta gama fahintar halin da nake ciki na tsoro a gidan yasa ban faye zama kamar da a dakin ba yanzun. Da sauri na karasa na karbi cibin a hannun ta na fara zuba mata a plate na gama ina rufe warmer din abincin take fadin kefa ba zakici bane yanzu ? Da sauri na dago kai ina girgiza kai tare da fadin mami tace in daina ci a nan yanzu naci a gurin su kande ai. Ikon Allah ita iyamin ta fadi hakan akan me zata hanaki cin abinci tare dani zama a gidan nan bai ganni ba don iyami ta bata wayau ta gareni yanzu. Tsoro da fargaba ne suka ziyarci zuciyana lokaci guda nan na shigawa hjy magiya don nima saida na fada nagane nayi kure wurin fadin hakan a gaban hjy. Zauna maza ki debi abinci muci ta fada a hasale rai bace da sauri na zauna na dibi abincin na fara ci don kada ta kawo wani zance. Kamar daga sama ya fado dakin da sallama yana saye cikin shada mai ruwan dark ash karamin dinki na maza akaiwa shaddan ta dan matse a jikin shi kadan. Ya shigo dakin a daidai lokacin da hjy ta mike zata shiga bandaki ganin shi bai hata shiga bandakin ba a lokacin. Dadircewa nayi na rasa inda zan saka kaina ganin dagani sai shi a dakin ina wuni yaya na fada tare da dan rusunar da kaina dake kasa ina wasa da spoon din da nake cin abinci dashi. Queen baki ganni ba baki ji wayana ba baki damu da kisan inda nake ba kuma ko ? Saida nayi dan dum kafin in samun kaina nayi bakina na fadin kayi hakkuri yaya . Yaci gaba da fadin a cikin harshen turanci a yanayi na tausayawa yake fadin Queen idan na kira wayan baki dagawa ya kike son inyi da raina ? Queen kin kuwa san halinda nake a ciki saboda ke yanzu kuwa akan ki Queen zan iya komai, komai ma da baki zata ba my Queen. Ki kallafa yadda na koma dan rikicin ki da mami ban taba samun matsala da mami irin wanan ba a rayuwana. Na rame saboda ke saboda kece zabina duk nayi wanan lalacewan haka ke bakya tausayina ne wai ? Nikan kasa magana nayi kaina yana duke a kasa din ba zan iya dago kai koda wasa in kalleshi ba a lokacin. Don na shiga tsananin rudani da tashin hankali ga kalaman shi don abin kamar almara wai a kaina mutum kamar ya jafar ke wanan maganan. Addu,a na soma don kariya daga ko wani irin masifa da yake son jefani a ciki don har lokacin duk da nake yarinya kalaman hjy yana yawo a raina. Da take fadin ta fahinci yana da wani manufa daya boye akan aurena daya nace sai ni wanda mahaifiyar shi ta kasa gane hakan. Wanan tambayan nakanyiwa kaina har yakai ina tsoron idan ba yankani ko sayar dani yake son yi ba don kawai banda gata a rayuwana don idan maganan hjy ba gaskiya bane don me yaya jafar zai tsalake kyawawan yan mata da mami ke taya mai ya nace saini. Ji nayi ya sake tausasa muryan shi yana fadin Queen kece zabina don nasan kece zata iya hakkuri da yanayina da yadda nake. Nikan kara tsorata nayi a raina don tabbas maganan hjy ya tabbata ke nan tunda yanzun ma ya fadi hakan da bakinsa a gabana. Ban kai ga karshen tunane ba naji yaci gaba da fadin ni nasan kina sona Queen don ba zaki kini ba saidai saboda mami kike kokarin boye hakan ga kowa a zuciyar ki. Zamu taimaki junane dani dake a rayuwan mu don kece kadai na yarda da inzauna da ita a tsarin rayuwana ba ko wace mace nake son aura ba. Don haka ki taimakeni Queen ke kadaice na yarda da ita a rayuwana ina son na kasance a tare dake don mu taimakawa juna dana tare damu duk hukkuncin dana yake kada ki ki hakan ki yarda da kaddaran rayuwan mu. Kaina na sunkuye a kasa nakai hannuna na share hawayen da suke zubo min don tsananin rudanin da na tsunci kaina a lokacin ciki. Na ringa addua ya Allah ka kubutar dani daga sherin wanan mutumin da bansan abinda ke cikin zuciyar shi ba a game dani. Ido kawai ya zura min yana kallon yadda nake faman sharan hawaye daga idanuwana a lokacin tabbas na bashi tausayi don nayi kankanta da abinda ke faruwa dani a yanzu. To yaya zaiyi hakan ne kawai mafita a gareshi da irin fitinan da mami ke shirin kunnu mai a rayuwan shi na yarda ya auri yar kawanta ko daga cikin yan uwan shi kamar yadda baffansa ya fada harda diban mai wa,adi akan hakan. Ya haka kuma ka zauna ka saka min ita a gaba tana sharan hawaye haka wani abin kuma ka sake mata na samu hankalinta ya fara kwanci a gidan nan yanzu . Hjy ce data fito daga bandaki tana tsaye tana muna kallon mamaki take fadin hakan cikin kure shi da idanuwanta fuska daure. Ya juyo gareta tare da wani irin sauke ajiyan zuciya yana dan gugan gaban goshin shi zuwa wuyan shi a cikin wani irin yanayi. Hjy na gane yarinyar nan tsoron mami takeyi kamar ranta ba zata bani goyon baya yadda nakeso da ita ba. Yadda yake magana ba kunya ta bude baki da ido tana masa wani irin kallon mamaki don hakan har hjyn ma saida taji tsoron shi a lokacin. Kubi yarinyar nan a sannu kaida uwarta wanan rigiman jafari yafi karfin daukar zuciyar yar nan a yanzu. Cikin takaici yace hjy kin san dai bana magana biyu na fadawa mami ban yarda da zabinta ba kuma zan taba yarda da hakan ba ta barni in zabi zabina shine kwanciyar hankalin mu gidan nan. Ta kaici ya kama hjy take fadin dan nan wai kana a cikin hankalin ka kuwa wanan zancen da kake fada haka koda yaushe. Shi kadai yasan halinda yakw ciki don haka ba tare da ya iya ba hjy amsa ba ya mike daga inda yake zaune cikin wani yanayi ya bar dakin namu cikin kunar rai. Haka ya fito a dakin yana maijin zuciyar shi na masa wani kuna da suya don rikicin da suka kwasa da mami a office din ta a kaina kafin ya dawo gidan ya sameni da zancen. Har dare banji hjy tayi min zancen ba ni kuma ban iya sake jikina da itaba har lokacin sai yawo muryan ya jafar kemin a kunnuwana kamar yanzu yake fada min maganganun daya fada dazun. Sam ban san suna falo ana rikicin abu daya ba a gidan don dai shi ya dage akan zai tafi don aiyuka sun taso masa a lokacin mami kuma tace bata yarda ya koma batare da aure ba. Shi kuma yace ta yarda da zabinshi don shi abinda ya zaba ke nan mami tace bata yarda ba ta fada mai a fusace. Yadda na fadama ko yanzu zan sake maimaita ma hakan don ba zan taba yin magana biyu ba mun shirya zancen auren ka da Iyayyen Suraiya kafin ka koma za ayi bukin ka da ita ku koma tare. Ta kare fadin hakan rai bace idanuwan ta sun kada sunyi jawur don masifa da takaicin sa da taji a lokacin. Ya dago idanun shi da suka canza kala alaman idan ya fadi magana baya canzawa yace mami na fada maki yarinyar nan ce zabina. Ni abinda nake nufi da yarinyar nan ba zaki taba ganesa ba a yanzu da na auri wanan din da kike nufi na aura mami gwara na zauna a hakan banyi aure ba. Ni da farko nayi hakan be don sama mata jin dadi da walwala na dauka don ke nayi hakan mami a matsayinta na wace bata da gata a yanzun. Koma meye manufan ka akan yarinyar nan nace ban yarda da hakan ba, idan zaka yiwa kankane kuma sai mu gani a yanzu. Ya mike tsaye yana fadin shikenan mami zan zauna hakan tunda haka kika zaba min amma ni nasan akwai ranan da zakiso hakan ace ya faru da kinsan abinda nake nufi da hakan. Ya mamud dake zaune yana sauraren su yace mami ki kyaleshi yayi abinda zaifi kwanta mai arai da wanan yawan gardaman da akeyi kan wanan zancen. Rufa min baki idan ba zaka tayani yakarsa ba ya amincewa abinda nakeso don kawai wani ra,ayinsa can na banza da baida dalili. Shima ya mike yana fadin kiyi hakkuri mami Allah ya zaba muna abinda yafi zama alheri a gareshi yai mata saida safe ya fita. Wanan zancen da sukayi ne a gaban hjy dake zaune tare dasu bata tofa uffan ba ta kafa hujja ga hakan.. Bayan kwana biyu da zancen ne ya shigo dakin bana ciki a lokacin yake tambayan Hjy a cikin dan zolaya ina matana ? Hjy ta dago ta kalleshi tare da fadin ubana ai ba wanan zancen tsakanin ka da yarinyar nan har abada. Ka tsaya tsakanin ka na dan uwa mai tausayawa a gareta ko a hakan idan kayi niya zaka iya tausaya mata ka taimaka mata babu mai hanaka wanan a gareta. Zuciyar shine ta harba da zancen hjyn take yaji wani irin kunci ya ziyarci zuciyar shi lokaci guda. Kasa daurewa yayi take idanuwan shi suka kada sukai ja lokaci guda bai iya magana ba ya mike tsaye dan barin dakin. Hjy ta dakatar dashi tana fadin kaga kada ka dauki wanan abin da zafi kaje kayi addua shine mafita ga mumini aduk sanda ya tsunci kanshi a cikin damuwa. Har yakai kofa yaji tana fadin ina son ka rabu da uwarka lafiyane jafari don yadda ta hau wanan zancen a karkace bata jin kira ga kowa a yanzu. Don dai yarinyar nan bata da wani gata a yanzu ka sani sai uwarka data daukota ta kawota gidan ta. Ya juyo yana fadin mami ta yanke min hukunci mai tsauri wanan karon kuma hjy ba zan iya jure hakan ba a kaina. Ka barta da yarta don Allah kaje ka auri wace take so din ita wanan din tunda kayi niyar taimaka mata sai ka zama mata gata nan gaba a rayuwan ta. Amma idan kaki jin maganan mahaifiyar ka sai ka kara jefa yar nan a wani hali nan gaba wa kake tunanen zai zame mata bango bayan ku da uwarku din a duniyan nan. Anan kuma ya kara dago kai ya sake kallon hjy din kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru ya juya ya fara tafiya yana fadi a cikin wani murya mai kariyan zuciya yana fadin sai da safe hjy daga hakan ya fice dakin rai bace. Da safe ne hjy take min zancen mai kama da warning a gareni tana fadin duk da nasan baki dauki wanan zancen ba tun farko a ranki. Hakan yai min dadi a yanzu yadda baki saka son yaron nan a zuciyar ki ba kamar yadda shi yasakaki din nan. Don haka kici gaba da nisantan duk wani da na iyami da komai nata a rayuwa ku samu a rabu lafiya. Saboda bana son ki sake shiga rayuwan kowa daya shafi a halin nan na iyami kiyi addu,a Allah ya kawo miji daidai ke a rayuwan ki. Idona ya ciciko da hawaye tabbas nasan iya gaskiya hjy ta fada min don tsakani da Allah tsohuwar nan take zaune tare dani. Na dinga share hawaye da bayan hannuna hjy tayi tankar bata ga me nake ba a lokacin tana maijin tausayina a kasan zuciyar ta. Hakan yasa dakin yayi shiru na dan lokaci kamar babu kowa a cikin sa lokacin dagani har ita kowa da nazarin da yake a zuciyar shi. Tabbas nasan nikan gaskiya hjy ta fada mami da ahalinta a yanzu sune gatana don a karkashinsu nake zaune idan wani abu nema ya same dolen dai sune zasuyi min tsaye akan hakan. Sosai hjy take kara jana a jikin ta hira zamu zauna muyi sosai zata tsaya ta zauna tana ban labari ko shawara. Na hanyoyin da zanbi na manta da komai har na taimaki rayuwana a cikin kwana biyune na sake sosai kamar baniba don har dan jikina ya fara dawomin a lokacin. Hakama mami duk da daure fuskanta gareni bai hana in samu kulawan da nake samu ba da farko a gidan nan. Iyaka dai zance nafi samun matsala gun mami da anty Aisha sai nuriya matar ya mamud ko shi din sai idan wani abu ya dan hadamu da su. Sai dai su samari mami din jalal da jamal babu wani sauyin fuska da suka canza min don har yanzu mutuncin dake tsakanin mu yana nan a yadda yake. Hankalin kowa a kwance don kowa ya fita wanan zancen shirmen da ya jafar ya tsiro min dashi tunda suna ganin ya fita zancen a yadda sukayi da mami a karshe. Sai gashi ranan ya shigo gidan ina daki kwance ya shigo dakin namu wurin hjy don dai kakarsu tana dakin ne duk wani na gidan yakan shiga dakin namu don gaida hjyn . Ina ganin shi na rikice ina kokarin barin dakin bayan mun gaisa dashi na mike da sauri zan bar dakin don har lokacin tsoron shi nakeji. Yake fadin karki fita dakin nan don ni ba dodo bane ya fada cikin daure fuska. Na juyo da sauri ina fadin kayi hakkuri ba don ka zan fita ba sai muryan hjy ke fadin ka daina kula yarinyar nan. Don kwanciyar hankalin kowa a gidan kaga kwanakin nan komai ya gama lafawa a tsakanin ku da mahaifiyar ku. Kwatsam sai ga mami ta bude dakin ta fado tana fadin me kake a nan ke kuma fice daga nan ki ban wuri. Juyawa tayi ta fara fadin hjy kina zaune zai shigo ya kebe da yarinyar nan bana son wani abu ya sake faruwa a tsakanin su kuma ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣6️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA BARKA DA JUMMA,A YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMIN, , , , Bayan kwana biyu da faruwan hakan da har hjy da kanta tayi mai iyaka dani a gidan don samun kwanciyar hankalin kowa a cikin maganan. Sai ya zamanto banda wani lakka a tare dani ni dai har ga Allah nasan bawai son yaya jafar nakeyi ba a raina. Saidai na rasa me yasa na damu da yadda hjy din tayi a lokacin hakan ne ke wayan sakani a cikin damuwa har yakai na fara rama a jikina wanda ban taba irin saba tun zuwana gidan. Da darene ni kadai a dakin ina kwance ashe hawayen ke zuba min a idanuwana ba tare da nasan hakan ba. Ba komai nake tunawa ba a raina sai yadda iyayyena sukai watsi dani haka kan abin duniya har hakan ke faruwa dani ba tare da kowa nawa ya san da hakan ba. Irin wanan tunanen da nakeyi yanzu ne ya karkare ramar dani hakan duk nabi na susuce har sai mutum ya dauka akan zancen mu da ya jafar ne nake wanan ramar haka. Hjy da dawowan ta ke nan daga falo taja tayi turus tana kallona a cikon mamaki da al,ajabi yadda ta sameni din a dakin. Jikin ta yayi sanyi lokaci guda tana fadin au kuka ke rusa haka yar nan ke kadai a dakin nan . Da sauri na gyara ina kokarin goge hawayen dake fuskana a lokacin shiga tayi bandakin ba tare da ta tsaya sauraron abinda zan fada ba a lokacin. Ta fito ta tayar da sallah da nake ganin shafa,i da wutirine zatayi har lokacin ina kwamce a yadda nake nade cikin kujera ban motsa ba. Muryan ta naji kamar daga sama tana fadin ni yar nan meye abin kuka yanzu ? Idan don maganan dayiwa yaron nan ne kiyi hakkuri wallahi ba nayi haka bane don in raba tsakanin ku. Nayi hakan don kawai a samu kwanciyan hankali ga wanan zancen dayaki ci yaki cinyewa tsakanin shi da mahaifiyar shi. Da kyat na iya motsa bakina na furta hjy ba wanan zancen ne damuwa na ba iyayyena da suka fita zancena a nan sune damuwana a yanzu. A, a yar nan don wanan ai ba zai sa ki rame har ki lalace haka ba lokaci guda wallahi anyi farko anyi karshe insha Allahu ba zan kara maganan nan ba a gidan nan irin haka a kanku shima din na kula da fushi yake dani a kwanakin nan. Aisha ce ta shigo dakin ta samemu muna wanan maganan duk da shigowan ta baisa hjy ta daina fadin abinda take fadi ba a lokacin. A daidai lokacin da hjy ke fadin Allah ya baku hakkuri kuskure nayi na aikata hakan . Aisha data fahinci maganan tsohuwar inda ya dosa Aisha taja wani irin tsuki tana fadin wanan zancen har yanzu nina rasa me yasa ya J ya nace akan wanan zeey din haka wallahi mami tace bata son zancen nan amma shi duk yabi yana kokarin dagawa mutane hankali akai. Da sauri naji hjy tace a, a yar nan kada in kara jin kin fadi irin haka so ba a yi mashi irin haka abune shi mai cin zuciya rabu da namiji kan abinda yake so. Idan an mashi hakan ba,a kyauta mashi ba don yaron nan bai taba nuna yana son wata ba haka kamar yadda ya nuna a yanzu. Daga shi har yar nan ai yanzu an zama daya dan yar nan yanzu tankar iyami ce ai ta haifi abinta bata da maraba da wace ta haifa a cikin ta tunda iyayyenta sun bata amanan rikonta a hannun ta. Da sauri Aisha ta dago tana fadin ba zasu taba zama daya ba kan da yaya jafar hjy ta yaya ma za a hadusu wai ? Wani kallo hjy ta watsa mata lokaci guda kafin tace ni ba ruwa da zancen nan yanzu daga fadin gaskiya ya J ya tashi makeni gidan nan. Dole ya makeki don kalamin ki baida dadi yar nan don yarinyar nan tana da hakkuri da mutuncine ko wanan maganan da kike fada yanzu haka ke kinga ya dace da ki fadi hakan a gabanta. Tsam ta mike ba tare datayi wani magana ba ta fice daga dakin hjy ta bita da harara tana fadin sakariya mara wayau idan Allah yayi saiku hana mugani. Indai biyayya gun nagaba nada dadi mu zuba gani nida uwarku data raina zancena a yanzu tunda ban isa in fada mata daidai ba a gidanta yanzu tana ganin ita ta ishi kanta ke nan yanzu. Ta juya inda nake bayan fitan Aisha dakin tana fadin ke kuma ki barsu da dansu wa yan nan zuciyar su ya kyankyashe da wullakanta dan Adam. Amma saboda shi har zaki wani shige daki kina hawaye haka don baki danayi yanzu sai tunanen shi. Ki matsa ki yada kanki wurin wa yan nan mutanen da suke raina arzikin tallaka a rayuwan su. Take jikina ya kara sanyi nace nifa hjy na fada maki ba wanan zancen kika samu inawa kuka ba dazun. Don waye kike kuka idan bashi bane din idan fadan danayi ne bazan kara shiga harkunku ba a gidan nan. A sanyaye na marairaice ina fadin kiyi hakkuri hjy insha Allahu ba zan kara ba tace shike nan ai. Nidai shawaran da zan baki shine wallahi ki natsu ki bar saka wanan zancen a ranki ki kara kama kanki da wanan zancen. Kinga tunda aka fara haka ko da Allah yayi kunyi wanan auren bazaku samu jittuwa da sarakuwar ki ba a hakan tunda har ta iya rufe idanun ta ta nuna hakan yanzu. Don hakane yasa nace mai ya fita wanan zancen don abindana hango maku din keda shi nan gaba. Amma badon bana son ku a tare ba ko wani abu can kawai dai abin ne da uwar taku keyi akwai cin fuska a cikin sa yanzu. Abi komai a sannu sannu iyayye ku su amince da wanan zancen don ina gudin abinda kaje ya dawo daga baya. Hjy kiyi hakkuri wallahi ba a kansa nake kuka ba nan na labarta mata abinda nake yawan tunane game da iyayyena a raina. Saida hjy ta gama saurarena kaf take fadin koma dai meye ba zasu taba mantawa dake ba a rayuwan su mussanman ma mahaifiyar ki dole tana can a cikin rashin ki tare dasu a yanzu. Haka ta kalleni a cikin tausayi tana fadin ki saki jikin ki ki kara kwantar da hankalinki ki nunawa iyami danta ke baya gaban ki a yanzu. Nace hjy ni komai ya wuce a wurina tun farko ban taba nasa wani alaka a tsakanin mu ba bayan na yan uwantaka. Can cikin dare ina barci nake jin wayana na varvirating a saitin kunnena duk da nasan babu mai kirana sai shi yanzun kuma ya daina kirana din tunkan ai wanan tsakanin su da hjy. Har kiran ya kare ban dagaba sai ma kokarin danne wayan da nake gudun kada hjy taji kiran. Kira uku na daga a dan rikice don nasan ba zai daina kira ba idan ba na daga wayan ba a lokacin. Murya kasa kasa na amsa da sallama don kada hjy ta jini jin muryan shi take na rikice gaba daya na rasa a wani duniyan nake. Wani irin tsoro da fargaban jin muryan shi suka ziyarci zuciyana wanda nake ganin kamar amsa wayan babban laifine nake aikatawa a lokacin. Wani irin ajiyan zuciya naji ya saka yayin da yake ji a bangareshi kamar susa nake mai a kwakwalwan shi don rikicewa. Ran sarauniyarta ya dade kin wuni lafiya ya rigiman hjy da tsufan ta ban san lokacin da dan murmushi ya subbuce min ba a lokacin. Yace nasan kina nan kina fama da rudu irun nata a kullun sai kara firgita min ke da takeyi. Aiko hjy ta wuce hakan a wurinta don da tana da iko da kai da ta faranta maka rai fiye da kowa a duniyan nan. Na sani amma yanzu itama din sun fara in mata ai nake gani kan hakan . Da sauri nace yaya ka daina irin zancen nan don maganan hjy shine gaskiya a garemu don Allah yaya ka barni da wanan zancen. Ka tuna ni kamar marainiya nake a cikin ku kune gatana a yanzu na rokeka idan kai sanadin dana bata da mami zan shi, , , , Amma so ance hana ganin laifi ko nayi shiru yace don haka kada kiga laifina a wanan bangaren . A raina nace tabbas akwai sauran rikici a tsakanin mu gidan nan yanzu don a gaskiya ba zan taba yarda da hakan ba a gareni don mami dai ba zata taba yarda da hakan ba a tsakanin mu tunda ni banda gata a wurinta. Yace ina son inji kin shirya zaki zauna dani komai ritsi komai wahala ni kuma nayi maki alkwarin inganta rayuwan ki dana yan uwan ki da iyayyen ki tun daga ranan da bakin ki ya bude da kin yarda dani ko ba tare da yardan mami din ba. Wanan maganan yafi karfin fahintana ka rufamin asiri a rayuwana koda zan soka yaya badan kudin ka ko wani abu zan soka ba zan soka ne tsakani da Allah kamar yadda nima kuka rikeni a cikin ku amana. Koda kuwa yin hakan yana da wani illa a gareni nan gaba zan daure in ga nayi abinda zan sakawa mami a rayuwana. To idan kuma mamin naki bata yarda ba kan wani dalili nata na daban zaki iya jure wanan daman da kika samu daga taimakon iyayyen ki da yan uwan ki ya tafi ga wata. Nace idan yin hakan zai kawo fahinta a tsakanin mu da mami a shirye nake da mata biyayya ko wani lokaci. Amma dai kin yarda har a zuciyar ki niba mai cutar dake bane zainab ya fada a cikin wani yanayi mai ban tausayi. Yaci gaba da fadin ki yarda dani kanwata ke kadai zuciyana ta amince dake zainab kece zuciyana take hasko min a yuwana kece rufin asirina kada ki yarda ki barni zainab komai ritsin mami a garemu na maki alkawarin rikeki a mana a rayuwana koda kuwa duk duniya zasu juya maki baya akaina. Nayi maki alkawarin rikeki amana har karshen rayuwan mu nidai muradina shine ki amince min zainab yardan ki kawai nake bukata a yanzu. Nayi maki alkawarin rikeki amana harga Allah zainab ba zaki taba dana sani a kaina ba matukar kika yarda da amsa min da eh yaya na amin ce. Ki taimakeni ki taimaki rayuwana kada mami ta zantar da hukuncin da zata dawo tana nadama a kaina daga baya akanshi. Yadda yake magana a cikin wani irin yanayi kamar roko a gareni yasa tausayin shi ya rufe min zuciya ban san lokacin dana bude baki don dakatar dashi nace. Na yarda yaya indai hakan shine rufin asirin ka da mami dama yan uwan ka na yarda da wanan koda kuwa hakan zai zama kadara rayuwana mutukar hakan zai zama rufin asirin ku a duniyan nan. Yace Alhamdullahi zainab na gode tunda kika fahince kamar yadda hjy ta fahinceni ga hakan yanzu kema din kin fahinceni. Zainab kece rufin asirina ke kadai ce wace na yarda da ita a rayuwana da zaki iya zama dani a irin yanayi na ko yaushe ba zabin mami da take soyi a kaina ba yanzu. Fatana inje ga iyayyen ki yanzu su amince dani kamar yadda kema kika fahinceni kika yarda dani . Na samu duk wani fari ciki da nike so a fanin rayuwan duniya ke kadai kika rage min a yanzu in mallaka . Idan har mun daidaita a tsakanin mu muka shirya zama da fahintar rayuwan mu to tabbas bani da matsala a duniyan nan fatana yanzu mu samu kiyamar mu. Idona na lumshe don jin abinda ya fada ina kiyasta maganganun daya fada min a zuciyana saidai na kasa fassara abinda maganan nasa ke nufi a fili. Katseni yayi da yake fadin to yanzu sai ki shirya tsana da tsangwaman mami a gareki don kinsan itace matsalan mu. Saidai hakan na dan lokacine ba mai dorewa bane idan mun bar kasan nan munyi nisa da ita komai a sannu zaizo ya lafa. Mun jima a hakan shike zuba min hiran da ba amsa tun ina amsa mai da eh ko a, a har ya fahinci barci ya kwasheni a lokacin ya sararawa ranshi. Washe gari koda muka tashi hjy bata nuna min komai ba har na shirya na tafi school sai bayan mun dawone da yamma muna zaune. Naji hjy ta jefo min tambayan da ya girgizani lokaci gudan don ban zaci taji me muke tataunawa a tsakanin mu a daren jiya din. Ina fatan kin fara shiri kan abinda koka tarawa kanki kika yarda da hakan da bakin ki ba wani ya fada min ba na jiki naji zancen ku kaf a kunnena duk yadda kukayi dashi. Kai na sunkuyar kasa a cikin kunya dajin nauyin hjyn data fito min da wanan zancen . Nayi rantsuwa akan wanan kudirin naku kece da hakkuri jikata a ciki nasan kuma babu wanda ya isa ya wuce kaddaran shi a rayuwa. Nasan kin yanke wanan shawaran ne ba tare da kinyi nazari a rayuwan ki ba na abinda zaije ya dawo ga auren shi gareki. Hakan kuma ya samo asaline ga yawan tausayin da raunin irin namu na mata ga da namiji da muke saurin yarda da bukatan su. Naso ace kin manta da zancen jafar a rayuwan ki saidai a yanzu kadara ta riga fata don kin riga da kin amsa mai bakin alkalami ya riga daya bushe gare ki ko. Dama ubangiji baya son ayi maishishigi ga al,amarin shi yanzu ni a nawa bangaren zan tayaku da addua insha Allahu ubangiji ya kade mana tsotsayin dake cikin wanan al,amarin naku amin. Duk yadda naso hjy ta wayar min dakai kan wanan zancen hjy takiyin hakan fafir dole na hakkura na kyaleta da gutun sharhin da tayi min din. A bakin hjy nake jin sunyi tafiya da ya mamud ko mami bata sanda zancen tafiyan tasu ba sai bayan tafiyan su ne tana neman ya mamud matar shi ke fada mashi sunyi dan balaguro da dan uwan shi zuwa wani business wajajen kaduna. Kansu tsaye sukaiwa garin mu tsinke su isa misalin karfe daya da wani abuna rana a gidan dagacin garin mu sukaiwa kansu masauki. Bayan gaisawa da gabatar da kansu gareshi dako waye mahaifin su take dagaci ya gane daga inda suke. Bayan fahintar juna take suka gabatar mai da abinda ke tafe dasu ba bata lokaci take ya gane kowa ake nufi mai gari yadan musguda yana gyara zaman shi tare da fadin. Kardai wanan yarinyar da uwarta ta kawo kara nan gurin mu kakarta da mahaifinta sunkaita birni aikatau ba tare da sanin wurin wanda aka kaita ba taka maimai. Ya mamud ya tare da fadin a gidan mu take aiki a hannun mahaifiyar mu hjy maryam lerai take zaune tare damu. Yanzun ma tafe muke da zancen auren yarinyar kanina gashi shike son auren ta sai kanin mahaifin mu gashi zaune tare da wan mahaifiyar mu Alh bello samu,naka. Munzo da zancen neman auren yarku ne wa dan mu kuma dan danuwana kamar yadda addini ya kindaya muna da al,adan malam bahashe. Maigari ya na,am tare da yabawa kamalan su da kuma yabawa ga iyayyen su ya nemi da sy bashi lokaci a nemo iyayyena da suka haifeni don a sanar dasu halin da ake ciki a kaina. Ba bata lokaci aka aika neman mahaifina dake bakin aikin shi a lokacin jin maigari ke neman shi don zuwan wasu baki da ba a san meke tafe dasuba a lokacin. Hakan yasa Abba ya nemi da yaje gida ya sauya tufafin aikin shi dake jikin shi da farko don zuwa amsa kiran maigari da bakin shi saidai gaban shi na faduwa don baisan abinda zaije ya sama ba a can fadan lokacin. Tunda Abba ya tunkari fadan ya hango tarin motocin dake wajen gaban shi ya shiga faduwa don baisan dame sukazo gareshi ba . Shida ba birni yake shiga ba kuma ya san wani ba ta yaya wa yan nan bakin zasu danganta dashi. Bayan ya iso sun gaisa a ciki mutunci dagacin garin mu ya gabatar mai da abinda suke tafe dashi a lokacin. Ikon Allah Abba yace lokacin da aka nuna mai ya jafar din da yake zaune ya hakince a gefe daya bai wa kowa magana ga cikar kamalanshi da zati kawai shida dan uwanshi daya gama cika wurin. Bayan bayane ne Abba yake fadin yana da magabata ga maigari sai su taru suyi magana abindaya dace yana fadan hakan ya fita daga zauren maigari yace bazaiyi magana ba kasancewar yarinyar yar fari ce a gurin shi. Ba a dauki lokaci ba yan uwan mahaifina suka gabata zauren maigari take aka tsayar da maganan aure kawun su wan mahaifiyarsune ya zo da wani zance da cewa mai zai hana tunda gasu ga jama, a a daura auren ga baki daya inyaso daga baya duk wani al,adan aure ya biyo baya. Take akai na,am da zancen shi abu na kudi haka suka zube kudi a zauren maigari aka yi yekuwa take gurin ya cika aka daura aure akan sadaki dubu dari don maigari da sauran iyayyena sunce dags hakan ba zasuso akara kwandala akaiba. Da mamaki a ransu da kawu ya bude bayan motar shi aka fitar dasu alawa da sauran abubuwa da duk ake bukata a wurun daurin aure. Karfe hudu na yamma an gama komai kowa ya watse ya nufi inda ya fito suma dai a ranan suka juya suka koma kaduna sai cikin dare suka shigo don jirgin sai karfe bakwai na marance yabar garin kaduna. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣7️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA INA MAKI FATAN ALHERI A KULLUN UBANGIJI ALLAH YA TSARE YA KARE YAIWA ZURI,A ALBARKA AMIN, , , , Ina bukatan addu,an ku gareni yar uwa badon halina ba sai domin Allah da annbinsa gareni Allah ya bada ikon yi lafiya Amin nagode ga wace ta samu lokaci tayi min dama wace Allah baiba dama ba taji tanasa hakan Allah ya kara haskaka muna al,amuran mu amin. Tunda ya dawo gidan bai fita ko ina ba yana dakin shi har wayewan gari mami bata sakashi a idon ta ba. A daren ranan ne kuma akai hira dashi a talabijin din NTA na kasa wanda mami tana zaune har da hjy kawai sukaga an haskoki shi a matsayin bakon da za ai hira dashi a ranan. Mamakine ya kama mami dake zaune tana aiki saijin sunan dan nata tayi a matsayin babban bakon su na ranan a hankali mami ta zare glass din dake idon ta tana mamaki don bai fada mata cewa sun gaiyace shi ba . Kowa dake falon ya mayar da hanlalin shi wurin sauraren hira da akeyi da ya jafar din a sannu ake masa tambayoyi yana bada amsa mami sai girgiza kai kawai take a cikin burgewa. Bayani ne na irin business din su ta yadda zasu tallafawa kasa a samu cigaba hakan daga kasashe daban daban na duniya. Ko wanan haskawan ya kasance sunyi nasaran shigo da na,urori n wutar lantarki da zata karawa wutan kasan haske ba tare da ansha wahalan wutan neper ba a kasa. An dauki lokaci ana hiran falon yayi tsit hjy tsohuwa ke fadin ni wanan da an barni sai nace jafari ne ai don kamar su datayi yawa sosai. Aisha dake gefe zaune ta nade kafafunta saman kujera taja tsuki tare da fadin dama wa kike kallo a tv idan bashi ba yanzu. Yayin dasu jalal suka hau mata dariya daga inda suke zaune suma suna kallon shirin tambayan da aka jefo maine yasa mami ta daka masu tsawa akan suyi shiru su saurara. Mai hira dashi yace mr jafar mu,azu mahadi laire kayi namijin kokari sosai wurin shigo muna da wanan kayan a kasan nan babu abinda mu yan kasa zamu ce maka sai godiya da kira ga irin ku matasa da suyi koyi da irin halinka a taru a gina wanan kasan ta farfado daga faduwan tattalin arzikin da take barazanan shiga a yanzu. Sai tambaya na karshe da zamuyima a yanzu ko enginer namu zai dan fadawa masu kallo da sauraren mu shekarun sa nawa ? Sai lokacin ya danyi murmushi tun fara hiran dashi tare da fadin iam just talatin da bakwai nake nema a yanzu. Matan ka nawa a yanzu ido ya dan lumshe kafin ya bude ya kalli mai tambayan ya furta matana daya sunan ta zainab bello Anchau . Itace matarka ta farko mai tambayan ya tambayeshi a cikin dariya sai ya dan lumshe idanu kafin ya waresu a hankali yace cikin murmushi itace auren namu baikai three days ba ai yanzu da mukayi. Don aurene na siri da ba kowa yasan da faruwan hakan ba sai yan kalilan ya fada yana gyara zaman shi. A daidai lokacin da mai hira dashi a tv ke fadin wow zanso naga wanan lucky girl din datayi nasaran sace zuciyar matashi kamarka da kasa ke alfahari dakai haka. Daidai lokacin ne a falon mami kuma abubuwa suka faru da dama a wurin don ba mami kadai ba har yayanta dake zaune a falon saida suka mike tsaye a cikin fargaba da tashin hankali. Hjy dai da ba turanci takeji ba sai binsu da kallon mamaki takeyi tare da mikewa tsaye itama tana fadin wai meke faruwane haka ? Don ganin yadda mami ta sake kofin glass din daga hannunta ya tarwatse a gurin lokaci guda tana batun fita hayacin ta a take. Tambayan su take meke faruwane haka a gigice Aisha na fadin ina wanan ma aiba zai taba faruwa ba wallahi wanan ai jawa kai raini ne da wullakanci. Ya jamal ne dake kan mami da take kokarin kiran waya hankali tashe ta kasa sai jalal ta mikawa wayan ya kira matashi ya juyo yana fadawa hjy cewa. Wai ya J ne ya fada yanzu sunyi aure da zeey kwana uku daya wuce din nan a razane tsohuwar tace aure ? Haka ya fada yanzu hjy a duniya kin kuma san halinshi baya magana biyu shi hakan ne tunda ya iya fadawa duniya kai tsaye. Shike nan hjy ta fada iyami kin kai ga yadda kikeso da yaran nan Allah ya gani yaron nan baida hakkin ki ko kadan. Shiyasa ubangiji yai maki hakan kina raye ki ci barnan ki da hannun ki ba sai gobe ba ace mutum ya tsaya yana jayayya da hukuncin Allah haka ? Allah ubangiji yasawa aure albarka ya kore shadan da shedanu a tsakanin yaran nan kuma Allah ya basu zuria masu albarka, , , , , haba hjy. Aisha da ta raba hankalinta gida biyu ke fadi haka ki duba kikaga yanayin da mami take ciki da kike wanan maganan. Ga kuma wayoyin mami din dake ake ta faman kira a lokacin wanan na shigowa har ya katse ba a daga ba wani ya sake shigowa daga kawayen ta da yan uwanta. Ban san meke faruwa a gidan ba ina dakin mu kwance ina karatu don jerabawan da muka fara zanawa yasa yanzu ban wasa da karatu na. Don damuwan da tashin hankali bai hanani mayar da hankali ga karatuna ba. Dan haya niya nake ji sama sama tunda ba tv ne kunne a dakin ba sai dan karan nauran sayin dake aiki dakin lokacin. Kamar ance in fita waje zubur na mike daga kwancen da nake na zura takalmina dake kofan daki a fararen kafafuwana da yanzu suka samu hutun jin dadi sun kara fari da kyai kamar bana taba kasa dasu don hasken su. Har nakai kofa naji wayana na kara najuya ina kallon wayan dake gefen filo ajiye na nufi wurin duk da ban debe tsamani ga kirana din ba shine dai. Na dauka da sallama muryan shine ya sauka a kunnena yana fadin queen kina inane yanzu ba tare daya amsa min sallaman ba. Dakin mu zan fita waje ne yanzu ka kirani kada ki fita nasan mami na gida yanzu akwai matsala idan kin fita yanzu wurin su. Kirjinane yai wani irin bugawa lokaci guda nace a hankali matsala akan me kuma yaya yanzun nan na gaida ita a falo ai. Na fada maki kada ki fita ki bari yanzun zan karaso gidan idan ma zaki fitone ki bari in shigo. Jikina yayi sanyi yayinda zuciyana ya shiga fargaba da tsoron jin abinda ya fada din naji yana fadin al,amarin mai girmane zai faru a yanzu tsakanin mu da mami don yanzu nagama fadi a tv an daura min aure dake. Aure na fada da dan karfi kafin in wurgar da wayan saman gado inje kasa a sulale don firgicin abindaya fada din. Shike nan wanan mutumin yaja min tashin hankali da fitina a rayuwana don me zai fadi haka a duniya dole mami ta dauka ai gaskiyane ke nan. Kamar an tsikareni sai kuma nayi zubur na mike na kwasa da gudu zuwa falo ban tsaya sauren gargadin da yaimin ba a wayan. Ina fitowa falon naja na tsaya turus don yadda gaba daya suka zubo min idanuwan su a falon lokaci guda. A hankali nake kokarin takowa zuwa garesu naji Aisha da mami sun daka min wani irin tsawa kusan lokaci guda suna fadin ke dakatanan gurin kada ki yarda ki karoso wurin nan bakar manya kawai Aishan ta fada. Hannu mami ta daga min itama tana fadin barta tazo ta fada min abinda ban sani ba tunda ta zamax munafuka tsakanina da dana. Idona runtse hawaye ya shiga tsiyayya a idon nawa na kai kasa ina fadin mami bazan taba munafurtaki ba a rayuwana. Idan nayi maki laifine don Allah ki yafe min mami idan kinyi fushi dani mami ina zan saka raina. Rufa muna baki yar iska ba kauyan banza bakar manya mai nacin tsiya kamar karya wace, , , , Tas tas Jamal ya kwashe Aisha da mari biyu masu kyau sai data duka a inda take zaune tana jefo min zagin. Mami ta dago da zuman ramawa Aisha marin yayi saurin kaucwa a inda yake tsaye ta hanyat jada baya kadan mami ke fadin ka mareta saboda wanan yarinyar jamal. Mami bakiji irin mugun zagin da take zagin diyar mutane dashi bane ita waya zageta haka ko meye laifin zeey a cikin zancen nan yanzu wace ke gida always tare daku. Shiru sukayi a dalilin shigowan yaya jafar da ya mamud gidan ya mamud da tun kan ya karaso yake fadin meke faruwane kuma yana kallon mami ya kuma juyo inda nake gurfane ina sharban kuka ya sake juyawa wurin da Aisha ke zaune yana fadin wai meya farune haka wai ? Wani irin ashar mami ta wulwulo ta duramin a tsorace na jada baya na makure a jikin bango jikina na kyarma hankali a tashe ban daina kukan da nakeyi ba har lokacin. Mami ta sake daka min wani uwar tsawa tana umartana da nadawo gaban ta take na mike jikina na kyarma na dan karaso inda suke zaune ita da Aisha. Ya jafar din ya samu wuri a gefen mami yakai zaune a cikin kwanciyan hankali yanayin shi yake. Banyi aune ba naji mami ta fisgeni da karfi nakai gurfane a gabanta da sauri ya jafar din yace subbahanallahi this is bad mami meye laifinta a wanan zancen. Wani kallo mami ta watsa mai kafintayi kukan kura ba wanda yai aune da ita lokacin takai min mari uku masu kyau a fuskana saida duk diyan nata suka mike tsaye don firgita. Ban samu bakin yin ihu na don gigicewan danayi a lokacin sai idanuwana da suka firfito waje kamar mai shirin bankwana da duniya . Ta koma inda ta taso tana fadin mara mutunci kawai kin cuci kanki wallahi ni baki cuceni ba zainab. Dama an fadi tsintarciyar mage bata taba zama magen gida sai ta hada da halin sata ashe zancen da ake fada min inyi hankali dake a yadda nasakaki a jiki ba karya aka fada ba. Har lokacin falon yai shiru kowa yana sauraren ta taci gaba da fadin wallahi yau ba zaki kwana min a gida ba har in maganan nan gaskiyane ya fada. Kuma yanzun nan ba sai anjima ba zaki barmin gidana babu ruwanki da wata zuri,ata yar iska. Kije can ku karata da tsitanki keda tambadaddun iyayyen ki da suka sakoki a cikin duniya suka watsar dake haka. Kai haba mami this unfear wallahi yarinyar nan ina ta sani a garin nan da za ayi mata wanan irin koran kare haka bafa itace mai laifin nan ba dankine mai laifi mami ya mamud ya fada rai bace. Tsam ya Jafar ya mike tsaye ba tare da yayiwa kowa magana ba a wurin ya nufo inda nake gurfane ina rusan kuka . Dakatar dashi mami tayi ta hanyar fadin jafar kana taba ta wurin nan saina tsine maka yanzun nan . Jin hakan ya dakatar dashi daga niyar tabanin da yayi da farko yana shafan kanshi a hankali batare dayayi magana ba ya juya ya zauna inda ya tashi din. Wani marin mami ta sake kaimin saida ya yunkura daga yadda yake zaune kamar zai tashi a lokacin. Iyami kina da sauran hankali kuwa hjy da take zaune tayi mutuwan kasko a zaune ta fada rai bace. Kai na girgiza don jin muryan hjy din nace wallahi hjy ban san komai ba akan laifin da ake nufin na aikata yanzu. Yi muna shiru munafukan banza da wofi kawai wa zaki kawowa rainin hankali a nan bayan kun asurce min da mugun alkaba,in kuna kauye. Yanzun wani karya zaki fada muna kin dauka bamu san me iyayyen ki suke maki bane a can gida kin rikita min kanda na rasa gane kansa gabaki daya. Hannu na dora a kai tare da girgiza kaina ina fadin wallahi mami ban taba tunane ko wayau aikata hakan ba ga kowa balle wanan da ake tuhuman na aikata din yanzu. Yadda ta zaburo zata kara makana yasa nayi wurin hjy da sauri na kankame a jikinta ina fadin hj ki ceceni ku mayar dani wurin iyayyena don Allah wallahi ban aikata komai da ake nufin munyi ba asalima iyayyena basu san wanan zancen ba . Mikewa yayi zubur tare da fadi cikin wani tsawa enough ya tsaya yana bin kowa dake falon da kallo na dan second kafin yace indai ba kasheta kuke son yi ba please mami ku barta hakana. Nina mai lafi ba yarinyar nan da bata san komai a wanan zancen ba don nina ganta nace ina sonta a duk yadda kuke ganin take ni tayimin a hakan. Hannu ya mika ya wufci hannuna daya daga inda nake gurfanen ya mike dani tsaye tare da nufar hanyar fita waje dani. Kon binshi nayi da karfi nake fadin mami ki taimakeni ki cece rayuwana kada ki bari ya tafi dani don Allah mami kicece rayuwana nima yarkine mami. Jin ya rikoni da karfi yana kokarin jana da karfi mubar falon da karfi na fara fadin innalillahi wa,innalaihim raji,un mami kada ki bari yaya ya tafi dani don Allah. Ganin mami bata ko kalleni ba yasa na juya wurin hjy ina fadin hjy ki taimakeni kada ki bari a cutar dani hjy. Hannu hjy ta mika mai tana fadin jafari miko min yarinyar nan nan kaga dai uwarku ta nuna yar nan yau bata kwana mata gidan nan . Mami ta juyo a fusace tana fadin hjy bafa zanbar yarinyar nan gidan nan ba yau taje can ta hadu da yan duniya irinta su dace. Nasani iyami yar ba zata kara awa daya ba a gidan nan ko ince ba zamu kara awa daya ba a cikin gidan dani da yar nan. Kai mamuda jeka ka da dan uwanka gamu fitowa ke kuma tashi ki shiga ki hado duk wani abin bukatanki dake gidan nan. Na dan tsaya nawa hjy ta daka min wani uban tsawa na mike tare da dan dingisa kafata da yai min nauyi ina shiga dakin naja na tsaya daga kofa ina bin dakin da kallo kamar yau na fara shiga dakin. Jin takon tafiya an nufo kofan dakin yasa da sauri na matsa wurin wardrobe dina na bude na fara fitar da takarduna sai wayana dana dauka na tura a school bag dina. Hjy ta shigo a cikin wani irin yanayi dakin wanda ban taba ganinta a cikin shi ba ta nufi wurin jakkar kayanta tana kokarin dauka da karfin Allah. Da sauri na karasa wurin ta na fada saman jikin ta ina fadin hjy idan kinyi haka kamar nice sanadin hadaki da yarki Allah ba zai taba yafe min ba kan hakan. Ni ba donke zan bar gidan nan ba yau don kare mutunci da martaba na haihuwa gun yar dana haifa da idon ta ya rufe a gabana take wanan irin tujaran da nuna dan adam ba kowa bane a wurin ta. Kamar yadda ta rantse nima haka yau din nan ba zan kwana a gidan nan ba sai mu tafi dake duk inda Allah ya nufa mu kwana a can. Ina ji ina gani ban iya tabuka komai ba hjy ta fice da dan jakkar ta a hannu ta nufi falo dashi simi simi na biyo bayan ta dauke da jakkar school dina wanda shi kadai na iya dauka a gidan lokacin. Kowa na tsaye cirko cirko a falon yanayin su babu dadi mami ke zaune ta sada kanta kasa a cikin wani irin yanayi na damuwa dkn bansan abinda ya faru ba bayan barina falon lokacin. Yanzu da gaske hjy tafiya zakiyi don wanan maganan zaki bar gidan nan ai koshi yaya din baice hakan gaskiyane ba har yanzu. Amma ke kin tashi kin hada kayan ki wai gida zaki bari saboda an taba yar dakinki ko ? Kada ka kawo min diba albarka ta fada tana kallon jalal da yai maganan a lokacin a hasale kafin ta juya wurin ya mamud tana fadin mu tafi ka kaimu titi ka barmu a nan zamu samu na Annabi da zai iya taimaka muna daga sama do na Allah basu kare ba a duniyan nan. Ta juyo inda nake tana fadi shige mu tafi kafin su halaki a gidan nan don an mayar dake bare. Simi simi na zo na wuce a gaban su duk suka bini da kallo mami bata iya cira kai ta dago daga duken da kanta yake ba ga wayoyin ta suna ta kara naji jamal na fadi Aisha ki kashe wayan nan ga baki daya don Allah su daina damun mu haka. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣8️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU MASOYA UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERUN SA YA TSARE MU DAGA AIKATA SABO KOMAI KANKANTASHI AMIN, , , Nagode yan uwa da adduan ku gareni ubanginji ya yayewa dukkan musulmi damuwan shi a duk inda yake Allahuma Amin. Sai bin hjy nake a baya tana jaye da hannu ina faman share hawa da hannuna daya. Min karaso security din ya jafar suna tsaye cirko cirko a gaban gida suna dakon mu da fitowan mu kokarin amsan jakar dake hannu mu suka shiga yi lokaci daya. Zuwa wurin motan da suka riga suka bude kofufinta tun kan mu iso wurin motar kofan yana a bude suna jiran isowar mu. Ba bata lokaci mu shiga sai wani girma da suke bamu kamar yadda suke bawa ogan su bayan mun zauna a motar sai ga ya mamud da dan saurin shi yana fadin hjy kuje zan shigo zuwa an jima ko safe inda kuke ina son naga mami ne a yanzu. Kada ka dami dani mamuda zauna da uwarku kada ta aikata abinda bai dace ba ga dan uwanka. Saida safe sukayiwa juna suka kama hanya damu duk da kuka nake bai hanani kallon titin garin ba don ba fitan dare nakeyi ba a garin. Wani gida da zance yafi na mami tsaruwa da komai ga motoci nan zube kamar wurin sayar dasu suka shiga damu gidan. Bayan motar ta tsaya ne da sauri security din dake gaba ya fito daga motar ya bude mana muka fito daga cikin motar zuwa cikin gidan a tare da biyu daga cikin su sai faman nan nan suke damu kamar wasu manyan baki. Gidane har gida don in tsaya fadan tsarin ginan zai bata muna lokaci yanzu ba zaka taba cewa wai a wanan kasan wanan ginan yake ba duk ko da lokacin darene don goma dare har ya dan gwauta a lokacin. A falo muka zauna a daidai lokacin da sako ke shigowa wayan wanda nake gani shine babban su ya duba tare da daukan jakkar hjy da nawa zuwa sama. Bai dade ba ya dawo da sauri falon suka fita ina makale a jikin hjy har lokacin don kamar dumin jikintane zai tsimakamin ga abinda nakeji a rayuwana. Muryan hjy ne ke fadin kinga dagani haka kada ki karasani yar nan ina yanzun dai komai yazo karshe a wurin ki. Ban daga din ba sai kara shiga jikinta danayi a lokacin bata kara tanka min ba illama tausayina daya kara shiga jikin ta a lokacin. Sun dawo dauke da ledojin abinci a hannayen su tare da abinsha dayan da ban taba tsamanin yana jin hausa bane yake fadin hjy ga abinci oga yace mu kawo maku kuci mu tabbatar da kunci kun koshi kafi mu fita yana magana cike da bada umurni a gareni. Kaiya dan nan wani abinci zamu ci a wanan halin kaimu inda zamu yada kan mu kafin gari ya waye mu kama gaban mu ko yanzu don darene da zance ka kaimu tasha kawai mu shiga motar kaduna zuwa gida. Don nasan idan Allah ya saukemu kaduna lafiya gida ba zaiyi wahala a garemu ba. Umurnin ogane mu sa kuci abincin nan kafi ku kwanta ya fada yana kokarin bude abincin dake gaban mu da sauri yaci gaba da fadin ki taimakemu tsohuwa kuci abincin nan kada mu samu matsala ga aikin mu don Allah. Jin abinda ya fada yasa jikin hjy sanyi ta dago habana tana fadin kinga tashi koba dadi ya zama dole muci abincin nan don wanan mai kiran samudawan yabarmu mu zauna lafiya gidan nan. Abincine irin na gani na fada sai kamshi ke tashi kallon abincin nayi na kawar da kaina daga kallon shi ina kokarin komawa in kwanta. Kinsan duk wanan abin don ki nakeyin shi don haka kada ki bari mu samu matsala dake a wurin nan hjy ta fada batare da ta kalloni ba. Dole na mike na sauko daga sama kujeran zuwa kasan wani kafet mai laushi dake shimfide a falon komai na gidan abin kallone. Jin abinda hjy ta fada yasa na fara kai abincin a bakina a hankali duk da ba komai nake diba ba sosai a spoon din. Bai wuce sau uku ba ina kaiwa a baki sai ga amai na shirin zubo min ganin hakan yasa hjy fadin ki barshi ida bakyaci kada ki jawa kanki wani matsala kuma. Haka yasani tashi daga wurin na koma inda nake kwance da farko na kara nadewa a cikin hijjibin da Allah ya taimakeni na dauko kafin in bar gidan mami din daga shi sai rigar dake jikina kawai na fito dashi gidan da mami tayi min koran kare akan laifin da bani na aikata ba. A can gidan mami kuma bayan fitar mu daga gidan tare da hjy mami ta kasa furta komai ga yaranta sai shiru da tayi tana faman karkada kafafuwanta a hankali. Ita kadai tasan irin yanayin da take ciki a lokacin don yanayin da take jin kanta zuciyar ta zai iya bugawa take a wurin idan tayi yunkurin yin magana a lokacin. Ya mamud ne daya dawo daga rakamu yake fadin mami da baki bar hjy sun tafi ba a cikin daren nan wanan abu bai dace ba mami hjy fa tai fushi dake sosai mami tunda har ta iya sa kafa ta bar gidan nan. Jajjayen idanuwan ta ta dago tana fadi da kyat mamud ya kake son inyi da hajiyan mu a gaban ka akai komai amma kaji irin hukuncin da hjy ta yanke min a karshe. Yau an wayi gari saboda wanan yarinyar mahaifiyata tayi fushi dani haka a rayuwana don kawai, , , , No mami don Allah ki daina fadin don zeey ce hjy tayi wanan don yaya J ne gashi a zaune badon zeey hjy tayi fushi dake ba mami jamal ya fada a cikin bacin rai. Mami kina saurin fushi yanzu wanda hakan bai dace ba idan munyi maki haka ba zaki taba jin dadi ba a rayuwan ki don me zaki bari har wanan zancen ya kaiku haka da hjy . Aurene dai an riga an daurashi a bisa jagorancin kawu hamza da baffa sulaiman da sauran yan uwa da abo, , , , Mamud zaka bace min a wurin nan kafin rayukan ku ya kai ga baci ko sai na saba maku gaba dayan ku wurin nan zaku fice ku bani wuri. Mikewa tayi kokarin sai kafanta ya kasa daukan ta da sauri jalal ya karaso inda yake ya kamata zuwa daki ko kallon inda sauran suke bata kara yi ba. Saida ya kaita daki ya zaunar da ita saman gado tare da tambayan ta ko akwai wani abinda zai mata a lokacin. Kai kawai ta iya girgiza mai ya juya yana kokarin fita daga dakin yaji ta ambaci sunan shi haka yasashi juyowa gare ta. Jalal ta sake fada ina son kai min aikin siri a gidan nan kayi kokarin bincika min inda yayan ku yakai hjy da yarinyar nan. Haka kuma ka saka ido ga duk wani motsi na yayan ku har idan ya bar gidan nan ya fita kamar yadda na haneshi dayi ka fada min. Yace insha Allahu mami zanyi abinda kikace yanzu kuwa zan saka ido ga duk wani motsi nasa Allah yai maka albarka ta fada tana kokarin hawa saman gadon da kyau tare da fadin ka turo min Aisha yanzun nan yace angama mami ya fita. Ya turo mata Aisha shi kuma ya fice wurin dan uwanshi don yasan yana can yana jiranshi don bai ganshi a falo ba inda ya barsu. Yana shiga ya samu jamal kwance rigingine yayi filo da kanshi ba tare da ya dago ya kalli dan uwan ba yake fadin. Yanzu kaine dan leken asirin mami ashe a gidan nan kallon shi jalal yayi da sauri yana fadin yaya akayi ka sanda hakan yana kaiwa zaune gefen shi. Nasan hakan zai faru kowama yasan da hakan ya dago yana fuskantar dan uwan tagwaicin nasa kafin yace dashi. Amma kasan idan ka fadawa mami wani zance kan ya jafar kajawa kanka matsala a gidan nan ko ? Hauka nake da zan fada mata wani abinda zai kara jefata a cikin damuwa komai ba zan fada ba koda kuwa nasan inda suke din . Kaje ya j na kiranka ya fada yana komawa kwance bai tsaya ba ya nufi part din dan uwan nasu. Ya sameshi yana waya don haka ya dakata a wurin har ya kare wayan shi inda ya fahinci dan uwan nasu yana shirin barin kasan a lokacin. A hanku zan bar hjy da yarunyar nan don ni zan koma wurin aikina ina da aiyukan da suke jirana a can ya fada ba tare daya kallo dan uwan nasa ba dake gefen shi. Amma bro in mami ta fahinci hakan zamu shiga cikin fushinta muna don yanzu ta ban assgment a kan ka da inda kuka kai hjy din. Fine yana da kyau ka fada mata ai ban kaisu ko ina ba sai gidana da ba wanda ya sani nan cikin garin abuja . Akwai wani abu kuma ya fada yana dago kai don kallon fuskan jalal din dake tsaye a gefen shi. Zamu kulasu yadda kakw so saidai nasan mami zata saka ido muma a kan mu why not ka wuce da yarinyar nan gaba daya ku bar kasan nan a tare. Ba yanzu ba ya bashi sa yana mikewa zai shige bedroom din shi ya barshi a wurin amma bro in har ma, , , , Ka iya bakin ka ya fada a gagauce ya shige ya barshi wurin tsaye girgiza kai yayi ya fita tare da rufo masa kofa ya bar dakin. Mami kan wanan daren yadda taga safiya haka daren yazo mata don hankalinta a tashe yake har lokacin abinda zuciyar ta ke bata shine nine na jawo komai tsakanin mahaifiyar ta da danta. Taga laifin anty safiya yafi dubu a wanan daren daga baya kuma ta fara hangen nacin jafar ne ya jawo wanan matsalan haka. Don me su baffa zasuyi mata haka har su daurawa danta aure da wata yar aikinta ba tare da sanin ta ba ma,ana dai sun goyi bayan yayi mata rasgin biyayya ke nan ko me ? Idan ko hakane zata nuna masu itace uwa a gareshi ba su ba don wanan auren yadda suka daurashi dolene su warwareshi da kansu kamar yadda sukaje aka daura din. Washe gari haka ta tashi babu karfin jiki a tare da ita har hakan ya jawo mata saukan kasala a jikinta ta kasa fita zuwa office wurin aiki. Kiran da ake mata a waya baya shiga yasa hjy maria nufo gidan mami din tsit ta samu gidan don ranan harsu kande sun shiga hankalinsu a gidan gani irin tashin hankalin da kowa yake cikin sa. Don a gaban su komai ya wakana tsakanina da mami din da kuma hjy da irin hukuncin da hjy ta yanke a karshe wanda hakan ya kara daga masu hankali suna ganin wautar mami din data yarda har hjy tabar gidan dani. A falo mami ta samu bakuwar nata ba tare da an kawo mata komai na motsa baki ba gaban ta wanda da ina gidan da yanzun na gama cika gaban bakuwar mami din da abin motsa baki koda kuwa ba zata taba komai daga ciki ba. Duk da mami na a cikin fushi hakan bai hanata kwalawa sabuwar mai aikin ta kira ba tana tambayan ta dalilin rashin kawowa bakuwar ta ruwa. Tace hjy kiyi hankuri bansan da zuwan ta bane tafi ki ban wuri da wanan magana kina ina har ayi bako baki sani ba meye aikin ki a gidan nan maza ki dauko mata kafin ranki yakai ga baci. Ta juya wurin bakuwar data rike haba tana kallonta da mamakin abinda ke tafe da ita hjy maria kin taso ashe ta fada tana kaiwa zaune. Na taso hjy maryam keda wanan labarin daya karade garin nan ko ince kasan nan baki daya jiya ke kuma ga wayan ki a kashe. Tsuki mami taja tana fadin yaron yanzun aisai ka barshi inda ka ganshi ni yanzu ba zancen shine abin damuwa ba a gareni sai zancen hjy na data sha min yaji kan wanan maganan. Subbahanallahi ta fada da mamaki tare da fadin mama din tayi fushi akan me kuma har hakan ya faru ? Kan dai zancen nan daya fada don me zan dauki mataki hjy tace tare da nuna fushin ta a gareni. Dama abinda yake so ke nan a tsakanin mu ai ya aikata hakan don yasan zata kama mashi ba hjy ba kawai could you imaging wai har da yayana da kanin mahaifinsu yaron nan yabi ta baya suka tsaya mai aka daura mai aure ban sani ba. Kai ki bari don Allah hjy maryam suko don me zasu mana haka yaro da gatan shi ai mashi wanan aure na mumuke kamar mara gata. Mami tace ai sai su san yadda zasuyi su walwale wanan auren don bai dauru ba wallahi indai nina haifi abina. Hakkuri za ayi abi abin a sannu tunda an riga da an daura a yanzu sai dai in wanda zaki maine ya biyo bayan wanan din. Kai ina nerve hakan ba zai yuyu ba ina fada maki ni har yanzu ai ban gama yanke shawara kan zancen ba don uffan bance da shi ba har yanzu. Ranan dai haka kawayen mami sukai ta zuwa gidan wai da sunan zuwa tayata murna jin danta yayi aure ashe basu sani ba kowa dai da irin gulman dake kawo shi gidan. A karshe dai mami tace duk wanda yazo masu gadi suce ta fita wani meeting sai dare zata dawo gidan. Bata ga shi ba kuma bata tambaya ba saima da darene ya mamud ya shigo da likita tana falo a lokacin ya tsaya gaida ita yake fada mata ya dauko likitane ya duba Jafar tun safe yana kwance a dakin shi. Bata tsunka mashi ba balle Allah ya sauwaka har suka shiga suka dubashi suka fito likitan yai mata saida safe. Tana kallon yadda yan uwan shi ke sintiri a part din shi a karshe ma tashi tayi daga falon ta shige dakin ta da zuman ta kwanta ta huta ko zata samu barcin da batayi ba a daren jiyan. Sai kuma ta samu dakin ba a gyare ba taja tsuki da masifa ta nufo waje tana kwalawa hannatu mai aikinta sabuwa kira da dan karfi. Sai gata da sauri tun kan ta karaso mami ke fadin wai ke ko kinsan aikin ki a gidan nan kuwa. Hjy nayi wani laifin ne kuma meya hana ki gyara min daki mami ta fada cike da takaici a fuskan ta a daidai lokacin ne kuma jamal yazo yana fadin. Mami ya J fa baya jin dadi sosai tun safe yau a kwance yake bai kuma ci komai ba har yanzu. Jamal ka ban wuri da wanan shirmen yaje ya kashe kansa idan zai iya indai kan wanan zancen ne ba zan taba yarda ba. Amma mami ai da kin je kin, , , , jamal na fada maka ka kauce min a wurin nan kafin ranka ya baci kaima. Jin hakan jamal din ya wuce a fusace ya nufi part din yayan nashi don ya kara duba halin da yake ciki. Zama tayi a falon tana jiran Hannatu mai aiki ta karasa gyara mata dakin inda ba a dauki dogon lokaci ba hannatun tafito tana fadin hjy na gama. Ta dan dago kai tare da fadin ok kawai ta mike don komawa dakin ta zauna saidai tana sa kai a dakin wani irin arm odor ya daki hancun mami kamar a lokacin hanne ke cikin dakin nata don hamamin warin hammatan dake tashi a dakin. Da sauri mami takai bakin mirrow ta dauki room fresh tana fesawa a dakin a cikin takaici ta aje ta nufi bandakin don ta dan kewaya. Bata saba ganin wurin nata a haka ba yasa bata tsaya jiran komai ba tafito ban dakin baya ta daure ta kewaya a matse. Cikin takaici ta zauna bakin gadon ta tana jan tsuki tare da fadi a fili wanan banyi tsamanin zamu kai ko ina da ita ba. Wanan gyaran daki kamar mahaukaciya ko yaro yana wanan aikin haka tana fada tana karasa shirin kwanciya matawa tayi ta dauko kwalin maganin ta da take sha duk dare kafin ta kwanta barci. Tsuki taja tana bata rai tare da jin wani bakin ciki a ranta take ta fara tunanen wani abu a wurin wanda ya kara bata mata rai maganin dai a ranan mami bata shashi ba haka ta kwanta don kiuyan da takeji zuwa falon . Baku zata iya kiran hanne yar aikinta takawo mata maganin don wani irin tashi da dakin kanyi idan yar aikin nata ta shigo dakin. Mukan tun safe muke saka idon ganin wani daga cikin su yaya bamuga kowa ba hankalin hjy ya tashi don tacewa dayan security din ya kaimu tasha mu shiga motar kaduna.. Yace aiko bakin kofan gidan ba a bashi daman ya barmu mu taka do ance ya kulada mune sosai ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 3️⃣9️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU YAN UW MUSULMAI UBANGIJI YA KARA MUNA IMANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , , Babu wanda yazo wurin mu a gidan har kwana biyu tun hjy na daurewa har ta fara magana a fili ina jinta don ba wani magana nake iyayi ba a lokacin don zunlumin da nake ciki da fargaba. Naji hjy ta fara fadin kamar tana zargin jikokin nata anya kuwa ya yan nan suna da gaskiya kuwa zasu dauko mu su dangwaran a wanan gidan babu wanda ya waigomu a cikin su kaf. Idan an dan jima kuma zakaji tace ni mamuda nafi ganin laifi shi da keda wayau ya barmu a nan zaune ga masu zubin kafirai din nan sun hanamu motsawa nan da can. Da iyanzu ai mun tsufa a gida da wanan zaman bamzan da bamu san dalilin yin shi ba a nan, wa yan nan katan banzan da suka saka gadin mu kamar mun aikata wani mugun abu. Nidai bankan tankata idan tana wanan magana don tsorona Allah tsorona mami da bansa matakin da zata dauka a kaina da iyayyena kamar yadda ta fada ba. Don har yanzu idona yana da kwancin jinin marin da taimin a fuskana yasa idona yai alaman kwancinyan jini ta geden dama. Ga damuwa fara exam dina dake damuna shima don ina ganin nayi hasaran shi ke nan idan ba, Allah ya gyara ba ina da rabo a rayuwa lokacin. Wanan yawan jininin na hjy yake kara tayar min da hankali tare da sakani tsoro da abinda take yawan fadi ko yaushe. Saida mukai kwana hudu cur a gidan ba tare da wani ya lekomu ba ga zaman kamar zaman takura da mukeyi . Iyakan security din nan ya shigo ya tambayemu abinda muke bukata duk daba wani amsa yake samu ba wurin hjy bai hana idan lokacin cin abinci yayi ya dawo garemu yana tambayan abinda muke so a kawo muna. Koda bai samu amsa ba haka zai kawo muna abinci mai rai da lafiya da kuma abin motsa baki wani lokaci. A yammacin kwana na hudune hjy ta sha fada har ta gaji saiga yaya mamud da Jamal sun shigo gidan muna zaune a falo mukaji shigowan su. Da sauri na mike zaune don a kwance nake a lokacin don jikina babu karfi saboda tunanen da yai min yawa a lokacin. Har kasa nake ina gaida su kamar yadda na saba a koda yaushe idan ina gaidasu din a cikin girmamawa. Da sauri na mike don barin falon a lokacin hjy ta dubeni da kyau tana fadin ina zaki kuma ke ? Dan dago kai nayi na kalli hjy tare da fadin zan shiga dakin ne hjy ki tsunci uwarwa a dakin ai yanzu tunda sun tuno damu fitan su fitan mu a gidan nan. Shiru su yaya sukayi sai dan bina da satan kallon tausayi da yakeyi yana kawar da fuskanshi gefe daya hjy dake gefe taci gaba da masifa tana fadin. Haka kawai , daku da uwarku zaku sakamu a gaba haka da wullakanci kamar kun samu marasa daraja da galihu kuna wullakantawa kamar baku san inda muka fito ba. Ko uwar takuce ta hana ku biyoni nan don na mara maku baya kan abinda Allah bai haramta ba take kokarin ita ta haramtashi. Dan murmushi ya mamud ya sake yana neman inda zai kai zaune da kyau tare da fadin korata kike kenan yanzu mu tafi. Ba koranka nake ba ta sake fada gwanin ban tausayi kafinta tace kasan hakan da kukai muna baida kyau mamuda dole raina ya dinga baci. Hjy kinsan lamarin mami saida tako dan haka muka nuna mata muma bamu san inda kuke ba a yanzu haka. Don ta dauka kuna gida samu,naka sai yau da mama Ramatu ta bugo waya take jin bakuje can ba hakan ne ya tayar da hankalinta yau ga baki daya. Kun min daidai yaran nan gara da kuka nuna mata hakan itama dana haifa bata san darajana ba ta barni a cikin dare nabar mata gida. Kada ku yarda ku nuna kusan inda nake wasan dadi sai kun barta ta ji jiki da kyau kafin ku nuna mata inda nake. Ke wanan tsohuwar da mugunta kike yanzun ma da mami ke cikin wani hali bai maki ba sai kin kara fitgita muna ita ke nan . Ja,iri uwarka kake goyon baya ko mai na kasa daurewa daga inda nake zaune haka yasa na mike tsam zuwa dakin da muke kwana da hjy. Gaba dayan su suka bini da kallon tausaya min hjy dake zaune ta nisa tare da fadin ina shi jafarin yanzun ? Yana gida baida lafiya ne aida kun ganshi nan tun ranan ya mamud ya fada yana mikewa tsaye tare da fadin . Yanzu ma shiya turomu muyi maki bayani don kada kiji mu shiru don baida lafiya sosai yace a gaida ke a tambaye ki idan ba wani matsala a tare daku. Ko kuma idan wanan gidan bai maku ba a canza maku wani ya fada kai wanan shike kara saka kuna shagala da duniya diyan nan. Wanan gidan ko a fina finan zamani ina na taba ganin irin shi da zai wani ce idan bai muna ba a canza muna wani. Fada mai ni ba wanan ne yanzu a gabana ba canjin gida ko wani abu kawai ina son in koma dakin mijinane albshin shi yazo ya dauki matarshi ya san inda zai nufa da ita kuma . Don dai yar nan ba zata koma gidan iyami da zama ba har abada indai da sunan irin wanan zama na wullakancin nan da tayi a yanzu. Shima ai ba zai taba hakan ba hjy yanzu damuwan shi shine da wanda yarinyar nan zata zauna a karshe a gidan nan don ta karasa karatunta kafin ya bar kasan nan da ita. Hjy bata iya ma ya mamud magana ba sai wani kallo data watsa mai kafin tace au ashe shi ba zancen mayar da yar nan hannun iyayyen ta yake a yanzu ba ? Don Allah hjy ki bar wanan zancen kedai yanzu munzo muji zaki zauna a nan tare da yarinyar nan nadan wani lokaci ko gida samunaka zaki koma a nemo muna wace zata kula da ita. Jikin hjy gaba daya yayi sanyi lokaci guda ta fara fadi a hankali yanzu yar nan idan na tafi na barta a haka yadda take tsorancen nan anya ba zata fada wani hali ba nan gaba don ko yanzu a firgice yar nan take nan. Goshi ya dafe kafin yace hjy mami ta kafe shima jafar ya kafe da nashi kudirin wanda kowan su yana da nasa manufa a nan. Zama hjy ta gyara a cikin mutuwan jiki ta fuskanci ya mamud tare da kura mai ido tana fadin mamuda ka hango abinda na hango gun dan uwan ka ke nan ? Wanda uwarku ta kasa zama ta natsu ta gane me yake nufi da kakaman shi a kullun kan wanan yarinyar don ni har gobe zuciyata ta kasa sakewa da wanan zancen. Don girman Allah idan akwai wani abinda kasani a game da dan uwanka ka fada muna mu sani tun yanzu. Ina mara masa bayane ga kudirin sa don samawa kanmu mafitan da yake fada a kullun daga bakin shi kada idanuwan mu su rufe akan kudi daga baya muzo aji kunya. Hjy abinda nake fadawa mami ke nan amma mami ta rufe idon ta gaba daya da za,a barni sai ince an canza mana mami din mune yanzu. Murmushin manya hjy tayi tare da fadin yaro yarone itace dai iyamin ba wanda ya canza maku uwarku, sherin mulkine da lokaci ke rudin rayuwan ta ya aiki a kanta yanzu. Sun dan dade zaune da ita suna mata bayani yadda zata fahince su a karshe dai suka yanke shawaran daya dace akaina da kuma hjy din. Sun dawo gida sun samu mami zaune a falo suna shigowa mami ke fadin mamud anya ba boye min kukeyi ba kusan inda hajiyan mu ta shiga kuke boye min haka ? Mami anbicika yarinyar ma bata gidan su ne ya tambaya kamar mai son jin amsa a lokacin. Ni rashin sanin inda take bai dameni ba yanzu inda mahaifiyata take shine damuwana a yanzu mami ta fada cikin kunnan rai. Mami ba saidana fada maki ba a ranan kinsan hjy sarai da rigima wai ita ta waye yanzu gashi tana shirin ballowa mutane aiki yanzu. Jamal ka fice ka ban wuri kafin ranka ya baci a nan mami kyaleshi hjy ba zata bata ba a cikin garin nan ai insha Allahu. Ta juya tana basu baya a cikin damuwa satan kallon juana sukayi kafin ya mamud ya mike yana fadin barin leka part dina in fito mami. Har ya fara takawa yaji muryan mami ta tana fadin shi jafar din har yanzu yana kwance ne wai yake nufi ? Mami yau fa saida dr Smith yazo har gidan nan ya dubashi jin bata furta komai ba yasa ya fara tafiya don barin gurin nata sai yaji tace me yace yana damun sa da yazo. Jin abinda ta fada yasa shi juyowa gareta ya fasa tafiyan da yakeyi a lokacin yana fadin mami ba wani abu sukace ba ai su hudune da abokan aikin shi suka shigo dayan ke fadin ya saka wani abu a ransa sosai ne ya jawo mai hakan. Baki mami ta tabe kafin tace idan ya halaka kansa akan wanan diyar tallakawan shiya sani don dai a karshe shizaiji kunya akan wanan yar har yake wanan shegantakun haka. Dan murmushin takaici dan uwan ya sake daga haka ya juya ya fice zuwa part din su bai nufi wuri shi ba saida ya biya ya gaida jafar din wanda a lokacin ya dan ji saukin jikin yana zaune a saman dogon kujera a mike kafa. Jikin shi na saye da jallaniyan maza sai bakin dogon wando dake kafan shi sai fararen santala, santalan kafanshi da suke a mike yana dan karkakadawa a hankali. Jin shigowan mutum a dakin yasashi dan juyowa yana kallon kofan tare da sauke idanunshi kan dan uwan nasa daya shigo. Har kun dawo ke na ya fada a cikin wani yanayi mai nuna alaman yana dan jin jikin shi har lokacin. Mun dawo ina tare da mami a falo tun dazun ya mamud ya fada yana kaiwa zaune tare da kallon dan uwan nasa kafin yace dashi kun zauna da hjyn dai ko ? Hjy ko yar rigima mun zauna saidai ta kafe akan lalai sai su tafi har gurin iyayyen yarinyar nan zainab sun zauna dasu kafin ta dawo nan ta zauna da ita ko kuma a turo wani ya zauna tareda ita din. Saidai ita ta tafi ta barta nan don ba zan so tayi missing din exam din ta ba a yanzu bana son tayin kukan hakan akaina ya fada yana yamutsa fuska. Yau zan je gidan da dare idan naji sauki da sauri ya mamud ya dago kai ya kalleshi tare da fadin kasan duk wani motsi mami ta saka muna matakan tsaro ko dazun da dabara muka kai gidan ai. Baida matsala don ni a yanzu ko mami ta sani ba matsala bane a gareni yanzu don kawai kace mu fito mata ta wanan hanyar. Kasan mami yanzu sai a hankali lamarinta zan daiso mu bita a sannu din ya mamud ya fada yana mikewa tsaye. Bai samu zuwa gidan ba kamar yadda yacewa ya mamud sai kashegari ne da ya kasance weekend ya fito zuwa don fita . A falo ya samu yan uwan shi tare da mami ya fito cikin shirin shi tsab ya nufo inda suke zaune ya zauna a tsakiyan mami da Aisha yana dan jingina jikin shi a jikin mami din . Cikin rashin ko in kula abinda ke faruwa a tsakanin su da mahaifiyar nasa normal kamar yadda suka saba a tsakanin su. Daga haka kowa na fira ya ja bakin shi yai shiru lokaci guda sai Aisha dake zaune a kusa dashi takura mai ido cikin tausayin yanayin shi take fadin. Ya J jiki yai sauki ke nan sai ina kuma yanzu ta fada a cikin zolaya sai taga bama sauraren ta yakeyi ba a lokcin. Aisha tayi masa kuri da idanuwa tana kallon shi sai tausayinshi ya kamata lokaci guda ta sake fadin ya J ko jikinne har yanzu you look so warried. Shiru bataga ya motsaba hakan ya tabbatar mata cewa yayi zurfi a cikin tunane gyara zama tayi a cikin kulawa a gareshi ta kara ambatar sunan shi da ya J ya akayine wai ? Yayi firgigit ya dawo cikin hayacin sa tare da sake mata takaitaccen murmushi a fuskan shi cikin dan basarwa ya fuskamceta yana fadin. Aisha ina tunanen tafiyanane ga kuma yarinyar nan zata fara zana exam a cikin kwanakin nan. Da sauri Aisha ta dan saci kallon mami dake zaune a gefen su kafintace ya j wace yarinyar kake magana ? Yace wife dina ko akwai wata da zanyi zancen ta haka a gaban ku bayan ita kin sani kin san ba wanan a gabana ai Aisha. Da sauri Aisha ta dukar dakai kasa a daidai lokacin da yake mikewa tsaye yana fadin zan fita daga can zan leka asibiti in dubasu. Aisha najin abinda yayan nata ya fada tayi saurin dago kai ta kalleshi da mamaki take girgiza kai tana kallon shi tare da fadin. Amma ya j ka tafka babban kuskure da har ka daurawa kanka aure da wanan yarinyar da tsiya ya saka iyayyen ta sakota shigowa duniya don neman kudi. A fusace ya juyo yana fadin shut up Aisha enough enough what ever she is, now she is free from that. Idan ba zaki taimaka ki samo min mafita akan zainab ba to ki ja bakin ki kiyi shiru da maganan matana a gabana haka. Kar ki manta she is part of us now don ta zama daya daga cikin mu ke nan kamar kowa wani kallo mami ke jefa mai kamar an hanata magana a lokacin. Ba wai wani abu bane ko tunane mami keyi tsaban mamakine kawai daya rufeta a lokacin ya hanata nagana don gaba daya sai take ganin yanayin shi ya sauyawa sanin ta a yanzu. Itako Aisha sai kai take girgiza mai tana fadin ya j kada ka tafka babban kuskure kazo daga baya kana daka sanin hakan da kayi. Don tallaka ka barshi yanzu inda ka ganshi da tsiyar shi shine mami ke maka nufi ba komai ba ya J a matsayina na kanwarka ina mai baka shawara domin mami ba zata taba yarda da ita a matsayin daughter inlaw din ta ba tunda tasan asalin ta tun farko. Waike Aisha ba zaki kamawa mutane baki ba a nan ke meye naki a cikin zancen nan manya na magana ki dinga saka masu baki haka. Har ya fice falon mami sai faman tunane take akwai wani abinda ke damun dan nata domin gaba daya shi yanayinsa ya canza mata. Babu alaman jin nauyin ta a idon shi ko bin zabin ra,ayinta kamar yadda ya saba nuna mata a baya don zata rantsewa da cewa yafi ko wani yaro mata biyayya a cikin yayanta kaf. Duk maganganun da yayi a lokacin bai daga mata hankali ba sai bakon yanayin data fara hangowa a tare da dan nata ne hankalin ta ya fara tashi da hakan. Ta shiga sake sake a kasan zuciyar ta ya zama dole gateta ta fuskacin danta tasa yanayin da yake ciki har ma idan asirine ta san wani irine aka jefoshi dashi. Don tasan matakin da zata dauka kafin dan nata ya kaiga shiga wani hali bata farga ba do zuciyar ts na raya mata jafar din yanayjn sa y canza ga baki daya a dan kwanakin nan. Ina zaune na rafka uban tagumi sai hjy dake sallah a gefe naji an turo kofan shigowa falon da muke din. Jin haka yasa ni saurin dago kai don ganin wanda ya shigo falon duk da dai nasan mazan nan ne dake faman dawainiya damu tun zuwan mu gidan basu huta ba. Saidai kuma dago kan nawa yayi daidai da shigowan ya jafar din falon da daddadiyan muryan shi da yake sallama daga inda yaja ya tsaya tsaye fuskan shi a gurina kai tsaye. Sallaman na amsa a daidai lokacin da yake lumshe idon shi a cikin wani irin yanayi kafin ya bude yana mai takowa zuwa in da muke zaune. Kaina na sada kasa cikin sauri a daidai lokacin da hjy ta shafa tana fadin yau a gidan duk da ina cikin fishi daku har uwar taku. Ya karaso inda take yana murmushi mai hade da sautin dariya yana fadin a yafe muna nima hankalina yana gurin ki ga baki daya wallahi. Sai daya zauna suka fara gaisawa dashi yana tambayan ta ya zama kadaici ya kuma hakkuri da abinda ke faruwa. Tace duk suna nan tanayi saidai zaman ne gaskiya guri daya ya isheta hakana gara ta koma gida dakin ta ta zauna a can zaifi mata sauki. Ya juyo a rikice yana fadin meya faru ne ko security din dake kula damune sukai mana wani abinda bai dace? ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣0️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GA YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI YA KARA MUNA IMANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , , Yadda na zauna na makure kamar ban falon a lokacin don yadda nasha jinin jikina tun bayan shigowan shi falon. A hankali ya dago kai ya dan kalli gefen danake kafin ya bude baki a hankali yace ya kike cikin nuna basarwa yai maganan ta hanyar daukan remote yana kunna tv dake kashe baya aikin. Ban iya bashi amsa ba don tambayan daya jefo min yai min nauyi a lokacin sosai. Saida ya kunna tv yakai tashan da yake so ya sake juyowa inda nake zaune a takure yana fadin ya naji kinyi shiru koda wani matsalane kuma ? Hjy ce tayi karfin halin bashi amsa tare da fadin ba dole ba matsala dai yafi wanan ka kawomu nan ka aje kamar wasu marasa galihu haka. Balle wanan yar bata tare da wani matsala tunda tana tare dani a yanzu ai murmushi zancen ta yayi yana gyara zama yace. Nagode hjy nagode da nuna kaunar ki garemu da ba don ke ba da komai baizo a sauwake haka ba yanzu. Sai da hjy na rasa meke damun mami har yanzu mami taki ta amince min aka ra,ayina, a rude na dan dago kai na dubeshi don jin abinda yake fadi a lokacin. Hjy naji tana fadin ka barta da kanta zata gane gaskiya ta biyo hanya don kanta amma gaba dayan ku saikun daure sai dai kafin hakan nafi tausayin wanan yar da ake nunawa hakan a yanzu. Na sake wani irin ajiyan zuciya da bansan fitowan shiba lokaci guda ina mayar da kaina saman kujeran da nake zaune. Daga hjy har shi lokaci guda suka juyo suna kallona sai shine ke fadin me ya faru zainab yanzu kuma ? Jin an ambaci sunana yasani dan dago kai daga yadda nake a zaune ina a hankali nace ba komai idanuwana suna kokari sako da hawaye lokaci guda. Idan da son samu ne ka bari muje in gana da iyayyen yarinyar nan ko hankalinta zai kwanta don yanzu gaba daya hankalinta ba akwance yake ba da kowa a nan. Idan hakan zai kwantar mata da hankali sai a shirya tafiyan ku hjy indai haka ba zai shafi karatun ta ba da zasu fara jerabawan su nan da mako mai zuwa insha Allah. Ba matsalan komai ai itama da alama bata wasa da karatun ta don duk wanan halin da take ciki bai hanata karatun nake gani ko yaushe tana rike da littafin karatun naku. Muryan shi na sake jin yana fadin zan koma hjy zuwa gobe an gama maku shirin tafiya in Allah ya yarda sai zuwa gobe da dareb zan shigo insha Allah. Kaji namijin gaske haka nake son mutum da saukin hali ko yaushe ba irin uwarka da ta kasa gane hakan ba har yanzu. Oh hjy kina akawa mamina ido da yawa har na fara jin kosawan hakan a yanzu acikin alaman mamaki hjy ta katseshi da fadin Allah ko ? To da kaida uwar taku duk saina juya maku baya muga ta tsiya a yanzu kuma . Yana dariya ya mike tsaye tare da fadin ko zaki daina sai bayan kin gama min aikina sai ki juya muna bayan ba matsala a lokacin . Amma a yanzu sarkin yaki idan kika ce kin juya min baya ai ban san ta inda zan fara kamawa ba a nan. Tashi ki takawa mijin ki mana kina zaune wuri daya haka hjy ta fada tana jifana da harara a take annurina ya kara gushewa lokaci guda na hade fuskana ga baki daya. Bazaki tashi bane a hakan har zaki kai ga yadda ake so kina wanan sanyin jikin haka da wanan yawan matan dake dakon shi kamar dan sarkin das. Simi simi na tashi tare da daukan hijjab dina na saka akaina na fice a falon cikin sanyin jiki nabi bayan sa kamar yadda hjy ta umurceni dayi din. Ban san da tsayin shi gaf da kofan ba, saida na iso gurin ne nakusa cin karo dashi a guri yana tsaye ya dafe kofan falon da hannu daya dayan yana waya dashi. Da sauri na dan ja baya tare da fadin yi hakkuri bansan kana nan ba a tsaye maimakon ya amsa min sai idanuwan shi manyattatu daya watsa min lokaci daya kafin ya saki wani shu,umin murmushin da bai kai ciki ba yana fadin. Kai na kawar gefe daya ina bata rai tare da turo baki gaba saboda neman hanyan da zan samu kawai nake in fita daga kangin shi ga baki daya. Madadin inga fuskanshi ya sauya ga abinda nayi mai rashi ya baci sai kawai naga yana min murmushi kamar ba jafar din dake da aji da class mai yawa haka ba yanzu a gabana. Hakan dana gani yasa a cikin dakewa nayi kokarin juyawa ina fadin dama hjy ce tace wai na biyoka nayima saida safe wai ina fadi har na juya na fara tafiya do barin wurin. Muryan shi na tsin kayo yana fadin ashe da badan ita ba baki san ki zo ki sallami mijin ki ba haka zamuyi dake idan mun tare a gidan mu. Ko irin tarbiyan da kika koya ke nan a yanzu baki san ki girmama na gaban ki ba kuma baki san tarbiyan ki na daga cikin abinda nakeso ba fiye da komai. Kalaman da yake fadi suka saka jikina sanyi a lokaci guda har ba kasa aiwatar da dan shirin dana kulla a zuciyana kan nayi mai rasgin mutunci ko zai rabu dani gaba daya a rayuwana. Sai gashi ya buge ga yabona wanda naji dadin hakan a raina don kowa ba son a yabeshi a rayuwan shi. Sai dai duk da hakan na dan turza dan zuciyana ta ban kwarin gwiwan fada mai magana nace ya Jafar. Don Allah kaji tsoron Allah ka rabu da rayuwana a yadda ka ganni kowa yasan ni ba yar kowa bace ban taba tunanen irin kalaman da mami suke jifana dashi ba a yanzu. Sai gashi a sanadin wani bukatan ka a kaina yakai mami tana aibantani tana aibantamin iyayyena da basuci ba basu sha ba a ka wanan magana. Kasa nakai gwiwa bibiyu a kasan tare da hada hannayena biyu guri daya ina fadin ya jafar na rokeka da kafita harkata kabar rayuwana ya samu sallama. Yau sanadin ka mami ta koreni gidan ta tayi min kazafi kala kala dani da iyayyena a gaban kowa har sai yaushe kake son kaiwa ga fita a cikin rayuwata hakane ? Duk wanda ya ganmu a yanzu haka yasan bamu dace ba don ruwa ba sa,an kwando bane ansan ni din ba ajin ka bane sai dai idan da gaske yadda nakejin ana fada da wata manufa kake son yaudarana. Kamar yadda mami suke fada kowa yasan kaiba tsaran aurena bane yaya tsadadden namiji kamar ka sai mace mai irin ajin ku bani zainab yar matsiyata ba haka don Allah ya jafar ko wani irin manufane a zuciyar ka katai makeni kabawa mahaifiyata ni kada in halaka. Hjy kaka ita kadai ce mai kaunata tsakani da Allah gaba dayan ku yaran mami a yanzu ban yarda da kowa ba a cikin ku ina maijin wani kunci da bakin cikin a zuciyana saboda abinda ake min a gidan mami. Wanda hakan ya kara nuna min banda gata da daraja dama a idon kowa wanda hakan ke kara haifan min da kunci da bakin ciki duk a sanadiyan halin daka jefani a ciki. Jin nayi shiru don kukan daya zomin a lokaci guda yana tsaye a inda yake kamar an dasa shi a wurin yana tsaye yai kasake idanuwan shi a kaina sai zuba hawaye nakeyi a inda nake tsugune na hada hannayena wuri daya alaman ina rokon shi. Tunane barkatai yake a gurin da yake tsayen ya zuba min idanuwa a lokaci guda ya na kallon yadda nake magana cikin fitan hayaci a tare dani ya rasa lalubo mafita yadda zai haneni fadin abinda nake fadi a lokacin. A hankali ya fara takawa don barin wurin ba tare da ya iya furta komai gareni don bai san amsan da zai iya ban ba a lokacin yasa ya zabi yabar wurin kawai zaifi mai saukin sauraren kalamina a lokacin. Duk da bashi ke tuka motan ba haka bai hanashi jin wani iri ba a lokacin don ji yake damuwan shi na kara shiga damuwa a lokacin gareshi. Motar na tsaya ya fito bai tsaya jiran a bude mai motar ba ya diro daga baya motar ya nufi hanyar shiga cikin gidan. Wayanshi ce ta dauki kara ya tsaya ya duba ya mamud ne ya gani a layi bai tsaya jiran komai ba yake fadin Kana ina gani nazo gidan ka wurin su hjy ban sameka a nan ba ya fada yace gani na dawo gida yanzu na barcan din na zo gida. Kada ka shiga ka jirani a waje ka ban mimtuna kalilan gani tafe insha Allah ya mamud ya fada ya amsa da OK sai kazo. Daga haka ya mayar da jikin shi gurin motar daya fito ya jingjna jikin shi a kai tare da tunanen dalilin dakatar dashi da dan uwan nasa yayi waje. Kodana koma ciki hjy tana zaune a inda na barta tayi min kallo daya ta kawar da kanta gareni nasan hakan bai rasa nasaba da shigowan da nayi ina sharan hawaye a fuskana lokacin. Don irin yadda ta kalloni din yasa na sake shan jinin jikina din tare da samun wuri na rakube kamar wata marainiya dani. Ban dago kai ga kallon ta ba sai faman dan share fuska da nake lokaci lokaci na tsinkayo muryanta tana fadin. Yarinya kin takurawa rayuwanki kin hana kanki kin hana rayuwa ki shakat babu farin ciki kullun sai tsangwama sai tashin hankali. Shima da yake namiji kuma ya dauki duk wani laifi ya hada a kanshi shi kadai bai tayarwa kanshi da hankali haka ba kamar ke. Mikewa nayi ba tare da nayi magana ba na nufi dakin da muke kwana a cikin sa na daura alwala tare da gabatar da sallah isha,i na kwanta. Ita hjy a nata tsamanin fushi nake don kawai in koma hannun mami da zama ko wani abu can a nata fahintar ta kasa gano inda na dosa da wanan damuwan da nake saka kaina a ciki. Don a tunanen ta ai hutu na samu na rayuwa ga hakan don ta dauka nasan koshi din waye da matsayin da yake dashi a lokacin. Ban kara fita falon ko neman abinda zanci haka na kwanta sai da asuba ba falka koshi itace dai da bata fushi ta tayar dani daga barcin. Bayan na idar da sallah ne naji muryan hjy na fadin idan kin sallame kije falo akwwi sakon ki a can yai min nauyi ne naga gara dai na barshi falon harda safe. Ban damu da nasan ko sakon may ba don ni gaba daya yanzu kowa ma haushin sa nake ji idan mutum ya shafi bangaren mami din. Taci gaba da fadin yanzu sun canza magana wai yau din nan zamu bar garin nan karfe bakwai na safe don haka ki tasho ki fara shirin tafiya ta kare da bani umurni. Dan juyawa nayi na kalli bangaren da take zaune ina mamaki a raina yadda kowa ke juyamu yadda yaga dama tun yanzu na fara fuskantan abinda ke gabana gaskiya talauci wani abin kine a rayuwa don zance talauci ne ya jawo min wanan gararan ba da walagigin rayuwa tsakanin mami da ahalin ta a yanzu. Badan naso ba namike don zuwa falo saboda abinda hjyn ta fada a karshe da cewa wata kila akwai wani fitinane kuma daga wurin uwar tasu yasa suka sauya ranan tafiyantamu. Nima zan fi so ai mu tafi yau hjy na matsu in bude idona in ganni a gaban iyayyena hakana . Au ashe ni ke nawa haukan ke nan yar nan ina ce ai yanzu daga gidan nan sai dakina zamu dira idan mun tashi nan. Ban yarda na juyowa ba a lokavin don jin abinda ta fada din don bansan amsan da zan bata ba kuma idan har na tsaya din don tsohuwar ta cancanci kawaici sosai a wurina. Akwatinane har uku a tsakiyan falon da sauran tarkace da ban san meye a cikin su ba tsaye nayi daga kofa kamar mai nazarin kayan a lokaci sai da murya hjy din ya dawo dani hankalina da sauri na dan zabura tare da kaucewa a hanyan da nake tsaye. Karaso man ki gani ta fada tana kaiwa zaine a saman kujera ga carbi a hannun ta tana ja tace jiya kin kwanta yaron nan jamal ya shigo da kayan nan . Tare da bayanin yau karfe bakwai na safe mu zauna a shirye kafin su shigo ban daga a wurin ba kuma banda niyar hakan . Kina tsaye kimkam dake a wuri daya ki zauna in maki bayanin komai kamar yadda sukai min kan kayan. Hjy ba sai na ji komai ni kawai a mayar dani gida ko zan daina jin abinda nakeji a zuciyana. Af kinsan Allah idan kin mun tsiya yanzun nan zan saka a fasa tafiyan nan ga baki daya, da sauri na dago ido na dan kalle ta sai kuma abin ya dan ban dariya nake fadin . Hjy ba haka nake nufi ba ai kawai dai na fadi hakan ne don ki ce wani abu gashi ko kin fada din tace yo dama ai nasan don ni kika fada ai. Don shi jafarin baya laifi a gurin ki sai ni da kika raina yar nema kikewa shegan taka irin haka ko ? Kinga maza dauki kayan na kije ki saka idan kinyi wanka donni nan da kika ganni a shirye nake ko yanzu suka shigo gidan nan na gama shirina tsab. Kallon ta nayi da mamaki a fuskana kamar zanyi magana don dai ni kan bana son in taba komai a cikin kayansu karshe mami tazo tai min gori tunda ma yan kayan dana tara a gidan ta bata yarda nabar gida da ko tsunketa ba . Haka na fito tsula sai dan jakkar littatafaina da nayi karfin halin daukowa a lokacin don ba zan taba yarda in zubar da karatuna ba a duk halin dana samu kaina a ciki. Sallaman da akayi a kofan dakin ne yasa mu dago kai don amsawa da sauri naja baya ina gaida shi yace zeey baki shirya ba ke nan yanzu ya J ya umurce ni daga massallaci in nufo nan nakaiku airport direct. Yanzu nan zancen da nake mata ke nan maza dauki wanan jakkan ki shirya a gurguje bamu da lokaci hjy ta fada . Ba musu na dan dauki jakkan data nuna min zuwa ciki ban tsaya ba wanka na shiga agurguje din da tace na fito. Sai lokacin na bude jakkan dake makare da kaya nau,i, nau,i na mata da sauri najawo wani jan material dake sama ko tsayawa dubawa ban yi ba. Sai danake sakawane na fahinci tsadan kayan a lokacin tsab na shirya a lokaci na fito na samu suna magana kuskus da jikan nata saidai gaba daya yanayinta ya sauya lokaci guda. Kalma daya naji shine tace ai gara ayita ta kare yau din a gaban iyayyen yarinyar nan tunda ba lalama take so ba ita. Jikina yai sanyi a hankali na tako zuwa inda suke hjy ta kalloni tana fadin kinbar kayan a ciki ne kuma don yanzu tafita zamuyi daga nan ba zancen karyawa a nan kuma. Zan mike ya jamal yace barshi na dauko da kaina ya mike ya shiga dakin bai jima ba sai gashi da dan troler din hade da school bag dina dana bari a ciki. Babu wani alama daya bari na shedan mun zauna a gidan kafin mu bar gidan zuwa airport ba bata lokaci jirgin mu ya daga, don mun so makara zuwa wurin. Baifi yan mintina ba ni a ganina sai gamu kaduna har jirgi ya diremu ko ga motoci sunzo daukan mu a filin jirgin . Nikan ina biye da hjy a bayan ta sai ya jamal dake directing din mu akan komai motan bai tsaya damu ba sai Anchau. Abin kamar a mafalki nake ganin shi son tafiya sai yake min sauri kamar masu tafiya a gajimare ba a mota ba. Ba farga a garin mu nake ba sai lokacinda aka karya kwanan unguwar mu abin ya ban mamaki matuka sai kawai gamu a gaban gidan mu. Mota biyu mukai amfani dashi a tafiyan ina kokatin fita daga motan don zumudi naji hjy na fadin ki bi a sannu ki tuna kina da aure a yanzu din. Don haka ki natsu sosai ki tuna ko a nan din kina da makiya tare da mahasda da zasu so suga faduwan ki don haka sai ki natsu kiwa kanki fada da kamun kai ki fara nuna yanzu ba da bane garesu. Hakan yasa naji wani iri n natsuwa yazo min lokaci guda na tuna da abinda na bari a gidan namu tun farko don haka har gyalen jikina saida na gyara yafashi kagin a bude muna mota don mu fito a lokavin dirin motar yaja hamkalin kannena sun fito don ganin ko waye yazo. Sannu a hankali aka bude kofan daga waje a bangaren da hjy take zaune kafinta ta fito a hankali ta sauka daga motar. Driver ya dawo bangaren da nake zaune ya bude min kofan a hankali na dan dauki lokaci kafin in sako kafana a kasa na sauke su a cikin kasan kofan gidan namu. Kyau ta kalman dake kafana kawai ya isa daukan hankalin wanda ke gurin a lokacin na karasa fitowa waje ina dan gyara gyalen kaina da kyau a hankali. Duk yadda zan kwatanta maku haduwa a lokacin ba zaki gane yadda shigan ya mayar dani ba sai dai idan kin gani a gaban idon ki. Takalma iri hill shoes din nan ne fari sol a kafata sai madaurin sarka fari da yake dashi. Dinkin material din dake jikina mai kama da half gown sai ta kasan shi akai ado da wani yadi mai kama da lace mai kore da baki a jikin shi. Hannun rigan yana da dan shara sharan hannaye har zuwa kasan hannun. Hjy ce gaba ina daga bayan ta rike da yar karamar jakka mai kama da post a hannuna shige guda da takalmin kafana ina takowa a hankali. Ga kannena ina gani kamar in shaka in rugume su sai dai ina ganin irin kallon basu gane mai shigowan ba da suke min a lokacin. Sai da muka karaso gaban sa,ade a hankali na bude baki kamar ban son magana tare da fadin haka aka koya maki taron baki. Wani ihu ta yanka tare da fadin wallahi yayan muce ta kwasa cikin gida da guda tabar kayan da take suyan awara a kofan gida. Ihun tane ya jawo hankalin kowa a gidan yayi daidai da Abban mu na gida dakin lantana a lokacin duk da misalin sha biyun rana ne lokaci ya nuna a garin. Abin mamaki sai ga innan mu a guje don ranan bata nuna wanan kawaicin ba nata da take nunawa a kaina na yar farin ta. Saidai gani tare da hjy yasa taja ta tsaya kuma da dan tsohon cikin ta da ya fara baiyana a lokacin a jikinta. Nikan ganin inna taja baya ta tsaya don ganin tsohuwar mai kamala da muke tare yasa na kasa daurewa na nufi wurun inna a cikin sarsarfa na rugumeta. Ina jin wani farin ciki da shaukin ganin mahaifiyata da nayi yau sai nake jin kamar anyayye min duk wani matsalolin da nake ciki a lokacin don ganin mahaifiyana a gabana. Wai abune kowa nake gani haka a idona Asabe ke fadi daga bayan mu ta fito daga dan lungunta ds yanzu duk ya gama yakucewa ba gyara kamar farko da Abban mu ke yawan gyara mata idan ya dauko lalacewa. Itace fa Asabe sa,adaty ta cabe tana fadin yau Allah ya dawo muna da yar uwan mu gida yan bakin ciki yau kan sai dai su mutu ko a kasa barci don bakin ciki. Masu farin ciki kuwa yau barci harda nasari don Allah ya baiya na gaskiyan shi a filin Allah kowa ya gani. Daga inda hjy take ta amsa da fadin kwarai yar nan dama haka al,amarin Allah yake ai idan ya tashi ikon shi ba wanda ya isa ya hana hakan. Yau ga yar ku ta dawo gare ku a matsayin matan jikana al,amarin aure daga Allah yake matar mutum kabarim sa. Da sauri Asabe tace balle munan ai kowa dan farin cikine da hakan ai hjy kayya hjy ta fada a daiyi sha,ani ai da ba haka akaso gani ga jikan nawa ba. ZAINAB IDRIS MAkAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣1️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE YAR UWA DON GIRMAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA , IDAN KIN SAN DARAJAN ALLAH, , , DOMIN BIYA ZAKI IYA TURA KUDI TA WANAN LAYIN BAKIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI TURA KATIN WAYA NAGODE, , , , Bayan an zauna an natsu a dakin inna ina sai yan dabarun mata takewa hjy don taron ta duk da bata san ko wacece hjyn ba a lokacin. Saidai cikar ido irin na hjy da kamala yasa kwarjinta ya dauki hankalin ko wa a gidan sai ga Asabe ta dawo tana fadin . Sannun ku dai da zuwa ta kara fada tana kokarin shigowa daga cikin dakin takai gurfane. Kaga Asabe do kinga yayar mu tazo da kama mai kyau har kina wani rawan jiki da zuwan ta a yanzu. Duka inna takaiwa sa,adatu da bayan hannu tayi saurin gwaucewa tare da mikewa tsaye tana ja da baya don barin wurin tana magana ciki ciki. Asabe na fadin rabu da ita sa,adatu ba hankali gareta ba ai koma me ye ai wanan zancan baya ne kike daukowa. Duk abinda ke faruwa hjy na zaune ta lura da komai daga inda nake zaune ina mamakin yadda sa,adatu takewa asabe a yanzu. Kamar ba Asaben da ko muryan ta mukaji a sa can baya sai gaban mu ya fadi don masifa da irin matsawa innar mu da sukeyi lokaci. Amma sai gashi yanzu na dawo na samu suna mata abinda sukaga dama a gidan. Haba dai sa,adatu ki daina haka mana na fada ina kallon ta don naga ran innan mu ya baci sosai a lokacin. Kinga kawata yaki zonan ki kyale su naga sun taru a kanki ke kadai haka hjy ta fada tana mikawa sa,adatu hannu tazo wurinta. A lokacin ne Asabe ke fadin ita wanan din ne hjy da kike aiki a gidan ta ko waye ita din tana kallona. Kafin na bata amsa hjy tace a, a , aha nidin dai kakar mijin tane nice na haifi uwar mijin nata don haka ita din matar jikana ne yanzu. Ikon Allah asabe ta fada sai mukaji zancen aure kamar a mafalki daga sama ba tare da wani sanarwa ba kawai. Ai kin san aure habo ne shi idan lokacin yinsa yayi koda shiri ko ba shiri ranan sai anyi shi Allah ya nufa matar shice shima. Har hakan ya faru da yar nan yarinyar arziki yar kirki aka dauketa aka mika a birni ba tare da an taba bin sawun wanan yar ba anga a inda take zaune ba. Sai gashi ubangiji ya tarfawa garin ta nono ta shigo birni da kafar dama tayi gamo da arzikinta taci kuci har wani nata shima ya raba yaci ya huta a karkashin innuwar ta a yanzu. Wani kuka Asabe ta sake daga gefen da take gurfane tana fadin yar nan naso cutan kaina da kaina da badan Allah ya gyara ba ki fada hannu na gari wa yasan hannun da zaki fada haka. Na aikata abu a cikon duhun kai nabi zugin da ya jawo min zagi da zunde a gari kan na sayar dake a hannun yan birni. Har zaure mai gari muke da iyayyen ki saida nayi rantsuwa akan ba sayar dake nayi ba a garin nan. Allah da ikon shi an gama kulla min wanan sherin da kwana biyune zancen auren kin nan yazo muna garin nan a cikin bazata. Wanda hakan kuma ya kara jawo muna kace nace a cikin garin nan wanda har yanzu mutane a kanshi suke wai ba a san mutum ba an dauki yarinya an bashi don kwadai. Cike da takaici nake sauraren abinda Asaben ke fadi na rasa abinda ke mun dadi sai hawayen dake zubo min a lokacin a raina nace ni haka rayuwana zai kasance da barnan suna. Wanan wace irin kaddaran rayuwace Allah ya jefoni a cikin sa don kawai ina ya mace nake gamuwa da wanan kaddarorin haka ko me ? Da sauri hjy take fadin yo meye haka ana zaune kallau zaki sakawa mutane kula a nan haka godiya ya kamata kiwa Allah da yanufa ba abinda mutane ke zargi bane ya faru dake din. Inna ma kuka take a lokacin cikin kunar rai tana fadin bari hjy munga abu a rayuwan mu kamar kaina farau haihuwa diya mata a duniya. Diya mace alherine hjy ta tare inna tana fadi don ni nan nafi kowa sanin dadin hakan don uwarsu ce ta zame min gata ga zuri,a na. Don haka ba za a zagi diya mace a gabana ba ban bada amsa ba don na haifa nasan dadin su a rayuwana. Gyaran muryan da Abba yayi daga kofa inna yasa mu dan dago kai muka kalli kofan da alama daga barci yake a lokacin saboda yanayin shi ya nuna hakan. Me kuma ya faru nake jin kamar kuka ke kenan baki gajiya dayiwa mutane kuka akan abunda baikai yakawo ba a gidan nan. Bawan Allah kada kaga laifin yarinyar nan raba da da mahaifi ba abin wasa bane don kukan yanzu na zuwan yarta ne takeyi. Sai akace don yarta tazo su mayar muna da gida kamar na makoki dama haka yana kallon Asabe data fada mai magana kamar ba Abban mu dana sani da farko mai taushi da sanyin raiba. Fuska a daure ya juyo yana fadin mama sannun ku da zuwa ashe kuns hanya tafe ? Hjy ta sauke ajiyan zuciya tana amsawa Abba gaisuwan a cikin dan sakin fuska sai bin kowa da kallo take tana mamaki a ranta. Taci gaba da fadin tafe nake da jikana don taki sake jiki tun bayan zancen daurin auren nan dayazo muna bata a cikin walwala sam. Shine na kawo ta gida zata kwana biyu mijin ta zaizo ya dauke ta su tafi don jerabawan da zata fara wani sati mai zuwa in Allah ya yarda. Saidai zanso nasan ko akwai wace zamu samu daga nan da zata tafi ta zauna muna da ita a can gidan nata na Abuja. Duk wanan bayani da hjy kewa iyayyena sai a lokacin nake jin komai daga bayanin da take masu din a yanzu. Abban ya gyara zama yana fadin tau hjy abune dake son natsuwa a yanzu zamu zauna bayan tafiyan ki mu duba wace ya dace ta bita can din inda halin hakan. Ba damuwa hjy ta fada tare da kara basu hakkuri kan yadda auren yazo batare da an gudanar da komai yadda al,ada ya tanada ba. Duk sai naji na muzanta sosai yadda hjy din ta samu gidan mu duk da dama ai tasan tunda har na iya zuwa aikatau a birni babu abinda zata sama a gidan namu. Ina tuna irin kallon kaskancin da Aishan mami ke min tun fara zancena da ya Jafar din wani kallon banza da raini take watso min aduk lokacin da zamu hadu. Da ace daga cikin su ne sukazo gidan namu a haka Allah kadai yasan irin abinda zasu fada akaina kan hakan. Saidai ita hjy babu hakan gareta zaune take saman tabarma da inna ta shimfida a dakin ta mike kafa hankalinta kwance dasu tana masu bayanin komai. Abba ya mike ya fita yana fadin bari ya dan fita sai ya dawo a daidai lokacin da ya jamal ya bada tsaraban da sukazo dashi da kayana a shigo dashi gida ke nan. Akuma fadawa hjy ta fito don rana nayi yau yake son ya koma Abuja ba zai kwana ba kaduna . Har lokacin banga lantana ba ba kuma danta a wurin har nakai ga tambayan sa, adatu wai lantana fa ? Saida ta tabe baki kafin tace dani tana dakinta mana tana bakin cikin da dawowan ki tunda tayi shela a gari da cewa wai an sayar dake gun yan birni. Wanan bakin cikine irin na hassada ga mairabo taki ne don tasan yanzu kinfi gaban ta har abada don haka ki daina saka zancen irin su a gaban ki yanzu. Fitan Asabe a dakin ya ba hjy dama yin zancen siri da innar mu sun dan dauki lokaci don gaba daya hankali na ga yan uwana da muke zuba hira agefe daya suna murnan ganina. Yan iya magana sunce kafin kaga biri biri shiya dade da hango ka tundaga nesa karfe goman safe dirka dirkan motoci uku suka tsaya a kofan gidan da muka baro zuwa kaduna yau da safe, a daidai lokacin da mu ke kan hanyar anchau zuwa garin mu. Su shiddane tafe mutum.bibiyu a mota dayasuke tafe saida suka karewa gidan kallon mamaki dan girman shi da tsaruwan shi kafin su nufi hanyan shiga daga ciki. Masu tsaron gidan ne suka dakatar dasu da tambaya wurin wa suka zo kallo rainin wayau hjy saudat tayiwa security din tana fadin zai bude kofa su shigo ko sai ranshi ya gama baci yasan kosu suwaye da zai tsaya tambayan su suda gidan dan su. Yana tsaye ko wace ta fito da abinda take fada mai a lokacin saidai ya kallesu kawai bai iya furta komai garesu ba. Yasan mami don suna haduwa a can gidan da wani lokaci yasa mami karasowa wurin da kanta gaisuwan girma yaiwa mami din tare da nuna sanaya a gareta. Tambayan shi tayi da fadin ko grandma da wanan yarinyar da ogan su ya kawo suna cikin gidan nan ? Da sauri ya girgiza kai tare da fadin babi kowa a gidan su kadai ne a ciki ko zan iya shiga in gani da idona mami ta fada. Kofa ya nuna tare da dan dukar da kanshi alaman girmamawa a gareta ta nufi kofan sauran dake mara mata baya suka bi bayanta zuwa cikin gidan. Bin ko ina na gidan da kallo sukeyi komai na gidan abin kallone don ya tsaru iya tsaruwa dai a kasan nan ba karya a cikin sa. Saida suka gama duba ko ina na gidan guide din na tsaye daga kofa ya rufe fuskan shi da madubin ido baki fuska babu sauki a gareshi. Da hannu mami ta yafutu wanda ke tsaye a kofa kamar an dasa shi a gurin yazo da saurin shi cikin girmamawa gaban mami din. Are you sure grany bata gidan nan ko ta zauna tare da wata farar yarinya haka kai ya girgiza yana fadin baiga kowa ba a gidan nan yana fadi yasa kai ya bar gurin ya koma inda ya fito da farko yaja ya tsaya ba tare daya kara kulasu ba. Yaran nan me suka mayar dani mami ta fada a hasale ta soma tafiya sauran suka mara mata baya suka bar gidan cike da takaici a ransu. Duk da mami bawai ta saba da ciwa mutane mutunci bane a yau kan data sameni a gidan nan da tayi min cin mutunci ta uwa ta uba don ta kula ba karya mutane ke fadi ba na asirce mata dane da saddabarun mu na yan kauye. Don wai ba a sako mu daga gidajen a banza kafin mu bargida sai anshirya mu da asiri idon mu idon mazan wasu da yayan su kamar yadda ya faru a tsakanina da ya Jafar din yanzu. Duk abinda hjy maria ke fadi a gefenta mami bata samu bakin bata amsa ba a lokacin don burin mami ranan shine ta same tayi min koran kare tsakani na da danta. Inyaso daga baya sai ta nemi shiri da hjyn su su shirya a tsakanin su sai gashi tazo ta samu gaba daya ma yadda ta samu labari mun rigada mun bar gidan a lokacin. Gida ta dawo bayan ta sallami kawayen nata na birni da yanzu suke manne da ita koda yaushe suna kara sakata shagalta da duniya . Dakin ta nufa kai tsaye don ta samu natsuwa a yadda take jin kanta magani ta fara sha kafin tabi lafiyan gado ta kai kwance. A daidai lokacin da barci ke shirin daukanta ne wayan ta yake ruri a jakka har ya katse bata daga ba . Wani kirane ya sake shigowa again da tsuki a bakin ta takai hannu tana daukan wayan dake cikin jakkan tare da duban screen din wayan nata taga sunan mama Ramatun tace ke kiranta. Ramatu ta fada a fili tana dauko wayan zuwa kunnen ta tayi sallama tare da gaida ita da kwana. Sama sama ta amsa mata gaisuwan mama Ramatu ke fadin sai ga hjy ta dawo yanzu wai ashe tana kaduna duk wanan neman da ake mata haka. Kaduna fa mami ta fada da mamaki kafin tace kaduna gidan wa ke nan wallahi wai ashe tana gidan hjy Tantano duk wanan neman da ake mata. Wani ajiyan zuciya mami ta sauke kafin tace da wanan yarinyar suke ke nan ko ? Wace yarjnyar Ramatu ta tambaya kafin tace au nagane ba tare suke ba gaskiya ita kadaice da kayan ta yanzu aka sauketa gida masu shi basu ko zauna ba wai suna saurine. Guntun murmushi mami ta sake a fuskan ta tare da ajiyan zuciya tace Ramatu yanzun na yarda da ake fadin jika yafi da dadi wallahi wanan abinda hjy tayi min akan yaran nan. Anywhere zan kira in an jima ki ban hjy din muyi magana tunda yanzu nasan mutanene a tare da ita ina fatan dai baki bari kowa yasan da wanan zancen ai. Haba dai antyn mu tayaya zan dabawa cikina yuka da kaina kan wanan magana ai wanan ba abin bari na waje yaji bane ace hjy tayi fushi dake tabar maki gida har baki san inda take ba tsawon kwanaki haka. Bari kedai Ramatu ko wa yan nan dake tare dani ai ban bari sun fahinci yaya kan zancen yake ba sam kinga min yar iskan yarinya zata ja a bagani a bangon jaridan kasan nan don tsiya. Dariya mama Ramatu ta kwashe dashi tana fadin ai sai dai kada a kara amma wanan yarinyar ta rigada ta cuci mu saidai kawai a dauki mataki don gaba kuma. Mataki kan kamar na dauka Ramatu don gaba dayab su saina nuna masu kuren su har shi jafar din ina binshi a sannu ne yanzu in samu akaiga auren nan shi da yar gurin saudat. Har yanzu zancen yana nan ke nan da kawai ki barshi ai daga baya zao gane irin gatan da kike so kimai idan yaga matsiyatan daya jawo a jikin shi suna batun rufeshi da bani bani. Barni da mara hankali mami ta fada tana maijin zafi a zuciyar ta kan abinda yar uwanta ta fada yanzu. Bayan ta kashe wayan idanunta ya dade a runtse tana tunane kafin ta mike zubur kamar ta tuna da wani abu a lokacin. Ficewata da dan sauri zuwa part din dan nata jafar har tana hada kafa a wurin sauri lokaci guda . Tayi sa,a tana murda kofan taji shi a bude bata tsaya jiran wani abu ba ta afka ciki part din kai tsaye da sallama. Yana zaune saman kujera sai farar takarda dake nade a hannun shi ya duka yana zukan farin garin dake saman dayan farar takardan dake aje saman table. Wani irin ja tayi baya kamar zata fadi lokaci guda kuma tabi bangon dakin tana dafa a habkali don yai mata makari daga inda take tsaye. Saida ta dafa bango ta samu numfashita ya dan daidaita ta samu fadin Jafar sai kuma idon ta ya sauka akan wasu tarin kwayoyin dake watse a gefen shi. Da wani irin rawan jiki mami ta ke nunashi da yatsan hannunta tana fadin Jafar yaushe ka fara wanan halin ban sani ba ? Yadda take maganan kamar wacce ke gudun wani yaji abinda take fadi din a lokacin a hankali ya dago kai ya kalli mahaifiyar nasa yana fadin . Mami kiyi hakkuri bansan zaki shigo a yanzu ba har na kai ga shan abinda zai kwantar minda hankali. Idan naci gaba da zama haka ban samu abinda zai taimakawa kwakwalwata ba zan samu matsala sosai shiyasa na sha wanan a yanzu don ya dauke mi ragamar hankalina na dan lokaci zuwa yanzu. Don ba zan iya jure ji da gajin yadda kike kokarin hanani abinda nakeso a rayuwana ba mami sai kuma ya mika mata hannu alaman dai ya fara fita hayaci shi a lokaci. Kamar wawiya haka mami ta koma lokaci guda do haka tabi hannun nasa daya miko mata zuwa gare shi. Don bata son ko cikin diyan ta wani ya riskeshi a wanan halin da ita ta riski dan nata a ciki. A hannu kuera ta zauna ta tsura mai idanu yayin da nasa idanuwan suke kamar a lumshe duk da tasa ba barci yayi ba a lokacin. Kanshi ta dauka zuwa cinyanta ta fara shafa a hankali take hawaye wani na bin wani suka fara sintiri a idanun ta lokaci guda. Babu abinda ya fado mata a rai sai irin wasoncin daahaifi su yabar mata kafin bari shi duniya akan ta kula mai da tarbiyan diyan shi kamar yadda sharia ya sharadawa musulmai. Mami hawaye wasu nabin wasu ta kasa controling din su tuni kanta gaba daya har jikin ta ya dauki canji lokaci guda ta rasa wani duniya take ciki a lokacin. Wai yau jafar dinta ne haka dumu dumu ta kama shi yana wana dabia da tafi kyamata ga diyanta. Ta rasa meke mata dadi a ranta gashi tana son fita ta koma dakinta ko zata samu ta fasa hawayen ta su samu zuba kasa ko zataji sanyin abinda takeji a ranta. Gashi kuma tana tsoron fita a lokacin kada wani ya shigo part din bayanta ya same shi a wana halin ko kuma ganta a cikin wanan yanayin da take yanzu a tambaye ta dalili. Asalima idan son samune daga ita sai shi idan ya farfado ta samu ta gargade shin sosai kan hakan don ya tsira da mutuncin shi a idon jama, a. Jin mami ta zurfafa ga tunanen da takeyi ne yasa shi dan dago kai ya kalle ta a hankali ya ke fadin go back to your room mami. Idan na tashi za shigo muyi magana dake anjima murya cikin rada mami ta sake fadin zan koma amma sai ka ban duk wanan abinda kake sha yanzu na fita dasu dakin nan hankalina zai kwanta. Murmushi yayi yana dan mikewa daga zaune tare da fadin kiyi hakkuri mami nasan na bata maki saidai nima din ba hakan naso ba dani. Nasani jafar yarinyar nan ta cuceni ta gama min da rayuwa jafar a sanadin ta yau jafar har shaye shaye ka koma yi haka. Cikin wani iri kuzari ya dago yana kallonta fuska daure kafi yace mami idan ma cutane ai yarinyar aka cuta tunda ita zata zauna da mashayi irina yanzu. Wani irin sauti gaba mami ya bada lokaci don ji abinda yake fada a cikin maye jiki babu karfi ta mike tare da aza kanshi saman filo tana fadin . Ka kwanta da wanan shirmen da kakewa mutane a yanzu yanzun ba lokacin maganan komai bane. Murya kasa kasa irin na wanda baya cikin hankalin shi a lokacin kamar mai shiri barci yace iam telling you mami itace muka zalinta, , , , ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU SIRI NE 🦅 4️⃣2️⃣ ZAINAIBA IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA DA FATAN KOWA NA LAFIYA UBANGJI YA BAMU HASKE GA AL,AMURAN MU AMI YA ALLAHU, , , YAR UWA LITTAFIN KUDINE KI TUNA HAKAN DON ALLAH KADA MU RIKE JUNA DANI DAKE DARI UKU NE KACAL SISTER TA BANK KO KATIN WAYA NAGODE, , , Kai duniya muji tsoron Allah wai mutane yanzu basa tunane ba a duniya za a tabbata ba zamu koma ga mahailicin mu Allah . Amma saboda son kai sai kaga idon mutum ya rufe akan duniya ya manta da za a koma wurin ubangijin talikai ya dinga yin abinda ya ga dama. Mami batai tunanen laifin daga gurin ta bane sai kokarin dora laifin abinda idon ta yagani akan dan nata yau takeyi a kaina. Tana tunanen da badon ni ba da danta bai shiga wanan halin ba data sameshi a ciki don kawai wanan matsalan har yakai ga wai ya fara shaye shaye haka saboda idon ta ya gama rufewa a lokacin. Ta dade kwance ita kadai a dakin kafin tayi karfin halin mikewa tsaye don zuwa gahatar da sallah la,asar da yayi tun dazun tun safe ta kasa kai komai a cikin ta har zuwa lokacin. A Inda ta idar da sallah take zaune har lokacin tana cikin zulumi da tunane halin data riski dan nata a cikin . Wayan dake gefen tane yake ta ringing ta kasa tashi ta dauka sai bin waya takeyi da idanuwa kawai a saman gadon. Mami wayan kine fa ke ringing Aisha ta fada daga kofa tana shigowa daki lokacin idon ta akan mahaifiyar tasu dake zaune wurin da take sallah. Dago kai tayi ta kalli yar nata a ciki wani irin yanayi na ban tausayi a gare ta da wanda ya ganta a lokacin dole ya fahinci bata a cikin hayacin ta. Mami lafiya Aisha ta fada tare da kaiwa zaune a bakin gado tana kokarin daukowa uwar wayan dake kara saman gado. Ajiyan zuciya ta sauke kafin tace duba min yayan ku idan ya dawo daga wurin aiki har ta mike tace ya mamud ke nufi mami kin yanzu bai dawo ba ai sai after six zai shigo. Hannu biyu ta dauka ta dora a fuskan ta a cikin yanayin nuna takura a rayuwanta a lokacin sai kuma ta fashe da kuka mai tsuma zuciya da tashi hankali. Take hankalu Aisha ya daga sai wanan lokacin ta fara nadaman rashin grany dinsu a tare dasu yanzu ina tasan zata dosa da wanan matsalan na uwar su da bata san abinda ke damun ta ba. Mami Aisha ta fada a sanyayye mami lafiya meke faruwa ne wai dake barin duba idan ya j na gida na kira maki shi. Karki soma ta fada a cikin wani murya mai nuna cikkaken umurni a gareta da sauri don tsoro ta koma ta zauna a inda ta tashi da farko. Ido ta kurawa mahaifiyar tasu kamar tana nazarin ta kafin tayi karfin halin fadin mami koma meke damun ki kiyi hakkuri don Allah ki daina zubar da wanan hawayen haka. Aisha will you believe da irin halin dana riski dan uwan ku yau a ciki koda yake barshi kawai bai dace ma in fada maki ba a yanzu. Mami wani abin yayi kuma after all he has gone through na yin aure bai fada maki ba ko ya dauko zeey din ne zuwa gidan na kuma ? Wani kallon takaici ta jefawa yar nata tare da mata gargadin ke yarinyace Aisha ta kawar da kanta ga kallon ta do takaici data kara bata na ambatan sunana a wurin. Aisha ta dade a zaune tana kallon yanayin mahaifiyar tasu dake a cikin tashin hankalin data kasa gane dalilin hakan a yanzu. Mikewa Aisha tayi daniyar barindakin dob ba zata juri ganin uwar a cikin wanan hali ba na bacin rai. Sunanta mami ta ambata ba tare data dago kai a yadda take ba taci gaba da fadi kada ki fadawa kowa halinda kika sameni a yanzu. Naji mami Aishan ta fada har ta soma tafiya taja ta tsaya tare da fadin but mami da sauri ta fara tafiya bayan hannu da uwar ta kara daga mata kuma. Koda Abba ya dawo gida da dan ledan shi dayayo cefane din a dafawa hjy ya samu hjyn ta fito zasu tafi don azzarlazalan da ya jamal ke mata tafito kada su makara. Af hjy wai tafiya zakiyi ne yanzu ga abin tabawa har na sayo a gyara maki kada kizo garin baki taba komai ba. Cikk yar fara a da nuna jin dadin yadda ake kulata a gidan namu hjy tace ai yata ta gama ban komai yaushe rabona da nasha fura da nono haka mai dadi. Ga kawata ta nuna Asabe bayan innar mu tana fadin ta kawo mi ganye shima na taba ko hakama aina gode. Ta nunani tana fadin saidai ga matar jikana nan don Allah ina son a bata duk wani kulawan daya dace da ita don yanzu ita din ba abin wasa bane a guri kowa. Kanne dakr gefe tsaye duk suka kalloni a lokaci daya don jin abinda hjy din ta fada akaina suna murmushi. Nauyi da kunyane ya kamani lokaci guda muna gaba nan muka barta da Abba da innar mu da Asabe suna maganan abinda bansan kome suke fada ba a lokacin. Muna tsaye a bakin mota tare dasu ya jamal duk da dai gaisuwa kawai mukayi dashi ya juya abinshi bai kara bi ta kan mu ba kuma. Wanan fa mai kama da balarabe yayar mu amma dai bai iya hausa ba ko don naji hausan nasa kamar da turanci ya amsa mana. Yayan mune ba bata amsa dashi batare da kara furta komai ba hankalina yana gun abinda suke tataunawa a kai. Abba ya san fito ya bar hjy da innan mu sai can ta fito ta amemu a wurin motar hannu ta mika min na nufi wurinta don na gane abinda take nufi da hakan. Dan rugumeni tayi kakar mai rada take fadin in kula da kaina zamuyi waya idan ta isa gida tana son in zama mai biyayya a duk yadda na riski kaina a ciki da mijina. Nauyi da kunya ne suka dan rufeni saiga idanuwana suna dan ciciko da hawaye a lokacin guda kamar kada in rabu da tsohuwar muna kalo haka ta barmu a gurun suka tafi bayan alherin databi kowa dake wurin dashi na kudi. Mun juya da zuman shiga gida muka tsinkayi muryan Abba da lantana har da innan mu da sauri muka karasa zuwa ciki don ganewa idon mu abinda ke guda. Lantanace ta cikuwaikuye abban mu dake tare ta a dole sai ta karbi ladan da Abba yabawa inna mu a gyara min abinda ya sayo a yiwa hjy dan abin motsa baki. Tunda na tunkaro wurin nayi arba dasu a halinda suke ciki na runtse idanuwana a hankali do abinda idona ya gane min . Kai kai kai amma yar nan baki da albarka yanzun nan da bakin ma a gidan sai kinyi wanan saida halin da kika saba ashe. Da badon mutane na sun tafi ba haka zaki barmu da abin fade a gidan nan saboda baki fitina irin naki. Inna don Allah ki mika mata ko manene a daina wana fitina indai a kaina ne ake wanan abin na fada cikin dan marairaicewa inna mu din. Ba ita kadaice mai bakin ci ba yau ina sin i gani idan na karfi ne tazo takwata tunda an fada mata mu bamu da hakki akan shi komai sai itace za a sayawa taci muna kallo. Af don kin fadawa yarki tsoron karba zanyi ko me ni kunya ma kika ban ace wai yarka ta dawo yawon bariki haka tana haska gari har zaki tsaya fada kan wana dan ledan hannun ki. Ina kwalayen da kaya dadin da aka saba zo maki dashi wanan karon ta kwabe ba a kawo din bane ko meye don naga kamar su dawo muka da gaiyan tsiyan ku gidane sun gaji da kwallon mangoro sun yar sun huta da kuda . Inna mu dai bata sake ledan ba tayi daki dashi muka bita ga baki daya mu yan dakin namu saboda Abban mu dake wuri ya hana ai magana a lokacin. Muna shiga daki akan kwalayen da aka jera a daki wanda lantana kewa gatse sa,adatu ta nufa tana tambayana ko kwalayen meye ina mata bayani . Banso akaiwa lantana ba a lokacin kada ta dauka don gatsen da tayine yasa aka kawo mata din kuma in ba akaidi ba inna tace sai tace ai daga bayane aka sayo aka kawo muna. Kwalayen madara ne na tea sai milor da sauran tarkacen kayan tea da katon din lemoka na sha masu tsada wani abinma sai baya mun bude muka ga meke cikin don har da kaji da ke dankare da kankara ga buhun shimkafa har uku ajiye. Kamar ba gobe har ina mamakin hali iri na innan mu kamar ba yanzu lantana ta gama mata cim mutunci ba don haka aka diban mata komai aka kai mata Asabe hakan aka kai mata komai da mukazo dashi. Mamakon injin tace a dawowa inna da kayan sai naji tana fadin wallahi karba zanyi ko yanzu don ba a barin mugu da makami ai. Ba a san zafin nema ba tunda ba jikin mutum aka kurza ba wanda yaje shi aka sani kuma sunan shi ya lalace ai. Kowan mu a dakin yaji me take fadi saidai da idanu kawai innan mu ta kallesu kowa ya shiga natsuwa a cikin dakin da alama dai warining inna ta bayar gaba daya a dakin . Allah sarki wallahi yahanasu ko yau na fadi na mutu a gidan nan kin biyani don bani da kaico gurin haihuwan ki don yar ki zata iya rungumar ku a yanzu ta zame muna gata. Gorin da aka zugani nasha maki na rashin haihuwan dana mijin yau ga diya macen ta jawo muna arzikin da za,a fade mu a gari muma. Aiko Asabe bata rufe baki ba saiga lantana na fadin kai Allah mungode ma dadin mu da gobe saurin zuwa wallahi. Yanzu ai sai muga ankai mutum makka shine zamuyiwa mutum ai murna ko a sauya mai gida kinga an rufe baki zagin diya mata a gidan nan ga baki daya. Har sukayi suka gama ina lafe a dakin inna ban samu abindana fada ba sai faman tunane nake a kasan zuciyana. A yanzu zancen ya jafar ya fara tasiri a zuciya don gaskiya innan mu tana so hutun da yake kira masu a yanzu. Ba inna kadai ba har yan uwana da Abban mu shi kanshi yana bukatan kulawan daya dace a yanzu. Kafin innan mu ta karasa girkin ta har barci ya daukeni a gurin saida akai kiran sallah a zahar kafin sa,adatu ta tayar dani daga barcin da ya dab daukeni. Sai lokacin na fito waje tun bayan shiga dakin daga wurin rakiyan hjy da muka tafi tun lokacin ban fita wajen ba ina dakin mahaifiyar a ciki damuwa . Nazo gida ban huta ba a can kuma ba zancen hutu ko kwanciyan hankali a gareni fara ma nan din na samu na lafe a dakin innan mu din. Bamu samu natsuwa da inna ba sai dare baya kafa ya dauke ne muka zauna zaman hira da inna din. Ban boye mata komai ba yadda komai ya faru a tsakani na da mami na labarta matashi a cikin daren nan ko zan samu sa,ida ga abinda nake ji a raina. Ikon Allah Inna ta fada tana ajiyan zuciya tare da fadin wata sabuwa cakwakiyar kenan ke shirin tunkaro mu ashe. Yanzu ita hjy da kanta take kyamatar ki da danta don kina yar tallakawa ko don wani mugun halin naki da koka boye min bansan da shi ba ? Da sauri na dago ido duk da babu wadattacen haske a dakin lokacin inna taga kallon razanar da nayi mata alokacin . Inna ki yarda dani da tarbiyan da kuka dorani tu farko ban kara wani hali ga wanda kika sanni dashi da farko ba ban yarda duniya ta rudeni ba inna don nasan kudi daine iyayyena komao dadewa wurin ku zan dawo zaman can din na dan lokacine. Kafin in kara inna ta tare da fadin kimar ki da kamalanki ne ne basu kai ta hada iri da ke ba kamar yadda mafi yawan masu hannu da shuni suke da wanan akidar bawai ke dince bata so ba a zahiri a yadda na fahinci zancen. Inna bata sona yanzu sam zama kawai nake a gidan dan hjy da danta daya jamin duk wannan abin a yanzu. Inna har fa sata mami da yar ta suka dora min a gidan sai da shi dan nata ya biya kudin yakuma sakatar dani duk wani aiki da nake a gidan da sunan biya haka na zaune a cikin su babu walwala ko sakewa komai akan hattara da tsamgwama nakeyin shi gidan na karasa fadi a cikin kuka. Subbahanallahi wanan wani irin rayuwa muke shirin fuskanta karfin mu ba daya ba balle na nuna jayyaya ko nace zan kwatar maki hakkin ki garesu. Bazanyi izzigili acikin sha,anin aure ba don aure abune mai rai da Allah ya hallita kamar rayuwa idan kaddara sai anyi shi idan kuma zama ya kare ko ana so sai an rabu a tsakani. Shine dalilin da yasa akeson musulmi ya yadda da kaddaran ubangiji maikyau ko marakyau ka yarda daga Allah komai yake. Kuka na sakawa inna don gareta kadai na dogara da zata tsaya ta kashe wanan auren don ita kadaice nake hango gatan mu a gareta da tausayawa don Abban mu yanzu sai a slow tun shigan lantana rayuwan shi. Da mamaki inna ke kallon yar nata a cikin tausayi da kulawa take fadin menene ne a ciki aure ne bautan ubangiji kowace mace da yadda akasin nata yake zo mata. Idan ma wani mugun haline gareshi har yake boyewa na roki Allah a sandiyar ki ubangiji ya sauwaka mai ko menene a rayuwan shi. Idan kuma da zuciya daya ya aureki ubangiji ya kara mashi sonki da kaunar ki a rayuwan zaman ku tare da zuri,a masu albarka. Bazan taba ja da ikon Allah ba don haka kema nake gargadi ki da ki yadda da kaddaran ki a yadda tazo maki. Allah yasan hikimar daya shimfida a nan ya tsameki daga cikin mu ya kaiki can cikin su kika zauna tare dasu har hakan ya faru yanzu. To a barwa Allah sanin sa a hakan illa iyaka gobe zan turaki can gurin kawuna Inda addu,oin da zai baki sai ya taimaka muna dashi kafin nan nizan fara zuwa naimai bayanin komai insha Allahu. Dan sheshekan kuka nakeyi kafin inna tayi shiru tana saurarena ba abida nake tunawa sai irin tsana da kiyayyana da yanzun nake hangowa a idon mami din ko yaushe. Sai zuwa can naji inna tace yoke ai ya kamata ki hankalta tun daga yanzu ki sancewa ubangiji mai sonki ne yar nan baki da wani zabi dayafi kita godewa ubangijimu . Dazun nan kika shigo gidan kin dai ga abinda ya faru a gidan nan shi kadai ya isheki ishara a rayuwa duk wani izzigilanci da ji da kai na lantana bai hana ta karbi abinda kika kawo a karkashin ki ba. Ko wanan ai wani babban baiwa ne da cigaba a wuri Allah wanda yake zaton ka da komawa baya yau a wayi gari yaci ta karkashin ka. Don haka hakkuri zakiyi kaddarar kice a hakan haka ubangiji ya tsara maki baki isa ki kaucewa hakan ba. Don yanzu idan nayi fushi nace zan kwata maki hakkin ki da karfi da yaji na dauki mataki sai mu taru mu nunawa ubangiji ke nan bai isa garemu ba. Haka dai inna tayi ta rarashina har barci ya dauke ni ban sani ba tun ina dan bata amsa har taji nayi shiru hakan yasa ta gane barci ya daukeni ne ta shiga nata tunanen a nan don abubuwan da take hangowa bata dai yarda ta nuna min hakan bane kawai. Tasan ina ciki wani mawuyacin hali mai wuyan sha,ani da wanan baiwar Allah da Allah ya hada rayuwana da ita don mutum ya nuna bai kaunan ka a cikin ahalin shi abune mai wuyan sha,ani don ita kanta zaman abinda take fuskanta ke nan in badon ta kwabe tsakanin lantana da Asabe ba aka gansu a rana. Don haka dole itama ta jajirce ta dinga yiwa yarta adduan fatan alheri ga halinda ta riski kanta a cikin shi duk da tsohuwan bata boye mata komai da take hasashe ba kan wanan auren nawa. Don haka take son inna ta kara kwantar min da hankalina na samu tsuwa ingano mai hakan da yayi, yake nufi akaina dashi din. Dole sai a cikin hikima da basiri inna zata iya fahintar dani manufan hakan a yanzu don hakane kawai zan samu natsuwa akan zancen. Washegari tunda ba idar da sallah barci na koma duk daba gajiya a jikina saidai rashin barcin da bamu samuyi da wuri ba nida inna. Can ciki barcin wani hayaniya ya kara tayar dani don muryan lantanace har kofan dakin mu tana magana kamar a cikin dakin take a lokacin. Da mamaki na mike kome ya faru suke wanan fitina haka da sassafen nan a cikin maganan na dan tsunci zancen daya hada fadan wai ashe lantana tace bata yarda da rabon da inna tayi a jiya wanda asalima ba inna bace ta raba kayan sa,adatuce ta diban masu komai ta aika dashi. A hankali nake gyara rigan barcin dake jikina a lokacin tare da fadin inna don Allah kuyi hakkuri meya kawo wanan zancen yanzu kuma. Daga gefe dayan kanwata ke fadin wai shikafa aka aika mata dashi shine tace yayi maya kadan ko jiya dai ta karbi abinda aka kai matane. Shine tazo yanzu take wanan fadan da innar mu wai sai an raba daidai ko a kara mata Abba kuma ya daure mata ginda a hakan wai a kara din. Karbo roban ki kara mata din Allah halima wanan fitina ya kare hakana baza a karaba tayi abinda zatayi din sa,adatu ta fada a hasale. Sa,adatu dan Allah ki bari a bata koda baku bata karewa zaiyi don ba zaku tabbata dashi ba ai har abada nafada tare da mikewa na nufi kofan dakin da lantana take tsaye. Abin mamaki ba lantana kadai bane akofan har abban mu yana tsaye a bayan ta tare da dan yaron su rungume a jikin shi da ganinsa a ckin damuwa yake sun kwana suna fitina kila a dakin. Buhu dayan na mika mata iyakata kofa dashi tana ganin haka tace yanzu naji magana kan dama wanda bai fita ya nemo ba yafi me nema rowa ai. Tana kokarin jan dayan buhun da muka kai mata kofa zata tafi dana baho da aka zuba nace halima dauki na bahon ki kawai kaka ta kara. Daya da rabi zamu tsira dashifa yayan mu kanwata Amina ta fada cikin dan marairaice murya nace ki godewa Allah da wanda kuka samu Amina. Kinsan wanda zaku samu gobe ai,shi alheri takine barta Allah zai kawo muna wani wanda yafi wanan din data dauka. Nayi mamakin ganin tunda safe ashe girki inna ta hada a gidan lafiyayye da zamu karya dashi da kayan miyan daya hadasu fada da lantana wanda Abba ya kawo muna da hjy. Kowa na gidan saida ta zuba mai daga Asabe kakarmu har lantana naji tace a kaiwa dan lantana abincin ma,anade tayiwa dan lantana kara. Wa yan nan dabi,un na inna sukan ban mamaki zakaga an mata abu saudayawa da zaran ta mayar da marta jan abu daya ya waddatar da ita ke nan bazata sake bi kan abinba kuma. Tana gamawa wanka ta shiga a gurguje ta shirya tare da fadin zata dan fita unguwa mukai mata sai ta dawo wurin muka zauna zaman hira da yan uwana ranan sa,adatu batayi sana,a ba sai labarin abinda daya faru bana gidan suke ban. Wanda hakan yasa na kara jina wasai kamar babu abinda ke damuna a rayuwa neme kuncin da nake ciki na rasa ga baki daya sai fari cikin daya mamaye zuciyana. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣3️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA BARKAN MU DA YAU YAR UWA UBANGIJI ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMINSA AMIN, , , , , Kofa a rufe yake koda ta murda don haka ta tsaya kwankwasa kofan don a bude maya daga ciki. A hankali yake bin kofan da kallo kafin yaji an tsananta buga kofan yazo ya bude yana tsaye mutum din shi sak saye da jallabiya baka a jikin shi sai farin jikin shi daya karawa jallabiyan kyau a lokacin a jikin shi. Yana buda kofan sukai arba da mami dake tsaye a cikin daure fuska da dakewa baya yaja ya matsa mata ta karasa shiga cikin dakin. Mami lafiya da safen nan ya fada yana msi bin bayanta zuwa wuri kujeran data nufa don ta zauna har lokacin tana mai bin falon da kallon abinda ta gani jiya yana dawo mata a ranta sabo fil. Saida ta zauna dakyau suna fuskantar juna dashi dole irin kallon da take mai yasa ya dan dukar da kanshi kasa don nauyi da kunyanta da yaji lokaci guda duk da baiyi tunane tasan halin data riske shi a ciki jiya ba. Sake dago kanshi yayi sau karo na barkatai yana dan kallon mahaifiyar tasu yana dukar da kai da idanuwan shi da suka fada a cikin yan kwanakin nan kamar wanda yayi cutar wata daya dashi. Saidai wanan karo ya kasa jimirin dukar da kan nasa gareta don irin idin data zuba mai tana kallon shi wanda ya kasa fassara ko kallon meye hakan. Wai mami lafiya na ganki a haka hannu mami din ta daga mashi kafin ta sauke wani irin zuciya da sai daya sake dago kai. Wani ajiyan zuciya mami ta sauke kafin tace friend magana nazo muyi a matsayi na uwarka kuma abokiyar shawaran ka a kullun. Jin hakan yasa ya gyara zama ya mayar da hankalinshi gareta sosai din jin abinda zata fada mai a lokacin. Wani ajiyan zuciya mami ta kara saukewa kafin tace Jafar yaushe kafara shaye shaye a rayuwan ka ban sani ba ? Tare da mika hannu gare shi tana fadin bani abinda kasha jiya a dakin nan na shigo har na fita baka a cikin hankalin ka. Ba tare da fargaba ba ko tsoron data tsamaci zai baiyana a fuskan shi ya dago kai yana fadin ba wani abu mai wahala ai nasha ba mami kawai dai don hankalina ya dawo daidaine nasha. A ciki tsoro da fargaban gami da tashin hankalin, abinda ya fada mami ta dago kai tana kallon shi a firgice tace kasan abinda kake fada kuwa ? Kwayoyin dake a ciki hijjab dinta ne data kwashe a jiyan ta fitar tare da watsa mashi su a gaban shi sama table yayin da idanuwan ta suka kada sukai jawur a lokaci guda fiye da yadda ta shigo dakin da farko tana fadin a cikin wani murya dake nuna gab take da fashewa da kuka a lokacin tana fadin. Why Jafar why da zaka jefa kanka a drug additct saboda wanan yarinyar kake kokarin bata rayuwan ka kome ? Mami yarinya ? Wace yarinya ke nan kike magana da har zata iya sakani wani abinda ba a sanni dashi ba dafarko kada a zargi kowa indan na aikara wani abinda bashi ba wanda ya isa ya sakani yi abinda ban tashi yi ba kai tsaye. Ya karasa fada yana kallon mahaifiyar nasa ido da ido babu wani nauyi ko kunya a yanayi shi ranan. Damm mami taji gabanta ya fadi don kallon da dan ke mata tare da bata amsa haka kai tsaye ba tare da jin nauyin komai a gareta ba. Wasu irin hawaye ne suka ziyarci fuskanta a lokaci guda tare da fadi a cikin rauni Jafar haka ka koma ban sani yaushe zuciyarka da rayuwan ka shika fara wanan harkan ina raye ? Mami ya fada a cikin wani murya mai nuna samuwa kafin yace kiyi hakkuri don Allah amma ni bansan na aikata wani abinda har zai sakaki hawaye haka ba a yanzu. Mami kan duk inda tashin hankali yakai hankalin mami ya wuce nan ga tashi ita kadai tasan irin halin da take jin kanta a lokacin. Shima kanshi halinda mahaifiyar tasu take ciki a lokacin ba zai iya jure ganin hakan ba gareta karfi hali kawai yake dakewa a lokacin. Mikewa yaga mami din tayi wace a tunanen ta har zuwa lokacin abinda yasha di a jiya bai sakeshi ba. Mami ta nufi kofa hankali tashe ya bita da kallon mamaki ba tare da ya iya furta mata komai ba a lokacin har ta fice daga part din nasa. Komawa yayi ya zauna saman kujeran daya mike tsaye gareshi da farko tare da dafe kanshi zuwa sama suman shi da hannun shi daya yana mai shafan gashin kanshi zuwa baya a hankali kafin ya furzo iska daga bakin shi ya mike zubur daga zaunen tare da fadin Oh shit . Don tuna ko meya faru dashi jiya din bayan security din shi ya fada mai zuwan su mami din gidan sa nacan daya ajemu da hjy. Direct wurin window din glass din dake falo ya nufa wanda zaka iya hango haraban gidan mami din ga baki daya, daga inda mutum yake tsaye daga cikin part din nasa. Glass din ya zuge tare da shakan iskan dake shigowa ta tagan alokacin yana mai lumshe idanuwan shi a hankali. Allah ya gani baiso hakan ba a yanzu baiso ace mami ta fara fahintar rayuwan shi na boye ba wanda daga shi sai mahaliccin sa yasa da yana wanan halin da a boye. Shikan shi bazai ce yasan lokacin da rayuwan ta fara mai hakan ba saida kawai ya tsunci kanshi dumu dumu ne a cikin harkan da ba addinin shi ya yardan mai yayi ba. Muna a cikin wani lokaci mai wuyan fassara a yanzu da dole sai iyayye da yan uwa an dage dayiwa yara addua da saka ido tare da nasiha ko yaushe. Baka zama talent a banza yanzu ko wani kuru a duniya sai ka karkata idan ba Allah ya tsare kaba da kaifi adduoin iyayye dake bin bawa. Kusan hakan ne ya faru da Jafar din don shi kanshi ba zai iya cewa ga taka maiman lokacin daya fara wanan harkan ba a rayuwan shi. Iyaka abinda ya sani shine shidai ko a yanzu yana iya kokarin shi wurin ganin ya gyara harkalan shi a kullun sai dai abin yaci tura har yanzu. Yau gashi har mami ta fara riskanshi ga yanayin da bai dace ace ta sameshi a ciki ba, Allah kadai yasan a yadda ta riskeshi din a jiyan ya fada yana maida hankali a wurin haraban gida tare da bin motan mamud dake shigowa gidan da kallo yana mamakin dawowan shi gida a wanan lokaci. A hankali ya bar wurin tagan zuwa cikin sakin bacin shi har lokacin yana mai jin kunan rai a tare dashi don baisan amsam da zai ba mami ba a yanzu tunda ta riga da ta kamashi red hannded a shaye ko. Ruwa ya shiga ya watsa a jikin shi duk sa safe saida ya watsa ruwan don jikin shi da yai mai nauyi a lokacin. Yanzu kuma zafin da yake ji ta ko ina a jikin shi yasa shi ya nufi bathroom kai tsaye tare da sakewa kanshi zuwa jikin shi ruwa gaba daya don yaji sanyi. Karfe hudun yamma mun gama duk wani shiri zuwa unguwan da innan tace muje mu gidan wani baffan ta dake can karshen layin su. Sea tsawale nake tafiya don idon mutane dake yawo a kanmu a duk inda muka wuce dan gungun mutane a zaune. Gidan irin ginan kauyen mune akwai zaure har biyu kafin ka kai kanka cikin gida gidane mai dauke da matan aure guda uku ko wace daga ciki an kewaye mata part din ta da dan kishefa guntun katanga da bazata iya ganin sasshen yar uwata ba sai idan ta shiga daga ciki. Nasan gidan don yana daga cikin gidajen da muka bude ido dasu tunda mukai wayau muna kai masu abincin sallah da yawon sallah kamar yadda al,adan bahaushe yake a karkara. Sashen uwargidan muka nufa tana ciki da taranta ta amsa muns muka shigo tun a waje muka fara gaida ita da yaran don zaman uwaye suke a gare mu tunda inna diyace a wurin su. Matar da fara,a take fadin a, a lale marhabi ga amaryan birni a gidan nan yaushe garin inji maki bako ? Kafin in bada amsa halima kanwata ta cabe da jiya suka zo gobe ko jibi zata koma idan anzo daukan ta. Ke kan fafi ba, a tambayeki ba sa,adatu takai mata dan duka a aika suna kokarin rikicewa da fitina a tsakar gidan mutane lokaci guda. Tsawa na daka masu tare da masu fadan haka da sukeyi matar baffan ina na fadin indai wa yan nan ne ai mun saba da halinsu ko yaushe suna gidan nan tare damu ai. Zama nayi saman tabarban da dayan yarta ke kokarin shimfida muna lokacin da muke maganan muka kara tusa sabom gaisuwa tare da tambayana yaya can ya nabaro su. Sai mukaji dauri aure kawai daga sama haka kokaiwa malam ashe kin gama karbe mai dan kudin sadakan shi kin tafi birni kinyi auren ki a can kin bar mallam a soro ko ? Da murmushi nayi tace ai ba a mamaki sa ikon Allah don wanan auren naki Allah kadai yasan manufan hakan gareku ubangiji yasa alheri ne hakan ya kawar da duk wani sheri daga gare ku . Wanda ke sakin suka amsa da amin ni dai a zuciyana na amsa ban iya amsawa a fili ba don kunya da kawaici irin na yayan hausawan asali. Tsaraban da inna ta debo masu muka zo masu dashi nayiwa halima signal da ido ta mika mata tare da mata bayani kamar yadda inna tayi muna bayanin a gida. Ta amsa da murna tare da fadin barin kaiwa malam ya gani kafin ya fita wurin daliban shi yasan kunzo don idan ya fita baku samu ganin shiba sai bayan magariba zai shego gidan kuma. Ta mike tare da daukan su kayan shayi da sabulen da nazo masu dashi ta nufi turakan malam din dake zaune saman buzun rago mai launin fari da baki a shimfide a kasa. Ga kwanon hura a gefen shi da kofin silver maidan girma na ruwa ya amsa sallaman umma hari matar shi lokaci guda. Bai daina shan furan ba saida ta kare mai bayanin tsab ya dauki kofin ruwan dake gefen shi ya kora kadan kafin yace sun iso ashe tun dazun su nake dan dako ban fita ba dama. Ki masu iso su karaso ya fada a cikin yanayin da malam bahaushe kanyi magana da matarshi a cikin gadara da isa . Har takai kofa yake fadin ji mana da sauri ta dawo baya don jin mai zai fada kafin yace na yanke shawara kecev zaki bi wanan yarinyar kamar yadda uwarta tazo ta bukata ai mata gada don ba wani abinda yahanasu zata nema muddin ina da karfin sa in kasa yimata shi kamar yadda zanwa dan cikina abu babu jin kyashi ko wani abu haka itama yahanasu din . Na sani malam inna habbi ta fada tana gyara tsayin ta don maganan yazo mata a bazata kuma bata da halin da zata musa hakan ga maigidan nasu. Da sanyi jiki ta fita daga dakin kafinta kawo wurin mu babu wani alaman damuwa a tare da ita alokacin sai fara,a dake fuskanta tana fadin mu isa mu yake jira a sashen shi dama ashe. Nan muka barta ta aika karamar su watau amaryan malam tazo ta raba abinda muka kawo masu din na tsaraba. Yana zaune a yadda matar tasa ta barshi muka shigo muka gaisa ya dan jamu da ba,a kafin ya dago yana sallaman su sa,adatu da su dan fita daga waje ya gama magana dani. Ba bata lokaci suka mike zuwa wajen mutanen gidan inda suke zaune kafin ya dago yace min amarya watau kin koma birni kin mana wayau ko ? A cikin dan kunya nake fadin ba gani na biyo ku kauyen ba malam tunda nan na saba dashi ni yadan yi murmushi yana tono wani abu a cikin kayan shi kafin yace. Dazun uwarku tazo min nan hankali a tashe tana fada min wani magana wanda nina dauke shi kamar zancen matane kawai. Don a iya bincike na tun dazun din ni alherin hakan nagani ta ko ina dan akasin shi baida yawa sai dai abinda ba,a rasa ba kawai wani lokaci na zama tare. Don haka yanzu dai karbi wanan ki fara sha ya miko min wani ruwan rubutu a wani tsohon goran yought daya dan dushe kalan farin shi. Dole hakana na karba na kafa kai kamar yadda yace insha da bissimillah in raga in shafe kaina har zuwa wuya sa fuska da sauran ruwan. Yayin da nake faman yi shi kuma yana kokarin yan tone tone acikin kayan shi yana nema wani abu, har lokacin dana aje mai goran magani a gefen shi. Kin sha kenan ya fada ba tare daya jiyo Inda nake zaune ba, na amsa da eh nasha malam nagode na fada a sanyayye. Kai haha dai wanan aiyiwa kaine ne hidima mukaiwa banza don a zauna lafiya balle namu jinin mu fatan mu dai ladabi da biyayya ga miji shine abin bukatan mu. Karbi wanan ya miko min wani abu kamar bawan icce yana fadin ki saka a baki ki dinga taunawa a hankali koda a wayane ki fadi bukatan ki gareshi yau kiga aiki da cikawan wanan. Na baki wanan din ne ba do komai ba sai irin bayanin sa uwarki tazo mi dashi koda yayi wana auren ne da nufin ya cutar dake Allah ba zai taba bashi ikon hakan ba a kanki wanan kuma dan bawan iccen da kike gani a hannun ki aiki shi gareki yafi akirga ki dai saka a baki kamar yadda nace dake yanzu ya kara bada da sauri na dan balle na jefa a bakina sauran na bude yar jakkana na kada a ciki. Addu,oi masu ma,ana ya ban tare da min nasiha akan zaman aure da rike duk wa yanda na sama a gidan da zuciya daya duk wanda yace zai bini da sheri abinsa zai koma mai zuwa safe zaibawa yaron shi wani rubutun akawo min na sha. A nan yake min bayanin tafiya da matar shi tare da hikimar shi nayi hakan wanda shi yasan dacewan zuwa da ita din da zamuyi da irin ranan da zatai min a can din idan mun tafi baidai fito fili ya fada min komai ba ya barshi a dunkule hakana. Munyi sallama dashi da matan gidan da muka samu su fito dukkan su waje ana girkin abincin dare gwanin ban shawa dasu kansu hade ake komai a gidan. Yamma lis muka shigo gidan mu don dan biye biyen da muka yan gidajen yan uwa da kawayena kafin mu shigo gidan . Sallama mukeyi ga lantana a tsakar gidan mu kamar ba musulma ba ta kyalemu bayan sai data juyo ta kallemu kafin ta hakademu gefe guda tana jan tsuki taci gaba da abinda takeyi a wurin. Muryan innan mune da taji sallaman mu daga dakin ta tafito tana fadin kundawo ke nan yanzu nake fada daku a raina don me zaku bari ai magariba kuna waje. Marigaba fa matattaram sheri ne ko sa,an ka ake son a samu a daidai wanan lokacin akanci galaban mutum ai mai sheri. Muna ta sauri wallahi inna nasan bakya son ai fita a wanan lokacin na fada ina kokarin cire hijjab din dana saka a jikina da zan fita. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣4️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA FATAN ALHERI A GAREKU KO YAUSHE ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMAN UBANGIJIN MU AMIN YA ALLAH, , , , YAR UWA KADA KI MANTA LITTAFIN NAN NA KUDI DON ALLAH KADA MU SHIGA HAKKIN JUNA DARI UKU NE KACAL ZAKI BADA , , , Kofa aka turo tare sa sallama a lokaci daya wanda hakan yasa ta mayar da hankalinta ga wanda ke shigowa dan karamin falon a lokacin wanda ba kowa ke zuwa falon ba sai lokaci lokacin don takardun aikin ta masu mahianci da take adanawa a falon nata. Mami lafiya naga kira yafi a kirga a wayana ban san da shigansu ba sai yanzu na duba mami ta dago kai a cikin wani irin yanayi mai ban tausayi ta kalli dan farin nata dake tsaye daga kofa a cikin damuwa ga yadda ya samu uwar nasu alokacin. Kara rikicewa yayi lokaci guda kai tsaye ya karasa shiga dan falon tare da samun wuri ya kai zaune a gefen ta. Mami wani abu ne kuma ya faru ko kuma jikin ne don office din ki na fara zuwa yauma akace min baki samu fitowa ba. A hankali takai hannu ta zare glass din dake idon ta yanayin da fararen kwayan idonta da suke ciki na bacin rai ya baiyana a sarari har dan na iya ganin yanayin nata. Jikin shi yai sanyi sosai lokaci guda yasan ba karamin abune ke jefa mahaifiyar tasu ga tashin hankali irin haka ba ga sanin da yai mata na jajirttatan mace a duniya. Dan gyara zama yayi ya fuskance ta sosai da kyau don jin me zata fada mai a lokacin kafin ta dago kai tace dashi. Mamud for long ka san da Jafar yana shaye shaye dama ? Maganan tazo mai a bazata saida yadan razana don yasan ta kwabewa kanin nasa ke nan yau tsakanin shi da mahaifiyar su din tunda har ta sanda hakan gareshi. Mami yasha wan, , , , hannu ta sake daga mai tare da dago kai ta kalleshi tana fadin ai tambayan ka nayi kawai ka ban amsa in sani. Ajiyan zuciya ya dam sauke kafin yace gaskiya mami ba zance na san lokacin ba saidai tun kan dai ya tafi Hong Kong nasan da yana dan taba abubuwa kadan ina kuma kokarin tsawata mai ko a lokacin. Sheshekan kukan data sake ne a lokaci daya ya kara tayar mai da hankalin shi sosai har ya mike ya isa gareta da sauri yana fadin. Haba mami kuka kuma at dis stage da jafar yake a kanshi aini ina ganin wanan bai kai abin kuka ba tukun illa a tsaye a fahinci waye jafar a yanzu ? Da sauri ta dakatar da kukan da takeyi din don jin abinda dan nata ya sake fada mata kan dan nata da take gani shine hasken rayuwan da kowa nasu nan gaba. Wanan dalilin yasa take kokari ganin ginashi a kasan nan tun tana raye don ko bayan ta ya kasance suna da bangon dafawa kamar jigon su. Shine hikima da kokarin mami na nacewa da auren shi da yar gidan mamman bello mai ritaya tsoho wanda ke daya daga cikin dattijan kasan nan dake fada aji a arewa. Sai dai shi dan baisan manufarta kan hakan ba duk da ya hango hasken a zancen ta tun farko saidai shi sam baida ra,ayin hakan a rayuwan shi. Yasa ya kaucewa wanan hadin da mami din ke sonyi mai da ko wace yarinya da bashi yaji zai iya zama da itaba a rayuwan shi don kawai wani siri nasa na daban can da bai damu da kowama ya sani ba a yanzu . Muddin dai din ya samu daidai da yadda yake son macen ta kasance a rayuwan shi nan din gaba. Mamud me kake son fada min a yanzu mami ta fada a cikin wani sabon tashin hankali a fuskan ta kuma wanda yafi na farko hadewa. Mami ba wani abu bane dubaga yadda jafar ke samun cigaba yanzu a kullun idan anyi duba ga yadda rayuwa yanzu ya koma ga mutane. Mumunan faduwan gaba ya kara zowa mami din hankali tashe ta furta hakane mamud nayi babban sakaci da damana na uwa a gareku da bana bibiyan bayan al,amuran ku akoda yaushe. Haka kawai daga kwancen yaji ranshi na raya mai yakira layin wayana a lokacin don jin yadda na samu gida da yan uwana. Kiran farko har zai katse yaji an dauki wayan ana fadin bata nan tana waje muryan karamar yarinya da bata kai mace sosai ba ke fadi a wayana. Ke wacece ke maganan ua fada yana dan murmushin da bai tashi yinshi a lokacin na sai yajo tace ni, nice halima kanwar ta. Au halima ya fada kamar ya santa a fili dama , kina lafiya ?, ta amsa da lafita kalau , ina yayan naki ta tafi ya tambaya . Bata fitaba tana nan tana gyarawa innan mu wurine yanzu aka gama fada da inna da lantana saboda wurin girji dan murmushi ya sauke don jin abinda yarinyar ta fada. Kafin yace fada kuma tace eh kullun lantana sai taja innan mu fada tace a raba wuri yana sauraren ta a daidai lokacin yaji wani murya na salati ana fadin yanzu wayan yayan tamu kike jagula halima? Ba jagula nake ba an kirata ne na daga ta fada daga a dan shagwabe amma ke din nan yana ji zasu kaure da fadan su da suka saba yi ko yaushe. Samun kamshi yayi da rashin kashe wayan yana saurare duk abinda ke faruwa har dawowana dakin da mukai magana akan abindaya faru yana jin komai bai kashe ko ya damu da kudinshi da a Ke jayewa ba a lokacin. Basu fada min komai ba tunda na dawo dakin sai da nayi shirin kwanciya barci ne waya ya dauki sabon ringiing a dan daburce na daga wayan, murya kasa kasa ina amsa mai sallaman shi . Don nagane shi duk da ban tubuta mai komai a wurin sunan shi ba har yanzu muryan shice take fadin ke idan ba,a kiraki ba ba zaki taba kiran mutum ba ko ? Ganin har innan mu na dakin zaune yasa na dan saci kallon inda take a dan kashe murya nake fadin kayi hakkuri na mantane ban kira ba. What ya fada da dan karfi har saida na dan razana da hakan na samu da kyat cikin rashin damuwa na sake fadin na mantane bankira ba. Ji nayi ya sake wani wawan tsuki a wayan tare da fadin ke kina da hankali kuwa ? Sai kuma ba bata lokaci yaci gaba da fadi kai tsaye ba tare daya saurari mai zan fadaba wanda dai bai wuce kalman hakkuri ba gareshi a lokacin Ke ki saurareni da kyau kiji may zan fada maki don gobe zamu fara deal din mu na abindana fada maki zai faru tsakanina dake na taimakon junan mu a tare. Don haka goben nan akwai wanda zaizo garin ku da safe daga kaduna zasu diba fili a saya a ginawa mahaifiyar ki wurin da zata zauna tare dasu halimatu fada ya kare daga yau a zauna lafiya. A cikin mamaki na dago kai na kalli inda inna take zaune tare da sauran yan dakin namu dake zaune a lokacin kafin in mayar da hankali a wurin wayan ina kallo a cikon mamakin ji abinda ya fada din. A Ina ma yasan wata halima can na fada a raina muryan shi naji yana fadin akan karamin abu za a dinga batawa inna rai yadda naji tana fadi dazun. A ina yaji wanan zancen na fada a fili ba tare da nasan zan furtan hakan ba yace wacce abin ya dama ta fada min tunda ke ba zaki kira ki fada min ba asan abinda za a kan wana case din. Koda na dago kaina gaba daya dakin idanunsu a kaina yake lokacin suna sauraren meke faruwa duk da bajin maganan sukeyi ba a lokacin. Har ya gama maganan shi na kashe wayan ina kallo da mamaki sa,adatuce ta fara fadin me yaji yayan mu ? Zancen fadan inna da lantana na dazun yake min fada ban sanardashi ba sai ji yayi ke nan yasa wani ya samai ido a kaina a garin nan kome ? Da hannu sa,adatu ta nuna min tsakiyan kan halima take zaune a kusa da ita tana lasan miya a kwanon data karasa cin abinci a lokacin. Itace dazun ta dauki wayan ki da aka kiraki ta fada mai komai yaji inna takai mata magara daga inda take zaune tana fadin waya aike ki mai shegen bakin tsiya da yawan magana. Inna tambayana yayi ina yayar mu nace tana waje wurin da lantana ke fada dake shine na fada mai komai daya faru inna ta karasa a cikin sanyin murya. Yanzu me kikayi ke nan yarnan zaki jawa mutane zancen gori da zunden mu a cikin garin da gidan nan kaf yanzu idan wanan zancen yazo kunnen jama,a ai sai a saka mu a baki. Da kyat na hade wani yawu mai daci da dumi daya taru min a baki tun barin wayan na kasa magana in furta komai sai binsu da kallo da nakeyi dakin duk lokacin da wani yai magana a cikin su. Bayan dogon nazarin danayi na yan mintina da har ya hana inji karshe fadan inna da halima ashe har dukan ta tayi a wurin ban farga ba. Ba komai na tuna ba sai abinda ya fada da bakin shi ki huta kowa naki ya huta ta karkashin ki ayi alfahari dake a cikin yan uwan ki wata rana idan kin daure zama dani yadda nake. Indai hakane na zan gwada in tabbatar da hakan daya fada min din idan har gaskiya yake har cikin ranshi abinda ya fada din a lokacin. To ya zama dole kodan farin cikin mahaifiyata da yan uwana in amince da tasa bukatan mutukar hakan ba zai sabawa addinina ba ko ya taba min mutuncina . Duk da nasan yin hakan wani gangancine nake kokarin aikatawa a rayuwana a matsayina na ba yar kowaba a duniyan nan nasa na tarawa kaina babban ganganci a rayuwana. Haka kawai na dauki waya da sauri na rubuta idan hakan zai zama farin cikin mahaifiyata da yan uwana a shirye nake da inyima biyayya idan hakan bai kauce wa addinin mu ba. Ina gamawa na sake karantawa batare da nazarin komai ba na tura mai sakon kai tsaye ina mai runtse idanuwana a hankali. Muryan inna ne ke fadin wani abin yace ta fada mai ne ko me yafaru ya furta hakan. Ba komai bane inna na bata amsa don hankalinta ya dan kwanta ina kokarin kawar da damuwan dake fuskana a lokacin. Ba zan so mu jefa ki a cikin wani halin rayuwa harda zaki takura ba saboda wanda daga baya za a dawo abin yazo ya damu mutane kuma. A,a inna don Allah ki cire damuwa a ranki kan wanan zancen don shi haka rayuwan shi yake da taimakon na kasa dashi ko yaushe. Allah ya kyauta inna ta fada tare da kaiwa halimatu wani sabon rankwashe akai ta sakr sake wani ihu mai karfi tana fadin inna bansan hakan zai maku zafi bane ai. A daidai lokacin dana tura mai da sakon yana kokarin fita falon mami don ya dubata a daidai tsakiyan falon sakon yashigo mai a wayan shi. Wani irin shu,umin murmushi ya sauke a fuskan shi wanda baisan lokacinda ya sakeshi a fili ba don saurin kamawa da tarkon shi danayi a lokaci guda. Caraf idon shi suka sarke dana mami dake zaune ta hakince tana ba mai aikinta umurni a lokacin. Ya karaso zuwa saman kujera ya zauna a kusa da ita ba tare data samu mai magana ba don ta lula acikin tunane halin da dan nata ya shiga ba tare da saninta ba. Idan ko har akan wanan yar matsiyatan abu kamar wasa ga zance naso ya juye ya zama mata babban magana a rayuwa yanzu kuma. Har yau kan ita mami a daure yake don ta rasa gano me yagano a jikin wanan yar har ya mace haka a cikin sonta . Yarinyar da ba a bakin komai aka dauke ta ba don yar aikine ba wata mai galihu can ba ko asali har yake neman jefa kanshi ga halaka haka ? Saidai maganan babban danta mamud ya kara jefata a cikin zargin dan nata a yanzu don tsoron ta Allah kada abinda dan uwan nasa ya fada ya kasance gaskiyane hakan . Ita dai a iya sanin ta da dan nata tun yana karami komai zayi a duniya zaiyi shine a cikin hikima da fasaha irin na masu hazaka da kwakwalwa. Sai gashi yanzu ta kasa gaskanta zarginta na canza halayen dan nata ga baki daya ga yadda suka san abinsu da farko. Fuskan shi a wayan shi yana duba tun bayan zaman shi wurin hankalin shi ya koma kan wayan mami tana magana da mai aikin da bazaice ga fuskanta ba tunda yakai zaune a wurin. Juyowa mami tayi tana masa duba irin na tuhuma lokaci guda don yadda ta ganshi din yazo ya zauna mata ba wani jin darr din ta ko kadan akan laifin da take ganin ya aikata dole yaji nauyin hakan a lokacin. Jikin shine ya bashi a lokacin da ana kallon shi yasa ya dago kai dan jin hakan da yaji a jikishi. Caraf idanuwan shi suka hade dana mami din lokaci guda sai yaji ya dan tsargu da hakan shima don irin kallon da uwar tasu take mai a lokacin don haka ya dukar da kanshi babu shirin haka saboda nauyin ta dayaji. Jafar may ye matsalakane yane yanzu mami ta fada tana mayar da hankalinta gareshi baki daya don ji amsan da zai bata a lokacin. Amma sai ta lura kuma har ya mayar da hankalin shi ga wayan ba tare da yasan tanayi ba a wurin da kai nake magana ta fada da da karfi tare da nuna bacin rai a fuskan ta. Firgigit yayi tare da sake dagowa yana kallonta yana fadi mami ban jiki bane na dauka da wanan kike ai har yanzu ya dan fada a tsarge. Jafar wai yake damun rayuwan kane a yanzu koka sake shan wani abinne kuma saboda wanan banzan yarinyar daka kwallafa rayuwan ka gareta don jaraba. Nafa gaji da wanan kwanaye kwanayen da kakein a gidan nan aure dai ne nace bada yawun bakina ba sai kasan yadda zakayi da yar mutane tun yanzu. Shiru yayi na dan lokaci kafin ya dago kanshi da yake a sunkuye ya dubeta tare da sake wani guntun murmushi a fuskan shi yana fadin. Mami kina ganin akwai wata wace har zata iya sauya min rayuwana a yadda nake har yaushe na hadu da wanan yarinyar taki da zata sakani wani abinda ba halina ba yanzu. Ran mami ya baci ainun da abinda ya fada a ranta tace mamud yayi gaskiya al,amarin yaron nan yayi girma ban sanda hakan ba kenan. Jafar yanzu duk yarda da amana dana baku ashe akwai wani rayuwa da zaka fada wanda ban san dashi ba a tare da kai har ka boye min kanayi. . ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣5️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU HAR ABADA YAN UWA MUSULMAI ALLAH YASA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA ALLAHUMA AMIN, , , , , , LITTAFIN NAN NA KUDI NA YAR UWA IDAN BAKI BIYA BA KADA KI SHIGA HAKKIN WANI DON ALLAH , , , Zan iyacewa gaba dayan mu dakin mun shafa da zancen zuwa wani bako da yafada a jiyan do bamu dauki abinda muhinmanci ba a rayuwan mu. Sai gashi kawai an kwadawa Abban mu sallama da sassafe ya fita zuwa waje ya dan jima sai gashi ya shigo yana kwalla min kira kamar a kidimance shima yake a lokacin. Da sauri na dago daga saman raggan katifan da nake kwance na sa,adatu data barmi in kwanta don ina bakuwa a cikin mu. Abba ina kwana nake kokarin fadi yayi da Abba ya dakatar dani da fadin yar sani wasu mutanene suka zo min da wani zancen yanzu a waje wai maigidan ki ya turosu daga birni zasu duba fili a nan kusa ko wani wuri za aiwasu aiyiuka ko ? Da sauri na dago kai na dan saci kallon Abba din dake tsaye ya kura min ido don jin karin bayani daga bakina a lokacin. Kai na girgiza tare da fadin Abba ban san da wanan zancen ba gaskiya na fada dan azauna lafiya kada Abba yayi zargin wani abu innan mu ta hada a lokacin. Ko wani zargi yazo ya shiga wanda hakan zai iya jawowa innan mu wani matsala a rayuwan ta tunda ba zanso hakan ya faru ba. Baki da labarin hakan Abba ya fada a cikin mamaki tare da kara kallon yanayin da nake tsaye kafin yace ikon Allah . Ya juya ya tafi ya barni a wurin runsunne kafin in tsinkayi muryan lantana daga sashinta tana kwalawa Abban mu kira da dan karfi kamar tana bashi umurni. Abba dake a rude a lokacin bai samu amsa kiran nata ba sai fita da yayi zuwa waje ya nufi gidan dan uwansa a nan cikin unguwan namu. Hakan baiwa Lantana ba naga ta yafa zani ta bi bayan Abban sai dai ganin bakin datayi a wajen gidan namu wanda wata kila ta firgitane da ganin fuskokin su a lokacin. Sai gata ta juyo da sauri ta dawo cikin gidan dama da daura gaba kawai ta dan yafa wani ragga a kanta tana rike da danta a hannu jalo jalo, ta fita daga gidan . Ba kunya ta nufi sashen Asabe don gulma innan mu sai aikinta takeyi ba tare data mayar da hankali ga abinda ke faruwa a gidan ba lokacin. Bamu san meta fadawa Asabe ba mundai ji Asabe na fadin subbahanallahi da safen nan haka baki a cikj bakin kaya idan dai ba wani yai masa cune ba aka turo akama min shi. Umma lafiya inna ta fada a daidai lokacin da Asaben ta fito a rude daga wajenta lantana na binta a baya. Ina fa lafiya yanzun nake jin mugun labari a bakin yar nan wai wasu baki da bakin kaya sunzo sun tasa dan nan a gaba zasu tafi dashi. Anya kuwa umma haka zancen nan yake yanzu fa ya fita nan naga ya kira yar sani yana tambayan ta wani magana kafin ya fita. Koma dai menene barin leka wajen in gananwa idona abinda ke faruwa dashi din haka tunda safen nan. Bayan fitan Asaben itama sai gata taja ta tsaya don irin mutanen da suke wajen gasu Abban mu a gefe daya tare da wasu yan unguwa suna magana a tsanake. Haka asaben ta fita tana ratsa mutane a dan gigice tana tambayan abinda ke faruwa ba wanda ya koma ta kanta karshe ma suka kwasa suka shiga mota zuwa gidan maigari. Nan suka bar asabe tare da wasu yan tsirarun mutane a wurin yan gulman da basu gane komai ba ala dole ko sai sun gano hakan suji kwam. Sai kusan sha dayan rana mudai tun muna saka rai da dawowa Abba har muka koma daki don mu karya masu wanka kuma suka shiga yin wanka don ka,idar innan mu ce tasa ruwan wanka kowa yayi wanka kafin rana ya dago. A wanan lokacin ne Abban mu ya dawo gidan ko yanzu shigowan ujula yayi yana kokarin fita daga gidan Asabe ta dakatar dashi. Abban ya dawo tare da dan mata bayani a takaice tare da fada mata cewa umma ba komai bane sai alheri haihuwace ke kokarin nuna dadin ta a gidan nan yau. Do yaron nan mijin Abu ne ya turo a sai fili a kusa damu nan za, ai masa wani aiki a wurin wanda bansan me za,a gina maiba amma dai aiko maiye dai karuwa mune ai. Hakane inji asabe ta fada tana gyada kai alaman gamsuwa da maganan shi tana fadi ikon Allah . Akan ya mace ne wanan baiwan ya sauka a gidan nan haka duniya kabar mutum a inda ka gansa don baka san baiwan da Allah yai mar ba. Ranan dai mutanen basu bar wurin ba saida suka tabbatar da an fara aiki yadda suke so sukayiwa kowa sallama suka bar garin da yamma lis. Injiniyan sa zaiyi aiki da ma,aikatan shi aka bari bayan sun samu masauki inda zasu zauna ko washe gari haka suka tashi da aiki wanda hakan ya jawowa mutanen unguwar mu ciniki a wurin su da safen . A kwana biyu da fara aikin kwantsan saiga shi a garin yazo dagashi sai wani abokinshi saikuma security dinshi da yazo dasu inda kallo ya dawo garesu. Zatinshi, izzashi da wayewa da kamala uwa uba ilimi da isa ya kara hakashi idon duk wanda ya ganshi a lokacin . Duk wanda aka fadawa wai shine mijina bai yarda don sam ansan shi din ya wuce ajin aurena saidai idan an masa dole a kaina sai ya aureni da wata manufa dai. Zancen zuwan shi yabi gari lokaci daya duk wanda yasan da hakan saida ya tofa albarkacin bakin shi kan zancen auren kowa da irin abinda yake fada kinsan kauye da samun magana. A ranan bayan ya gama ganawa da iyayyena tare da zaga aikin ginan da akeyi babu kama hannun yaro don kudi na shan kashi sosai ga aiki ga kayan aiki sai shigo dashi ake tun ranan da aka fara aikin. Ganin zuwa matar malam illiya yasani shan jinin jikina sosai don abinda malam din ya fada min ranan da naje gidan shi din. Ba wani bata lokaci muka hada tafiya inda halima ta nace saita bini nan dai aka kwasa sai karshe aka yarda mu tafi tare idan matar malam zata dawo su dawo tare. Ba takura ga zaman mu don motar mu daya ni matar malam da kanwata motar daya sai scurity din dake gaban motar a zaune tare damu. Munbar kauye da zance a bayan mu tafiyan dan lokaci ya kaimu kaduna na dauka ba zamu tafi gidan mami ba kamar zuwan mu. Sai gashi mun sauka a gidan inda muka samu Nazifa da anty salma kawai a gidan Rufaida bata nan sunce bata faye zama gidan ba yanzu sosai. Sunyi matukar mamakin ganin mu a lokacin saidai sa yake a tare muke dashi daga mu harshi babu fuskan yun wani zance a lokacin . Na dauka zama kwana kaduna sai baya munyi sallah munci abincine anty salma ta shigo tana fadin wai ya J yace mu fito zamu tafi. Ba a cikin wani sakewa muke ba dukkan mu har anty salman da take min kallon mamaki a fakaice ta kasa ko dan sakewa damu Nazifa kan tun ganin farko da mukai mata a falon ban sake sakata a idona ba har wanan lokacin. Rufaida dasu Ruby sun zo gidan gulma sun samu mun wuce don ko mami dake Abuja har labarin zuwan mu gidan ya isar mata a lokacin. Sai ashar ta kundumawa dan nata damu tare da fadin a fada mai maza mu bar mata gida kafin ranshi ya kaiga baci. Ba wanda zai iya fada mai sakon har muka bar gidan don dama da abinsa zaiyi a kadunan yasa muka tsaya a nan. Karfe takwas na dare muna a cikin wani rantsetsen gida da ban san ko a ina wanan gidan yake ba haka mudai namu idone kawai. Alhamdullahi komai a kwai a gidan babu ne kawai babu ga gidan da girma duk da darene bai hana mu gane hakan ba. Irin su cultizen su club ko Iliminaties, dai da sauran su ai zubur mami ta dago tana fadin what, what, mami ta kara fada tana gyara zama jalal yace yes of course mami don yanzu ai kinsan duniya saida wanan kuma muddin sunan har zaiyi fice ka kaiga wani matsayi nan gaba. Kirji ta dafa tare da fadin innalilllahi wa inna,alaihim rajin sai ra hada da mikewa tsaye a daidai lokacin kuma shi ya mamud ya shigo falon tare sa jamal. Jalal ke fadin mami nifa bawai nace hakan bane naga kin daga hankalin ki sosai kwatance kawai nayi maki ai da hakan ya fadi a cikin damuwa. Mami kan ta shiga wani hali a lokacin don bata masan me take fadi a gaban diyan nata ba a lokacin. Mamud naci amanan mahaifin ku nayi sake da zamani ya cuceni ta fada tana komawa zaune yarfan saman kujera a cikin wani irin yanayi na damuwa da tashin hankali. Jalal ya mamud ya kalla tare da fadin kai wai meke faruwane hakane naga mami a wanan yanayin ? Ina fa daki kwance yazu ta kira ina zuwa take tambayana wai irin su culties din da turai da saura Asian countries ke sashi nake mata bayani shine na ganta a hakan ? Da sauri ya juya inda mami take zaune yake fadin haba mami hakan ai ba kyau ki fara zargin dan cikin ki da kanki har duniya ta zarga mai hakan akan shi. Mamud idan har jafar ya kasance a cikin irin wanan kungiya bazan taba yafe mashi ba a rayuwana ku sani. Haba mami ki bar wanan magana don Allah ko akan dan wani ne balle naki yana illiminaties zai dinga sallah jamal ya fada . Da sauri ta mayar da kallonta gun jamal din tana fadin Allah yasa hakan ne jamal na shiga uku da wanan yaron abinda ban taba zato da tsamani ba a cikin zuriata yana kokarin faruwa dani haka. Jin sam batun na mami yai yawa yasa ya mamud dagowa da sauri a cikin bacin rai yana fadin kai jalal take her to her room kai jamal zo muje ya fada tare da fara tafiya. Jamal din ya mara mai baya nan suka bar mami da Jalal yana kokarin lalashin mami din don ta daga su shiga part din ta su kaucewa idon yan aikin gidan a falo. Ranan dai haka suka kwana a cikin tashin hankali a don kosu hankalin su a tashe yake kan wanan zancen sabanin mu dake gidan nasa tsundum ciki zaune sai damuwa da kewan gida kawai a lokacin ne a ramun babu wani tunanen komai a tare damu. Kusan zance zuwa da matar malam.yai min dadi don sai ta zame min kamar hjy data tafi ga kuma halima da ba abinda ya dame ta a rai sai faman zuba surutu da tambayayoyi da takeyi hankali kwamce tana ci da sha duk ko da dare ne muka shigo gidan bai hanata bude ciki ta dura abinci ba. Duk da munga shigan shi gidan a lokacin hakan baisa ya kwana nan tare damu ba gidan mami ya wuce ya kwana a can kamar yadda ya saba kwana din . Da safe dan uwan shine ya tayar dashi daga barci ta hanyar buga mai kofa ya fito da mamaki yake kallon ya mamud din dake tsaye a kofa ciki damuwa. Lafiya dan uwa ya fada bai bashi amsa ba tasa kai zuwa ciki dakin kai tsaye ya bishi a baya daga inda ya barshi tsaye a kofa . Zama sukayi suna fuskantar juna na dan lokaci kafin mamud di yace kai abubuwa fa suna son baci a bangaren mami don yanzu kokarin zarga wani zance takeyi. Daga baya ke nan ya fada yana mikewa tsaye don ni yau zan bar kasan nan da dare zan koma baki aikina ba zan dawo ba sai yarinyar nan ta gama zana exam din ta zanzo in tafi da ita. Ya zakayi da mami mamud ya fada yana kallon dan uwan nasa yace cikin ko in kula akan mefa ? Komai ma kana ganin zancen nan data dauko zata barka ka koma idan kuma har ka tafi kabar yarinyar nan baka gudun wani abu ya biyo baya . Wani abin me zai biyo baya matace fa ba zaman kowa takeyi agarin nan ba yanzu sai zamana don haka duk wani mataki daya kamata na dauka akan hakan na riga dana dauka a yanzu ko. Saida ya mamud din ya dan kurawa kanin nasa ido na dan lokaci kafin ya ware hannayen shi yana fadin shike nan har idan ka shiryawa hakan ai ba matsala. A shirye nake ga duk wani barazanan da mami zata iya kawo min kan wanan matsala ya kare da fadin OK ga dan uwan nasa sai ya gyada mai kai alaman gamsuwa. Bayan fitan dan uwan daga part din shi ya dade zaune a wurin yana dan tunane a ranshi kafin ya mike ya shiga bandaki ya watsa ruwa jikin shi tare da shiryawa kafin ya fito. Kai tsaye part din mami ya nufa daga nan dakin yana rufe yasan tana gida don babu inda take fita idan ba wani dalili ba a irin wanan ranan ta jumma,a. Da sallama a bakin shi ya turu kofan tare da dan rike hannun kofan kafin ya sake turawq ya shigo cikin dakin gaba daya. Tana zaune a cikin shirin ta na doguwan riga leshi sai mayafin kayan dake saman jikinta da alama dai shirin fita take a lokacin itama duk da baranan fitan ta bane yau. Tunda mami ta hango dan nata taji gabanta ya fadi don kwarjin sa sai kara fita fili taga yana mata tunda zancen auren nan nasa ya taso . Wanda take gani a yanzu zancen sa ta fara zargi nasane ya fara baiyana mata hakan gareshi don wani asirttacen baiwa nasa da yanzu ta kara hangowa gareshi. A hankali ya kai zaune a gefenta yana kamo hannunta tare da fadin mami antashi lafiya ya gida ya aiki ba tare dajin shakkar komai ba. Cikin basarwa mami din ta jaye hannun ta tana fadi kalau nake tunda yanzu kana ganin kakai ba zaka iya bin umurnina ba koka fada min idan zakai abu. Jiya me ya kaika kaduna ba tare dana san zaka shiga ba sai kawai wai inji kana min gida da wanan shegiyar yarinyar kauyen. Yasa na ce ace kabar min gida tun kan na bata ma rai daga kai har ita sai in saba maku ba wani aiki bane gareni hakan. Mami ai ba wanda ya fada min sakon ki sai yanzu nake jin hakan garwki but iam sorry hakan ba zai sake faruwa ba insha Allah. A hankali ta lumshe ido cikin jin wani irin yanauin amsan daya bata din a cikin rashi damuwa da furcinta garshi ke nan. Yau kaduna zan tafi ta bashi amsa tana mikewa daga inda take zaune lafiya dai mami zaki tafi kadunan ya tambaya cikin son jin amsan da zata bashi. Eh akwai abinda zai kaini mai muhinmanci can yau din idan na gama da wuri yau din zan dawo garin nan. Tana magana a cikin wani irin yanayi dake nuna akwai abu a zuciyar ta sake damun ta a lokacin shidai shiru yayi bai tankata ba a lokacin yana zaune a inda ta barshi. Saiga jalal ya shigo dakin kallo daya yaiwa yayan nasa ya kawar da kai a cikin tsarguwa mami take fadin dauki jakkar can fita min dashi gurin mota kafin in fito. Ok mami ya fada ya nufi jakkan ya dauka Allah Allah yake ya bar dakin a lokacin don a tsarge yake kada yai laifi a wurin yayan nasa kuma don ya dauka mami ta fada mai komai zai zargeshi. Bayan fitan dan uwan da kaya shima ya mike yana fadin mami Allah ya tsare hanya ya dawo daku lafiya sai dai yau da yamman nan na nake son in, , , , , Jafar wani kungiya ka shiga da ban taba sanin kana a cikin wani hali ba sai daga bayan nan nasan da hakan tare dakai ba. Mami kungiya kuma name ya fada yana kallon ta a ciki mamaki karara a fuskan shi don jin abinda ta fada mai din game dashi. Wani cultu kakeyi jafar don jikina ya bani wani abu a game dakai ba dadewan nan ba. Mami ya fada a cikin mamaki tare da fadin cult kuma ai da ina cikin wani cult din daba haka ba da yanzu na wuce sanin kowa a kasan nan ni wanan baya gaba ko kadan ya fada yana hade rai ya nufi hanyar fita daga dakin ta bishi da kallo kawai da nazari a zuciyar ta. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣6️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU YAN UWA TARE DA KARA BAKU HAKKURI DA YANAYIN DA LABARIN YAZO MUNA SABODA KARATUANA A YANZU DON ALLAH A KARA GAKKURI DANI YAN UWA NAGODE, , , , , Zan iya cewa tunda gari ya waye ban leko waje ba daga dakin da muke ciki zaune mu uku din kamar muna gidan kaso don tun shigan mu gidan muka shiga sakin ba wanda ya fito daga cikin mu har halima dake daukin zuwa abuja din a lokacin. Sai gata baki ya fara mutuwa tun ba,aje ko ina ba a lokacin tunda taji matar malam na fadin Allah ya cecemu da wanan gidan har za a yanka mutum a bizzime ba,a san an yanka kaba. Hankali halima din ya fara tashi tun jin furcin Maizube matar malam din muna zaune ga gari ya waye zugun zugun a dakin da muka kwana din wanda shima munsan da zamu kwana ne ta hannyan kai muna kaya dakin danaga anyi yasa na jasu zuwa dakin muka shiga. Kofan aka kwankwasa wanda yasa kusan lokaci daya muka dago kai zuwa kofan kafin a sake nocking na biyu wanda yasa nayi karfin halin mikewa zuwa kofan lokavin guda . Na bude tare da kallon wanda ke bakin kofan a lokacin shine yana tsaye yabawa kofan baya ta hanyar saka hanayen shi a ciki aljihun wandon jikin shi. Wanda jin karan budan kofan shima a lokacin yasa shi dan juyowa zuwa gun kofan mukai arba dashi da sauri na zube kasa don girmamawa ina gaida shi da kwana. Bai amsa ba sai cewa da yayi zaki kashe mutane karfe sha daya ake nema baku fito kun karyaba har wanan lokacin haka ? Dan daburcewa nayi na rasa me zanyi a lokacin don rudewa da nayi yau shine a gaba muke magana haka kai tsaye dashi sabanin da can da hjy kan muna shamaki a tsakanin mu. Zasu fito yanzu na samu bakina na fada lokaci guda na fada ya juya ya bar kofan kamar maiyin sauri kada wani ya ganshi wuri lokacin. Dakin na koma tare da fada masu abinda yace sai maizube ke fadin aiko nan ma aka kawo saimu karya ko. Ciki da daurewa nake fadin kinsan su a table ake karyawa nan saboda haka mu fita zuwa falon inda zamu karya din yanzu, don yana fada wai naki fitowa daku can ku karya. Maganan da maizube keyi yanayine dake nuna alaman tsoro da karfin hali a lokacin don gaba daya ta gama tsunkewa da al,amarin gidan ga baki daya. A takure dai kowa yake haka muka iso falon dana lalubu muna inda dinning din yake da abunci a jere sama shi a aje muna. Dole na nemo karfin hali da jarunta lokaci guda na sakawa kaina don kawai halimatu da matar malam da kiris suke a lokacin su fasa ihu a gidan don tsoro. Basu ba ni kaina duk da zama a gidan mami ya taimaka min matuka saidai duk da hakan wani abu ban san shiba a gida wanan ne farkon ganina a gida nasa. Abinci ne mai rai da lafiya aka shirya muna don karyawa wanda nasan halin yadda ake abin karyawa nawai don mu din bane yasa aka shirya hakan . Kawai dai haka abin yake a garesu ko yaushe dan magana halima tayi min na zuba mata harara daga inda nake take fadin yayan mu duk wanan mu zamuci duka ? Na watsa mata harara tare da cigaba da kurban tuwan shayin da nake kurba a lokacin a hankali duk zuciyana ina ji wani irin yanayi a lokacin. Text ya shigo min a wayana na dan saci duba a hankali ko daga waye duk da wayana layin mutum.dayane a cikin sa lokacin. Ki bisu a hankali kada ki takurawa bakina a gidan nan yin hakan yana cikin bin umurni na a yanzu kiyi duk abinda zakiyi su kwantar da hankali su gidan nan da kowa, ya rubutu min saida hakan ya ban mamaki don ban san a inda yake tsaye yana kallon mu ba alokacin. Ki dibi duk abinda ranki ke so a gurin nan halimatu duk namu ne do mu aka ajeshi a nan na bata amsa a cikin dan wayen cewa da fuskana kamar babu komai a raina. Ba laifin sun sake jikin kamar yadda ya kamata sunci abinci daga nan bamu koma daki ba a kokarina na bin umurnin shi a lokacin kamar yadda yace din. Sai zuwa karfe daya saura ya shigo suka gaisa da maizube matar malam kamar yadda muke jin a gida kowa na kiranta da wanan sunan na maizube matar malam. Ba wani sakin fuska ko sabo a gaisuwan ya mike tare da fadin halimatu zo naji mana ya fada ba tare da ya tsaya ba na kalleta itama ni din take kallo da mamaki tare da jiran umurnina . Dan dukar da kaina kasa nayi kafin na dago na kalleta ta mike don ta gane me nake nufi da hakan daga kallon ta danayi din. Tun ina zuba idon ganinta har na dan far tsoron haka sai gata tare da security din gidan niki, niki da kaya ana shigo mata dasu cikin gidan. A hankali na sauke ajiyan zuciya tare da bin kayan da ake shigo dasu da kallo inda na dan fahinci wani abu a lokacin. Maizube tana gefe a zaune itama dai ba sai an tambayi damuwa a yanayin nata ba lokacin har zuwa lokacin da suka gama shigo muna da komai acikin gidan. Wata mace tayi sallama ta shigo da fara,a a fuskanta ta zauna suna gaisawa da maizube tare da muna bayanin itama a gidan zata zauna tare damu . Itace wai mai aiki kula da komai yadda ya dace da fatan zamu ji dadin zama da juna yadda ya dace ta kare da fadin . Itama dai musulmace yar uwan mu don haka mu sake jiki da ita don Allah don komai ya tafi daidai a gidan. Abubuwan dake faruwa a lokacin koda nake yarinya mai san karancin shekaru da ban wuce sha shidda ba na dan fahinci wasu abubuwan a lokacin saboda natsuwa da fahintar dake gareni . A waya yai min bayanin komai yadda zan fahinta daga kayan har yadda zamu zauna da matar data gabatar muna da kanta a matsayin mai kula da gida ya min bayani tare da ja min kunne akan komai. Yana fadawa halimatu a ranan zaiyi tafiya bata fada min ba sai bayan mun sallame sallah a azahar tana muna hira fitan su da inda sukaje ashema ba tare dashi suka fita ba da wanan bakuwar matarce ta sayo muna kayan nan da akazo dashi gidan. Kallom halimatu nayi tare da fadin yau zai koma ina ya fada maki halima tace yace wuri aikin shi kuma wai muyu karatu sosai kafin ya dawo. Na dauka shirmen halimatu ne sai gashi da yamma kawai ya shigo yana sallaman maizube da niyar zaiyi tafiya a ranan zai dan jima bayana nan . Ta shiga jero mai addu,an neman tsari da kariya a gareshi da alaman yaji dadin hakan don irin alherin da ya aje mata yana karbawa da amin ya mike. Ta kalleni tana fadin wai nikan ba zaki bishi baje harda kinji zaiyi tafiya kina zaune a daki kinki ki motsawa tun dazun. Ba don naso ba dole na mike nabi bayanshi kamar yadda tace dani din inyi sai gashi har muna kokarin cin karo dashi a kofan da sauri naja dan baya kadan kada mu gwaure . Ya lura sarai da yanayin kaduwa dana shiga na kaduwa dana ganshi a gabana lokacin. Tsadadiyar muryan shi ya ratso dodo kunne na yana fadin lafiya ina zaki tafi ko wani abu kike nema ne ? Dan dukar da kaina nayi kasa tare da fadi a cikin dan damuwa dama dama dai na fito ne don in sallameka kawai ina wasa da yan yatsun hannuna duka biyu nake magana. Yana tsaye yana kura min ido yana kallona tare da dan sake murmushi a fuskan nnasa tare da dan gyara tsayin sa dakyau har lokacin idon sa a fuskana. Kamar aafalki naji muryan shi again yana fadin to ai gani saiki sallameni din inji tunda ke baki san abinda ya dace ace kinyi ba. Kada ki manta komai da zamuyi a tsare yake a kan mu ba tare da kowa ya fahinta a gidan nan ba ina nufin kuwa har wanan yar aikin da zata zauna daku ba zata fahinci zaman mu dake ba kawai dai a matsayin mata da miji masu kula da junan su kowa zai dauke mu. Na dago kai da sauri na kalleshi do jin abinda ya fada din sai yayi daidai da idon shi a kaina ya daga min gira da kafada tare da fadin idan kinyi hakan kin taimaki kanki. Yana fadin hakan ya juya ya wuce ya barni tsaye da mamaki a wurin don na kasa fahintar inda zancen shi ya dosa a lokacin. Gashi ba wai wata kawa ko abokiyar hira ke gareni ba a lokacin da zan kaiwa shawara na har mu gane me hakan ke nufi da zancen shi a kaina. Ance idan bawa yana son walwale al,amari shiafi yawa haka yafi zuwa mai a daidai tsakiyan sallah don sai shedan yaso ya shagal dakai daga barin sallah ya hasko ma abinda ya shige ma duhu a lokacin. Nima kusan hakan ne ya faru dani a daidai sallah la,asar danazo yi don yanayin damuwan dana shiga yasa na tayar da sallah a vikk kuncin zuciya. Tiryan tiryan abinda yake nufi kr zuwa min a rai na har da wanda ban san zankai ga tunane ba saida na fahinci komai a lokacin. Sheda kenen yaso ya ribanceni ta hanyat bata min sallah a lokacin na farga da hakan da sauri na mayar da hankalina a gurin ibadana. Bayan na idar ina zaune wani shu,umin murmushi mai hade da sautin dariya yazo mi lokaci guda . Hannu na daga tare da yiwa Allah godiya akan haska mi hanyar dayi a lokaci daya. Sai muryan maizube ke fadin lafiya dai yar nan daga idar da sallah kin soma dariya haka kamar an maki bushara da aljanna. Karfe shidda saura kiran shi yazo min na sameshi na falon shi duk sa bansan wurin ba haka nayi kokarin mikewa zuwa amsa kiran nasa. Yana zaune a cikin shiri shi sai kamshi ke tashi ko ina a falon na shigo da sallama a bakina ba dauka ya karba hakan ba don ba lale bane ya amaa din. Banyi gigin hawa kujera dake falon ba a lokacin don haka naja nakai kasa zaune dan nesa daga inda yake hankalin shi yana gun abinda yake a system din shi yayin da falon yai shiru na dan lokaci kamar babu kowa a wurin. Kafin yadago kai yana fadi a uzurce OK kinzo ko tare da dan lumshe ido ya sauke su akaina a hankali kamar yana nazarina a lokacin. Yau zan tafi kamar yadda kikaji na fada dazun wa mama don haka komai na kula sa gidan a yanzu zai dawo karkashi ikon ki a garin nan. Duk wani kokari idan kinga dama ta yadda ba wanda zai fahinci meke tsakanina dake a wanan zama namu yanzu. Yanzu wasan mu zai fara don a bayana abubuwa zasu faru da dama na sani saidai idan kin iya tsirar da kanki abin zaizo mako da sauki ko yaushe. Da sauri na sake dago kai na dan kalleshi inda yake zaune din yace yes daga ni sai ke muka san irin zaman da zamuyi a tsakanin mu a yanzu. Barazan mami ko wani dan uwana kada ki yarda ya kaiki ga furta masu komai dake tsakani mu ki tsaya kaida fata a matsayin matana kike a gidan nan barazan wani ko wata ba zai fitar daken ko ya tsoratar dake ba garesu. Kaina gyada a hankali don ganin yana maganan ya tsureni da idanuwa shi idona suka dab ciciko da hawayen nadama . Don tabbas na jefa kaina a tsaka mai wuya duka bangare biyun da nasa dana mahaifiyar su din dama wanda ka taso daga baya. A hankali ya lumshe idsnuwan shi tabbas tausayin yarinyar ya kamashi don yasa ya jefa yar mutane a wani hali . Wanda rashin wayau da ilimi ya kaita ga yarda da bukatan shi a kanta ba tare da nazari komai a game dashi ba kuma. Yace kada kiji komai ba zasu iya illanta min ke ba dan kina a cikj matakan tsarona ta ko ina muddi dai kin iya kanki da bakin ki ko yaushe. Ba tare dana iya furta mai komai ba na sunkuyar da kaina kasa hawaye na ci gaba da zuba min a hankali. Shigowan yaron shi da shima na gansa a cikin shirin shi da alaman tare zasu tafi ke na tafiyan. Ganin yadda nake zaune ina hawaye ya da kalle ni ba tsamani ko zato naji yana fadin lafiya take wanan kukan haka ko an mata wani abin ne kuma ? Bai bashi amsa ba sai mikewa da yayi tsaye yana gyara kayan jki shi tare da fadin zamuyi sallama da ita ka bamu wuri ya fada mai ba tare da kallon inda yake ba yana daukan kaya. Haka ya fita daga daki ranshi bace yana dan satan kallona a inda nake kamar mai tuhumana a lokacin. Murya shi naji a daidai inda nake tsugune ina hawaye yana fadin zainab al,amarin mai girmane ba zaki gane ba a yanzu sai nan gaba zaku gane manufana. Sai dai ya yanzu ke din kanwa ce a gareni zanso ki rikeni tankar kece Aisha na da muka fito ciki daya da ita wurin kulla da amanata da komai nawa. Idan ki mun hakan na maki alkawari har abinda baki zata ba a rayuwan ki bikatana kawai ki nuna ma duniyake din matatave ta suna kuma yar uwata a badali. Kin min alkari hakan ya fada tare da dan tsugunowa saiti inda nake makure ina kuka kafin in magana aka turo kofan tare da fadin kasan fa jirgin mu takwas zai daga kana nan tun dazun. Kabar falo nan na fadama ya dan fada a hasale tare da nuna mai kofan a ciki zafin rai da sauri ya juya ya fice shima bai tsaya din ba ya mike tare da fadin ga key din daki nan zamu dinga waya duk abinda kike so zaki iya fada min idan na kiraki mu zamu tafi. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣7️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA ALLAHUMA AMIN, , , Duk yada naso na boye damuwana a lokacin nayi iya kokari wurin boye hakan saidai hakan bai samu ba don saida maizube ta fahinci hakan a tare dani . Sai gashi ta koma lalashina wai a zaton ta saboda tafiyan ya jafar dinnne nake haka idanuwa da suka hau saboda kukan nadama danayi a lokacine. Ba komai yasani wanan kukan ba sai fahintar inda na jefa rayuwata dan kawai tausayi da biyayya ga ya jafar din da yake zaton don deal din shine na yarda dashi da bukatan shi gareni. Saidai kuma a yanzu kalaman shi sun fara jefani rudani don ban san a matayin da nake a garshi ba da wanan tunanen ya barni a gidan suka daga zuwa inda yake aiki. Ranan kan mami tayi fushi sosai Allah ya taimaka a gaban hjyn taya kira yana sheda mata zancen tafiyan shi inda ta haushi da sababi saidai ta makara ga hakan don yana shiga jirgine ya kirata. A zaton mami din tare dani ya wuce don idonta ya rufe a wurin har take ikirarin da sai dole ya dawo dani kasan nan inma don hakan ne ya guje mata din. Aikin ma gaba daya zai bar can ne ya dawo nan kasan kusa da ita inda take iya ganin komai da yakeyi din a gabanta. Saidai mami bata san da ta makaro ga hakan ba gareshi don a yanzu kan ba zata iya taro dan nata ba kai tsaye yadda take so din tayi. Wai ke iyami yaushe kika koma hakane hjy ta fada a hasale daga gefenta ta dora da fadin zaki raba auren da Allah ya nufa sai anyi a tsakanin su ne ko me ? Ta dago don fadin abinda ke a ranta hjy ta katse ta da fadin yadda kike zaton zaki iya yiwa danki baki ko ki tilasta shi ya saki yarinyar nan. Ki tuna nima hakan ina da hakkin da zan tursasa ki a kanshi dan ni dince dai na haife ki ai . Hjy yarinyar nan bawai sonta yake ba ko wani abu shima dole da akwai abinda yake nufi da yin hakan a zuciyar shi tunda bawai sone ya hadasu ba ai. Iyami bana sonki da shiga tsakanin yaran nan wallahi wararana kunyan hakan zakiji da kin daure kinba yaran nan goyon baya a yadda yakeson abinsa . Da Komai da zaiyi ai dole ya fada maki ko ya sanar dake amma zuciyar ki yana rudin ki kin hana kanki sakat da nasu haka . Karfi da yaji kin hana yaron nan ya zauna ya huta a zuciyar shi balle kiji sirin zuciyar shi kinsan irin illan da kike jawa kanki ga yin hakan da kikeyi kuwa. To idan ma har baki sani ba gara ki san abinda kikeyi ki bar yaran nan hakana idan ko kinki kin tsaya kina jayayya da ubangiji ne . Sai Allah ya dauke ki a zauna lafiya ayi kuma bada ke din ba kinga sanadin hakan sai sauran diyan naki su zauna a marayu ke nan ba uwa ba uba garesu kuma. Ina kema idan har talaucin yarinyar nan ne damuwan ki a haka uvan yaran nan ya aureki baki da komai a tare dake ilimin ma a gidan sa duka kika same shi ai. Jikin mami yai sanyi ga abinda hjy ta fada dan tabbas kawar da ita din ba komai bane a gurin ubangiji ai. Ganin tayi shiru hjy taci gaba da mata nasiha sossi inda take fadin ki kyakeshi da abinsa inma har akwai abinda yake nufi da hakan ai lokaci zai fadi hakan ga kowa. Jalal da yanzu ya zama dan gaban goshin ta yana zaune a gefe yace mami gaskiya hjy ta fada ya j ai ba yaro bane yanzu. Yana da right din da zai zabawa kansa abinda duk ya dace dashi kuma ai kinji hjy ta fada kila daddy mu ya biyo a wurin zabe shima. Ran kwashi takai mai saida ya dafe wurin don zaifi tare da fadin aini na bar wanan zancen yanzu tunda na gane gaba daya kuna goyon bayan sa a yanzu kan hakan tunda yanuna maku yana da kudi da zai iya yin komai. Ni kuma wallahi bana rsoro ko shakkar sa idan da ya biyo ta hanyar arziki dani zai iya hakkura dashi a hakan yaje yayi abinda yake so din ai duniyace dai ko , ? Baki zaki masa ya kara lalacewa ko mai idan ma kin masa din dake dashi duniya zata zaga ai hjy ta kare magana a cikin zafin rai. Har suka dawo abuja mami bata kara tayar da zancen komai akan da nata ba ko ni do tana zaton tare muka tafi dashi hakan yasa fushinta ya kara karuwa a zuciyar ta saidai batayi zancen da kowa ba kuma. Sannu a hankali muka fara sakewa da wanan matar da ta gabatar muna da sunan ta da anty Fadila kamar yadda muke kiranta dashi. Don da safe zata shigo har dakin da muke su gaisa da maizube ta dan ja halimatu da fira tun bamu sakewa har muka fara sakewa da ita a yinin farko da mukayi tare a gidan. Sai ya kasance duk abinda zatayi zata kirani muyishi a tare da ita a cikkn sakewa da kulawa kamar uwar da ke koyar da yarta wani ilimi na duniya a yanzu. A cikin hikima da basira take koyar dani zaman duniya da tako aka komai da rashin saka ido ga wani ko wani abinda bai shafeni ba can zamu zauna tana da bamu labari da zai dauke muna hankali ga komai. Sai gashi mun dan sake da ita har ina iya tambayan ta abinda ya dan shige min duhu wani lokaci tayi min bayani akan komai . Tun Saturday ta kaimu saloon aka wanke min kai akai kitso shiga school monday driver ya kaimu school don fara shirin jerabawa. A school di muka hade da yaran ya mamud wanda a wuri su ne mami ta samu labarin ina kasan bai tafi dani ba ashe . Tayi mamaki matuka don jin hakan koda ta tura ai mata bincike sai ta gane ina zama da fadila ce inda ta zaci ko wani alakane a tsakanin mu bata danta bane ya hada mu. Inda ta gano ko waye Fadilan da kuma aikinta saidai ta kasa fahintar komai ta kawo ido ta saka a hakan don nasihan da hjyn ta tayi mata a kanmu. Wanda nasan Allah ne ya dorani a kan mami din ta basar da zancen binciken komai a kaina har na samu daman fara jerabawa hankali kwance. Yanzu kan ina waya da innar mu tun zuwan mu sabanin da cab da dif idan mun tafi har take fafa muna ginan da akayi a gefen gidan mu itace ashe aka ginawa gidan da zata zauna a ciki. Inda sa,adatu take labaranta muna abinda ya faru bayan angama aikin ginan dayasa a ginawa innan mu sai lantana ta fara bala,i akan bata yarda da hakan ba dole sai Abban mu ya san yadda za a yi itama ta shiga ko a gina mata nata sashen da zata shiga. Wani wan mahaifin mu kuma makwabcin mu ya fito yana fadin baki isa ba lantana don arzikin yartane ya kaita ga hakan don babu abinda baki fada akan tafiyan wanan yarinyar birni. Yanzu da tafiyan ya kai ga alheri gare ta zaki fito kice ke baki yarda da hakan ba dole sai mijin ku ya dauki mataki a kan hakan wani irin mataki kike son ya dauka kan haka din a yanzu ? Ko so kike yace ba zata shiga ginan da arzikin haihuwan ta ya jawo mata ba ta dalilin diyar ta data haifa . Yanzu sai kije can ke mai haihuwan diya maza ki jira su girma kema su gina maki naki ai don Allah ba ai mashi ganganci ga hukumcin sa. Idona ya kawo ruwa lokaci guda da take muna wanan bayanin ban karasa sauraren abinda take fada ba na kashe wayan . Zama nayi cike da nazarin wanan abinda ya faru da innan mu din wanda a sanadiyan na da abindana jefa kaina a cikin sa wanda bansan ko me hakan ke nufi ba har yakai innan mu din ta fara samun saukin rayuwa a tare da ita. Don haka ya zama min dole in jure duk wani kalubalin rayuwan gidan dan mami dana mami din a yanzu tunda har na gano hakan zai iya haifarwa mahaifiyata da yan uwana da zaman lafiya a rayuwan ta. Karatuna nake sosai kuma ina fahintar hakan don bamu tare da wani mstsalan komai a tare damu a gidan zaman kadaicine kuma wanan Fadila din tana iya kokarin ta wurin ganin bamu shiga damuwa da komai a gidan. A haka har Allah ya taimaka na gama zana waec dina muka zauna jiran zana neco din mu wanda a lokacin ne na samu dan natsuwa sosai tare da maizube da halimatu da yanzu itama take zuwa makaranta tare dani. Na mayar da hankali sosai wurin koyon girki tare da anty fadila da sauran abubuwan da take koya min na zaman duniya a cikin hikima da basira . Zakace ya da kanwa muke da ita a yadda nakan bata girma da kuma daraja sai hakan ya kara sawa matar sona a ranta sosai. Don a yanzu mun sake da juna zata fada min kai tsaye idan nayi wani abinda ba daidai ko bai dace nayi shi ba a take zata tsawata min kan hakan a karshe kuma in bata hakkuri. Sai ya kasance a dan watannin da mukayi da ita wani irin sabo da shakuwane ya shiga tsakani mu sosai har yakai ranan take tambayana labarina ? Sai kawai na danyi murmushi ba tare dana furta komai ba a hakan muka bar zancen ba tare dana fada mata komai ba. Da yake ita din mace wayayyiya a cikin hikima irin nasu nasu na manyan mata take dan tambayana wasu abubuwan a cikin hikima har take samun amsa daga gareni. Take kuma sakani a hanya yadda zan kula da komai da zaizo min a bazata daga ko wani bangare. Yau ban tun safe ban leka falon ba ina daki kwance na tashi sa ciwon mara wanda kan dameni duk karshen wata. Har daki anty Fadila ta kawo min magani nasha wanda hakan ya sakani barci bayan nasha magani sai bayan karde hudu na samu fitowa falo na zauna. Bandade da zama a falon ba halima ta shigo dauke da ledan corn a hannunta tana ci ta samu wuri a gefena takai zaune. Na dago kai na kalleta ina mamakin ta a raina ban kaiga karshen mamakin ba ta jefo min tambaya tana fadin wai anty sai yaushe zamu tafi gaida hjyn ki sa kike aiki a gidan ta. Gabana ya fadi don jin abinda ta fada saida na tattaro dauriya a raina kafin ince da ita kin santane ko wani abin kike son yi a gidan nata ? Kai ta gyada min alaman a,a tare da shan jinin jikin ta a yadda na bata amsa din cikin bacin rai don bansan zancen gidan mami duk da ina kwana ina wuni da zancen mami din a raina. A hankali na zame na kai kwance daga inda nake zaune tsaban tunane sai kawai naji hawaye suna zubo min ba tare da nasan zuwan su ba. Dafanin da akayine yasa na dago kai anty fadilace a tsaye kaina tana kallona yadda hawaye ya bata mun fuska lokaci guda. Badai ciwon bane har yanzu ta fada a cikin kullawa tana zama a gefena tare da mayar da hankalinta gareni. Kafin in bata amsa halimatu dake gefena take fadin yayan mu bansan ranki zai baci ba da bance muje gidan hjy din ba . Wace hajiyan anty fadila ta tambaya da mamaki a fuskanta a hankali na amsa da mami mahaifiyar ya Jafar. Anty fadila tace kan me kukai zancen ta har ya kawo wanan hawayen haka ? Bazaki ba tunda tun farko ta nuna bata kaunar ki da danta kina garin nan kuma ta sani bata nuna kulawanta kan danta ya barki amana a gurin su ba maizube ke fadi daga bayan mu. Don haka ki nisanci su kamar yadda suka nisance ki a yanzu saboda da talaucin ki ko rashin gata ta nuna bata kaunar danki dake dafarko . Sai yanzu kuma ke zaki kwashi kafan ki zuwa gidan ta ko zaki kai kanki ne su kara wullakantaki a can . Ki zauna a matsayin da Allah ya ajeki gidan nan ki bi umurnin mijin ki har sai idan shi ya furta zuwan ki gidan dan mahaifiya ba wasa bace ai amma yanzu kan babu inda zaku tafi gaskiya. Maizube nima bance zan tafi gidan mami ba a yanzu don nasan mami har yanzu tana rike dani a zuciyar ta. Duk da ba zan iya matawa da alherin ta a garni ba har gobe don ta dalilinta har na kai hakan a yau da sunan auren danta a kaina. Maizube tace dani ato ki daiyi wa kanki fada don babu inda zaki tafi don ni bazan zama babban kwabo ba a cikin ku duk da muke matalauta muna rike da mutuncin mu a idon kowa. Murmushi Fadila tayi tare da fadin hjy maizube ba a hakan ai idan ma har zasu tafi din aiba haka kawai zamu barsu su kadai din su tafi ba dole saida shirin hakan ko ? Maganin dai kar ayi kar a soma dan ba a san da wace zata tare su ba abar zancen nan har wanda take zama don shi ya dawo kasan nan inma zuwan ne sai su tafi tare dashi din zaifi. Jinsu kawai nake yi don sam ban amince da zuwan ba nikaina a lokacin don nagama tsiracewa da mami din yadda muka bar gidan tare da hjy a yadda tayi min koran kare a gidan ta harta amince da mahaifiyar ta tabar gidan donni. Wanan zancen da akayi a gaban Fadila yasa ta dauki wani haske a cikin zancen sai da muka zauna daga ni sai ita take kara tambayana abinda ya faru a tsakanina da mami din. Shiru nayi na dan lokaci kamar mai tunanen wani abu sai can naji tana fadin zanso nasan wani abu daga bakin ki duk dana dade da gano komai amma zanso ji dafa gare ki din yanzu. Wani tsorone ya lullubeni lokaci guda na janye na dauki hannuna na dora a fuskana kafi in sauke na dukar dakai na kasa. Karo na biyu ta koma kiran tana fadin kina jina kada ki boye min komai ki daukeni kamar yar uwa a gareki don ni din a yanzu mai taimakon ki ne zainab. Wani sanyi naji a raina tare da yarda da ita lokaci guda duk da Banso fada mata komai ba amma ya zama dole ta danji wani abu a gurguje na dan fada mata saidai ba duka ba don ban san yadda zata dauki zancen ba a ranta. Bakina ta zubawa ido har na kare na kare fadan abinda zan iya fada mata na zamana da mami da haduwan mu da ya jafar din a gidan mami har na kare sai tace. Zainab yau zan baki shawara kamar yarda ya da diyarta zata bata shawara ya amfaneta. Tagumi nayi ina sauraren abunda zata fada min din a lokacin ita kuma taci gaba da kawo min misali na zamantakewa da mutane a duniya. Yadda mama maizube take nufin kiyi danzun nake ganin bashine mafita ba gareki zainab don ko yaya suka samu matsala a kanki da mahaifiyar shi ki tunafa uwa uwace a gare shi. Duk yadda kika dauka da zafi ko iyayyen ki suka dauka hakan ba zai taba mashi dadi ba a ranshi duk ko yadda yake sonki. A sake na ce yanzu yaya zanyi anty don mami ba zata taba yarda dani ba a cikin a halin ta ni kuma na sani auren nan namu nadan lokaci ne dashi. Tsaki taja tana fadin ki bar wanan zancen do Allah kefa mace ce zainab duk wani abu da ake bukata a mace kina dashi zainab lokacine kawai zai nuna hakan akan ku. Kedai kawai yanzu duk abinda nake koyar dake ki maida hankalinki ki koya do zama daku na dan lokacine da zaran contrac dina ya kare daku tafiya zanyi in barku a gidan nan. Yanzu lanbanta zamu nema zaki dinga tura mata sakon gaisuwa da girmawa tare da nuna mata ke din yace a gareta har gobe. Ya zama dole ki koyi halin kissa da kisisina irin na mata masu son kama gidan su a hannun su yanzu . Ta yadda zaki iya tunkaran kowa da wanan kalubalin dake gaban ki domin yanzu sai da wanan akan samu riban rayuwa mai dorewa wanan sanyin ba zai kaiki ko ina ba a rayuwa. Rashin wayen ki ko sanin duniya zai iya haifar da komai a kanki har aci galaba akanki a cikin sauki don wanan shirun da kike ganin tayi irin su hjy da abinda take shiryawa a hakan. Da sauri na dago kai don jin abinda ta fada din nace amma anty ta yaya kamata zan iya ja da mami matar da ta kafu da komai akan danta dama kowa ? Murmushi tayi tare da fadin kina kwankwanton hakan ne zainab ai tun damazo gidan nan na fahinci akwai wata a kasa tsakani ku. Naso tafiyan ya tafi a hakan inyi aikina in wuce saidai ke din yarinyace mai saurin shiga ran mutum a lokaci daya saboda halinki na sayi da girmamawa ga kowa don baki dauki duniya da zafi ba a yadda na fahince ki. Don hakane ma kike ganin har abinda ba a ssni na koyar dake ba nake kokarin koya maki don na taimakawa rayuwan ki. A sanyayye nace anty nagode da wanan taimakon naki gareni in Allah ya yarda zaki sameni da amfani da duk abinda kika koyar dani insha Allahu. Tayi murmushi tana fadin ya zama dole in taimaka maki zainab don nasan wata rana hakan zai min dadi nima a rayuwana. Kin ganni nan nasan halin maza kamar yunwar cikkna ina da yara biyu na barsu badan naso ba saboda halin da namiji a yau. Don haka ba zanga wata mace yar uwana zata fada a halaka ba in barta ta dandani irin ukubar dana sha a baya. Sau nawa ya kiraki a waya tun bayan tafiyan shi ta jefo min tambayan da ban zata ba a lokacin da sauri na dago kai ina tunanen hakan ? Bai kirani ba anty na bata amsa kai tsaye do babu zancen boyo yanzu a tsakanin mu kuma tunda ta fahinci komai. Zai kiraki naji ta fada idan mun fara dana masa tarkon muna mata ai idab yasan wata baisan wata ba zamuyi mai karya baki da lafiya zai zo idan har kina da muhinmanci a rayuwan shi . Saidai zaki bani goyon baya zaki koma ki kwanta ciwon na kwana biyu do wanan kanwar taki mai shegen surutun tsiya zai iya tambayan ta idan hakan gaskiyane kin sani. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 4️⃣8️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERIN GAREKU TARE DA BAN HAKKURI RASHIN SAMUN UPDATE KO DA YAUSHE DA FATAN ZAKUYI MI AFUWAN HAKAN YAN UWA, , , , , , , Ina kwance tun safe kamar yadda ta umurceni da yi hakan din sai dai tunane ya addabi rayuwana yadda wanan wasan da take shiryawa zai kaya muna. A gogon dakin na bango na duba da karfe sha daya saura na safe tun bayan sallah asuba nake kwance ni ba barci na koma ba don tunane ina kwance a falke ina faman dakon tunane a zuciyana. Wayana dake gefen gado wanda tun daren jiya na ajeshi da zamu kwanta ban kara bi ta kansa ba ya dauki kiran agaji. Hannu na mika daga inda nake kwance din na dauko wayan da zuman ganin wanda ke kira layin don ban taba zaton kiranshi bane a lokacin. Lanba ce ta kasan waje aka kira layin dashi na kurawa kiran ido ban daga ba ina nazari a raina har kiran ya gaji ya katse lokaci guda . Wani kiran ne ya sake shigowa lokaci guda ina kallon wayan na fitar da sautin kida na kasa dagawa don na farko ban sheda ko lamban waye ba a lokacin. Na biyu kuma idan na dauka shine mai kirana me zan fada mai don bamu riga da mu aje magana abinda zan fada mai ba. Jikina gaba daya yayi sanyi a lokacin a cikin daurewa kiran na gaf da tsukewa na kai hannu na danna dauka. A hankali na kara wayan a kunne na lokaci guda ina sauren mai kiran nawa hello din daya fada a gadarance yasa na fahinci ko waye a layin shidin dai ne ya kira wayan a lokacin. Ya kara fadin hhy ya kuke me faru dakene dazun fadila ke fada min baki da lafiya tun jiya ko fita daga daki bakyayi. Saida na tattaro wani karfin hali a tare dani kafin in iya budan bakina nace a hankali cikin yanayin wanda ciwo yake damun sa na furta banda lafiya ne da kyar. Baki sa lafiya ita fadila me take jira dake a gida bata kaiki asibiti ba ko bata san aikin ta bane wai ? A hankali na lumshe idona tare da fadi a marairaice cikin sanyin murya ta sani ita dince ma take kula dani yanzun haka na basa amsa. Ta kaiki asibiti ya kara tambaya ta kaini jiya da yamma na samu kaina da fadin hakan duk da nasan komai karyane shirin hakan mukai masa. Zan turi maku da sako idan wanan bai isa ba aimin magana ya fada kamar a kage yake da ya kashe wayan shi a lokacin. Yaci gaba da fadin idan har kuna da matsala da ita zan iya canza wata a samo wace zata kula dake fiye da ita. Ban san lokaci danace a rude laifin me tayi koda mahaifiyata ce ita ai iya kar taimakon da zatayi min ke nan . Naji ya saki ajiyan zucuya tare da fadin ta kyautawa kanta don bana son wasa da aiki a rayuwana. Idan ma laifi ne ai ba ita bace mai laifin don ba itace ta rabani da uwata ba na fada can kasan makoshi na a hankali na dauka ba zaijini ba. What me kike fada ? Shiru nayi tsayin lokaci babu amsa daga bakina bai kuma kashe wayan nasa ba a hankali na runtse idona ina sauke numfashi da kyar don gabana sai faduwa yake daurewa kawai nayi a hakan. Ba zaki magana ba naji ya fada a cikin dan daga murya nace to ai kaine ka rabani da mami kuma ka , , , , Look ina wasa dake ne zainab yaushe har raini ya shiga tsakanin mu haka dake ko so kike na bar aikina nan na dawo na zauna Nigeria daku ? Kit na kashe wayan tare da maida nufashin dake sauka min na tsoro da sauri don ban zaci zan iya fadan hakan ba ni kaina. Aje wayan yayi daidai da shigowan anty fadila dakin cikin sauri na dago kai a firgice ina fadin anty wallahi shine ya kirani yanzu din na fada ina kallon ta kamar mara gaskiya. Na sani ta fada tana zama a gefen gadon da nake kwance nima mikewa nayi ganin ta zauna din a dakin. A haka zamu kamo shi sannu a hankali har hankalin shi ya karkato zuwa gare ki don maza a yanzu sai da kisa da iya zama dasu a cikin dabara. Na bude baki da zuman magana ke nan aka turo kofan inda nayi shiru maizubd ce ta shigo tana fadin wai nikan jikin ne yau ta hanaki leko waje yar nan ? Fadila tace jikin ne nima yanzu naji shirun yai yawa na leko ta na same ta a kwance sannu ta fada tana kallona a cikin damuwa da nuna kulawa a gareni. Na amsa a cikkn daurewa ina kokarin yaye bargon dake saman jikkna wanda ya dameni a lokacin don dole nake kwance dashi. Ki tashi ki karya fadila ta fada a cikkn kulawa nace zan watsa ruwa kafin na fita yasa suka bar dakin don na samu kintsawa hankali kwance. Dogon riga mai laushi green mai adon dawisu a gaban rigan zuwa kasan shi na saka a jikina sai gyalen shi danayi dan kwanlin dashi a kaina. A falo na same su zaune suna kallo na fito daga yanayi tafiyana ya nuna ban cikin dadin rai a tare dani. Dining na nufa kai tsaye abinci na nan a gurin na diba kuma sai na kasa cin komai don hankalina yana gun yadda mukayi a waya dashi. Da ido Fadila ke warning dina a yadda nake cin abincin da sauri na gyara sallon cakulan abincin a hankali cikin yanayin yauki da yanga kamar yadda ta koyar dani. Muna falon har lokacin da halimatu ta dawo daga school tashigo da murnan ta tana kokarin fada min ajiki. Anty fadila ta daka mata tsawa tana fadin kada ki fada mata yinin yau bata da lafiya gaba daya da sauri ta juinda inda nake zaune ta dan langabe kanta tana fadin. Yayan mu sannu ya jikin na dan gyada mata kai alaman amsawa gareta ta zauna gefena tana fadin kinga yau tare da yaran gidan hjy din nan muka yi yawo a school. Wanan akwai ki da iyayi har sai kin daukowa mutane zance a garin nan yaushe har kika sansu da kike kokarin cusa kanki garesu maizube ta fada. To ba saboda yayan mu nake kula suba ta fada tana turo baki gaba alaman zancen da maizube tayi bai mata dadi ba. Halimatu tashi ki shiga ki cire kayan ki na fada cikin bata umurni ta mike da sauri zuwa dakin kamar yadda na umurce ta tayi. Alwala na dauro na gabatar da sallah tare da mika kukana ga sarki Allah wanda yafi kowa sanin dumbin damuwan dake tattare dani a rayuwana. Kafin na mike na koma na kwanta dan banjin fita falon da ya zame muna wurin fita kawai a gidan don ko haraban gidan bama fita idan ba fita ya kama yi ba. Amma kuma sai barci ya gagareni a lokacin sunayen Allah mai girma na dinga kira don na samu natsuwa har barci ya daukeni a hakana. A cikin barcin nake mafalki da ya jafar yana tsaye ya harde hannayen shi yana kallona na tun karo inda yake tsaye. Saiga wani yazo ya tsaya a tsakanin mu ya bani baya don haka ban samu ganin fuskan maishi ba . A haka ina kalon su ban samu karasowa inda suke tsaye din ba ina kallo wanan mutumin ya jayeshi gareni ya tafi yana waigena a inda nake tsaye. Sunan shi na kira da karfi wanda hakan yai daidai da bude idanuwana daga barcin da nakeyi din na falka a razane na gannin a cikin gumi. Zainab wanan ihun fa Anty fadila ta fada daga kofan tana tsaye kai na dago ina kallon ta a tsorace take fadin nazo zan wuce naji kamar kina ihu na shigo. Anty mafalki nayi na bata amsa take fadin barci a wanan lokacin baida kyau gashi har biyar na yamma yayi yanzu kina kwance. Dago kai nayi na kalli lokaci sai na tuna da zancen sallah na mike don zuwa nayi alwala bayan fitan ta na samu fashin sallah yazo min a lokacin don haka na tsaye kawai na gyara jikina na fito daga bayin. Naso na manta da zancen mafalkin nan danayi saidai abin ya tsaya min a raina sosai har yakai ina ganin abin kamar a zahiri a idona don irin kallon da yake min a lokacin. Jafar da tun safe hankalin shi na ga ya sake kiran Fadila yaji ya jikin nawa saidai kuma aiki yai masa yawa yau din sai dare ya samu kansa yana hutawa a gidan sa. Wayan shi dake gefene ya dauki kara ya dan dago yana kallin wayan da mamaki don gani mamice ke kiran shi a lokacin. Duk da yasan a can Nigeria yanzu akwai sauran lokaci dare bai wani yi ba a can ya dauki wayan kafin kiran ya katse mai. Da sallama a bakin shi ya daga wayan tare da mika mata gaisuwa a cikin girmamawa kagin ta furta dalilin kiran nata garshi. Ba tare data amsa mashi ba take fadin Jafar wai me kake son mayar da kanka a cikin kune ? Duban wayan dake hannun shi yayi cike da mamaki kalamin mami din yana fadin mami nayi wani laifi ne yanzu kuma ? Au baka ma san da kayi min ba daidai ba ke nan ashe har yanzu kana nan da zancen yarinyar nan zainab har wata can wai kanwarta tana kokarin cusa kanta gun yaran nan a school din su. To kayi gagawan yiwa zainab da duk wani nata iyaka da zuri,ata a garin nan tunkan ranku gaba daya ya gama baci gareni. Jafar din ya kasa gane me mami take fada don haka ya natsu da kyau yana gyara zaman shi do n kara fahinrar inda zancen nata ya dosa dashi. Idan kana son kanka da lafiya na fada ma ka sallami yarinyar nan zainab tun kan raina ya gama baci dakai a gidan nan. What mami ya fada dan jin abinda ta fada a kan zainab din wace ke matsayin mata a gareshi duk da yasan auren bawai wani abu ya daukeshi ba shima. Yace mami amma kinsan akwai aure ai a tsakanin mu dan haka babu zancen saki a tare damu mami kinsan da hakan. Jafar ni kake fadawa akwai aure a tsakanin ku in yarda tunda nasan baka fito ta inda ya kamata ace zan yarda da hakan ba. Kamar yadda na aurar da dan uwanka a inda nake so haka kaima nake da burin maka aure na gata kowa ya san da zancen. Bazan taba amincewa da wanan aure naka ba na fadama gata da daraja kamar ko wani da zan ma a kasan nan ban yarda da auren da zaka sa mutane su kalle da ban san komai ba. To wallahi kaji na fadama koda wasa na kara jin zancen wanan yarinyar ya fito a bakin ka gabana saina bata maka rai fiye da yadda bakai tsamani ba. Dan haka na gargade ka da ka ja mata kunne akan yayan gida dan karsu kara nuna sun sansu ko a ina ne kuwa. Jafar din dake jin zancen mami din kamar al,amara dan ya shiryawa hakan ko wani lokaci yace. Mami za a kiyayye ba zasu kara shiga harkan diyan ki ba ko jikokin ki insha Allahu zan tsawara masu kan hakan. Har ta gama fadan ta sai hakkuri yake bata ranshi idan yai dubu ya gama baci da hakan don shi sam baiga abin fadan mami ba a nan. Aikin da baiyi ba ke nan dan gaba daya ranshi ya gama baci da zancen mami din a hankali idanun shi suka soma sauya launi. Ya dinga jin zuciyar tana masa radadi da zogi ya mike zaune game da dafe kanshi tare da sake wani irin huci mai zafi lokaci guda. Ba shakka har idan ya yarda da abinda mami din su keso a gare shi komai zai iya faruwa dashi a karshe. Don haka ya zama wajibi garshi ya jawa zainab kunne kan duk wani abinda ya shafi mami dawani nata . Saidai kuma ta yaya zaiga laifi zainab di bayan tana gida kwance bata da lafiya a inama ta fita har taga wani da mami ke wanan maganan haka wai. Shi a rayuwan shi ya rasa gane dalilin wanan kiyayyan da mami takewa wanan yarinyar da bata san komai ba a game dashi. Idan ma taimako ne ai ita zainab din ta taimaka amma son zuciya ya rufewa mami din ido ta kasa gane hakan ta ko ina saboda wani dalili nata can na daban. Ba shakka son zuciyar mami din yayi yawa ga wanan magana data kasa hakkura da jerabawan ubangiji a gare shi . Don haka ya zama dole ya nunawa duniya yarinyar nan tana zaman matar shine da kowa ya kamata ya sanda hakan yanzu . Ba zai damu da wani ra,ayi ko son kai da mami ke shirin nunawa ba a nan don sam yarinyar bata da laifi asalima ai laifin nasa ne gaba daya bana yar mutane da ya jefa a tsaka mai wuya ba. Duk da yasan da ita kanta zainan din idan hankalinta yazo ta mallaki hankalin kanta akwai kalubali mai yawa a gaban shi. Wanda yasan kafin lokacin zai iya magace komai a tare dashi da duniya ba zata zargeshi ba kan hakan. Wanan wani damane ya samu da zaiyi amfani dashi don kawai ya fitar da kanshi daga wani tarko da mami ke shirin dana mai wanda zai dawo ya damesu gaba daya. Da kyat ya tashi ya iya kulle kofan shi do baya bukatan kowa ya dameshi a wanan lokacin yana da bukatan ya kebe kanshi shi kadai ko zai samu natsuwa a wana lokacin. Zazzabi mai zafine ya rufe shi a wanan lokaci tare da dumbin damuwa a zuciyar shi tabbas da mami tasan koshi waye ba zata tsaya tana fada akan shi ba. Da mami ita kanta ba zata yarda ya auri yarta da ta dauko amana ya gani a gaban ta har yaga dacewan ta da wanan dama nasa ba ya kulla alakan aure da ita. Wani iri yake jin kanshi a lokaci daya ga azaben ciwon kai dake damun sa ga matsanacin kasala gaba daya ya rufe shi a lokaci guda sai yake jin duk zaman garin ma ya fita mai a rai tankar ana hura masa wuta a jikin shi. Wani irin nadama da dana sanin biyewa abokai na kurciya ya kamashi a lokaci daya a haka har gari ya waye mai duk da bugun kofan da yake ji ana masa baisa ya bude kofan nasa ba a lokacin. Kwana biyu ya dauka a gida bai fita ba don yanayin jikin nasa da yake ji wanda ba komai ya haddasa masa hakan ba sai tsananin samuwa da halin da yake ciki. Ya mamud ne da ya sha kiran shi a waya ana fada masa yana barci har yakai ga fahintar dan uwan nasa baida lafiya ya samu mami da zancen. Da farko mami bata tayar da hankalin ta ba saida sukai waya da babban yaron shi yake fada mata yadda jikin ogan nasu ya tsananta a lokacin hankalinta ya tashi. Da kyar ta samu aka sadasu a waya dashi take fadi a cikin tsigar lalashi jafar baka da lafiya baka kira gida ka fadi. Yanayin yadda yake magana ya kara sa mami a cikin damuwa ta kara kwantar da murya gareshi tana fadin meke damun ka hakane friend ? Mami kirji na da zuciyana kamar zasu fashe nake jin su ina jin zuciyana kamar an daure min shi gaba daya na rasa abinda yake damuna. Mami tace kayi hakkuri ka daure kuje asibiti dukkan al,amari ubangiji yasan dashi ka daina saka aiki ko wani damuwa a zuciyar ka hakan nan. A haka mami ta samu ta rarashi dan lelelen nata har dai yaji zuciyar shi yadan sausauta mashi daga irin kuncin da yake jin kansa a ciki lokaci guda. A bangaren mu kuwa bamu san wainar da ake toyawa ba iyaka dai anty fadila ta kasa samun shi a waya. Tun hakan yana damun ta har takai ga furta min cewa kwana biyu fa bata samun oga a waya idan ta kirasa. A cikkn rashin ko in kula nake fadin anty isan ya damu ai shi da kansa zai kiramu yaji lafiyan mu wata kila aikine yai masa yawa. Kai ta gyada min alaman a,a zainab raina yana ban ba lafiya dai sai dai duk abinda ake ciki zan barshi zuwa gobe ko jibi idan bai kiraba zan nemi abokin sa na nan muji ko lafiya yake a can. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣0️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA IDAN KIN GANI KARKI KARANTA IDAN BAKI BIYANI HAKKINA BA NA FITAR MAKI DA HAKKI NA FADA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH, , , , Kina jina malam ya fada na amsa a sanyayye da ina ji malam kada kisa damuwa ko kadan a wanan mafalkin naki don har gobe haske na gaban duhu. Matuka kina rike da ayar Allah a tare dake babu wani shedani ko wani mahulunkin da zaiyi galaba a kanki face sai in hakan mukaddarine daga Allah dama yana a cikin kaddaran ki. A iya binciken da nayi na gano wanan mutum wani shedanine dake tare da mijin ki a kullun wanda ya sha alwashin ganin bayan duk wata macen da zata rabi mijin naki. Ba akanki kawai yake shedan shi ba duk wata mace hatta uwar data haifeshi da zai iya sai yayi sanadin raba alakan shi da ita. Saidai a garemu wanan abin matukar zaki rike adduan dana baki kafin kuzo wanda shi din makamine dama ga mumuni ga bayin da suke mika al,amarin su gurin ubangijin su koda yaushe. Malam shidin ba mutum bane kamar yadda nake yawan ganin sa a mafalki ko na tambaya a cikin sanyin murya da damuwa. Murmushi naji malam din yayi tare da fadin a buncike na dai shi din mutum ne kamar kowa saidai shedanin gaske ne na kwarai. Hasbunallahu wani imal wakil na fada a sanyaye tare da sauke ajiyan zuciya don tsoro da fargaban da ya ziyarci zuciyana a lokaci daya naji malam din yace. Saidai abinda nake so dake Abu shine ki kwantar da hankalin ki da sannu zaki fahinci waye shi wanan mutum din cikin masu alaka da mijin naki. Shi mutum masheranci ba kasafai kake saurin gane shidin makashin ka bane sai idan ka kwantar da hankalinka a sannu zaka fahinci duk wani mai binka da sheri a doron kasa ko ta wurin maganan sa ko yanayin kallom sa gareka da dai sauran su. Mun dauki lokaci tare da malam yana kawo min ayan Allah da hadisai har saids hankalina ya kwanta naji duk tsoron dake raina a lokacin yana gushe min a lokaci guda. Bayan sallama da malam din na koma gaban gado na zauna da wayan a hannuna na fara tunane wanan wani sabon kaddarane kuma ke shirin tunkaroni a yanzu. Ina zaune ashe hawaye na zubo min ban sani ba sai jin muryan anty fadila nayi a kaina tana fadin me kuma ya faru haka zainab ke kadai a daki zaune kina hawaye haka ? Kaina dago ina sauke sanyayyen ajiyan zuciya ina kare mata kallo tana tsaye da wani leda a hannunta fari ta karaso shigowa cikkn dakin tana maimaita tambayan ta a gareni lokaci guda. Meya farune kuma don nasan ba zaki zauna haka kawai kina zubar da hawaye haka ba ke kadai a daki zainab ? Ki saki ranki dani wallahi na fada maki ni mai taimakon kine ko da yaushe zainab don ciwon ya mace na mace ne yar uwanta ko kuma zancen fadan da mijinki yayi min ne ya sakaki wanan kuka yanzu ? Kaina girgiza ina kokarin kakaro murmushin dole a fuskana kada ta dauka wani abu nake boye mata haka don ban da niyar fada mata wanan sirin nawa. Nace anty ba komai bane kawai tunanen makoma na a gidan nan nakeyi sai hawaye yake zubo min ban sani ba ina kokarin share hawayen dake fuskana din. Dafani tayi tana fadin kinga irin mazan ku dama tsada sukeyi koga matayen auren su idan kinga mutum da kyau ga ilimi ga dukiya uwa uba wayewa lamarin shi gaskiya sai a hankali dama. Nasha fada maki ba sanya zakiyi ba saifa kin dage zainab a wanan zaman naku kada ki damu da duk wani hali da yake nuna maki a yanzu . A sannu a hankali komai zai daidaita a tsakanin ku ke barin fada maki gaskiya daga yan mata har manyan matan barikin garin nan. Duk idon su akan irin mazajen nan suke ko yaushe burin duk wata mace a yanzu shine ta samu gidan hutu irin wanan ta yadda zata shiga tsara ta nunawa duniya ita watace a gari abin kwatance. Ke bari ma dai in maki na mahaukaci ai yanzu idan kayi sa,a ka damki namiji kada kayi sakaci dakoma wayeshi kama abinki ki damke ta yadda matan waje zasu gane ayya yana gaba da tsakuwa wurin taunawa. Don haka kama jiki kafin yazo ki nuna mai ke yanzu ba da bane a gurin ki kinsan kanki kinsan ajin ki ta yadda zaiji shayin yi maki wani iskancin su na maza can. Dago kai nayi da sauri ina kallon ta don jin abinda ta fada ni ta yaya zanwa mutum kamar ya jafar wani sallo ko kissa can har yasan ni din mace ce ta fada a duniya. Tace kina mamaki ko zainab zakice nace maki lokacin da zaki kama shi a hannun ki kina juyawa yadda kike son abinki da kowa zaiji a ransa dama ace shine a matsayin ki a lokacin . Jin abinda ta fada yasani sauke wani irin ajiyan zuciya mai dan karfi don jin zancen ta nakeyi kamar almara a kunnuwa na. Har yaushe hakan zai faru da take ta fada a gareni ni din da ban ko gama sanin matsayina ba a zuciyar shi har take min hasashen hakan yanzu. Kina da kyau da zaki sace duk wani zuciyan da namiji zainab irin kiran ki maza da yawa suke so a rayuwan su saidai in hakan bai samu garesu ba dai. Kin koga yadda kika koma a cikkn kan kanin lokaci zainab yanzu wasu kayan ne na sayo maki irin wanda ya kamata mace na sakawa a cikin gidanta don jan hankalin mijin ta ba yanzu zaki amfani da wanan kayan ba sai lokacin da mijin ki ya dira a kasan nan. Dan murmushin yake na sake mata a fuskana kawai ta fara daga kayan har kala biyar babu wanda zan iya fita ko falon gidan dasu a ganina balle wai gaban shi ya Jafar din da take nufi. Godiya nayi mata a fili a zuciyana kuma fadi nake Allah ya sauwaka min sakace wata karuwa can riguna haka duk a bude kamar rigan turawa marasa tarbiya. Zai maki kyau sosai ta fada tana kara dagasu tare da fadin ina gani su naga sun dace dake sosai yasa na sayosu tunda akwai kudi a hannuna. Nagode na kara fada a cikkn kulawa da nuna girmamawa a gareta kuma na kula da hakan yayi mata dadi sosai ta mike tana fadin don Allah ki saki ranki na fada maki saifa kin jajirce sosai ba a sanya a harkan aure. Kwana biyun nan nikan na mayar da hankalina a wurin addua ne sosai da kai kukana gun ubangijina Allah kuma sai nake jin natsuwa da kwanciyan hankali yana kara shigana ko wani lokaci. Hakama maizube na kula da tana tayani da addua don itama tana bata lokaci sosai wurin fadawa Allah al,amarin mu. Falon gidan muke zaune bayan sallah la,asar wanan ya zama muna kamar dabia a gudan a wanan lokacin mukan hadu nan mu dinga fira da juna ana dariya. Wanda hakan kan min dadin a rayuwana har in manta da wani abu a tare dani gashi a sannu ina matawa da tsoron mami a cikin zuciyana. Saidai tunanen hjy da kewan ta har yanzu yana nan daram zaune a raina don tsohuwar ba abun mantawa bane a rayuwana don jinta nake kamar itace Asabe kakata a guna. Yun hadarin yamma ya zama kamar al,ada a garin abuja din haka yanzu ko an hada bai faye damuwan mu ba kamar farko. Da wandone baki irin na mata mai dane jiki a jkina iyakarshi idon kafana hakan yasa santala santalan kafana fitowa fili gasu fari sol dasu don tsaban samun dadin da nake ji yanzu tare da rashin wani aiki da banayi a yanzu yasa kafan ya kara min haske sosai. Sai dan riga irin na mata dake dan bude daga kafadunshi zuwa iya gwiwana mai launin kalar kampala jikin rigan wanda ya dauki kalar jikina da kyau. Sai hula dana saka a kaina mai ribon ta baya ya gashina dana daure yasa yadan dago ya kara min kyau. Wanan duk aikin anty fadilace wace take matsa min da nayi wanan shigar tun ina kunyan hakan har nazo na daina ina fita hakan kamar yadda ta umurceni dayi din. Ruwane ya gwauce kamar da bakin kwarya muna zaune muna hiran mu bamu daga a falon ba don sanin lokacin sallah baiyi ba a lokacin. Duk da ruwane mai karfi da akeyi hakan bai hananu mu jin dirin motoci da horn a gaban gidan ba lokaci guda saidai hakan bai wani damun ba don ji muke kamar hadirin ne haka. Don haka hankalin mu kwance muke hiran mu batare da kawo komai a ran mu ba lokacin sai ji mukayi kawai an turo kofan falon da muke zaton a rufe yake. Don bamu barin kofan kasafai a bude hakana a namu zaton yana rufe a lokacin ashe a bude yake jin aturo kofan yasa hankalin mu ya koma a kofan lokaci guda. Shine ya shigo falon ba tare daya dago kai yasan damu a falon ba yana dan kakabe ruwan daya dan taba mai jiki daga waje wajen shigowa gidan. Gaba dayab mu a cikin mamaki muke kallon kofan don jin anturo da mamaki karara a fuskokin mu sai ganin shi mukayi tsaye yana kakaban ruwa a jikin shi. Kafin ya dago kai ya sauke idon shi garemu idanuwan shi masu haske kamar kwan lantarki ya kura min ido da maki a fuskan nasa. Tsaban rudewa da fargaba yasani mikewa lokaci guda don rabona da ganinsa yanzu kusan shekara daya ke nan ake batun rufewa tun bayan daya dauko mu a kauye tare dasu maizube da halimatu ya tafi sai wanan karon dana gansa. Idanu ya kara watso min sun kara fari da girma gasu dal dasu tankar hasken lantarki saboda tsaban jindadin da yake samu. Ga wani girma da kwarjini daya kara baiyana mai alaman jin dadi ya zaunu mai a yanzu fiye da lokacin daya barmu a baya. Masangalin kujera na dafa a cikin kyarman murya nake fadin sannu da zuwa yaya . Sai lokacin ya dan yi kamar wanda yai shock a cikin basarwa da dakewa ya amsa da uhmmm yana karasowa cikin falon. A daidai lokacin ne kuma aka sake turo kofan saiga wanan yaron nasa ya shigo dauke da jakkar kayan shi yar karama. Shima tsayawa yayi yana kare muna kallo cike da fara,a anty fadila take masu sannu da zuwa da signal ta nuna min in karbi kayan a hannun yaron nasa da yake rike dashi a bayan shi. Na karasa cikin takon da bansan inayin shi ba zuwa inda suke tsaye din na dan gwauta ya jafar din zuwa amsan yar jakkar kayan. Sai cewa yayi cikkn wani murya mai shrge dana mata barshi kawai zan karasa dashi ciki ya fada yana kokarin wuce inda nake tsaye. Da sauri anty fadila ta amsa da fadin is her duty give it to her ya dago yana kallon ta a cikin mamaki kamar ba zai bayar ba sai kuma ya mika min jakkar. Kamar kullum wanan yaudararen idon nasa ya watso min wanda na riga dana saba ganin wanan kallon nasa tun ina a gidan mami zaune idan sun shigo tare da yayan. Zama sukayi a falon yana gaiswa da maizube da halima datake murnan ganin yaya din sai faman washe baki da takeyi don ganin sa. Bankai kayan dakin ba don a rufe yake tun lokacin kitchen na nufa a can na samu anty fadila tana hada masu abin sha tana ganina tace good oya dauki maza kikai masu wanan. Na dauko har lokaci yana zaune suna hira da maizube sama sama na dire masu ruwan da drinks a gaba shi kamar yadda ta koyar dani din inyi idan ya shigo. Wanan yaushe ta koma haka yaron nasa ya fada a daidai lokacin da nake mikewa daga dukawan danayi ina aje ruwan cikin kashe murya. A takaice na amsa masa da kwanaki wanda ni kaina bansan zanba da amsar hakana ba alokacin fito min tayi a bazata. Kaishi kawai ya girgiza cikin wayayencewa gami da basar da disgashin da nayiba take. Na juya zan bar wurin naji ya din na fadin dawo ki zuba muna yanauin maganan sa kamar a kasalace yake a lokacin. Na dawo badon naso ba na fara zuba masu a hankali abin mamaki sai bayan na zubane wanan yaron ya mike ba tare daya dauki nasa yasha ba yana fadin. Zai fita yaga sauran wa yanda suke tare dasu a waje ba tare da ya jafar din ya bashi amsa ba yaba zaune ya dafe kanshi da hannun shi daya har ta fice falon bai masa magana ba. Dauka nayi nikan na mika mai a cikin ladabi da girmamawa sai naji yana fadin thank you bayan ya karba daga hannuna. Banyi mamakin jin kalman daga bakin shi ba don godiya ga bature ba wani abu bane wanan na saba da godiyan su tun a gidan mami. Saidai naji dadin hakan a raina don godiya wata kalmace mai nuna yabawa ga mutum ga wanda akaiwa hidima. Yana gama sha ya mike tsaye ya nufi hanyar dakin da yake shine nasa din a gidan wanda har lokacin dakin yake rufe. Ina ganin ya shige na sauke wani irin ajiyan zuciya lokaci guda kamar wace ta tsira daga wani abun tsoro. Maizube ne ta fara mikewa tana fadin wanan yaron yai muna bazata shigowa haka babu sanarwa a garemu Allah yasa dai abincin da akayi zai gamshe shi. Anty fadila tana kitchen din zata bada umurnin abinda za a girka masu yanzu na fada ina kokatin zama. Ke kuma ina zaki zauna nan miji yana gari ai tashi zakiyi kije inda yake ko da wani taimako da zaki masa yanzu. Wani iri naji a raina idan naje mezan masani don dai kawai in basar da zancen ta sai kawai na mike kamar zan nufi dakin sai bayan ta shige dakinta na dawo na shige nawa ba tare da nayi abinda tace min din ba. Ban dade da shiga daki ba wayana ya dauki kara da mamaki na isa inda wayan yake na dauka anty fadilace ke fadin kina inane ? Daki na bata amsa a takaice tace ki sameni a kitchen kai tsaye ta kashe wayan haka yasa na mike tsaye nafito zuwa kitchen din. Nan na samu sunata aiki a kitchen din tare da banufar dake dafa muna abuncin a gidan tana min bayani muna aikin har muka karasa daidai lokacin da aka shiga sallah magariba don dama yanayin hadarin ne yasa garin duhu kamar magariba yayi a lokacin. Bayan mun gama jera komai nakaiwa su maizube nasu a dakita na koma dakina don gabatar da sallah na. Wanka na farayi kafin nayo alwala nafito na tayar da sallah din ban daga daga gurun ba sai danayi duka sallalolina gaba daya nayi kafin in tashi in gyara jikina. A cikin wani dogon riga har kasa mai laushi sai kaina dana gyara tare da daura dan kwalin rigan ta hanyar sako bellen daurin gefena duka biyu wanda yin hakan yabada wani ma,ana a gareni. Fitowa nayi falon ban samu kowa a falon ba sai kayan abincin da aka jera masu saman table masu kyau na zamani da daukan ido wanan duk aikin anty fadilace. Ina shirin komawa bayan na karewa falo kallo da irin kamshin dake tashi a cikin sa saboda gyara na musaman daya samu dan shiga dakin danayi don yin sallah. Anty fadilace ta fito take fadin yyauwa dama yanzu nake shirin shiga surin ki na kiraki ki samu mijin ki a daki ki fada mai abinci na dinning ki kula da wanan matukar yana gari a tare dake wanan yana a cikkn aikkn ki daga yau. Dan jin nayi ina tunane a raina na yadda zan iya tunkaran shi da wanan zancen kamar ta shiga zuciyana taga abinda nake tunane a lokacin. Take fadin kwaliyan ki yayi kyau matuka yanzune kika nuna min kina amfani da shawaran da nake baki kullun. Don haka sauran aiki yana gareki kije ki sameshi a dakin shi tunkan ya fito hakan zai kara kawo kusanci a gareku ko yaushe. Idan kuma ya fito ki tabbatar da kin zauna sai idan ya gama ci kina zaune a gurin wanan ma wani isimine na mata da mata da yawa suke sakaci dashi tana gama fadi ta juya don barin wurin A hankali na ja kafana zuwa dakin bakina yana cike da addua na tun kari dakin nasa yayin da gabana sai faduwa yake min din tsoro da fargaba abinda yin hakan zai iya jawo min idan na kai kaina gareshi din. A kofa na tsaya na da runtse idanuwana tare da tattaro karfi da kuzari azuciyana na kai hannu ina kwankwasa kofan. Kusan sau uku ina kwankwasa kofan kafin naji ana kokari bude kofan daga ciki hakan ya dan sani ja baya a hankali tare da tsoron hakan a raina. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣1️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA DON GIRMAN ALLAH YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA, DARI UKU NE KUDINSA DON NEMAN KARIN BAYANI KI KIRA WANAN LAYIN 08036959257, , , , , Shiru babu wanda ya bude kofan hakan yasa na tura kofan a hankali na shiga dakin csn na hango shi zaune saman sallay yana azzakar da counter a hannun shi. Jin alama an shigo mai dakin yasa shi dago kai a hankali daga inda yake zaune ya hada gwiwan shi biyu wuri daya ya hade da hannayen shi saman kafan da counter din shi yana danawa a hankali. Idon shi ya sauke a kaina kafin nayi karfin halin karasawa wurin shi a hankali ina fadin bansan kana ibada bane dama nazo fadama abinci na saman dining an shirya ma. Kai ya gyada min a kasalance ba tare da yai min magana ba ganin haka yasa na juya da sauri don barin dakin don gabana dake fadawa ban ko tsaya yiwa dakin kallon tsab ba don ganin irin alatun dake cikin dakin nasa. Duk da ganin namu dakin da muke ciki ya kai iyakar haduwa wurin tsaruwa sai naga wanan din nasa kamar shagone na shiga. Ke jimana naji muryan shi a bayana yana fada a hankali naje na tsaya ba tare dana jiyo na fuskance shi ba don yadda yai maganan. Da ban nan mami tazo gidan nan naji tambayan yazo min a bazata don haka na basa amsan tambayan da fadin ya mamud daine yakanzo dubamu sai ko ya jamal da yazo sau biyu . Tsaki yaja yana mikewa tare da fadin ba wanan na tambaye ki ba ai nasan da mamud yana zuwa dubaku ai. Gabana yayi dam sai nayi shiru don yadda ya katseni a cikin fada lokaci guda abin ya ban mamaki matuka. Don haka tun bai fadi komai ba kuma naja kafana na bar dakin don gudun wani fadan kuma. A tsakiyan falo na hango Tajjuddeen tsaye kamar yana nazarin wani abu saidai yana ganina ya nufo inda nake da sauri yana fadin. Me kika shiga yi dakin ogo a yanzu wa ya baki daman shiga masa daki a wanan lokacin? Idanu na zaro a tsorace don don jin irin tambayan daya jefo min a bazata wanda imani da tsoro tambayan ya mamayeni lokaci daya. A cikin karfin hali na bude baki nace waya aikoka tambayana wanan dalilin yanzu. Wani irin kallon tsana ya watso min kafin yace dani babu saidai hakan kada ya baki daman kusanta kanki gareshi kuma. Kaina na dukar kasa nayi dan shiru kafin in dago a fusace ince dashi matsayin ka da kimar ka baikai ka yi man wanan tambayan ba a yanzu . Kafin in bude baki in bashi amsa ya nunani da yatsa a fusace shima yana fadin ke ni zaki rainawa hankali ashe baki da kunya da nake ganin ki haka ? Gaskiya jackson ya illanta maki rayuwa daya tsaya ya mayar dake mace haka mara moriya gashi kina neman kai kanki ida matsayin ki bai kai ba. Idanun sa sun kada sunyi jawur zuwa tsatsan bacin rai dani haka nima domin maganganun shi sun daga min hankali sun tsoratani lokaci guda. Na runtse idanuna ina jin kuna da radadi a zuciyana kafin in bude udanun nawa na sauke su a kanshi cikin tsana ina fadin . Dakata wai malam ka daina yaba min kalamai kamar wani ya aikoka gareni kai a wani matsayi kake da zaka tsareni da wanan maganan akan mijina. Ciki da alaman mamaki ranshi bace ya ware idanuwan shi a kaina yana fadin what ke kanki daya kuwa yarinyar nan kinsan ko wa nake a wurin jackson ? Nima a fusace nace gomane gareni kai waye da har zaka tsareni da wanan dokan akan ya jafar din. Daki kuma ko gobe zan shigesa ne don dakin mijinane bana wani ba kai wani matsayi kake dashi a wurin shi daya har ya baka daman yi min wanan tambayan ? And kuma ka sani duk duniyan nan banga mahalukin da a yanzu ya isa min wanan banzan tambayan da kai min ba a yanzu kokai ka fadane a cikkn maye kila. Kamar yadda kace rayuwata ta samu illa idan har hakane ina ganin ai wanan damuwatace bana wani ba ko ? Daga hakan na juya na barshi a wurun tsaye baki bude yana bina da kallon mamaki don jin abindana fada. Nayi kokarin mayar da mood din fuskana a hakan bai dameni ba saboda kar ya gane maganan shi yayi min ciwo sosai a raina. Harna nufi hanyar dakina sai na canza shawara na nufi dakin anty fadila a lokacin saidai bata a cikkn dakin yasa na jiyo don na koma dakina cike da bacin rai atare dani. Da kyar na samu na karasa daki na shige a take naji wani irin zazzabi yana neman ya rufeni lokaci guda. Gado na fada na dafe kaina gabana yana faduwa nake fadin wanan sace irin bakar ranane haka gareni da har wani dan aiki zai fada min irin wanan magana kai tsaye. Komawa nayi na zube rigingine ina lumshe idona yayin da buguwan zuciyana yake karuwa gareni lokaci daya. Na dade kwance a hakana kafin tunane yazo min ina tambayan kaina shi din wai wani irin matsayi yake dashi a gurin ya jafar din da zai min wanan kalamin haka ? Cikin wani hanzari na mike zaune bandaki na fada na dauro alwala nazo na hau sallaya na fara sallah ko wace ruku,u da sujjada sai na gayawa mahaliccina Allah damuwata kafin na danji sanyi a zuviyana. Ban kara fitowa falon ba kamar yadda anty fadila ta umurci inyi don wanan maganan da mukayi da tajjudeen din ranan ga abi kuma ya tsaya min a raina sosai don ko barci bai barni nayi ba sai faman tunane da nakeyi a daki ni kadai. Washe gari ma ban leko waje ba har wuraren sha biyun rana ina dakina a cikin damuwa da fargaba da zancen wanan mutumin a raina . Gashi lokaci daya duk nabi na susuce ga baki daya idan mutum ya kalleni zai fahinci ina cikin damuwa a tare dani. Suko a zaton su maizube ina wurin yaya jafar dinne a can na kwana a wurin sa don hakane ma tunda ta shige dakinta bayan zuwan shi bata sake fitowa ba har wanan lokacin. Anty fadilace da tajini shiru ta leko dakin sai ta sameni a kwance cikin wanan yanayin na damuwa a tare dani din. Tunda ta shigo dakin take watsa min kallo a razane kamar tana nazarin yanayina yayin da niko ganin ta dakin nawa yasa na dan kakaro fara,an dole a tare dani. Saida ta kai zaune a kusa dani take fadin meke faruwane dake haka kin rame haka a cikin kwana daya ? Kina da wata damuwa ne a tare dake da ya mayar dake haka lokaci guda duk kin zabge ko wani abin ke damun ki haka ko kuma ganin mijin kine ya sakaki fargaba ? A ladabce nace da ita a, a anty lafiyata kalau illa dai kewan innata da kannena da nakeyi duk kwana kin nan. Murmushi tayi taba fadin baki tashi kewan su ba saida mijin ki ya dawo kika saka damuwa haka a zuciyar ki lokaci guda. Kaina na sada kasa ina dan murmushin yake kafin naji tace kinga fada min damuwan ki zainab don nima akwai abinda yake damuna dan zuwan mijjnki garin nan . Don ba wani ya fada min ba Allah ya nufa inji komai a kunnuwa na yau din nan da safe na fito don duba masu girki dazu. Da sauri na dago kai ina kallon ta don jin karin bayani daga abinda take hashe din lokaci guda kuma sai kunyar hakan ya lulubeni dan ganin yadda take kallona na kasa fassara hakan. Naji tace watau zainab dazun din ne na tsunkayi wanan mutumin na tare da mijin ki yana waya a hasale . Saidai jin abinda yake fadane yasani maida hankali in saurare shi dan na fahunci zancen kamar ya shafeki ko wani a gidan nan duk da ban tabbatar da hakan ba gaskiya. Don naji yana fadin gaskiya ogan mu bai kyauta min ba ni a yanzu na tsani na bude ido inga wanan yarinyar a gidan nan. A yanzu nayi nadaman yardan da mukayi har wanan mukai sake yarinyar nan ta kai haka tare dashi don yanzu gaba daya ta juye ta zama wata haddadinyar mace sosai. Katseta nayi ina fadin anty wallahi dani yake don jiya nan da kika turani kiran yaya don na fito part din ya tsareni yana fada wai in daina shiga gun yaya din nan dai na labarta mata komai daya faru tsakanin mu. A gigice tace wanan zancen da daure kai yake wallahi don haka kawai baki masa komai ba zai tsaneki haka ba tunda bashi ke aureki ba ai. Me hakan ke nufi ne gareni kuma anty na tambaya cikin damuwa da tashin hankali a tare dani. Kinsan wasu basu iya samun wuri ba ai sai sucd basa son kowa ya rabu yaci arziki sai su kadai hanyar jirgi daban ta mota daban don haka ya tsaya a matsayin sa zanwa maigidan magana kan hakan ai ta fada tana mikewa tsaye. Ki tashi ki fita ki sake gidan kine mijinki ne banga wani da ya isa yazo yai maki wani iyawa ba a nan yanzu gaskiya don haka kada ki fara kiyi sake har hakan ya faru dake. Har ta soma tafiya nace anty dama kin kyaleshi ai kada ki masa magana har sai idan ya kara min irin hakan zan so ayi mai magana din. Saida ta dan tsaya kamar tana nazari kafin tace to shike nan tunda haka kikaga yafi a barshi in halinsa ne zai sake raina maki wayau ai dan iska damani sam bai kwanta min a rai ba ko kadan. Bayan fitan ta wanka nayi na fito saida na dan dauki lokaci sosai ina kimtsa jikina a gaban mirrow kafin in shirya in fito waje sha biyu har ya gwauta a lokacin. Tun daga nesa nake dan jiyo hayaniya a falon gidan ina dan jin muryan ya jafar din kamar yana fada sama sama wanda ban taba ganin hakan ba a tare dashi. A hankali na tako ba tare dana san ko su waye yake tare dasu ba dasu a falon a lokacin hankalina kwance na nufo falon . Wanda na gani sanya saura kiris na juya don saida na kadu sosai ba kowa bane sai mami da anty Aisha a zaune tare dashi a falon . Gaba dayansu suka juyo suna kallona a cikin mamaki da kaduwa da ganin canzawa da nayi na lokaci guda. Mami ta dan yatsune fuska gami da tsuke fuskan a lokaci guda ta mike tana fadin ni zan koma ke nan tunda na ganka kaji sauki. Saura kiris na sake futsari tsoron ganin mami din a bazata naga Aisha ma ta mike kamar a bazata ta ganni tana fadin cike da mamaki a fuskanta. Zee a gidan nan dama kike zaune wai ko zuwa kikayi kema bata karasa ba don wani tsawa da mami ta daka mata lokaci guda yasa tabi bayan mami din da sauri. Har lokacin na kasa magana sai ido nake binsu dashi a cikin tsoro da fargaba kafin na tattaro karfi da kuzari lokaci guda na bisu zuwa kofan fitan da suke shirin fita ina kokarin gaida mami din a cikin ladabi. Tana kokarin shiga mota na karaso wurin da sauri tare da dan rusunawa ina kokarin gaida su banyi mamaki ganin irin yadda ta amsa min gaisuwan nawa a dakile ba don ba yabo ba fallasa. Irin kallon da Aisha ke bina dashi na mamaki yasa na kara shan jinin jikina ban bar wurin ba sai da naga motarsu ta daga daga farfajiyan gidan don ko kallona mami bata kara yi ba a wurin. Ajiyan zuciya na sauke don abin ya ban mamaki wanan wani irin kiyayya mami take nuna min hakane na ba gaira ba dalili a kaina. Juyawa nayi na koma cikin falon gidan jiki ba karfi don ban taba zaton zamu hadu da mami irin haka ba a wanan lokacin. Bansan har na tsaya ina tunane ba a wurin saida naji takon mutum a bayana firgigit nayi tare dajuyowa shine a tsaye daga kofa ya tsura min ido kafin ya fara takowa zuwa inda nake a nutse. Yaja ya tsaya a gabana sai nayi saurin dukar da kaina kasa ina wasa da yan yatsun hannuna a hankali. Maman ki har yanzu fushi takeyi damu kiyi don haka kiyi hakkuri da duk wani abinda zaki ga tayi maki a yanzu. Samun kaina nayi da sake dan guntun murmushi a fuskana ina fadin ayyah mami har abada mami a matsayin uwa take a garen ai. Don nima nayi missing din uwata mai tausayina da kauna na har kullun saboda kin bin umurnin ta danayi Zan shanye duk wani bacin rai da mami zata nuna min har zuwa lokacin da Allah zai huce mata zuciyar ta akaina. Ina fadin hakan na juya na fara tafiya don barin wurin don kiris nake dana sake hawaye a fuskana don bacin rai ga yadda mami din tayi min kamar taga mugun abu a lokacin. A bangaren mami kuwa rai bace ta shiga mota sai masifa takeyi tare da fadin na fara yarda da zancen mutane da suke fadin harda asiri a wanan zancen. Yaushe na koma haka har yaushe na samu sauyin yanayi haka gaba daya na canzawa ganun ta idan badon a ko ina ta ganni zata iya shedani ba don zaman da tayi a tare dani da shakuwan da mukayi a baya. Da sai tace wanan watace mai kama dani dai amma ba ni zainan din da ta sani band na canza haka lokaci guda a dan watannin da tayi bata ganni ba. Muryan Aisha ya katse mata tunane da take fadin mami kinga yadda yarinyar nan ta koma lokaci guda. Aisha ki rufa mi bakinki indai a kan zancen yarinyar nan ne zee ne kada in saba maki a gurin nan yanzu ki barni naji da abinda ya dameni please. Jin hakan tayi shiru ta barwa ranta abinda ta hango a tare danni wai zeey din mamice wanan ta koma haka kuwa kodai mai kama da itace takoma haka haka wai ? Har mami takai gida hankalinta a tashe sai innuwana take hanngowa a idanun ta tana kokarin kawar da zancen a ranta. A gaskiga tasan yarinyar ba laifi a ko wani ba gare saidai zuciyar ta ya kasa natsuwa da hakan a kanta ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣2️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA BARKA DA JUMMA,A YAN UWA UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMIN ALLAH, , , , , , KADA KI MANTA LITTAFIN NAN NA KUDI NE DARI UKU NE NA FITAR MAKI DA SHIGA HAKKIN WANI NA FADA MAKI GASKIYA YAR UWA DON KIRA ZAKI IYA KIRANA DA WANAN LAYIN 08036959257. Don Allah yar uwa ki guji shiga hakkin wani kada ki raina nauyin hakki a gareki kiji tsoron Allah don akwai ranan tambaya. Ganin mami ya tayar min da sabon miki a rains don haka na shige dakina kai tsaye na fara darza kuka kaman an aiko min da sakon mutuwa. Tambayan kaina nake menayiwa mami dana cancanci wanan sakamakon haka a gareta ? Kafin in koma neman mafita a raina na abinda zai fitar dani wanan sarkakkiyar duhun dana jefa kaina a cikin rashin sani. Duk da nasan ba nina jafa kaina haka kai tsaye ba yadda ake zato banda zabi a kan hakan daya faru dani sai yadda akayi dani a yanzu. Ina cikin wanan tunanen naji an banko kofan dakin an shigo da sallama ta murya na sheda anty fadilace ta shigo dakin ashe. Tun a kofa take bina da kallo rai a bace don a zatonta kuka nake na wani abu a yanzun ma kuma. Sai bina take da kallon mamaki na wanan sallon iskancin dana tsiro yi a gidan bayan dawowan shi kasan ga yadda muka aje zanyi a baya da ita yanzu nazo ina masu faman koke koke haka a gida. Wanda hakan ke nuna alaman kasawa a gareni bayan duk abinda ta koyar dani a bayan shi wanda hakan ke nufin zaman mu a tare baiyi tasiri ba kenan a yadda nake nunawa yanzun. Wuri ta samu takai zaune a gefena ba tare da tayi min magana ba na dan lokaci kafin na dago kai na dan kalleta cikin wani yanayi ina fadin a cikin muryan kuka. Anty me nayiwa mami da take nuna min wanan irin kiyayyan haka a fili shin anty don danta ya zabeni a matsayin sarakuwa a gareta hakan laifine anty don kawai banda gatan daya dace in zama sarakuwar nata ko mai ? Ajiyan zuciya naji ta sauke tare da fadin meye damuwan ki da matar da ba,a gida daya kuke zaune da itaba yanzu. Na katseta da fadin amma ai a gidan danta nake zaune anty don haka mami nada daman da zata shigo gidan nan ko wani lokaci kamar yadda dazun tazo na ganta ina gaida ita ta kyaleni. Tazo gidan nan yau ke nan ta tambayeni cikin mamaki tazo anty na bata amsa wasu hawayen suna zobo min a idanuna lokaci guda naci gaba da fadin . Har kofan gida na bita ina gaida ita mami ta kyakeni shin anty ni a haka rayuwana zai kare a gidan nan bansan matsayina a gun mami din ba ? Zata soki zainab na fada maki hakan yafi a kirga kedai kawai a yanzu kiyi kokarin Allah ya mayar dake wani abu a rayuwa. Amma fa sai idan kin cire damuwa da wanan shirmen hakan zai faru dake don idan kin matsa kin tayar da hankalinki karshen sa ki zama wani abin ki fiye da hakan ga kowa. Do haka nake fada maki a kullun ki daure ki zama wani abin kwantace a duniya kafin hakan ya faru in ma har bata kaunar ki da danta ai ba kece kika dauko kanki kika kawo gidan nan ba kawo ki akayi da sunan aure. Don haka ta samu danta daya kawo ki din tayi fadan haka dashi bake ba ke meye laifin ki a cikin zancen nan bayan cutar da rayuwan ki da akeyi yanzu. Ta yaya mijin ka zaiyi tsawon tafiya irin wanan ya dawo a cikkn kasa ba tare da nuna maka wani kulawa ko damuwan shi a kan ka ba. Don hakane nake kokarin nuna maki hanyoyin da zamu bi har mu samu a samu kanshi gareki idan ma wani abin ne akai maku a tsakanin ku har hakan ke faruwa. Har wani lokaci muna dakin tana bani shawara akan mami dama shi ya jafar din akan inta kokarin in kawar da wani kunya ko nauyinsa a raina indinga cusa kaina gareshi ko yana nuna min baya son hakan da nake mai. Jinta kawai nakeyi a raina sai fadi nake ta yaya zan kai kaina inda za,a wullakantani a daukeni ba kowa ba. Zandai zauna a matsayin tallafawa rayuwan iyayyena da yan uwana a gidan sa don ni kaina nasan da bankai matsayin mata ko masoyiya a gareshi ba. Bayan nayi sallah la,asar ne na fito zuwa dakin maizube inda na sameta zaune tana shan ferfesun a cikin wani plate mai zurfi a gaban ta sai tururi da yake tashi da kamshi a cikin plate din. Ta dago tana fadin yanzu nake fadi in gama in kara lekaki zuwana biyu dakin yana rufe na dauka ai kina wurin mijin kine tun dazu ? Dan murmushin yake nayi iya fuskana a raina ina fadin wani miji da baima san da zamana a gidan nan ba . Zama nayi saman gado ina gaida ita tare da fadin tun safe ina daki kwance ban dai fito bane tunda yanzu gidan akwai maza masu shigowa ko wani lokaci. Tace nima abinda ya zaunar dani dakin nan ke nan kada su takura da zaman mu haka shiyasa ma na fadawa malam zan dawo zuwa jibi tunda dai Allah ya dawo da mijin naki lafiya kuma. Da sauri na dago kai ina kallonta tare da fadi cikin mamaki ki koma gida kuma maizube shifa ba mai zama bane kasan nan wata kila wani abin ma ya kawoshi yanzu haka dayazo din. Don dazun ma naga mahaifiyarshi tazo gidan nan da safe sai naji tace a cikin mamaki ta shigo gidan nan bamu sani ba yar nan ai a gaisa dai ko ? Maizube koni fitowa nayi na gansu a falo tare dashi haka kuma naga ta mike a cikin bacin rai ta bar gidan nan ko gausuwa dana bita waje nayi mata ban samu amsawan arziki a wurinta ba ta wuce. Kai wasu dai sun dauki duniyan nan da zafi a ransu har yaushe wanan matar zata sauko daga fushi da kaddaran Allah da takeyi ne daku ? Kada ki yarda ki biye ma duk wani hali datake nuna maki na kyama a gareki dan ba ita kike aure ba biyewa halinta kuma mijin ki ba zaiji dadin hakan ba don mahaifiyarsa ce ita. Kinga kuwa ba zai taba lamuntan hakan ba koda itace bata da gaskiya kuwa ranshi zai bacine ga abin da zaki mata ke don haka ki daure ki hade tunda ba ko yaushe ne kuke haduwa da ita ba sai irin haka idan tazo ko kinje inda take din. Shima kasa ki daure da halinsa ki zauna kiyi hakkuri mai hakkuri yana tare da riba wata rana duk wanan abin zai zamo tarihin rayuwa a wurin kine a kuma hada da addua ga komai da sadaka don kariya ga ko wani irin bala,in rayuwa. Insha Allahu zan yi maizube na gode da shawaran da kuke bani a kullun keda anty fadila a gidan nan ba zan taba matawa daku ba a rayuwana na fada idanuna yana kawo hawaye a lokaci guda. Nikan yaya kowa keson nayi ta cusa kaina ga ya jafar ne mutumin da har yau ko murmushin arziki ban samu a gurin shi ba balle wani maganan arziki irin na mata da miji ya shiga tsakani na dashi. Ta yaya ake son in biye masa har muyi zaman auren da mutane suke hasaso min rayuwan jin dadi nan gaba dashi. Don in kawar da zancen nace amma dai ba yanzu kike nufin komawan ki gida ba matar malam ? Me zan zauna inyi a nan kuma tunda Allah ya dawo da mijin ki lafiya wurin ki kuma ai sai a raina muna hankali kuma idan na zauna haka. Haba dai wa zai damu da zaman ki a nan don Allah kada kice zaki tafi ki barni a gidan nan ni kadai ba zan iya zama dasu ba wallahi. Zaki iya mana ta ban amsa ko wace mace da kike gani haka ta koyi zama a gidan mijin ta harta saba da hakan kema a sannu zaki saba da zama ke dayan ai. Maizube ban dauka wanan zaman da nakeyi a gidan nan ba na aure ne ba subbahanallahi naji ta fada da sauri har naji tsoro na dago kaina. Idan ba zaman aure kikeyi ba zaman me kikeyi a nan kada ki yarda ki bata auren ki don wani dalili can da kike hange . Kowa da yadda kaddaransa ke zo masa a rayuwa wanan shine naki kaddaran rayuwan kke zuwa mai Allah yayi akwai aure a tsakanin ku wanda muke fatan harda zuria idab Allah ya yarda nan gaba a tsakanin ku . Jinta kawai nakeyi duk da nake yarinyace ni amma nasan hakan ba mai yuyuwa bane a tsakanin mu don ruwa ba sa,an kwando bane. Tambayana tayi da naci abinci kuwa itama dai nasan kokarin kawar da damuwa a zuciyana takeyi lokacin. Idan nabar nan zanje na duba abinda zanci na bata amsa da hakan na dan dade zaune ina tunane kafin in mike zuwa falo na bar dakin nata. Ina ficewa falon na nufa dining erea dan samun abinda zan saka a cikina don naji cikina ya fara kugi a lokacin. Kai tsaye wurin dining din na nufa kayan abincin dake wurin na fsra budewa a hankali gaba daya hankali na gurin abinda nake dubawa din duk sai naji ba zan iya cinsu ba a yadda nakeji lokacin. Haka yasa sam bansan yana falon ba a lokacin yana zaune shi kadai a cikin falon ya tasa takardu da laptop din shi a gaba yana aiki a cikin su. Zaune yake yabar abinda yakeyi ya zuba min ido daga inda nake tsaye ina bude kayan abincin danaga basu min ba nakai zaune daga inda nake tsaye din a cikin damuwa na kai zaune ina dafe kaina da alaman damuwa a tare dani sosai a lokacin a fuskana dana kai zaune din. Kaman ace in dago kai daga inda nake zaune din don jin nauyin da jikina yayi kamar akwai mutum da yake kallona a lokacin yasani dago kai zuwa inda kujerun falon suke ina dagowa na dora idona akansa zaune. Shine a zaune saman daya daga cikin kujerun dake falon zaune ya zubo min manyattatun idanuwan shi a kaina sai kace wani tsohon maye. Wani kallo dana kasa fasarashi a lokacin naga yayi min mai nuni da ma,anoni da dama a gareni lokaci guda nayi saurin kawar da kaina gareshi tare da kara daure fuskana sosai na tamkesu. Saboda kawai na kona masa rai don na dade da sanin halinsa yanzu a dan zaman danayi dasu a can gidan mami din don ba abu bane mai wuya ya disgani a wurin. Karshema sai na mike don barin falon a lokacin don ba zan iya zama a cikinsa ba yana zaune a gurin yana zuba min idanu duk da naga tulin takardu a gaban sa. Ina zaki naji ya fada a daidai lokacin dana mike ina shirin tafiya din jin hakan yasa na dan juyo dan kallon inda yake zaune din. Ni ya zubawa ido yake kallo wanan karon ma dai babu daure fuskan nan nasa a idon shi don haka ban tsaya bashi amsa ba nayi kokarin barin wurin kai tsaye. Muryan shi na koma ji yana fadin wai ba dake nake magana bane kina da alaman taurin kai a tare dake zainab . Har sau nawa kike son in maki magana akan mami da yanzu kike wanan damuwan akan ta mami ni ta haifa ba ke ba don haka ki barni da mahaifiyata wanan ba damuwa ki bane ke . Kalaman daya fada din sun matukar ban mamaki a raina ko dai wanan mutumin ya mata da shi yai sanadin rabuwana da mahaifiyar shine haka? Don Allah ya jafar ka barni da abinda kaja min a rayuwana kayi sanadiyar hadani da mahaifiyar ka data nuna min kauna ta hanyan mai dani wani abu a rayuwana. Ban zauna a gidan nan don wani dalilin ka ba sai don haka iyayyena suka zabar min a rayuwana yau gashi har wani daga cikin yaran ka yana ganin kamar auren Allah da Annabi kayi dani har yake kokarin yi min iyaka da kai a gidan nan. Don Allah ya jafar na rokeka kamar yadda wanan mutumin ya fada min jiya a kanka na nisanci kaina daga duk wani lamari ka . Nima a yanzu ina rokon ka ka samin ido kawai a gidan nan inyi zaman salama da rugumar kaddaran rayuwana a yadda yazo min dakai. Ni kaina nasan gaskiya mami da wasu ke fada nidin ban dace dakai a sa,an aure ba idan makana da wani mafunune a kaina kan hakan da kayi yaya ina rokon ka ka tausayawa iyayyena kada kaja a illanta min rayuwana a gidan nan tunda har an fara yi min gargadi a kanka. Wani kukane yazo min lokaci guda na kasa karasa abinda zan fada a lokscin don kukan dayazo min a lokaci guda din. Yayin da shiko tun dana fara magana ya zuba min ido tare da tattara hankalin shi zuwa gareni yana kallona ba tare dayayi maganan komai ba har lokacin dana ja gwiwana da yai min sanyi a cikin karfin hali don barin falon. Kasake yayi wani irin kunci da makina suna suna sauka mashi a zuciyar shi tunane barkatai yayi a wurin don ba mamakin karfin halin tunkaransa in fada mai wanan maganan gaba da gaba hakane ba ya daneshi. Sai jin abinda na fada akan wanin danace yana kokarin yi man iyaka dashi a gidan nan ne tunanen shi a yanzu don yasan ba kowa ne zai mun barazan hakan ba sai Tujudeen kawai. Ranshi yaji ya baci lokaci guda don me tajudden din zai masa wanan katsalandan a rayuwan shi ya tsorata yarinyar nan har ta tsorata dashi haka ? Mikewa yayi da zuman bin bayana sai kuma ya koma ya dakata don zuciyar shi data gargadeshi dayin hakan a lokacin. Da karfin gaske yake jin zuciyar shi na buga masa ya fada kan kujeran ya koma ya zauna yana lumshe idanuwan shi tare da jin magana kamar a yanzu nake fada mai su. Mai Tajuddeen ya dauki kansa ne a yanzu da har zai mai wanan katsalandan din a rayuwan shi ba yau ba ya sani yana kishin wanan yarinyar duk da yasan dalilin shi na auren ta din. Gashi har ya kai yaja masa raini a wurin ta ta yadda har ta iya kallon tsaban idanun sa ta fada mai magana haka iya son ranta ba tare da taji nauyin sa ba kamar yadda take ji a baya can. A daidai kofan fitowa daga dakin sa muka hade da taju din wani kallo ya bini dashi na tsana ban tsaya bi ta kansa ba na wuce zuwa cikin part din mu kai tsaye. A hankali ya tako zuwa tsakiyan falon har yakai bakin kujera bai iya dago kanshi ya kalli mai zuwa ba a lokacin kafin yai wani yunkuri ya tsunkayi muryan anty fadila tana fadi a bayan su. Sir ko kuna bukatan wani abin motsa bakine a yanzu a kawo maku tana kokarin karasawa inda suke zaune take magana. Sai lokacin ya cire hannun shi daya dafe goshi shi dashi ya dago jajjayeb idanuwan shi ya sauke a kanta tare da kada mata kai cikin karfin hali alaman a,a. Ganin hakan koda baiyi magana ba ta gane mai yake nufi da hakan yasa ta juya da sauri ta bar wurin donta fahinci ogan nasu yaba cikin bacin rai a lokacin. Zama taju din yayi a kusa dashi tare da tsura mai ido don ganin yanayin daya ke zaune a ciki. Don baya son yana ganin sa a wanan yanayin yafi son ganin sa a cikjn yanayin nishadi da kuzari a tare dashi ko yaushe. Don haka bayi kasa a gwiwa ba ya soma fadin wai lafiya na ganka haka ka zauna jiki a mace ? Bai bashi amsa ba sai mayar da kanshi da yayi saman kujera ya daga kai sama tankar yana tunanen wani abu mai muhinmanci a lokacin. Taju din ya kai hannun shi saman kafadan shi yana fadin wai meke faruwane da kai my man ka fada min matsalan ka ko wanan yarinyar ne take son bata min ranka ? Cikin yan dakiku taju din yake jerawa jafar din wanan tambayan cikin bacin rai tare da kulawa a gareshi. Yayin da jafar din ya sauke wani yar gajeruwan ajiyan zuciya ya dago kai tare da sauke jajjayen idanuwan shi ga taju din . Kai taju din ya gyada mai tare da fadin nasan itace damuwan ka a yanzu don tun da muka shigo gidan nan naga yadda ta koma lokaci guda nasan za a samu matsala dakai don canzawan yarinyar nima ya ban mamaki matuka. Bai bashi amsa ba sai dan shiru da yayi ya kurawa carpet ido kamar yana nazarin abinda zai fito bakin shi lokacin. Kafin yace dashi ba itace damuwana a yanzu ba kaine taju don me kuma waya baka izinin shiga harkan gidana haka kai tsaye har kayi kokarin wuce iyakarka dani. Taju din ya dago kanshi a razane yana kallon shi tare da shan jinin jiki don jin abinda ya fada din. Kasan al,adan kasan mu kasan komai don me zaka wuce iyakar ka dani ka shiga harkan matana waya baka wanan daman yaushe har ka samu wannan matsayin haka ? Kai ya dago da sauri yana dan kallon sa kafin jafar din ya nuna shi da yatsa yana fadin daga yau ban son ka kara shigowa gidan nan matukar bani na nemaka da kashigo ba. Duk da ran taju din ya baci amma a fili sai ya daure yana fadin yanzu don wanan shine har ka wani tashin hankalinka haka ? Sai kace wanan wani babban matsalane ni kawai nayi warni dinta ne don ta kiyayye shiga dakin ka kai tsaye bada wani manufa na fada mata hakan ba ai. Murmushi jafar din yayi cikin bacin rai kafin yace dashi kasan nasan ka nasan halinka duk abinda zakayi ina warnin din ka akan yarinyar nan a tare dani. Taju din ya marairaice murya kamar zaiyi kuka cikin ban hakkuri da nuna yayi laifi a gareshi nayin hakan iam sorry hakan ba zai kara faruwa ba tsakanin mu. Shiru sukayi a falon yayin da kowa da abinda yake tunane a ransa kafin taju din ya sake fadin cikin yanayin kyarmar murya kayi hakuri please. Sai lokacin ya dago kai ranshi a bace yana fadin kasan da kayi babban kuskure na bata min shirina akan wanan yarinyar don bazan so na rasa wanan yarinyar ba a rayuwana don ina matukar jin tausayin ta a rayuwana zaman ta yana da ma,ana mai yawa a gidana. Taju din ya kara fadin nayi kudkuren yin hakan zuciyanane ya kasa hakkuri da ganin tana yawan shige maka da take kokarin a yanzu. Wani kallo jafar din ya watsa mai da yasa ya mike ba shiri yana fadin iam sorry hakan ba zai sake faruwa ba tsakanin mu. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣3️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA ALLAH SARKI YABON GWANI YA ZAMA DOLE JINJINA GAREKU ADMINS DIN WANAN GROUPS DIN WATAU ZAURE BIEBI ISAH DA HUGUMA GROUP DA ZAINAB MAKAWA GROUP1 WA YANNAN GROUP DIN SUNCANCANCI YABO A KO INA WALLAHI DAMA SAURAN GROUP IRIN NASU DA BANSAN DASU BA A SHAFIN SADA ZUMUNTA NA WHAFFS, DALILI KUWA SHINE DUK KYAU DA DADIN NOVEL IDAN NA KUDINE BASU YARDA A JAFASHI A WANAN GIDAN NASU. WANAN YA NUNA SU DIN UWAYENE NA GARI MASU IYA BADA TARBIYA GA IYALAN SU DAMA AL,UMMA GA BAKI DAYA A DUNIYA SABODA KARE HAKKIN DAN ADAM YA ZAMA DOLE IN YABAWA WANAN ADMINS DIN GASKIYA IDA BAN FADA BA BAN MASU ADALCI BA A RAYUWA. ALLAH YA KARA TSARE MUNA IMANIN MU DA ZUKATAN MU ALLAHUMA AMIN DON HAKA ZAN TURA WASU NOVEL DINA KYAUTA GA WANAN GROUP UKU AKYAUTA SABODA ALLAH DA ANNABINSA . Tsaye yake a tsakiyan dakin yakai gwauro yakai mari ya kasa zama a dakin ya tuhuta babu abinda yake tunane sai abinda ya faru a tsakanin mu dashi din da yammacin ranan. Ya akayi har wanan yarinyar ta samu courge din da zata iya duban tsaban idanun shi ta fada mai magana haka kai tsaye ba tare data jin tsoro ko kunyar idan shi ba. Anya kuwa zai iya wanan yarinyar nan gaba a yadda yake tunane idan ta kara wani shekaru a hannun shi kuwa ? Kai da sake ya fada a fili yana dafa gado ya kai zaune tare da hada hannayen shi wuri daya yana fadin yaushe ma ta zama hakan ne a gidan nan. Wanan tana da banbaci da zainab din da ya sani a baya wanan kamar idanuwanta ya bude yake gani idan ba karya yakewa kansa ba. Tun shigowan shi garin nan ya fahinci canjin rayuwa a tare da ita gaba daya ta canza mashi ta koma wata babban mace da bai taba zaton kawan ta hakan ba a yanzu. Ya zama dole ya lalubo hanyar da zai kwantar mata da hankalita har ta iya manta da wani zargin da take dashi a yanzu akan tajudeen din dayayi mai katsalandar a rayuwan shi ya tashi rushe masa komai daya shirya a baya. Kwance yakai saman gadon rigingine yana mai lumshe idanuwan shi a hankali kamar mai wani nazari a lokscin. Kafin ya mike zubur yana kiran layin wani abokin shi ba,ajima ba ya dauki kiran suka fara gausawa dashi. Bayan gausuwa daya biyo baya yake tambayan abokin nasa kai mota nake so na mata lates one wanda sai ya girgiza mutum idan an bashi shi. Dariya abokin nasa ya kwashe dashi yana fadin mutumina kayi sabon kamu ke nan kuma ? Dama nasan wanan zaben yar kauyen da kayi zai dawo ya bata ma rai daga baya dan irin diyan tallakawan nan ba ka taba samun su a yadda kake son su. Balle kai mutum irin ka wayayye na gani na fada idan babu wata a kasa har zaka fada tarkon irin wa yan nan diyan kauyawan masu kame maza har gwiwa. Dan murmushi ya sake dan ya gaji da sauraren maganganun shirmen da abokin nasa Amadi yake fada mai a lokacin kan zainab din da shi kadai yasan abinda ya tsara a tsakanin su. Cikin karfin hali yake fadin ba abinda kake tunane bane Amadi wanan dai yar kauyen da kake fadi din itace zan sayawa motar da babu wace mace dake da ita a garin nan ko akwashi kuwa baifi mace daya ko biyu ba a cikin kasan nan. Kai mutumina da gaske kakeyi wanan magana kace yar kauye tayi tasiri a rayuwan ka haka ban sani ba nafa sanka a baya da kyakyamin mata balle wanan data zama yar , , , , , Dakata Amadi banson jin haka ga iyalai na don Allah ya fada muryan shi na nuna warning ga abokin nasa lokaci guda. Amadi din cikin sauri yake fadin Iam sorry mutumina nasanka da riko da wasa nake maka nima nasan ai kai baka harka da mata dama. Idan an samu sai ka kirani ya fada yana kokarin kashe wayan da yake ji kamar ya yarda ita lokaci guda don haushin da abokin nasa ya basa a lokacin. Ya rasa meyasa mutane suke shiga zancen abinda bai shafesu ba kodan irin haka yanzu ya zama dole yayi wasa da idan mutane akan wanan yatjnyar su sancewa ita din mata take agare shi kamar matan kowa. Ya dade a kwance kafin ya mike tsaye ya shiga bandaki ya watso ruwa ya dawo ya tayar da sallah ya dade zaune a gurin shi ba addua yakeyi ba kuma shi bai daga ba sai faman tunanen daya addabi zuciyar shi a lokacin. Yana jin ana kwankwasa kofan shi yaki tashi ya bude sai kallon lokacin da yayi ta hanyar daga kai ya kalli agogon bangon dake dakin nasa makale don gwajin lokaci. Har kusan sati daya nikan bamu hadu ba dashi a gidan duk dako nasan yana gidan haduwane kawai bana yarda muyi dashi. Dan nima da baya na danyi nadaman tsayawa in masa rashin kunya a gaban shi duk da hakan ba halina bane aro nayi na yafa a lokacin. Saboda bacin rai da takaicin maganan da tajudeen ya fada min a ranan na kwata na juya na rasa gano dalilinsa na fada min wanan bakar maganan haka kodan yaga maigidan bai dauke ni a matsayin mace bane a gurin shi yasa hakan ban sani ba. Bawai yadda yayan ya daukeni yake damuna naba a,a hakan ni bai taba damuna ba a rayuwa saidai yadda shi taju din yai min magana a cikin tsanane damuwana a lokacin. Da yammane ina zaune a keance a dakina ban dade da fitowa daga gurin maizube ba da yanzu kusan duk zaman daki muke a gidan ga baki dayan mu. Naji an turo kofan dakin nawa bayan an kwankwasa saudaya sai turo kofan da akayi din lokaci daya da kwankwasan kofan. Ba tare dana juyoba ina kwance a yadda nake jin kamshin turaren yasa kirjina bugawa lokaci daya nayi yun kurin juyowa da sauri don ganin wanda nake zaton ya shigo dakin nawa. Yaja ya tsaya a bakin gadon da nake kwance din yana kare min kallo na dan lokaci guda yana karewa dakin dake gyare fes da kallo. Ido nima na dan dago na kalleshi na lokaci guda kafin in mayar dasu kasa ina kokarin mikewa zaune. Ki kwanta abinki ba wani abu nazo yiba dama na shigone in ganki tunda kina wasan boyo dani a gidan nan yanzu. Yana fadin hakan fuskan shi yana a kaina dauke da bada umurni a gareni lokaci guda. Ban kwanta ba kamar yadda ya bukata din sai gyara zama danayi ina mai sadda kaina kasa lokaci guda dan kallon da yake min din. Da kyar na iya buda bakina ina fadin kayi hakkuri koda zan fito ka fita lokacin yasa baka gani na. Yace ke nan ba,a koya maki gaida mutane ba kike nufi ko me daba zaki iya shiga ki gaidani ba ? Na dago ido da sauri don in saci kallon shi don jin abinda ya fada lokacin still dai ni din yake kallo har wanan lokacin. Ya tsura min idanuwan shi manya shi da suka canza cikin kankanin lokaci da fara maganan shi a kaina . Karasa saukowa saman gadon nayi ina gyara bujen jikina dayan yi squeeze nadan hade hanaye a wuri daya ina fadin . A cikk kyarma ina gudun naje dakin nakene kuma ai min wani fassara na daban shiyasa na daina shiga amma kayi hakkuri dan Allah. Har zuwa lokacin baiyi magana ba sai na kara dukar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna a hankali. Hannu ya tura a cikkn aljihu yana fadin nasan matar malam ta gaji da zama a garin nan don haka gobe za a mayar da ita gida ita kuma halimatu tunda tana karatu sai a barta a nan tare dake . Kai na dago da sauri ina kallin shi wanan karon nan kawar da idona ba daga kallon shi cikin murya mai dauke da son yin kuka nace. Don Allah ka barta ta kara min wasu kwanaki kafin ta koma don idan ta tafi zan shiga damuwane sosai ga hjy har yau ban daina kewar ta ba a gidan nan. Babu mutanene a gidan ko kinmata itama tana da aure ne kamar ki da zan aje matar mutane anan na wata da watannk ai sai a yaba min rashin hankali. Hakan da naji ya kara sa hankalina tashi sosai ya juya kamar zai tafi yana fadin gobe ma zanso na roke shi arziki yai min ai. Kinga yanzu ai gidan kine zaki iya zama ke kadai yadda kika girman a lokaci guda da sauri nabi kaina da kallon dan jin abinda ya fada min din. Yes ya fada tare da sauke min wani irin kallo daga sama na har zuwa kasa yana fadin wa zai ganki a yanzu ya dauka kece zainab din mami a baya mai gudun mutane. Baki na turo gaba ina fadin niban wani girma ba dan Allah ka barmin ita nidai mu zauna a nan tare na fada kamar zanyi kuka a lokacin. A dan rikice yake fadin me akai maki kuma yanzu don shagwaba kawai daga magana kina shirin yiwa mutane kuka yanzu kuma. Idona dago kamar zanyi kuka nace bakai bane kake shirin mayar da sai nayi shiru kuma dan na rasa abinda zan fada mai a lokacin. Yace a cikin zaro idanun shi waje da akai maki me a hankali na furta zaka maida maizube gida mana. What me kike fada dama nufin ki a nan zata tabba tare dake ko me kedai yarinyar nan da alama shagwababiyar mace ce ke . Zama nayi a cikin fushi saman gadon na basa baya yasa kai ya fice daga dakin saina tsunci kaina da sake hawaye lokaci guda. Shike nan yanzu maizube zata wuce ta barmu ke nan ba zan sake ganin wani dan gida ba sai yadda hali yayu ke nan dani duk da naji bada halimatu za,a tafi ba hakan bai hana hankalina tashiba a lokacin. Karshe na mike zuwa dakin nata sai dai na kasa fada mata abinda nayi niyar fada har na shigo dakin a lokacin dan bansan yadda zance da ita kada ta tafi ta barmu ba tunda itama tana son zuwa gidan a lokacin duk da daulan da muke cikin sa kuwa. Washe gari ba karamin mamaki nayi ba abinda ya hadawa maizube na tafiya kowa sai sam barka da ita da anty fadila da take hada mata kayan tafiyan a wuri daya don kuka ya hanani tabuka komai a lokacin. Nasiha da bn baki nasame su gwargwado wurin boyar Allah nan sai kara jadda min kalman inyi hakkuri da rayuwa wata rana idan Allah ya yarda zan dara kan aurena. A mota sukai tafiyan don har gida za a kaita ga tsaraba mai tarin yawa an hadata dashi ban tsaya naga tafiyan ta ba don kukan da yazo min a lokacin dole na koma gida na fada saman gado. Duk dauriyan halimatu itama da taga zasu wuce saidai tayi hawaye a lokacin ranan haka muka wuni sukuku damu sai gidan ya koma muna shiru kamar babu kowa a cikinsa lokacin. Ban fito ba wunin ranan ina daki rufe sai faman tunanen da nakeyi na gida wayana yai kara na dauka innan muce a layi ta kirani tana min godiyan abinda ya jafar ya aika masu dashi. Saidana hade wasu hawayen bakin ciki tare da saita muryana nake fadin inna ai hakan yiwa kaine duk da bansan abinda ya aika masu dashi ba a lokacin. Bayan mun gama waya da inna na sake wani irin kuka mai karfi ni kadai a daki babu wanda zai ban hakkuri dole na kyale naba kaina hakkuri. Suna zaune da ya mamud a haraban gidan mami zaune suna shan iska yazo mami bata gida ta fita zuwa unguwa yasa shi fitowa haraban gidan ya zauna nan ya mamud ya saneshi suka zauna suna magana. Ganin yadda yake ta bayani dan uwan yai shiru ya zurfafa a cikin tunane yasa ya mamud din dan kiran sunan shi a cikin kulawa tare da mayar da hankalin shi gare shi. Jafar meke damun ka na ganka haka yau ko wani abu ya farune yana kallon fuskan shi cikin kulawa yake tambayan shi. Ya sauke ajiyan zuciya firgigit yana kallon dan uwan nasa ya mamud din ya sake fadin meye matsalan kane jafar a cikin yan dakiku ya mamud din yake jera mai wanan tambayan. Ido ya lumshe a hankali tare da sauke numfashi mai kama da ajiyan zuciya yana fadin watau mamud ina cikin matsala da damuwa dani kadai na sani. Sai kuma wani abin mamaki shine a dawowan nan nawa da nayi sai na sake tarar da wani abin mamaki a gidana wanda shine ke kara ban mamaki a yanzu. Shiru yayi na dan lokaci kafin ya numfasa yana kada kafa a hankali yayin da mamud din ke sauraren shi. Ido ya bude yanaci gaba da kada kafan shi yace abin mamaki wanda ban taba tunane bashine waina dawo gida na samu wanan yarinyar gaba daya ta sake min lokaci guda. Guntun tsaki ya mamud din yaja lokaci guda yana fadin yanzu akan wanan har kabi katada hankalin ka haka sai kace wanda yake cikin wani babban matsala. Shi girman ya mace aiba wani abu bane duba ga irin rayuwan da a yanzu take a cikinsa ko kana nufin a yadda ka dauketa haka zata tabbata a gidan ka koda yaushe. Kai ya girgiza yana fadin bashine nufina ba mamud sai ka jira kaji karshen zancen mana kafin ka yanke min hukunci kasan abinda ya sakani a damuwa akan hakan. Ya mamud din yayi kasake yana sauraren dan uwan nasa tare da zuba mashi ido don a yanzu ya tabbatar da duk abinda kanin nasa ke shirin fada mai matsalace babba don ba akan girman nawa dayaga na masa bane lokaci guda. Huci yayi ga bakinsa sai wani gumi dake tsarso masa a goshin sa tankar wanda ya watsa wa kansa ruwan zafi a lokacin. Shikan mamud yana ganin yanayin dan uwan nasa yayi saurin fadin wai jafar meke damuwan kane haka ? Nifa gaba daya duk ka sauya min kamar ba kaiba wanan wani irin damuwane akan zainab din wanda ya susutaka haka har ka tayar da hankalin ka haka wai ? Mumushin karfin hali yayiwa dan uwan nasa yana fadin mamud kafi kowa sanin bawai na auri yarinyar nan bane don na zauna da ita irin na ma,aurata a yanzu. Jafar wai wani irin magana kake kokarin fada min a yanzune wai don me ake aure a rayuwa badan mutum ya aje iyali ya haiyayya fa shima ya bar baya kamar yadda iyayyen mu suka barmu. Yanzu fa jafar kana kokarin rufe bayan talatin da biyar ne a rayuwa don in ban manta ba wacan zuwan naka mami ke fadin kana talatin da biyu a duniya. Me zaka jira da matar ka Allah ya baka mace ta gari da zaka inya controling dinta yadda kake so agidan ka tun a yanzu kan kanta ya karasa wayewa. Nida aca tun farko irin matar da mami ta zaba min ke nan ba wanan ba da nake fama da ita a gidana yanzu don ban isa in tsayar da Nuriya wuri daya ta tsaya ba. Shine abinda nake lurar da mami akan auren ka da yarinyar nan zainab a kullun do ko ita mami Nuriyan bata ragawa ba kasani. Jafar din ya dukar dakai kamar yana sauraren dan uwan nasa abinda yake fada nan ko wani duniyan tunane ya fada a lokacin. Can ya dago kai yana kallon dan uwan nasa kafin yace a cikin kyarmar murya kaman mai shirin kuka a lokacin, mamud mafita nake so a yanzu kan wanan auren nawa. Shiru mamud din yayi don ya rasa inda dan uwan nasa ya dosa da maganan shi yaji jafar din na fadin bana son in rasa wanan yarinyar a yanzu mamud don ina matukar jinta a cikin raina rasa zainab a rayuwana tankar rushewan wani bangaren rayuwanane a yanzu. Cikin mamaki ya mamud ya dago kanshi yana kallon dan uwan nasa da mamaki don har yanzu ya bai fahinci abinda dan uwan nasa yake nufi ba. Can ya dago kai yana ftambayan kanin nasa No jafar ka daina fadan haka don Allah ko akwai wani abinda yarinyar nan tayi makane kake son ka boye min dai ? Kai ya girgiza yana gyara zaman shi tare da lasa saman labben na sama yana mai shafo kanshi a hankali cikin damuwa. To jafar wanan wani irin wullakanci kake son yiwa yarinyar nan haka koka mai damu mutanen banza a daukemu wawaye wadanda basu san abinda sukeyi ba . Nace ka fada min meye damuwan ka da ita kana kawo min wasu dalilai marasa tushe a yanzu. Mamud ba zaka gane bane amma gaskiya nasan bazan iya kula da hakkin yarinyar nan a yanzu ba ko nan gabama. Innalillahi ya mamud ya fada tare da wani irin zabura daga inda yake zaune din kafin yakai ga cire hulan dake kanshi yana dan fifita dashi a hankali don ya samu iska a jikinshi. Kafin ya iya buda baki ya furta a sanyayye jafar baka da lafiyane ko wani abinne ya sameka kake boye muna. Kai jafar ya kada mai alaman a,a ba hakan yake nufi ga maganan shi ba da akwai dai wani zance can kasan zuciyar shi. Jafar ka tuna koni wani abin ya shigewa duhu daya shafi rayuwana kai nake nema in fadawa ka ban shawara akan hakan don me kai a yanzu ba zaka fada min naka damuwan ba a gabana. Mamud nasan da hakan shawara kawai nake son ka ban har lokacin da komai zai daidai min a rayuwa na fuskanci matata. Wani irin ajiyan zuciya ya mamud din ya sauke lokaci guda tare da fadin anya jafar kana da lafiya kuwa ? Yanzu dai na gama fahintar wanan yarinyar batai maka komai ba don haka koma menene yake damun ka a rayuwa ka lalaba matar ka ta hanyan kyautata mata a rayuwa ta yadda zaku zauna lafiya da ita. Saidai ka tuna kada ka yarda ka cutar da yarinyan nan da yawa katuna ba a duniyan nan zamu tabbata ba har idan ka cutawa rayuwan wanan boyan Allah Allah zai saka mata ta ida baka zata ba. Kai jafar din ya sunkuyar a kasa don baida abinda zai fadawa dan uwan nasa a yanzu saidai ina son wanan maganan ya tsaya iyani dakai kafin komai ya daidaita ya mamud din ya fadawa dan uwan nasa. Da sauri jafar din ya dago kai yana fadin nima hakan nakeso bazan so mami taji wanan zancen ba don zata dauke shi da wani fassara na daban. Kada kaji komai jafar ka tuna duk abinda ya same ka mekyau ko mara kyau kamar ya shafeni ne koni. Saidai zan so ka maganan ta makakewa ya mamud din don motan mami daya shigo gidan zuwa parking spece yasa suka mayar da hankalin su gareta tare da mikewa suka nugi wurin motar nata lokaci guda. Kujeran da nake zaune sama anty fadila ta kala kafin tace dani waini na tambaye ki mana zainab wai tunda maigidan nan ya dawo ya nemi ki a shimfidan shi kuwa ? Kai na dago da sauri ina kallon ta don ban fahinci inda zancen nata ya dosa ba yasa nace a cikkn mamaki shifida kuma anty ? Kamar ya shimgidan shi don ban fahinci mekike nufi ba wallahi kayya ta fada cikin daure fuska a gareni. Tana fadin waike zainab wace irin yarinya ce haka mara wayau da hankali ke an fada maki haka zaman aure yake wai ? Iyakar mace taci tasha ta saka mai kyau ajikinta ta kwanta shine zaman aure tsakanin mata da miji kawai a rayuwan su. Idan shi bai neme ki ba bana fada maki hanyar da zaki bi ki ja mijin ki a jikin ki ba zainab kada fa tunanen da nakeyi ya zamo gaskiya a gareku gidan nan. Me kike tunane anty na tambaya cikin marairaice murya don a zatona wani abin kuma ta hango a tare dani sai naji tace dani barshi kawai hasashen hakan kawai nakeyi akan ku bai zama lalai haka din bane. Amma dai gaskiya zuciyana ya fara zargin wani abu a gidan nan yanzu, saidai abinda nake so dake shine koda shi bai nemeki ba zainab kiyi hakkuri ki daure ki kai kanki a gare shi mugani . Da sauri nace ban fahince ki bafa anty ina mai kallon fuskanta don karin bayani a gareni ki dai gwada abinda na fada maki din ta fada tana mikewa daga wurin da take zaune din zuwa kitchen din gidan. Nan ta barni zaune ina tunanen maganan ta ta yaya zan kai kaina da kaina wurin ya jafar din yadda take nufi din. Sam hakan ba zai taba yuyuwa ba kenan nidin fitsarariya kenan take nufi ko ms sam hakan ba zai yuyu dani ba wallahi sai dai duk abinda zai faru ya faru na fada a raina ina masifa da ita cikin zuciyana. Ni a wurins tun daga ranan da nashigo gidan shi har rana mai kama data yau nan taba tunanen wanan abinda take nufi ba a yanzu a tsakanina da yaya jafar din don haka sai maganan nata baiyi tasiri ba a zuciyana ko kadan. Itama daga wanan ranan bata kara yimin irin wanan maganan ba ta kawo ido kawai ta saka min naci gaba da yan harkokina na yau da kullun duk da bawani abu bane illa zaman falo saiko dan fita haraban gidan da yamma wani lokaci musha iska a waje shine kawai abinda nakeyi a gidan. Don shi kanshi ya jafar din bayama zama a gida ko garin kwana biyu zakaji baya kasan ya dan fita zuwa wano kasa na kwana biyu kafin ya dawo. ZAINAB IDRIS mAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣4️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA DA FATAN MUN WUNI LAFIYA UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN, KADA KI MATA DA LITTAFIN KUDINE KIBAN HAKKINA KO KI BIYA RANAN DA NADAMA BAIDA AMFANI GA BAWA. DON KIRA ZAKI KIRA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 08036959257 KO TURA KUDI BAKIN ZAKI TURA GA WANAN ACCOUNT DIN KAMAR HAKA 2254380105 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA AMIN, , , Shi hakki gaskiyane yar uwa zaki ban a ranan da nadaman hakan baida amfani a garemu baki daya don haka karatun wanan novel bai zama dole a gareki ba yar uwa ki barshi shine sauki a gareki da zaki gane gaskiyan hakan a gareki da fatan masu imani zasu fahince ni. Ya mamud yana zaune sai faman tunanen zancen shi da dan uwanshi yake a zuciyan shi tun ranan da sukai wanan maganan ya kasa sukuni a zuciyar shi. Don ya rasa dalilin dan uwan nasa na fadan wanan maganan haka dole akwai wani dalili nasa da yake boye mai a zuciyar shi. Don haka ya zama dole yasa ido kan kanin nasa har ya fahinci halinda da dan uwan nasa yake boye mai. Ta yaya zai iya fahintar hakan bayan ba agari daya ko kasa daya suke rayuwa dashi ba a yanzu koma dai meye zai gane a sannun wanan alkawari yai wa zuciyat shi. Don haka ya yanke shawaran da zuciyar shi zai fara tunkarana ko zai iya fahintar wani hali daga gurin dan uwan nasa saidai kaico ta yaya zai iya fahintar hakan dadin mace mai mutunci ke nan da ace matarshi mai kaunar yan uwanshine da ita zaiyi amfani har ya gano abinda yake so a wurina din. Ko yanzun ma bai baci mai ba don zaiyi amfani da daman shi na namiji ya tursasata zuwa gidan don kawai su sada zumunci a garemu ta hakan har dan shakuwa zai shiga tsakanin mu ai. Da dare suna zaune cikin ikon Allah itace ta dauko zancen jafar din da kanta take cewa dashi yanzu dai kanin ka shi ya fita zancen kowa a garin nan tunda yazo sau daya nasa shi a idona yana ganin bai neman komai a wurin kowa yanzu. Shi jafar din ya dago yana tambayan ta da mamaki tare da fadin ina mamakin wanan halin naki Nuriya ? Jafar naga ko yau muna tare dashi a gidan nan shekaran jiyama mun dade dashi muna hira a waje saida mami ta dawo muka bar wurin. Kece dai bai samun fuskan da zai sake dake a wurin ki don hakane shima yanzu bai damu da ya shigo inda kike ba don yana jin rashin mutuncin da kikewa mahaifiyar shi ko yaushe. Ni din ai duk wani laifi a kaina yake karewa dama a gidan nan fon hakane na kama kaina da kowa don na fahinci ba kauna akeyi ba. Babu wanda bai kaunan ki gidan nan saidai halinkine basa kauna a yanzu don ba kowa zai zauna anaciwa uwarshi mutunci ba yana kallo a zauna lafiya da maishi. Ko haka kokaga sunayi wa naki iyayyen su don kawai ina auren ki shine laifi a garsu baki daya ya kamata ki natsu ki gane hakan zai iya jawa yayan kima bakin jini a gurin su. Bai damu da bacin ranta ba yaci gaba da fadin kin rasa gane cewa shi arziki na Allah ne ba fina jafar yayi ba daya bashi arziki ya barni duk da ina gaban shi . Yanzu haka da taimakon jafar din nake samun ci gaba a rayuwana ko yaushe ba tare da mami tasan da hakan ba din shi ke tallsfa min ba tare dana roke shi ba. Kai kaga zaka iya hakan don ni ban gaji komawa baya ba a gidan mu don haka kaje kaita jiran ya taimaka maka din. Fita batun ta yayi yaci gaba da abinda yakeyi a falon ba tare daya kulata ba harta kare fadan ta ta shige daki ta barshi falo zaune. Kai ya girgiza a cikin takaici yana fadin kina da matsala wallahi ni dai baki isa ki rabani da yan uwana ba wallahi ya fada cikin jan tsuki. Kwana biyu dayin wanan maganan ta fito don zuwa unguwa ne motar ta haka kawai ya tsaya tayi tayarwa yaki tashi ranta ya gama baci sosai tana ciki tana kokarin ganin motar ta baci taga fitowan shi daga cikin gidan nasu yana waya. Kaita kawar gefe kamar bata ganshi ba sai kokarin tayar da motanta takeyi kawai motar taki tashi kuma. Har ya dan wuce ta ya nufi inda motocin shi suke ya dawo inda take ya tsaya tare da kashe wayan da yakeyi yana fadin madam lafiya kuwa ? Wani nauyi da kunya ne ya kamata lokaci guda bai tsaya jiran me zata fada ba yace motar taki ta tashine ya tambaya yana kallon ta. Wallahi lafiya na ajeta yanzu kuma na tayar taki tashi ta bashi amsa yace fito mu gani da hannu ya kira yaran shi mutum biyu sukazo wurin banda taju dake can ya kura masu ido yana bin Nuriya da kallon tsana. Donshi ya ki jinin yaga wata mace ta rabi jafsr din a rayuwan shi koda kuwa yan uwan shine idan ba Aisha daya san kanwar shice ita har yakan dan sakar mata fuska wani lokaci. Da sauri sukazo wurin ya nuna masu motar su duba matsalan ta a daidai lokacin Nuriya din ta koma gefe shi ta tsaya itama. Ganin suna bata mai lokaci yaja tsuki yana fadin idan ta fara baki matsala a kawo maki wata ki daina hawan wanan din don kada ta tsaya maki wani wuri da babu kowa a kusa. Sai taga ya shiga kiran layi ba tare da ya tsaya ba yake fadin a kawowa matar brother din shi mota yanzu mai lafiya na mata zata fita unguwane yanzu. Bin bayan shi tayi da kallo tare da mamakin abinda taji yana fada a bakin shi tace a ranta lalai mijinta yayi gaskiya daya fada mata halin dan uwan nasa gashi tun ba,aje ko ina ba Allah ya nuna mata hakan . Wanan dalilin yasa suka yanke shawara da mijin ta su sameshi har gidan shi suyi mai godiya wanda hakan ya zama dalilin zuwanta gidan namu a wani rana. Na gaji da zaman daki da takura kaina yasa na fito falo na samu halimatu zaune tana kallo na zauna ina fadin halimatu wanan kallon yai maki yawa baki damu da duba littatafan ki ba na karatu. Wanan film din nake son kallo yayan mu yanzu ai na fito dan na kalleshi inga yadda za a ci gaba ta fada hankalinta yana kan tv dake aiki. Wuri na samu na zauna kafin in kalleta ince da ita amma dai kin san sanyin AC din nan yayi yawa halimatu anya halimatu kin dauki rayuwa da sauki kuwa ? Ina jiye maki ranan da zamu koma gida a gaban iyayyen mu ranan da zaman gidan nan ya kare muna dagani har ke don baki dauki duniya da sauki ba ke nake gani. Da sauri ta dago kai ta kara kallona tana fadin gida kuma anty me zamuje yi gida har mu zauna kuma ? Halimatu kanki daya kuwa na tambayeta a cikin bacin rai sosai don dai nasan yanzu halima ta dan san duniya tana da shekara goma ko sha daya ai wurin haihuwa. Tundani inada shekara sha shidda da dan kai da haihuwa yanzu na sha bakwai nake nema in rufe a duniya saidai tashin mu da wayau mu ba iri daya bane da nasu yanzu. Sallama akayi bakin kofan duk da garin ya hade da hadari ruwa na iya saukowa ko wani lokaci . Bakon abune garemu muji sallaman bako a gida don haka gaba dayan mu hankalin mu ya koma ga kofan don ganin mai shigowa din. Ya mamud ne tare da Nuriya da yaran su biyu ke tafe ban san lokacin dana mike tsaye ina sake fara,a a fuskana ba kafin in tuna da waye Nuriya a gurina na mayar da fara,a na dan daure fuska ba yabo ba fallasa garesu. Sannuki da zuwa na samu kaina da fadi tare da dan matsawa a inda nake tsaye a cikin farin cikin ganin su a wanan lokacin. Zainab kuna lafiya ya jafar ya fada a daidai lokacin daya karaso cikin falon gaba daya ya fada ya samu wuri ya kai zaune da gudu yaran suka shige min jiki don murnan ganina da sukayi kafin yarinyar tace anty kin barmu yanzu bamu da mai koya muna assignment a gida kullun sai aunty ta dokemu a school. Kan yarinyar na shafo naji dan namijin na fadin ke ba mommy tace mu barce mata anty ba mu kirata da zainab . Ba uwarba har uban yaji kunyar maganan sai naji yace kuce mata anty matar unclen j daga yau kunji ko ? Kasa nakai gurfane a gefen kujeran daya zauna din ina fadin yaya ina wuni ya gida ya aiki dasu mami da anty Aisha ? Ya amsa dan maganan shi a cikkn sauri sauri da lafiya kalau zainab ya kuke na komai dai lafiya ko ? Na amsa kai kasa da lafiya kalau yaya na juya gurin matar nasa ina gaida ita ba tare dana mike ba sai bina takeyi da kallo ta amsa min da kyat tana wani shan kamshi a fuskan ta. Ko jafar na gida ta fada a cikin wani yanayi na nuna gajiya a tare da ita tana bin ko ina na gidan da kallo da sai kamshin ke tashi wanan aikin anty fadilane hakan. Kafin in bata amsa Anty fadilane a bayan mu take fadin au baki mukayi gidan ashe sannun ku da zuwa a cikin fara,an ta ta karaso inda muke a falon a daidai lokacin na mike daga gurfanen da nake din tana gaisawa dasu. Don ita koda yaushe fuskanta a cikin fara,a yake irin mutanen nan ne da baka saurin gane fushinsu tare dasu. Nuriya ta amsa tare da kara maimaita min tambayan ta da jafar nace yana gida wurin shi muka zo ta fada tana kawar da kai gefe daya daga kallon mu. Bari matarsa ta duba maku shi don dazun nan naga shigan shi gida anty fadila ta fada tare da kallon inda nake tayi min nuni da ido. Cikin sanyin gwiwa naja kafana da har lokacin ina rike da hannun yarinyar jikan mami da suke kira da husna zuwa part dinshi din. Kwakwasa biyu nayi a kofan kafin naji an bude kamar dai kofan da remote yake amfanine don sai kaji an bude ka dade tsaye ba wanda zai bude ya fito kamar dai wance karon da nazo. Don haka sai na murda na shiga da sallamana a bakina can na hangoshi yana kwance saman gadon shi da laptop dinshi a gaba ya daga kafa daya yana aiki. Ga cup a gefen shi da wani ruwa mai ruwa zuma a cikin kofin da alama dai yana aiki yake shan juice din. Kai ya dago yana kallon mu har na karaso bakin gadon ina fadin sannu da aiki yaya su ya jafar ne dama suka zo suna falo. Yarinyar dake rike a hannuna ya tsurawa ido kafin yace Husna tare da daddyn ku kukazo ne yana mikawa ya yarinyar hannu tazo wurin shi. Bin dakin nayi da kallo ko ina na dakin a gyare yake fes sai walkiya yakeyi don gyara ga komai na dakin farine tundaga kan gado wardrobe da mirrow zuwa labullayan dakin duk farare kalane. Juyawa nayi dan fita daga dakin yake fadin ki tsaya ki hada min wanan takardun jin haka yasa na tsaya har saida ya sauka daga saman gadon na nufi gadon don tattara mai takardun nasa. Ba wasu takardu bane masu yawa zube saman gadon don haka sai bai daukeni lokaci mai tsawo ba wurin hadawa na aje mai kusa da jakkan dana gani nasa saman gadon . Gyara gadon karayi dan dan takuran dayayi don hawan saman gadon dayi a lokacin nafito tare da ja masa kofan dakin. A zaune na samesu a falon yana hira dasu a cikin sakin fuska ga abin sha da motsa baki an cika masu gaba dashi wanda nasa hakan aikin anty fadilace . Har lokacin Husna tana makale dashi ajikin shi yana dan mika mata biscuit tana ci a hankali haka yasa na gane yana da son yara ashe shima. A daidai lokacin dana karaso ya mamud ke fadin kawai nazo na samu madam tana murna da motar daka bata . Na dade ina gurin canza mata mota tun lokacin da motar ta fara bata matsala saidai hakan bai samu ba sai gashi ka rigani bayarwa ashe zaiyi godiya yace Kai haba dai madam ai tafi nan garemu wanan yaran haka data haifa muna kyawawa haka dasu ai taci a biyata da abinda yafi wanan ma yanzu. Ai, ashe dama dan yaran ka ka bani wanan kyautan to nagode Allah yanu muna naku yaran watarana kuma ta fada tare da dago ido tayi min wani kallo da bansan ma,anan shi ba. Wanan kamar gobe ai ya mamud ya fada yana mika hannun shi cikin snacks din dake gaban su ajiye dakina na juya na nufa dan in duba abinda zan iya ba yaran a lokacin. A cikin dakin na samu halimatu a kwance tana karasa kallon da takeyi a falon suka shigo gidan a lokacin ban tsaya ta kanta ba na bude wardrobe dina na fara bi da idanu don na rasa me zan basu a lokacin. Idona ne ya sauka wurin sunkin sabulan kasan waje dake a wani gefe sai turaren da bab san ranan shafasu ba a jikina don ko yaushe cikin kawo min turare aka a gidan tun kan wani ya kare. Suna debo na saka a leda nafito kitchen na nufa wurun kayan kwalaman da ake ajewa na zuba a ledan saida ledan ya cika na fito daidai lokacin da har anty Nuriya ta mike tsaye a lokaci suna shirin tafiya. Da sauri na karaso ina fadin cikin yar murya karama har zaku tafi ke nan anty dan har yanzu ina da dan tsorin su da shakkun su a raina don haka bana iya sake jiki dasu. Eh dama ba zama zamuyi ba don akwai hadari a garin saida muka fito mukaga hakan ta fada tana fara takawa don fara fita daga falon. Da sauri na mikawa yaron namiji ledan dake hannu ina fadi karbi wanan ka rika maku nagode yaron ya fada don tun lokacin dana koya masu yin godiya a makaranta idan wani ya basu kyautan wani abu na koya masu yin godiya ga mutum. Ya mamud ne ya tsaya yana fadin zainab mun gode mu zamu tafi sai a kara hakkuri a zauna lafiya da kowa da sanu zaki saba da bahagon halin wanan mijin naki ya dan karasa maganan sa a cikin barkwanci. Nagode yaya na fada a cikin ladabi gareshi yaci gaba da fadin ina fada maki kullun zainab ki daukeni kamar dan uwan ki na jini har in jafar yayi maki wani abu zainab don Allah ki kirani ki fada min. Har wurin motan su muka rakasu saida kyar Husna ta yarda ta shiga mota wai zata zauna a wurin uncle ita ina jin ya mamud yana lalashinta da tabari zai kawo ta sufita yawo tare da uncle da anty sai ta washe baki tana dariya dan yarda da hakan daya fadamata din. Bayan tafiyan sune na sauke zuciya tare da juyawa don nakoma ciki tsaye yake ya dora hannayen shi duka biyu saman weist din shi. Tare da kura min idanuwan shi a kaina sai hakan yasani na tsargu dashi dan irin idanuwan daya watso min din lokaci guda . Na fara tafiya naji yana fadin da alama kina son ganin baki a gidan nan ko don naga kamar zuwan su ya sakaki nishadi yanzu haka ? Tambayan nasa ya ban mamaki saidai babu hali bada amsa a gareshi don gargadin kowa a gareni shine nayi mai ladabi da biyayya a kullun. Don hakane na kakaro murmushin dole a fuskana da ban tashi yiba na soma tafiya don na kagu na bar gurin a lokacin. Saidai kuma zuwan su baida ma,ana gareki saboda kin nuna masu irin zaman da kikeyi dani a gidan nan . Da kina da wayau da kin nuna masu nidin mijin kine ai ta hanyar zama a kusa dani ko kiyi dan wani abinda zai nuna mudin mata da mijine ai. Da sauri na dago kai ina masa kallon ido da ido na dan lokaci kafin na mayar da kaina kasa na dukar da sauri dan ba zan juri mai irin wanan kallon ba. Da fatan kin fahinci abinda nake nufi da hakan koda kuwa mamine ta shigo gidan nan ya zama dole ki nuna nidin mijine a gareki yanzu ina fatan kin fahinci mai nake nufi da hakan ? Kai kawai na gyada mai ba don na gama fahintar mai yake nufi da hakan ba a lokacin sai washe garine nake fadawa fadila yadda mukayi dashi . Nisawa tayi tare da kallona a cikin mamaki take fadin akwai magana ke nan zainab mijinki bai shirya amsan ki a matsayin mata a yanzu . Na rasa me hakan da yakeyi yake nufi don yana da wata manufa ta daban ke nan akan ki koda ya aure ki. Kallonta nayi cike da fargaba a tare dani tace kwarai burin ko wasu ma,aurata shine su raya kansu da madara ko zumar kauna . Amma shi mijinki nasa daban ne akan auren ku zainab dole akwai inda ya dosa dake a rayuwan shi don babu zancen kankanta a tare dake yanzu. Kedin kinkai matsayin da duk wata mace cikakkakiya ake tunanen takai kamar yadda yace hakan ba laifi mu kuma sai muyi amfani da wanan daman wurin jefa mashi kaunarki a zuciya mu gani bashi din ya fadi hakan ba bude kunnuwan ki ki saurareni da kyau yanzu. Mutukar baki ko mamin naku sukazo gidan nan ke kuma sai kiyi amfani da naki daman na ya mace ki dinga shammatar shi dole shi har idan lafiyayin namiji yake dole ya fada tarkon da zamu haka masa din. Amma fa zainab hakan ba zai samu ba sai idan kin kara jajircewa sosai kin kawar da wanan kunyan naki da kike dashi irin na matan hausawa. Zaki iya hakan koba zaki iya ba don in sani kada in bata lokacina don naga kema kina da kafiya akan wani hali naki na daban. A hankali na gyada mata kai tare da furtawa a hankali cikin kyarmar murya da zan iya anty insha Allahu. Nan dai tayi ta koyar dani hanyoyi dabab daban da zan tunkari matsalan dake gabana din ina mata godiya wanda ni kaina nasan gaskiya ta fada min ga wanan bahagon auren da Allah ya kaddareni da yinsa a yanzu da kurciyana. Ban yarda da shawaran fadila ba kadai don jajircewa nayi sosai ina raba dare wurin mika kukana ga ubangjji mahaliccina sai gashi ina ganin sauki ga al,amarin nawa cikin dan kankanin lokaci. Eh dole ince hakan do kuwa yanzu ankai shi da kansa zai shigo har dakina mu gaisa da safe haka kuma idan zamu kwanta barci duk na fahinci hakan a yanzu. Duk da dai ba wani sakin fuska amma zai shigo mu gaisa ya tambayeni idan banda wani matsala a tare dani ko kuma idan ya dawo wani lokaci ko dakinsa baya shiga zai shigo har dakina yayi min ya gida tare da tambayan badai matsala ko ? Idan muna dashi zan fada mai ko idan muna son wani abu zan dan sake infada mai komai sai yin hakan da yakeyi ya dan jawo muna kusanci a tsakanin mu. Inda nakan shiga part dinshi da safe in gaidashi kafin shi ya shigo nawa part din da sunan gaisawa dani. Bangaren taju kuma yanzu ba kasafai nake ma ganin sa cikin gidan ba sai can ba a rasa ba zamu dan hadu dashi sama sama muke gaisawa dashi din ba tare da wani sakin fuska ba ga kowan mu. Kwaliya kuma irin na daukan hankalin maza kamar yadda fadila tace na jajirce gutin yinsu iya gwargodon hali ina bakin kokarina saidai kallo daya zai min ya kawar da kanshi gareni. Sai wanan abin kuma ya fara damuna a zuciyana mutum kamar dutse shi baya ko sanin na ina mai wani kwaliya a hakan. Kamar yadda yace indinga nunawa udan baki sun shigo hakan na daure tun ina jin kunya har na fara daina kunyanshi ina nuna muna normal dashi ai a zaman mu . Don a gaban baki mu har wasa da dab dariya zamuyi kamar ma,aurantan gaskiya ne ni da shi ai sai idan sun tafine mukoma kamar yadda muke baran baran. ZAINAB IDRIS MAKAWA ws🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣5️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU HAR KULLUM MASOYANA TARE DA FATAN GAMAWA DA DUNIYA LAFIYA ALLAHUMA AMIN. YAR UWA BAZAN GAJIBA WURIN TUNATAR DAKE SAUKE NAUYIN HAKKIN WANI A KANKI DON ALLAH IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WANI AKANKI NAGODE IDAN KIN FAHINCI MAI NAKE NUFI. Rayuwa mai dadi haka rayuwan namu ke gudana a gidan har zuwa lokacin daya fara zancen komawa inda ya fito. Ban dauki zancen wani abuba ni dai nasan ya share sati uku a kasan nan ban kuma san mr ya kawo shi kasan nan ba balle. Iya ka dai nasan da cewa dan zunwan shi kasan yasa na dan saki jiki dashi don zaimun magana in bashi amsa ba tare da jin tsoron shi ba a yanzu, ko kunyar shi ba. Inda shima kamar hakan yana mashi dadi yadda na dan fara sake jiki dashi din ba tare da nuna tsoro a garshi ba. Don haka kawai tun ranan da ya mamud ya kawo su husna muka fita tare yawo dasu da halimatuna . Sai hakan ya zama mai kamar jiki ina zaune kawai zai bugo in shirya mu shiga gari . Inda a dan fitan da mukeyi din zai saya muna abubuwa mu dawo gida dashi sai dai duk fitan da mukeyi din bamu taba zuwa gidan mami har zancen komawan shin nan ya taso. Zaki iya cewa banda zuciya don har yau ban manta da mami ba a cikin raina . Ba hakana bane mai karatu mami ina jinta a wani bangare na zuciyana sosai ta yadda ba zan iya mantawa da alherin ta gareni ba har wanan lokaci. Da yammaci ana gobe zai tafi ya shigo gidan ya sanemu zaune a falo a falon shima ya zube sabanin yadda yake idan ya samemu a zaune yawuce mu saidai mu gaida shi, ko juyowa bayayi garemu yake amsa muna gaisuwan mu. Muna gaida shi ganin ya kai zaune ya zuben saman kujera tare da kai wuyan shi ga masangalin kujera ya nisa da dan karfi lokaci guda yasa duk muka sha jinin mu a falon don dama mu uku ne zaune a falon. Zainab naji ta ambata a cikn wani murya dake nuna kasala a tare dashi har lokacin kanshi yana dage a yadda yake saman kujeran. Yayin da idanuwan shi suke rufe har lokacin alaman lumshewa a dan sanyaye na amsa mai da na,am yaya hannu ya miko inda nake zaune din yana fadin zo ki min massage din kai. Dan jim nayi kafin in juyo in kalli inda anty fadila take zaune daidai lokacin da take yunkurin tashi don barin falon lokaci guda. Jin ban taso daga inda nake ba don ni ban ma fahinci mai yake nufi ba a lokacin yasa shi bude idanuwan shi ya sauke a kaina. Babu kowa a falon dagani sai shi a lokacin don da hannu fadila tayiwa halimatu nuni da su bar falon har suka fice bai sani ba din idon shi dake rufe kanshi kuma dage a sama. Bakiji me na fada bane ya dan fada cikin daure fuskan shi zubur nayi na mike ina fadin banji ba yaya . Kizo ki tausa min kafa na da kai ki fara tausa min kafana tukuna ya fada yana mai da kanshi a yadda yake zaune da farko. Mikewa nayi na fara takawa a hankali zuwa inda yake din a hankali kamar wace kwai ya fashewa a ciki lokacin. Har na zagayo zuwa bayan kujeran saida na runtse idanuwana kafin in daga hannuna in dora a kan nasa a hankali na fara dan cakula mai kai din. Wani irin shock naji a daidai lokacin dana dora hannuna saman kan nasa don taushin kan da kuma santsin sumarsa kamar na dan bature ba african ba. A hankali na ci gaba da dan matsa masa kan ina jin yadda yake sauke numfishin shi shima kamar yana jin dadin abinda nake masa din. Saitin goshinshi ya nuna min adaidai lokacin yana gyara zaman shi yana fadin ki tausa min nan gurin yana min ciwo sosai wallahi. A raina nace yanzu da ciwo ya sameka ne kasan amfanina a gareka ko ko a fili kuma cewa nayi dashi sannu a hankali yace nagode. Can naji ya sake wani irin ajiyan zuciya tare da fadin ki kara tausa min shi da karfi zaifi don ciwo yake min sosai. Hakan yasa na takankare iya karfina ina dan dana masa saitin goshin nasa da dan karfi kafin inji ya rike min hannayen nawa lokaci guda yana fadin. Ai sai ki fasa min goshi da wanan irin dannan da kike min a daidai lokacin kuma mukaji an shigo falon babu ko sallama. Wanda haka yasa dagani harshi muka dago don ganin ko waye ya shigo a lokacin haka babu ko sallama tunma dai ni da naji kunyar yadda maishi ya same mu din. Don sai a dauka ko wani wasan mata da mijine mukeyi a lokacin do yadda yake rike da hannayena a hannun shi. Ba kowa bane sai taju tare da wani dayan security din shi suka shigo a lokacin idanuwan su kar akan mu tundai taju din da kamar idon shi zasu fado kasa don mamakin yadda ya samemu din a lokacin. Ganin su baisa ya sake hannuna dake rike da nasa ba a lokacin saima kokarin zagayo dani ta gaban shi da yake kokarin yi din. Ki matsa min kafana ya fada kafin ya sauke kallon shi garesu a inda suke tsaye di kamar an dasa su wuri daya. Can na tsinkayi muryan shi yana fadin me kuke anan kun tsaya mi saman kai haka ? Kamar wa yanda aka tsikara lokaci daya suka fara takowa zuwa inda yake zaune din ni kuma na kama kafan shi na fara murzawa a hankali lokacin . Naji dayan yana magana duk da acikin harshen turanci suke maganan nasu na gane mai suke fada don zancen ticket din jirgi naji sunayi wai babu jirgin da zai tashi direct a gobe sai sun shiga na wani kasan an sauke su a can. Tsuki naji yayi tare da fadin shi ba zai sauka ko wani kasa ba saidai su bari ranan da jirgin zai tashi suyi booking zaifi. Yana fadan haka ya mayar da idanuwan shi a yadda suke mai da farko ya kara lumshe su a hankali. Duk da ban dago kai ba nasan da mai kallona a cikin su don jikina da ya bani hakan lokaci guda yasa na dan dago kaina da yake a duke na dan kalli inda suke tsaye din. Wani kallon tsana da ki taju din ke aika min dashi lokaci guda wanda yasa nayi saurin kawar da kaina daga inda suke din tsaye. Daga haka suka juya dan barin falon saidana dan dauki lokaci ina matsa masa kafafun nasa kafin yace dani ki huta hakana nagode. Daga haka kuma ya yun kura da niyar mikewa a daidai lokacin da nima na mike din muka dan gwaura kan mu da juna da sauri ya ja jiki shi yana fadin kiyi a hankali fa. Nikan falon na bari gaba daya don a rikice nake sosai a lokacin tun wanan shigan da nayi ban kara lekowa falon ba sai washe gari. Don dan tunanen dana fada yasa dana samu barci ban falka da wuri ba sai da gari ya waye tarrr, . Wuraren takwas saura na safe aka buga min daki a hankali kamar maishi baison aji shi da mamaki na mike zuwa kofan na bude. Anty fadilace a tsaye ina budewa ta shigo da sauri tare da mayar da kofan ta rufe taja hannuna zuwa bakin gado tana fadin. Zainab kinji abinda naji jiya a gidan nan kuwa idan ba kunnuwa ke min karya ba wallahi tunane na ya zama gaskiya ke nan kan mijin ki. Anty meya faru na fada a dan rikice tace wai kina nufin ke bakiji hayaniyar da akayi a gidan nan ba jiya duk saboda ke . Ni kuma anty na fada ina nuna kaina a cikin mamaki da abinda ta fada din kaina. Wai ke duk wanan hayaniyar kina nufin bakiji ba zainab wallahi fada sosai naji sunayi idan ma banyi karya ba zainab har djka naji wallahi a tsakanin su Innalillahi na fada sai data kalli inda kofa yake tace cikin kashe murya wanan mai kama da mata din taju shine ke nuna kishi ki a kanki . Ni meye ruwana dashi dan Allah na dai gane wanan mutumin baya kauna na sam a gidan nan don irin kallon tsanan da yake jifana dashi ko wani lokaci. Ba zai kaunace ki ba don yasan kedin zaki iya canza mijin ki ga rayuwan da sukeyi a ko wani lokaci idan kuna kebewa daga shi sai ke a gidan nan. Ke ni da farko har naji tsoro na dauka barayi ne suka zo muna saida na saurara na gane a cikin gidan nan muryan ke tashin kuma fada sosai naji a tsakanin su. To Allah ya sauwaka na fada ba tare dana fahinci komai a cikin zancen nata ba takeci gaba da fadin wanan abin ya ban mamaki matuka wallahi. Wata kila wani aikine ya hadasu fada don jiya naga sunzo mashi da wasu takardu a hannu su suna mashi bayani. Zaisa su ambaci suna ki a cikin fadan su zainab ke yarinyace karama wallahi don magana a yanzu baida amfani dake sai nan gaba. Baki na turo gaba ina fadin kai anty yanzu fa na girma nima ina da wayau kamar kowa. Mikewa tayi tsaye tana tsuki tare da fadin ni bari in fita kada ya tsurani da farar safiya haka cikin dakin nan ya dauka gulma mukeyi. Tana fita nikan ban kwanta ba na shiga wanka tunda gari dai ya waye tarr a lokacin na dan dauki lokaci a bayin don haka dabi,ana yake ina dan dadewa a cikin bayi idan na shiga. Ina wanka zuciyana cike da tunane zancen da tazo ta fada min din sai cewa nake me ya hadasu fada hakane har da duka kamar yadda anty ta fada duk dai ba abinda ya shafeni bane don tare na gansu ai. Na fito daga bayin ina tsane ruwan daya taba min kaina dagani sai dan tawul karami da daure gaba don dakina ne ko halimatu sai jefi jefi take shigowa inda nake . Banyi sanyi a gwiwa ba don ganin ko waye ya shigo dakin a lokacin na dago kai da sauri ina kallon kofa da dan karamin tawul a hannuna. Ar,ba mukayi dashi yana tsaye a kofan dakin bai karasa shigowa ba yake fadin ke me wanan matar ta shigo yi dakin nan yanzu. Da sauri na dan kara kallon shi ina fadin wace mata ke nan yace wanan mai aikin nace abinda zata girka ta shigo tambayana. Saida ya bini da wani irin kallo kamar yana zargin abindana fada mashi din don rashin yarda da hakan yace Are you sure na daga mai kai kawai ashe bakin mu yazo daya da ita don itama data fita daga dakina ta same shi zaune falon sai data kadu tana gaidashi a cikkn tsawa yake fadin ina ta fito ? Tace mai wurin madam ina son tambayan ta break fast ne ya bita da wani mugun kallo kamar na tsana ta wuce zuwa kitchen kai tsaye. Abinda yasa nace hakan kuwa don akwai ranan da ta taba fadan haka a gareni a cikin wasa yasa na rike wanan kallaman nima a yanzu. Fita yayi daga dakin da sauri ta hanyar bugo min kofar dakin da karfi da ganin sa a hasale yake dai a lokacin. Nikan har na shirya ina mamakin hakan a raina duk dana shirya ban fito da sauri ba sai wuraren goma da wani abu na safe. Da alaman har ya karya ya fita lokacin don kamshin turaren shi daya bari a falon wanda ke nuna ya shigo ya fita don wani lokaci da haka nake gane fitan shi gidan ko dawowa shi gida . Zama nayi na karya kummallo nima ba tare da wani damuwa da kara bin zancen shi ba don na fawalawa Allah al,amarina da dadewa ko. Ibadane dai akansa nake ko yaushe ina raba dare ina kai kukana ga Allah kamar yadda malam mijin mai zube da innan mu ke yawan tunatar dani yin hakan ko wani lokaci. Sabbin masu gadi da security na forces ne aka watsa yanzu a gidan ta ko ina ban san da hakan ba saida fadila tazo tana fadi. Banyi mamakin hakan ba don girman gida dama yaci ace akwai masu aiki wadattatu kamar hakan a gidan. Kwana biyu tsakani suka bar kasa ya tafi ya barmu da tulin abi arziki a tare damu ta yadda ba zamu nemi komai mu rasa ba a gidan ko a waje. Bai kira wayana ba tunda ya tafi har kusan sati uku da tafiyan shi gashi ina son zuwa wanke kai a saloon don yanzu na saba da hakan. Gashi kuma fita bada yardab shi ba yana cikin gargadin da maizube tayi tamin kafin ta wuce hakan yasa na gane wanan dabi,an baida kyau. Mace ta dinga fita gidan ta ba tare da sanin maigida ko umurnin sa tunda naji maizube tana faman jaddada min hakan ko yaushe yasa na rike wanan a raina sosai. Don hakane nake faman jiran kiransa a waya don na fada mai ina son fita zuwa wurin wanke kaina da yake min kaikayi yana son wanki a lokacin. Bai kira ba kamar yasan ina jiran kiransa sai bayan kwana biyu sai ga kiranshi ya shigo a wayana . Banyi gagawan daukan waya ba don haka fadila ta koya min sai gab da zai katsene na daga wayan nasa da sallama a bakina. Ke wata irin yarinyace wai a dinga kira baki daga waya sai ya katse sai naji yaja tsuki kayi hakkuri na fada a hankali . Numfashi naji ya sauke tare dan ja kadan kafin yace ya kuke hope ba matsalan komai a gidan kowa kuma na aikinsa yadda ya dace. Bamu da matsala na fada a sanyayye saidai wurun wankin kai nake son zuwa dama kuma sai baka kira ba in fadama. Sai idan na kira zaki fita a wanke maki kanki ke wata irin yarinyace wai da gidadanci haka wai ? Amma kasan fita bada umurni ba baida kyau a musulunci don haka iyayyena suka horeni dashi tun a gida . Shout, up ki kama min baki da wanan irin maganan meye amfanin motocin dana aje maku a gida hakana . Shiru nayi banyi magana ba sai sauraren shi da nakeyi kawai yadda ya hauni da bala,i don fadin gaskiya kawai. Waishi wani irin mutum ne haka mai bahagon haki kamae dai ba musulmi ba duk wani dabi,a na musulmai shi sai a slow harkan shi dai . Muryan shi na tsikayo a cikin wayan yana fadin akwai wasu masu aiki da kabir zai kawo maku yau zasu dinga dafawa masu gadi da sauran aiyukan gida abinci da fatan zaki kula da hakan. Insha Allahu na bashi amsa ina sauke numfashi don tunanen dana danyi na da lokaci nasa saida naji muryan shine na dawo a cikin hankalina. In tafi wurin wanke kai din na kara tambayan shi lokacin dana fahinci yana kokarin kashewayan nasa lokacin. Ki tafi ya bada amsa a dan hasale yana kashe wayan shi sai bin wayan nayi da kallon mamaki kamar shine a gabana. Abin mamaki kwana biyu dayin wanan wayan dashi sai ga wani kiran nasa ya kara shigo min dauka nayi da mamaki ina bin wayan da kallo tare da tambayan kaina wani abu ya samu kuma yanzu yasa ya kira wayana. Don dai na fahinci shi baya kirana sai idan akwai wani dalili magana da zai sa ya kirani din zai kira layin nawa ina dauka da sallama naji muryan shi yana fadin. Ke ki shirya kuje asibiti ku gaida hjy samu,naka tana nan an kawota asibiti jiya tana tambayan ki . Innalillahi nace kafin in tambaya cikin muryan dake shirin sake kuka ina fadin yaya meya sameta da sauki jikin nata ko ? Idan kije zaki gani ya fada yana kashe wayan sai nabi wayan da kallo a rude don iya kacin maganan ke nan daya fada min. Banyi sanyi a gwiwa ba na fada wa fadila muka shirya a gurguje don zuwa duba jikin hjy din duk da ina fargaban haduwa da mami a wanan lokacin. Ba yadda zanyi don dole in tafi koda bai umurce da haka ba don hjy tafi gaban haka a wurina don nima a matsayin jika makusanta ta daukeni a zuciyar ta. Abinci lafiyayye da mara lafiya zata bukata da sauran abin sha duk anty fadila ta shirya wanan muka fito driver yana waje suna jiran mu tare da wani security daya. Dukkan mu uku baya muka shiga munsha kyau sosai damu duk da asibiti zamu tafi gaida mara lafiya din. Ba wanda yai magana a cikin mu ido kawai muka zuba masu sai gashi sun kaimu har asibitin da aka kwantar da hjy din. Bamu sha wani wuya ba don komai na zuwan mu kamar a tsare yake busa umurnin shi a wurin su din don yai masu bayanin komai kafin mu fito. Gabana yana faduwa sosai duk da a cikin dan dakewa nake saboda zaunar dani da fadila tayi ta tsara min kkmai. Dakin maikyau kamar mutum a gidansa yake fadila nagaba ina tsakiyan su muka shiga dakin da sallama a bakunan mu. Mami ne saman gado zaune sai Aisha dake gefe da wayan ta a hannun ta tana duba har yanzu wanan bakar sana,an nata yana nan mata ashe Nuriya kuma da yaranta suna saman kujera suma suna nasu harkan na daban. Amsa sallaman sukayi batare da sun san ko suwaye suka shigo ba a lokacin sai daga baya da suka gane mune naga mami din ta kawar dakai ga duban mu. Gaida su mukayi a bisa al,adan bahaushe idan yaje dubiya ya samu mutane a gurin ya fara gaudasu tare da tambayan jikin mara lafiya din. Ba yabo ba fallasa suka bamu amsa wanda Aisha ce ta iya amsa muna din a lokacin ba wanda yai muna nuni da wurin zama don haka muka tsaya a tsatsaye daga dan nisa kadan dasu. Ba wanda ya kara bi ta kanmu muna tsaye saiga security din da mukazo dashi ya shigo dakin rike da basket din abinci da sauran tarkace. Yana gaida su da tambayan mai jikin mami bata samu amsa mai ba take tambayan wanan kayan fa a cikin daure fuskan ta . Yace madam ne ta zo dasu duba mara lafiya ku koma dasu ta fada a gimtse fuska babu sauki sai ga ya mamud ya shigo dauke da ledan magani mai tambari asibitin a hannun shi. Daga kofa yaji abinda mami din ta fada ya cewa security din ya aje tare da fadin zainab ashe kun shigo yakuke ya gidan. A dan rakube na amsa mai tare da gaida da tambayan ya maijiki yace taji sauki ko dazun da safe saida ta tambayeki ai. Kai mamud nace a fita da kayan nan kace a ajesu koda matsiyaciya nake banga abinda zai kaini cin abincin yar yaudara ba ai. Komai idan na wa yan nan ne bazan taba karban shiba ni haba haba mami haka bai dace ba wallahi. Zainab fa tana da daman zuwa nan ta kawowa hjy a bu don yanzu itama she is part our family ai tunda danki ke auren ta nagani. Zainab din tazo ne hjy dake barci ta fada kamar a mafalki lokaci guda shi ya amsa mata da eh hjy ai gata a tsaye ma akanki. Hannu hjy ta miko min tana fadin yar nan ashe da rabon kara ganawan mu zo kusa dani ki zauna tana kokarin yunkurawa daga kwancen da take. Da sauri na karasa bakin gadon ina fadin hjy ashe baki da lafiya hakane wallahi ban sani bane sai dazun nake ji. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣6️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA UBANGIJI ALLAH YA KARA MUNA IMANI YASA MU CIKA DA KALMAN LA,ILLAHA ILLAH MUHAMMADAN RASULLILAH ALLAHUMA AMIN, , , , Hannuna ta rike na wani dan lokaci tare da sauke idanun ta gareni tana fadin ance mijin naki baya kasan nan ashe ya koma inda yake ke nan. Ganin gani kusa da mami a inda take zaune har kamshin jikina yana dukan hancin su daga ita har Aishanta. Yasa mami jin wani irin tsana na ya kamata tundai data dubu yabayina gaba daya na canzawa sanin da tayi min a baya can. Hakan yasa ta mike dan barin dakin ga baki daya ranta kuma a bace da abinda idonta ya gane mata game dani din lokaci guda . Don a kullun zata ganni sai taji tsana da take min yana kara karuwa a zuciyata duba ga yadda danta ya gyarani cikin dan kankanin lokaci kadan. Ina kuma zaki hjy ta tambaya a cikin yanayi zafin ciwo har lokacin hannuta ya rike da nawa take fadin. A zuba min abincin da zainabu ta kawo min inci tana rufe baki Aisha da kanta ke duke saman wayan ta tace kai amma hjy nan dazun nan fa aka gama fama dake kici abinci kika ki ci. Yanzu kuma kice wai a zuba maki wanan da baki san ma komeye a cikin sa ba don gulma da iya yin ki na tsofi. Uwarke ce gata gabana yar iyayi a zuba min abuncin gidan jikana in ci inace dazu da abinfa mamuda yakawo min na karya dashi. Sam basu ji dadin wanan maganan tsohuwar ba a lokacin babu yadda zasuyi dole aka bude abincin a lokacin sai kamshi ya bude dakin lokaci guda. Ya mamud ne ke fadin zako taci ko don wanan ganyen da akai amfani dashi don alaihu ne da anty zanci kaidai da albarka hjy ta fada a hankali. Ina kallo don keta Aisha ta zubo mata da yawa tana wani toshe hancinta kamar maijin warin abincin a hancinta. Da sauri anty fadila ke fadin kai ina zata iya cinye wanan abinci haka mai yawa ai saidai dan kadan yanzu tunda bata jin dadin jikin ta. Ban iya bawa mutum abu kadan ba ta fada a dan hasale tare da nufar hjy da abincin bayan ta gama fadan bakar magana ga anty fadila din. Da kyar hjy ta dan tashi zaune tare da taimakona a daidai lokscin da mami ta fake ga waya ta fice daga dakin ke ban. Fitan ta yasamu sakewa don har ajiyan zuciya na dan sauke a hankali don naga ta fice daga dakin hankalina ya koma a kan tsohuwar dake jin jiki a lokacin karfin hali kawai takeyi a yadda take din. Mun dade a zaune kafin mami su shigo tare da kawayen ta su uku dakin wani kallon banza suke bina dashi hakan yasa na kara shan jinin jikina sosai. Sannu sukaiwa hjy din tare da fatan samun lafiya a gareta daga nan suka buge da hira wanda yai kama da haibaici a gareni. Muryan hjy ne daga kwance take fadin kowa dai ya iya wanke allonsa sai bangon ya tsage kadangare ke samun wurin labewa. Kai mutum bakai kayi kanka ba balle kayi wani shi dan mutum dama ba abin rainawa bane a duniya wata dan hakin nan daka raina wata rana yazo ya tsone ma ido. Shiru dakin yayi na wani lokaci kafin dayar matar da tun dama na santa a gidan mami din ta fara mikewa tare da fadin babba Allah ya kawo sauki tare da aje mata kudi gefen gadon ta ta bar wurin. Kusan duk haka sukayi suna ficewa daga dakin kafin mami ta mike tana bi bayan su a can waje suka tsaya suna gulmana . Ba komai suke fada ba sai cewa da matar nan ta farkon fita da tayi daga dakin kai hjy wanan yar ko zaki iyata nan gaba ? Sai dayan tace aini imani duk ya kasheni gani wanan yarinyar gaskiya hajiya danki yaki sauraren ki a kanta don gaskiya wanan yar matar manyace sak. Ki duba lokaci guda yadda yarinya ta sake a baki daya kamar wata da wani a kasan nan ina ga ta kara nan gaba don ba iya nan zata tsaya ba. Humm bari kedai hjy dada ni kaina abin yana ban mamaki sosai a raina canzawan wanan yar a cikin kankani lokaci haka kamar abin hadin baki. Don yanzu ma baya ko saurarena akanta dana dauko mashi zancen zai nuna min baya so shifa matar shi yake so . To ba,a barshi banza ba hjy ina kuwa zai saurara maki akanta yana ganin wanan a tare dashi ai ba zai saurare ki ba. Ni ai yanzu matsalata hjyce don naso yi masu koran kare a asibitin nan sai dan bakin nan hayaniyar shi ya tayar da hjy daga barci da yau na nuna mata iyakana a wurin nan. Kai da kin barsu dayan matar da batayi magana ba tun fara zancen gaba dayan su kallonta sukayi lokaci guda. Taci gaba da fadin aurene dai ya riga da yayi shi don haka nidai naga kiyi hakkuri kawai ki bar yara nan su zauna lafiya a tsakanin su tunda kinsan halin wanan yarinyar tun farko. Ki duba fa ita matar namuda fa bata gaida kowan mu ba har muka fito dakin nan yanzu ina laifin wanan din da har kasa ta gaidamu tunda tasan mu din yaya muke dake. Amma dai hjy karima zancen nan naki baimun dadin ji ba wallahi akan me zaki wani ce ta barshi da matar sa wa zata nuna a matsayin mahaifin matar shi ranan da hakan ya taso. Kai hjy saudat kina wani zance wallahi yaushe har haka zai taso din kowa fa da ubansa yake tunkaho komai lakacewan shi kuwa . Nidai a wanan zancen hjy maryam hakkuri zan baki kiyi hakkuri ki zauna lafiya da yarinyar nan kada aje har girman ki yakai ga faduwa a wurinta wata rana don zuciya bata da kashi. Daga haka ta fara takawa zuwa wurin motar ta inda driver ke jiranta su tafi ba tare da ta tsaya koda yin sallama dasu ba. Muyi sallama dasu don ba fuska a garemu da zamu dauki lokaci a wurin su don haka muka fito don mu tafi bayan hjy din ta dan samu barci a lokacin. Ashe da daren ranan batayi barci da dadi ba haka yasa washe gari ya jafar yanke shawaran zuwa Nigeria din don hankalinshi ya tashi da yadda ake fada mai ciwon nata. Ban san da zuwan shi ba saidai nayi sa,a mun aika da breakfast da abincin rana asibitin duk da mami tayi magana da aka kai na safe din amma bamu fasa aikawa dashi ba. Don ko washegarin da jikin nata ya rikice mun tafi asibitin mun duba jikin nata duk da mun sameta tana barci a lokacin. Har muka fito kuma bata falka daga barcin ba sai ya mamud ne yace zai fada mata munzo idan ta tashi kuma ya fada mata din don da aka kai abincin dare take fadin tana gaidamu gobe akawo mata abinci da wuri don abincin gidan mu take iyaci nasu mami yana da yaji sosai. Can cikin dare muke jin ana dokan kofa kusan tare muka fito lokaci guda da fadila saida ta tambaya yake fadin shine ta bude kofan. Ta bude da sauri ya shigo muna mai sannu da zuwa ya karba muna yana kokatin shigewa part din shi yar jakkar hannun shi aka shigo mai dashi ciki na karba don in kai mai daki. A tsaye na sameshi a dakin yana kokarin cire kayan jikin shi sama sama na gaiyar dashi na fito saida safe ne ya fice zuwa asibitin . Ya dade a can har muka aika da abin karyawa kamar yadda muka saba bawa driver ya kai ko anty fadila taje da kanta. A can aka sameshi tare da hjyn da sauran yan uwa da sukazo daga kaduna don duba jikin tsohuwar da suke jin ya matsa mata ana fama da ita yana son zai wuce da ita can a dubata taki yarda. Wai ita tafi son a barta ta mutu a dakinta idan mutuwa ya tashi zo mata ana dai ta fama da ita taki yarda har lokacin da ya dawo gida don ya huta saboda gajiyan dake jikin shi din na tafiya. Barci sosai yayi daya dawo sai yamma ya tashi don kansa tunda dai mu ba shiga part din mukeyi ba sai idan wani abu ya taso yake kaini part din nasa. Har mun gama abinci da za a kai har fruit's salad mun hada mata ko zata sha duk wanan dabaran anty fadilace don kawai a burge mami dama wanda ke wurin lokacin. Fitowan shi sai cewa yayi in shirya mu tafi asibitin a tare duk wanan yana cikin hikimarshi na kawar da idon mutane ne a kan mu. Hakan bai zama min bako ba a wirina don nasan yakan yi mun hakan idan yana son fita tare dani wani lokaci kafin ya tafi. Dakin makil yake da yayan hjy din da sukazo zasu kuma kwana a nan kashe gari su koma wurin su biyar ne mata sai maza ukku. Ana faman hayani da dararaku kamar ba mara lafiya a dakin ya shigo ina biye a bayan shi fuska murtuk don halin daya samesu din a ciki. Suna gaidashi yana amsawa sama sama bai tsaya ba sai bakin gadon da hjy take kwance mama Ramaru tana kusa da ita suna da magana. Yake fadin hjy na fada maki ki yarda mu tafi a kaiki asibitin can a dubaki ki daina wanan wahala haka don Allah. Budan bakinta sai cewa tayi bazan tafi ba sai idan da matarka zamu tafi nima wanan kafan yana damuna wallahi. Dakin ne yayi tsit sai mami da tace aiko tare da Ramatu zaku tafi hjy tunda dai Ramatu tafita sanin komai ai . Ta yaya zamuyi tafiya zuwa gidan shi matarshi na nan idan ba da ita zamu tafi ba saidai a fasa wanan tafiyan kuna abu kamar baku da lissafi a zuciyar ku. In dai wanan ne ai mai sauki ne har in kin yarda din zaki tafi yaya mamud din ya fada yana dan dariya. Ya juyo gareni yana fadin zainab ko ba zaki rakata ba tunda hankalinta yafi kwantawa da tafiya dake din can ? Dan murmushin yake na sake a fuskana mami tace dama ai burin ta ke nan ita tunda iyakarta kaduna Abuja dama. Yanzu ko abin nema ya samu ga ba saban ba ai sai tafiya hjy rigima kawai kike son dorawa mutane kan tafiyan nan. Wani iri naji kamar hawaye zasu zubo min lokaci guda don yawan muzantanina gaban mutane da mami din ke mun . A cikin dakewa na daure Allah ya taimakeni hawayen bai zubo min ba sai dan dukar da kai danayi kasa sauran mutanen dakin duk sun zubo min ido a kaina. Ji nayi ya riko hannuna yana fadin mami yarki ai ta waye yanzu ba kaduna ba ko Abuja ba ko inama zata iya shiga yanzu ai ya fada yana kokarin rugumeni a jikin shi cikin rashin damuwa da duk wanda ke dakin a lokacin. Kai jafar a gaban mu kake kokarin rugume matar ka don ka saba da dabi,un ku na turawa a can mama Ramatu ke fadin hakan tana mashi dakuwa. Mama ai matatace ko ina ina iya rike abata wanan shike nuna irin son da nake mata ai kuma ku sheda koba haka ba besty na ? Ya dan rugumo kafadata zuwa jikin shi yana dan murmushin da shine iya dariyan shi a hankali na lumshe idanuwana don irin abinda naji a lokaci guda. Kada ka bata muna yarinya din nasan zainab na da kunya ita mama ko kin mata ita din matanane a yanzu ? Kai jafar kaikan a Allah shirye ka yanzu kan sai a barka inda aka ganka wanan aure ya saka zama mara kunya yanzu. Mama ai idan ban kulata kuma bakwa jin dadi don amana take garemu baki daya a wurin nan ai. Ni kaina nayi mamakin yadda ya bushe idon shi haka a wanan lokaci yana zuba masu rashin mutunci mutumin da baya magana sai yaso hakan. Yanzu dai kinji mamaku tace saida matana zatai tafiya don itama tasan amdanin ta gareni ai shike nan gobe za a fara shirin tafiyan mu a tare. Amma sai naga kamar ku tafi kawai da Ramatu don ko anje da zainab din can me zata iya maku banda karin nauyi kuma. Wata daga cikin matan tace ba haka hjy je so ba ai gara dai a tafi da ita din zaifi ko banza ai gidan mijin tane za a. Ni dai ina daga tsaye ina jin irin shawaran da ake yankewa a kaina akan tafiyan da hjy tace ayi dani tare da ita. Mami bar wanan zance don Allah tunda hjy ce ta zabi yin hakan ya mamud ya fada a dan hasale yana kawar da kanshi gefe daya dan baiji dadin yadda mami din take nuna min a gaban mutane ba. Saida muka fito daga asibitin yana waya har lokacin da muka baro dakin wani kuka yazo min lokaci guda tun ina kokarin rike kukan ban san lokacin da yazo min ba da karfi. A rude yake fadin subbahanallahi ke ke maye haka wani abin akai maki yanzu ko meye ki keyi kuma zaki tayarwa mutane da hankali a banza. Ban sauraren shi ba illa sheshekan kukan da nakeyi wiwi kamar an aiko min da mutuwa don bacin rai. Umurni ya bawa driver da karfi ya dakatar da motar har na bayan suka tashi dakan motar da muke cikin sa Allah dai ya gyara basu dake mu ba din. Wai me ke faruwane haka kika tayarwa mutane da hankali haka da kukan banza kaina na nade cikin gyalen dana yafa a jikina sai sharban kuka nake babu kakautawa. Shirune ya dan biyo a mitan bayan security din shi sunzo ya karesu ta yanyar dakatar dasu da hannun shi suka koma baya da sauri. Can na dago kaina a hankaki tare da hade hannayena a wuri daya ina fadin don Allah yaya ka mayar dani wurin iyayyena don mami ba zata taba kauna naba muddin ina tare da kai. Ke kanki daya kuwa kike fadin wanan maganan gareni yanzu zaman mami kike a yanzu ko nawa da tasoki ko kada ta so ki ai ba akarkashin ta kike ba . Dan Allah rufe min baki kada na saba maki yanzu a wurin nan haka kawai dan shagwaba zaki saka mutane a gaba kina min kukan banza. Dan Allah yaya kayi hakkuri ka mayar dani gaban iyayyena ba zan iya zama haka mami tana kina a kullun ba tsanar da mami take min yana min yawa a zuciyana. Maimakon inga yayi fushi sai kawai naji ya dan rungumoni zuwa jikin shi yana rarashi a cikin tsigan da ake rarashin yaro idan yana shagwaba wa iyayyen shi. Saida yaga nayi shiru ya ba driver umurni ya tayar da motan har muka kai gida ba wanda yai magana a cikin mu. Mota na tsayawa nayi saurin kokarin budan motar ta gefen da nake zaune saidai motar tana rufe har lokacin ba,a bude ba. Sai lokacin na dan juyo da fuskana zuwa duban shi a hankali da fuskana daya koma ja saboda kukan da nasha a lokacin abu ga faran mace take gaba daya fuskana duk ya sauya kalar ja lokaci guda. Ban yarda mun hada ido dashi ba nayi kasa da kaina don nauyin shi da nake ji yadda ya zuba min ido yana kallona da yanayin dana kasa fassaran shi ko na tausayine ko kuma wani abu. Ki share haayen ki ya fasa a hankali don kada su dauka anyi maki wani abune idan kika shiga masu haka kinsan halimatu nada wayau sosai zata iya gane kinyi kuka. Dole badon naso ba na share fuskana da gyale na yana kallona har lokacin kafin yaba driver umurnin ya bude motar na fita a hankali shikan ko motsi baiyi ba alaman fita daga motar. Haka na dinga hada kafana har na shige cikin gidan nayi arzki babu kowa a falon suna cikin dakunan su do magariba daya kawo jiki. Gado na fada na saki wani kuka gwanin ban tauayi ni kadai a dakin har na gaji naba kaina hakkuri na mike don gabatar da sallah saboda lokacin dake wucewa . Ina wurin da nayi sallah a zaune na kasa tashi aka turo kofan dakin nawa fadilace ta shigo don ta duba ko mun dawo a lokacin ta samu mun dawo din. Kallo guda tayi min ta fahinci cewa nasha kuka tare dani da sauri take fadin zainab meke faruwane yanayin ki ya nuna kinyi kuka haka mai yawa. Zuwa tayi inda nake zaune din tare da zama a kusa dani tana fadin meya samu kuma zainab kun fita lafiya kin dawo da kuka haka ko yayi maki wani abinne kuma. Kai na girgiza idona yana kawo hawaye nace a cikin kuka mamice dai ta tsanane bata kaunana har cikin ranta yanzu. Meye laifi ne anty don kawai ya jafar ya aureni meye laifina tasan bada yarda na haka ya faru ba tsakanin mu ? Baki da laifi zainab kowa ya sani amma zata daina ai idan ta gane hakan ba laifin ki bane kema nan gaba zata gane dantane mai laifin bake ba ni abinda na yarda dashi ke nan kedai ki kara hakkuri zainab. Bafani nace ai tafiyan nan dani ba anty hjy ce ta kafe sai dani zata yarda ta tafi can inda yake zance ba zan tafi bane ni ? Dake zai tafi zainab ta tambaya cike da mamaki a fuskan ta tana kallona kai na gyada mata alaman eh. Za ako samu matsala wallahi saidai idan kin daure hakan ba komai bane zai zamo maki alheri ta wani bangaren rayuwa. Anty idan mami ta barni ke nan har haka zai faru ni dai kawai gara yaya yace ya sakeni ko rayuwana zai zauna a cikkn sallama yafi. Ina amfanin wanan zama namu da mukeyi hankalin kowa a tashe gara kawai ya sallameni na koma gidan mu in zauna a gaban iyayyena ko kasa sukeci muci shi tare dasu. Ki bar fadin wanan magana kiyi addu,a Allah yasa hakan shine alheri a rayuwan ki dama kowa da abin ya shafa. Anty kina ganin haka zamu zauna da sunan aure tsakani da mami da danta har ma da kowa daya shafi mami din ? Yanzu fa a asibiti babu wanda ya nuna damuwan shi a kaina danaje sai hjy hjy kuma kinga ai tsohuwace basa jin maganan ta ko a yanzu. Duk zasu bari ta fada amma fa idan kin jajirce wa kowa haka zai faru nidai shawarana har gobe gareki shine . Kiyi kokari shakuwa da sabo ya shiga tsakanin ki da mijin ki har ki fahinci wani abu daga halayen shi na boye da baki sani ba tayi min wanka da jurwaye cikkn maganan ta. Kaina daga hawaye naci gaba da zuba min a idona take fadin kwarai zainab don ba mami bace matsalan ki a yanzu matsalan ki shine mijin ki ya daukeki a macen aure ya dauko ki. Kada kiji ina yawan fada maki haka ki dauka da wasa nakeyin zancena a a zainab akwai matsalan da nake hango maki nan gaba wanda yafi wanan da kika saka a ranki duk na mami shirmene gaskiya . Anty wani matsalane wanan na tambaya cikin son karin bayani daga gareta kafin tayi murmushi tana fadin ba zaki fahinceni ba a yanzu. Saidai shawaran da zan baki shine ki sa ido ga wa yanda mijjn ki yake mu,amula dasu sosai ki fahinci wani irin rayuwa yakeyi dasu. Musanman wanan taju din don ni sam ban yarda dashi ba amma don Allah ki boye wanan zancen a cikin ran ki har lokacin da zaki gane wani abu din. Sai ta kawar da zancen data dauko din da fadin yaushene tafiyan naku yanzu kuma mu a nan za a barmu ke nan ko me ? Ban sani ba anty saidai tunda hjy za a kai asibiti ban tsamani tafiyan zai dauki lokaci ba don naji yana fadin za a soma shirin tafiya daga yau din nan. Kai amma zanso na danje maki wani guri kafin tafiyan duk da hakan ba matsala bane gobe insha Allahu zan fita na dan je wani guri ai gara da naji da wuri tun lokaci bai kure muna ba. Don haka kada ki yarda ki saka uwar miji a damuwan ki don irin su mami hakan suke son gani a gareki ko yaushe sai ransu su kuma yayi dadi da hakan . Sun san komai ya lalace maki ke nan daga bangaren su har na mijin naki baki ba sauran kwanciyan hankali a tare dake. Don haka ki saki ranki ki duba matsalan mijin ki dake gaban ki ba wanan shirmen ba da tana da iko ko auren ki ba zaiyi ba ai. Ta fita ta barni da funanen meye wanan matsalan da kullun take kiramin ne ni har yau na rasa gane me hakan ke nufi waine wai ? Ina shiri kwanciyane ya shigo dakin nawa ina saman mirrow zaune halimatu bata dade da fita a wurina ba don tun tafiyan msizube ta koma kwana tare da anty fadila watarana kuma mu duka ukun muke kwana a daki guda idan mu kadai ne a gida. Wuri ya samu ya zauna bayan na amsa maushi sallaman daya shigo dashi fuskan shi a kaina yana kallon yanayi na a lokacin . Saida ya zauna yake fadin kin gama kukan shagwaban naki ke nan ke sai yaushe zaki girma ne wai a gidan nan? Daga cikin mirrow na dago kai muka hada ido dashi nayi saurun dukar da kaina kasa da sauri don ba zan juri kallon da yake min ba din saboda yanayin da hakan yakan sakani idan yana min wanan kallon. Gobe sai ki shirya zamuje ai maki photo na fita waje saura idan mun fita kuma ki min wanan shagwaban naki da kika iya . Ban tankashi ba har ya kare maganan shi ya fita waje sai lokacin na sauke ajiyan zuciya tare da fada da kaina watau shi wanan mutumin bai ma san ina yi ba ke nan ya mayar dani wahalalallah . ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣7️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA BAZAN GAJI DA TUNATAR DAKE KAN HAKKIN WANI BA WANAN LITTAFIN NA KUDINE DON GIRMAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA. Yar uwa kada kiga namatsa da magana don tunatar dake sauke nauyin haki nake fadan wanan kalman a kullun don akwai ranan tambayan hakki ga kowan mu. Kamar yadda fadila tayi alkawari hakan ne ya kasance don tun safe yati muna sallama kan zata duba haifiyarta da yara. Sako ta bari a fada mai idan har ya neme ta bata gidan a fada mashi ta tafi duba mahaiyar nata bayan tafiyan ta sai gidan ya koma muna shiru. Don hakane ba fito ba tunda ni kadaine a gidan kwanciya nayi daga nan barci mai nauyi ya daukeni har tsawon wani lokaci ina kwance. Ashe shima ya fita zuwa asibiti duban hjy tun safiyan har lokacin daya dawo gidan baiji motsin kowa ba sai yan aiki dake aiyukan su a kitchen da wajen gidan. Hakane ya bashi mamaki don rashin jin duriyan kowa daga cikin mu ba yasa shi zuwa dakina direct daya fito daga part din shi. Kofan yake ta bugawa har sau uku ba a bude ba yasa kai tsaye ya turo kofan ya shigo dakin nawa. Akwance ya hango saman godon nayi ruf da ciki ina sharan barcina hankali kwance sai hannuna dana danne da zai iya min ciwo idan na falka daga barci. Sai gashina dake daure dan kwalin dana daure ya koma gefe daya da barcin da yai nisa a lokacin ban ma sanda hakan ba. A hankali ya tako zuwa inda nake yana tafe yana kare ma fuskana kallo mai kama da barcin ma a wahalce nakeyin sa a lokacin. Da dukawa yayi a hankali yana kokarin dan dagani tare da ciro hannun dana danne saboda dadin barci tare da sauke idon shi a kan fuskana kurruciyana da yake gani ko yaushe ya kara fito mashi fili a idon shi. Yanayinb Numfashi da naji ya surku min duk da a cikin barci nake lokaci hakan bai hanani sanin bakon yanayi ya surkumin ba a lokacin. Da sauri ba bude idona a daidai lokacin daya kura min idon shi a kaina shine tsaye a kaina saidai ina ganin hakan kamar duk nauyin barcine mafalki nake a lokacin. Don haka na mayar da kaina saman hannun shi din da yake kokarin gyara min kwanciyan tare da juyawa a yadda nake kwance din. Bai san lokacin daya dan saki murmushi a fuskanshi ba don wautan kurciyan daya ga nayi a lokacin har da Ac dakin ya rage min yadda yaga na koma takure na kwanta kamar sanyin yana damuna lokacin. Saidaya fita daga dakin karan rufe kofan yasani bude idanuna da sauri tare da kallo kofan shigowa dakin. Ya riga ya fita a lokacin sai kamshin turen shi daya bar min a dakin lokacin yake tashi ta haka na gane cewa ya shigo dakin a lokacin ba mafalki akeyi ba ashe. Da sauri na zabura na bude idona tare da mayar da hankalina gun agogon bangon dake manne a bangon dakin. Mika nayi kafin in koma in lafe ina runtse idona a hankali tare da tunanen meya kawo shi dakina a wanan lokacin. Ganin anyi azahar har ana neman uku da wani abu yasa na mike zuwa ban daki da sauri na dauro alwala don sallah a zahar. Ban fita ba bayan na idar don sanin da nayi yana gidan a lokacin ya hanani fita duk da na fara jin yunwa a cikina amma haka na daure na lake a dakin ban fito ba. Banyi tsamani akwai wanda yasan tare da halimatu zamu tafi ba don koni sai a wanan shigowan na san da zancen tafiyan ta a bakin shi. Ya shigo yana fadin yau ina wanan mai aikin naki ta shiga dago kai nayi na dan saci kallon shi tare da fadi ina wuni yaya. Saida ya da bata fuska kadan nasan halin malam baushe ne yaki jini maikom in bashi amsa sai kuma na dauko mai wani topic yanzu na gaisuwa. Bayan ya amsa min tare da maimaita tambayan shi garen ta tafi gaida mahaifiyan ta tace a fada ma kara daure fuskan shi yayi kamar hakan baimai dadi ba. Kada ku dauki kaya mai yawa don tafiya ya fada yana daidai fita daga kofan dakin nawa daya shigo jin haka yasa nake masa kallon mamaki ta hanyar binshi da idanu. Ko baki gane abinda na fada bane cewa nayi kada ku dauki kaya mai yawa daya wuce kala biyu ko ukku . Nida wa kenan na tambaya batare da na shirya tambayan shi a lokacin ba saiji kawai nayi bakina ya subuce min lokaci guda ina tambayan shi. Dake da sadiya mana ko a nan dama zaki barta kike nufi ya jefo min tambaya kamar a hasale yana kokarin juyawa ya fita daga dakin. Nan ya barni zaune mamaki da imani ya cika min ciki don ban taba zaton haka ba daga gareshi sai tunane nake ni kadai a dakin . Wai shin dama haka rayuwan shi yake kodai nine yakewa hakan yanzu don ina matsayin matar shi amma kuma naji ko anty fadila takan yaba kokarin shi sosai garesu kaf masu aiki a gidan. Sai lokaci na tuno da ita don haka na mike ina zaton ta dawo zuwa wanan lokacin sai bayan magariba ta dawo gidan. Inda ta leko dakina ta samu ina sallah a lokacin ta wuce zuwa dakinta ban fito ba saida na gama duk ibadan dana sabayi kafin in fito zuwa dakin nata. Na shiga da sallama tana waya sai ido datayi min nuni dashi in zauna na nufi bakin gadonta na zauna tare da bin dakin da kallo. Zainab kingani sai wanan lokacin na samu dawowa ko da sauri na juyo inda take tare da dan nisawa nadan sauke a fili na mayar da hankali gareta ina fadin sannu da dawo ya su mama yaran ? Ban samu ganinsu ba don na fada maki inda zantafi ai tun jiya dan dama mama na bita wurinta na karbi sako tare da fada mata zancen tafiyan ki. Dan murmushi nayi cikin jin kunyan abinda ta fada taci gaba da fadin tayi murna kwarai dajin haka tana maki fatan Allah yasa ki zauna can daga wanan tafiyan kusa da mijin ki kada ya dawo dake nan kuma. Nan ma dai kaina sada kasa don nasan abune mai wuya zamana a can tare dashi tunda ba hakan ya tsaraba a tunane na. Kai yau nasha wahala zainab sosai wurin zuwa wanan kauyen can kauyen Narasawa ne naje don shi can yake zaune yana bada magani. Da sauri na dago kai don jin abindata fada ina mamaki kuma a raina da irin halinta na kula yanzu a kaina tayi wanan tafiyan tun safe har dare haka ? Kinsan nasan zaman da kikeyi a gidan nan dole hankalina ya daga dan ganin zai tafi dake can inda babu kowa da zai saka maku ido tsakani ki dashi. Duk da dai ba tsanmani da zai iya cutar dake ba ko wani abu makamancin hakan tunda naga yana da dama sosai gaskiya saidai riga kafi ance yafi magani. Hannu ta mika tana jawo handbag dinta data fita dashi zuwa unguwa da safe tare da dauko wani dan kwalba karami tana fadin wanan yace in baki da zaran na iso dashi zaki shanyeshi gaba dayane lokaci guda saura sai ki shafa a fuskan ki amma sai kinyi bissimillah zaki kafa baki ki shanye shi. Miko min tayi na karba hannu na rawa tace yanzu zaki shashi dan haka kiyi bissimillah kisha yanzu don nasan halinki da rashin daukan abu da muhinmaci zainab. Dan dariya mai kama da yake na sake a fuskana tare da kokarin bude dan kwalban data miko min ba tare da tunanen komai ba danjin bissimillah datace inyi kafin insha nasan koda na cutarwa ne Allah zai tsareni don bissimillah danayi kadin insha din. Duk da inada yakinnin tsakani da Allah take taimaka min dinndon naga alama hakan sau tari da yawa a gurinta. Saida na zuke dan ruwan dake cikin kwalba a gabanta kafin tace makaru ne sosai kingan shinan yana da amfani sosai a jikin mutum. Sai wanan kuma wanka zakiyi dashi sau uku kinga yau ke nan zaki fara gobe da safe kuma kiyi sai da yamma kuma shike nan kin gama dashi. Sai wanan gaskiya shi amfani dashi kamar zai maki wuya nake gani zainab don yace zaki shafa ne ta yadda zai iya shakan shi sosai a jikin ki. Ni kuma naga yaushe har zai shaki wanan din idan kin shafa saidai kawai mu gwada sa,an mu akai kinga kamar yadda zaku shiga jirgin nan har in wuri daya zaku zauna dashi hakan zaiyi tasiri gareshi ko ya kika gani ? Banda abin fada don haka na kada mata kai kawai da na amince da hakan tunda banda zabi bayan wanan tunda don ni take wanan kokarin haka. Miko min tayi na karba ina fadin nagode anty tace babu godiya a tsakani mu zainab don nima kin mun kokari sosai shiyasa dole nataimake ki ai zainab. Kinga aikin nan wallahi ba don ke ba da yanzu na rashi ga baki daya to sai Allah ya taimakeni ke din yarinyace mai dubaiya sosai wallahi. Don ba karamin rufamin asiri wanan aikin yai min ba wallahi don har mutane suna ganin yanzu na samu wani babban aikine don rufin asirin da suke ganin mu a ciki ni da iyayyena a yanzu. Saidai ina jiwa karki tafi ki manta dani zainab don kin san mu mata zumuntan mu sai idan muna tarene yafi karfi sosai haka ke faruwa tsakanin mata da yawa wani lokaci idan ana wuri daya anfi zumunta mai karfi. Saidai saukin abin tunda muna nan tare da halimatun ki zaki dinga tunawa dani don rabuwan mu a yanzu gaskiya zan shiga wani matsala nake gani. Duk da naji wani iri a raina saidai ya zama dole in fada mata tare da halimatu din zamu tafi yace duk da ban san yadda mami zata dauki tafiya da halimatu din ba idan taji hakan. A sanyaye nace anty ai dazun ya shigo yana fadin tare da halimatu din zamu tafi can wai bai yarda a barta na ba . Yanayin fuskantane ya sauya lokaci guda kafin tace min dama nayi tunanen hakan tuntuni don da wuya ku bar halimatu a nan tare damu bakinan. Shike nan nasan sallamata zaiyi idan zaku tafi don aikina ya kare ke nan a gidan nan dama dan kunake zaune a nan. Tausayi maganan ta ya bani a kasan zuciyana ban san lokacin danace da ita ba koda ya kama ki bimu can din anty ba zaki iya hakan ba. Zainab ke nan yanzu har kina tunanen zai aminta da ku tafi dani can idan ma shi ya yarda da hakan idan kin roka min iyayyena nakejiwa da hakan. Yanzu dai tashi kije kada mu makara kiyi wanka da wanan ruwan maganin kamar yadda malam din yace ban fada maki ba yace ki dage da addu,a da sadaka. Saidai abune mai wahala a can ki samu wanda zaki bawa sadaka kamar nan hakan yasa nayi tunane idan kina da hali saiki bar dan wani abu anan wanda za a rika bayar maki da sadaka lokaci lokaci. Ko ba a hannuna ba zaki iyabawa innan ki tana maki wanan sadakan don yana da kyau mutum ya dinga sadaka lokaci lokaci. Mun dauki lokaci tana dan kara min haske kan abubuwa da dama sai nake jin wani iri a raina kamar nace na fasa badon hjy kakarshi ba babu inda zanje gaskiya. Nayi kamar yadda tace dani kan maganin yayin da tafiyan mu ya kan kama don sai shirin tafiya sukeyi gadan gadan mu namu idone kawai lokacin. Karfe uku jirginmu zai tashi zuwa kasan ghana sai ya biya can ya cika fasija kafin mu dauki hanyan tafiya kasan da zamu din. Ranan kan na shiga damuwa sosai kafin tafiyan mu don yadda zamu rabu da anty fadila wanda ban sani ba ko mun rabu ke nan har abada kamar yadda ta fada min dasafe. Zama nayi na dafe habana da hannayena duka biyu har hawaye na zubo min a lokacin ban sanda hakan ba. Kai wanan kuka naki yai min yawa wallahi kada mubi hanya dake kina min wanan kukan a dauka sato ki nayi haka. Anty fadilace nake tunane yaya ya zamu barta a nan yanzu mu tafi gashi aikin nan dashi ta dogara kuma yanzu, , , , Kukane ya kubuce min daga hakan na kasa fadan abinda zan fadi a lokacin don kukan daya rinjayeni a lokacin na rabuwa da matar data nuna min kauna bayan uwata da mami ke nan. Wani irin kallon banza ya watsa min tare da fadin kinsantane ko ta dalilin wa kika santa ke wai wace irin yarinyace da bata da tunane. Wani irin sani kake son in mata bayan wanan danayi mata mun saba da ita a gidan nan ta dauke mu kamar yan uwanta na jini tana zama damu tsakani da Allah yanzu kuma ace za a rabamu da ita. Baiyi magana ba illa fitan da yayi daga dakin ranshi a bace nan ya barni na ci gaba da kukana ba wanda yasan inayi har sai lokacin da tafiyan mu ya gabato mai aiki ya shigo yana fadin ance mu fito da kaysn da za a tafi dashi. Duk da yahana mu tafiya da kaya mai yawa hakan bai hanani daukan kayan da muke so ba kuma baiyi magana kan hakan ba. Kuka sosai mukayi lokacin rabuwan mu da anty fadila din kamar ba gobe a ranmu yana ciji mota zaune yana kallon abinda mukeyi din uffan baice damu ba don haushin da muka bashi a lokacin muma yaya ya iya damu ina batun dauko mashi wata yayi ya damu mata duka can. A airport din mun samu mami dasu hjy a can suna jiran mu sai bayan mun fito daga mota lokacin mami ta bamu baya tana magana da wani da nake zaton dan uwansune . Muka iso inda suke tsaye gaidasu mama Ramatu nayi har kasa kafin in juya wurin mami din in gaida ita ta amsa a cikin wani irin yanayi ba yabo ba fallasa gareni haka na mike jiki ba karfi na koma gefe daya na tsaya halimatu tana biye dani duk inda nasa kafana. Bayan mami ta gama magana da mutumin ta juyo tana fadin ita wanan fa ina rakiya tayo maku dai ko ? Ban bata amsa ba don yadda take magana akwai rashin mutunci a idanunta gareni ya mamud ne suka karaso shida iyalinshi yake fadin. A,a mai masaukin hjy ashe har kun karaso kuma hjy dai tace sai da kece zata yarda ta je a dubata don bata zuwa gidan gwauro ta zauna ba mata a gidan. Dariya akasa mata tana fadi da kyar kunga laifinane kan hakan muryan mami ke fadin wai wanan da kuka zo da ita fa tana kallon halimatu din. Kila da ita zasu tafi mana mami Nuriya matar ya mamud ta fada tana wani yamutse fuskanta ita kamar me kyamar mu. Dama abinda nakewa gudu ke nan gashi ko ya fara faruwa a mayar da gida kanar kasuwa kowa yazo cin banza ya tafi. Haba haba mami hakan baida kyau wallahi kema ai gidan ki a cike yake da yan uwa dan ta dau, , , Ya jamal bai karasa maganan shi ba mami ta katseshi da fadin jamal ni kake kokarin yiwa wa,azi akan abindana sani kome ? Ba wa,azi bane mami ya fada yana juyawa don barin wurin ranshi a bace don dashi zamuyi tafiyan ashe . Wai me ke faruwane kuma ya jafar ne daya iso wurin yake tambaya shiru kowa yayi har mami din dai nuriya ce take fadin mami ke magana kan wanan yarinyar tana nuna halimatu din wai da ita zaku tafine ? Eh tare zamu a ina zamu barta tunda tare da yar uwanta take zaune dama ni nace a bamu ita don kada zainab din ta zauna ita kadai dama. Amma ai baka fada min da ita zaku tafiba ko ta fada a dan hasale shima cewa yayi but mami wanan ai issue din family dinane OK. Zatayi magana hjy tace kai iyami ki bar wanan zancen tunda kinji abinda ya fada daga nan aka fara kiran masu tafiya har aka kawo kanmu. Duk da na taba shiga jirgi daga kaduna zuwa abuja sai naga wanan din kamar daban ne shi saboda checking din da yai yawa sosai. Kujeran mu daya dashi su hjy da mama Ramatu suna bayan mu sai na jamal da halimatu a can baya. Tunda muka zauna tunane ne a gabana shiko system din shi ya bude yana wani aiki a ciki har jirgin ya daga damu na runtse idanuwana a hankali ina tunanen iyayyena da a waya kawai nayi sallama dasu. Ba wani dadewa ake sanarwa mun iso kasan ghana za a dauki sauran fasinja anan muci gaba da tafiya tun wanan lokacin naga ya lumshe idanuwan shi a hankali. Jirgin bai dade a nan ba ya daga bayab fasijan sun shiga mukaci gaba da tafiya har lokacin yana a cikin wani irin yanayi da ban kawo komai a raina ba a lokacun kan hakan da yayi din. Barci ne ya daukeni har ban sani ba na dan kwanto saman jikin shi bai tayar dani ba ya barni a hakan yadda nake don na samu barci sosai a lokacin. Bumu isa ba sai washegari mun dai dan fita a wani kasa sai lokacin na yaba da karfin halinshi dana gani na zyaa Nugeria a hakan din nabina gaji ga hjy da ake bata taimako don kada ta galabata don jikin da take ji. Mun isa lafiya kuma mun samu taro a wurin su don har mota uku suka zo taron mu wanan baiban mamaki ba ga dan sanin da nayi koshi waye din . Kallo kan bani kadai ba harsu hjy da mama Ramatu da jalal da suka saba shiga kasashen duniya saida suka kalli abubuwan mamakin da muke gani a kasan kamar ba duniyan mu daya dasu ba. Bayan tafiya mai nisa daga airport din muka shiga wani unguwa mai yawan gine ginen zamani sosai na kasan wani katafaren gida aka shiga damu. Tun abin yana babu mamaki har muka gaji da kallo muka zubawa sarautan Allah ido zuwa lokacin hjy ta gama gajiya sosai don tafiya mai nisa da mukayi. A cikjn gidan ma munsha kallo don kamar gaba daya yan aikin gidan mazane duk suna saye da uniform a jikin su iri daya. Wani katafaren falo aka shiga damu sai nake ganin abin kamar a mafalki wallahi ba ido bude nake ba. A falon ne naga wasu mata biyu yan kasan sun fito suna muna sannu da zuwa tare da kawo muna ruwa da drink's suka aje a gaban mu. Ban yarda nayi nisa da halimatu ba duk da wuri daya muke zaune dasu mama Ramatu har hjy dake kukan kafanta yana damunta sosai shi kuma bai shigo ba har lokacin. Muna kanta muna faman mata sannu da jiki sai gashi sun shigo tare da ya jamal da sauri sukayo kanta tare da tambayan meke faruwa da ita. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣8️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA FATAN ALHERI A KULLUM UBANGIJI ALLAH YAJI KAN MAGABATAN MU YASA IN TAMU TAZO MU CIKA DA KALLAMAN SHAHADA AMIN, , , , A rude yake magana cikin waya a dan kallaman da nake dan tsunta daga abinda yake fadi shine naji cewa ai sauri ai bucking din asibitin da kuma abubuwan da za,a nema ya sani. Su kawai na danji daga cikin wayan da yakeyi din a harshen turancin su na can mai kama da yaren kasan. Yana gama waya yake fadin a kira masa julie sai wanan mutumin da suka ahigo tare da sauri ya nufi cikin gidan yana kiran mai suna julie din . Kamar yare yayi mata don sai naga tana kada kai kafin ta juyo guri mu da fara,a a fuskanta tana muna magana ido kawai muka zuba mata don bamu fahinci mai take nufi da hakan ba. Saida ya jamal yake fada muna tace mu biyota zuwa ciki za,a shigo muna da kayan mu dakin na daban aka ban za a bawa halimatu nata nayi saurin dakatar da hakan tare da fadin zamu sharing din daki daya da ita she is my sister. Wani kallo tayi mi sai kuma ta dan dukar da kai cikin girmamawa tana fadin shike nan ta juya ta tafi muka bude dakin muka shiga. Bamu dade da shiga ba sai ga kayan mu ta shigo muna dashi dakin lokacin ina tsaye ina bin dakin da kallo ikon Allah wai yau mune a cikin wanan irin daulan da muke gani a film din turawa. Kofan ban daki na nema na shiga nan ma saida na tsaya naba ido abincin sa wurin kallo da dabara har na gane , inda zan danna ruwa ya zubo. Wanka nayi sosai ga sabulan wanka nan sai wanda ka zaba kayi dashi kafin in fito har halimatu tayi barci don haka ban tayar da ita ba. Jakkana na bude na fitar da zani sallah da hijjab sai dai ban san inda gabas yake ba a gidan don haka dabara yazo min a karon farko nayi amfani da app din wayana na gane gabas din galrin. Sallolin dake kaina na fara ramawa a gurguje don kada lokaci ya kara wuceni na dade a zaune ina neman kariyan Allah daga duk wani sheri da tsari dazamu tunkara a wanan garin dama mutanen da zamu zauna dasu din ga baki daya. Barcin na fara ji don haka na mike na samu gefen gado na kwanta nima a gefen halima ina kallon yadda take barcin ta hankali kwamce. Sai tunane nake barkatai akan yadda rayuwan mu zai kasance a wanan tafiyan namu da bamu san kowa ba babu alaman kuma yan jinsin mu na hausawa a wana gidan ko akwaisu ma banga alama ba dai . Barci sosai mukayi har suka fice kai hjy asibiti ban sani ba don ita ta hana a tayar damu don cin abinci tace muna tare da gajiya kasan yaran basu saba irin wanan dogon tafiyan ba haka. Sai bayan karfe uku da rabi kamar an tayar dani na falka don wanan irin mafalkin danakeyi a baya shine yau ma na sakeyin shi don tun bayan da malam mijin maizube kakan mu ya ban addu,oi ban sakeyin wanan addu,an ba sai wanan ranan kuma. Gabana ke faduwa sosai ga wani irin zufa dake fita min a duk kafofin jikina lokaci guda muryan halimatu naji a bayana tana fadin . Yayan mu halan mafalki kikayi hakane ina ta kiran sunan ki sai faman wani irin magana kikeyi kamar kina shan wahala a cikin mafalkin naki. Addu,an da nake karantawa ne ya hana in juyo in fuskance ta don a lokacin duk a rikice nake sosai don wanan mafalkin yafi sauran da nakeyi rikitani sosai. Abinka da yarinta ina wanan addu,an sai na nemi damuwan nawa na rasa shi lokaci guda a daidai lokaci kuma na fara jin cikina na kugin neman agaji don rabona da naci wani abu tun a gida Nigeria kafin mu taso. Banci komai da aka aje min ba a ciki jirgin don hankalina ba a kwance yake ba lokacin fin tsorin daya mamaye min zuciyana. Ki tashi ki watsa ruwa a jikkn ki ki canza wanan kayan mu fita mu leka hjy daga nan mu samu abinda mukaci na fada ina kallon halimatu da har lokacin take kwance. inane ban dakin ta fada a dan kasalance don har lokacin bata gama warwalewa daga gajiyan datayi a jikinta ba da hannu na nuna mata ta mike ta shiga. Ajiyan zuciya na sauke tare da mayar da idona ina bin dakin da komai dake cikin sa da kallo ina mamaki a raina. Yayan mu ban iya kunna ruwan ba don ban taba ganin irin wanan kayan ba muryan halimatu a kofan ban dakin ta dan rufe jikinta da tawul di bandakin dake rataye a ciki. Mikewa nayi ba tare da nayi magana ba na tura kofan na shiga nuna mata yadda zata kunna ta kashe nayi na fito. Bakin gado na zauna na hada tagumi ina tunane wanan rayuwan tawa shine rana zafi innuwa kuna don rayuwa rashin incin kai nakeyi a gidan nan yanzu. Har lokacin da halimatu ta gama shirmenta ta fito daga cikin ban dakin ina zaune ina faman tunane kokarin shafa mai takeyi na dakatar da ita da fadin baki dauro alwala bane kiyi sallolin dake kanki halan ? Ban tsaya jin amsan taba naci gaba da fadin halimatu kin dai ga rayuwan da muka fuskanta sai kinyi da gaske wurin maida hankali ga ibada a wanan gidan yanzu. Kina daijin idan innan mu ta bugo waya zancenta garemu shine kada muyi sakaci da ibadan mu kuma mu guji duniya da abinda ke cikin ta ga baki daya. Kada ki yarda inji ko in gani kina sakarwa wani namiji fuska koda kuwa shi wanda yakawo nan dinne don yanzu mutum ba abin yarda bane. Don Allah halima kada ki yarda mubawa innan mu kunya a idon duniya kina daida wayau kin kinsan komai don yanzu ido aka zuba mata damu a garin mu. Nagane yarinyar ta fahinci abinda nake nufi take naga yanayin ta ya canza itama lokaci guda take fadin yayan mu idan nayi wani abinda bai dace ba inna tace kimin fada kadana sake. Zanyi halima kuma ina kanyi don ban yarda da wa yan nan mutanen ba wallahi don haka ki kara kama kanki da kowa wallahi. Yanzu kiyi sallah dai mu fita kada ace mun shige daki mun kyale hjy bamu kulata ba tun da muka shiga. Sallah ta tayar kamar yadda na umurce ta sai bayan ta idar ta shirya muka fito daga dakin gidan tsit kamar babu kowa a cikinsa. A hankali muke takowa babu kowa dakin su hjy kuma yana kulle don na murda naji shi a rufe na juya ke nan ina shirin fadin dakin a rufe yake naji ana fadi a bayan mu. Da sauri na juya wanan matar ne da aka kira da julie tsaye a bayan mu tana magana cikin girmamawa a garemu taci gaba da fadin dun tafi asibiti tun sha biyun rana. Boss yace idan mun tashi a fada muna muci abinci kafin ya dawo gida a cikin harshen turanci take min bayani yadda zan fahinta. Da taimakon ta har muka je dining din abunci ne gurin a jere ta shiga bude muna tare da muna bayanin shi duk ciki babu abincin da muka sani dan dama dama wani shinkafa da aka dafa da ganye shi nake zaton zamu iya ci daga cikin abincin dake gaban mu din. Halimatu jan ta raja,a ga wani katon tallatalo da aka bamkareshi sai maiko yakeyi yana daukan ido naji tana fadi a hankali wanan din naman meye yayan mu ? Ban sani ba halimatu don haka kadama ki sa rai zakici shi don bamu san ko naman halal bane. Tace amma aishi yaya yana sallah don haka ba zai yarda a ci mushe a gidan sa ba ko ? Kada ki fara kici wanan nama na fada fuska a daure abincin dana zuba na mika mata taja plate din zuwa gaban ta dagani har ita bamu iya cin wani abin kirki ba don dan danon abincin da mukaji daban danamu na Nageria. Bamu kai ga tashi wurin cin abuncin ba aka turo kofan duk da muna dan nisa da wurin hakan bai hanani jin lokacin da aka shigo gidan ba. Shine tafe tare da mama Ramatu sai jamal dake bayan su dauke da jakkar kayan hjy da suka fita dashi . Da sauri na mike tsaye ina masu sannu da zuwa shida jamal suka amsa min gaidasu danayi mama Ramatu idon ta ta sauka kan abincin dake gaban mu din. Yauwa jamal mama sai ku zauna kuci abinci zan dan shiga in watsa ruwa a jikina don duk a gajiye nake wanan tsohuwar taku duk ta rudani wallahi. Ya jikin nata mama na tambaya ina kallon fuskanta jiki da sauki tana asibiti anbarta can suna dubata koda yake ku ai ba damuwa da jikin nata kukayi ba kuna nan kun saka abinci haka a gaba. Da sauru na dago kai ina kallon mama Ramatu din don jin abinda ta fada haba mama idan basuci abinci ba zamu taru a hakane a rasa wanda zai kama wani a cikin mu. Jamal ai gaskiya na fada kana sane dai hjy tanace sai azo da zainab kasan nan anzo din kuma har ta fara manta abinda ya kawo ta nan yanzu. Amma mama sai nake ganin itama mutumce kamar kowa dole tana bukatan hutu tare da ita don me kuma yanzu za a kawo wanan magana koke da kika tafi ai cewa akayi ki dawo basu bukatan kowa a can. Ni dai jikina ya mutu ina tsaye ko kwakwaran motsi ban iya ba don cin fuskan da nake fuskanta a wurin sarakuwan nawa ina tunanen na rabu da mami ashe kuma ga wata tare damu yanzu. Juyawa nayi na fara tafiya don zuwa dakin mu naji halimatu ma ta biyoni a bbaya gado na fada ina sake kuka lokaci guda. Yayan mu ki daina masu kuka haka shi yasa suke jin dadin maki abinda sukaga dama ko yaushe dan Allah kiyi shiru ki kyalesu yaya. Halimatu cin abinci laifi ne kuma yanzu shike nan yanzu mu bamu da yancin yin komai a gidan nan don kawai mu din iyayyen mu suna tallakawa kome halimatu ? Kyalesu yayan mu muma ai watarana zamuyi kudi mu rama abinda suke muna tunda suma badashi aka haifesu ba ai. Zancen halimatu ya dan sakani dariyan yake a cikin kuka har nace kai halimatu kedai yarinya ce yaushe zamu arziki irin nasu a duniyan nan mu da gidan mu ko akuya bamu da balle shanu. To aini ina tara kudin da nake samu tun zuwana wurin ku sunanan idan mun koma gida sai inba inna tasai abin kiwo dashi ko karamane ta sake. Halimatu amma dai ke din nan da sheg, , , , ban karasa ba aka turo kofan dakin wanda ke rufe da sauri muka juya don ganin waye mai shigo muna indai ba mama Ramatu bace ta biyomu har daki tazo tayi muna wani cin mutuncin na fada a cikin zuciyana. Ya jafar ne ya shigo yayi wanka ya sauya kayan jikin shi zuwa na mazan kasan maleshia mai zubi irin na indiyawa a jikin shi sai kamshi ke tashi jikin shi sosai. Da murmushi dauke a fuskanshi ya karaso yana fadin halimatu bataci abincin ba kema baki ci ba donta tashi kada ki damu da rashin cin abincin ta damuwa ta saka a zuciyar ta ita. Keko kinga idan kina wasa da cin abinci mama zasuce ban rike amanan dana dauko naki ba idan kin koma gida akaga kin rame sosai. Zan dinga ci ta fada sai kuma tace saidai abincin ne baya da dadi a bakin mu naso kuma in dan dibi naman nan naci sai yayan mu ta hanani ci wai don ba a san ko naman meye ba. Zainab kika hanata cin abincin ko me ya fada a dan hasale yana kallon fuskana a cikin mamaki yaci gaba da fadin ko kina zargin naman ne ko wani abu. A hankali na girgiza mai kai ina fadi da kyat naga munyi kankanta da mu fara cin abinci hakana manya basu fara ba . Halimatu tace kuma yayan mu kaji abinda wanan maman ta fada dazu bayan ka shige daki wai bamu saba ganin abinci haka ba munzo mun zauna munaci bamu damu da ciwon hjy ba. Da sauri ya dago yana kallona tare da fadin wace mama kardai nace mama Ramatu ne tayi wanan maganan mara dadin ji gareku ya tsatsareni da ido yana kallona ranshi a bace. Ganin nayi shiru na dukar da kaina kasa sai hawayen dana fara fitarwa daga idanuna yasa shi fita daga dakin da sauri ya barmu muna binshi da idanu. Halimatu zaki ja min wani tsana a gidan nan kuma wurin mama yanzu don mami zata kira tace ga abinda nayi mata yanzu kuma shiyasa duk abinda akai min bana yarda ya sani ko yaji don gudun irin hakan. Bansan ya sukayi ba dai can da dare shi da kanshi yazo ya kiramu har dakin wai mu fito muci abincin zance mai a koshe muke sai dai yanayin fuskanshi bai barni na fadi hakan ba. Bayan fitan shi daga daki na kalli halimatu ina fadin tashi kije kuci bana jin cin komai a yanzu kuma na koshi dana dazun. Haka ta fita kamar bata so jin abindana fada ba can sai gashi dakin yana fadin ki taso muci abinci na fada ko bakiji bane a cikin umurni yana tsareni da idanun shi manya masu ban tsoro. Da sauri na aje littafin dana dauko ina karatu na nufo inda yake saida yaga fitana daga dakin kafin ya biyo bayana naji yace min dakata a nan. Da sauri naja na tsaya ya karaso inda nake hannayen shi ya raba yasani a tsakiya yana bina da idanuwan shi. Da sauri nayi kasa da kaina don irin kallon da yake min din ki saurareni da kyau kiji me zan fada maki kuma ki kiyayye. A duk lokacin da muke tare dasu mama ko wani na gida dole ki nuna masu cewa ni di mijin kine kuma kina kula dani kina bani hakkina na miji ki a gaban kowa. Da sauri na dago kai yace yes kin san dai abinda nake nufi da hakan ba sai na tsaya maki gwarigwariba kan hakan. Don ban son wani ya zargi wani abu a tsakanin mu zamu zauna a daki daya yanzu har zuwa lokacin da zaku bar kasan nan ku koma Nigeria tare dasu. Don zaman ku a nan zai iya takurawa rayuwana da sauran aiyukana amma for now zaki nunawa kowa cewa kina kula da hakkina nima hakan zanyi kokari in nuna masu a fili. Understood ya fada yana kara tsareni da idanuwan shi sosai cikin warning dina ga abinda ya fada din da sauri na gyada mashi kaina don dai kawai ya jaye jikin shi a kaina lokacin. Jikina sai wani irin rawa yake min don tsoro banji ya daga gurin ba kamar yadda nayi tsamani sai can naji ya sauke ajiyan zuciya ya ya jaye jikin shi a hankali. Nima jin hakan yasa na bude idanuwana da suke min a rufe na sauke a bayan shi don har ya fara tafiya a lokacin cikin wani irin yanayi sai kuma naga yaja ya tsaya nima tsayawa nayi dan nisa kadan dashi. Zoki rike hannuna a haka zamu karasa wurin su ya fada ba tare da ya juyo ya kalli inda nake ba yake magana. A hankali na tako zuwa inda yake hannu shi daya miko mi har lokacin bai kalli inda nake ba na rike tare da dan runtse idanuwana ina jin wani zafi a raina naji ya fara takawa dani kara matso dani yayi a cikin jikin shi sosai a haka muka karasa wurin daning din. Suna zaune su uku halimatu mama Ramatu da ya jamal duk suka dago kai suna kallon mu kafin shi ya jamal din ya sauke kanshi daga kallon mu yana murmushi a fuskanshi na gani mu tafe haka a gaban su. Don shi ya gama fahintar komai a game da dan uwan shi din don yayi sancin sosai ya ga me yake ciki a rayuwan shi ko kokarin boye masu hakan kawai yake yi yanzu. Muna zama yake fadin amarya da angone waya fada maki ana fushi da cin abinci zainab ai kinga angon ki yaje ya rarashe ki kada ki ja mashi wani matsala kuma ana fama dana hjy. Zata iya yin fushi jamal tunda abincin da aka dafa don ta ana mata gori a kansa gidan nan nikuma ita nace a girkawa . Murmushi yake mama Ramatu tayi kafin tace fadin gaskiyan da nayi dazun shine fushinta a yanzu don kawai na fadi gaskiya . Mama bazan so wanan halinba gun iyalina gaskiya ban kawo kowa a nan dan ya takurawa wani ba ina hjy da bakinta tace a barsu su huta mu tafi dazun irin hakan bai kawo girma gun babba. Yana magana yana kokarin zuba abincin daya bude tare da turo min plate din abincin daya diba a gabana tare da dan kashe murya yana fadin ci koda kadan ne don Allah. Ni wanan draman na mutumin nan dame yayi min kama hakane idan yana abu sai ka rantse da Allah da gaske yake abinsa bazaka dauka hakan shiri bane yake a gaban mutane. A haka cikin kulawa ya samu har na danci abincin zaikai cibi biyar ita kuma mama Ramatu har ta kare cin abincin bata sake yin magana ba saida zata mike ne take fadin ke sai kizo mu kwana a dakina tare dake . Tunda ita a daki mijin ta zata kwana da sauri ya dago yana kallonta don jin abinda ta fada sai kuma ya wasance da fadin hakan ma yana da kyau zaku iya kwana a taren idan yin hakan ba a takura maki ba mama ? Ba komai ainina bukacin yin hakan kada a barta a daki ita kadai ta juya wurin da halimatu ke zaune tana fadin idan kin gama saiki sameni a dakin mu ina kinsan dakin dai. Zan rakota ya fada batare daya dago kaiya kalli inda maman take tsaye ba sai cewa mama tayi ina jiranta don dakin yai mi girma na kwana ni kadai a cikin sa. Kaina yana duke a kasa zaka dauka kunyar maganan mama nake ji yasa ban dago kaina ba a lokacin. Mama juyawa don ta tafiya dakinta yayi daidai da shigowan mutum biyo a gurin banyi saurin dago kaina ba don ganin ko suwaye suka shigo lokacin. Saida jikina ya ban ana kallona na dan dago kai a daidai lokacin da mukai arba da taju tsaye ya dan duka a bayan ya jafar din suna magana saidai idon shi a kaina yake. Gabana na ya fadi lokaci guda a take na tuna da kalman shahada na dinga jerosu har uku lokaci guda kafin inji dan natsuwa ya sauka min lokaci guda. Sun gama magana yana kokari barin wurin da sauri naji ya jafar din na fadin kun gaisa da madam da tazo . Juyowa yayi ba tare daya bashi amsa ba yana fadin anzo lafiya ya hanya lafiya kawai na bashi amsa dashi ina kawar da kaina daga kallon inda yake tsaye. Barin su wurin yayi daidai da mikwan ya jafar din yana fadin yana zuwa suka fita tare dasu lokaci guda. Sai lokacin na sauke wani irin ajiyan zuciya dana baiyana shi a fili wanda ke nuna nayi zurin tunane a lokacin. Ki yi hakuri zainanb kici gaba da masa addu,a da sannu komai zai daidaita a tsakanin ku nasan ki da yawan ibada a baya ko yanzu ki dage da adduan don ba wanda yai tunanen hakan ma zai iya faruwa ga wanda yasan mijin ki ko waye. Saukin abin bai yarda kowa ya takaki yadda yaga dama ba don yana tsaye a kanki akoda yaushe. Dago ido nayi na kalli ya jamal din dake magana yace kwarai duk abindake faruwa a tsakanin ku na sani zainab shima yasan nasan komai akai. Ki kara daurewa muci gaba dayi masa addua wanan shine jerabawan da Allah ya sako mai a rayuwan sa shikuma . Ba zanso inyi magana mai zurfi dake ba a yanzu nan gaba zamuyi maganan idan muka samu lokaci irin haka kedai ki kara hakkuri har zuwa lokacin da gaskiya zatayi halinta. Idona da suka ciko da hawaye lokaci guda na daga ina fdin nagode ya jamal ba komai ya fada yana mikewa daga gurin don zuwa dakin shi. Kallom gurin da halimatu take zaune nayi itama ni take kallo don bata fahinci me maganan namu ke nufi da ya jafar din ba. Nace idan kin gama saiki tashi mu tafi ki shirya zuwa dakin mama din kada taga kin dade bakije ba tare muka mike zuwa dakin mu. Tana shiri kwanciya naji ta jefo min tambaya yayan nikan sai banga wani abinda har suke ganin laifin ya jarar akanki ba kowa ya tashi magana sai yace kiyi hakkuri dashi. Baida laifi halimatu sune kadai suke ganin hakan don kawai baida lokacin tsayawa tare damu koda yaushe na bata amsa da hakan. Kema kuma ina son ki kama bakinki idan kije kwanciya dakin mama duk abinda ta tambaye ki koba yau ba ki fada mata baki sani ba. Kai kawai ta gyada min alaman taji tana min saida safe har kofan na rakata na dawo dakin nayi shirin kwanciya tare da tunane kala kala a raina. ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 5️⃣9️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR UWA LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA DARI UKUNE KUDINSA DON ALLAH DON SON ANNABI KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON ALLAH. Dakin na mayar na rufe kafin in koma in kwanta a takure a wuri daya saman gadon ba mama Ramatu kadai ke tsoron wanan gidan ba harni kaina tsoro gidan ke bani don girman shi. Wanda zuwa yanzu ban gama tantace cewa gidan ko mutum nawa ke cikinsa ba komai kan yaji na alatu saidai gareni hakan duk raggagene a idona. Don a yanzu dai na fara fahintar akwai wani boyayyen al,amari da ya jafar din yake boyewa mutane wanda kuma dan uwan shi yasan da wanan zancen a yadda yai min magana dazun kafin mu shigo daki. Koma meye ina rokon Allah ya kara tsareni daga fadawa cikin halakan shi don ni zuciyana yafi tsaya min da shan jini kila yakeyi. Idan ba haka ba ta yaya mai shekaru kamar ya jafar zai tara wanan arziki haka a duniyan nan . Mutum nawa yazo ya sama a duniya suna neman kudi fiye dashi basu tara hakan ba wani irin tsorone ya lulubeni lokaci guda ni kadai a dakin. Can barci barawo ya fara fisgana naji kamar ana dukan kofan dakin da nake ciki a dan firgice na bude idona na saurara da kyau. Kofan ne ake kwankwasawa ba karya kunne ke min ba saida aka kwankwasa kusan sau uku na mike tsaye a cikin kyarman jiki nakai kofan tare da tambayan waye ? Ki bude kofa kin tsaya kina tambaya a ciki rawan jiki nakai hannu na bude kofan daga ciki shine a tsaye yana saye da kayan barci a jikin shi yana kare min wani irin kallo da bansan na maye ba. Bayan sa nabi da kallo kamar ina tunanen zanga wani tare dashi ya taka zuwa cikin dakin yana fadin da a haka kika kwanta ba tare da kashe wuta ba ? Kasa nayi da kaina ina wasa da yan yatsun hannuna da nakejin kamar suna taimaka min wurin kare kaina daga abin sherin daya zo min a lokacin don zuciyana ta fara zargin sako. Kizo ki zauna magana zamuyi dake da fatan zaki fahince ni ya fada yana mai bina da kallo inda nake tsaye. A rude na kai kasa ina fadin don son da kakewa manzo ya jafar kada ka cutar dani kamar yadda kaiwa iyayyena alkawari hakan kafin ka daukoni daga gidan mu. Yarda da amicewa yasa suka bakani da kuma girman mami da suke gani ga idon su don Allah kayi hakkuri bazan kara ba . Zaune yayi sororo da mamaki yake kare min kallo tare da sauraren abinda nake fada mashi din a cikin tsoro. Cikin karfin hali ya iya furta zainab wai meke damuwan kine haka naga a tsorace kike dani tunda muka sauka garin nan . Ko kema kin fara daukan zancen mutanen me a kaina yanzu ki zo ki zauna magana nazo muyi dake don Allah ban kuma son ganin wanan hawayen da kike zubarwa tun safe a gidan nan yanzu. Jin abinda ya fada yasa na dago ido na kalli fuskan shi babu wasa a cikinsa ko kadan a lokacin yasa na dan tako zuwa bakin gadon nakai kasa zaune. Kai kawai ya girgiza tare da bina da wani irin kallo kafin yace ki saurareni da kyau kiji abinda zan fada maki yanzu. Kindai san bamu kadai bane a wanan gidan yanzu akwai mama da jamal sai kuma hjy dake asibiti kafin ta dawo gidan nan ko ? Daga inda nake zaune na gyada mashi kai a hankaki yace good abinda nake so dake shine yanzu kin daiji maganan da mama Ramatu tayi dazun wurin cin abinci ? Kai na sake dagowa na kalleshi gabana sai faduwa yake lokaci guda don bansan abinda zai fada ba kan maganan mama din. Yace kokin manta da abinda ta fada na a matsayin ma,aurata muke don haka a daki daya zamu zauna dake right ? Na gyada mai kai a tsorace alaman eh nagane yace toh don haka zan baki zabi duk wanda yafi maki sauki zaki dauka a ciki. Na farko zaki dinga zuwa dakina da sunan kwana a can dan kaucewa idanun mama tunda ta fara wanan maganan ina zargin ko mamine ta sakata saka muna ido a gidan mu. Sai zabi na biyu ko ki bar kofan ki a bude zan dinga shigowa karfe hudu na asuba yadda zata dauka a nan gurin ki na kwana tare dake . Ido na sake zubo mashi lokaci guda don jin abinda ya fada din ya gane me nake nufi sai naji yace indon ni ki saki ranki don mata basu a gabana ko kadan . Do bantaba daga ido na kalli wata mace da sunan sha,awa ba a rayuwana saidai inwa mace kallon dayan biyu shine ko in kalleta a matsayin yar uwa a gareni ko kuma abokiya kawai ni haka rayuwana yake. Don haka zuwanki dakina bashi zaisa wani abu ya kasance a tsakanin muba dake zuwa kawai zakiyi don kaucewa idon mama da sauran mutane. Ajiyan zuciya na sauke lokaci guda ta yadda har yake iya jiyo sautina daga inda yake zaune baki ya mere min tare da fadin wani kika zaba yanzu. Na amince na bar kofana a bude ya tareni da fadin baki gudun mama ta gane wanan din plain ne muka shirya hakan dake ? Sai nayi shiru kaina a kasa don haka ni zabina shine ki je can part dina zaifi min kwanciyan hankali don ba daki daya bane a gun saiki zauna a cikin guda hakan yayi maki ko ya kika gani. Yayi min na fada ina maidana sanin zuwa wanan tafiyan da hjy ta saka ayi dani ina zaune kalau a gida a cikin kwanciyan hankaklina. Ya mike tsaye a daidai lokacin tare da fadin sai ki tashi mu tafi part dina a yanzu saidai ban son sa ido ga duk abinda zajiji ko ki gani a can din wanan ba hurumin ki bane kinji. Ya fara tafiya ni kuma na kasa tashi don jin irin dokokin daya tsara min wanda nasan suna da wuya in iya ketare su duk lokaci guda. Jin ba motsa daga inda nake ba har yakai kofa ya jiyo gareni yana fadin ki tashi mana kinyi zaune ko baki fahinci abinda na fada bane yanzu ? Da sauri na mike na dauki hijjab dina da zanyi sallah dashi nabi bayan sa kofan ya rufe da kansa muka nufi part din nasa. Tsaruwa iyaka ke nan dan an narka dukiya wurin hada part din kamar wani aljannan duniya wani daki ya bude min muka shiga yake fadin nan yayi maki ? Kai kawai na gyada don a tsorace nake da za ai min ihu koda kadan ne zan iya sake fitsari ko in ruga da guda a yadda nake tsorace. Zaki iya yin komai iyaka dakin nan daga haka ban yarda ki leka ko ina ba idan kin shigo dan dama da rana kina da right din shiga ko ina na part din nan daga haka ya fita naja wani irin ajiyan zuciya tare da bin ko ina na dakin da kallo. Na gano inda bandaki yake na shiga na dauro alwala don in gabatar da sallah saboda barci ba nawa bane kuma yanzu ya zama dole in kai kukana a wurin Allah maji rokon bayin sa. Ban yarda na gusa daga kofa ba nan a kasa barci ya kwashe ni a gurin da nayi sallah tare da jera kirari gun ubangiji mahalicci ina mika rokona garesa. Rashin barcin da ban samu da wuriba yasa har na makara ga sallah asuba sai da rana ya haskani ta window dakin na tashi ina sallati na nufi ban dakin da sauri. Ban fito ba saida na gabatar da sallah a kofa mukai kicibis dashi a cikin shirin sa naja baya ina gaida shi da kwana ya amsa min a dake kamar bashi ba kuma. Dakina na nufa sai dana kusa na tuna da dan makullin dana aje a dakin don haka na nufo don na dauko a kofan muka hade da taju dake fitowa shima a cikin shirin shi. Ban ko tsaya gaida shi ba na wuce dakin ya bini da wani iri kallo nidai na shige na dauko key din na fito na bude dakina na shiga. Zuciyana fam da tunanen me kuma ya kawo taju part din sa tunda safe haka ban tsaya ba na fada ban daki nayi wanka na fito na shirya a cikin wani dogon riga baka ta mutanen kasan Egypt mai hannu shara shara rigan barci ne fam a idanuna don haka na kwanta don in rage nauyin da idona yayi min na rashin samun barci. Barci sosai ya daukeni lokaci guda saida zasu karyane ya leka dakin nawa ya sameni ina rankon barcin da ban samu nayi ba da daren. Baiso ya tashini ba saidai don asibitin da zamu gurin hjy dole yasa ya tayar dani din ta hanyar dan bubuga nin da yayi na falka dan razane. Ki tashi ki karya zan kaiku ku duba jikin hjy ne yanzu ya fada har lokacin babu walwala a tare dashi ban tsaya bin ta nasa ba na shiga bandaki na kewaya na fito na samesu a dining zaune nima na zauna tare da gaidasu da kwana. Kai kekan ai garin nan yayi maki barci haka kamar mai sabon ciki kodai dan nawa ya aje kwansa ne bamu sani ba. Fuskana na daure don na fahinci me maganan ta yake nufi don haka ko idona ban dago na kalli wurin da take zaune ba. Har lokacin da muka gama aka fito zuwa asibitin wanan karon bashi ke jan mu ba don yace akwai inda zai tafi zai samemu a can asibitin. Mun samu hjy tana barci saidai bamu dade a dakin ba ta falka daga barcin muka shiga yi mata sannu da jiki tana amsa muna a hankali. Ya Jamal ne yake fadin ko yazo yaja mata kafan da aka daureshi da wasu karafuna tace tunda kafi dan uwanka rashin tausayi. Shida ya kawoni nan ban ganin kowa ko sallah asuba yanzun haka ban samu yinsa ba na rasa yadda zan masu bayanin ina son inyi sallah tun dazun. Har muna hada baki wurin kiran subbahanallahi nida mama Ramatu mama tana fadin ashe bayi ke nan idan ba ibada shi bai fada masu idan lokacin ibada yayi su taimaka maki kiyi ibadan ki ba. To ina nasani yar nan ni wanan abin ai ya koma min ciki yanzy kan ace mairai ba zaiyi ibadan sa ba yana kwance haka sharkaf. Fita ya jamal yayi sai gashi sun shigo tare da likita yana masa bayanin ba za a bar ruwa ya taba kafan nata ba sai bayan kwana uku don hakane ma ake mata wanka a kwance. Nan dai ya dan kara bayan nan shi ya fita ina zaune nayi tagumi can na nisa nake fadinb hjy ko za a kawo maki dutse kiyi niyar taimama akan sa. Haka za a yi yar albarka kinga abinda yafi ke nan gareni yanzu ya jamal ya fita ya dan dade kafin ya dawo dauke da wani dan dutse a hannun shi karba nayi na shiga ban daki na sanke shi da kyau na fito dashi . A natse tayi komai kamar yadda sharia,a ya fada har sallah a kwance tayi don nasan hankalinta ba zai taba kwanciya ba idan ba sallah ta samu tayi ba. Mun dade a wurin hjy har karfe dayan rana kafin yaya din yazo tare da wanan bindin nasa yana biye dashi a bayan shi kamar jelan shi. Ni yanzu yakai ma bana son sam naga wanan mutumin don haka kawai nakejin na tsaneshi a cikkn rayuwana na kula bani kadai na tsani wanan mutumin ba har ya jamal ma ya tsanesa sosai don ban taba ganin lokacin da suka gaisa dashi ba Bayan tambayan jikinda yayi ne yake dan duba jikin nata musaman kafanta dake daure da karfe yace ya kike jin jikin ta dan dago tana fadin da sauki sosai saidai sallah da bata samun yine a nan. Yanzuma sai zuwan mu ta samu tayi sallah ga shawaran dana bayar tana dan saka min albarka tare da fadin kaikan jafari kayi dacen mata wallahi tafi matar mamud sau dubu a gurina. A gurinki kikace hjy shima ko mamud matar shi tafi mai kowa shima a wurin sa kai rabu dasu ka kara rike matar ka kaji wa yan nan suma a sannu zasu gane abinda nake nufi watarana. Mama zaku tafi gida ku huta ko ya jafar ta fada kamar yana son a kawar da zancen zamu tafi kan ko don mu samu muyi sallah muci abinci. Sai kuzo a mayar daku gida yanzu dan ni office zan koma daga nan ba gida nayi ba yanzu ina da aiki da zanyi sai dare sosai zan dawo gidan. A tare muka fito dashi sai da ya dan tsaya da kaninsa sukai magana lokacin har mun kai bakin mota muna jiran a bude muna . Kafin su tako zuwa inda muke tsayen har lokacin ban yarda na daga idona na kalleshi ba don tsoro shi dana fara ji a yanzu. Cikin basarwa yace zainab lafiya ko kike ko dai ganin hjy a hakane yasa na ganki wani iri dake yau ? Wanan haka take bata da sabo kullun a cikin jan jiki takewa mutane dan bambamcin su kadanne da matar mamud don ita din akwai girmama na gabanta gaskiya. Karasowa yayi inda nake tare da dan dago habana yana fadin ki kula da kanki don Allah wanan shirun yayi yawa sosai. Ya fada yana dan buga min kafadana a cikin wasa dan dariyan yake na sake mai na bishi a yadda yake so muyi gaban mutane da wasan basajan nasa. Kamar ance in dago ido daga wurin motar shi taju ne ya kura muna ido kamar maye yana kallo abinda ke faruwa a tsakanin mu. Wani kallo tsana na watsa mai yayi saurin kawar da kanshi gefe daya a raina nake fadin sai nayiwa wanan mutumin tsiya zai rabu dani da wanan kallon nasa na maita. Saida muka wuce kafin su biyo bayan mu idona naga window mota idan ba idona yai min gizo ba zan iya cewa kamar na gansu suna kiss a cikin motan saidai bazan tabbatar da hakan. Kuma ni san ban kawo komai a raina cewa wani abinda bai dace ba sukeyi a tsakanin su don ban zaci hakan ba ga ya jafar din gaskiya. Innalillahi danaji ya jamal ya fada ya dawo dani ga dan tunanen da nakeyi a lokacin ne kuma naji mama daga gefena tana fadin kai jamal lafiya kake wanan tsabihin haka ? No mama babu komai ya fada yana dafe kanshi a cikin takaici mama ta kara fadin ko mantuwa kayi a asibitin mu koma ? Babu komai mama wani abu dai nagani ya daga min hankali kin dan kasan nan ba na musulmai bane tace nima haka nake gani ai kamar ma matan su a tsirara suke waisu wayewa. A gidan ma bayan munyi sallah mun fito cin abinci kasa fitowa ya jamal din yayi a lokacin saida kyat mama ta samu ya fito. Ina kula dashi bai wani cin abincin ba sai tasa shi gaba dayayi yana faman tunane shi kadai bayan kwana biyu da haka ina cikin dakin nan da nake kwana kamar wata manya a gidan. Nake dan jiyo hayaniyan su daga falin dake tsakanina dasu wurin kofa na koma ina saurare wanan karon hausa naji anayi don haka na saurara dakyau ko zanci. Wallahi wallahi kaji tsoron Allah ka guji ranan haduwan ka da Allah ya J ka dauka idan kayiwa mutane wayau zakaiwa Allah wayau ne ? Ina zaka da alhakin wanan yarinyar da kake cutarwa a rayuwan ka ai gara ka saketa ka zauna kaita aikata sabon Allah ka zaifi ma sauki. Jamal ni kake fadawa magana haka kai tsaye me kake tunanen ka taka a yanzu naji jamal din na fadin Allah . Niko ya mamud ya sake hanyar Allah zan fada mashi gaskiya a yanzu balle kai da muke da shakuwa dakai ina zaka kai Alhakin iyayyen mu a kanka ga irin tarbiyan da suka bamu a baya. Kudi ko ilimi ba hauka bane bazan fadawa kowa wanan abin ba zan dai tayaka addua idan kana da rabo a wurin Allah Allah yasa ka daina wanan harkan daga haka naji ya fita ya gaura kofan falon yafice daga part din. Da sauri na koma saman gado na dafe bakina don kada sautin hawayena a fito fili sai can naji kamar ana taba kofan dakin Allah yasa ban yarda in kwanta ban sakawa kofan key ba har mai tabawan ya gaji ya daina tabawa. Washe gari har na fito kamar mai sanda a falo na samu ya jamal a zaune yayi tagumi jin motsin fitowan yasa shi dago kai ya kalli kofan da yaji an taba din. Mukai arba dashi a dan rikicewa nayi sai naga ya kawar da kanshi daga kallo hakan ya bani daman shigewa dakina dana bude hannuna na rawa kai tsaye na fada ciki. Sauke numfashi nayi a hankali kamar wata barauniya da aka kama a lokacin nikan na shiga uku na fada a fili . Ban yarda na fito ba sai wani lokaci dana kwatanci ya jafar ya bar gidan a lokacin na fito na rame sosai don damuwa da nake ciki a yan kwanaki nayi wani irin fari sosai saidan wuyan dan aje. Yunwa ya fito dani babu kowa a falon duk da nayi mamakin rashin ganin halimatu yau da banyi ba wurin dining na nufa na hada ruwan shayi babu madara don bakina da nake jin shi babu dadi a ranan kamar na kwanta ciwo da dadewa. Babu abinda nake tunane tun daren ranan sai kakamin ya jamal din ga dan uwan shi ina kuma tambayan kaina wani abune yaya jafar yakeyi boyayye da ba wanda yasan wanan abin. Kisha tea din kada yai sanyi mana kin zauna kina tunane ke kadai a nan da sauri na dago idanu ina saukewa a kanshi. A cikin daurewa nake gaidashi da ya jamal ina kwana saida ya zauna yake amsa min da lafiya zainab ya kika tashi ya bakunta kuma lafiya na fada ina dukar da kai kasa. Zainab kisha kada tean yayi sanyi ya kara fadan hakan gareni da sauri kamar mai jiran umurnin shi na dauki cup din na fara kurba a hankali. Mama Ramatu ne ta fito daki tana dan dariya halimatu na bayan ta tana fadin wanan yar akwaiki da wayau tsiya wallahi. Dago kai mukayi muna kallon su har suka karasu inda muke na aje cup din hannuna a hankali tare da zamewa saman kujera ina gaida ita kamar yadda na saba a kullun. Ta amsa min a cikin fara, a kafin tace dani lafiya kike kuwa yau naga kin rame lokaci guda haka ko wani abinne ya sameki kuma anya kuwa zainab ba shigan ciki ke gareki ba ? Da sauri ya jamal ya dan kalleni sai kuma ya kawar da kanshi daga kallona sai naji na tsargu da wanan maganan bandai yi magana ba ina zaune na tasa kofin shayina a gaba ina dan wasa da bakin kofin a hankali. Takon shine ya mayar da hankalinsu ga kofan part din shi yana saye a cikin kananin kaya da suka fitar mai da suran jikin shi har kurciyar shi ya kara baiyana a fili zakace ko dan shekara ashirin zuwa samane a lokacin. Ya iso gurin tare da fadin mama an tashi lafiya cikin girmamawa a gareta ta amsa mai da fara,a tana fadin yanzu nake zance da matar ka kodai rabo ya shigane bamu sani ba gata sai faman rama takeyi haka a tsaye. Da wani irin mamaki yace ciki a dan zabure sai kuma ya mike tsaye yana kallona a cikin mamaki yake fadin mama ciki ga zainab din ? Kana mamakin hakan ne ga macen aure yanzu fa shekara da kusan rabi da aurenku meye abin wani mamakin hakan a nan Allah ya ingatar kawai musha buki wanda ka hanamuyi da aure sai muyi shi a sunan baby. Kai mama bata dai da lafiya ne tace yanzu take fada min da dan zazzabi ta kwana jiya nace kila gajiyan tafiyane yaja mata hakan. Amma kuna da abin dariya wallahi wai me kuke mamaki a hakanne gun matar aure har zaku tsaya wani zance ko baka shiryawa haihuwan bane a yanzu kana dabi,an ku na turawa. Gyara zama yayi yana fadin kai haba mama har guda nawa wanan yarinyar take da zata haihu a yanzu at list dai ta kara yan shekaru nan gaba kafin ta haihu. A naka tsarin kenan amma aishi Allah ba ai masa dabara idan ya tashi nuna ikon sa akan bawan sa ina cikin ne aimu muna maraba dashi. Mikewa ya jamal yayi yana fadin zan fita daga can zan leka wurin hjy in dubata duk da yau nasan basa bari a shiga da safe. Ba zaka jira yayan ka ku tafi tare ba ko akwai motan da zaka shiga ne a wajen yace zan shiga taxi daga nan ai ba nisa da gidan nan. Barshi ya tafi mama ya jafar ya fada ba tare daya dago kai ya kalli kowa ba a wurin yaci gaba da hada tea din shi da yakeyi. Wai ko lafiya kake da dan uwan ka kuwa mama ta tambaya tana kalon shi yakecewa lafiya mama me kika gani ? ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 6️⃣0️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE DAN DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA SHI HAKKI BAIDA KADAN MUSULMIN KWARAI KE GANE HAKA, , , , Kwana biyu na rasa gane mai ke tsakanin su yaya dan ko yaro yasan akwai matsala a tsakanin su don ya jamal idan ya fita baya dawowa gidan sai dare. Daya shigo kuma ba,a sake ganin shi sai wata safiyan ko ance ya tsaya ya karya zaice yana sauri ne kada hjy taga ya dade zai karya idan ya isa asibitin. Ashe mama Ramatu ta fahinci hakan a tsakanin sai gashi ta kasa hakkuri muna zaune muna karyawa bayan fitan ya jamal bada dadewa ba tana tambayana . Zainab niko sai naga kamar yaran nan akwai abinda ya faru a tsakanin su kwanan don gaskiya ba haka na saba ganin su mussanman ma shi jamal da jafar akwai shakuwa na sosai a tsakanin su. Kofin dake hannuna ina dan kurban ruwan shayi na aje tare da fadin mama nima na kula da hakan saidai ban tsamani abin yayi nisa haka sosai ba a tsakanin su. Gaskiya suna da matsala don shi jafar baya ko zancen kanin nasa idan ya fito bai ganshi ba da safe idan da dane da mukazo baya karyawa sai ya nemi dan uwansa sun zauna tare. Ke mijin ki bai fada maki abinda ke faruwa bane tsakanin su da sauri na girgiza kai ina fadin ba muyi wanan zancen dashi ba gaskiya. Tsuki tayi tare da fadin ina zakuyi wanan maganan don ko yaushe fuskan shi a daure idan bashi yaga daman yin raha don kansa ba. Zanwa jamal magana idan ban fahinci komai ba zan fadawa hjy ko zata san maike faruwa a tsakanin su haka. Nidai ban kara tofa komai ba naci gaba da kurban tea din dake hannuna a hankali har nakai rabin kofin na aje. Yau ma banga shi jafar din ba ko sakkon fita yayi ne don kwanakin nan naga da wuri yake fita sai dare kuma yake dawowa wani lokacin ma bamu haduwa. Ina ganin kamar ya fita tun dazun don yace yau yana da meetinga office na shara mata karya ina Allah Allah kada kuma ya fito ta gane karya nayi mata ashe. Sai Allah ya taimakeni ashe ya fita din don na sara a gaba gashi ranan bamu zuwa asibiti duba hjy don tana bukatan hutu don alluran da akai mata tana son dan hutu ya sa sukai muna gargadi da hakan. Don haka bayan karyawan mu a falo muka zauna da mama ana dan hira da kallo wanda kusan hiran na mutanen kasan da muke muke zancen irin shigan su da yadda suke magana kuma a cikin sauri. Can mama ta fara jefo min zance kan zaman mu da yaya sai na rasa amsan da zan bata lokaci guda don haka kawai na dan daure fuskana ina dariyan yake. Amsan da ban bata ke nan din na gane nugun cikina take son tayi taji wani abu a dangane da zaman mu ko shi kanshi yaya din . Ganin naki bata amsa yasa ta kawar da zancen da fadin ai ban tsamani hjy zata barku ku koma a tare damu ba don naji taja fada tun kafin tafiyan nan wai ya kamata ace kin biyoshi nan kema, sai ku zauna tare a nan. Amma mama ni nafi son in zauna Nigeria don nan din babu wanda na sani babu dadin zama a kasan nan ga baki daya wallahi. Budan bakin halimatu dake kallo kamar tana jin yaren su sai cewa tayi amma dai anty aida mu zauna nan din tunda mijin kima yana nan ai inna fa tace kada ki yarda mijin ki yayi nisa dake. Da sauri na kalli halimatu din ita kanta tasan irin hararan da nayi mata sai ta koma ta kwanta da sauri saman kujeran da take kwance da farko daga haka bata kara jefa muna baki a zancen mu ba . Barci ne ya dauki mama don haka hiran namu ya tsaya a nan ina zaune sai faman tunanen maganan da mama ta fada min na rashin jittuwa a tsakan yan uwa biyu da basayi a yanzu. Tunane nake ko a sanadiyana suke wanan fitinan indai hakane kuwa zan tun kari ya jamal da yadaina damuwa da zancen mu don nima hakan yayi min daidai wallahi don ni har yanzu tsoron ya jafar din nakeyi da ganin girman shi akoda yaushe. Da wanan tunanen har lokacin sallah yayi na tayar da mama do muje muyi sallah kads mu shagala don a rayuwana bana yarda inyi wasa da lokacin sallah ko kadan. A gurin dana sallame sallah nayi zaune ina ci gaba da tunane a raina na yadda zan tunkari ya jamal din karshe dai na daure dole in hakan garesu a yanzu kada hakan ya kawo masu matsala. Ban fito ba sai bayan da nayi sallah la,asar koshi na fito ne don halimatu da har lokacin banga ta shigo dakin ba tunda tayi sallah azahar ta fita. Bata falon danake tsamani don haka kai tsaye na nufi dakin mama da sallama tun kan na tambaya na hango halimatu din kwance tana barci saye da hijjab din datayi sallah. Wayancewa nayi da gaida mama tare da tambaya ko taci abinci kuwa tace tun dazun mukaci da mutumiyar tawa aini naji dadin zuwa da yar nan kasan tunda gata tana debe min kewa sosai wallahi. Mama tana dai damun ki da surutun ko yaushe indai halimatu ne shiyasa suke dasawa da ya jafar idan yana gari ai. Yarinyar tana da shiga raine mahaifiyar ku gaskiya tana ba yaro tarbiyab daya dace wallahi kunyi sa,an uwa tagari ba kadan ba. Mama mu gode kamar yadda anty fadila tace in dinga fada idan wani ya yaba wani abu nawa daya shafeni. Yanzu mama yau ba zamu je gun hjy ba ke nan sai ranan da suka bayar za,a ganta yayi wanan kasa gaskiya suna da doka mai tsauri wallahi. Ai inda sukafi kasan mu ke nan wurin sanin aiki da canne kyale duk wanda zaizo zasuyi a dameta sai idan an hadu da likitan da yasan kansa zai dan tsawatawa mutune su daina shiga. Dan wanan hiran da mukeyi da mama yasa naji har zuciyana ya dan sake don hira sosai mukayi da ita har lokaci yaja bamu sanda hakan ba. Zaune a office din shi ya mike kafafuwan shi saman table din dake gaban shi yana rike da kanshi da hannu daya irun zaman da yayi yana nuna yayi zurfi a cikin tunane. Don alal hakika yana cikin damuwa da maganan da sukayi da dan uwan nasa kwanakin da suka wuya har ranan ya kasa samun natsuwa a tare dashi. A karo na barkata yana kiran layin kanin nasa yaki ya daga a karshe ma sai computer ke fada mai wai layin na busy ko yaushe idan ya kira. Yanzun ma daya kira computer din daine ke fada mai yadda ya saba fada mai layin na busy haka yasa yagane dan uwan ya sashi a black list din wayan shi. Kararawan office din nasa ne yayi kara hakan na nufin akwai mai son shigowa office din a lokacin. Da kamar ya kyale maishi ya koma ya dai daure ya ya danna alaman ba mai so shigowa daman ya shigo. Yana budewa suka baiyana mai su uku aboka shi ne tun na kurciya da suke shashancin su a tare wanda kusan ta sanadiyar sune ma ya samu aiki a kasan nasu a yanzu saboda hazakan shi da kuma basu son rabuwa dashi don zaman shi star a cikin su. Ko wanin su yana cikin shiga ta alfarma kamar yadda suka saba shiga saidai na kananan kayane irin suit. Ya matsa kadan daga kofan ya basu wuri don su shigo daga ciki basu shiga ba illa kokarin hugging dinsa da sukayi daya bayan daya. Kafin su wuce suka karasa cikin office din kujerun dake officen din zube gefe daya suka zube a sama. A sabule ya biyo bayan su zuwa ciki shima ya samu daya daga cikkn kujerun ya zauna a kai dayan mai suna philis yake fadin ya labarine na ganka a haka kuma. Sai dayan ya karbe da fadin kwana biyu bamuga ka leko club ba yasa yau na gaiyaci friends muzo mu duba ka ko lafiya. Jafar din bai amsa kowan su ba illa mikewan da yayi zuwa wurin firdge din dake office din ya bude tare da fito da kananan kwalabe ya dire a gaban su ya juya ya dauko kofuna hudu ya dawo inda yake zaune da farko ya zauna. Ido ya zuba masu mai nuna alamun shi a gajiye yake ba zai iya zuba masu abinda ke cikin kwalban ba a lokacin. Kallon shi dayan da baiyi magana ba tun shigowan su yayi yana fadin cikin kulawa wai ya nagan ka hakane gaba daya ka birkicewa sanin ka damu. Jafar din ne ya dago idanunsa da suka kade sukai jawur alaman yana cikin tashin hankali dai sosai. Mikewa yayi ya nufi wurin window din office din nasa ya zuge wani haske ya baiyana a office din lokaci guda ya gyara tsayuwan shi yana kallon motocin dake wucewa kasan office din nasu. Binshi sukayi da kallo tare da mikewa suka nufi inda yake din tsaye don da alama jafar din baison damuwa cikin halin da yake ciki din a lokacin. Ji yayi daga bayan shi a dafashi hakan yasa shi juyowa ga wanda ya dafa shi din cikin su gaba dayan sune a tsaye a bayan shi suma fuskansu ya nuna sun shiga damuwa kan damuwan shi. Whatff bro wai meke faruwane dakai haka ka fada min damuwan ka mana ko zamu samu mafita akan matsalan dake damun ka ? Dan dariyan yake yayi yana kallon su kafin ya girgiza kanshi yana fadin banyi tsamanin zaku iya min amfani ba a yanzu don wanan family issue ne ba maganan ku bane ko na wani. Da matsalane dakai da family din kku ke nan a yanzu ko hakan yana da nasaba da zuwan yan uwanka da tj yace sunyi a gidan ka akan sanadiyar kakanka da bata da lafiya wai ? Da manaki ya juyo yana kallon su watau taju har ya kasa hakkuri yakai karanshi ke nan a wurin su yanzu wanda shine dalilin zuwan su ashe ? A dan zafafe ya buda baki da kyat don ranshi ya gama baci dasu yana fadin oh ashe kunzo ne yanzu kuyi min fada ke nan ? No no no ka fahince mu jackson munzo nan ne yanzu a matsayin abikan ka bawai munzo muyi wani maganan daya shafi tj din bane. Nima ai a yanzu nafi ma sha,awan ka samu sabon dan hannu dan shi tj din kakai shekuru dashi kuna harkan nan. Hannu ya daga mai tare da wani irin tsawa yana fadin stop that nose's jooo, wuu bana cikin mude din wanan zancen a yanzu don zuciyana a jagule yake da komai. Kallon juna sukayi kafin dayan yace dashi ko zaka samu fita yanzu muje kadan sha wani abu ko zaka samu relief a zuciyar ka ? No ba bazan iya shan komai a yanzu ba don gidana a cike yake yanzu da family dina shan wani abu a gareni yanzu hadarine sosai. Zaka iya don ba bakon abu bane sha a gareka don haka ka daure kawai mu fita yanzu kadan samu relief a rayuwan kan ko tunanen ka da damuwan ka zai gushe maka na dan lokaci ka koma daidai. Tun bai yarda da hakan ba har yakai ya yarda ya biyewa son zuciyar su sukaci karfin shi akarshe suka fita tare zuwa inda sukan hadu su hole. Ranan don bai cikin dadin rai shi ruwan kwalba yaita dinkirawa cikin sa yana kuma jan coicane har ya fara fita cikin hayacin sa. Da haka har ya raba dare a waje cikin mayen kuma yajawo motar shi zuwa gida don shi din dan hannu ne sosai a wanan harkan. Ina dakina da nake kwana a kwance na kulle kofa na dinga jin kamar a dukan kofan duk da nasan kofan a bude yake don bani na saba rufe part din ba . A cikin daurewa da fargaba da tashin hankali na fito a cikin sanda zuwa falon part din babu tantama kofan ne ake duka da karfi. Allah ya sako min wani dauriya na nufi kofan na bude saidai abinda na gani shine yafi tashin hankalin da nake ciki. Don ya jafar ne a cikin maye yake dukan kofan gashi rataye da corth din rigan shi a kafadan shi sai layi yakeyi. Innalillahi wa,inna alahim raj,un na ambata tare da da duban bayan shi ko akwai wani a tare dashi ko wani a falon sam na manta da darene sosai lokacin kowa ya shige part din shi ya kwanta. Ina can ina tunane ji kawai nayi ya fado min a jiki yana fadin take me to your room zee i want sleep now. Gabana ne ya fadi jin shi a jikina da nayi lokaci guda ya kara fadi cikin wani murya na maye take me to your bakiji ba ne ? Ni kan ina zan iya kama mutum kamar ya jafar mai karfi haka da jin koshi a tare dashi a cikin dabara na samu na kaishi dakin nawa ya zube da takalman shi da komai saman gadon ya kwanta rub da ciki ba bata lokaci naji ya fara sakin nasari. Da sauri na dafe bakina tare da sakin wani irin kuka lokaci guda kamar daga sama naji yana fadin are you crying zeey ? Dago kai nayi na dan kalli inda yake kwance har lokacin yana kwance a yadda yake din ba tare daya motsa ba yake wanan maganan tashi nayi na sawa kofan dake bude key. Ban daki na nufa a can na raba dare ina darza kuka a cikin tashin hankali sai maimaitawa nake ya jafar dama dan giya ne ashe. Don babu tamtama nasan yadda yan giya suke mayensu idan sun sha don muna da yan giya a kauyen mu idan sun shawo muna kanana zamu bisu muna waka sunyi marisa sun sha kwaya har sai manyan gari sun kore mu zamu bar mutum. Ashe nima zan auri mashayi da zai rika min marisa a gida ina kallo a cikin tashin hankali da fargaba. Yanzu ni yaya zanyi wani irin hukunci zan daukarwa kaina kan zama da mashayi a gida daya ya zama dole gareni tun ban makara ba insan inda dare yai min daga hannun ya jafar din. Dama abinda mutane ke yawan fada min kalman inyi hakkuri da hakayan sa da zan gani nan gaba ? Dama ashe sun san komai suka boye min shima yasan yadda yake ya aureni a hakan don kawai ya cutawa rayuwana ke nan. Dama wai mami tasan danta haka yake kuwa har ta tsaya tana nuna min wanan kyamar don kawai ina yar talaka ni ko ina yar talakka ai talaka yasan mutuncin kansa da kuma abinda Allah ya hanemu yi. Gudawa daga garshi ne yazauna min a zuciyana saida kuma ta ya zamu iya gudawa yanzu daga kasan nan tunda shiga jirgima sai idan mutum ya shiryawa hakan. Ina ko yaya zanyu zanyi ne don mu gudu dani da kanwata daga hannun wanan mashayin tun baikai ga illanta min rayuwa na ba. Haka nayi rabin kwana a cikin makewayin can na dauro alwala na fito ashe ina ban dakin anyi ta dukan kofan ina ban daki a lokacin banji ba. Ashe taju ne ya falka yaji dukan kofan da akeyi kamar a cikin mafalki kafin ya nemi tufafi ya saka a jikin shi har mun nufi dakina kamar yadda ya bukata in kaishi dakin nawa. Ya fito bai ganshi a waje ba ya nufi kofana yana duka don yaji kamshin turaren a falon ya dade yana dukan kofan nawa ba,a bude ba har ya hakkura ya koma daki . Ranan ba karamin hauka yayi a dakin ba shi kadai dan ya tarwatsa kayan dakin da dama yana hauka wai mun kasance a tare da yaya a daki daya yana zaton wani abu zai wakana a tsakan nin mu ke nan idan mun kebe din mu kadai. Har washe gari ya jafar din yana kwance bai falka ba ni kuma ina takure a wuri daya naci kuka har idanuwa na sun canza kala don kukan danasha tun dare har zuwa safe ban runtsa ba ga barcin da ban samu ba shima yana barazana a idona. Karfe taran safe a lokacin nasan su mama sun tashi ko dan ita ta saba fitowa tun safe a gida ko nan din ma da sunyi wankan safe sukan fito falo su zauna. Ina cikin wanan tunanen lokaci guda naji ya motsa sai kuma ya sake komawa ya lafe ido na tsura mai daga inda nake zaune din a takure. Can kamar wanda aka tsikara ya mike zubur tare da dafe goshin shi yana murza idanun shi lokaci guda kuma ya bude su ya fara bin dakin da kallo. Zubur naga ya sauka daga kan gadon tare da karewa kanshi kallon mamaki har lokacin bai ankara dani a inda nake a zaune ba . Zama ya koma yayi bakin gadon tare da jan wani irin uban tsuki lokaci guda kafin kunnuwa shi ya fara jiyo mashi sautin kukana a inda nake takure. Da sauri ya mike tsaye tare da nuna ni da yatsa yana fadin ke ke lafiya na ganki haka mske faruwane wai ? Ya akayi nazo dakin nan wai a nan dakin na kwana kome juyawa yayi ya dan kalli gadon na dan lokaci guda tare da juyowa gareni ya sake kallona yana fadin . Wai wani abu ya farune kike wanan kuka haka ki fada mi ina tambayan ki kin yi shiru jin da yayi banda lokacin bashi amsa yasa shi jan wani itin uban tsoki ya duka yana daukan riganshi dake saman gadon. Kai na dago ina kallon shi tare da mamakin shi wai yana nufin baisan abinda ya aikata bane a daren jiya ko me yake nufi da wanan basarwan ? ZAINAB IDRIS MAKAWA 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅 6️⃣1️⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Littafin kudine yar uwa don girman Allah da darajan Annabi kada ki karanta idan baki biya ba don Allah da son da kikewa Annabi. Ranan nayi kuka har na gaji a daki ba wanda ya sani don na kulle kaina a cikin daki ni kadai kada wani ya fahinci hakan. Tunane kala barkatai nayi a zuciyana ina nemawa kaina mafita saidai abu dayane ya tsaya min a zuciyana shine ta yaya zamu gudu daga wanan kasan yanzu ? Gashi ko yanayin tafiyan da mukayi ya nuna ba a kusa da kasa mu muke zaune ba a yanzun don tunawa da nisan tafiyan da mukayi kafin mu iso nan. Wayyo ni Allah wayyo kaina na fada a fili tare da kara sake wasu sabbin hawaye masu dumi daga fuskana lokaci guda. Ya jafar me yasa ka kasance a haka dama don shine ka yaudareni ka nace saini zaka aura don ni din na kasance ba yar kowa ba ko kuma don ni din yar kauyece daba zan fahinci halin da kake ciki ba Allah masani. Ya Allah ka kiyashe aikin aikata sabo komai kankantan shi a rayuwan mu don kawai biyewa duniya ko wayewa mutum yana dan musulmai ya jefa kanshi ga mahalaka irin wanan . Tir da hali irin naka ya jafar dama mai hali irin naka idan kuma kai mai shiryuwane ubangji Allah ya gagauta dawo dakai hanya madaidaiciya a rayuwan ka. Mu kuma Allah ka tsaremu daga fadawa halaka itin wanan duniya da rahira na karasa da amin ina share hawayen dake zubo min a fuskana. Shima ya jamal ranan ya kasa fitan safen da yakeyi don ashe akan idon shi dan uwan nasa ya dawo a cikin mayen sa gida yaga komai yadda ya wakana a lokacin. Don yana shirin zuwa kofan ne ya samu ya izashi cikin part din a lokacin ne yaji fitowana daga dakin ya kara labewa yana kallon yadda muka kwashe dashi har shigan mu part din nasa. Baiyi barci ba don damuwa da tashin hankalin daya shiga a lokaci don bai dauka abin dan uwan nasa ya girmama haka ba sai yanzu da idon sa ya tabbatar masa da komai ya gani da idon sa kuma. A, lal hakikanin gaskiya yaso auren dan uwan shi da wanan yarinyar da farko saidai a yanzu yana jin tsoron kasancewar shi da yar mutane. Kada yazo ya jefawa mutane yarsu a cikin halaka da dana sani a karshe duk da yana shedar zainab din da hakkuri da juriya ga ladabi gami da biyayya . Ko wani namiji zaiso ya samu mace mai irin wanan halin nata saidai shi dan uwan nasa gashi Allah ya basa irinta mai hali na kwarai da kowani namiji yake fatan ya samu din. Wanda yasan hakan na daga cikin abinda yaja dan uwan nasa ga zaben wanan yarunyar don juriya irin na zainab din a yadda ta zauna a gaban mahaifiyar su suna gani. Dama ace ya mamudne yayi katari da irin wanan mace mai hali irin na zainab din yasan da yanzu lafiya lau take zaune da kowa a gidan nasu. Yaja wani dogon tsuki yana juyawa daga inda yake kwancen a fili yace mami da ace kinsan halin da dan ki ke ciki da yau kin daina tsanar yar mutane da hattaran ta don kawai wani akida naki can na daban. Da kinyi nasaran aura mashi yar kawar ki da kike da burin yi har yanzu akan dan naki da yanzu asirin ki dana kowan mu ya gama tonuwa a kasan nan ga baki daya . Don babu macen da zata zauna da miji mai hali irin na ya j abin kyama ga kowa a zauna lafiya haka kamar yadda yarinyar nan ta kawar da idonta a kan hakan gareshi. Wani tunane yazo mashi zubur ya mike zaune yana tambayan kanshi wai dama zainab din tasan halin ya j dinne take zaune dashi a haka ko kuwa dai a yanzu ne ta fara gani da idon ta ? No no no yarinyar nan bata san komai ba don batayi wayyon da zata gane hakan ba da yanzu ta nuna wani alama kan hakan ai. Lailai ya zama dole ya tunkareta kai tsaye da wanan zancen yaji ra,ayinta kan halin dan uwan nasa kai tsaye idan da shawaran da zasuyi suyi shi a tare tun kan wani ya ankoro da wannan halin na yayan nasa su shiga bakin mutane. Wanan dalilin ne ya hanasa fita gidan ranan ya fake ya tsare yana jiran fitan yayan nasa da fitowan ita zainab din ya samu su maganta wanan babban maganan daya taso masu din yanzu don shi yafi komai daga masa hankali saboda yaga yayan nasa yayi nisa ga harkokin nasa ko a yanzu taron shi sai an shirya masa sosai. Sai dai gashi a gidan yau baiga fitan ko wani daga cikin su ba haka dole ya hakkura ya tafi duba tsohuwar dake asibiti don yasan zuwa yanzu tana can cikin damuwan rashin ganin shi akan lokaci da batayi ba. Barci mai dadi ya kara daukan shi bayan ya samu ya watsa ruwa a jikin shi tare da kokarin yin sallah da ya kubce masa don yanzu wurin tara da wani abu na safe ya koma gado ya sake kwanciya don nauyin da idon sa yake dashi har wanan lokacin na barci. Abokin shi philis ne ya kirashi a waya yasa ya daure ya mika hannu a hankali ya dauki wayan nasa dake daga gefen shi a yashe saman gado wanda ya zama masifa yanzu ga mutane. Don mutum yana tashi barci shedan zai zugashi yakai hannu a waya kafin yai yunkurin yin komai a rayuwannshi. Yoou bros philis ya fada dayaji ya dauki wayan nasa a lokacin don jin muryan shi da yayi lokacin a cikin magagin barci. Wai har yanzu baka gma barcin bane karfe sha biyu da wani abu yanzu fa na rana ko yau a kwance kake nufin zaka wuni don dan abinda ka taba a daren jiya din ya kare a cikin dariya. Jafar din ya mitsike idanu dakyau yana kallon agogon dakin nasu can ya tuna da waya a hannu shi yace jiya nasha wanan abin over kan kun zugani da yawa. Uhumm philis dinyace ta bangaren shi yana dariya tare da fadin kada ka zamo raggon maza fa don ban sanka da wasa ba mutumina ? Zan sauka kasa yanzu inga mai gidana ke ciki idan na watsa ruwa zan fito zuwa karfe biyu nan idan na samu time ya bashi amsa da hakan tare da kashe wayan shi. Mikewa ya daure yayi daga kan gadon a hankali sai lokacin idon shi ya sauka ga ta,asan da taju yayi mashi a dakin a daren jiya. Dakin yabi da kallo ko ina tare da jan tsuki mai karfi yana fadin zanyi maganin wanan gay din dan iska duk akan me yayi min wanan barnan haka a daki. Daidai zai mikene ya tuna da zancen kwanan da yayi a dakina ya kara jan tsuki don fahintar dalilin taju nayi masa wanan aika aikan haka a daki. Daurewa yayi ya shiga wanka tare da kara tsarkake jikin sa ya fito kara bin dakin yayi da kallo yana mamakin taju din a ransa. Tsuki ya kara yi ya nufi wurin tufafin shi yana dauka tare da magana kamar wanda ya tabu yana fadin duk ba komai ke jefani a tashin hankalin nan ba sai sakaci da addini na da nakeyi kan wanan shegun abin kyamar dana jefa kaina a ciki saboda abokai da ba addinin mu daya ba giya da wanan harkan da mukeyi. In banda sherin wa yan nan ai da yanzu yana zaune lafiya a cikin salamansa kamar kowa amma komai a yanzu zaiyi sai a boye jamar wani mara gaskiya a cikin yan uwan shi. Gashi saboda shan da yayi daren jiya ya jawo mai har yar mutane ta kamashi a haka saboda fita hayacin shi dayayi kan giyar da cocaine din. Ahaka har ya shirya ya fito sai sai gidan tsit yake kamar babu kowa a cikin sa a lokacin don su mama basu dade da shiga dakin su ba lokacin. Abinci ya fara nema don jin cikin sa da yakeyi kamar ya yi kwanaki baici abinci ba a cikin sa yake jin yanayin kansa a lokacin. Ina kwance a dakina duk da hasken ranan daya gauraye daki a lokacin ni duhu nake gani a dakin ko ina saboda daci da radadin da nake ji a zuciyana. Ga tunane ya tsaya wuri daya cak don ban san abin yi ba a yanzu don banda wani mafita da zai fisheni ga kangin shi a kasan mutane. Ina daga kwance kaina na kallon sama saboda nayi kukan har na gaji nabawa kaina lafiya don idona daya fara yi min dishi dishi a lokacin. Jin an budo kofana baisa na dago kai naga mai shigowa dakin ba a lokacin illa ina kwance a yadda maishi ya sameni. Tun daga kofa ya hangoni yadda nake kwance din nayi motsu mutsu dani alaman nasha kuka har nagaji tun daren jiyan. Jikinshi yaji yai mai sanyi a lokaci guda shi kanshi yasa bai kyauta min ba yana tsaye ya rasa abinda zaice min sai faman kallon . Kallona ya tsaya yakeyi ya rasa kalman da zai fara min magana dashi wanan ne rana na farko daya taba jin kunyar wata ya mace a rayuwan shi bayan mahaifiyar shi. A da kan bai dauki abinda yakeyi a matsayin wani abu ba face holewarshi da lokaci kawai sai gashi yau yarinyar daya raina ma wayau a da ya fara jin kunyarta a duniya. Da kyar ya iya kaiwa zaune a bakin gadon a kusa dani yayi gyaran mutya yana fadin lafiya kike zainab na ganki haka ? Ban dago kai na iya kallo shi ba tunda ya zauna a wurin ina a yadda nake a kwance din har lokacin dan girgiza kai yayi kafin yace . Wai bakiji ina magana dake bane zainab meke faru dakene kika koma haka lokaci guda ? Jin abinda ya fada yasa na dan juyo kadan na kalleshi a cikin takaici da jin hsushi da tsanar shi lokaci guda daya sauka min a zuciyana. Da kyat na daure cikin sanyin murya nace damuwata ba matsalan ka bane yaya abinda ya shafeni ni ya shafa. Yanayin muryan da nai magana dashi dole yaba mutum mai saurare a lokacin tausayi a lokacin don gaba daya muryata ta dakushe dan kuka. Yace amma ai hakkin ki yanzu a kaina yake duk wani damuwan ki ya shafeni ko don haka ki fada min damuwan ki nace ko menene ? Ko kuma a yadda kika ganni a daren jiyane ya sakaki daukan wanan matakin a yanzu kina son ki halaka kankine ko kuma addu,a ya kamata ki min a matsayina na mijin ki a yanzu. Addua ? Addu,a fa kace ? Kai bakaiwa kanka addu,a ba ka daina wanam halin sai nice zan ma addua a karba min ? Yaja dogon numfashi bayan jin abindana fada ga mamaki daya hanashi kwakwaran motsi don dai yasan girma ya gama faduwa ke nan . Inaga nasan sauran abinda yake aikatawa bayan wanan ashe da rashin kunyar yafi wanan da bai taba zato ba a wurina. Numfashi ya sake ja tare da fadin to tashi muje asibiti a dubaki idan lafiya kike a yanzu ? Barshi don ni lafiyata kalau a yanzu yaudaran ka kawai ne abinda ya dameni a zuciyana . Ya jafar ka cuceni ka yaudareni ka yaudari iyayyena da suka aura min kai a matsayin miji yau suji mijin da suka aura min suke kiranka da surukin kirki ashe tsohon mashayin dan giyane haka basu sani ba. Haba ya jafar ya kake son nayi da rayuwana da halinda muke ciki da mahaifiyar ka da yan uwanka zanji ko da wanan halin rayuwa naka na boye da Allah ya baiyana min a daren jiyana gani. Lokaci daya yaya kazo kashiga rayuwana ka nuna isa da gadaranka a kaina don kawai ina karkashin mahaifiyar ka ba tare da kayi tunanen nawa rayuwan ba. Na hakkura a hakan nake zaune tare dakai don biyayya ga iyayyena duk da mutane da dama sun san da wata manufa ka aureni don ni din ba ajin auren ka bace ai. Amma haka na hakkure nake zaune tare dakai duk da mami har gobe ta nuna bata ra,ayin zamana dakai. Wace matakace da kai yaya ranan da ka tsaya gabab mahalicin ka don kare kanka a wanan rayuwan ka tuna fa shi mutum ba a bakin komai yake ba ga Allah. Yanzun nan Allah na iya ikonsa a kanka kana takama da lafiya da arziki da ilimin ka zai iya mashe ka gawa lokaci guda. Ko kuma ya karbe lafiyan da kake takama dashi lokaci guda zai iya maisheka miskini mara moriya kana kuma a raye. Kukane yazo min har na kasa karasa zancena na juya na fara kuka sosai a cikin tashin hankali da bacin rai ga abinda ya faru din. Kai ya dukar a kasa don wanan maganan dana fada yafi komai nauyi a wurin shi sai yaji wani irin gumi yana feso mashi lokaci guda gashi ya rasa abinda zaice dani don yasan gaskiya na fada mai . Don nauyi mami da yan uwanshi a iya su zancen zai tsaya idan sun san da haka nawa iyayyen kuma da wani ido zai iya kallon su idan har sunji. Don haka sai ya zuba min ido kawai yana kallona da mamaki kamar ranan ya fara ganina a duniya. Nima ban fasa kukan takaicin da nakeyi ba can naji yakai hannun shi saman kafadana yana fadin is OK kukan ya isa haka nasan na aika abinda Allah ya haramta ga musulmi . Saidai ina rokon ki da ki taimakeni ki mun adduan Allah ya rabani dashi har abada a rayuwana yadda ya fada a cikin wani murya mai ban tausayi zakace bashi yake maganan ba. Majina na share da kyalen dana aje a wurin don share hancina tunda safe kafin na dago kai ince ko nayima addu,a yaya tunda kai baka da niyar bari ba fasawa zakayi ba ai. Shikan yau mamakin zainab din yakeyi a ransa sai fadin yake ashe haka wanan yayinyar take ina kallonta shiru shiru ashe akwai aiki ja a gabana rana data gama gane koni waye ? Saidai a fili yace waya fada maki bana addua akan hakan ko yaushe abune dai idan Allah ya jarebaka dashi yana da wuyan sha,ani. Duk cikin maganganun da yai min a lokacin babu kalman ban hakkuri ko nadama a tare dashi don a gadarance yake fadan maganan shi kamar yadda ya saba idan yana magana. Kinci abinci yau ya tambaya a karshe banza nayi dashi ba tare dana bashi amsan tambayan nasa ba sai ajiyan zuciya da nakeyi don kukan dana sha a ranan. Kinga yanzun dai ki tashi kiyi wanka ki fito mu sauka kasa kici abinci don kada wani ciwo yazo ya kamaki kuma ? Ba zan iya cin komai ba don bakina bai da dasin cin wani abu a yanzu na fada ina gyara kwanciya ta hanyar dunkulewa a wuri daya. Yana zaune shiru banji ya motsa daga inda yake zaune ba sai can naji yayi ajiyan zuciya da karfi ya mike tsaye. Ni a zatona ya fice daga dakin ne a lokacin ashe ban dakina ya shiga ya hada min ruwa mai zafi sai ji nayi mutum yana kokarin cicibana lokaci daya. Don Allah yaya ka bari bana jin yin komai a yanzu zan tashi idan zuciyana ya sake min bai tsaya saurara min ba sai daukana da yayi dani yana shiga ya tsomani a cikin bahon wankan dake ban dakin . Lokaci guda na sake wani irin ajiyan zuciya a tare dani juyawa yayi ya fita ya ban wuri a yanzu kan idona ya bushe don na nemi kuka na rasa a idona. Haka na daure na watsa ruwa tare da alwal bayan na cire tufafin dake jikina na samu har na gama na fito a zatona yana dakin har lokacin don haka ban yarda na fito ba sai dana leka naga baya dakin. Zani da hijjab dina na dauko a wardrobe na nufi inda nake sallah na tada sallah ina sallah naji an kwankwasa dakin an shigo. Ashe julie ce ya umurta da takawo min abinci ganin ina sallah tana ta mamakina har tana tuntube a dakin wurin aje kayan abincin da ta shigo min dashi. Saida na gama sallah na mika kuka ga ubangiji kafin na mike na samu wasu kaya na zura a jikina ban ko kalli abinda ta aje min a dakin ba. Na koma bakin gado na zauna ban koma kwanciya ba sai ga mama da sallama a dakin a karon farko data shigo dakin nawa ke nan tun zuwan mu kasan. Amsa sallaman nayi halimatu na biye da ita a baya mama ke fadin zainab ashe bakiji dadin jikin ki bane sai yanzu mikin ke fada muna. Ni na dauka yau yana hutune ai kuna tare shiyasa ma ban yarda wanan yar taragagan tazo inda kike ba don yau banji fitan shi ba shima. Dan dariyan yake cikin katfin hali na kakaro a fuskana ina fadin tun darene bana jin dadi mama . Tace haka dai shima ya fada muna ai kwa fadawa mutane tunda gamu a gidan ai yanzu ina dadin hakan da kukayi ai ko sannu kawa mutum. Tana kai aya ta dora da fadin yace kinki cin komai tun safe ga abinci nan yasa a kawo maki sai ki daure kici don Allah don yace yayi yayi kici kin kiya. Badon naso ba don biyayya ga mama Ramatu na daure na kurba ruwan shayin bayan shi ban taba komai ba a kayan ina gamawa na koma na kwanta har lokacin suna dakin tare dani. A bakin su nake jin wai ya fita zuwa asibiti ya duba hjy amma ba zai dade ba zai dawo a raina nace shi dai ya sani don ni na tsane shi a yanzu. ZAINAB IDRIS MAKAWA Kwana biyu ina daki kwance a cikin damuwa bana fitowa ko falon gidan a inda muka saba dan zama dasu mama muna hira. Asibitin ma suke zuwa su duba hjy don ni ban iya fita yanayina kamar nayi jinyar kwanaki nake jin kaina. Ya jafar yakan shigo ya dubani na dan lokaci saidai zai kare tsayin shi har ya bar dakin ban dago kai na kalli inda yake tsaye ba hakan kuma bai nuna fushin shi ga yadda nakeyi mai din ba. Ranan dai dana kwatanci ya fice gidan na dan ja kafana na sauka kasa babu kowa a falon haka yasa na dan nufi wajen gidan don nasha iska kadan ko zanji jikina ya kara sakewa. Wasu tsuntsaye dake kiyo ne a haraban wurin suka dauki hankalina har yakai na shagala ga kallon su sun dauke min hankali yadda suke ciyar da junan su abinci. Barka da fitowa matar yaya naji an fada a bayana koda ban juya ba nasan ko muryan waye don muryan su yana da kama dana dan uwanshi hakan bai hanani gane ko waye a wurin ba yake gaidani. Dan juyowa nayi tare da kakalo murmushin don dole ina fadin ya jamal ina wuni a cikin ladabi shima dan gyara tsayuwan shi yayi yana amsa min lokaci guda. Tare da fadin ashe kwana biyu baki da lafiyane duk da nasan sanadin rashin lafiyan naki mijin kine ya jawo maki shi . Da sauri na dan dago kai na sauke a kanshi don jin abinda ya fada yace yes zainab na sani shine yaja maki wanan ciwon don halaiyan shi da kika fara gani wanda da farko yake boye muna hakan ko ? Don mu kanmu bamu san da hakan ba saboda ya boye muna koshi waye a wurin mu saidai ni tun ganin yadda auren ku ya wakana dashi na sa ido ga harkan yaya don in gano dalilin shi na bijerewa mami. Da kuma dalilin dayasa ya zabe ki a matsayin wace yake son luluba a cikin bargon arzikin ta ya fito a mutum sak kamar kowa. Wai zainab kinsan ke din mai arzikine arzikin da ba kowa Allah keba irin sa ba sai kebabu daga cikin bayin sa . Shifa arziki da kike ji a wurin Allah kala kalane gun mutanene suka dauka arzikin dukiya shine arzkin da kowa zai samu yayi alfahari dashi. Allah nama bayin sa arzikine ta hanyoyi daban daban akwai masu arzikin "ya"ya akwai arziki na hali akwai mai arziki na baiwa da arzikin hakkuri da arzikin wadatan zuciya da dai sauran su. Kamar ke zainab kina da arziki dana fahinta wanda Allah ya baki wanda ba kowane zai iya fahintar haka ban sai mai natsuwa zai gane baiwan da Allah yai maki zainab. Kallon da nayi masa na ban fahince ka ba yasa yace yes Allah yai maki arzikin bawai da hakkuri wanda ba ko wace mace take da irin wanan baiwan ba haka. Ki duba duk da karacin shekarun ki zainab amma kin iya rike sirin mijin ki a zuciyar ki ba tare da kin fadawa kowa yasan halin da dan uwana ke ciki ba. Na gani da idona ba wani ya fada min ba irin halin da ya dawo maki a ciki gidan nan last two days da suka wuce don a buge ya shigo gidan nan ya tayar dake. Ban sani bako wanan ne karon ki na farko da kika ganshi a cikin wanan halin idan kuma har kin sani tun baya na dai yaba maki wurin kokarin boye masa siri da kikayi. Idona ne ya kawo kwalla lokaci guda yace no bana son kiyi kuka a yanzu don kuka ba naki bane zainab a yanzu. Saboda yakine ja a gaban ki dake tunkaran ki a yanzu don sai da taimakon ki zamu samu har mu shawo kan wanan matsalan don wanan yakin zainab ba naki bane ke kadai yanzu ya shafi kowan mu a yanzu. Yanzu yin fushi ko kauracewa ya J baya da amfani a garemu baki daya don ni nan na nuna mashi bacin raina yan kwanaki da suka wuce kan fahintar wasu halayan shi danayi da yake boye muna. Sai na fahinci fushi ko bashi baya baya hanashi aikata sabon daya samu kansa a ciki saidai ma ya kara kangare muna ta wanan hanyan. Zainab a yanzu ya zama dole muja ya J a jikin mu fiye da yadda muke a yanzu dashi mu sanman ma keda kike zama matar shi. Don ta hakan har Allah ya taimakemu ya bamu sa,a akan wanan halaiyan da yake aikatawa a boye don zainab gaskiya matakin da kike kokarin dauka bashi zai sa auren ki dashi ya rabu ba a yanzu. Yin hakan kuma kamar kara turashine ga abinda yakeyi a yanzu shike nan kinga rayuwan shi ya kara shiga wani hali ta sakacin mu ashe ? Don ke kanki ba zaki so kiga wani cikin yana irin wanan halaiyan ba kinga shike nan ko yaushe kina cikin damuwan hakan fiye da kina gidan sa ashe. Dama alkawarin Allahne duk wanda ya kama hanyar aljanna zaita haduwa da abubuwan da zuciyar shi bata so haka kuma wanda ya hanyar wuta zaita haduwa da abubuwan da zuciya keso . Shi yasa akace daga cikin hakkuri da akeso mutum yayi cikin rayuwan sa harda hakkurin biyyaya don Allah . Don hana zuciya aikata sabon data ginu akanta farat daya abune mai wahalan gaske sai a hankali ana jan hankalin maishi anayi masa nasiha da addua a hankali tare da nuni ga hukuncin da ubangiji ya tanadar kan abin sai kiga maishi ya bar abin ba tare da wani tashin hankali ba. Don haka zainab ina rokon ki a yanzu kada kice zaki bar yaya don wanan halin da idanunki ya gane maki a kanshi dama wanda baki gani din ba a yanzu bana fatan hakan a gareki. Don ni kaina bazan so mami ko wani namu musanman ma mama Ramatu dake nan yanzu tare damu har ta fahinci wanan abinda yaya keyi ko taji hakan daga bakin ki. Don haka zainab hakkuri zan kara baki kan hakan saifa kin jajirce gami da masa addua da saka ido kan duk wani al,amarin daya shafi rayuwan shi. Ki nuna kedin matar sunnace a gareshi wace tasan right din ta na aure bawai ina nufin sai kin fito fili kin nuna ya baki hakkin ki na matsayin ki na mata a garshi ba. A,a a cikin hikima da basira irin naku na mata ya kamata ki fata yakin da kika shirya a kansa yanzu ta hanyar sake jiki dashi ki daina wanan ja bayan da kikeyi a yanzu gareshi. Mijin kine zainab idan yayi ba daidai ba ki fito fili ki fada masa abinda yayi din baida kyau ga Allah da al,adan mu a sannu in yana da rabo sai kiga ya bari. Katse shi nayi da fadin to amma ya jamal kana ganin a matsayina na ba kowa ba a gareshi yaya zai yarda yaji nasiha ta ? Me zai hana zainab ya bani amsa zai saurara maki don nasan shi di yana son ki kuma yana tausayin ki a zuciyar shi. Wanda hakan nema har ya yanke shawaran ya aureki ya kawoki gidan shi ku zauna a tare ku kuma rayu a tare dashi duk ritsi duk wahala. A karshe ina mai kara baki hakkuri ka wanan kaddaran da kika samu kanki a ciki a matsayina na dan uwan ki yayan ki bawai kanin mijin ki ba. Hawayen da nake dannewa ne suka zubo min lokaci guda nace ya in sha Allahu zan gwada sharanka a kansa nima a matsayina na kanwarshi kuma matarshi a yanzu. Nagode zainab da kika fahinci ne kafin wani yasan wanan abi kunyar da yaya ke kokarin sakamu a idon duniya nima zanyi iya kokarina in dinga fadakar dashi kan abinda yake aikatawa din a yanzu. Na barki lafiya ni zan je asibiti yanzu sai dai ina son wanan damuwan da tashi hankalin ki daina yinsa daga wanan lokacin ki fito a matar auren ki sak a gidan nan ba tare da kin damu da warning din kowa akan hakan ba. Nina barki lafiya ya fada ya juya ya tafi ya barni a wurin ina binsa da kallo zuciyana kuma da dinbin tunane kan aikin daya dangantani dashi din a yanzu. Duk da nasan dama wanan din aikinane yin hakan inda hali kuma da jajircewa ya zama dole in shanye duk wani damuwa don in ba haka ba zuciyana tana gab data tarwatse a yanzu. Sake tambayan kaina nayi ta yaya zan iya duk wanan abubuwan yanzu don ni mace ce mai kunya da sanin ciwon kaina. Don haka ko zanyi ba zan iya zubar da kimana da darajana don kawai ina son wani ya gyara halinsa. Yana zaune ya dafe kanshi da hannu daya kamar yadda ya saba idan yana cikin damuwa a hankali ya juya yana dan sauke ajiyan zuciya. Ya zubawa desktop din dake gaban shi ido ya rasa gane me yasa ya kasa cire tunanen wanan yarinyar a zuciyar shi haka ? A hankali kifa kansa saman hannun shi tabbas yana da yakinin yanzu ba tausayin zainab da kuma son ya taimake kamar yadda yai alkawari da farko bane. Yana jin burbushin wani yanayi daba zai iya fassara ko me ye ba a zuciyar shi don yarinyar ta zame mashi kamar wani bangare na rayuwan shi a yanzu don yana jinta kamar ba zai iya rayuwa mai farin ciki ba idan yai nisa da ita. Sai dai yana matukar tausayawa kansa da yarinyar domin kuwa yasan idan zasu tabbata a haka rayuwan su a cikin garari zai tabbata don ba zai iya tabukawa kansu komai ba a zaman su. Kamar an tsikare shi ya dago a yadda yake da sauri yana fadi a fili idan ta gujeni fa don sanin koni waye a yanzu ? Ko kuma ta kasa boye hakan a zuciyar ta har ta fadawa wani wanan maganan da yake siri a tsakanin su don yarintan da yake a kanta tayi kankanta rike wanan sirin a zuciyar ta yanzu. Wayan shi ya zaro daga gaban aljihun yana kokarin kiran layina sai a lokacin ya tuna ai banda layin kasan nan da zai kirani dashi a yanzu. Wani wawan tsuki ya sake tare da fadin Oh shit wanan wani irin wauta nayi da sakaci ai hakan sai na kara saka zargin wani a kan hakan . Mikewa yayi tsaye lokaci guda yana shirin fita daga office din tare da tatara kanyan shi dake yashe saman table din. Daga haka ya fito da sauri drivern shi daya hangoshi ya karaso inda yake don ya karbi yar jakkan dake hannun boss din nasa. Mota ya shiga baya an bude Allah Allah yakeyi ya isa gida yayi mata warning kan zancen don ya fahinci ta dan warware da safe kafin ya fita. A falo muke zaune muna hira dasu mama da suka shigo suna ban labarin sun hadu da wata yar kasan data dinga zuba masu yare a cikin masifa suna mayar mata da zagi da hausa. Muna cikin dariyan hakan sai ganin shi mukayi a daidai lokacin ya shigo duk da ba a daidai lokacin yake dawowa gidan ba. Idon shi a kaina daya shigo falon yana mamakin yadda ya sameni yau ina dariya don bai taba samuna a haka ba tun zama a gidan nasa. A cikin daurewa da danne zuciyana na samu kaina da masa sannu da zuwa ina danne zuciyana don har lokacin ina mai jin kyaman shi don ina kallon a cikin yanayin dana ganshi a ranan. Amsawa yayi a cikin basarwa kamar yadda ya saba yi ako yaushe yana kokarin shihewa muka samu muryan shi yana fadin ke zainab zo ki sameni a ciki daga haka ya shige zuwa part din sa. Ina mamakin jin haka a raina na tsinkayi muryan mama tana fadin kai wanan yar da shirme kike har yanzu miji ya dawo baki tashi ki taresa irin na yan zamanin nan har sai ya bukaci hakan a gareki ? Dan turo baki nayi a gaba ina nuna bazan iya hakan ba halimatu ta saka min dariya na juyo ina fadin mama zan mari wanan yarinyar fa idan bata daina ba. Jeki zan mata fada mama ta fada itama tana kunshe dariyan ta dan wautan yarintar data gani a fili a gareni tare da fadin shi kuma jafar abinda ya sayawa kansa ke nan yanzu ? A part din nasa na sameshi a falon shi tsaye yana sintiri kamar wani abu na damunsa a lokacin na shigo na sameshi a hakan. Banyi magana ba ya juyo yana kallona na dan lokaci kafin yace me kike fadawa su mama ? Ban fahinci tambayan ka ba na tambaya a hankali naji yace kin fada masu ke nan ko ? Me na fada na sake tambayan shi cikin karfin hali ido ya tsura min kamar yana son fahintar wani abu a gareni kafin ya juya yana fadin shike nan ya fara tafiya. Ai basai na fada masu ba inshine tunanen ka kai da kanka idan baka daina ba zaka sheda masu kokai waye watarana. Wani irin juyowa yayi lokaci guda yana kallona ni babu fa,idan fadin wanan yanzu a bakina do abin kunyane a gareni don haka inama fatan Allah ya rabaka da wanan kazamin hali naka a yanzu yaya. Daga haka na juya na fara tafiya na barshi a wutin cike da mamakina nima tafiya nake ina mai yaba karfin halina na yaba bajinta na haka a gareshi lokaci guda. Ina fadi a fili ashe zan iya kamar yadda ya jamal ya gaya min saina cire tsoro a zuciyana na dasa mashi shakkana da tsoro a ransa. Dakina na fada na mayar na rufe tare da fadawa saman gado ina runtse idona wasu hawayene suka silalo min lokaci guda. A fili na furta yaya meyasa ka zabi wanan rayuwan a tsakanin rayuwan da zata zubar maka da darajan ka da kimarka a idona lokaci guda. Me ake da dan giya a rayuwa gara in rufe ido in koyi tujara akan hakan tun yanzu don in samu makamin yakarshi akan wanan harkan. Shima mamaki ne ya kasheshi a wurin wai haka yarinyar nan take dama koko yanzu ne ta fara hakan don ganina da tayi a cikin wani yanayin da bai dace ba. Zanyiwa tufkan hanci tun kan raini da wullakanci ya shiga tsakanin mu nan gaba da ita don ba zan lamunci karamar yarinya ta rainani ba. Zuciyar shice ta bashi amsa lokaci guda da fadin kai ka ja da baka yarda ta ganka a wanan halin na buguwa ba. Ido ya runtse lokaci guda yana maijin zafin kansa akan hakan ya bude kofa ya shiga dakin ya bi da kallo lokaci guda. Sai lokacin taju da yaima korar kare a ranan ya fado mai a zuciya don gashi yanzu yana son shi a kusa dashi ba halin hakan don yadda yake jin kansa yau ba zai iya daure hakan ba. Kayan jikin shi ya dan tage ya shiga bandaki ya watsa ruwa a jiki shi ya fito sallah ya gabatar kafin ya fito don yaci wani abu a cikinsa don rabonshi da yaci abinci tun daren jiya daya dan sha wani ferfesun da suke sha wanda ke kara masu karfi a jiki. Falon ya fito tare da danna kararawan kitchen don kiran daya daga cikin masu dafa abinci a gidan julie ce ta fito da sauri don tasan kiran maigidan ne a lokacin don shi kadai ke danna kararawan kiran su bakinshi basu taba kiransu haka ba. Tazo ta dan duka cikin girmamawa tare da fadin can i help you sir ba tare daya dago kanshi yace ta kawo mai abinci yaci ta juya da sauri tana fadin an gama. A daidai lokacin ne kuma na fito daga part dina zuwa falon wanan karon na sauya kayan jikina zuwa wando da riga masu kame jiki don fara gwada shawaran anty fadila dana yanke a raina. Tafe nake kamar bansan yana falon ba zaune na nufi wurin tv ina kokarin kunnawa tun shigowana falon ya sauke idon shi a kaina. Da sauri ya kawar da kanshi kamar wanda yaga wani abin tsoro a lokacin yana dan shafan kanshi don dan kwana biyun nan da yayi bai sha komai ba ko shakawa. Yana jin kansa a wani irin yanayi na daban da ke sakasu a cikin wani hali har zuwa lokacin da julie din ta kawo mai abincin kanshi na duke a kasa yana shafa a hankali don yanayin da yake jin kansa a lokacin. Tana ajewa take sanar mashi ya dago kai da jajayen idon shi da suka rine masa yakai kallon shi ga abincin . Kiran ta yayi don har ta juya zata wuce ciki yace ta dawo ta bude abinda ta dafa din daga inda nake ina jiyosu nace ta tafi ta barni in bude mai na fada cikin dakewan zuciya. ZAINAB IDRIS MAKAWA A hankali na fara takowa daga inda nake tsaye zuwa dining din a cikin tafiya mai kama dana hawainiya da nakan yi idan ina tafiya don sayin halina bai tsaya iya halina ba kwai har yanayin magana na da tafiyana a cikin sanyi nakeyin sa wanda sai mutum ya dauka sallone ya mayar dani hakan. Ba iyanan abin ya tsaya min ba don har yanayin kukana idan ina yi a kusa da mutum sai zuciyar mutum ya shiga wani hali a lokacin don tausayi. Gabana na faduwa na karaso inda yake zaune a gurin daning din a cikin tafiyana mai kama dana hawainiya da zaka dauka sallone ya mayar min da tafiya hakana. Har na karaso inda yake zaune yana mamakin sauyina a cikin lokaci guda na yadda na sauya ma sanin da yayi min da farko na mika hannu a hankali na fara bude warmer din dake gabana har lokacin yana zaune ya rike haban shi da hannayen shi duka biyu ta hanyan yin tagumi dasu yana kallona. Wani irin ferfesu na gani a ciki tare da wasu irin ganyayyaki da wani icce da ban san ko na meye ba na nufi dayan kulan zan bude naji ya dakatar dani yana fadin zuba min wanan din. Da mamaki na juyo na dan kalleshi har lokacin yana zaune a yadda yake saidai wanan karon bani yake kallo ba. Plate na jawo na soma zuba abinda ke cikin warmer din a hankali saida yagaji ya bude baki da kyat yana fadin ya isa hakana mana a cikin dakewa. Mayar da marfin nayi na rufe naja kujera daga gefe daya na zauna ya dauki spoon ya fara kurban ruwan a hankali ta hanyar ja a cikin sallo. Duk ina zaune gefen shi ina kallon shi ba tare dana motsa a inda nake zaune ba shi kuma ya mayar da hankali yana kurban abinsa hankali kwance. Sai mamakin haka nakeyi a zuciyana a daidai lokacin ne wayan shi yai kara kamar ba zai daga ba ya dauka daga inda yake zaune. Turanci mai kama da yaresu na chaina yakeyi naji yace outside da dan karfi kafin ya kara magana aka shigo gidan a daidai lokacin. Mutum hudune dukkan su uku suna da kama da yan kasan sai na hudun nasu ne launin shi ya dan bambamta da sauran. Tunda na daga ido na kallesu naji sam basu kwanta min a rai ba don yanayin shigan su ma yana nuna basu da tarbiya ko kadan. Ina zaune a yadda nake a wurin ban ko motsa ba balle alaman tashi don shigowan su din sai dai a cikin daurewa nake zaune don yadda suka sameni a lokacin jikina babu hijjab a tare dani. Duk wani iskancin da suka shigo dashi lokaci daya suka shanyeshi a fuskan su sai sukayi wani irin sayin a wurin. Barin ma shi philis daya fi kowa iya iskancin don baida kunya ko kadan shi a gaban kowa yana iya nuna halinsa. Addua nake a bakina kamar yadda malam yace inyiwa wanda duk ban yarda dashi da zarab zamuyi arba da maishi. Yar uwa addua kan gaskiya ne don shi philis din da numfashinsa ya kusa daukewa yake tambayan zuciyar shi wanan wace irin kyaune da ita haka kamar ba black girl ba ? Tun kan su zauna dayan ke kallona yake fadin wanan queen din fa kanwar kane Jackson ko yar uwarka koko ka fara harka da matane kuma ? Sai dai wanan din ai tayi kankanta da yawa gaskiya sai dai idan sister din kace ko ? Wani kallo ya watsawa philip din lokaci guda yana fadin wanan ba business din ku bane kun shigo muna gida haka babu notices bayan kun san family dina na gidan nan. Mu kuma ba haka addinin mu ya koyar damu shiga gidan da yan uwa suke tare da yardewan mutanen gidan. Dukkan su dariya sukayi idon su na a kaina kara daure fuskana nayi garesu don kar suga damana a lokacin . Mikewa nayi a lokacin Allah ya taimakeni ina saye da wani bakin dogon riga nawa na larabawan jordan mai shara sharan hanaye sai dan dinkin maternity daga zuwa wuyan rigan don yana da fadi bai matse min ba a jikina. Cikin wani irin murya da ba yaya din ba harsu din sun mutu a saurare duk da basu jin yaren da mukeyi nida shi nake fadin. Ka karasa ci ne a kwashe kayan yanzu aifa tuni yanayina ya tafi da imanin su lokaci guda har wasun su na rayawa a ransu wanan ai mutum zai iya gwadata ya gani a cikin mata. Ki barshi julie zata fito ta kwashe ki koma ciki kawai yanzu ya fada fuskan shi a daure saida abin yaso ya bani dariya sai na fuske na fara tafiya don barin wurin. Shima yaya mikewa yayi yana kallon agogon hannun shi yana fadin kuna nan ke nan don ni fita zanyi yanzu. Duk wani kallo suka bishi dashi lokaci guda suna mamakinshi don yin hakan da yai masu kafin su mike subi bayan shi zuwa waje don shi har yakai kofa a lokacin. A wajen gidan suka sameshi ya dafa kan mota ya dan bada nauyin shi ga motar suka sameshi a wurin suna fadin. Kamar bakai murna da zuwan mu ba yau gidan naka bayan babban tukwicin da mukazo ma dashi har gida bayan ka kori tj a gidan ka musan yanzu kana cikin matsuwa a dan kwana biyun nan da kayi ba harka a tare dakai. Sai lokacin ya dago daga yadda yake yana sauke idon shi akan saurayin da suka kawo mashi har gida wanda suke kira da sunyi mai sabon kamu har gida. Don yaron dan kasan Egypt ne sabon dan hannune shi farkon shiga harkan shi ke nan a yanzu don haka sukaga ya dace da jacksom din . Wani irin kallo yakewa saurin da yake tsaye yana dan wani kame jikin shi kamar wata mace sabon shigan karuwanci a fagen maza. Tsab ya gama kallon saurayin kafin yayi murmushi yana fadin a cikin wani yare kasan nafi son baki kamana don nafi ganewa hakan. Dariya suka saka tare da fadin ka dai gwada wanan din ka gani zakaji dadin zama dashi sosai don yaron zai iya dakai a yadda yaken nan sosai. Dan murmushi ya kakaro a karo na farko a fuskan shi tun zuwan su gidan ya bude baki da kyat yana fadin ya gode da kulawan su gareshi. Ya riko hannun yaron zuwa gareshi tare da jawoshi jikin shi a daidai lokacin ya jamal ya shigo gidan idon shi kan abinda yake faruwa. Bai tsaya kulasu ba ya wuce abinsu cikin jin haushin su gabadaya don ya gane mai ake kullawa a wurin . Saboda yasan taju yabar gidan tun washe garin daya dawo gidan a buge yaji suna fada sosai da taju din har yakai yai mashi korar kare ta yadda ba zai iya dawowa ba gidan lokacin. Bin ya jamal din sukayi da kallo kafin yace kai wanan lafiyayyen guy din fa haka ko kayi sabon kamune ko bamu sani ba ? Wani kallo ya sakewa mai maganan kafin yaji dayan na fadin amma wanan ai suna da kama sak da jackson wata kila dan uwansa ne na jini ai. Sai gudan yace amma guy din ya hadu ya shima dan hannu ne in tayashi don nidai guy din yayi min wallahi. What ya fada da karfi tare da fadin blood brother dinane fa kake fadan wanan maganan a kansa. To meye a ciki don na nemi dan uwan ka a harka bro ina duk karuwan kan mune hakan da inje waje ina neman wasu . Zuwa lokacin ran yaya jafar din ya kai kololuwar baci don ji yake kamar ya shake abokin nasa a wurin saboda takaici. Kadai rigani magana ne don ni gaba daya ya tafi da imanina a wurin nan don guy din ya hadu sosai. Dayan ya karbe da fadin saidai baku ganin cewa duka yan uwan nasa suna da jin kai sosai don gaba dayan su babu wanda ya gaida mu. Don ko kallo bamu ishesu ba dukko yadda muke da daraja a gari nan ake girmamamu sai gashi su ko kallo bamu ishesu ba ai. Cikin wani tsawa ya dakatar dasu yana fadin zan halaka mutum a wurin nan idan baku rufe min baki ba yanzu da kazamin maganan nan naku. Kallon yanayin shi sukeyi don sun fahinci ranshi ya gama baci a lokacin ga baki daya kafin suji yana fadin. Ai wanan wullakanci ne da cin zarafi ku rasa wanda zaku danganta da wanan abin sai dan uwana na jini. To bari kuji shi wanan harkan da kuke ganin munayi kowan ku nan yasan da addinin shi bai yarda da hakan ba. Idan baku sani ba yau ku sani a kullun ina mai nadaman shiga wanan harkan naku da kuka koya min wanda addinina da al,adana duka ya haramta wanan abin ga wanin mu. Yau gaskiya nayi nadaman sanin ku a rayuwana tunda har zaku iya kallon kanina ku nuna mashi sha,awan ku a fili babu dayan ku nan da ban ganin girma da daran dan uwanshi koda yan aikin gidan ku ne. Daga haka ya juya rai bace ya bude motarshi ya shiga yana kokarin barin su wurin ranshi a bace. Ganin hakan yasa suka san ranshi ya gama baci sosai alokacin da maganan su don sanin halin shi da sukayine zai iya sharesu har abada ga baki daya daga wanan lokacin. Ganin ya shiga mota yana kokarin tayarwa ya wuce suna bashi hakkuri ta hanyar daya dace yasa ya jamal din sauke numfashi yana barin wurin da yake tsaye yana sauraren su a cikin takaici ya shige gidan. Babu kowa a falon kai tsaye ya wuce zuwa part din shi yana mai jin zafin hakan daya faru a zuciyar shi. Yana jin da zai iya a ranan zai bar gidan dan uwan nasa ya koma Nigeria saidai hakan ba zai yiyu ba don dole ya tsaya kodon hjy dake asibiti da kuma mu da muke zaune a gidan cikin rashin sani. Don haka yaba kanshi hakkuri yana mai fadi a ranshi cewa fushi yanzu ba nasa bane idan shi yai fushi da dan uwan nasa mu yaya zamu kasance kuma ? Bamu hadu dashi ba bama wada yasan da dawowan shi gidan a lokacin sai bayan sallah magariba da muka fito falo muka ganshi ya fito falon ya samemu muka gaisa dashi a wurin. Mamane ke tambayan shi kona biyun nan wai meke damun shi ita fa batagane yadda ya canza ba akwana biyun nan idan anyi magana yace ba komai alhalin ba haka tasan shi ba a baya. Mama banu komai wallahi ni dai kawai yanayin garin nan ne bai mun ba mun saba a gida muna ganin yan uwa da abokai ko ina. Ta katse shi da fadin kai banda abinka baka ganin yaran nan matane basa fita ko ina amma a haka sun sake jikin su suna sha,anin su a gidan nan cikin rashin damuwa. Balle kai na miji kamarka kana nuna haka a yanzu mu mata muce me ta fada a cikin raha. Daga inda nake na saci kallon shi na fahinci akwai wani abinda ya bata masa rai a lokacin saidai banyi magana ba fun zaman shi a wurin suna ta hiran su da mama kan ciwon hjy da ake samun saukia yanzu kan jikin nata . Don ko yanzu za a iya sallaman ta ta dawo gida saidai dan binciken da suka tsaya yi a kanta ya hana a sallamota daga asibitin yanzu. Mikewa nayi don tunanen daya addabi zuciyana a lokacin na dan kallesu ina fadin mama ni zan shiga daga ciki . Ke ko tun yanzu muna nan muna rage dare don ni wanan shiga kwanan da wuri haka ya fara isata wallahi aiba jamal shi kadai zaman garin nan ya isa ba a yanzu harni nan zama wuri dayan nan ya isheni wallahi. Gashi mijin ki dawowan shi ba maza ba a gidan nan niko yanayin aikin nasane yake haka har dare ko wani lokaci dan gara yau ma ya dawo gidan nan yau da wuri. Dan murmushi nayi ina gyara zamana ba tare da yin magana ba a lokacin sai naji ya jamal na fadin kila ta gajine da zama ai. Ina fa gajiya ai bata dade da fitowa ba kazo kila dai don ta ganka zaune wurin nan ne take son ta tashi. A,a mama ya jamal ai tun ina gidan mami mun saba dashi yana daga cikin masu tausaya mi a lokacin dashi dasu ya mamud . Mu din ne bama tausaya maku ashe ta fada tana kallona a cikin zolaye nace da sauri a,a mama ba haka nake nufi ba wallahi kowama yana sona sosai wallahi. Ai baki sani ba zainab wallahi ban gama danin halinki ba sai a dan zaman nan namu nan yanzu na kara tantace koke waye. Gaskiya jafar yayi dacen mata idan kun dore a haka don ba ko wace sarakuwane tasan darajan iyayyen mijinta kamar yadda kike nunawa din. Dadin wanan yabon da mama tayi min a yanzu naji na dukar da kaina ina dan murmushi kasa kasa naji tace kai gaka ba wani sakin fuska kakewa dan uwanka ba kwanan nan aida gobe sai mu rokeshi mu dan fita yawon mike kafa . Tunda hjy dai taji sauki ba kamar yadda mukszo kasan nan da ita ba a cikin tashin hankali lokacin. Taji sauki yanzu kan sai dai kuma yanzu data dawo zata fara fitina da mutane kamar yadda ta saba yi a kullun . Dakuwa mama ta mika mai daga inda take zaune tana fadin ja,iri ai kuma naga hankalin ku ya tashi ai data kwanta ciwo. Yana dariya ya mike tsaye yana fadin mama ni zan shige akwai dan wani aiki da zanyi matar yaya saida safe ke nan ya fada yana kallona. Har muka tashi a gurin ya jamal dake dakin shigewan mu yana jin mu nikan ina shiga dakin ban daki na shiga na dauro alwala na fito. Nafilan da na saba yi duk dare kafin in shiga wanka nayi kafin in dora da shafa,i da wutiri na mike na gyara jikina tsab yau da yake mun dan dauki lokaci muna fira a falon sai yasa ban samu zuwa na kwanta a makwancina da wuri ba. Na gama tsab na jawo kofana lokacin wata zuciya tana fada min inyi kwanciyana kawai a dakina tunda dare yayi a yanzu. Saidai na wuce kada hakan ya jawo min laifi a wurin shi kuma tunda mun aje hakan dashi tun zuwan mu garin. Na fito na jawo kofana na rufe na nufi hanyar part din shi kai tsaye sai dai nayi mamakin ganin kofan a rufe a ranan. Murdawa nayi don ina jin dan kida yana tashi a ciki yasa nasan baiyi barci ba a lokacin idon shi biyu wata kila yana falke yana sana,arshi ta latsan waya ko computer. Kofan na dan duka kusan sau uku a lokaci daya naji na a bude ba don haka nayi niyar juyawa in koma dakina. Naji ana bude kofan haka yasa ni waigo don na koma in shiga tunda ya bude part din a yanzu. Saidai ana budewa ne idona yayi tozali da wani farin matashi a tsaye daga shi sai tawul daure a kungun shi yana rike da kofi a hannun shi da wani abu a cikin sa. Da mamaki nake kare mai kallo a cikin wani yanayi dana kasa gane koshi waye da har ya shigo part din yaya din kuma gashi daga shi sai dan tawul a jikin shi. Muryan yaya naji daga bayan shi dake fitowa daga cikin daki yana fadin who is there ? Cikin tambayawa sai saurayin ya jaye daga kofan don yaya din ya hangoni shima dai yana daure da towel kamar daurayin na farko. Wani irin faduwa gabana yayi lokaci guda nake kallon shi da mamakin ganin haka karara a fuskana. Yanayin fuskan shine ya canza lokaci guda munayin arba da shi a wurin yake fadin ke mekikeyi har yanzu baki kwanta ba. Saida nayi mai wani kallo na raini na sauke akan cup din dake hannun shi na juya ba tare da na bashi amsa ba na koma dakina na rufo da makulli. Saman gado na fada lokaci guda wanan karon ban iya yin kuka ba sai tambayan kaina nake me nagani me sukeyi haka a ciki ? Ta yaya shi yaya zai yarda ya kawo wani bako a part din da muke kwana a tare har zai yarda wani bako yazo haka ya kwana a ciki harda tubewa haka dashi. Anya waiko yaya yasan addini kuwa yasan abinda shari,a ya tanada kuwa yau aiko matsayin kanwarsa nake bazai kawo wani kato a part din shi ba yasan ina cikin part din kuma. ZAINAB IDRIS MAKAWA Ban fito daga dakin ba sai dana kwatanci fitan shi a gidan don wanan abin na daren jiyan daya tsaya min a raina. Ina mamaki duk dakunan dake wanan gidan ya jafar ya rasa inda zai sauke bakon shi sai part din shi alhalin yasan bashi kadai bane a part din nima a nan nake kwana. Anya kuwa ya jafar yasan addini kuwa sosai ai ko ba matar shi nake ba zaman kanwarshi nakeyi a gurin shi balle wanan kasan mutane da nazo ta dalilin shi. Ya kamata ace ya tsare min mutumcina da kimana na ya mace a gurin kowa balle kuma ina zaman matarshi ta sunna a yanzu. Idona kodai kodai sai dan fuskana daya kara yin fau ya wani zuke saboda kwana a kusan rayen da naye a daren jiyan . Nayi mamakin ganin ya jamal a gida shi da yake fita tun safe zuwa duban hjy a asibiti sai gashi yau na ganshi a gida tare dasu mama a falo zaune. Gaba dayan su ido suka zuba min har na karaso inda suke zaune ban zauna ba saida naje gaban mama na tsugunna na gaida ita da kwana. Kafi in juyo wurin ya jamal shima na gaida shi ta amsa tana fadin yanzun ko maman ku ta bugo waya tana tambayan ki nace baki tashi ba tukun. Ashema kina falke ban sani ba na tashi tun dazun mama bandai fito bane kawai ina ciki ina fitar da kayan wankina. Wurin halimatu na juya ina fadin halimatu lafiya kuwa don yanayin ta danaga ya canza lokaci guda. Ta dan nisa tare da fasin yayan mu ina kwana ashe ba barci kikeyi ba ma ? Lafiya kalau take don yanzu take muna zuba a nan tana bamu labarin karatun ta ana dariya kece ma dai yanayin ki ya nuna kamar dai baki da lafiya yau. Lafiya ta kalau mama na bata amsa ina mikewa tsaye sai naji halimatu na fadin yayan mu ina wanan rigan da nazo dashi sabo shi nake son in saka yau jumma,a. Yana daki mana ki duba na bata amsa ina zama sai take fadin ban ganshi bane tunda mukazo kuma naga kin dauko min shi. Na dauko mana yana daki ki duba kafin in gama magana mamata mike tana fadin barin kdan kewaya na fito yanzu da wanan rigiman na sadiya don ni kadai ke kiranta da halimatu kamar yadda muka saba tun a gida. Barin mama wurin yayi daidai da barin halimatu don haka aka barni dagani sai ya jamal zaune a wurin. Sai dan shiru ya biyo bayan hakan can na dago kai na dan kalleshi nace ya jiya ya jafar ya ban mamaki a gidan nan. Banso na fada ma wanan maganan ba amma ya zama dole in fada mashi a yanzu don shi kanshi yaya yasan haramun ne sauke bako haka balagage a part din shi kuma yasan ina a cikkn part din. Wani kallon mamaki ya jamal ke min hakan ya hanani ci gaba da maganan da nake son fada a lokacin. Kai naga ya girgiza yana fadin nasan ba zaki so hakan ba idan kin gani don ke ba jahilan addini bace zainab don nasan kinsan kanki duk da kina yarinya karama. Da sannu zaki fahinci abinda ni na kasa fada maki daga cikin halayai shi saidai ke wani mataki kika dauka da kikaga hakan ? Na bude baki da zuman magana naji halimatu na fadin nifa ban gani ba yayan mu sai kuma muryan mama tana fadin kijeki duba mata tunda yau fitina take ji kan riga kamar karamar yarinya dake tana hararan ta. Mikewa bayi don bin umurnin mama din muka jera zuwa ciki da halimatu din muna shiga dakin take fadin nafa ga rigan yayan mu. Dama ina sin ki tasone in fada maki abinda mami ta fada a kanki da ta kira wayan wai cewa tayi dake wai kece yar mulki dan tallaka bai iya samun wuri ba za a ce har yanzu kina kwance kina barci. Inji mami din ta fadi hakan don Allah daga yau kome mami ta fada a kaina kada ya kara damun ki kuma ki bar fada min don in banji ba banji bane kin gane ko ? Ta gyada min kai alaman eh nace ai sai ki dauki rigan ki saka a jiki kada su fahinci abunda kikazo fada min ke nan yanzu a daki. Tace ai ya jamal ya ce mata mulkin me kikeyi bayan ke ake cuta a kullun don dantane ai mai mulki sai tayi dariya tana fadin yai min daidai ai ba dai taji dadi a gidan nan ba wallahi tunda tace ita yar naci ce da kwadai zataga wullakanci saita raina kanta wallahi. Niko basu san ina jin komai ba don ina tsaye daga kofan shiga part din mu nake jin komai. Ido na tsura mata ina mata wani irin kallo kafin ince watau halimatu bakya ji ko saidai da kika fada min komai yanzu. Ai na bari tunda kince in bar fada maki wanan din ne kadai na fada tana wani turo baki a gaba tare da daukan kayan dake gabata data fitar ta saka ta fice a dakin. Zaune ta barni ina faman tunane sai yaushe mami zata daina hattarana kan dan ta ne dan da ba wani dadin zama dashi nake ji ba a tare dashi. A hankali na mayar ds idona na runtse wuri daya don yanzu na daina wanan ruwan hawayen da nakeyi saidai yawan tunane kawai da shiga halin damuwa. Duk aikin da yakeyi a ranan rashi bace yake idan ya tuna abinda ya faru a daren jiyan tsakanin mu ya rasa laifin waye a cikin mu har hakan ya faru. Shin laifina zai gani ko laifin Nabil daya bude kofan ko kuma laifin shi da sakacin shi yasa har hakan ya faru. Da bai bada daman in shigo shiyan in dinga kwana saboda dan maganan da mama tayi ba da duk haka bai faru ba a daren jiyan. Inda Allah ya gyara banga komai daya faru ba a tsakanin su da tashin hankalin da zai shiga a yau yasan yafi wanan girma. Da yanzu asirin shi ya gama zubewa a idon kowa don yasan ba zan iya rike kaina ba a lokacib mutane zan tara masa a gida don wauta. Gashi har raini yana son shiga tsakanin mu don dan abinda idona ya ganar min ranan yakai yanzu ban tsoron shi kamar da can baya. Ji itin kallon dana watsa mai a daren jiyan da sauri ya tambayi kanshi ko dai yarinyar nan tasan abinda nake yine tayi min irin wanan kallon ya tambayi kansa. Da sauri ya girgiza kanshi tare da fadi a cikin hausa kai ina bata gane komai ba kawai dai nike tunanen hakan. To wanan kallon tsanar fa na meye take min shi haka a daren jiyan don kawai ganin wanan gay din a karo na farko a part dina ? Koma dai meye ya zama dole in canza komai yadda wani bazai taba fahintar komai ba saidai jamal fa ya tambayi kansa yana dan murza goshin shi. Idon shi ya lumshe yana dan juya kujeran da yake zaune a kai ya zurfafa a cikin tunane. Karshe ya furta a fili wama zai yarda da wanan idan har sun fada tunda ba ganina akayi dumu dumu ina aikatawa ba ai. Zan fara da zainab don dole in tsawata mata kan ta fara zargina da wani abu na tabbatar da haka zata ja bakinta ta rufe gum. Har yamma ranan bai samu tsinana komai ba a office ya dai kula zuwan su a garin nan yana son ya jawo mashi koma baya aikin shi a yanzu don haka sai ya jajircewa abin. Dama hakan yake gudu ya faru dashi gashi kuma yarinyar da yake dauka ba wayau komai a tare da ita tana shirin jawo mashi matsala babba. Ya mike yana mamakin kansa wai yau shine da jin kunya da nauyin arinyar daya raina ma wayau ya fito daga office din driver shi yazo ya jashi saida suka hau hanya yake tambayan shi inda zasu tafi asibiti ya bashi amsa ba tare da dago kai ba. Ya samu hjy a zaune tana shan fruit salad da jamal ya sayo mata don tana yawan shan yayan icce sosai tun a gida yasa tun ranan data fara sha take sa ya sawo matashi tasha don yafi mata wanan abincin nasu na kasan dadi a bakinta. Turo kofan yayi da sallama sukai arba da jamal dake zaune a gefen gadon yana duban yadda take shan fruit din a cikin tausayin ta. Shima idon shi ya mayar kan tsohuwar data dago tana amsa mashi sallaman shi tare da fadin a,a maigidan ka samu isowa ke nan ? Ina nan tare da wanan sabon mijin dake son kwace maka ni a yanzu don naji na fara son shi a yanzu fiye da kowa. Dan murmushi jin abinda take fada ya karaso bakin gadon dashi yana fadin kinji sauki ke nan tunda har kin fara zancen miji yanzu. Yo za a fasa zancen mazane tunda gaku har ku biyu a gabana ai duk inda kaga mata sun kai uku a zaune zancen ke nan balleni da har biyu ke bori a kaina koma ince uku don mamud ma kullun muna gaisawa dashi a waya. Kice ke kasuwane dake haka ashe ban sani ba zan jaye don ba zan iya takara da kowa ba akanki don haka daga yau a fitar dani a cikin lissafin mazan. Mikewa ya jamal yayi zubur ba tare da magana da kowa ba ya nufi hanyar fita daga dakin hjy ce tasa murya tana fasin kai kuma jamilu ina zaka a zaune kalau. Fuskanshi ya dan bata kafin yace zanje nan wajene in dawo ba dadewa zanyi ba ai ya fada yana kokarin tafiya. Yaka zo nan nawa ta fada a cikin damuwa don tana lura a yan kwanakin nan kusan haka suke da dan uwan da zaran ya shigo sai jamal din ya fice daga dakin. Daga inda yake tsaye yana kokarin zaunawa yace barshi kawai ya tafi ba gani ba a a jafari ba yau ba ina kule da abinda ke wakana a tsakanin ka da dan uwan ka yanzu ? Zama yayi yana murmushi ba tare daya kalli idon tsohuwar ba jamal din dake kofa a tsaye bai juyo ba bai kuma wuce ba. Ta yaya kuke zaton zumunci zai dore a haka kai karami har kayi karfin halin yin fushi da yayan ka meyayi zafi haka tsakanin ku har ya kawo wannan ? Kaine babba jafari a sanadin ka kuma muke zaune a kasan nan yanzu don me ba zakayi hakkuri da kanin ka ba koma me yayi ma matukar abin bai sabawa addinin ku ba . Wani irin malolon bakin ciki jamal din ya hade kafin ya juyo yana fadin a cikin daurewa nifa hjy babu komai a tsakanin mu . Don haka zan tafi ya fada yana kokarin juyawa ta mika mashi dakuwa da hannun ta tana fadin karbi nan dan nema ka maidani tsohuwa ban san komai dake wakana a gabana ba ko yanzu ? Bajin dadin uwarku bane ta sameku a wanan halin don babu uwarda keson ganin rashin jittuwa a tsakan yayayen ta ba a duniyan ko wacecw kuwa. Basai naji abinda ya hada ku fada kaida dan uwan ka ba kuyi kokari dai ku dinga tausa zuciyar ku don Allah . Koma meya faru a tsakanin ku don Allah babu komai hjy shi yarone ai yasa yake wanan fushin dani haka ya jafar ya fada. Wani irin kallon tsana ya watsawa dan uwan nasa kafin yace in ni yarone ai Allah ba sa,an kowa bane yana kallon duk abinda bawan sa keyi a ko ina yake daga haka ya juya ya bar dakin tare da barin hjy da mamakin shi. Don bata taba ganin yayi fushi irin haka ba a gabanta ta juya tana kallon jikan nata dake zaune a gefen ta tana fadin. Akwai wani abinda kake aikatawa ne mara kyau jafari don wanan kalamin nasa ya sakani a cikin duhu sosai. Ki tambayeshi mana hjy shida ya fada ni dai nasan ban aikata komai ba da har zai fadi hakan ya fada cikin daure fuskan shi. Dan hira mai kama da nasiha hjy ta dinga jansa dashi har suka kai wani lokaci kafin ya mike yana fadin shi zai tafi don zai biya wani wuri kafin ya karasa gida. Sai bayan fitan shi ba a dade ba jamal ya shigo mata da leda a hannun shi yana sallama ta kalleshi ta kawar da kanta gefe . Au fushi kike dani don kawai na batawa masoyin ki rai hjy to tunda bakya son gani na bari in koma inda na fito ashe. Ka koma Nigeria idan ka tashi tafiya dan nema marasa ta ido har zaka tsaya kana daukan wanan zafin haka da dan uwan ka dake gaba dakai. Hjy ke nan ya fada yana girgiza kanshi tare da fadin bai fada maki abinda ya hadamu ba ke nan ya tafi ? Saida ta dan harare shi take fadin kai ka tsaya ayi maganan ne daka fita ku dai daina hakan baida kyau wallahi irin haka ke kawo matsala a cikin zuria kaga na baya yana raina na gaba dashi idan an saka ido sai abin yai girma. Hjy badai gaisuwa bane ya jawo hakan to zan gaidashi zancen ya kare hakan yai maki ko ya fada yana kallon fuskanta. Dan mere baki tayi tana kallon shi daga saman har kasa tana fadin zauna naga kamar abinci ka sayo zakaci yanzu ko ? Naci a waje ya bata amsa wanan kena sayowa shi yana kokatin bude ledan daya aje a gefen shi kamshi ya bure dakin. Muna zaune a falon don mama tafi son taga mun hadu wuri daya tana jan mu da hira har hakan yakai mun dan saki jiki da ita tunda ma halimatu da yanzu suke daki daya da ita. Ya shigo da sallama shi duka muka waigo muna amsa sallaman tare da gaidashi da dawowa . Zama yayi akan daya daga cikkn kujerun falon suna dan hira da mama wanda gaisawane tare da tambayan ta idan ba matsalan komai ? Naso na share shi amma sai naga rashin dacewan hakan a gaban mama don ko a lahira wani nacin albarkacin wani. Na mike zuwa kitchen din gidan wanda baifi shigana daya ba tun zuwan mu gidan sai kuma yau din dana shiga. Na fito daga kitchen din ina saye da dogon rigar atampa a jikina wanda akai mai dinkin free haka tunda na sanyo kai a falon gaba daya ya maida hankalinsa gare ni. Ya zuba min ido yana mamakin irin girman dana kara lokaci guda har na iso gareshi bai kawar da idon saba a kaina. Cup din da goran ruwa dana dora a tire na aje agabasa ina fadin ga ruwa yaya bai iya amsa min ba na dago na wuce ta gaban shi. Ga ruwa nan matar ka ta ajema a gaban ka mama ta fada tana kallon shi duk da ya nuna bani yake kallo ba a lokacin . Saidai hakan bai hanata fahintar abinda zuciyar shi ke raya masa ba a lokacin sai ji yayi mama na fadin ai haka ya mace take dama. Gata kamar ba zainab ba dai a yanzu gaba daya ta sauya wa wanda ya santa a baya a hankali ya dauki kofin tare da wani irin yar sanyayyar ajiyan yana bude ruwan. Falon na bari gaba daya don nasan kons zauna karshe mama zata ce inbisa ne yasa na bar falon ga baki daya na shige ciki. Wani tunane yayi a zuciyar shi yana kai ruwan a bakin shi da sauri ya aje cup din kamar wanda ya tuna da wani abu a lokacin a ransh ya nufi hanyar part din shi da sauri ido mama ta bishi dashi tana tausaya mashi . Mutum baida hutu a rayuwa kullun yana cikin aiki haka kamar injin ko lokacin kansa baida shi. Wanka ya shiga ya fito ya shirya falon shi ya zauna waya yakeyi da mami sun gama ya kira ya mamud sun dan dade a wayan kafin suyi sallama. Ya dan zauna ya mike dakina ya nufa baiyi zaton ina ciki dakin ba koda ya shiga sai gashi ya hangoni akwance saman gado nayi rub da ciki kamar ina barci. Kamshin turaren shine ya sanar dani shine ya shigo min daki a lokaci ba halimatu ba dake yawan shigowa wurina idan ina dakin. Sani hakan baisa na dago a yadda naken ba ina kwance naji yana fadin jiya ina maki magana don kin rainani kika wuce kika barni a tsaye ko waima me kika zauna jira a daki baki shigo da wuri ba ? Ban iya bashi amsa ba don jin tambayan da yayi min saida ya kara fadin watau ke yanzu ki rainani ko ? Don kawai kinga in tausayi ki ko har kike son ki wuce matsayin ki a wurina raini nason ya shiga tsakaka . Sai lokacin na dago ina fadin ni kaina ban san kana da bako ba a part din don da ban shiga ba nayi kwanciyana a nan. Bakon ki ko nawa ya fada a dan hasale nace kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allah. Don dukkan mu musulmai muke haramune wani bako ya shiga dakin da yake kebabbe a wurin mu koda yarone balle wanan din da yake baligin kansa ya zauna a tsakiyan mu. Dabi,un shi ma sam basu hallata ba yadda ya zauna kusan tsirara a gidan daba na muharamin sa ba yana yawo a hakan a tsirara dashi. Rasa abinda zaice dani yayi yana sauraren yadda nake fada masa magana haka akan abinda shi ya kasa ganewa nake nufi ko ? Wanan maganan ya kona masa rai sosai a cikin dakewa yake fadin kinsan ni bansan abinda ya dace ba sai ke . Kada ki kara gigin kai dare kuma idan baki manta ba na fada maki banda saka min ido a gidana ga duk abinda kika gani. Ban saka ido ba yaya asalima da nasan da zuwan sa na zanyi gigin shiga maku daki ba don hakan ya sabawa addinina ai. Wani kallo yai min ya juya don a yanzu babu abinda zai fada min da zai kare kanshi ga abindana fada bayan wanan don haka fita dakin shine alherin sa. Don na fara wuce tunanen sa a yadda ya daukeni da farko ashe kallon mai saman ruwa yake min don na wuce nasa tunanen ke nan shi yana min daukan karamar yarinya sharr ashe abin ba haka yake ba. Lalai iyayyen arewa na bawa yayansu tarbiyan sanin kai tun suna kana zasu fara fahintar addinin su. ZAINAB IDRIS MAKAWA Yau ya kasance jumma,a tun safe danayi wanka na saka wani dogon riga silk mai taushi bakin a jikina rigan baida kwaliya ko ina a jikin shi. Falo na fito don ingaida mama da kwana anan din na samesu zaune wanan karon harda ya jamal suna zaune. Mun gaisa na zauna da kur,ani a hannuna ina jiran karfe tara ya buga indanyi karatu don mun saba da hakan koda nake gidan mami ina karatu duk ranan jumma,a da alhamis a wanan lokaci. A hankali na bude dama da alwala na nafito na fara karatu a hankali jin suratul kafi nake ja yasa halimatu dake gefena karbewa tana bina a cikin daga murya sosai ta yadda duk wanda ke gidan zai iya jiyo muryan mu. A kasa nake zaune sai itama ta zamo ta dawo kasan a kusa dani ta zauna munayi a tare har yakai matan dake kitchen din gidan da mamakin mu suka fito suna leken mu daga kofan. A daidai wanan lokacin ya fito part dinshi a hankali yake takowa jikin shi yana saye da farar suith kal sai yar jakar da yake fita da ita rike a hannun shi. Da mamaki yake karasowa inda muke jin yadda muke karatun mu hankali kwance kuma cikin rashin damuwa da kowa muke karatun mu. Take yaji jikin shi yai sanyi lokaci guda sai faman tunane yake a zuciyanshi tare da fadin yaran nan haka suke da ilimin addini ashe ? Idan ko hakane akwai aiki a gabana don dole watarana zata fahinci wani abu daga gareni wanda iliminta zai iya haska mata hakan. A hankali har ya sauko ya kai zaune saman kujera hankalin shi yana gurin mu yana jin karatun yana taba mashi zuciya kafin ya juyo yana fadin antashi lafiya mama ? Kafito mama ta fada tana dan gyara gyalen jikinta data yafa a jikinta tare da gyara zaman ta sai halimatu ta dago tana gaidashi ya amsa tare da fadin yau karatu ake munane a gidan nan haka ? Ta danyi dariya tana noke kai mama ke fadin ai gara suyi don karatu a gida yana saukar da rahaman ubangiji ga kowa dake gidan. Sadiya ai akwai kokari ko karatun bokon nan haka takan dameni dashi a daki wani lokaci har ta isheni. Ya kara kallon halimatu din yana dan murmushi sai a lokacin ya jamal da hankalin shi kega waya ya dan dago kai yana gaidashi. Ya amsa kafin ya mike ya nufi wurin cin abinci don ya karya ba tare da kara furta wa dan uwan nasa wata kalma ba daga gaisuwa da sukayi kawai inda shima ya jamal din ya mayar da hankali ga abinda yakeyi. Ina kai aya na mike a hankali na nufi dining din na sameshi zaune yana waya da wanda naji ya kira da philis. Abincin na soma budewa har lokacin ban bude bakina munyi wani magana ba dashi sai kokari zuba mai abincin da nakeyi a plate. Ina gamawa na juya don in koma in karasa abinda nakeyi na jiyo muryan shi yana fadin zanan zainab. Cak naja na tsaya a wuri daya kafin in juyo inda yake ina fuskantar shi don jin abinda zai fada min a lokacin. Kujera ya nuna min da hannu saida na kalli kujeran duk da na gane me yake nufi da yin hakan na dan gusa zuwa wurin kujeran na zauna. Kin karyane ya tambayeni kai na girgiza mai alaman a, a da sauri yace sai zuwa yaushe zaki karya din ? Sha biyu na bashi amsa a takaice ina kokarin tashi naji ya kara fadin ke baki gudun yunwa yaja maki ciwone, ki debi abinci gayanan gaban ki kici ya fada cikin daure fuskan shi gareni. Ba musu na jawo plate zuwa gabana na fara diban abincin na zuba kadan duk yana kallona na mayar da warmer din na rufe naji yace wanan ne abincin da zakici din ? Kai kawai na gyada don ban son maganan komai dashi a yadda nake jin kaina don na gama fahintar yana da rauni a bangaren addinin mu sosai Tunda har zai iya nuna tashin damuwa kan abinda ya aikata min na kawo wani kato a dakin da nake a cikin sa nayi magana ya nuna hakan ba komai bane a gurin shi. Ko yanzu ma shiyasa na koma ga Allah don yayi min mafita gareshi dama wa yanda yake mu,amula dasu baki daya ko ranan haka maza suka shigo muna gidan kai tsaye bai nuna wani damuwa akan hakan ba . Gashi kuma shidin ashe mashayine na kwarai ban sani ba wanda nake zaton ko yan uwanshi da iyayyensa ma basu sanda hakan ba dan dama dama ya jamal da shima a lokacin yace ya fara sanin halinsa ke nan. Wata kilama yana da wasu halin na boye da ban sani ba tunda ina jin yadda anty fadila take yawan fada a kanshi ko yaushe. Inko hakane ni wace irin wawiyace da ban fahinci mai take kokarin nuna min ba a lokacin to ta yaya zan sanda hakan tunda bata fito fili ta fada min gaskiyan maganan ba kai tsaye. Da babu abinda zai kaini biyo shi kai ko gidan shima ba zan zauna ba don abin kunyane a kauyen mu aji wai mashayi nake aure ni Abu. Bansan sanda na girgiza kaina ba na furta bani ba zama da mashayi a rayuwana sai naji yace me kike fada ? Sai lokacin na tuno a gaban shi nake na dago ido na kalleshi ya dago kai ya tsareni da idon shi sun kada sunyi ja a lokaci guda yana son tantance sanadin maganana na zuciya da har ya fito fili. Why zainab kike son ki ja matsala a tsakanin mu har mutane sunyi muna dariya musanman mami idan taji wani abu yana wakana a tsakanin mu haka sai suyi muna dariya ita da abokanta damasu mara mata baya. Nasan kinyi hakuri sosai da kika iya boye wanan zancen a zuciyar ki kin nuna min ke din mace ce jaruma a cikin mata duk da karancin shekarun ki kuwa . Don haka ki daure ki min addua Allah ya rabani da wanan halin don kece mutun ta farko da nake bukatan adduan ta bayan mami, don ni kaina bansan lokacin da nayi zurfi ga wanan dabian ba a rayuwana. Idan ka hangomu zaune wurin dining din zaka dauka wani hiran mata da miji mukeyi a tsakanin mu a lokacin. Don har mama dake kallon mu daga inda take zaune don shi ya jamal tuni yabar falon ya fice daga gidan tun zaman mu a wurin. Cikin mamaki na dago kai ina mashi kallon mamaki don jin ya ambaci waini matarshi ce a yau a karo na farko zamana dashi. Nace am not your wife dan dama dama ka kirani da sister ka zaifi sauki garemu hakan . Cikin daga hannu kada mama ta fahinci make faruwa a tsakanin mu yace dani to to naji dama aike kanwatace tunda ke din yar mamice. Yana fadin haka ya mike don gudun kada asirin shi ya tonu a gaban mama da halimatu dake can zaune dan nisa damu. Nan ya wuce ya barni zaune na tasa abinci a gaba ina kallo naji mama na fadin har zaka fita ke nan yau dai ka saka zainab karyawa da wuri haka. Bata son cin abinci bansan meyasa hakan ba ta saba zama da rashin karyawa da wuri tun a gida. Tun daga wanan ranan ya saka min ido kan karyawa da safe na dai gane yana neman wani hanya na dan shakuwane a tsakanina dashi don haka na kara shan nin jikina dashi. Allah da ikon sa sai ga hjy an sallamota gida taji sauki sosai kamar ba ita bace akazo kasan da ita a tallabe. Dawowan hjy gidan ya kara muna sakewa da an,nashuwa ko yaushe muna kusa da ita tana kara jan mu a jiki tare da bamu dariya da barkwanci kamar yadda muka saba a baya da ita a gidan mami kafin mu bar gidan. Saidai tsakanin ya jafar da ya jamal har yanzu babu jittuwa a tsakanin su suna dai gaisawa sama sama a tsakanin su. Tun hjy bata farga da har yanzu babu shiri a tsakanin su ba har yakai yanzu ta soma fahintar suna nan a yadda suke sai ta soma zargin akwai wani abu dake faruwa mai girma a tsakansu. Babban abinda yafi damunta shine ni kaina ta fahinci irin zaman da mukeyi dashi na wasa da hankalin mutane gashi idan ta fambayeni sai ince mata lafiya muke zaune dashi. Don haka tasha alwashin tambayana don jin irin zaman da mukeyi a tsakanin kafin shi ta tunkareshi tasan ba zata fahinci komai a bakin shi. Ranan ya jamal zai fita da mama data matsa ya kaita wani shago daya bata labari nima nace zan bisu zuwa shagon muyi kallo. Saida muka shirya hjy tace na zauna gida ba zamu barta a gida ita kadai ba badan naso na zauna din don naso fitan tunda a gaban yaya mukai maganan fitan har nace nima zan bisu y yarda. Bayan fitan sune tasa na debo fruit muna na debo a cikin bowl biyu na shigo dashi falon hjy kan tana shan nata saidai ni na saka nawa a gaba sai wasa da spoon din hannuna nakeyi ina faman tunane. Hjy ta aje cibin dake hannun ta ta tsura min idanu na dan wani lokaci sai ta lura ban ma san tana kallona ba a lokacin. Abu lafiya kike kuwa shiru ban dago kai ba ta kara fadin Abu nace meke damuwan ki haka kike wanan tunane haka ? Abu fa ta fada a karo na uku tana tafa hannayen ta idon ta a kaina firgigit na dawo a cikin hankakina ina dago kai tare da duban inda hjy take zaune. Ni take kallo a cikin mamaki baiyane karara a fuskan ta kafin tace dani me kike tunane haka yar nan kinga mu kadai ne a gidan nan yanzu. Ki saki jiki ki fada min abinda ke damun ki a rai ki dauka ni din mai baki shawaran da zai fitar dake daga hakin damuwan da kikene . Ko yanzu kin daina daukana a matsayin kawarki jafari ya kwace min ke kin daina yayina sai shi kadai ? Da sauri nace a, a hjy har gobe kina nan a matsayinki na kakata a zuciyana yanayin fuskana kawai ta kalla ta fahinci akwai wani abinda ke faruwa a tsakani mu da yayan. Duk sai nabi na tsargu da irin kallon da take min a lokacin don haka sai na dukar da kaina kasa ina ci gaba da wasa da cibin dake hannuna. Zainabu hjy ta sake kiran suna na dago kai a hankali ina amsawa da na,am tare dan kallon ta tace . Kinga ki fada min meye damuwan ki da mijin ki kada ki boye min komai ki daukeni tankar nice na haifi mahaifiyar ki ko mahaifin ki. Na dan gyada kai a hankali alaman gamsuwa a gareta kan abinda ta fada taci gaba da fadin tun zuwan mu ina kule da yanayin yadda kuke zaune dashi. Nayi shiru na tsayin lokaci kaina na a duke a kasa ina dan guntun tunane anya zan iya fada mata matsalan mu kuwa ko banza fa itace ta haifi mahaifiyar shi. Kuma ta nuna tafi son shi a cikin jikokin ta kaf idan na fada mata a wani yanayi tsohuwar zata shiga don jin jikan nata ashe mashayine na gaske. Don haka na yanke shawaran fada mata wani abin na daban na dan dago kaina tare da fadin hjy bana cikin matsalan komai dashi Ta dan tsura min ido na tsawon lokaci kafin tace kin tabbatar da hakan zainabu na gyada mata kai kawai sai naga tayi murmushi kadan a fuskanta kafin tace dani. Amma ni ga dan nawa fahintar sai naga kamar har yanzu babu wani mu,amulan aure dake wakana a tsakanin ku illa kawai gaisuwa da dan kulawa a gaban mu koba haka bane zainabu ? Da sauri na dago kai na kalleta sai kuma na dukar da idona saiga hawaye yana zubo min daga idanuwana lokaci guda. Ai kinga irin ta zainabu ina son ki sani ni mace ce yar uwan ki kuma manya sunce kowa ya rigaka kwana yana rigaka tashi. Hjy babu komai da dawani matsala ai zan sanar dake kawai dai ni karatu nake son inci gaba dashi yasa nake tunane na tsunci kaina da fadin haka a gareta. Hjy ta kalleni ta girgiza kai tare da fadin to shike nan amma kada ki dawo da baya kina dakin sanin kin fada min gaskiyan da bakiyi ba. Koda yake dai mai daki shiyasan inda ruwa ke masa yoyo ai idan kinfi bukatan ki tafi a hakan dake dashi aiga fili ga mai doki sai mu zuba ido mu gani zainabu. Ban yarda abinda kika fada ba a yanzu domin ni nasan kin boye min ne kawai don kina daukana ta bangaren jafari nake. Amma ni nasan da akwai abinda kike boye min a zuciyar ki namiki tambayan amsan daya ce ki bani sai baki ban ban ba kina kawo min wani zancen karatu. Karatu kan ai dole kiyishi zainabu tunda kina auren wanda boka ya huda ko jiyan nan naji yana magana akan karatun ki har nace ya barki a nan basai kin koma gida kinyi a can ba nan kusa dashi zaifi mai saukin yawan sintirin da zaiyi idan kina can Nageria din. Da sauri na dago kai a karo na barkatai na sauke kan hjyn don jin abinda ta fada na wai in zauna nan tare da yaya a kasan mutane inda bansan kowa ba. Eh hakan nace kuma ya amince da hakan don haka idan zamu koma ba tare dake zamu tafi ba a nan zamu barki keda kanwarki. Amma hjy da baki fada masa haka ba don shi kanshi yayan zaifi bukatan zamana a can gida da nan din ya dai amsa makine don baya iya mussata maki zancen ki gareshi . Eh hakan yana da kyau tunda harkin fahinci hakan keda kanki sabanin ke da yanzu kika fara daukana a wani matsayi na daban. Zainabu nasan ki nasan halinki don haka ban yarda da abinda kika fada ba a yanzu. Domin ke kullun yar ba komai ne saidai duk wanda yasan ki ya dubeki a yanzu yasan da akwai matsala a tare dake zainabu. Na dauka nice mutum ta farko da ko ban tambayeki ba zaki iya budan bkin ki ki fada min halinda kike ciki da mijin ki a gidan shi. Tunda ninayi tsaye har wanan auren naku ya kullun a tsakanin ku saboda ni nasan halinki da nasa da kyau don ke yarinyace da bata gama mallakan hankalinta ba har yanzu. Hawaye naji sun taru min a idanuna lokaci guda ina tausayawa kaina halin kuncin da nake ciki a wanan lokacin da abin zai fadu tabbas hjy kece ta farkon da zan fara fadawa wanan maganan a yanzu. Amma a fili nace da sauri na mayar da hawayen nawa ban yarda sun digo a gabanta ba sainace hjy addu, a kawai zaki tayamu dashi a yanzu nan gaba idan bai daina ba zan fada maki insha Allahu. Bayan ta dan tsura min ido tace to shike nan Allah yai maki albarka kin nuna min kedin mace ce ta gari mai rikon amnan mijinta ako wani hali ta tsunci kanta zata iya rike mai sirin sa a rayuwa. Madalla dake zainabu insha Allahu hakkuri ki ba zai tabe a banza ba kici gaba da hakkuri da addua kuma kada ki yarda ki saka damuwa a ranki kinji. Har muka bar wurin hjy tana min kallon tausayi don nasan tana da magana a zuciyar ta saidai ban bada daman hakan ba a lokacin. To me zan fada mata ince ga yadda jikan ta yake ai saidai tajishi a bakin wani na sani ko in fada ta sake ribcewa ciwon dayafi wanda ta taso a yanzu. Dakina na shiga cike da tunane na dan watsa ruwa tare da dauro alwala na fito na tayar da sallah azahar sai uku da rabi su mama suka dawo da sayyaya mai yawa tare dasu. Ban fito ba don tunanen da nakeyi kan zancen mu da hjy ba abinda ya tsaya min a rai sai zancen karatuna da zanyi a nan . Shike nan yanzu babu zancen komawa gida a garemu ke nan sai tsawon wani lokaci anya kuwa zan iya daurewa in zauna da wanan mashayin haka? Idan na zauna a nan dagani sai shi ta yaya zan iya shawo kansa babu kowa nasa a kusa dashi irin ya jamal da zai saka mai ido kan abinda yakeyi tunda ni ba zaiji magana na ba. Ya zama dole ke nan a gareni in kara jajircewa akan yadda zaman mu zai kasance a yanzu bayan tafiyan su hjy da mama. Zan kuma kara sa mai ido inyi iya kokarina wurun rabashi da wanan halin da yardan ubangijin mu sai dai babban matsalana a yanzu shine rashin layin waya da banda shi a tare dani. Don ina son muyi siri da malam mijin mai zube sai kuma matsalan anty fadila da nake son ya dawo da ita kusa dani don da taimakon ta zan iya samun nasaran abinda na dosa a yanzu. A takw dabara ya fado min a rai nace da hjy ya kamata na hada wurin shawo kan shi ya yarda fadila ta dawo nan mu zauna tare da ita . Ko abunuwa zasu zo min da sauki yadda nakeso don tafini sanin ta kan duniya ko naso yin abu bazan iya ba don hankalina baikai na hakan ba a yanzu. ZAINAB IDRIS MAKAWA Ya fito daga wanka da safe ya samu wayan shi dake ajiye saman bedside din shi yana ringing yayi saurin kai hannun shi ya dauka kada ya katse. Bakon lamba ya gani yayi kamar kada ya daga saidai ya daure ya dauka don baisan wanda ke kiranshi da wanan layin ba. Don tsayin kwanaki biyu ke nan maishi yana yawan kiranshi a daidai wanan lokacin don haka maishi yasan shi kenan farin sani yasa ya kirashi a wanan lokaci . Ya dauka da hello muryan taju ne akan layin ya fara magana da fadin nasan kayi fushi dani sosai yasa na kiraka na baka hakkuri don banzaci hakan zai faru ba ni kaina zafin kishine ya sakani yin hakan a lokacin. Saida ya gama sauraren shi yake fadin ka dauka dolene nake tare dakai dama ko kuma bazan iya zama idan babu kaiba. Taju ya saki wani dan ajiyan zuciya yace kayi hakkuri bana iya rayuwa idan bada kai ba boss kasa ka maye gurbin na da son wani bayan ni. Hankalina a tashe yake tun ranan da haka ya faru a tsakanin mu kayi hakkuri ka rike kaunar dake tsakani da kai bana iya jure ganinka tare da wani kuna rayuwa ina kallo. Ya jafar yayi murmushi a tausashe kafin yace taju ke nan kana sane kayi kokarin tona min asiri don kawai wani bakin kishin ka na banza can. Taju ya katse shi yana fadin Iam sorry boss banyi haka a cikin hankalina ba a lokacin kasan irin son da nake maka a rayuwana. Jafar din yaja wani uban tsoki tare da furta is too late now don na dade maye gurbin ka da wani so ka manta da wanan a tsakanin mu. Yana fadin haka ya kashe wayan shi taju ya kalli wayan yaga ya kashe abinsa idon shi ya runtse yana jin wani zafin son jafar din na ratsa zuciyar shi lokaci guda. Don tunda ya samu jafar ya bar sauran abokan harkan shi don jafar mutum ne har mutum yana da tabbacin idan jafar ya barshi rayuwan shi yana cikin gararari ke nan. Shiko jafar din wayar ya jefar saman gado ya koma gefe ya zauna ya tallafi kanahi da hannayen sa biyu zuciyar sa tana masa azalzala. Don shi yanzu zuciyar shi ta kasu biyu don yasan kirsis yake da asirin shi ya tonu muddin wanan yarinyar mai wayau na gidan nan. Bai mu maganan zancen karatun mu ba ko zancen tafiya ai bada mu za a tafi ba asalima dai dan kwana biyun nan na kula da yana yawan daure fuskan shi ga kowa a gidan. Ni hakan bai dameni ba tunda dama ba wani shakuwa bane tsakanin mu saidai abinda na zata ko hjy ta zauna dashine shima kamar yadda ta zauna dani tana bincikena kila shima sunyi hakan dashi. Ranan dai da safe muna zaune a dakin hjy yake cewa mu shirya zamu fita karfe hudu na dauka badani yake magana ba saida ya kalloni yana fadin bakiji bane na dago kai ina fadin naji a sanyayye. Daga inda hjy take zaune naji tace umhumm kawai tana dan kawar da kanta gefe daya daga barin kallon kowa a dakin. Mama Ramatune tayi karfin halin da matarka zaka fita ko damu duk don kayi magana ta baibai bamu fahince ka ba gaskiya a nan ? Da ita nake mama akwai inda zamu tafi tare yau ya bata amsa daga haka ya fice ya bar dakin hjy ta bishi da kallo tare da fadin miskilin banza kawai ya kama daure fuska kamar bai taba dariya ba. Fushi yake don nayi masa nasiha yake faman daure fuska haka don yasan yayi laifi yana gudun naci gaba da fada. Jin hakan yasa na dago kai da sauri ina kallon hjy don bansan me tayi mai fada a kai ba itama din ni take kallo kafin ta kawar da kai tana fadin . Ni dai na fada mai gaskiya don kada yaga kamar amana wasane duk wanda yai sakaci da rikon amana zai fada ranan lahira. Karfe hudu shaf na shirya don gudun kada inyi laifi a gareshi saida na dan zauna zaman jiran shi kafin ya fito daga part din shi. Ina dakina kwance ina jiran fitowan shi ya shigo dakin tun daga nisa yake karewa kyakyawan surana kallo. Kyakyawan suran kafafuwana da ya dan fito har zuwa sharaban kafana suna waje don yadda na kwanta din a lokacin. Ya tsaya ya shagalta da kallon su saboda yadda ya hangosu sunyi bul bul dasu tankar bana taka kasa dasu a yanzu. A hankali ya tako zuwa inda nake kwancen na shagalta da karatun wani littafi dana tsunta a gidan na labarai. Banji shigowan shi ba dakin haka ma takon shi zuwa bakin gadon duk ban ji shi ba a lokacin. Sai ji nayi girshi a na ja min rigar jikina daya tattare har zuwa sharabana dake waje tunda ni kadaine a dakin sai ban damu da hakan ba. Wani irin zabura nayi lokaci guda ina kokarin sake ihu don nasan halimatu dai ba zatayi min wanan haukan haka ba. Na juyo da wani irin sauri ya jafar na gani tsaye a kaina ya mayar da hannayen shi ya rungume saman kirjin shi. Da sauri na yunkura na tashi zaune ina kokarin gyara rigan nawa ya sauka da kyau kafin in dago kai in jefeshi da wani irin fitinannen kallo. Yace cikin daure fuska ki tashi mu tafi kina nan kwance lokaci yana kurewa gaki nan kwance ? Yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin kai tsaye nima tashi nayi saida na gyara fuskana irin dabi,an mata kafin in fita na sameshi cikin mota zaune yana jiran fitowana. Nayi mamakin ganin shi a gaba wurin mazaunin driver ke nan mu kadai zamu fita yau ba tare da kowa ba na tambayi kaina . Kafin in iso ya bude motar na zagaya zuwa dayan gefen na zauna tare da rufo kofan bai tsaya jiran komai ba yaja motan muka bar gidan. Tafiya mukayi mai nisa da gidan hankalina yana gun motocin danake gani tankar masu shi suka kera abinsu don kyau kafin naji yace may kika fadawa hjy har take tambayana zaman mu dake ? Da sauri na juyo na dan kalleshi tankar bashi yai maganan ba don hankalin shi gaba daya yana ga tukin da yakeyi lokacin. Kaina na mayar a wurin window motan naci gaba da kallon da nakeyi na motoci da gidajen su har ma da al,umman garin da nake gani kamar aljannu a idona. Yaci gaba da fadin na dauka kina da wayau da farko ashe abin ba haka bane don na manta ke din karamar yarinya ce da bata iya rike siri a cikinta ashe ? Daga cikin tsakiyan kaina nake jin sautin kalaman shi wanda babu tamtama idan nace zan bashi amsa a lokacin bazan fadi daidai ba. Barin fada maki kiji daga yau sai yau ba hjy ba ko mami data haifeni kika kara fadawa magana na sai kin kwamce da baki sanni ba wallahi. Wani irin juyowa nayi tare da kallon shi lokaci guda ina fadin kana dai wahal da kanka domin ni banga riban fadawa wani abinda kake aikatawa ba bayan Allah. Allah kadai ya kamata nakai kukana gareshi ba wanin Allah can ba don shi daya halice ka kuma ya kawoni karkashin innuwan ka na zauna shi yasan yadda zaiyi dakai. Naci gaba da fadi cikin muryan dake son nuna kuka nason zuwa min bakaji tsoron mahalincin kaba nawa zakaji yaya ? Ya dago kai yana kallona ido da ido tare da sauraren abinda nake fadi babu kuma alaman tsoron shi a fuskana ko kadan. Da sauri ya maida kanshi ga tukin da yakeyi zuciyar shi yana tafasa tare da jerowa kanshi tambayoyi wanda basu da amsa gareshi a lokacin. Wani irin fisgan motan yayi lokaci guda saida tsoro ya kamani a zuciyana amma a fili saina dake da hakan ban yarda na nuna mashi hakan ba. Fuskan shi kawai zaka kalla kasan rayuwan shi a bace yake wani babban moll ya packer motar sai daya dan sako iska daga bakin shi ta hanyar furzoshi da karfi lokaci guda alaman hade bakin ciki ya dan fadi a dake ki fita mu shiga nan ba tare daya kallo inda nake zaune ba. Fita nayi kamar yadda yace dani din shima ya fito muka jera zuwa cikin wurin inda mutanene birjit wasu na shiga wasu na fita da kwalaye mai kama da jakka a hannun su. Bai tsaya ba sai fannin kayan mata naga ya danyi magana mai kama da yare kafin matar ta nufoni tana washe baki. Kaya take daukowa sai ta zaba tana gwadawa a jikina tare da yaba yadda yayi min kyau nidai ina tsaye kimkyam kamar an dasani a wurin muka koma fannin takalma nan ma tana biye damu a baya da taimakonta har saida yace sun isa. Halimatu ma ta samu nata rabon don sayayya sosai mukai mata su man shafi da turare masu tsadan gaske ya saya muna . Bayan ya biya mun fitone ya biya wani shago a nan ya barni ya shiga naga ya fito da shigen jakar da aka sako muna kaya a wancan shagon sai dai ya riko daya a hannun shi yana zuwa wanan din ya saka a gaban mota kusa da kafan shi sauran aka sa a bayan mota. Hanyan gida ya dauko a lokacin har magariba ya dan gwauta ga yadda yanayi ya nuna na garin don wuri ya fara duhu ko. Mun shigo gidan babu kowa nasan sun shige yin sallah a lokacin don haka nima na nufi dakina don sauri in gabatar da nawa sallah kada lokaci ya kara kurewa Idan kin tafi kayan ku fa wazai shigo maki dashi dakin naji muryan shi yana fadin haka a bayana. Naja na tsaya wuri daya ba tare dana juyo ba ban kuma wuce part dina danayi niyar tafiya ba duk da ina sauri. Naji takon tafiyan shi sai muryan shi naji gap dani yana fadin banyi wanan maganan dake ba don ki fadawa hjy munyi. Ba halina bane fallasa sirina wanan abune daya shafeni a yanzu ni daya har in baka tuba ka daina ba nasan watarana idon su zai ganan masu kamar yadda Allah ya nuna min nima . Don Allah ba ai masa wayau ga duk wani abinda mutum yake ganin yana boyewa dole akwai wata rana da Allah zai fallasa shi ga mugun aikin sa. Allah ya baka ikon ganewa ka tuba ka daina don kan ka juyoni yayi da karfi har saida na dan firgita don ban zaci haka daga gareshi ba a lokacin. Da sauri nayi kokarin ja baya daga rikon dayai min din saidai na kasa hakan don ba karamin riko yai min ba a lokacin. Wani zafi hakan naji har kasan raina. Na dago a fusace don mashi kashedin hakan da yai saidai muna hada ido dashi kwarjinin shi da zatin shi ya hanani hakan gare shi. Kaina na mayar kasa da sauri don ba zan iya jurewa irin wanan kallon da yake min ba a lokacin wanda na kasa fassara hakan a raina. Shiru na dan lokaci kafin muryan mama ya shiga kunnuwan mu tana fadin kuma nan kuka tsaya ina dai lafiya na ganku haka ? Lafiya mama muna dan maganane a nan yana fadin haka ya sakeni da sauri na juyo ina fadin sannu mama tace har kun dawo ashe ? Mun shiga yin sallah ne yanzu ma wayana na manta dashi a nan inda na zauna nazo dauka shiko a lokacin har ya kai kofan part din shi don haushi. Don ba haka yaso ba yasone ya ban wahala sai na raina kaina sai ga mama din ta kwafsa mashi don fitowan ta a lokacin. Kayan da yake maga wani daga cikin yan aikin gidan ya fara shigowa dashi niki niki a cikin dan guntun turanci na ce dashi ya kai part dina mama tabi kayan da kallo. Tace ashe ku sayayya kuka fita waini wanan abin naku na daure mun kai yau ina antyn mu dake fadin sai kuma tayi shiru ganin haka nace banyi sallah ba mama. Jeki ki sallah kada ki makara don lokaci yaja sosai na juya da sauri na barta wurin na wuce zuwa part dina. Sallah nayi kafin na samu wuri na zauna a dakin ban fito ba don injin nauyi da kunyan mama a yadda ta samemu dashi a falon dazun don haka nai zamana a dakin kawai. Wanka nayi na shirya kwanciya na saka hijab saman kayan dake jikina na nufi part din shi har na shiga falon nasa . Sai naga wanan dan jakkan daya riko da kanshi aje saman kujera har na dan wuce wata zuciya tace na koma naga meya sayowa kanshi ne haka bai bari wani ya dauko mashi ba. Saida na kai zaune na bude ledab a hankali idona yai arba da kwalaben dake ciki kwalban kawai abin kallone. Zuciyana bai yarda da hakan ba ina kkkarin karata ko meye a cikin kwalban naji an fisge kwalban a hannu na tare da fadin get out from dis part stupid yana nuna min hanyar fita. Har abin naki yakai kiyi min bincike who give you dis right da zaki taba min kayana a hasale yake magana kamar zai mareni ko me ya tuna kuma oho. Ya duka ya dauki saurab kayan nasa nima mikewa nayi da sauri na fice daga part din sauri zuciyana cike da zargin shi. Ina shiga dakin na rufo kofa tare da saka ma kofan key na nufi gado na fada saidai ban kwanta ba ni ban kwance kuma bana zaune sai tunane nakeyi a raina. Dama wai haka aure yake ne nake ganin mata suna walwala ko wani lokaci kaga kamar basu da damuwa a tare dasu. Meyasa ya jafar yake min hakane koba komai yakamata ya rikeni tankar kanwarshi ta jini a gidansa tunda yasan yadda mukai aure a tsakanin mu. Tunane kala kala nayi shi a wurin karshe na mike na dauro alwala don barci ya kaurace min gaba daya a idona ranan. Sallah nayi raka,a hudu na dade wurin ina addua ina mika kukana ga Allah kafin naji sanyi a raina har barci ya daukeni. Naso makara ranan don ban kwanta da wuri ba a gagauce nayi sallah na koma na kwanta sai barci kuma. Kodana tashi shadaya na safe wanka nayi na fito bayan na shirya na fito don gaida hjy don nasa zata damu da rashin ganina da batayi da wuri ba ranan. Da sallama na shiga dakin ta saidai ita daya na sama tana zaune tana nafila na samu wuri na zauna harta idar bandade da zama ba naji tana fadin zainabu kin fito ? Eh hjy ina kwana ta amsa min a cikin fara,a tare da fadin ai mijin ki daya shigo nan nake tambayan shi yace jiya baki kwana da dadi ba. A raina nace makaryaci ke nan shikan ya hada duk wani abin ki da Allah ya hana Allah dai ya shiryoshi ya daina wanan hakin . Saidai a fili dan murmushi nayi ina fadin ciwo kaine kawai ai hjy kuma nasha magani ya bari. Dole ki ciwon kai jiya kun fita kun dade tunda baki saba fita irin haka ba dama kin dai kara cin wani abuko yanzu bayan kin tashi. Zan daici hjy na fada a cikin ladabi to kinga ga wanda suka kawo min niba dadin abincin su nake ji ba ki tashi ki diba kici yanzu. Dole haka na mike na dan dibi kadan na zauna nan gabanta kinga da haka zaki ta kamo zuciyar shi don kinga yanzu shi na masa fada ya nuna min yayi biyayya ga magana na yanzu . Don haka kiyi ta hakkuri bana son har uwarku ta gane wani rashin jittuwa yana shiga tsakanin ki da mijin ki ta yadda zata dara muna. Kinga Ramatu da kike gani diya tace nasan halin abinna kamar me yanzu tana zaman idon uwarku ne a gidan nan nasan duk abinda suka kitsa kan zuwa nan da ita . Don baki san yadda tafiyan ya wakana bake ta nuna idan bada Ramatu ba saidai a fasa tafiyan dole mijin ki ya yarda da hakan mukazo tare. Don haka nake son kafin mu tafi ta koma ta fadawa uwartaku zaman lafiya kukeyi tare dashi kinga duk wani shirin su sai ya tafi a banza ke nan. Saidai abindake wakana tsakani shi da dan uwanshi na rasa ko menene ya hadasu haka a yadda nasan su a tare nasu yafi zuwa daya. Sai gashi yanzu naga suna wasan kura da kare kamar wani abu na faruwa a tsakanin su ko kinsan meya hadasu haka wanan abin ke faruwa ?. Da sauri nace nima hjy haka na fahinta don ranan ma naji mama nawa ya jamal fada kan hakan yace da ita ba komai . Saboda na gane hjyn tana son tayi min wayau manya taji wani abu daga gurin yasa na fasa mata hakan don ta barni. ZAINAB IDRIS MAKAWA Akwana a tashi ba wuya a wurin Allah sai gashi har hjy ta gama shan maganin da aka bata suka koma da ya jamal don shi yayi tafiya wata kasa a lokacin yasa yabar komai a hannun jamal din. Suka bata sallama da sharadin zata dinga zuwa checkup duk bayan wata uku lokacin da naji hakan nayi murna kwarai don a zato zata zauna damu nan ke nan ga baki daya har lokacin da asibiti zasu sallameta baki daya. Saidai me ranan daya dawo daga tafiya baiko shiga dakin shi ba ya zarce wirin hjy sun gaisa tare da dan taba hira dashi har ta sako mashi zancen da asibiti sukayi. Shima cewa yayi da ita ashe zama chaina ya kamaki ke nan yanzu zaki shakara tare damu a nan ke nan ? Da wani irin sauri ta dago kai tana fadin ai in kaga na kara sati daya a kasan nan to bansan hanyar gida ba kenan idan kuma har ban sani ba sai in buga gida suzo su dauke ni. Hjy kamar wace dai ake kora ya fada a dan galabaice yana dan mika don zama cikin jirgi da yayi yasa shi gajiya don har dubai suka je bayan sun gama meeting. Hjy ta kalleshi tana fadin jeka ka huta mana tunda ka debo gajiya haka da yawa ni bance kuma da kai ana korana ba a nan. Iyakar gata dai kan aikun nuna min shi a duniyan nan nikai na godewa Allah na godewa haihuwa don yai min albarka. Ya mike yana fadin ni dai kan baki haifeni ba uwata dai ta iya haihuwa tunda itace ta haife ni ai hjy tace ja,iri waya haifi uwar taka da kake yabo da ban haiho ta ba har zata haifeka. Yau dai na gane fitina wanan tsohuwar kike ji dashi zuwa Nigeria kuma baki zuwa sai ranan da likita yace ya sallameki kwata kwata mama ce kadai zata koma ke ko kina nan tare damu. Dakai da likitan kunci gidan ku na gane abin naku hadin baki ne ni ko da kafa sai in karasa gida ba matsala bane a gareni. Zakiko hadu da kura dasu zaki hanya in takaman ki zuciyana ya fita yana dariyan yadda ta takankare tana masifa dashi don yace ba zata tafi ba. Ance sabo turken wawa bansan dan zaman mu tare ba har akwai sabon da ya shiga tsakanin mu hakan sai bayan tafiyan nan nasa . Duk ko da yatafi bamu cikin dadin rai dashi don har lokacin akwai fushin daukan mai kaya da nayi ina dubawa ya dauki fushi dani sosai a gidan. Har tafiyan nan ya kamashi yana cikin fushin haka dani ko zancen tafiyan a bakin hjy na farajin zaiyi tafiya wai. Na nuna mata nasan da zancen sai dai na manta da sunan kasan don yana da wuya mama Ramatu ke fadin ni dai yar nan kada wata rana ki ba dana kunya da wanan kauyancin naki. Hjy tace haka yarki tayi kafin ta waye itama aishi jafari ya mai da tarihin ubansa ne a rayuwa don haka ku bar ganin laifin shi haka. Da zai tafi kuma sai safiyan ya shigo min daki bayan ya shirya har an fita mai da kayan shi ina zaune saman dan stol din mirrow dakina ina shafa mai da nayi wanka. Ya shigo dakin ba tare da tsayawa ba yake fadin zaiyi tafiya zai kwana biyu a can idan muna da wani matsala in kira Samuel in fada mashi ko menene . Daga haka ya jiya zai fita a dakin na samu na bude bakina da kyar ina fadin Allah ya kai lafiya Allah yasa abinda akaje nema a samu . Na gode ya fada ya fita da sauri nabi bayan shi da kallo tare da sauke ajiyan zuciya na mayar da kaina ga mirrow ina kallon kaina a cikin madubin dake gabana . A hankali na raya a raina wai ina nake da matsalane a jikina da ya jafar bai min kallon mace ne har yanzu yadda naga wasu maza sunawa matansu dai ? Nidai banga inda na kasa ba da bai ma son ko ya kalleni idan har ya tsura dani haka a dakin da sauri kuma na kawar da wanan tunanen a raina ina fadin . Kenan har na damu da ya tabeni ke nan kamar wata jarababba dani nikan ina zan yarda da wani tabi kazami dashi yana shan giya kuma ya dawo ya tabani. Yau ma daya dawo ina kwance ina tunanen shi ashema yana cikin gidan ko a lokacin ban sani ba saida zai shiga part dinshi ne kamshin turaren da yake amfani dashi ya bugo hancina don kofa a bude halimatu ta barshi da zata fita . Saida naji gabana ya fadi sosai shiru na saurara banji motsin shi ba a dakin na sauke ajiyan zuciya a hankali tare da gyara kwanciya naci gaba da karatuna da nakeyi. Har wani lokaci hankalina bai kwanta da rashin ganin sa ya leko ba kuma ban daina jin kamshin sa a hancina ba saina dauka kewan shi kawai ke damuna nake jin hakan. Karshe dai waya ta na jawo na fara gamen a ciki tunda layin da nake dashi na Nageria ne bai zuwa ko na kira dashi. Nayiwa ya jamal magana ya saya min da zai fita ranan mama ta hana ya sayo min wai kila mijina baida bukatan na rike wayane a nan yasa bai sayo min ba don haka kada ya soma ya sayo min su samu matsala dashi. Don haka ya jamal din yaki sayo min layin da zanyi amfani dashi amma bayan wanan duk abinda mukace muna so idan zai fita yakan sayo muna yazo muna dashi. Wani lokacin ma idan bamu ce ba zai sayo din tundawa halimatu da take mai oyoyo idan ya dawo tkan zauna ta mai surutu sai ya gaji ya barta. Shikan gaskiya bamu da matsala dashi ko kadan don a kannensa yake daukan mu wani lokacin ma har ya tsawata wa halimatu idan tana wani abin. Hankalina ya dauku sosai ga game don haka banji shigowan shi dakin ba sai dai kamshine ya sanar dani hakan yasa na dago kai da sauri na sauke a kanshi. A lokacin yana tsaye daidai kaina ya sanya fararen kaya a jikin shi farin wando da wani riga mai kama da t shirt din maza saidai yadin shi mai laushi sosai saidai hannun rigan bai sauka har kasa ba. Saida na dan firgita dan ganin shi girshi hakan a gabana cikin rawan baki nake fadin yaya sannu da zuwa ya hanya ? Idon shi akan wayan dake hannu da nake game ya amsa min tare da fadin ina sadiya banganta part din su hjy ba dana shigo. Ban san inda ta shiga ba na basa amsa yasa yai min wani kallo kafin yace kila suna tare da mamane don itama ban ganta a dakin ba. Kokarin sauka daga kan gadon nayi ina ganin ya juya zai fita don hankalina ya tashi da cewa da yayi halimatu bata gidan. A daidai lokacin da muka sauko falon ne kuma naga ana shigowa da kayan da ya dawo tafiyan dasu yana tsaye yana magana da Samuel akan kayan. Dan ganin Samuel di na kallon direction din daya fito yasa shi dan juyowa yana kallon wurin nice nake kokarin gyara daurin gyalen dana rufe kaina dashi lokacin. Na karaso ina jin yana fadin ku kai wanan part din ta wanan kuma ya nuna part din hjy da nufin su kai can sauran yace su shiga mai dashi wurin shi su adana. A kawo abinci ko fita zakayi na fada cikin karfin hali da daurewa yace ba yanzu ba sai da dare zanci daga haka ya juya zuwa part din shi ni kuma na shiga wurin hjy don jin abinda ya fito dani. Na samu hjy tana kallon kayan da suka aje a gabanta tana mamaki nayi sallama take fadin ni wanan menene kuma a ciki suka shigo muna dashi haka ? Ya jafar yace su shigo dashi nan na bata amsa ina zama zan tambayi su mama sai gasu sun shigo mama na fadin ashe jafar ya dawo yanzun muka ganshi a waje zamu shigo . Ya dawo yana tambayan ku nake fada mashi kun fita mike kafa da jamal yake fadin ku rage fita a garin nan sosai. Da gajiyane man kullun mutum yana guri daya a zaune mama Ramatu ta fada tana kaiwa zaune fuskanta a abinda ta gani daure. Wanan kuma fa hjy ta tambaya tana kallon mahaifiyar tasu hjy tace miskilin danku yace a shigo dashi bai min bayanin ko meye a cikin sa don baima shigo ba tunda ya fita dazun. Fita halimatu tayi sai gata ta dawo dauke da cup cike da milk a cikin sa sai snack a dayan hannun nata. Allah yagani ina jin kunyar wanan rawan kan na halimatu a gaban su duk dako nayi mata fadan haka a dakina don ban manta da gorin da mama tayi muna ba a farkon zuwan mu gidan kan abinci. Yanzu ko tana nuna muna ba komai saidai ni ban yarda da hakan ba tunda har hjy ma data haifeta tace min nayi hankali da mama din ke nan ba sona da gaske takeyi ba. Shiyasa a kullun nake cikin jawa halimatu kune da ita din kada taje tana sake maganan gidan mu a gunta watarana a samun abin mana gori dashi. Nikan mikewa nayi da niyar ficewa daga dakin sai naji mama na fadin ai jafar din naga ya fita ina kuma zaki ana zaune ana hira. Ikon Allah ke haka kikeyi a gidanki idan mijin ki yana gida wanan saka idon har ina kuma Ramatu ? Haba dai hjy don na fada mata ya fita ai laifine kuma hakan yanzu gani nayi dai ko ta fita baya gidan ai . Ki barta ta tafi nace maki bana son wanan saka idon tsiya akan yaran nan bansan dalilin ku nayin hakan ba ko kukan mata kuma kuna da diya mata ne a gaban ku. Yanzu kuma hjy meya kawo wanan maganan daga fadin baya nan ta zauna shine na wanan maganan haka ? Ramatu ina dai horon ki da wanan dabian ko ita wace kike tayawa din wata rana zatai nadaman hakan mujuri zuwa rafi dai akace inji hausawa. Tashi kije mama ta fada a dan hasale tana kallona nace dama daki zan koma in dauke kayan dana bari a gurin. Jeki kawai ban tanbaye ki ba kada kuma kija min wani laifin gun hjy yanzu nikan jikina yayi sanyi haka na fita na bar masu dakin. Ashe hjy taji wayan mama Ramatune da mami da take fada mata ya jafar baya garin yai tafiya sai mami kecewa da ita. Ta kara saka ido a kaina ta kula da kyau kada ta bari in samu wani sakewa ko kadan dashi don ta tsani ta bude ido taji muna tare da danta wallahi. Ta kare da fadin sai yanzu nake yarda Ramatu da ake fadin asiri sukai min ita da iyayyenta tun kan tazo ki duba fa. Yadda na dauki yarinyar nan kamar ba yar aiki ba a gidana tankar wata jinina na jiki na mayar da yarinyar nan wai lokaci guda jafar yazo ya birkice min a kanta. Yau itace a kasan chaina zaune abinda ke kara ban haushi da takaici muga namu yayan zaune a gida Ramatu yau wa yaki nasa yasamu miji kamar jafar wai ? Mama Ramatu tace shine abin da nake fada maki ai anty lokacin nace irin yaran nan ba abin yarda bane wallahi kinki ki gane hakan a lokacin. Sam ban yarda ai tayi wani abin sakewa ko kadan tana nan yadda kika santa har yanzu saima dawowan hjy gidane ai ta dan sake jikin ta. Sun dauki lokaci suna magana a kaina itako hjy tayi kamar tana barci ne a lokacin basu sani ba don ta dade da kwantawa a lokacin yasa mama ta dauka barci takeyi har lokacin. Jin hakan shine dalilin da hjy take samata burki ga duk abinda tayi ta gane da manufa take min shi sai ta taka mata burki a take. Kayane na ban mamaki na shiga tsara saidai duk kyausu nikan basu min ba don sai na dauka shigan yan iska yake son mu dinga yi kawai a kasan nan yanzu duk da dogayen rigunane basuyi kama da wanda na saba amfani dasu ba masu gyale da nake yafa gyalen a kaina wani lokaci. Haka na halimatu dana gani a ciki suma dai din masu tsadane sosai daganin su na tattara na saka muna a wardrobe hakama takalma da jakkunan na aje a gurin ajesu. Sai da dare na shiga part din bada niyar kwana ba kamar yadda na saba shiga yana zaune na sameshi da waya a hannun shi sai cup din daya rike yana shan abu a cikin wanda bansan ko meye ba yake sha a lokacin. Har na karaso inda yake zaune yana kallona a cikin tsarguwa da daure fuskan shi gareni nima duban kofin nayi na kawar da kaina tare da kaiwa kasa na rusun na ina fadin munga kaya mun gode Allah ya karawa dukiya albarka. Ya gyada min kai yana zaune yadda yake saidai wanan karon ya mayar da kanshi a makarin kujeran yana mai lumshe idon shi a hankali. Ina fadin haka na mike ba tare da wani jinkiri ba na juya na fito daga part din zuciyana cike da zargin abinda naga yana sha din a lokacin . Ya Allah ka kawo wa wanan bawan naka dauki ka rabashi da wanan hali da duk wani abin hani daka hani al,umman Annabi ka dashi ya Allah. Na fada idona yana mai cikowa da hawaye haka na kwanta na dunkule a wuri daya zuciyana yana min tunane kala kala lokaci guda. Yanzu koda ace muna kwana a tare ne nayi fushi dashi haka yaya zai barni cikin rashin kulawa ko damuwa da hakan? Ashe da gaske ne da yake yawan fadin shi mace bata gaban shi asalima saidai yai mata kallon yar uwa ko abokiya kawai a idon shi. Idan ko har hakane akwai aiki ja a gabana don ba zan zauna a rayuwa haka da miji kamar kurman maza ba. Shin wai shi wani irin mutum ne haka koko shan giyar dayakeyi ne ya mayar dashi hakan ba,a sani ba ko kuma wanan dalilin ya zabeni a matsayin matar shi don ya cutawa rayuwana haka dai nayi ta faman tunane barkatai har barci yai gaba dani. Bayan kwana biyu da faruwan hakan nake jin zancen tafiyan su hjy wanda hakan ya tayar min da hankalina sosai. A cikin hakan ne ranan sai gashi ya shigo muna da takardun karatun mu wanan abin ya ban mamaki matuka. Duk ina karama haka bai hanani fahintar hikiman shi na kyautata min a gaban su don kawai su dauka kwai fahinta a tsakanina dashi. Idan ka gani zakacd duk dadin duniya ya kare a guna yadda yakan sayo min abu mai tsada ko ban kulawa a gaban su. Nikan da abin yakanzo min bambarakwai bana iya boye mamakina a fili ko rashin sabo da haka daga gareshi. Na samu hjy a daki ita kadai muna hira nake fadin hjy tafiya zakuyi ke nan idan kun tafi nasan rayuwana yana cikin garari a gidan nan. Hjy ta dago kai tana fadin akan wani dalili har zaki shiga garari yar nan sai lokacin na farga da kato baran da naso yi a gaban ta ashe. Da sauri nace hjy idan ba wani da zan dan dinga hira dashi haka ai sai damuwa ya kamani ko tunda shi yaya ba zama yakeyi a gida. Tare da fadin kuma din yace karatu zaku soma ai bada dadewa ba saidai tunanen gaskiyane don nima ban amince na barku haka daga ku sai wa yan nan yan arnakun ba a gidan nan gunda shi din dai bai zama. Zan kara mai magana kan wace zata zo ta zauna daku nan don kwanaki nayi mai bai ban amsa ba kan hakan. Barshi dani nasan yadda zan fito masa a yanzu dole ya yarda da hakan ai tunda dai ba zama zaiyi ba daku a gidan. Ana gobe zasu tafi dagani har halimatu mun kasa tsayar da hawayen mu kuka sosai mukayi ranan saida muka ba kowa tausayi. Shi da kanshi yaya ya rarashi halimatu don tace ita bin su hjy zatayi ta koma Nigeria da zama daya tambaye ta dalilin ta tace nan din yaya ba a fita kuma bama jin yaren su ai suma basa jin namu kuma. Da kyat ya samu ya rarashe ta hanyar cewa muma bada dadewa ba zamu je Nageria yanzun ta bari su hjy su fara tafiya don kada tayi fadan zuwa damu. A airport ma ban iya tsayar da hawayena ba sai faman kuka nakeyi hjy ma hawayene yazo mata tana sharewa da gefen gyalen dake jikin ta. Ta dan dafani tana fadin zainabu wanan shine aure dakike ji ana fada a rabaka da iyayyen ka da kowa naka zuwa inda baka taba rayuwa a ciki ba sai halin da kaje dashi. Shiyasa kike jin ana fadin aure yakin mata don idan ba mace ba babu namijin da zai iya barin gidan su har abada sai kadan da suke shigewa duniya. Gidan ya koma muna ba dadin zama mu biyu kawai ke rayuwa a cikin sa haka zamu suni zungun a gidan idan dare yayi kuma kafin ya dawo ma mun shiga kwana koda kuwa ba barci zamuyi ba a lokacin sai mu zauna muyi ta hira ko labarai a tsakanin mu muna dariya. Har ranan da zamu fara fita zuwa school din yayi a zatona shine zai kaini school din sai gashi driver yasa ya sauke mun don an gama biyan komai a lokacin. Sai gamu a bakon wuri muna faman robon ido don ganin bakar fata a wanan wajen sai can ba a rasa ba zaka gansu jefi jefi kuma ba yanayin musulunci a tare dasu. ZAINAB IDRIS MAKAWA Karatu kab zance ba dadi gaskiya da farko har ina shawaran fasawa a raina don kalubalin launin fata na farko da nake gani. Sai nabiyu yanayin shigana da ya zama masu abin kallo a can don na kasa amfani da kayan da yaya ya sayo min ko guda har wanan lokacin. Sai na uku shine karatun gaskiya ba fahintar shi nakeyi ba gashi dai turanci ne amma sai yake min kama da yare sukeyi idan suna bayanin su. Wanan dalilan yasa na saka damuwa a raina sosai har nake shawaran na daina fita kawai idan yayi magana nace dashi fasa kawai. Wanan shawaran na yanke a raina bazan kara zuwa daukan lectures ba shike nan nasan ma ba zai tambaya tunda baida lokacin mu sam. Itama dai halimatu kusan wanan matsalan take fuskanta sosai a karatun ta tana yawan min korafi kan challenges din da ake mata a school din da take zuwa din. Ranan da nake wanan tunanen a ranan ne ya shigo muna dakin mu har mun kwanta ya buga min kofa misalin karfe takwas na dare kenan a kasan. Da mamaki a fuskana nake kallon kofan kafin inyi karfin hali na mike daga inda nake zaune a kasa ina bitan karatuna don banson a tambaye ban sani ba yasa nake kwakwafewa da bita duk dare. Kofan na bude a hankali yana tsaye har lokacin sai dai yanayin shi ya nuna ya gaji da tsayi a wurin don bugun kofan. Zan iya cewa kwana kusan uku ke nan bamu hadu dashi ba a gidan do lokacin da muke fita bai fito daga part dinshi ba da safe. Ko idan mun dawo har dare bai shigo ba don haka bama haduwa kuma bana gane meke faruwa a kidan da dare. Ina wuni nace a sanyayye daga can cikin daki kuma halimatu ne ke gaidashi ya barni a tsaye wurin ba tare da amsa min gaisuwa na ba yana kokarin shiga dakin. Da sauri na jaye jikina na bashi hanya ya karasa shiga daga ciki yana fadin sadiya karatu ya boyeki yanzu ba a ganin ki ko ? Dan dariya tayi ta kara gaida shi na juyo zuwa cikin dakin daga inda ya barni a tsaye yana tambayan halimatu din I hope karatun dai sauki ko ? Tace ba, ba dadi yaya don bana fahintar me suke fada sosai dan dariya naji ya kwashe dashi kafin yakai tsugune yana fadin. Sadiya in kin daure zaki fahincesu ai kin taba ganin wanda ya samu a cikin sauki kowa kikaga ya zama wani abu a duniya jajircewan shi ne takaishi ga hakan. Ki daure ki fahinci me ake koyar dake zaki gane watarana har kizo ki fisu ga baki daya ajin ko baki son inna da Abba suyi alfahiri dake wata rana . Kai maddala da haihuwan da sukai maki yan uwa su huta ta gareki bakiga mamina yanzu itace abin kwatance a dakin su. Kai halimatun ta daga mai kamar tasan komai yace good wata rana kema sai kin fita a rayuwa amma fa hakan bai samuwa sai kin daure kin natsu zaki gane hakan. Ilimin mace ko da bata aiki bai taba tafiya a banza don zata waye tasan mai duniya ke ciki har ta taimakawa yayan ta itama . Halimatu ne ta katse shi da fadin ai yanzu yaya na fara ganewa kuma sun daina tsokana na da sukeyi da tunda na fasawa wata baki a cikin su ranan. Yace subbahanallahi sadiya ki daina fada fada ba kyau nan ba ruwansu sai su kulleki ba matsala bane a garesu nan. Alaman tsoro karara ya baiyana a fuskanta lokaci guda don jin abinda ya fada tace na daina ai yaya bazan kara ba. Kada ki kara kinji tashi kije falo zakiga wasu kwalaye da komai saman kujera ki kwaso kizo dasu nan ta mike da sauri zuwa inda ya aike ta kafin shima ya dago kai ya juyo gareni yana fadin. Baki dai da matsala wurin karatun ki ko na dan girgiza kaina a hankali alaman a,a ga sytem nan na sayo maki don su nan komai saida shi sukeyi zakiji saukin karatu. I hope kin san yadda ake amfani dashi dai ya tambaya nace eh duk da ba iyawa nayi sosai ba gana Anty Aisha da nake gidan mami takan dan bani in jagula kafin matsala ya shiga tsakanin mu dasu. Halimatu ta dawo dakin dauke da kwalaye niki niki ba bita da kallo ya karasa bakin gado ya zauna ta zubesu a gefen shi zata juyo yace dawo nan ki zauna . Karamin kwalin ya dauko yana kokarin budewa tare da fadin wanan naki ne sadiya zai taimaka maki wurin karatu sosai. Da sauri na dago ido ina kallon shi da mamaki halimatun ce za a bawa laptop haka karami mai kyau da tsada. Halima ta dan rike mai hannu tare da fadin yaya na gode Allah ya saka da alheri ya kara yawan arziki mai albarka yayi murmushi kawai. Wanan abin yaban mamaki gaskiya shiru nayi da bakina har ya fita a dakin ya dago kai yana kallona tare da miko min sauran kwalayen dake gefen shi. Nima ba wani magana ko nuna murna kan kyautan haka na karasa na amsa a can kasan makoshi nace dashi angode. Na nufi gefen shi na aje tare da juya na duka ina tattara takardun dana bari a kasa ya bini da kallo yana dan girgiza kai ya mike tsaye zai bar dakin. Sai kuma ya juyo yana fadin idan idan fa abincin da kuke tafiya dashi bai maku ba zaku iya magana su canza maku akwai komai idan babu zasu sayo ma. Yayi kawai na basa amsa don ni haka kawai yanzu nake jin wani irin haushin shi a raina wanda na rasa dalilin hakan ni dai kawai haushinsa nakeji kawai. Shima ya fita yana tunane a zuciyar shi don ya zaci zanyi murna sosai da wanan kyautar saidai kuma yaga sabanin hakan. A fili yake fasin kai mata dai suna da kama da hawainiya yau ka gansu fari gobe baki ji wanan yarinyar har tasan wani abu can fushi da mutum yanzu . Toma wai me akai mata take shan wanan kamashi da mutane haka ta nisanta kanta da shiga mutane ta kuma hana yar uwanta sakewa yanzu. Ban yarda halimatu tayi amfani da su ba don yana fita dakin da murnan ta ta shiga budewa ina kallon ta saida ta gama budewa ta koma ga nawa ta fara budewa. Laptop ne samfarin Apple da abin cajin shi sai wasu tarkace nasa a cikin kwalin ta koma ga dayan kwalin ashe wayace kiran iphone ya sayo min nina dauka duk takarcen laptop din ce duka ashe wayace a ciki. Mamakine ya kamani kwarai da ganin haka bayan wanda ke hannuna baiyi komai ba a lokacin. Haka na dauka ina kallo cike da mamaki sai naji banji dadin rashin godiyan da bai ma da muhinmamci koma dai me yakeyi kanshi ruwansa ai tunda har yai min alheri haka ya kamata in gode mashi sosai ai. Muryan halimatu ne ya dawo dani ga tunanen tana fadin yayan mu sai ki ban wanan tshon naki ke nan ko ?. Haba halimatu ya kamata ki tsaya a matsayin ki ko kin manta da cewa mu din diyan tallakawane wai ? Koni kina gani da taka tsantsan nake takona a gidan nan don ban yarda na zurewa komai ba tunda auren nawa kila wa kala ne kindai san komai. Ko yau ko gobe mami na iya cewa danta ya sakeni kinga sai mu koma gun iyayyen mu da zama ki fada min idan mun saba mun shagala a cikin daula haka ? Idan mun koma gida halimatu waye zai bamu wanan dadin wani hali kikeson mu shiga a lokacin idan mun saba da wanan gatan haka ? Kai ta dukar kasa tana wasa da hannayen ta nace niko wanan laotop din daya sayo maki ba zan yarda kiyi amfani dashi ba a yanzu balle wata waya can. Saidai idan nawa zaki dauka ki dinga amfani dashi ba zan hanaki ba halimatu amma ki rike wanan abin sam wallahi ba yanzu ba gaskiya. Ta dago kai da sauri don jin abinda na fada nace eh haka nace ko baki yarda da hakan bane yanzu in kira Inna in fada mata tunda ga waya na samu yanzu ? Tace na yarda mana yayan mu baga shi zamu dinga amfani da naki ba nace haka nake son ji halimatu shiyasa nake jin dadin ki wallahi yar kanwata. Haka na kwana da wanan abin har washegari banji dadin yadda ban nuna mai jin dadin abinda yasayo min ba. Karshe dai na yanke shawaran inje in sameshi tunda ranan ba aiki nayi masa godiya don yasan na yaba da kyatan nasa gareni. Na shirya tsab dani waini a dale zan shiga wurin maigida yasa na danyi kwaliya daga cikin ire iren kayan da yake sayo min a yanzu. Halimatu na barcin ta hankali kwance saman gado har na gama shirina na fita dakin bata sani ba na jawo kofa na rufo. Tunda na tun kari kofan haka kawai naji gabana yana faduwa bansan dalilin hakan ba gareni cikin daurewa har na karasa na tura kofan falon yana bude na sa kai na shiga da sallamana. Duk da nasan ba lalai bane in sameshi a falon lokacin don yau ranan hutu ne ga kowa saidai ina shiga idona yai arba dashi a zaune saman kujera daga shi sai tawul a jikin shi daure. Wanan Nabil din dan kasan Egypt yana kwance shima kamar yadda ya jafar din yake sai dan karamin tawul a jikin shi ya dora kan shi saman cinyar yaya danin suna dariya. Innalillahi na fada da karfi tare da saurin juyawa na bar falon gurin sauri ma ban ko rufo kofan ba a yadda na sameshi haka na bar masu shi a bude don gigita. Daki na koma na mayar da sauri na isa bakin gado na zauna gabana sai faduwa yakeyi fa fa fa fa kamar zasu iya biyoni nake gani nakai kallona ga kofan naga ai na saka sakata dana shigo. Gudun kada ya biyoni a baya shi kanshi karo na biyu ke nan da nake ganin sa ba tufafi a jikin shi ko wani lokaci kuma tare da wanan shedanin mai abin mata. Don ni yagin yan daudon garin mu dake suyan kaji da masa nake gani a gareshi ko yaushe idan na gansa a gidan. Haka kawai nake jin tsanarshi a raina balle yanzu da nake yawan ganin sa a gidan tun da su hjy suka bar garin . Yake yawan zama a gidan ko yaushe ko zamu hadu bangaidashi shima bai gaidani saidai ya wuce in wuce na kumayi warning din halimatu sosai kan kowa itama bata kula sha,anin sa sam. Don ya koma kamar dan gidan don wani lokaci zaka ganshi a dining zaune yana cin abinci ko yana falo mu yana kallo ko wani abindai a gidan. Tambayan kaina nagi wai ashe maza suna haka dama to aini banga mata suna wanan rashin kunya ba koda yan uwane . Da zarab sun fara girma zasu fara boyewa junan su tsiraicin su su kuma nisanta jikin su ga kowa koda kuwa daki daya suke. Wanan din hakan shine wayewan ko turancin koko zama da jajjayen fata yasa yaya yake kokarin barin addinin shi ne wai haka ? Gaskiya shi kan yaya ya fita daban nake gani da yan uwan sa wai dama haka yake baida kunya ashe kana ganin sa da farko zaka dauka mutumin kwarai ne yasan addinin shi. Ka ganshi kamar kamili a idanu wallahi na dauka shidin wani uztazune farkon ganina dashi da sanin danayi masa. Gashi da tausayi ga idanu da kawar da kai ga kowa da yake tare dashi bai shiga harkan kowa kona yan uwansa kuwa. Amma zuwan mu nan duk na raina wa yan nan halaiyan nasa ga baki daya sam baida riko ga addinin shi nake gani. Ni banyi barci ba kuma ban fita ba ban yi wani abu a dakin ba har lokacin da halimatu ta tashi ta sameni a hakana. Ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin wani dan riga a jikin ta take fadin yayan mu muje mu karya a kasa ina zaune kamar an dasani a wurin . Ban motsa ba kuma ban bata amsa ba har ta kara maimaita abinda ta fada ki je kici na fada ba tare dana kalleta ba . Itama wani irin kallkn zargi take min lokaci guda har lokacin idona sai hasko mi yanayin dana samesu a ciki yake min. Ko naje na hado muna ne ta fada na girgiza mara kai tare da mikewa don ban yarda in barta ta fita da wanan dan iskan dake gidan ba a yanzu tunda na gane nan ya kwana tunda a tube na gansa ai. Irin tarbiyan da innan mu tabani na nisantamu da maza dama kowa nake kokarin ba halimatu a yanzu don sam ni ban yarda da tarbiyan su ba a kasan. Tare muka fito muka zauna har saida taci ta koshi take fadin yayan mu ba zakici bane nayi dan murmushi na fara tsiyaya ruwan tea a cup sugar kadan na zuba na kafa kai ina kurba a hankali. Shine ya fara fitowa nayi saurin kawar da kai daga kalon su saiga dayan ya fito wanan karon sunyi wanka sun saka tufafi a jikin su saidai ina ganin bai kula damu a wajen ba don ya fito yana waya tare da sauri ya fita. Saiga shi Nabil din ya biyo bayan shi shima suka fice a tare na aje cup din ina jin wani iri a raina godiya na ga Allah halimatu bata kula dashi ba kartace zata gaidashi. Tun wanan lokacin nikan ban fito ba ina daki haka nayi weekend din kumshe a dakin sai ko idan na dan fito da halimatu ba zan dadeba zamu koma ciki. Bansan kome ya gani ba da daren lahadi muna shirin kwanciya sai gashi ya shigo dakin namu kallon halimatu da hankalinta ke gun waya yayi yana fadin halimaru . Ya kamata dai a saka maku kayan kallo a part din nan tunda baku fita falo yanzu ku zauna ka barshi muma ba jimawa zamuyi a kasan nan ba gida zamu koma. Yaushe ke nan ya tambaya ko gobe ne idan ka shirya sallaman mu na basa amsa ina kawar da idona garshi . Baki shirya tafiya ba ke nan idan dai nine zan sallameku ashe na gane bakya son a zauna lafiya dai ? Idan dai wanan dan isk, , , sai kuma nayi shiru kafin in sake fadin gaskiya ba zan iya zama gidan nan da wanan katon daka aje muna ba a gidan nan . Wani kallo yai min da sauri yake fadin wani katon ko bakon nawa kike son kira da kato yanzu kina da hankali kuwa ? Shiru nayi ban kara magana ba na dukar da kaina kasa shiru yayi shima ya ya tsura min ido na dan lokaci kafin ya juya ya fice a dakin. Muryan halimatune ya dawo dani daga tunane yayan mu zamu koma gidane ko ?. Wallahi nima ina son inje gida sa,adatu taga yadda na koma a yanzu duk sun san nafisu wayewa yanzu ? Halimatu ki barni don Allah kin cikanu da surutu wallahi na fada a dan hasale yarinyar fa bini da idanu don tasan batayi min komai ba na hauta da fada haka. Munyi haka dashi kwana biyu sai na bar ganin Nabil din a gidan nasa din maganan da mukayine dashi ya sallameshi . Tun dana kula da hakan na danji sanyi a raina ranan har muka fito falo muka zauna a cikin sakewa don yan aikin sukan ba ruwan su damu basu kuma shigowa inda muke kasafai sai idan sun shigo yin wani abu a gurin mu din. Tunda na samu waya yanzu akai akai nake kiran innan mu saidai ban fada mata matsalan danake fuskanta a gurin shi ba. Idan ta tambaye mu muna lafiya nakance lafiyan mu kalau nakan bawa halimatu suyi ta hira da yan uwan mu tana basu labarin abubuwan da muke gani a nan. Suma sukan labarta mata abindake gida har sukan zolayeta da ta dawo gida tace dasu sai tare da yayan mu idan zata zo mu koma tare. Hakan nawa innan mu dadi a ranta takan nasa muna zaune cikin salama da jin dadin rayuwa nida mijina ke nan wanda take alfahari da hakan ko yaushe. Idan mutane sun tambaya takan ce muna lafiya ita kan gaskiya sai sam barka don yanzu ta huta gaskiya don haihuwan diya mace yai mata rana a rayuwan ta. Da ace innan mu ta sanda zaman hakkurin da nakeyi da bata furta hakan a kaina da zata kwanmace in dawo gida gabata zaifi. Irin wanan tunanen nakanyi idan na tuna da alfaharin innan mu din a kan auren nawa da zata san halin da mijin nawa ke ciki dayi tir da Allah waidai da halin sa. A nan falon ya shigo ya samemu nayi mamakin ganin sa gida a wanan lokacin don rabona ma da ganin sa tun ranan da mukayi wanan zancen dashi. Ya shigo muna gaidashi ya amsa muna da kyat ya shige part dinshi binshi mukayi da kallo halimatu ke fadin kamar dai yayan mu baida lafiya fa ? Nikan ban kara bi ta kansa ba tunda banga ya fito ba har muka shige dakin mu bai fito ba dare yayi ina shirin kwanciya naji waya na ana kira na dauka bakon layi ne na kasanbake kiran dashi. Da tsoro na dauka na kara a kunnena muryan shine naji murya a ciki ciki yana fadin. Zainab ki shigo banda lafiya sosai ki taimaka min don Allah ? A dan razane na mike tare da jan hijjab dina na fita a firgice na bar dakin wanan karon ma a tsorace na shiga part din. Baya falon nasa don haka nasa kai zuwa dakin da nake zaton shine na kwanan sa don nan din nake tsanmani dakin sa. Da sallama a bakina na shiga na hangoshi saman gado sai faman juyi yakeyi yana wani irin nishi da kugi mai sauti tun daga kofan nake iya jiwo shi. Da sauri na karasa kusa ina fadin yaya meya sameka a rude nake magana don bansan irin taimakon da zan bashi ba a lokacin. Da kyar ya iya dago kai ya dan kalleni tare da min nuni da hannu yana fadin da kyar duba cikin fridge ki dauko min magani nan a wani kwalba fari. Na juya da sauri zuwa inda fridge din yake na bude idona ne ya fara tozali da kwalaben giya dako ba a fada ba nasan na giyane duka. ZAINAB IDRIS MAKAWA Hannuna na rawa nake daga kwalban a hankali ina kallo daga wanda yai rabi sai wanda ya kusa karewa saiko wanda ba,a ma bude ba. Wani iri nake ji a zuciyana naga kwalban da yai min kwatance in dauko mashi na dauka na koma da sauri har lokacin yana a yadda na barshi yana nishin . Mika mai nayi zan juya naji yana fadi cikin wani yanayi ki taimaka ki bude min don Allah ki bani ba zan iya komai ba yanzu. Dan hararan shi nayi babu wanan tausayin nasa a fuskana irin na dazunna balle marfin roban na zuba mai a marfin na mika mai ina kawar da kaina gefe daya. Don na gane shi din ba abin tausayi bane gama wani labari dana karanta na wani mashayin giya da yadda giya take wahal dashi kuma bai daina sha ba. Ki taimaka ki kaini bandaki na watsa ruwa ko zanji dan karfin jikina bayan ya miko min marfin ina kokarin rufewa. Dago kai nayi da sauri na dan kalleshi kamar zanyi magana sai dai na dake don alama ya nuna yana jin jikin nasa sosai a lokacin. Cikin daurewa na juya ba tare da yin magan ba na nufi bandakin na hada mai ruwan mai dan zafi Na dawo na sameshi a kwance wanan karon saman kafet yake kwance a tsakiyan dakin shi. Ban san lokacin dana kai durkushe ba gaban shi take idona ya fara fitar da hawaye lokaci guda. Sai wani nishi yakeyi mai ban tsoro wanda hakan ya kara firgitani a fili baima san ina gaban shi ba don idon shi a rufe yake yana faman juyi. Ko yaji kanshim jikina ko kuma zuciyar shi ta bashi ina gurin ne ya bude ido a hankali ya sauke a kaina. Cikin wani irin murya yake fadin ki daure ki taimakeni zainab zan mutu yana mika hannun shi zuwa inda nake gurfane muryan shi tankar ba nasa ba. A cikin rudu nace yaya mai zan ma yanzu wa zan kirama ya kaika asibiti shi zaifi ba zama gida da wanan ciwon ba tun kan dare yayi. Ji yayi tankar ya rungumeni don wani irin sha,awan dake taso mai lokaci guda kamar ransa zai fita. Ya lumshe ido ya mika hannunn shi ya riko hannuna yana fadin kirjina da marana kamar zai fashe wani irin ciwo yake min. Ya danke hannuna sosai ji nayi jikin shi na wani irin kadawa tausayin shi ya kamani lokaci guda har na manta da haushin sa da nake ji a raina ina jin tankar na yaye masa ciwon ya huta da wahala. A hankali na runtse idona don tausayin shi da nake ji ga kuma hannun shi daya rike nawa ina jin wani yanayi a tare dani. Ga jikin nasa da yanayin zazzabi gashi yayi wani irin rama lokaci guda jikin shi kamar ba nasa ba babu kuzari a tare dashi. Ya dan dade rike da hannuna a jikin shi a hankali yake sauke ajiyan zuciya alaman ciwon na lafawa a lokacin. Nace yaya tun yaushe ne baka da lafiya haka baka kula har ciwon yai nisa haka a jikin ka ? Da kyat ya bude ido ya kalleni a sanyaye idon shi da kyat yake iya budan idon yake fadin zainab yau two days ke nan ina fama haka. Idona na runtse runtse lokaci guda na shiga wani irin damuwa da dan tunanen halin da yake ciki din. Cikin daurewa nace kaci abinci kuwa yace na dan sha ruwan coffee da safe na mike tsaye ina fadin bari na debo ma wani abu kadanci yanzu. Sai lokacin na tuna hannun mu yana sarke dana junadashi da sauri na kalli hannun don har lokacin bai sakeni ba na dago na dan kalle shi muka hada ido nayi saurin dukar da kaina kasa. Nace bari na kara hada ma ruwan dumin ka watsa ko zakaji jikin ya sakema yace to zainab tunda kina son inyi a yanzu. Tsikar jikina naji ya tashi don irin kallon da yake min a lokaci na zare hannuna dake sarke da nasa na juya ya dan bini da kallo. Ruwan dumi na kara hadawa wanan karon yafi na farko zafi don zazzabin da naji a jikinshi dazun. Na matsa mai maclen ga brush sanan na fito na sameshi har lokacin a inda na barshi kwance a kasa. Murya kasa kasa nake fadin na hada ruwan a bandaki yaya ka tashi kayi wankan ko ? Jin yayi shiru gabana ya fara faduwa na dauka wani abune ya sameshi kuma lokacin ganin yadda ya lefe baya ko motsi . Hannuna nakai saman wuyan shi a hankali ina tabawa naga ya dago kai a hankali yana kallona cikiin wani irin yanayi na zafin ciwo nacin sa sosai. Ya mike yana mai mika min hannun shi na kamashi ya mike tsaye yana dafani har zuwa bandakin saida ya fara alaman tube tofafin jikin shi nayi saurin fitowa naja masa kofan. Ina fitowa na nufi gadon da yake a yamutse na gyara mai shi tsaf na kara gyara mai ko ina na dakin sannan na daga filo na aje mai kudaden dana gani a dakin. Saidana shirya komai tsab a dakin na fitar mai da wasu kaya masu laushi na dora saman gadon sa. Kitchen na shiga nasa julie ta hada mai kalar abincin sa da yakw ci idan baida lafiya a take jiki na rawa ta fara hada mai abincin na koma in gani ko ya fito daga bandakin. Sai jin kakarin amai naji shi yana yi daga cikin bandakin da sauri na isa kofan bandakin ina kiran sunan shi a hankali. Da kyar ya amsa min a wani irin yanayi sai can ya bude kofan ya fito yana rangaji ya nufi bakin gado ya zauna. Da sauri na karaso wurin ina masa sannu ya kai kwance daga shi sai tawul a jikin shi yana maida numfashi a hankali. Sannu da jiki na kara mai na dan dade a tsaye saman kanshi ina kallon yanayin da yake ciki na ciwon dake damunsa din. Kafin in juya in fita zuwa kitchen inda na samu julie ta hada abincin tana kokarin dauka takai masa na karba tare da yi mata godiya na bar kitchen din. Still dai a kwancen yake ya dora hannayen shi saman goshin shi ya rufe fuskan shi dashina aje abincin tare da fadin yaya ka daure ka saka kaya a jikin ka mana sai ka danci wani abu. Da kyat ya mike yana gyara tawul din dake jikin shi na kawar da idona da sauri daga kallon shi don abinda naga yanayi ban taba ganin namiji tube a haka gabana ba sai wanan ranan. Da kyar ya iya saka kayan a jikin shi ina mashi sannu a yadda nake kaina na duke ina kallon kasan ties din dakin dake sheki da daukan ido. Shima hankalin shi na gurina don yana tausaya min saboda ganin yadda na damu cikin dan lokaci kananki da ciwon shi. Yaci gaba da kallon yanayina bai iya magana ba har ya gama shirin shi ya dawo gaban abincin dana ajemai ya zauna . Da sauri na mike ina kokarin zuba mai yana kallona yana mamakin yadda na sa aka hada mai wanan abincin don gaskiya shi kadai zai iya ci a lokacin. Nagama na juya zan bar gurin ya dago kai ya bini da kallo can naji muryan shi yana fadin kada ki fita ki barni ni kadai yanzu. Jikinane yayi sanyi don jin abinda ya fada nace zan duba halimatu ne in dawo don bata san na bar dakin ba tana barci. Daga haka na fita na barshi a dakin ina tunanen yadda lokaci guda yayi laushi haka kamar bashi ba. Tana kwance abinta tana barci har lokacin hankali kwance na kara ja mata abin rufan ta data rufe dashi na shiga bandaki na kara wanka don dan aikin danayi naji jikina ba dadi. Na fito na gyara jikina na shirya na fito tare sawa kofan key ta baya zuwa part din yaya yana kwance share share saman gadon. A hankali na mayar da kofa na rufe na karasa bakin gadon ina kallon shi kafin in mayar da kallona wurin abincin dana zuba mai. Baici komai ba nake fadin yaya bakaci abincin ba ai ya dan dago da kyat yana fadin amai na kara yi danaci. Allah ya sauwaka nace mai tare da nufa wurin kayan ina hadawa yace ki barsu har da safe a fita dasu bari na fita dashi yanzu kada ya bata dakin na dauka ba tare jiran jin abinda zai fada ba. Na dawo tare da rufo kofan a hankali na samu gefen gado na zauna tare da tsura mai idanu ki kwanta zainab na gode ya fada a sanyayye. Zan kwanta a can na nuna sofan dake can gefe daya a dakin naji yace No ki kwanta kawai a nan bari nina koma can yana kokarin mikewa tsaye. Ni dai ido na kura mai har yakai ya kwanta tare da dunkulewa a wuri daya na dade a zaune ina kallon shi kafin na dan kwanta a hankali don dare yayi sosai a lokacin. Barci ya daukeni a yadda na kwanta din har bansan a inda nake ba sai can cikin dare cikin barcin nake jin wani irin nishi a gefena. A hankali nake bude idona na dauka da farko ko mafalki nakeyi saida kara bude idon naji a fili nake jin nishin na fitowa a gefena. Idon na ware gaba daya sai a lokacin na tuna a inda nake tare da dan dawo da hankalina wurin danake jin nishin nasa. Ban fahinci halinda yake ciki ba nayi yunkurin mikewa zaune ya kankame min jikina yana fadin please kada ki tashi zainab ki taimaka min in samu relief daga gare ki . Hakana daure yana kankame dani har lokacin da naji ya sake wani ajiyan zuciya mai karfi kafin naji jikin shi yayi lakwas na dan lokaci. Nidai ina wuri daya a takure a cikin tsoro da fargaba sai naji ya sakeni ya juya yana gyara kwanciyarshi sai lokacin na sauke wani irin ajiyan zuciya tare da dan juyawa. A hakan har na koma nayi barci na sai asuba na falka don lokacin tashina sallah yayina sauka saman gadon a hankali don kada na tayar dashi ya falka don a zatona ya samu barci. Sai na ganshi a wurin sallah shi yana sallah abin ya ban mamaki ganin hakan fasa shiga bathroom din nasa nayi na juya zan fita yake fadin ki shiga nan kiyi mana. Kamar munafuka na shiga nayo alwala ban dade ba na fito sallah nayi kafin in mike na bar dakin zuwa namu. Ina budewa halimatu na dagowa take fadin yayan mu har naji tsoro na falka ban ganki ba da dare tsoro ya kamani . Kai halimatu ina zani yanzu ai gani na dawo na bata amsa ina cire hijjab din dake jikina na nufi bandaki kai tsaye don in kewaya. Saida na fito ina shafa mai nake fadin jiya jikin yaya ya matsa mai saida ya kirani da dare na sameshi tace da sauri yaya jikin nasa yayan mu ? Yaji sauki yanzu na barshi yana sallah kafin in fiti na bata amsa naci gaba da abinda nakeyi na bata baya. Idan zaki koma zanje in gaudashi naji ta fada nace ba tare dana juyoba ki bari idan ya fito falo ku gaisa ban yarda da zuwa part din shi ba. Nima kinga ai saida ya kirani na tafi aka hada mai abinci nakuma hada mai ruwan wanka shine har ya samu barci. Na dade ban koma dakin ba har wani lokaci banji motsin shi har kusan sha dayan rana kuma ban koma na lekashi ba. Na dai yanke shawara a raina in lekashi inga halin da yake ciki yana barci sosai lokacin saidai na kula da baici komai ba tun safen . Sai kofin dake aje a saman dan table din glass din dake dakin da kwalba a kasa a raina nace Allah yasa dai ba abin yasha ba da sasasafe haka a cikin shi watau giya. Na juya zan bar dakin ya bude idon shi a hankali ya kira sunana na juyo inda yake kwancen ina fadin sannu yaya ya jikin ? Naji sauki ya fada yana kokarin mikewa zaune daga kwancen nayi saurin fadin akawo ma abincin ne ? No ki barshi yace tare da yunkurawa ya mike na bishi da idanu kasa kasa ina kallon shi a yanayin da yake tafiya a cikin rangaji. A zuciyana nace ka sha ka bugu ina zakaci wani abincin a yanzu Allah dai ya rabaka da wanan halin ga baki daya. Ya dan jima ya fito ya sameni a zaune can gefe ya samu daga karshen gadon ya dan kwanta ta hanyar daga kafan shi daya yana dan kadawa a hankali. Gaskiya yaya yakamata ace ka daina wanan abin yanzu na fada kamar am matso bakina in fada mashi hakan. Ido ya kura min sai na kasa karasa fadin abinda nayi niya kao tsaye da farko don tunanen danayi tayi ke nan dama a dakin. Don sai nake gani kamar giyance har tayi mai over ya sakashi a wanan rashin lafiyan da yakeyi a yanzu. Ina jin ki ya fada sai na dago kai na dan kalleshi ya tsura min ido yana kare min kallo cikin wani irin yanayi dana kasa fassarashi kona meye haka yake min. Kafin inji yace dani me kika daukeni ne zainab kin dauka ban san me nakeyi ba har kika samu matsayin da zaki fada min magana kai tsaye haka yadda kike so. Ni sa,an kine zainab ko shike nan don ina auren ki yanzu kike ganin kina da right din da zaki fada min maganan da duk yazo maki a baki. Ganin yadda ya taso yana fada dani yasa na dukar daina tunda ya fara maganan sa ban dago kaina ba. Wasa wasa saida ya kwana biyu bai fita ko kofa ba yana dakin sa a kwance ni kuma ina faman jinyar shi har yaji sauke ya fara fita . Gashi ya rame yayi baki dan lokaci guda ya fada sosai ga wanda yasan yadda yake a baya da yanzu din. Ranan mun fita zuwa school sai gaahi kwatsam ranan mun dawo daga school mun sami anty fadila a gidan kamar a mafalki muka ganta a falon kwance tana barci. Ga jakkata na kaya ajiye gefe daya da farko ban ganeta ba sai muka kama mata kallon mamaki don ganin mace bakar fata irin mu a gidan kwance tana barci. Halimatu ne da rigiman ta taje ta dan leka fuskanta a hankali ta sake wani ihun murna daya falkan da ita daga barcin tana fadin lah anty fadilace. Anty fadila na fada a daidai lokacin da itama ta falka a cikin tsoro dama da tsoro tayi barcin don sai bata gaskanta cewa gidan da muke bane a ciki. Munyi murnan da ihun ganin juna kafin in shige ina fadin ina zuwa na nufi part dina kai tsaye na bude na shiga da jakkan dake hannuna. Yau kan yaya ya gama min komai tunda har ya kawo muna anty fadila wanan kasan sai nakeji kamar innan muce yakawo muna a lokacin. Sai bayan mun gama murnan mu na ganin juna ne aka fara gaisawa da juna tare da tambayan ya bayan rabo ? Wanan part din dasu hjy suka zauna na kaita dakin a share yake don a kullun masu aikin shara mutum biyune suna gyara ko ina na gidan tsab. Munyi wanka da sallah kafin mu fito falo mu hadu har lokacin yaya bai dawo gidan ba duk da jikin shi bai gama warwarewa ba a lokacin don zakace yayi wani jinyane a gida. Fadila kan sai mamaki takeyi a yan watannin da mukayi bama tare da ita wai mun kara girma mun waye haka lokaci guda a nata ganin. Irin shirmen hjy tayi tana fadin wai ko ciki nake dashi a jikina na koma haka na cicciko nayi fresh dani farina ya karu sosai gwanin ban sha,awa dani. Murmushi nayi kawai itama dariya tayi tana fadin gaskiya a binciki wanan sauyin naki zainab, don ni gabaki daya kin sauya min ne ai ga sanin danayi baki. Lafiyanyyen aka shirya muna a dining don haka kai tsaye muka nufi wurin cin abincin halimatu ne ke fadin lokacin dana fara bude abincin. Anty yau zakici abincin kasan nan kiji tunda muka barku mukai missing din abincin muna gida wallahi kila naman kawai zaki iyaci sai ferfesu. Ta kalli halimatun tana dan murmushi tare da fadin nima nayi missing din ku sosai sadiya daga inda nake na harari halimatu tagane me nake nufi ta mike batare da cin komai a wurin tana fadi bari je inyi assigment dina ta barmu a wurin mu biyu. Ga mamakina sai naga taci abincin sosai ba tare da nuna komai ba kamar yadda mu muke nunawa ga abincin don har yanzu ba komai muke iya ciba sosai. Sai bayan mun gamane mun bar wurin zuwa wurin kujerun falon muka dasa hira yaushe rabo kamar munyi shekaru bama tare. Da alama dai zainab komai yana tafiya daidai a yanzu tsakanin ki da mijin ki sabanin yadda kuka baro mu gida. Don alamun sauyawan ki kawai ya nuna min hakan a yanzu don ance labarin zuciya a tambayi fuska naga farinciki sosai yanzu a tare dake. Wata karfafan ajiyan zuciya na sauke tuni annurin fuskana ya dauke na dan kalleta ina murmushin dole lokaci guda. Tace haba dai zainab kada kice min komai na nan har yanzu a yadda kuka barmu dashi don ni nayi zaton ai zaman ku wuri daya haka zai kara kawo shakuwa a tsakanin ku yanzu ? Kai na gyada mata ina fadin kwarai akwai canji sosai yanzu ba kamar baya ba anty don yanzu akwai dan shakuwa a tsakanin mu dashi. Sai dai wasu halaiya nasa ne na boye dana sani a yanzu suke tayar min da hankali sosai wallahi ban a cikin natsuwa ko kadan anty ga ba wani najikina da zan fadawa ya taimaka min da shawara. Kina nufin yanzu kin gane abinda na dade ina kokarin fahintar dake game dashi ke nan zainab ? Kai na gyada mata alaman na gane hakan sai ga halimatu tana fadin yayan mu nikin ban gane me ake nufi da wanan ba. Na juya gareta cikin kulawa ina karban takardan dake hannuta take nabi komai da akai masu na fara yi mata bayani a tsanake yadda zata gane. Wanan ne ya dauke min hankali na bar zancen hiran da mukeyi da anty fadila muka buge ga kararu dama aikin mu ke nan idan mun dawo ko kafin mu gama har lokacin dawowan yaya gida yayi. Nan dai muka gaida shi da dawowa ya amsa muna yadda ya saba karbawa sai fadilace ta gaidshi a karshe yasa ya dan juyo yana fadin. Af sorry kun iso lafiya ta amsa cikin danjin nauyin shi da lafiya kalau boss mun same ku lafiya ? Lafiya ya bata amsa a takaice ya bar wurin zuwa part din shi kai tsaye ta sauke ajiyan zuciya tana kallona ko zan mike nabi bayan shi a lokacin sai taga sabanin hakan. Ina zaune munci gaba da hiran mu da halimatu kafin inji tace mijinki fa yadawo daga aiki zainab kina zaune ? ZAINAB IDRIS MAKAWA Yana zaune yana sauraren wayan da mahaifiyar su takeyi da dan uwan shi tana wani lalashin shi a cikin wayan tare da kara warning din shi kan abinda take bukata. Daga inda yake zaune yaja wani irin tsuki yana kawar da kai gefe daya wanan yasa mami dago kai ta dan kalleshi taci gaba da magana da danta tana nanata mashi zancen guda da cewa wanan kidahumar yarinyar daka dauko da kanwar ta. Kana faman kashe masu kudi idan sunyi karatu a can uban wa zasu yi da karatun turai a kauyen su. Wani kallo jamal yaiwa uwan ya kara kawar da kai daga kallon ta karshe ma yayi kwanciyan balance kanshi na kallo sama yana tunane. Waikai jamal meye tsakanin ka da dan uwan ka ne ina lura tun dawowan ku kasan nan baka son zancen daya shifi jafaru sam. Wani irin dago kai yayi daga yadda yake kwancen yace wa mami waini ina ruwana da zancen kuni. Kaga jamal Ramatu ta fada min komai daya faru a can don haka yau ka fada min dalilin fadan ku da dan uwan ka kafin shima in kirashi inji meya hadashi da kai. Mami ni babu abinda ya hadani dashi fa ita maman bata fada maki bane ita data kawo maki wanan labarin. Ba wani zance na tambayeka ba illa ka fada min meya kawo wanan a tsakanin ku don na fara fahinyar abin naku gaba gaba yakeyi a yanzu. Mami ba zakije ba kikace idan kinje zakiga abinda ya hadani dashi ai da idon ki don ni ba zan iya furta komai ba a yanzu. Me kake nufi wai ko har yanzu bai daina shan giyan dana haneshi din bane wai dako hakane sai ya hadu da bacin raina. Mami da ace ya tsaya ga giyaje kawai aida abinda sauki don yaya jafar gaskiya a yanzu yana cikin wani hali da abin bai faduwa. Jamal me kake son ka fada min ne wai akan dan uwan ka a yanzu wani hali mai muni ya fada ko me ko matar daya daukarwa ransa ne matsalan shi ko ? Ta tambaya cikin son ji idan nice matsalan dan nata har suke wanan rikicin a tsakani su haka aiko da ta raba wanan kazamin auren kowa ya tsaya masa akanshi. Haba mami zainab fa matar rufin asirine a wurin mu da badon ita bace ya aura da ace wata ce da yanzu duniya tasan abinda yake ciki ai. Don babu macen da zatayi hakkuri da hakan ta zauna lafiya ba tare da anjisu ba . Ko ita din ai kwadaine daba haka ba ai ba zata yarda ba don kawai yana sha tace zata zauna ko tayi masa tonon asiri. Wai jamal me hakan ke nufine kana mun magana haka a dunkule kafito fili mana ka fada min abinda ke faruwa na sani. No mami ya mike tsaye tare da fadin nifa ba zakiji komai a bakina ba gara dai kije ki zauna kwana biyu ki fahinci komai da kanki zaifi. Yana fadin haka ya juya ya fice daga falo mami ta bishi da kallon da bata san tanayi ba a lokacin don zuciyan ta daya lula a cikin tunane kafin ta sauke wani irin ajiyan zuciya na dan lokaci . Tana jin kanta na wani irin sarawa lokaci guda da sauri ta jawo wayan data aje gefe tana neman layin mama Ramatun ta a lokacin. Kira daya biyu gana uku ta daga tare da sallama da gaida ita lokaci guda ta katse ta da fadin Ramatu tambayan ki zanyi don girman Allah kada ki rufe min idan ma hjy ce ta haneki da sanar dani wani abu daga cikin halaiyan da jafar yakryi a can. Ramatun tace jafar kuma anty me akace maki yayi muna van na assha kuma don daini gaskiya harga Allah banga wani abinda yakeyi ba daidai ba muna gidan sa. Zan binkita in san ko meye yakeyi har yai sanadin hadasu fada da jamal haka yanzu jamal ke min wani bayani a dunkule wanda ban gane hakan ba har idon shi na kklarin kawo hawaye lokaci guda. Gaskiya iya abinda na sani na fada maki ran nan don dukkan su sunki su fada muna kome ke faruwa a tsakanin su. Bata bari ta gama bayanin ta ba ta kashe wayan din wani iri da take jin kanta a lokacin ba zata iya tsayawa ta saurari zancen yar uwan nata ba sam. Ranan kan haka mami ta kwana tana tunanen duniya a karshe dai zuciyan ta yake fada mata kodai wanan tsintaciyat magen yarinyar ne ta kawo rigima a tsakan yaran nata Da wanan tunanen ta kwana a ranta haka ta tashi washe gari cike da damuwa a ranta sallah kawai ta idar ta dauki waya ta kira ya mamud. Yayi mamakin jin kiran mami da sassafe haka sai abin ya daga mai hankali sosai bai tsaya ba ya nufo part din mami din yanayin muryan ta ya nuna tana cikin tashin hankali. Direct dakin ta ya nufa yayi nocking aka amsa mai ya shigo tana zaune a saman dogon kujeran dake dakin ta jikin ta saye da hijjab dark blue wanda ya kara haska farin ta a fili. Mami lafiya ya tambaya a rude yana turo kofan dakin idon shi a kanta cikin nuna kulawa a gareta. Bakin gado ta nuna mai da hannu kafin ya karaso inda take yakai ya zauna a wurin yana kallon ta ido da ido tare da kara maimaita tambayan shi a gareta. Sai can ta dago kai a hankali ta kalleshi tana fadin jiya muke magana da jamal kan dan uwaka yai min hausa a dunkule dana kasa gane abinda yake nufi da hakan. Don amsan daya ban shine inje kasan da kaina zan fahinci may ya hadasu fada da idona don shi yaki fada min kasan kuma halinsa tunda bai fada ba ba zaya fadi din ba ke nan. Hakan yasani a rudani daren jiya banyi barci ba sai karshe nake hasashen idan ba a kan wanan yarinyar zainab bane haka ya faru a tsakanin su ? Ya mamud ya dago kai yana kallon mami din cikin rashin fahinta abinda hakan ke nufi yace mami akan me zasuyi fada don zainab ? Shine abinda na kasa fahinta nima idan bashi ba har me zai hadasu fada haka kafasan tsakanin shi da jamal sai Allah. Kai ya mamud din ya girgiza yana fadin sai dai idan wani abin na daban ya hadasu amma banyi tsamanin wanan zai iya hadasu ba gaskiya. Amma koma meye mami ki kwantar da hankalin ki zan binciki shi jamal din a tsanake ya fada min komai. Amma baka ganin kamar yadda shi jamal yace dani da farko wai ya kamata naje na saka ido akan abinda ke faruwa da rayuwan dan uwan naku wani abune daya danganci hakan a tunanen ka ? Mami duk da hakan dai ki kwantar da hankalin ki zanga shi jamal din muyi magana zai fada min komai insha Allahu. Na jima a zaune falon kafin in mikewa zuwa daki don lokacin sallah da yayi nan na samu halimatu a kwance tana kallo nake fadin ba zaki tashi kije kiyi sallah ba. Ina shiga ban daki nake wanan maganan na tura ban dakin na shiga koda na fito halimatu bata dakin a lokacin. Sallah na idar ina zaune a wurin ina jera addu,oi ji dawowan ta dakin don yanzu tun lokacin da sa,adatu ta samu waya take turo muna yan wakokin hausa da comedy a wayana. Nayi fadan hakan bata daina ba shi yasa ko yaushe halimatu take lake da waya tana kallo cikin irin haka ne yau ma tana dube dube a wayan taci karo da video da wayana ya dauka na convesetion din mu da Nabil a dining. Taso wuce shi sai kuma ta kunna tagani wani video ne kada ta wuce shi yake yadda mukayi da Nabil ne tiryan tiryan ke zuwa a cikin wayan har wucewan shi da zuwan ita halimatu din. Ido ta fitar waje tare da mikewa kafin in shafa addu,ana in juyo gareta lokaci guda naga ta fice dakin da sauri ina mamakin hakan a raina. Na idar na koma saman gado na kwanta da niyar inyi searching din wani abu a system dina naji an turo kofa da karfi na dago kai. Na dago da niyar fada don nasan halimatu ce zatayi min haka sai na gansu tare da anty fadila sun shigo lokaci guda na dago da niyar yiwa halimatu din fada. Sai dai yanayin fuskokin su ya hana inyi magana a lokacin ido kawai na tsura masu har suka karaso inda nake suka zauna. Na dan dago ina fadin anty kin tashi ashe na shiga dazun na sameku kuna barci na barku kada in tayar daku. Na tashi tun dazun ai zainab ta kalli halimatu tana fadin danje falo ki jiramu ko dakin mu sadiya. Ba musu tace tau anty fadin haka yasa na san da magana a bakin ta lokacin na gyara zama ina saurarenta wayana ta miko min tana fadin zainab yaushe wanan abin ya faru haka ? Wani abu anty na karbi wayan ina tunanen abinda ya faru din tace min hakan ki kunna ki ga abinda nake nufi a wayan ki. Da sauri na kunna wayan don ganin abinda take magana a kai har gabana yana faduwa don bansan abinda take magana kanshi ba. Tun zuwan shi ta bayana da harara da sanda kada inji motsin shi har irin abinda ya wakana a tsakanin mu dashi gaba daya wayata tayi recording. Dago kaina nayi a sanyayye tare da fadin na rasa mai nayi wa wa yan nan mutanen suka tseni ganina tare da yaya nina me yasa wanan mutumin ya tsaneni kamar yadda wanan bakin fatan taju shima ya tsaneni hakan yake nuna min yanzu. Wani kallo fadila tayi min tare da fadin kishi sukeyi dake mana ai sune yanzu kamar kishiyoyin ki gareshi ke har ma sunfi kishiya macev illa ai. Saboda me anty nida banda power a gurin yaya da zansa a wani abu ya faru da aikin su don me zasu tsaneni hakan nan don Allah. Ke nan ke har yanzu baki fahinci me sukeyi da mijin ki yake zama dasu ba haka ai dole su tsaneki tunda sun fiki sanin dadin shi ai. Nace sun fini kan anty tunda suna tare dashi kowani lokaci suna kuma aikin suna samun a karkashin shi ko yaushe yasa suke ganin kamar zan tare masu wani abin. Wani irin kallon takaici da tsuki tayi daga inda take zaune ta mike tsaye tana fadin a sannu zaki fahinci abinda yasa suke tsanarki din. Harta fara takawa take fadin wanan video na wayan ki shedane a gareki zan turashi a wayana don wanan ba abin wasa bane idan ya gane kinyi recording din komai a wayan ki. Ko anty na tambaya da dan tsoro a idona ina kallon ta nake fadin kina ganin zai iya min abinda ya fada din anty ?. Tunda ya fada ai zai iya kishiyar kine fa shi don kamar a karkashin shi kuke dukan ku kinga ko komai zai iya maki ai kan yayan naki. Har kwana biyu ina da tsoro da fargaba kan maganan na samu anty fadila ranan da zancen take fadin abinne da wuyan sha,ani zainab. Idan baka iya kama barawo ba ance sai ya kama ka kinga wanan maganan sai nake ganin kawai ki barshi har wani lokaci . Don akwai ranan magana sai dai kiyi hankali dashi kada kibada wani kafan da zai samu ya cutawa rayuwan ki ko kadan. Nayi shiru ina nazari don na kasa fahintar laifin da nayi suke tsanana haka kawai sai na share zancen a raina. Ban yarda wani dalili mai karfi ya hadamu hanya daya dashi ko wani abu kuma yana gidan zaune tare damu yana kuma abinda yaga dama a gidan fiyema da kowa. Don haka zai ta dakawa masu aiki tsawa yana basu umurni har jikin su yana rawa idan ya buga masu tsawa da karfi kan dan kuskure kadan. Ranan yaya ya fita waje a nan ya samu halimatu a zaune waje tana shan iska zama yayi da ita suna hira saiga Nabil din ya fito yana zuwa ya dan dafa kafadan jafar kamar yana sum batar sa. A cikin kalaman hausa halimatu ke fadin wallahi yaya na tsani wanan mutumin tunda yace sai ya halaka yayan mu. Ke sadiya akan me zai halakata kuma meye rusan sa da ita da zai halakata kodai kawai tsanarsa ne yasa kikai masa sheri ? Wallahi yayan ba karya nakeyi ba shi ya fadi hakan idan baka yarda ba ka duba wayan yayan video din nan a ciki idan bata goge shi ba. Hankalin shi ya tashi sosai lokaci guda yaji wani irin tsoro ya kamashi dajin hakan a bakin halimatu ga kuma shedan data fada na hakan. Zubur ya mike ya barta a wurin zaune tabishi da kallo kafin ta mayar da kanta ga abinda takeyi kafin yazo wurinta ya zauna. Ina kwance dakina na kunna kira,a a wayana ina karatu hankalina ya dauku sosai ga karatun naji an turo kofan dakin lokaci guda. Ban damu nasan kowaye ba don a zatona ko halimatu ne ta shigo dakin don haka take min duk lokacin da taga dama a dakin. Saidai hancina ne ya sheda min wanda ya shigo din a lokacin nayi saurin dago kai don in gaskanta shidin ne ya shigo min dakin nake jin kamshin sa. Lokacin har ya kawo bakin sofan da nake kwance ya mika hannu ya dauki wayana dake gefena ya shiga duban abinda yake nema din cikin wayan. Shiru nayi ina sauraren abinda zai fada game da wayan dake hannun shi can naji ya kunna video muryan warning din da Nabil yai min min ne ranan yake tashi. Da wayan a hannun shi ba tare dayai min maganan komai ba ya juya ya fita daga dakin mikewa nayi nabi bayan shi. Na zata part din shi zai nufa sai naga ya nufi hanyar fita daga gidan kai tsaye ban tsaya ba ina biye a bayan shi naja na tsaya da naga ya nufi guiden. Halimatu na zaune ya wuceta ina mamakin hakan kai tsaye sai can inda Nabil yake saman kujera ya zaune ga cup din giyan daga gefen shi. Wellcome dear ya fada yana wani shu,umin murmushi a fuskan shi yana zuwa ya dauke shi da wani irin wawan mari a fuskan shi sai da jini ya fito mai a hanci lokaci guda. Yayi kasa tangal tangal zai fadi ya kara kai mai wani naushi tare da fadin dan iska sister nawa kakewa barazanan kashewa ashe ?. Jackson me nayi maka kake dukana haka akan abinda ban sani ba, make faruwa laifin me nayi ma kuma, wani marin da shaka ya kara mai lokaci guda. Take baki da hancinsa suka fara fitar da jini lokaci guda saida ya dan dade a duke kafin ya dago har lokacin da mamaki a fuskan shi. Shikuma yana tsaye a cikin matsanacin fushi yana kokarin kara mai naushi a fuskan shi. Karan da halimatu ta sake yasa ya shi dan jin wani iri yayi saurin juyawa da sauri ya bar wurin a cikin bacin rai. Part din shi ya nufa yana huci yana cicika ya bugo kofan da karfi ya shige ciki baiko san dani a wurin kofan falon ba. Da sauri na nufi waje don jin karan halimatu danayi daga gefen garden din muka hade da ita zata shigo ciki a tsorace. Hannunta na rike muka shiga ciki direct sai part din su anty fadila na gyaran dakin muka shiga yadda muka shigo a firgice yasa ta gane akwai wani abinda ke faruwa lokacin. Take tambayan mu ya na ganku haka a tsorace wani abune ya faru saidai na zauna na kalli kofa nake fadin . Wallahi anty ina daki kwance ya jafar ya shigo ya dauki wayana baimun magana ba ya duba abinda zai duba ya fita nabi bayan shi sai na hangoshi yana dukan wanan mutumin dakw zaune a gidan nan. Meya hadasu haka ta fada hankali a tashe kafin tace yanzu mijin naki yana ina zainab ? Yana part din shi na bata amsa a takaice babban magana ta fada akwai rikici sosai a gidan nan ashe ? Waima ya hakan ya faru ne wai har yakai su ga hakan don nidai tunane shine wanan video din abinda ya faru tsakanin ku ne ya kawo wanan rikicin haka. Yaya zai san da wanan video tunda ban fada mai komai a kai har yanzu wata kila dai wani abin na daban ne ya faru. Zainab duk yadda akayi ya samu labarin wanan video din a wani wuri sai kuma ta juya inda halimatu take tana fadin sadiya kin fada mai wanan maganan ko ? A yadda yanayin ta ya nuna kawai zai tabbatarwa mutum amsan abinda ake tambayanta da din. Kafin tace a sanyayye ban fada mai ba na dai ce dashi bana son wanan mutumin yace saboda me ? Nake fada mai abinda yaiwa yayan mu yake fadin bai yar, , , ki muna shiru waya aike ki fada mai wanan zancen sadiya ? Tayi wani wiki wiki da ido na fada maki ba komai ne sadiya zata sani ba daya shafi mijin ki a yanzu. Halimatu meyasa kika faye surutu haka waya aikeki fada mai wanan zancen barta ai idan surutu ta iya ai sai an dafa wanan bakin mai yawan surutun tsiya fadila ta fada a dan hasale. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE YAR UWA KADA KI DAUKARWA KANYI NAUYI KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA. BA TARE DA DAUKAN NAUYIN KOWA A KANKI BA DON ALLAH, , , Bayan anty fadila ta karewa halimatu fada taja mata kunne sosai tare da tsoratar da ita illan yawan surutu a gaban kowa haka. Ban kara jin duriyan shi ba har dare muma dari dari muka koma a gidan don abinda ya faru ranan don hankalin mu ya tashi ga baki daya a gidan . Can cikin dare ne sosai ina barci nake jin hayaniyar su sama sama har na kai ga mikewa tsaye don firgitan da nayi saboda a tsorace na kwanta dama. Takawa nayi zuwa kofa har na bude zuwa inda nake jin sautin na tashi sosai na hayaniya a gidan. Muryan ya Jafar naji yana fadi a cikin fada duk son da zan ma ba zai taba kai wanda nakewa yan uwana ba . Tun farko ban yarda ka shiga rayuwa naba saida na fada ma muhunmancin yaran nan a gurina ka yarda amma yau kaine da samun daman warning din ta akaina waya baka wanan matsayin na taba min family na . Me kake tunanen kaika a gidan nan idan baka sani ba yau ka sani yarinyar nan she is my everything in dis world mu ba haka traditional din mu yake ba dole ne namiji ya zauna da mace ko yayane kuwa. Muryan Nabil din naji kadan kadan da alama yasha wahala sosai a wurinyana fadin kayi hakkuri son kane ya rufe min ido har nake jin ban son ganin ta a gidan nan. Amma hakan ba zai sake faruwa ba insha Alllahu nayi ma alkawarin hakan kayi hakkuri kada ka koreni don Allah ya fada a dan marairaice. Kamar ma kuka yake yana magana motdin da naji a bayana ya sa tsoro ya kamani har na tashi kurma ihu sai ji nayi an rufe min baki da hannun maishi. An jani zuwa part dina fadilace ashe itama hayaniyar nasu ya tayar da ita ta fito saida muka shiga dakin take fadin . Ke baki tsoro su fito su sameki a wurin kijawa kanki wani laifi wanan ai ba abin saurarara bane ga mutum don abin babu dadin ji wallahi. Anty a cikin barci naji hayaniyar tasu shiyasa na fito kada fa yaya ya illata abokin nan nasa nake gudu a kaina na karasa a dan maraice. Ya nakasa shi mana ina ruwan ki ke wanan su ta shafa ki koma ki kwanta kuma kiyi kamar bakiji komai ba don kadama ki soma yi mai wanan zancen kashe gari. Tana fadin haka ta fice dakin nabi bayan ta na rufo kofan da sauri na koma bakin gado na zauna ina tunanen irin kalaman da naji suna fada. Karshe dai mikewa nayi daga wurin na nufi ban daki na dauro alwala na fito na fara sallah har tsawon wani lokaci kafin barci ya saceni a gurin danayi sallah barci ya daukeni nan. Wanan ya jawo min makara gashi a ranan zamu koma makaranta hutun mu ya kare late na fita daga gidan sukuku dani jiki ba karfi. Duk zirga zirgan da nayi a school wanan zancen bai fita a zuciyana ba sai faman kulawa nake ina warwala a cikin zuciyana. Sai yamma lis na dawo gidan a gajiye don ba abinda nake bukata a lokacin sai wanka da bukatan hutu bako zancen cin abinci a raina. Gashi kuma magariba ya gabato a lokacin don haka na fada bayi nayi wanka dana fitone na zauna wurin mirrow ina gyaran jikina sai naji an turo kofan dakin nawa. Dan waigawa nayi kadan halimatu ne ta shigo tana fadin yayan mu ashe kin dawo tun dazun nake duban dawowan ki ai. Eh na fada ba tare dana dago kai na kalleta ba a inda take tsaye taci gaba da fadin yau kin dade sosai yayan mu. Eh na fada ina rufe man dana shafa tare da fadin kin san yau dole mu dade ai tunda yau muka koma school din. Tace yaya Jafar ma ya dawo naga ya murda kofan ki yaji a rufe ya sake fita amma bai tambaye ki ba ya fice. Don kamar ma ranshi a bace yake muna gaidashi da kyar ya amsa muna gaisuwan ya fita abinsa bai tsaya kulamu ba. Mikewa nayi a wurin ina fadin halimatu kin faye surutu wallahi ba anty ta fada maki ba komai ne zaki fada ba wai. Tace ta fada min na wuce ta kai tsaye zuwa wurin kayana ina dubawa ta sake fadin yayan kin sani wanan shegen Nabil din yau ya tafi naga ya dauki jakarshi da yamman nan ya bar gidan nan. Wani irin juyowa nayi na harareta kafin in juya naci gaba da neman rigan da zan saka a jikina ba tare da yi mata magana ba. Saidai can kasan zuciyana na cike da zargin maganan data fada min ke nan yaya ya koreshi saboda wanan case din namu dashi ke nan. Riga na saka kafin na tayar da sallah magariba tare da umartan ta ita ma taje tayi sallah yanzu zata fice na kirata na nuna mata kofan bandaki koda ban fadaba ta gane me nake nufi da hakan don haka ta shige simi sim ba tare da wani magana ba. Anan tayi sallah mun idar muna zaune kowa na addua anty fadila ta turo kofan ta shigo tana fadin wai ashe tana nan ? Dama wanan yar rigiman ce ban gani ba nake neman ta don ban san kin dawo gidan ba ma sannu da dawowa ta fada tana kallona. Sannu anty na fada ina shafa addu,a a jikina tare da fadin yau zirga,zirga yai min yawa a gajiye na dawo gidan nan don driver ya dade shima yana jiran na fito. Karatu ko ina sai an daure kafin dadin shi yazowa mutum sai kiga wata rana sai labari insha Allah. Zo muje ki ci abinci ta fada tana kallon halimatu dake zaune a gefena a wurin da mukai sallah din. Idan nayi isha,i zan taso yanzu ta fada tana kallona nima ban tankata ba jin abinda ta fada lokacin. Halimatu ta fara mikewa ta fice ni kuma na tsaya nade kayan danayi sallah don bana barin su a wurin idan nayi sallah. Na nufi kofa ke nan ya shigo dakin ba tare da yai magana ba yake miko min wayana dake hannun shi kaina dago ina karba nake kuma gaidashi lokaci guda. Ya amsa min a yanayin yana a cikin damuwa har lokacin nake fadin a cikin karfin hali yaya yau ko lafiya kake naga yanayin ka a haka ? Tambayan nawa yazo mai a bazata don ba wani dogon zance mukeyi a tsakanin mu ba dama ya dan buda baki da kyar yana fadin . Kawai na gajine daga wurin aiki nake yanzu ina son in watsa ruwane Allah ya taimaka na basa amsa dashi ina bin bayan shi bayan ya juya zai fita. Kusan lokaci daya muka fito daga dakin nawa ina binshi a baya baisan dani ba saida muka kawo kofan part din shi. Mamaki a fuskan shi yake kallo na ya dan kauce na shiga ban tsaya ba na nufi bedroom din shi direct ban dakin na nufa na hada mai ruwan zafi. Na fito daga bandakin naga dakin a hargitse ko ina dan dakin yana bukatan gyara a lokacin don haka na zage na fara gyara yana tsaye da waya a hannun shi yana magana a wayan dakin na shiga gyara a hankali kamar yadda yanayina yake nake aikina. Ya gama ya cire kayan shi ba tare da damuwa da ina dakin ba a lokacin ya shiga ban dakin har na karasa gyaran dakin na fita bai fito ba. Gashi ina aikin ina tunanen irin yadda yaya yake durawa cikin shi ruwan barasa don irin kwalaben dana gani a dakin bazakace shiya durawa cikin shi giyan ba haka. Nikan da mamaki na bar dakin idona yana kokarin zubar da hawaye lokaci guda dan tausayin halin da yake ciki kuma gashi a matsayin mijina yake zama gareni da wanan halin. Na gyara dakin ne dan kawai abinda naji yana fadawa Nabil a dare jiya game da matsayina gareshi daya fada. Gashi yanzu nima ina jin a raina na na fara son kasancewa da mijina tunda dai a zaman mijina dai yake gashi idan yayi wani shiga ya fito kokai waye sai ka kalleshi ka kyasa mai dan kyau da kamala da baiwa irin na kyau da Allah yai mai ga zati da kamala a fuskan shi . Ban nufi dakina ba falo na sauka wurin su fadila na samu sun ci abincin na zauna take tambayana bazakici abincin bane ? A koshe nake na bata amsa da hakan ina kaiwa kwance don aikin dana danyi yanzu jikina ya saba da hutu dan bana aikin komai. Shiyasa da na danyi aiki kadan jikina zai yi ciwo don rashin sabawa da hakan da banyi ba a yanzu. Gashi a kullun wani irin kyau da kwarjini nake karawa sai wani haske da annuri da nake karayi ko yaushe. Makerin budurcina a lokacin yagama fitar min da duk wani sura da akeso daga jikin diya mace su baiyana na cikan budurci sun fito min fili. Ni kaina nasan a yanzu nakai lokacin shiga tsarana idan ana kwatance a fagen kyau da kira na ya mace. Kawai ba zato ba tsamani aka shigo gidan kai tsaye ba sallama ba komai sai ganin katan maza mukayi su uku a kanmu sai wani binmu da kallo sukeyi kamar mazurai. Gashi dan rigan dana saka a jikina na shan iska mai dan hannun shimi ne a jikina sai tsagan dake kasan rigan daga gefe daya. Irin dai rigunan matan su na zuwa wani taro na muhinmin din nan shine lokacin saye a jikina wani purple dashi haka mai laushi. Mun razana da ganin su haka yasa ni mikewa tsaye da sauri sai bin jikina sukeyi da kallo irin na yan iskan turawa din nan. Who are you people ? Na fada a razane a cikin bacin rai sai dayan yace dani we are jackson Friends . Na kallesu a yatsune ina fadin wanan gidan Muslim ne bamu da jackson a gidan nan na basu amsa a cikin gatse. Muryan ya Jafar ne ke saukowa daga sama yake fadin kai ku koma dakin ku yanzu ina da baki a gidan. Juyawa nayi na kallo inda yake fuskan shi a daure tamau kamar bai taba dariya ba a rayuwan shi. Jin abinda ya fada yasa na mayar da fuskana inda suke su duka na bisu da dan harara kafin ma inyi magana har fadila ta fara takawa don barin wurin duk a tsorace take a lokacin da ganin bakin nasa. Dakin sa muka shiga basu ba har yaya din bin mu yayi da kallo saidai shi din kallon don me muka tsaya dasu muna magana haka. Kafin ya juyo don yace dasu su zauna sai ya samu sun mutu a tsaye suna kallon mu ya fara magana a daidai lokacin suke sauke numfashi tare da fadin. Waaawooo wanan ai ba kowa ne zai sameta ya kyaleta ba sai dai kai jakckson da baka son harka da mata sai maza kawai da ka hada both da zaka more a wurin wanan yarinyar gaskiya. Wani irin mugun kallo ya watsa masu yana kaiwa zaune tare da jawo remote din tv dake aiki da muka bari a wurin yana aiki. Ya juyo ya kallo su lokaci sun kai zaune daga tsayen da suke suna shakiyanci a tsakanin su fuska daure ya kallesu yana fadin meya kawosu wurin shi. A cikin dariya dayan dayafi zama shakiyi a cikin su yake fadin ai da ganin mu gidan ka kasan maganan daya kawo mu tunda kaki daukan wayan mu tun dazun. Don me zakaiwa sabon guy din ka haka jackson kana son ka zama mai kamawa da sakewane ko yaushe. Gaka da sa,an samun gayu irin da kowa ke son ya samu amma sai ka dinga sakacida wanan daman naka. Kodai yanzu ka fara canza ra,ayine ka fara sharing din both side samun wanan zukekiyar yarinyar a gidan ka ? Don ba kowa zai zauna da wanan bai morewa rayuwan shi ni,imar dake jikin ta ba na mata koda kuwa baya jin dadin hakan a zuciyar shi. Stop it philis, She is my wife you can't talk haka a kanta kamar yadda kaima kasan ba zan taba fadin wani zancen banza ga family din ka ba ya fada yana mikewa tsaye. Suma din mikewa sukayi don sun san shi sarai zai iya ficewa ya barsu wajen hakan ba karamin aikin shi bane wanan. Da sauri dayan ke fadin haba man kada kai fushi damu mana mun san ba,a kyauta da hakan don kowan mu nan baya wasa da sister shi ko wata yar uwansa. Jin hakan yasa ya koma ya zauna yana huci tare da kallon su daya bayan daya kafin ya sauke ajiyan zuciya. Ya hade hannayen shi wuri daya yana sauraren abinda zasu fada dayan dayake abokin shi na sosai yace man dazun wanan sabon guy din naka ya samemu da wani zance . Mun kira wayan ka yafi a kirga kaki ka daga yasa mukazo har gidan nan don mu baka hakkuri kan abinda yai maka don bai boye muna komai daya faru ba a tsakanin shi da sister din ka. Wani irin kallo ya dago kai da idanun shi da sukai masa ja ya jefesu dashi kafin yace masu ku barshi kawai bana son kowa a kusa dani a yanzu. Kada kace hakan jackson kasan baza mu iya daina wana harkan ba a yanzu don haka kayi hakkuri da wanan guy din don rashin sa gareka babban hasarane a wurin ka. Don akwai masu son su kasance dashi na mika kudi masu yawa aka bakashi don haka kada kayi sakacin dazai kubce maka. Let him go ya fada da karfi tare da mikewa tsaye kallon juna sukayi suma suna mikewa suna kallon shi . Kada kaiwa kanka sakaci da wanan guy din don kowa sonshi yake a garin nan ya juyo ya kallesu yasa kai ya fice daga gidan. Basu fita ba saida biyun suka juyo suka kalli dakin dana shiga kafin subi bayan shi shida abokin shi da sauri dama sun fi shakuwa a tsakanin su. Ban yarda na fito dakin ba sai da zan kwanta na dauki drink da snack na shige dakina dashi sai bayan na gama abinda nakeyi nasha na kwanta. Washe gari nayi samakon fita school acan ma na bata lokaci sai yamma na dawo gidan. Bayan sati da yin hakan monday na shiga school a dan makare tun daga nesa nake jin hayaniya na tashi department di mu na hanzarta na shiga. Abin mamaki na tarasa a wurin wai ana taya wasu ma,aurata murnan aure a tsakanin su . Dan murmushi nayi na gefen fuska na ratsa mutane ina neman wurin zama daga can baya na samu wuri na zauna a wuri daya. Wata na samu irin yan ra,ayin rikau din nan na addinin buda su na kasan jin hayaniyar yai yawa yasa na dan juya wurin ta duk daba wani shiri mukeyi a tsakanin mu ba ina tambayan ta ina ango da amarya don ni duk maza nagani a wurin gaba dayan su babu amaren. Saida ta tabe baki take fadin wai a tsakanin sune sukai auren ai ga ango nan da bakin kaya amaryan kuma da fararen kaya a jikin ta. Na dan gyara zama tare da kallon ta da kyau ina fadin kai shirme ke nan ina aka taba aure tsakanin namiji da namiji kuma in ba shirme ba ? Sunayi ta fada tana runtse idanuwan ta a daidai lokacin da ake bi ana raba alawa bayan dogon adduan samun zaman lafiya da akai masu a tsakanin su. Malami ya shigo aka fara lectures ni dai zaune nake tunane ranan nayi kala kala a raina kafin a fito don yin break. Wanan matar mai addinin buda na sama take kara wayar min dakai game da auren jinsi da akeyi yanzu a tsakanin maza da maza ko mata da mata. Driver na kira ya mayar dani gida don yau banjin za a karasa lectures din dani don irin rudanin da zuciyana ya shiga tun bayan bayanin da naji daga wanan matar. Gidan na shigo suku suku dani gaisawa kawao nayi da fadila na wuce zuwa dakina jiki ba kwari . Don gaba daya zuciyana da kwakwalwana sun fara kawo min wami zargi akan ya jafar din. Sai nake tariyo wasu abubuwa can kasan zuciyana wanda nake ganin zargine kawai nakeyi alokacin ba gaskiya zuciyar nawa ke fada min. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN NAN NA KUDINE KIWA ALLAH KI BIYA KAFIN KI KARANTA DON FITA HAKKIN JUNA BA TARE DA SHIGA HAKKIN JUNA BA. Washegari na kasa tashi don zazzabin daya rufeni lokaci guda saboda tunane daya tsaya akan lalai akwau ayan tambaya akan ya Jafar da wa yan nan mazan dake zaraya a dakin shi. Ba tare da wani shamaki ko tsoro ba wanda koni matar shi banda halin yin abinda sukeyi a gidan kai tsaye sai tare da umurnin shi. Wanan dogon tunanen ne yasa na fashe da kuka lokaci guda ba tare dana sanda zuwan shiba a lokacin. Har yakai zazzabi ya sauka min hakana dunkule ni daya a daki ina rawan dari gashi na kasa tashi in kashe AC dake aiki a dakin. Washegarin ma da kyat na iya tashi nayi sallah na koma na nade saman gado har saida halimatu ta shirya zata tafi ta shigo sallamana ta sameni a hakan. Taje ta fadawa fadila suka dawo tare dakin tare da ita da kyat na tashi nasha tea din data hado min a lokacin. Da kyat na samu na kurba sau biyu na koma na kwanta ban dade da kwanciya ba wani irin amai yazo min lokaci guda. Da gudu na mike zuwa bandaki saidai kafin nakai bandakin har na sake aman ko sai da kyat na karasa ciki. Hankalin fadila ya tashi sosai don halimatu ta rigada ta wuce kada ta makara bus ya wuce yasa aka turata ta tafi ba don taso tafiyan ba a lokacin. Fadilace ta gyara dakin har ban dakin ta saka kamshi tare da bude dakin don iska ya shigo haka yasa shi sanin cewa ina gidan ban fita ba. Don ya fito a cikin shirin shi yana sauri har ya zauda kofan part din nawa sai kuma ya dawo baya da mamakin ganin kofan nawa a bude . Hakan ya sanar dashi ban fita zuwa school ba ranan ke nan ya shigo cikin dakin tun daga nisa ya hangoni saman gado a kwance ina rawan dari. Lokacin fadila ta fita zuwa dakin ta don ta dauko min magani da tazo dashi irin namu na Nigeria da muke sha a can gida. Zainab ya fada a dan rude yaji ban tankashi ba yasa yakai hannu ya kware bargon da nake rufe dashi ya kai hannun shi a hankali kamar mai tsorona yana taba jikina daya gama gashewa lokaci guda da zafi radau. What ya fada a razane a cikin dan rudewa tare da fadin baki da lafiya kike kwance haka zainab baki fadi an kaiki asibiti ba ? Nan ma ba amsa sai kara lefewa da nayi don kware bargon dayayi yasa na kara jin sanyi na shigana lokaci guda. Fadila ce ta shigo da saurin ta dakin dauke da magani cikin karamin plate sai goran ruwa da cup a hannun ta daya. Tana ganin shi ta kadu da sauri zata juya ta bar dakin sai ya dago kai yana fadin meye wanan kika dauko ? Paracetamol ne da maganin amai na dauko zan bata tasha don jikinta da yai zafi ko zai taimaka mata ya sauka. No kada ki bata barta na kaita asibiti yanzu zaifi waina yaya akayine ina gida baku fada min bata da lafiya har haka ba sosai. Sir nima yanzune Sadiya ke fada min tazo sallaman ta zata tafi ta sameta kwance haka a dakin zazzabi ya rufeta. Mayar da kanshi inda nake yayi ya dan tsura min ido kadan kafin yace dani tashi ki shiya muje asibiti yanzu. Kamar banji me yake fada ba don duk da halin ciwon da nake ciki hakan bai hanani jin wani irin takaicin shi tare da tsanarshi ba a kasan zuciyana. Kara maimaita maganan shi yayi da fadin tashi ki taimaka mata ta shirya ina waje ina jiran ku. Da karfi na dago a hasale ina fadin wallahi ba zan tafi ba na kwanmace na mutu a hakan da ka kaini asibiti. Mene yace da mamaki yana kallon yadda nake magana da kyat a cikin karfin hali na koma na kwanta ina kaduwa saboda sanyin da nakeji a lokacin. Ke wani irin sakarci ne wanan kije asibiti zaki tsaya kinawa mutane gardama haka ? Ba za a tafin ba na kara fada a yadda nake kwance ina kaduwa da kyar kake jin magana na idan inayi. Wai meke damuwantane ya juya yana tambayan fadila ta girgiza kai tare da fadin nima haka na ganta yau sir ban san meke damunta ba. Juyawa yayi ya fita dakin fadila ta matso kaina tana fadin tashi kisha wanan din mu gani ko zai taimaka maki kafin ku tafi. Sai lokacin nayi magana ina fadin bazan tafi ba wallahi anty na tsani yaya jafar bana son ganin shi don, , , . Wani irin yun kurin amaine yazo min lokaci guda ya hanani karasa zancen danake son fada a lokacin. Da kyar na mike na shiga ban daki wanan karon yellow din amai nake alaman dai fever mai karfi ya kama jikina lokaci guda ko. Da kyar da bin bango na samu na fito daga ban dakin na koma na samu wuri na kwanta ina mayar da nunfashi da kyar tare da lumshe idona ina jin wani irin takaicin kasan zuciyana. Ba barci ne ya daukeni ba amma haka na lafe kamar mai barci a lokacin don yadda nake jin kaina na saramin lokaci guda. Haka dai nake kwance tana tsaye a kaina cikin damuwa sai can kamar bayan awa guda naji ya sake shigowa dakin. Wanan karon tare da wani likita suke shida kanshi ya hau gadon ya dagoni na bude idanuna da sukai ja don bacin rai ga ciwo na sauke a kasan zuciyana. Likitan ne ke fadin meya sameki pretty girl tare da juyawa ya tambaye shi is she your sister ? Yace dashi yes yace yaushe na fara ciwo haka yace da dare kamar yasan hakan sai likitan ya ciro kayan aikin shi ya shiga aunani na dan lokaci guda tare da yi min tambayoyi ina bashi amsa da kyar. Allura yai min da magani nasha sai barci na dauki lokaci mai tsawo ina barci kafin in tashi ina neman abinda zanci ga zufa yana fetso min a jikina. Tea nasha sai naji dan karfin jikina na tashi nayi sallah azahar kasa tashi nayi sai kuka don tunanen abinda ya tsaya min a rai. Fadila ce ta turo kofa ta samu ina kuka ni kadai a cikin dakin da sauri ta karaso inda nake tana fadin zainab lafiya wai meke faruwa ne dake haka ? Alama ya nuna akwai wani abinda ke damun ki a zuciyar ki kike boyewa kai na dago a hankali na kalleta tare da fadin. Ba komai anty fadila na fada ina mayar da kaina wasu hawaye masu zafi suna fito min ido kawai ta tsura min kafin ta sauke ajiyan zuciya ta juya ta fita. Bata dade ba ta dawo dauke da abinci ba tare da tayi magana ba ta aje a gaba kafin ta samu wuri takai zaune kasa a kusa dani. Zainab kome ke damun ki don Allah ki daure kici abinci kada wani ciwo kuma ya shige ki a yanzu don nasan tun jiya baki ci komai a cikin ki ba. Kai na dago da niyar yin magana sai ta dakatar dani da hannu tana fadin don Allah ki daure zainab kome meye da baya mayi zancen a tsanake dake. Jin haka yasa na kai hannu a hankali na jawo abincin na fara ci a hankali badon yai min dadi a baki ba duk da itace ta dafa don irin abincin mune na gani. Na dan tsakura na mayar na rufe tare da daukan ruwa na kurba sai can na sauke ajiyan zuciya ina fadin na tsani yaya jafar anty fadila. Subbahanallahi zainab meye maki haka da har zaki tsaneshi irin haka lokaci guda. Ban iya magana ba illa fadawa jikin ta danayi ina sheshekan kuka har nayi nagaji na kyale don kaina tayi shitu tana kallona kawai tare da nazarina. Ki daure ki tashi a kasan nan kada sayin kasan ya kamaki ki koma saman gado ta fada tare da mikewa tana dauke kayan abincin dana ci. Mikewa nayi kamar yadda ta ban shawara na koma saman gado na kwanta a haka wani barcin ya daukeni don barcine a idona saboda rashin samun barcin dare da banyi ba. Wasa wasa kwana biyu nayi a kwance ina jinya idan ya shigo dibani bana yarda ko in kalli inda yake haka kuma yayi maganan shi ya gaji bana tankshi haka zai fita daga dakin. Akarshe dai koya fahinci wani abune baya shigowa sai idan ya dawo daga wurin aiki zai lekoni ya yai min sannu a tsatsaye ya fice. Har naji sauki na fara fita school kamar yadda na saba saidai duk wanda yasan ni yasan na rame sosai a lokacin. Don nasawa raina tsanan komai na yaya a gidan ko abinci banda yadda zaiyi ne da ba zanci abincin gidan shi ba yadda nakeji tsanarshi a raina. Ashe wanan matar yar gargajiyan kasan kwana biyu da banzo ba ta damu da rashin ganina kuma bata san wani da nake hurda dashi ba a school din balle ta tambayeshi ni. Bayan mun fito daga lectures ne muna break ta sameni zaune ta gaidani itama ta samu wuri ta zauna tana tambayana dalilin rashin ganina kwana biyu da batatyi ba. Nake fada mata tun ranan nan da muka rabu banda lafiya ina gida kwance yasa ban shigo ba tayi min sannu da jiki na amsa da godiya. Muna nan wurin zaune don na fahinci itama irinane bata son hayaniya itace ta dauko hiran lectures din da akayi bana nan har ta ban handout din ta na kofa don karatu tare dayi min bayani. Saidai taga hankallon ya dauke ga kallon wasu mutum biyu da suka wuce mu suna rugume da juna yasa ta kura min ido na dan lokaci tana nazarina. Dafani naji tayi na waigo da sauri take fadin lalai ni bakuwace a wanan kasan wanan ai yanzu ba komai bane a nan don yanzu basa ko boyon wanan abin. Gashi kuma babu wani addinin daya yarda da wanan dabi,an na auren jinsi suna dai yine don ko wani addini suna da tarihin mutanen farko da aka halaka kan wanan dabi,an. Dan murmushin yake nayi tare da fadin ni abin ya daure min kaine ai tun ranan da tayi min wanan bayanin ina mamakin yadda mutum zai auri dan uwan shi namiji haka ? Me mutum zai gane ga hakan nan dai ta shiga bani musalan abubuwa da dama wanda ban sani ba da ace tasan halin da nake ciki da ta bar duk wani bayanin da take min a lokacin don yadda zuciyana yake tafasa. Dala dala tayi min bayanin su a gurguje tare da irun alamoninsu da yadda sukan fara approching din mutum har su ja ra,ayin shi ga abin. Haka na koma gida bayan mun rabu a cikin wani sabon tashin hankali har yakai na kasa rike abin a zuciyana. A weekend din na samu anty fadila da zancen a dakin su ina kuka nake mata bayani ban boye mata ba nace na fara zargin ko yaya Jafar shima wanan akidan yakeyi da yake yawan mu,amula da maza yan uwan shi a daki daya. Kai haba zainab yaya zaki saurin zargin mijin ki da wanan dabi,an marakyau haka har ma idan kina zargin sane ai zaki iya saka ido ki fahinci wasu halaiya nasa harki gano hakan . Amma baki yankewa kanki hukuncin da baki sheda ba irin hakan da sauri don kinga yanzu kece dakin fada mutane zasuyi saurin yarda da maganan ki. Wanan zancen da mukayi yasa na tsiro gyaran dakin yaya da kaina a wanan lokacin duk naci karo da wani abinda ba daidai ba a dakin zan kwashe in zubar dashi . Haka kuma giyan shi har yakai yanzu ya boye abinsa a inda ban sani ba sai ga wautana na dauka ya barsha ne a yanzu. Sai ranan ko yaya akayi ya shigo dashi dakin ban sani ba na gasu a falo ya aje su a cikin leda washegari na shiga gyara na gansu na kwashe duk na farfasa su. Wanan abinda nayine ya kawo muna matsala a tsakanin mu karo na farko a zamana dashi don ina zaune a daki da dare ina karatu ya shigo min dakin kamar mahaukacin zaki yana fadin. Ke ina abinda kika daukan min a dakina suke kamar ba zan dago kainba saida ya kara tambayane. Na dago kai na dan kalleshi nace wani abune ke nan nidai nasan abin haramun na gani a dakin na dauke na zubar. Ke kada ki kawo min maganan banza a nan tun kan a haifeki na haddace alkurni balle ke yanzu kizo min da wani maganan banzaki can . Indai gyaran ke nan da kike min daga yau sai yau idan bani na bukaci da ki shiga min part dina ba. Ba tare dajin komai ba a raina don duk wani tsoron shi ko nauyi ya kawo a zuciyana nasa don haka na kalleshi ido da ido nace yafi min nono fari yaya don dama don Allah nake maka. Idan badon Allah me zai kaini gyaran dakin da Allah kasa na fushi da mai shi don abin haramun din da ake aikatawa a ciki. Har ya juya ya waigo da wani irin karfi tare da fadin me kike nufi da wanan zancen naki kina nufin dakin nawa haramun ne ko me ? Ba dakin ba yaya kai kanka haramun ne don shi kake aikatawa ga shan giya ga babban abin da Allah ya haramta da kakeyi a dakin. A cikin wani irin tafiya ya fara takowa zuwa inda nake zaune ina karatun daya sameni a dakin banji tsoron shi ba ko kadan ban kuma motsa ba daga yadda nake zaune. Hannun shi ya mika kamar zai cafkeni ban san abinda ya tuna ba kuma ya fasa tare da dan kafeni da ido na dan wani lokaci. Nace idan kayiwa kowa wayau yaya kana ganin zakaiwa Allah ne yau gashi har nayi wayau gane abinda kake boyewa mutane na halin ka. Ka tuba ka koma ga Allah tum kan lokaci ya kure maka zaifi na yarda ni yarinyace ban san komai don ka yaudareni ka yaudari iyayyena. Amma yanzu idan na zauna da kai da wanan halin naka nina jawa kaina idan wani abu ya sameni. Don haka yaya na rokeka ka mayar damu gurin iyayyen mu don Allah tun kan masifan ka ya kai ga shafan mu. Gara in zauna a cikin talaucin gidan mu da in zauna a cikin wanan sabon Allah tare dakai nayi ma alkawarin in dai nice babu mai jin wanan zancen a bakina har duniya ta tashi. Na fadi hakan don kawai ya kyalemu mu koma Nigeria don yakai yanzu tsoron lamari shi nakeyi ga baki daya. Wani irin kallo yai min ga idanun shi sun kara rinewa lokaci guda ga baki daya halittanshi ma ya sauya lokaci guda . Naga ya juya ya fice yabar dakin da sauri wani irin kuka na fashe dashi lokaci guda ina mulmula saman gado kamar mai iska. Tunda wanan abin ya faru tsakanin mu ban kara sashi a idanuna ba har tsawon sati biyu gashi nasawa kaina damuwa da tsoro duk nabi na lalace lokaci guda. Ashe tafiya yayi bamu sani ba don bani kadai ce na shiga damuwan rashin ganin sa ba kowa ma a gidan ya damu da hakan. Ranan sai gashi kwaran ya dawo ana shigo da kayan sa gidan muna zaune a falo suke mashi sannu da zuwa da kyat na iya budan bakina na gaidashi. Ya amsa shima a dakile ya shige part din shi kai tsaye sai daga baya aka shiga mai da kayan shi part din shi. Har kwana biyu da dawowan shi babu wani sakewa a tare dashi nima ban bi ta kansa ba do yanzu banda damuwa a gida ga anty fadila tare damu. Can kuma school ga kawata da yanzu muka saba da ita sosai muna kula junan mu sosai da ita kamar mun dade da sabawa . Idan ma ina da damuwa bai wuce son komawa gida Nigeria dana sawa kaina a yanzu don hankali ga baki daya ya koma gida. Yakai kamar sati daya da dawowa sai gashi dakina da yamma ya shigo ina zaune ina waya da Amaya kawata ya shigo. Wuri ya samu ya zauna ganin haka nima na natsu ga sauraren shi do jin abinda zai fada a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA ALLAH YAI MUNA DAUKI YA KAWO KARSHEN WANAN TASHIN HANKALIN DAYA ADDABI AREWA DAMA SAURAN KASASHEN MUSULMI NA DUNIYA ALLAHUMA AMIN 👏🏻👏🏻👏🏻 DON ALLAH YAN UWA KUYI HAKKURI KU KAI ZUCIYA NISA KAN SHIGA HAKKIN WANI KI DAURE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALLAMA ALLAH YASA MUFI KARFIN ZUCIYAR MU AMIN, , , , , , Juyuwa nayi na kalleshi a hankali yana zaune kamar mai tunane ya harde hannayen shi a guri daya kanshi na kasa sade. Banji tausayin shi ba sam ko kadan a raina saboda yadda nakejin shi a raina illa shirun da nima nayi na dan lokaci ina sauren shi. Gyaran murya kafin ya fara magana murya ciki ciki naji ya furta kalman sunana da zaina....b . Ban dago kai na kalleshi ba saidai yadda na natsu yasan ina sauraren shi a lokacin maganane kawai banyi ba lokacin . Magana nake son muyi dake a tsanake dan wanan zancen na ranan ya daure min kai a ranan saboda ban fahinci abinda zancen ki ke nufi ba. Don naji kina kokarin kafirtani yasa na fice na bar dakin nan ko kuwa kina tsamanin don har yau ban dubeki a matsayin mace ba kike dauka wani abu nakeyi na daban. Da farko naji tsoro da kunya don jin abinda ya fada sai dai a cikin karfin hali nace yanzu fa yaya na wuce daukan da kake min na yar kauye kuma diyan talakawa. Wani kallo yai min don jin abinda na fada hawaye na zuba min a idanuwana shar shar naci gaba da fadin kaji tsoron Allah yaya . Kada mutuwa ya riskeka acikin sabon Allah kai musulmine kuma musulunci ya haifeka gaba da baya yaya. Kasan irin hukuncin da Allah ya tanadarwa wannan abin saboda wanan ubangiji ya kifar da mutanen wani zamani mai tsawo kana sane da ukuban kabari ga bawa mai sabawa fadan Allah. Yaya bayan wanan yau idan mahaifiyar ka ko wani yaji wanan ko daga kasan ka na haihuwa aji abin ashan da kakeyi a nan yaya da wani ido zaka kallesu. Wani dauka kake son duniya tayiwa duk ahalin ka saboda kai yau idan Allah ya baka zuria nan gaba a duniya yaya duniya zata daukesu yaya ? Kasa cigaba da maganan nayi dan sheshekan kukan dazo min bazan iya furta komai a bakina ba ga lokacin. Shiru yayi yana sauraren sautin kukan nawa yana dan girgiza kai a hankali tare da dan buga hannayen shi cikin juna. Bai hanani kukana ba shima din a lokacin na zuciya yake yi don ya gama fahinta na ganeshi baro barone kawai ban fito fili na fada mai hakan ba. Lalai mutum abin tsorone tunda har wanan abar da nake rainawa ta san yadda zata fahinci komai game dani . Duk taka tsantsan din da nakeyi wai ace yau yarinyar nan sai data gano hakan ina ga mami idan har labarin nan yaje mata sai yaya ke nan. Idanuwan shi ya runtse a hankali yana jin wani abu yana tokaro mashi kan zuciyarshi lokaci guda. Cikin muryan kukan naci gaba da fadin ina rokon ka katai maka muna ka mayar damu gida wurin iyayyen mu don Allah. Koda kuwa ta hanyan wani mumunan kazafine ko sheri zaka lakaka min ta hanyar da duniya ni zasu tsaneni na yarda da hakan yaya matukar zaka mayar damu hannun iyayyen mu din Allah. Nayi ma alkawari har abada ba maijin wanan zancen daga bakina don ba abin alheri bane da zan fada har wani yai ma kallo dashi a duniya. Yau nima laifin ka yaya ya shafeni don abinda ya taba mutuncin gidan ku a duniya ya taba rayuwana nima don alherin ku gareni ba abin mantawa bane. Nasan kayi nisa a cikin wanan akidar fitan ka a yanzu sai Allah daya halicce ka yaya zan taya ka da addu,a Allah ya rabaka da wanan halin ga baki daya dakai da sauran yan uwa musulmai da suka bace suka makance a wurin sabawa Allah da munanan aiyukan da ubangijin mu yafi tsana ga bawa. Yaya yau idan mahaifiyar ka ta samu wanan labarin da wani ido zaka iya kallonta a yadda mami take da mutunci da kima a idon mutane. Ya isheki zainab ya fada da karfi a cikin wani irin yanayi na bacin rai yana min kallon ido da ido daga inda yake zaune nayi kasa da kaina kawai don ba zan iya jurewa kallon shi ba ko kadan. Zaki iya fada min komai a yanzu amma kada ki yarda ki jefa sunan mami a wanan zancen wurin nan . Zan iya sauraren don abinda zaki fada banda wanda kike fada min game da mami din yanzu wanan tsakanina ne da mahaifiyana. Ni mutum ne mai yancin kansa kamar kowa ina da daman da zanyi wa raina duk abinda ya dace dani a rayuwana. Ki sani ban auro ki don ki zaunar dani kina min guntun wa,azin ki ba a nan don tun kan ki sanda hakan na sani. Kasa daurewa nayi don jin abinda ya fada na dago da sauri ina fadin yaya ka sani kake aikata abinda Allah ya la,aci maishi. Ina zaka da wanan nauyin mai yawa a kanka ka tuba ma Allah shi mai karban tuban bawan sa idan har bawa zai tuba tubana tsakani da Allah har abada. Nidai ina maka adduan Allah ya taroka yasa ka gane gaskiya ka daina wanan halin kafin mutuncin ka da kimar ka ya zube a idon duniya don Allah ba zai taba boyeka ba ga abinda kakeyi yanzu. Saurarena yake yana mamaki yadda nake fitar da lafazi kamar wata tsohuwar mace a zuciyar shi. Ki ci gaba da min adduan tunda har kin gane abinda nakeyi din mara kyau ya fada yana mikewa amma gida ba zan mayar daku gida ba kamar yadda kika bukata. Bayan shi nabi da kallo lokacin da yake fita dakin sai dai a yanzu ba kamar yadda ya shigo yake tafiya ba. Don yanzu a dan hasale yake takawa ya fice daga dakin rayuwan shi da hankalin shi a tashe don bai taba zaton zan gane hakan gareshi ba da sauri. A tunanen shi wayau na da hankalina ba zai kai har in fahinci abinda yake aikatawa ba haka da wuri. Sai gashi a bazata na fito mai a fili dana nasan da abinda yake ciki wanda bai taba kawo hakan a ranshi ba. Mace mace ka barta komai kankantar ta ta wuce yadda mutum yake daukatan watau don wanan yarinyar yar kauye da yake gani gidahuma har ta iya zaunar da mutum kamarsa tana jero mashi zance haka. Part din shi ya shiga ya mayar da kofan garam don ba mai kara bane kofan da kowa na gidan yaji sautin bugawan da yayi a lokacin. Oho god ya fada yana sasauta kwalan rigan shi sai zufa ke sharto mashi ta ko ina a jikin shi lokaci guda. Zaune yakai ya mike kafa tare da dafe goshin shi ga wayan shi na kara ana kiran shi ya kasa dauka a lokacin. Don yadda yake jin kansa na juya masa ya dade bai sha cocaine a rayuwan shi ba badon baidashi ba sai ranan yaji shi kawai yake son sha a lokacin. Mikewa yayi ba tare daya tsaya kula wayan shi dake ruri ba a lokacin ya nufi inda yake aje kayan aikin shi ya dauko ya dawo tare da jawo dan table din dake gaban shi. Ya zuba a gurguje ya fara shaka yana daga kai kamar kadangare kafin ya mike zuwa kitchen din dake part din ya nufi wurin fridge ya bude ya dauko kankara da cup ya saka tare da dauko kwalban giyan shi ya dawo ya zauna. Bai daga ba sai da yayi tatil ko dagawa bai iya yi a wurin nan ya zube babu shirmen da baiyi ba a dakin shi kadai a cikin dakin. Kamar zai buga yake jin kanshi a lokacin ya manta da inda yake balle maganan dake damun shi har safe mai gyaran gida ya shiga ya sameshi kaca kaca a dakin shine yazo ya kirani hankali tashe. Ranan nayi kuka kamar Allah ya aiko ni karshe dai haka na daure na kamashi da kaina na kaishi bandaki na tubeshi haka kawai dabara yazo min in watsa mai ruwa masu sanyi a jikin shi . Ruwan na sauka a jikin shi yayi firgigit tare da ajiyan zuciya wanan katon ma kukan baizo min ba juyawa nayi na fita daga bandakin. Dakin nasa na fara gyarawa kafin na koma falo na gyaro na na saka kamshi a ko ina saboda amai da sauran najasan daya sake. Na koma dakin zaune na sameshi da tawul daure a kugun shi ya zauna ya hade hannayen shi wuri daya tare da dukar da kanshi kasa kamar mai tunane. Ina ganin shi haka a zaune nayi saurin juyawa zan fice dakin sunana naji ya ambata har lokacin mayer bata gama sake shi ba nake gani. Kizo ki dauko min kaya na saka a jikina ya fada kanshi yana duke bai dago ba dan jin nayi kafin na juya na nufi wurin kayan nasa na bude. Rasa wanda zan dauka nayi dayake nasan kayan nasa farare ya faye sakawa na dauko wani wando fari da riga shirt fara na kawo mai. Under fa ya fada bayan na aje mai kayan a gefen shi na juya na dauko singlet da box dake jere a wurin. Ina ajewa na fice dakin ban tsaya ba daki na koma na haye gado dama na shirya zan tafi school ne yanzu kuma na makara da zuwa school din. Nayi kuka har na gaji kusan awa daya ya leko part din nawa ya sameni a kwance na kifa ciki yasan ba barci nakeyi ba a lokacin. Yau ba zaki shiga school ba ke nan ya fada yana tsaye sai kamshi ke tashi daga jikin shi kamar bashi bane dazun a cikin najasa hakanan yanzu ko yasha wanka yana kamshi. Ido na dago da sukai min ja dan kuka ya gani yayi kamar bai gani ba wani kallo na watsa mai ya juya da sauri ya fita daga dakin. Nan ya barni kwance na dasa sabon kuka a fili tare da dinbin nadama da dana sani yafi dubu ina blaming din kaina da iyayyena. Nayi sati bana yarda mu hadu dashi a gidan idan na dawo ina dakina ko wurin su fadila na daina shiga ga damuwa da yai min yawa. Da ka ganni zaka gane hakan saboda ya nayina daya nuna hakan lokaci guda Fadila tayi tambayan duniya nace babu komai karatu ne kawai yai zafi ya sakani komawa hakan. Kyaleni tayi ba don ta yarda ba bata kara tanka wanan maganan ba ta saka min ido amma a ranta tasan akwai abinda ke damuna dana koma hakan lokaci guda. Tsakanina dashi kan kamar sarakai muka koma don shi baison mu hadu ni kuma ban son gani shi sam don na tsaneshi har kasan zuciyana a yanzu. Ranan na manta da wayana a dakin fadila don haka wayan a can ya kwana dakin nasu tun da asuba kafin nayi sallah asuba na bude daki na fito don in buga masu su bude saboda maya zata turo min wano sako a wayan tunda dare nake jira. Ina budan kofa mukai kicibis da wasu samari biyu suna fitowa daga part din yaya ko shigan su ma abin tsorone dan da gani su tantiran matasan kasan ne. Wani irin kallo suka bimu dashi sai da tsoro ya kamani don ganin su wayan da ban dauko ba ke nan na koma daki da sauri na rufe wasu hawaye suna zuba a idona. Sai zance nake kamar mahaukaciya a daki ni kadai da sauri na mike tsaye dan karamin jakkana dake aje tun zuwan mu kasan. Kaya nashiga hadawa lokaci guda a gurguje na fito da dan troler dina zuwa part din su fadila na buga masu kofa suka bude. Anty ku dauko kayan ku mu bar gidan nan tun kan gari ya waye muna a nan gidan kallon mamaki fadila ke min. Saida na kai karshen magana take fadin kanki daya kuwa zainab ina kike nufin mu nufa da wanan safiyan haka yanzu. Duk inda muka samu na bata amsa ina fadin ba zan zauna gidan wanan mai sabon Allah ba kuma. Kiyi tunane zainab nan fa ba kasan mu bane muna a garin mutanene yanzu ina kike son mu tafi yanzu idan mun bar gidan nan. Hannun halimatu na jawo tare da daukan akwatina ina faman ja muka fice a gidan tana tsaye tana kallon mu da mamaki a fuskanta. Ganin da gaske mukeyi yasa ta nufi part din yaya jafar dake kwance shame shame saman gadon shi ko sallah safe baiyi ba ta shiga dana mashi door bell babu kakautawa lokaci guda. Tsuki yaja yana mamakin waye wanan da safe haka yake damun sa dan nawan da yayi kafin ya bude kofar yasa har muka samu taxi muka shiga muka bar unguwan. Yana budewa tana tsaye a cikin damuwa tace sir kazo ga madam can da sister ta zasu bar gidab nan sun dauki bag din kayan su sun fita. What ya fada tare da kallon jikin shi daga shi sai bathrobe din dake jikin shi daya dauko yasa da zai fito kofan. A hakan ya fito abinda bai taba yi ba tun kan ya fito yake fada da fadila don me bata fada mai ba da wuri ta bari muka fita daga gidan. Babu kowa wajen gashi ba ranan aiki bane sai yan tsiraru mutane dake zirga zirga a unguwan. Kai ya dafe da hannu daya tare da fadin shit yarinyar nan tana son caza min kai a garin nan how come zata bar gidan nan ya fada a fili. Sai kuma ya juya wurin fadila ya hauta da fada don me zata bari har mu fita bata sanar mashi ba yanzu gashi mun doshi wani wajen da ba,a sani ba. Nan ya barta ya juya cikin gidan a gurguje ya dauki key din mota da kanshi yai driving ya rasa inda zai tafi sai tafiya yake a unguwa yana dube dube ko zai ganmu. Muko mai taxi ya tambaye mu wani wurin shakatawa da muke yawan zuwa nace ya kaimu lokacin ya ajemu na biyashi kudin shi. Sai lokacin na fara wiki wiki da idanu na rasa abinda zanyi a lokacin abu na farko shine na fara tambayan ko halimatu zata ci wani abu don nasanta bata wasa da ciki ta ko kadan ita. Wurin masu hada irin abincin su a bakin titi din nan naje aka hada mata taliya da tarkacen su don ita tana iya cin abinci su yanzu. Wuri muka samu muka zauna taci saida ta koshi niko ina ta faman tunane a raina na inda zamu sai dabaran zuwa hotel ya fado min a raina. Tana gamawa muka bar wurin don kallon da ake muna yayi yawa a lokacin munyi sa,a mun samu hotel mai dan saukin kudi muka kama bayan na nuna masu ID card dina na karatu. Dakine mai dan gado da tv a ciki sai ban daki da sauran tarkace a cikin dakin wanka halimatu tayi ni kuma ina zaune ina faman tunane a raina. Yaya ina zamu daga nan halimatu data gama shiri take tambayana nace gamu dai tukunna halimatu gida nake son mu tafi daga nan idan mun samu hanya. Abin kurciya sai ta hau murnan jin wai gida zamu tafi tausayin kan mu ya kamani a hakan barci mai nauyi nayi sosai a lokacin daga ni har halimatu data kwanta a gefena tana danna laptop itama tayi barci. Da wani irin matsakacin yunwa na falka ina neman abinda zanci a cikina lokacin fita nayi na nemo muna abincin na dawo dakin dashi . Na samu halimatu falka a dakin tana wuri wuri da idanu sai gani na shigo ta sauke ajiyan zuciya tare da tambayan inda naje ? ZAINAB IDRIS MAKAWA MASHA ALLAH ANOTHER FRIDAY AGAIN MAY ALMIGHTY ALLAH ACCEPT OUR IBADA FOR THIS FRIDAY ALLAHUMA AMIN, , , , YAR UWA TUNI GAREKI KI BIYA KI KARANTA WANAN LABARIN KARUWAN DA ZAKI SAMU A CIKI YAFI ABINDA ZAKI BADA YAWA UBANGIJI ALLAH YA TSARE MUNA ZURI,AN MU AMIN, , , Kwanan mu biyu a dan karamin hotel din ga wayana na kashe tun fitowan mu gidan wayan yake kashe ban kunna ba. Haka yasa duk kokarin yaya wurin gano inda muke baiyi nasaran gane komai ba hankalin shi ya daga ga baki daya har yakai rahoton batan mu a wurin yansandan kasan. Ban komai a dakin sai ibada da kuka sai kuma tunanen hanyan da zanbi mu tsare a kasan da bamu da kowa illa shi da ya kawo mu garin. A kwana na ukune hakkurin halima ya kare ta matsa min sai mu fita tare sayen abincin kamar yadda na saba fita in sayo muna duk abinda take so a cikin dabara. Yau kan ta tubure min akan tare zamu fita haka na daure muka fito har waje da ita muka sai abinda zamu saya muka koma ciki. Saidai irin kallon da mutanen ke min yasa na dan tsargu don da farko na dauka don launin fatan mu daban da tasune yasa suke kallon mu haka. Bayan na dawo dakin ina zaune ina kallon yadda halimatu take cin abincin ta hankali kwance kamar ba abinda ya dameta. Wani tunane yazo min lokaci guda na mike na fara tattara kayan mu da sauri naja hannun halimatu muka fito key din su na mika masu don basu biyo mu kudi ba mune ma muka biyo na kwana biyu a wurin su. Yana tsaye sai waya yake faman yi daya kashe wanan ya dauki wanan ya rike kunkurun shi da hannu daya. Yayin da dukkan aninaiyan suit din jikin shi suke bude ta gama daka ganshi kasan hankalin shi a tashe yake sosai lokacin. Waya ya shigo mai ya dan juya ya kalla rai bace tare da jan guntun tsuki yana kawar da kanshi gefe daya. Bayan kiran ya katse wani ya sake shigowa ya daga a hasale muryan mace yaji tana fadin yaran da ake nema aka bada wanan layin. Na gansu yanzu a hotel din green land akusa da child center na wanan birnin yace hold on ki kara fada min yadda bayanin shigan su yake. Ta shiga mai kwatance tare da siffan mu da yanayin komai namu da sauri ya mike ya figi key din shi sai inda suke parking din mota ya shiga daya daga cikin motocin dake wurin. Ganin haka security din shi suma suka bi bayan shi da sauri duk inda yabi suna biye dashi har zuwa green land motel dake gefen garin. Inda muke takai da security din hotel din akan kin barin mu mu fita daga cikin hotel din da sukayi don kawai su tabbatar idan bamu bane ake nema. Muna tsaye wiki wiki ya iso wurin a har gitse halimatu na ganin shi tun daga nesa take nunashi da hannu tana fadin lah ga yaya a cikin harshen hausa ta sheka da gudu ta fada jikin shi . Shima rungumeta yayi a jikin shi na dan lokaci kafin ya dago kai ya kalleni ba tsoro ko kadan a fuskana illa kara daure fuska danayi kawai. Mayar da hankalin shi yayi wurin ma,aikatan hotel din suna mashi bayanin tun zuwan mu da yadda suka gane mune ake nema a tv. Godiya yai masu tare da basu abinda akai alkawarin ba wanda ya ganmu dayan security din ya duka zai dauki dan jakkan kayan dake gabana don har lokacin ban ko motsa a yadda nake zaune ba. Wani tsawa na daka mai tare da fadin don't touch my bag ya dan dago daga inda yaya yake shikuma yace da mutumin ya dauka su tafi. A daidai lokacin da yake takowa inda nake zaune ya tsaya a gabana na dan wani lokaci kafin yace kiyi hakkuri mu koma gida muyi magana a can yanzu idon mutane na a kan mu. Na dago kai na dan kalli wanda suke wurin idanuwan su ko na akan mu suna dan magana kasa kasa. Haka yasa na mike badon naso ba na fara takawa a hankali yana rike da hannun halimatu suka biyoni a baya. Motan shi muka shiga saida mukai nisa da hotel batare da ya juyo ba ya fara magana yana fadin daga yau idan zaki kara irin wanan kada ki soma ki tafi da sadiya. Don ba zaman ki takeyi a garin nan ba ni da kaina na karbota hannun iyayyen ta don haka baki da ikon aiwatar da wani abu a kanta yanzu. Amma kada ka manta ita din yar uwatace bana wani ba idan ba don niba bazata zo nan kasan ba tare dakai. Don haka ba zan barta ta zauna a gidan da fasadi yazama ruwan shan don sabon Allah ya zamo shine alkibilan ka ko yaushe. Dan murmushi naji yayi bayan hakan bai kara furta komai ba har muka isa gidan mota na tsayawa na fito na barsu da halimatu a baya. Ban bi takan kowa ba part dina na nufa yana rufe na dawo part din fadila sai ganina tayi kamar daga sama ina shiga gado na fada ina kuka. Sunana ta kira da karfi zainab kece wai Allah mun godema ina kuka shiga haka a wanan kasan mai yawa kuma gashi ba kasan mu ba ? Jin yadda nake gumjin kuka yasa ta bar tambayan da take min din don itama hankalin ta ya tashi a yadda ta ganni na shigo dakin. Saiga halimatu tana jan dan troler din mu da gudu ta fada jikin fadila tace sadiya kun dawo wallahi tun tafiyan ku hankalin kows gidan nan a tashe yake. Shi kanshi me gidan baya zama gida kullun cikin neman ku yake ko za aji labarin ku mundai godewa Allah tunda kun dawo lafiya ai. Bari na kawo maku abinci kuci ta fada tana kokarin mikewa halimatu tace anty a koshe nake yanzu bazanci abinci ba. Muryan shine daga kofa yake fadin ki taso an bude part din ki daga haka ya juya ya fice abinshi bai tsaya jiran komai ba. Dafani fadila tayi tana fadin zainab kin ki ki saurareni ne ranan da baki tafi ba wallahi duk da tafiyan naku ya dagawa mijin ki hankali sosai . Saidai kusa lefin tafiyan naku duk a kaina ya dora shi yaga laifina sosai dana bari kuka tafi nasan da a Nigeria muke babu abinda zai hana ya koreni tun ranan. Zainab koma me yai maki mace da hakkuri aka santa bada saurin fushi ba don kinyi kankanta dayin yaji a shekarun nan naki. Jin abinda ta fada yasa na dago kai nace amma banyi kankanta a wurin hisabi ba ko anty ? Kina ganin yanzu idan na mutu Allah ba zai mun hisabi bane kwadayi ko son duniya yasa in zauna a gidan mai sabon Allah irin haka. Yaya jafar ba irin mutanen da suke shirin tuba bane da sabon Allah da sukeyi a rayuwan su har sai yaushe yaya zai daina wanan halin ya tubawa Allah. Kuka yaci karfina ta samu ta lalabani da ban baki da magana masu taushi har na tsagaita kukan da nakeyi din. Ban bar fakin ba sai bayan sallah magariba na koma part dina nayi wanka na kwanta duk da nasan ba barci zanyi ba a lokacin. Tun ina tunanen matakin da ya kamata in dauka har barci yai awon gaba dani a wurin ashe yazo yana kwankwasa kofan ban budeba a lokacin. Washegari na kunna wayana da ya kwana yana caji a jone sako ya fara shigo min wanda duk kusan sakon maya ce tana tambayan rashin gani school kwana biyu. Sai kuma sakon shi yaya da yake tambayan muna ina don Allah mu dawo gida idan sakon shi ya sameni. Zamuyi magana in fada mashi damuwa na ba sai na bar gidan haka ba yana dai tsoratani ga barin gida da mukayi a wanan kasan haka. Tsuki nayi bayan na gama karantawa na wurga wayan saman gado na mike zuwa wanka nafito na shirya tsab don fita school . A falo muka hadu da fadila fuskana babu walwala na gaida ita ta amsa min a cikin fara daganin shirina ba sai an tambayi inda zani ba. Hakan baisa ta kyaleni ba take tambayana bazan tsaya in karya bane nace banjin cin komai a yanzu ina kokarin fita falon. Nakai kofa take min a dawo lafiya da farko banga driver dake kaini school ba har na nufi katafaren get din gidan naji ana mun horn a bayana na waiga. Driver ne a cikin wata yar mota daganin motar taci kudi masu yawa kafin a mallaketa. Madam ga motar da oga ya canza muna yanzu wancan satin aka kawo ta yace an tsaya service din tane. Kamar bazan shiga ba son dan guntun tunanen danayi a zuciyana sai dai na bude na shiga muka fice gidan. A school kan nasha kallo don photo na da yai yawo a garin ko ina ana cigiyan mu nida halimatu na. Fuskewa nayi na shige class din mu nan ma dai ban tsira ba maya ce ta tareni a cikin fara,a da mutuntawa tazo ta rungumeni. Dama wuri daya muke zama da ita nan muka zauna muna dan hira amma bata sako min zancen batana dataji ance munyi ba a garin. Sai biyu muka fito break wurina samu nayi alwala da sallah kamar yadda na saba kebewa in yi sallah idan ina school. Maya na zaune gefe tana karatu har na gama take cewa mu dan taka wurin cin abinci don ita yunwa takeji. Mun zauna a wurun an bamu dan abincin su da akeci da tsunke na tasa nawa gaba ina tunane ban taba ba. Dafani maya tayi na dago firgigit na kalleta abincin ta nuna min da ido alaman inci abincin mana. Dan murmushi na kakaro a fuskana na fara cakulan abincin da dan tsunken dake hannu na kadan naci na ture plate din abincin daga gabana na dauki ruwa na kurba kadan. Koda baki fada min ba nasan kina da damuwa a ranki wanda hakan ya shafi matsalan gidane ko ? Kasa nayi da kaina don idona da suka cika min da hawaye lokaci guda ban sa amsan da zan bata ba a lokacin gashi banda abokin shawara bayan fadila. Fadilan kuma yanzu na kara wayau ba komaine zan iya sheda mata daya shafi mijina ko banza kasan mu daya koda ba garin mu daya ba. Don a tunane ban dauka da tasan wanan zancen na yaya ba ashe ita kar take daukana tana dai taka tsantasan ne don kada aikinta ya kubce mata. How can i help you ? Ta kara fada tana kallona na dago kai a hankali na kalle ta a lokacin har hawayen da nake tarewa sun fara zuba a idona ko. Tisui ta miko min daga cikin jakkanta na karba na dan goge fuskana dashi a daidai lokacin ta mike tsaye tare da fadin time yayi na komawan mu last period. Mikewan nayi muka jera zuwa ciki saidai babu wanda ya iya magana a cikin mu don kowa da irin tunanen da yakeyi a cikin ranshi. Haka na koma kwana biyu bana son magana da kowa a gidan don gaskiya ina cikin damuwa sosai na tsorace da al,amarin yaya zuwa yanzu. Wanka nafito ina tsaye a dakin ina tsane ruwan kaina da dan karamin towel da daura gaban zani a jikina . Ranan babu inda zan tafi don satine kowa na gida yana hutu a ranan kamar daga sama sai ganin yaya nayi a dakin. Kallo daya yai min ya kawar da kanshi da sauri na nufi wurin gado na daki hijjab dina na saka a jikina ya kai zaune yana dan tabe bakin shi alaman ko a jikina ni. Dan shirune ya biyo dakin kafin naji muryan shi yana fadin wai ke meke damun ki haka kike rama? Kinbi kin damu kanki kin sakawa zuciyar ki wani damuwa da bai shafeki ba haka ? Zaka iya fadin haka idan kaga dama kuma hakan ba zai ban mamaki ba ko kadan duba ga yadda ka tara kai shedan nama fitsari ko wani lokaci. Yau dan musulmi dakai yaya kake wanan fasadin a rayuwan ka kamar dan wasu arnaku da baisan addini ba da abinda Allah yace. Wani kallo yai min a harzuke take idanuwan shi suka kade sukai wani irin ja jajir ban fasa fadan abinda zan fadi din ba duk da ganun hakan danayi. Yaya yau yaya mami zataci danta na kwana da maza yan uwan shi mazan ma ba daya ba yaya har maza biyu a lokaci guda. Wa,iyazu billahi ko dabbo bi yan a halal kitabi bazasu taba aikata hakan ba don sun san da Allah ya hanesu da hakan suna tsoron azaban da Allah ya tanadarwa mai wanan dabian. Wani irin kallo yake min lokaci guda kamar ranan ya taba ganina a rayuwan shi ji nayi kawai ya dankeni iya karfi shi. Sai dana dan sake karan wahala muryan shi naji yana fadin uban wa ya fada baki nazo dake nan ne don ki saka mi ido ga al,amarina. Kin isheni kin dameni da fitina irin naki kada ki dauka don na saka maki ido kamar wani abu nake bukata a wurin ki. Mace kike ni kuma mata ba ra,ayina bane na daukoki nan ne don rufi asirina in rufa maki ki rufa min asiri. Idan kina da ra,yin yadda kikaga dama kofan hakan a bude yake maki zaki iya morewa rayuwan ki don yanzu nagane kin girma. Irin naki ra,ayin ba zan iya daukan hakan bani don haka zan baki dama kiyi duk abinda zai kawo maki sauki da jin dadin rayuwan ki matakur ba zaki shigo min gida da wani ba. Wa iyazu billahi na fada da karfi kafin inyi luuuu yaji na sake a jikin shi don tun lokacin daya fara magana idona ya fara rufewa a hankali. Da karfi ta fara girgizani tare da kiran sunana a rude saidai ba alaman farkawa alokacin a rude ya nufi bandakin ya debo ruwa a wani dan roba yazo inda nake kwance saman gado kamar yadda ya barni ya dinga shafa min a fuska a hankali. Wani iri ajiyan zuciya na sauke tare da bude idanuna a hankali ganin shi gaba na tsura mai ido kamar ban taba sanin shi ba a duniya. A hankali na mayar da idona na rufe ya kira sunana a sanyayye da zainab har sau uku na sake bude idon da kyar na sauke a kanshi . Ruwan ya sake shafa min a fuska har saman wuyana a hankali na sauke wani irin ajiyan zuciya na bude idon ina kallon shi. Wani irin hawaye masu zafi suka dinga fito a idanuwana saboda zancen shi da suke min yawo a kwakwalwana a lokacin. Mikewa nayi kokarin yi da sauri don gaba daya na tsorata dashi Allah ya ban sa,a na samu na jaye daga inda yake tsugunne . Na fara ja da baya a hankali ina girgiza kai tare da fadin yaya dama kai ba musulmi bane ashe ? Idon shi naga ya runtse don jin abindana fada yaya kai da bakin ka kake fadin hakan alhalin ina matarka na sunna. Baka tuna ko yanzu ko anjima yau ko gobe Allah na iya karban rayuwan daya baka aro a kyauta ka koma gareshi. Can kasan makoshin shi naji ya sake kiran suna da fadin ke baki san wasa bane a rayuwa ? Na fadi hakane don ki saurara min ga abinda kike yawan fada min amma na fadi hakane bawai ina nufin hakan ba har zuciyana. Dan Allah yaya na rokeka kayi hakkuri ka mayar dani gida wurin iyayyena tun kan rayuwana ya samu illa. Nayi ma alkawari kamar yadda nasha fada ma ba zanyi wanan zancen da kowa ba a gidan mu. Enough ya fada da karfi sai dan shiru ya kura min ido a hasale can yace ban aureki ko dauko ki nan dan mu rabu ba. Na daukokine a bisa wani dalili nawa da ba lalaine ki sanshi ba a yanzu tunda naga kurciya na wahalal dake. Abinda nake so dake idan zaki iya yanzu shine ki kawar da idanun ki ga al,amarina gaba daya. Ki maida hankali ga karatun ki da kikeyi idan zaki iya kuma ki mun addu,a idan kin samu lokaci. Idan kinyi hakan babu wanda zai ji mu dake har zuwa lokacin da komai zaizo ya daidaita zuwa lokacin kema kin idar da karatun ki . Kinga kina da zabi idan zaki koma gida a lokacin sai ki koma amma yanzu ina rokon ki kwantar da hankalin ki ida nufi a tsanake. Kaina kada a tsorace tare da hada hanayena wuri daya ina rokon shi da fadin na rokeka ko meye manufan ka yaya kada ka cuta ma rayuwan mu nida yar uwata. Baiyi magana ba ya mike tsaye ya dan tsura min ido kafin ya sa kai ha fice daga dakin na dora hannuna a kai ina neman kuka a idona na rasa. Jikina yai wani irin sanyi ga tsoro dake saukar min duk a lokaci guda haka na wuni sukku a gidan na kasa saka ko tufafi a jikina. Jina shiru yasa fadila ta biyoni ta sameni dakin wani irin zazzabi ya rufeni a rude take tambaya abinda ke damuna sai kaduwa nake a cikin bargo. Da sauri ta juya ta fita can sai gasu tare kasancewa ranan bai fita ko ina saida yamma yakan dan fita bai dadewa kuma yake dawowa gida. Sai gasu tare dashi ya dan tataba min jiki yaji yadda jikin nawa ya gashe radau da zafi fita yayi sai gashi da magani ya hawo kan gado ya tayar dani ya bani maganin . Banki sha ba don jina nake kamar zan mutu a lokacin ya dan dade rugume dani a jikin shi kafin barci ya dauke ni. Nasan yayi hakan ne don ya kawar da hankalin fadila daga wani zargi don baiyi zaton tasan komai a game dashi ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA RAYUWA TANA FARUWA WUCE TAKE KAMAR BA AYI BA UBANGIJI ALLAH KA NUFE MU DA AIKATA ALHERI A KULLUN DA BIYAYYA TSAKKAKE A GAREKA ALLAHUMA AMIN, , , , , Sun gama duk wani shirin daya dace ga tafiyab su kamar yadda suka tsara abinsu gaba daya gidan zasu zo mai hutu wanan karon har yan matan mami da har yanzu suna lake da ita a gidan. Ya jamal ne yace sai a rage yawa mami tace don me za a rage sun riga da sun sa rai ga tafiyan nan bayan hakama. Shida ya dauki diyan talakawa zuwa can yana biya masu komai sai nasa da zamu dan je muyi sati biyu ko uku acan mu dawo zakace wai wani a rage yawa. Barima in kira yar iskan yarinyar in sheda mata don kada muje tace zata yi muna halin su na yan talkawa da kuwa naci mutuncinta sosai wallahi. A take ta fara kiran layina fitowa na daga class ke nan kira ya shigo min na dauko waya ganin mamine yasa na dauka da sauri na fara gaida ita. Bata karba gaisuwa ba sai cewa da tayi ke ki bude kunnuwa ki kiji da kyau duk sanda na shirya zaki iya ganin mu gidan ku. Zanzo inga irin iskancin da kikeyi don samun wuri a gidan shi don na kula yanzu gaba daya kuna kokarin jaye hankalin shi gareni da yan uwan shi. Sai ke da iyayyeb ki kawai ya sani a yanzu zan zo zan sa ido na gani idan har hakan gaskiyane ba zan daga maki kafa ba wanan karon. Zaki san ni maryam ba sa,an yin ki bane har uwayen ki dake kauye suna maki tafi har idon jafar ya rufe a kanki. Daga inda nake ina sauraren ta na runtse idanuwana don iyayyena data sako a cikin zancen naji wasu irin hawaye sunzo min suna kokarin zuba a idona. Da kyar na iya budan bakina na furta mami Allah ya baki Allah ya kawo ku lafiya naji ta kashe wayan. Nabi wayan da kallo na girgiza kai tare da barin wurin na cin ma Maya a inda muke zama na zauna. Kallon yanayi tayi taga ya sauya gaba daya take tambayana abinda ya sameni zan iya cewa ranan ne karo na farko dana fara ba Maya din labarina a takaice. Ranan haka na dawo gida da bacin rai a tare dani ban fadawa kowa wanan zance ba haka na barshi a zuciyana ina dakon wahala. Ba abinda yafi batawa mami rai kamar yadda akace karatuna har na kusa gamawa a yanzu don dan watanni ne ya rage muna mu karasa don haka take jin wani irin tsana tun lokacin da jamal ya fada mata hakan. Ga karatun su baiwani ci gaba ba wanan lokacin dani a can na kusa kammala karatuna zuwa wanan lokacin na zama wata irin classic queen don daula da nake samu zakace yar wani basarake ne nidin. Don gaba daya na tattara damuwana da tsoro na aje a wuri daya na fuskanci karatuna zuwa wanan lokacin . Addu,a kan kullun muna kan yinsa ba fashi halimatu ma yanzu girma ya soma zo mata don haka na kara taka tsantsan tare da sa ido ga duk wani al,amarin ta. Banda kawa kaf kasan bayan Maya duk da ba addinin mu daya ba hakan bai hanamu kawance ba don babu wanda ke tabo addinin wani a tsakanin mu. Iya ka dai abu gudane idan lokacin ibada yayi zata rakani inyi ibadana ko ta tuna min is time for pray. Inda nima hakan zan tuna mata da nata lokacin ibadan su idan ta shagala da karatu inda na kulla da yaya jafar yanzu. Kawar da kai da nake ga al,amarin shi yanzu mun koma kamar wa da kanwar shi ga yawan alheri da kyautatawan da yake muna yanzu. Don mota ko yaushe a cikin canza min shi yake da yayi yan watanni a gurina zanga ya sawo min wata an dauke wancan na farko. Sutura ba,a maganan shi a wurin mu har fadila don yadda yake dan gayu dan kwalisa haka yayi kokari ya mayar damu muma da sutura tun bayan iya sakawa har yazu na iya irin kwaliyan su saidai ban yarda na kaucewa addinina ba da hakan. Mun samu hutu muna zaune gida don bikin kirismeti da zasu yi a kasan ko mu da bamu addinin su an gyara muna gida yadda ya dace. Amma saidai duk wanan abin baisa na daina jin tsanar shi da kyamarshi a raina ba sai dai ina kokarin ganin na nisance shi ga duk wani abinda zai kawo muna matsala ga hakan. Falo muke zaune dukkanmu mu uku kallo mukeyi fadila da halimatu da yanzu bakina ya saba da sadiya kamar yadda kowa ke kiranta a gidan dole nima na kama kiranta da sadiya yanzu. Sai fira suke tsakanin su da fadila yayin da hankalina ke ga karatun da nakeyi ga drinks da dan tsunken da nake zuka sai snack a gabana da nake dan hadawa ina ci. Kofan aka turo alaman mutum ya shigo gidan a lokacin hakan baisa na dago kaina daga karatun ba sai da naji sallama muryoyin da ba zan taba mantawa dasu ba a rayuwana. Muryan jalal da jamal ne don sune farkon shigowa gidan da sauri na dago kaina don jin muryan su da nayi mukai arba dasu na mike tsaye. Ya jamal kune tafe na fada cikin farin cikin ganin su na nufi inda suken a lokacin aka turo kofan sai ga mutane na shigowa. Tsaye nayi ina mamakin hakan a raina nace yanzu yaya yasan da zuwan su shine bai sanar min ba in san da hakan in shirya. Mamice da hjy kusan na karshen shigowa gidan ganin hjy na manta da kowa don suna tsaye soror sai kallon mamaki suke min gaba dayan su a lokacin. Sannun ku da zuwa nayi masu ina kokarin amsan jakkar hannun mami data rataya a kafadan ta kamar yadda ta nasaba amsa idan tadawo lokacin da nake gidan ta. Fuska a daure tana yatsune fuska tace No ki barshi kawai sai banji dadin hakan da tayi min ba a gaban kowa don yan matan suna tsaye sun daskare a wuri daya sai kallon mamaki suke min. Fadila har ta mike ta shiga kitchen ko ta hado masu abin tarbon baki ta kawo ta zube a gaban su bissimillah nayi masu wasu suka fara dauka . Wasu kuma mamaki ya hanasu ai watar da komai suna zaune kawai sun zuba min ido tare da bin ko ina na gidan da kallo. Na gaida mami ina masu anzo lafiya ta katseni da fadin yar mulki ashe kina gaida mutane ke nan ? Dama tsiyan tallaka ya samu wuri ke nan sai yayi kokarin mallake komai ya dauka komai a banza akayi shi. Haba iyami daga zuwa da wanan zaki tarbi yarki dashi ina shi arziki Allah kewa bawa shi. Na dauka ai wanan zancen ya rigada ya wuce tun tuni a wurun ki don da rabo ya ratsa ai yanzu sun kai ga diya biyu a gidan nan rabon dai ne dake nesa ya kawo hakan. Hjy da wanan ta daukeni uwa ai da ba hakan ba banga ranan da zan dauki zainab a matsayin sakuwana ba a zuciyata. Maimakon inyi fushi irin da ko hawaye sai murmushi da na sake a fuskana kadan mami kiyi hakkuri ko na kira ba s dagawa yasa na daina kira yanzu. Kowa shiru yayi yadda nake magana babu shayin komai ga hausan nawa zakace ma yare nakeyi a lokacin. Komawa nayi saman kujera na zauna tare da harde kafafuna daya saman daya wanda bansan nayi hakan bani don sabo a yanzu. Na dago kai a hankali na kalli inda su Aisha suke zaune dasu Rufaida nace kunzo lafiya ya hanya ? Firgigit sukayi saida Aisha ta mike take fadin lafiya nuna muna dakin da zamu sauka don Allah ta fada tana nuna gajiya a tare da ita. Sadiya take her to my room na fada sadiya ta mike da sauri tana fadin muje ita da kanta taja logued din ta zuwa dakin nawa. Na juya wurin fadila nace a gyarawa mami dayan dakin part din can sai dayan na sauran sisters hjy zata zauna a dakin ta. Nuriya kan ido ta zuba min mamaki ya hanata sauke numfashi ga yaran ta da alaman basu ganeni ba ma su. Haka na fada ma Fadilan komai yadda zata kai kowa masaukin shi har nuriya da yaranta da mijinta. Wai ina shi jafar din yaje ya mamud ke tambaya mami ta amsa da fadin nima shi nake son in tambaya ai yanzu. Yana ciki na bata amsa kai tsaye shine baki fada mai zuwan mu ba muka kallo juna da fadila a daidai lokacin da mami din ta mike tana fada. Wai zan rabata da danta da yan uwan shi dama burina ke nan inga kowa bai mameshi ba nasa ni dai har yanzu murmushi kawai nakewa fadan nata . Duk da raina yana baci a yanzu yadda take kokarin tozartani a gaban yayan nata dake zaune. Da ace mami tasan nima maraba nake nema da dan nata da bata tsaya bata baki ba haka don ni a yanzu godiya zan mata idan har ta rabani da danta. Haba mami ya mamud ya fada baki sani ba ko tana da dalilin yin hakan amma yaya zainab zata hanaki ganin danki kuma ? Kai mamud wai meyasa baku son ana zancen yarinyar nan ne haka wai ? Yanzu har sai mun tabayeshi zata fada mai munzo koda a ce bamu bane muka zo gidannan Ina part din nasa yake ta tambaya mami yana ciki baya son ana shiga mai part na fada maki ya jamal ke magana tare da nuna mata saman inda dakin shi yake. A fusace mami ta nufi can din tayi sa,a kofan na bude ta tura ta shiga tana fada yadda ta samesu da yadda ya ganta a bazata ne yasa kowan su shiga rudani. Shi dama a irin wanan lokacin da ake zaman gida yake samun lokacin sheke ayan shi yadda ranshi ke so a gidan. Da baya baya mami ta fito daga falon a daidai lokacin na iso wurin don gudun abinda zai biyo baya a lokacin. Ji tayi na rike ta ta baya nayi part dina da ita ba tare da kowa yasan meya ke faruwa a lokacin ba mami na biye dani har zuwa bakin gado na zaunar da ita kamar mutum mutumi. A daidai lokacin Aisha ta fito daga wanka yanayin data ganmu ciki yasa taja ta tsaya daga kofan bayin tana kallon mu da mamaki. Don yanzu ta barmu a falon mu fada gamu kuma tare a cikin wani yanayi ina ganin ta nace mami don Allah ki natsu kada hankalin saura ya tashi zan mamaki bayani daga baya . Na mike tare da fita daga dakin da sauri na nufi part din nasa ina shiga yana zaune daga shi tawul a jikin shi daure a kugun shi. Jin shigowana yasa ya dago kai gareni yana kallona nima kallon shi nakeyi tare da fadin kasan zasu yau yaya ka tsaya aikata wana fasadin ? Kamar ya nasan zasu zo bake kika gaiyato su suzo dama ba ni na fada da mamaki a daidai lokacin da dayan katon gardin ya fito daga dakin da sauri yana gyara aninin rigan jikin shi. Yana son fita daga dakin da hannu na nuna mashi ya koma ciki ya tsaya yana kallona da mamaki na juyo wurin ya jafar din ina fadin kowa na gidan nan yanzu don har ya mamud da Family shi suna tare. What , ya fada da dan karfi nace sosai kuwa zan fita zan fada masu baka gida don mami ma yanzu haka tana dakina a cikin wani hali. Shiru yayi har na gama bayani da zanyi na juya don barin wurin naji ya ambaci sunana a sanyaye da zainab . Jin hakan yasa na tsaya cak may yasa kika bari mami tashigo part din nan ya tambaya yana dago kai. Banda hujjan da zan dakatar da mami zuwa part din danta idan baka manta ba kuma kayi mi warning na daina shigo ma part din ka matukar bakai ka nemeni ba. Don haka babu yadda zanyi in shigo ma don kai da kanka kayi warning dina akan ha, , , , , Koma su waye kice dasu gani saukowa kada kice masu komai tunda mami ta riga data ganni ko yanzun zanyi wanka in sauko. Ban tsaya jiran abinda zai karasa fadi ba nasa kai na fice a dakin cike da takaicin shi a raina lokaci guda. Dakina na koma don kowa na masaukin da aka bashi suna sauke gajiya ina shiga dakin na samu Aisha tsaye a kan mami data kasa magana tun fitana dakin. Tsugunne nakai gefen gadon tare da dukar da kaina hawaye na zuba min a idanuwa tana kwance bata ko motsa a yadda take ba. Jin sheshekan kukan nawa yayi yawa Aisha da take a rude take fadin mami wani abu ya farune da na shigo daki halan ? Shiru ba amsa daga gurina har mami din da idonta kawai ta tsurawa kofan shigowa bata ko kfttasu don gaba daya ta fice cikin hayacin ta a lokacin. Aisha dan fita ki bamu daki mami ta fada ba tare data iya dago kai ga yar nata ba Aishan ta fita tana dan waige da sauri. Sai bayan fitan Aishan daga dakin muryan mami yazo min a kunnena tace zainab na amsa da na,am mami. Wani irin rayuwa kukeyi gidan nan da mijin ki ne don yanzu na sameshi dana shiga a cikin wani hali. Alama ya nuna kin san komai a kan hakan don yadda kika taroni daga baya zuwa dakin nan ya nuna min kin san abinda idona ya ganan min ke nan ? Kai na dago cikin hawaye na dan kalleta sai kuka ya rinjayeni ganin hakan itama mami ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi. Jin ana nocking din kofan yasa nayi saurin share hawayena na mike zuwa budan kofan hjy ce tare da ya mamud . May ke faruwane da zuwan mu mami ya mamud ya fada a lokacin mami ta kara karfin kukan da takeyi din gwanin ban tausayi. Kai kai haba mami wanan ai saiki dagawa mutane hankali mu dauka wani abu mumunane ya same ki daga zuwan mu ko kin samu wani sakone mara dadi daga gida ? Haba dai wani sako iyami zata samu har ya daga mata hankali haka tana wanan irin kukan haka yanzu ? Hajiya take fadin hakan tare da juyowa inda nake gurfane nima kukan nakeyi sosai a lokacin . Wanan abin naku akwai daure kai wallahi ko dai wani abune ya samu shi jafarin bamu sani ba sai yanzu da zuwan mu zamu samu labari ? Cikin karfin hali nace da ita lafiya yake hjy dama dai magana ce muka danyi da mami ya saka ta kuka don Allah kuce ta yafe muna zan bar yaya jafar din idan haka shine zai sa mu samu jituwa da mami dagani har yayan. Jin abindana fada mami ta rage kukan da takeyi tana fadin zainab ni dama baki min komai ba zainab don dai rashin biyayyan da kukaki min ne ai tun farko nake wanan haukan daku. Mami kiyi hakkuri ki yafe min ki roka min ya jafar ya sakeni in koma gida zaifi muna sauki. Shout up zainab a kul na kara jin wanan zancen a bakin ki zan saba maki rai a wurin nan abinda ya riga ya wuce ya wuce ko ya mamud ya fada Yau zainab da bakin ki zainab kike fadin hakan duk hakkurin da kikayi da wanan auren ai yanzu kun zama daya kike furta ya sakeki ? Zata ce hakan dole hjy don jafar mutumin banza ne a yanzu na fahinci dalilin shi na zaben zainab dayayi a matsayin matan auren shi. Wanda dacan hankalina bai kawo min haka ba sai yanzu dana fahinci waye jafar din don rayuwan jafar baida kyau hjy. Jafar ya fita daban a cikin yayana da al,umman musulmai baki daya hjy zan iya fadin yau nayi dana sanin haihuwan jafar da cikina wallahi. Wa,iyazu billahi mami don Allah ki bar fadin haka ko mai yai maki haka mai zafi kiyi hakkuri ki tausa zuciyar ki akan shi. Idan kaga na yafewa jafar har mun shirya dashi ya daina wanan halin banzan da yakeyi a rayuwan shine zamuyi zaman da uwar shi. Don haka yau ba sai gobe ba gaba dayan ku ku shirya mu bar masa gidan shi don banga amfanin zaman mu a gidan mai fasadi irin jafar ba. Wa iyazu billahi iyami dan naki kike aiban tawa haka da bakin ki har kina kiranshi da mai fasadi wani irin aikin asha yake aikatawa mai muni haka. Please mami don't tell her abinda idon ki ya gane maki don hjy bata da karfin zuciyar daukan wanan maganan a yanzu na fada da turanci. Gaskiyane ya mamud ya fada shima a cikin harshen turanci sai hjy tace nasan dai ba zai wuce akidan nasara ba da yake yawan dauka kuma ko yaushe mukai waya ina masa huduba da hakan. Jafar din ne ya turo kofa ya shigo da alama ya danji wani abu daga cikin zancen namu a dakin don kofan a rufe yake lokacin. Yayi wankan shi fes ba zaka taba cewa shine ba mai mumunan halaiyan nan idon shi akan mahaifiyar su dake darzan kuka saman gadona. Kafin ya mayar da kallon shi wurin hjy dake tsaye a kan yarta ni kuma ina rusunne a gefe ina hawaye. Hannun ya mikawa ya jafar yana fadin so you surprise me zuwa haka babu sanarwa duka family baki daya. Cikin dan basarwa ya mamud di yace dokan mami ne hakan ta hana kowa ya sanar daku zuwan mu saidai ku ganmu kwatsam. Nayi dana sanin wanan zuwan yafi dubu dana san abinda kake aikatawa a kasan nan da ban taba taka kafana zuwa gidan ka jafar . Dan murmushi yayi irin na masu karfin hali tare da fadinn haba mami me yai zafi haka kuma da bazaki zo gidana ba . Ai ko baki zo don ni ba zakizo don yar ki nan ki ganta kiga inda take zaune tunda kin huce damu. Shidai na gani sai dai kuma kai ja,iri da zuwan uwar taka ka bata mata rai haka me kayi haka da zafi har ka fice mata a raine lokaci guda ? Dan murmushi kawai ya sake tare da kallon mamud yana fadin ina madam da yaran su ke ko har dasune tafiyan . Kowa na nan ya mamud ya fada tare da fadin muje daga waje don mami ta huta ya soma tafiya yana fadin hakan. Shi kuma ya mara mai baya muryan mamine ya dakatar dasu din da wani irin tsawa take fadin mamud na fada ma kafita ka samo inda zamu sauka gobe zamu bar kasan nan da yardan Allah. Lokaci daya suka juyo gareta da mamaki suna kallon ta hjy ce ta katse su da fadin kekan tir iyami da wanan halin naki na rikau. Don kawai danki ya bata maki rai zaki fadi haka gareshi idan kinyi hakan ma kanki kika bawa kunya ai. Kada ki manta wanan tafiyan ba iya diyan ki kawai kikayi shi ba don haka ki shiga hankalin ki tun kan duniya ta saki a baki. Ki fada muna laifin yaron nan kuki fitowa fili ku fada daga ke har matar tasa sai kwanaye kwanayen da kuke muna a yanzu. Wanan maganan da hjy tayi yasa jikin mami sanyi amma kuma sai ta sake wani sabon kuka mai tayar da hankalin mutum . Ya mamud din ne yajashi suka fice daga dakin suka sauko kasa nan ma babu kowa duk suna dakunan da aka saukesu suna mayar da fadi a game dani da kuma irin gidan da muke zaune. Inda Aisha ke basu labarin ai basu ga kallo ba sai idan sun shiga dakina da nake zaune a ciki a nan zasu sha mamaki wai duk zee ce da wanan daulan haka. Har suna hada baki wurin fadin ki bari don Allah nan ma din kadan ke nan ashe muka gani bisa ga nata din ZAINAB IDRIS MAKAWA YA HAIYYU YA KAIYUMU BIN RAHAMATIKA YA ASTAGIS UBANGIJI KAI HASKE GA KABARIN DUK KAN MUSULMIN DA SUKA RIGAMU GIDAN GASKIYA ALBARKA KALMAN LA,ILLAH HA,ILALLA MOHAMMADAN RASULILLAH DA SUKA TABA FADA A RAYUWAN SU ALLAHUMA AMIN , , , , , Gidan yayi shiru lokaci guda baka jin motsin kowa a gidan sai na,orurin dake aiki kawai na gidan a lokacin. Mami dake kwance ta mike a hankali zaune taji zaman bai mata dadi don zuciyar ta daya cushe wuri daya a lokacin. Haka yasa ta saukowa daga saman gadon a hankali ta gyara hulan dake saye a kanta ta nufi kofan fita daga dakin. Ba kowa falon don haka ta nufi wurin shan iska inda zaka iya tsayawa kaga duk wani abinda wajen gidan ke ciki daga inda kake tsaye. Jamal ta hango tsaye shi kadai a cikin duhun yana tsaye ya harde hannayen shi guri daya yayin da kafafuwan shi ma suke a harde mashi. Hankalin shi gaba daya ya mayar dashi gaban gidan jikin shi na jingine da dan bangon wurin yana tunane ga iskan sayi yana huro mashi a jiki. Jin motsin mutum da yayi lokacin yasa shi dan juyowa inda yake jin tafiyan mutum din mami ya gani don ya sheda ta duk da akwai duhu a lokacin. Hakan bai hanashi sheda mahaifiyar tasu ba da take tafe itama mami din ta sheda ko waye a wurin tsaye duk da duhun dake akwai din. Mami baki barci ba ya fada cikin mamaki da tare da juyowa inda take yana fuskantar ta. Jamal ban dauka zan kara barci da idanuna ba kuma a wanan halin da dan uwan ka ya jefa kanshi a ciki na rayuwa irin wanan. Mami yanzu kin gani ke nan kema abinda na gani gareshi nake wanan fushin dashi . Jamal na gani Allah ya nuna min da idona yau naga mugun gani da idanuwa ga dan dana haifa da cikina . Sai wani irin kuka yazo mata lokaci guda jamal din yace mami ba kuka zakiyi ba don yanzu yaya addua da taimako yake so a garemu don yayi nisa a cikin wanan harkan ko yanzu. Jamal dole inyi kuka yau jafar ne a cikin wanan halin haka jamal ina zan saka rayuwana dan dana haifa aka bar min amana shine ya zama haka a rayuwa. Wanan kaddaran bawane, mami duk mai rai baya wuce kaddaran shi a rayu don haka zama ya kamata ayi asan hanyar da za a fitowa wanan maganan tunkan zancen nan yayi bosting kowa yasan hakan. Sani kuma na yaushe jamal tunda matar tasa ta sani kila kuma yan uwanta nan da suke zaune suma duk sin sanda hakan ko ? Kai haba mami zainab tana da matukar wayo bazata bar kowa yasan wanan zancen ba rufa min baki wani wayau can. Zata dai iya yin hakan don ta kare kanta itama tunda take zaune dashi ai kila itama din yar hannun ce ke nan ai yanzu. Ina mami baki san waye yarinyar nan zainab ba ashe har yanzu don koni danagani da idona kuma a kusan tare zance munga wanan abin amma bata yarda nasan da hakan ba . Saida na fito mata da zancen da kaina ta yarda tayi min bayanin komai don haka nake ganin ko yanzu ba zata taba barin kowa yaji hakan ba a bangaren ta. Jamal ke nan duk da kai yaron har yanzu baka tunane ko ita yanzu ya bata ta yasa bata yarda ta tona mashi asiri. Shiru Jamal din yayi yana tunane kala kala a zuciyar shi kafin yaji muryan mami yaci gaba da fadin nima haka wanan tunanen yazo min . Don yadda naga tana kokarin rufa mai asiri dole akwai wani abinda itama take boyewa nata don ko hjy dake dakin muna magana da mamud cewa tayi kada a bati taji komai don tsufa. Sai wanan karewan da takeyi din ya tsaya min a zuciyana na fara zargin itama ta dade da lalacewa ta wanan fannin yanzu. No mami kada kiyi zargin hakan a dai bincika a ji ai zata fadi gaskiya koma meye ba zata boye maku gaskiyan ba nake tsamani. Kana wasa da wanan yarinyar jamal ya katse da fadin haba mami yanzu kuma meya saura na zargin zainab gareki. Ga gaskiya tayi halinta baro baro za a tsaya zagin yar mutane damafa ya J yayi amfani da yarinyar nan zainab ne ya aureta bada yardan ta ba yabi ta wajen iyayyenta ya aureta. Don kawai ya kawar da idon mutane a kasan ace yana da aure ai ba haka kawai yake zaune ba. Don kada mutane damu a gano abunda yake aikatawa din wanan hikima yayi yaki yarda da auren hadin da kika so yi masa a baya. Don yasan idan daga bangareki ne yarinyar ba zata taba yarda ta boye shi ba yadda zainab din ta boye shi na shekaru. Idan ma cutane mami yanzun dai kingani yar mutane da aka baki amana aka cuta don mutuncin ki iyayyen ta suka gani tun farko suka yarda suka aura mai ita ba tare da wani kwankwanto ba can. Kai jamal ni kake kokarin nuwa yaran nan kome ina dukkan ku ta dalilina kuka san yarinyar nan dai ?. Koma meye zan zauna da ita ai in fahinci komai wallahi idan yarinyar nan tana da hannu cikin wanan matsalan gaba daya sai na sabawa rayuwan su. Don me zai shiga daki haka da wanan katon suna wanan wasan banzan idan ba wani abu suke aikatawa ba hakan ? Ok mami hakan yana da kyau ai ki bincika kiji komai don zaki gane mai gaskiya a cikin su yanzu ai idan kin bincika din. Sai dai kuma mami ki sani danki fa abinda kika gani shine gaskiya abinda danki ke aikatawa a kasan nan don shi sam bai damu da diya mace ba a rayuwan shi. Ga abu kin gani da idon ki mami zaki tsaya kina wani kwanaye kwanaye akan yar mutane ? Yanzu dai ai abin cikin duhu ya fita fili Allah ya nuna maki wanan sirin da danki ke boyewa sheka da shekaru yanayi. Ji kawai yayi mami ta fadi kasa a wurin somamiya da sauri ya nufi kanta yana kiran sunan ta cikin tashin hankali. Gashi su biyu ne kawai a falon dabara ya fado mai na ya yayyafa mata ruwa ya nufi kitchen da sauri ya dauko goran ruwa mai sanyi ya dawo dashi inda take. Ya yayyafa mata sai gata ta farfado lokaci guda sannu yake faman yi mata sai ta koma luuuu ta kara somewa kuma. A daidai lokacin fadila ta fito don motsin da take ji tun dazun a gidan idon ta yai arba da mami kwance kasa somamiya . Ga Jamal a kanta sai faman gurgizata yakeyi ihu ta yanka don tsoro lokaci guda muke bude kofofin gidan muna fitowa daga dakun nan mu. Kai ranan munga tashin hankali asibiti suka nufa da ita kai tsaye dashi da yaya mamud sai jamal da jalal da suka bisu. An barmu gida hankali tashe don bamu san halin da mami ke ciki ba a can don duk sun bar wayoyin su a gida tunda ba fitowan girma da arziki sukayi ba daga dakunan su. Tambayan nasha shi wurin Aisha amsa daya nake bata shine nima ban san dalilin hakan ba nadai ga mami a wanan halin tun bayan shigan ta dakin yaya . San nan na samu sa,ida a wirin su da tambayan da suke min hjy kan iya damuwa ta damu sosai da yar ta mami a halin data shiga. Basu dawo gidan ba sai washe gari suke fadin anba mami gadome asibitin da aka kaita tana can kwamce tare da jalal da jamal. Duk da hankali ya dan kwanta tunda sunce ba wani case bane sosai wai gajiya ne yai mata yawa na hanya. Nikan a raina nasan ko meye umul,aba,isin hakan da takeyi naja bakina nayi shiru don kada wani ya farga ya gane nasan wani abu. Gani da test a ranan Maya tana ta kirana dole haka na sance jiki na fice zuwa rubuta test din fadila kawai na fadawa inda zan tafi a lokacin. Allah ya taimakeni ba a fara ba saura minti biyu za a fara na shigo ban dade ba aka fara test din muna fitowa nayi sallama da maya na tafi. Na dawo na samu sun tafi asibitin duban mami sai fadilace kadai a gida sadiya bata riga data dawo gida ba daga makaranta don ni nayi saurin dawowa ranan. Da kaina na shiga kitchen muka hada masu abinci tare da mai aikin daya data saura a gidan don sauran sun dauki hutun sun tafi gida. Fadilace ke fadin rashin kyautawana da ban je asibiti duba mami ba nace da zuwana da rashin zuwa daya yake a wurina. Don yanzu jira nake kawai ta ba danta umurnin ya sallameni mu koma gida don shi kawai nake jira yanzu. Da sauri ta kalloni da mamaki tana fadin kada ki fadi haka zainab don nasan boss bazai taba sakin ki ba ai. Saboda wasu dalilai nasa kina da rana da amfani a wurin shi sosai wanda ba kowane yasan da hakan ba. Saki ya zama dole yanzu gareshi don lokaci yayi da zaiyi hakan na gaji da ganin laifina da mahaifiyar shi ke min ko yaushe. Gara na bar mata danta a zauna lafiya ta aura mashi yar masu arzikin da take so ya zauna da ita. Ina shima yasani ai zainab babu macen da zatayi wanan hakkurin da kikeyi a gidan nan yanzu. Don haka ki daina ma wanan zancen zainab don haka ki shirya muje anjima mu dibo ta ko ran mijin naki bazaiyi dadi ba idan bakije ba ai. Amma anty don ta katseni da fadin please zainab kada kice ba zaki ba din ko rashin zuwan ki a yanzu ai tasan da wani abu a kasa don abin zai iya damun kowa nan gaba. Nace shike nan anty zan tafi da yamma idan Allah ya kaimu sai ki shirya idan sadiya ta dawo mu tafi dukkan mu. Sun dawo gidan saidai ba wani damuwa a tare dasu don jikin mami din da sauki sosai sun dai kwantar da itace don ta samu hutu da natsu a can. A falo suka zube wasu kuma suka shiga yin sallah masu rikon addini ke nan daga cikin su irin hjy tsohuwa da anty Na,ima sai Aisha data shiga itama don laluran ta ba laifi ta tsaya tayi sallah a dakin. Don na shiga na sameta tana sallah amma su Nuriya dasu Rufaida suna falo ana hiran garin wanda a cikin hiran nasu suke sako habaici a ciki. Dawowan Sadiya ba ta dade da shigowa ba a lokacin kowa na falo zaune har mazan suna cin abinci duk suka bita da kowa da abinda ke zuciyar shi . Lokaci ne na mike zuwa daki na samu Aisha kwance tana waya nan daki na shiga ban tsaya ta kanta ba na fara watsa ruwa a jikina. Nafito nake shiryawa don fitan da zamuyi zuwa duba hjy muryan Aisha ya daki dodon kunnena da farko tsuki mai karfi naji taja. Hakan baisa na waigo inda take ba don zatona da wanda take wayan take tsukin sai naji muryan ta na fadin tsiyan banza ashe da gaske ake fadin dan talakka bai iya samun wuri ba dama. To bari kiji wallahi zainab idan wani abu ya samu mahaifiyar mu wallahi ni da kaina zan dauki mataki akanki koda kuwa ya j zai halakani nima. Na juyo ina fadin au dani kike zance ashe amma dai kafin ki halakani din zai fi kyau shi J din ki fara halakashi don shi musabbabin komai da mahaifiyar ku ke ciki. Ni meye nawa a ciki don bani nakar zomo ba rataya akabani don haka kowa ya sakar mun mara nayi fitsari . In laifine jeki gun dan uwanki ki tsure shi donni ba haifana kikayi ba da zaki sakani gaba zaki fada min rubish. Tunda na juyo na fara magana Aisha ta tsura min ido tana kallona da mamaki karara a fuskanta har nakai karshen magana na juya ina daukan kaya da zan saka. Can naji tace min lalai Aisha wuyan ki nan ya isa yanka zainab ni kike fadawa magana haka kai tsaye ? Kamar ba zan bata amsa ba saida na dauko kayan na aje na dago ina fadin nafada maki indon wanan auren kaddaran na dan uwan kine harke kuke son takura min a rayuwa don Allah yanzu ba sai anjima ba kisa ya sakeni na koma gun iyayyena yafi min zama da wanan kaddaran. Fadila ce ta turo kofan da sallama tana fadin madam we are ready ke muke jira ki taimaka ki fito min da takalma da jakka kayan nan. Tace yes ma ta nufi inda nake aje su tana daukowa tsuki Aisha taja tana sauka a gadon ta nufi hanyar fita daga dakin. Yadda ta fita yasa fadila gane akwai wani abu atsakanin mu lokacin ta kalloni bayan fitan Aisha din tana fadin meya faru kuma ? Ba komai na bata amsa tare da rolling din dan kwali a kaina ina fadin muje ko tace ok muka fito na rufo kofa da key. Muna saukowa duk idanuwan su a kaina don shigan da nayi ya girgizasu a wurin da alama kuma akwai maganan da sukayi akaina lokacin. Zamu fita nace dasu don su basu gajiya da kallona ni har mamaki abin ke bani yasa ban nuna masu na tsargu da irin kallon da sukan min ba a yanzu. Bin bayan mu Rufaida tayi da leke har lokacin dana bude mota muka shiga na fice gidan ta juyo tana fadin what ? Wai kunsan kuwa yarinyar nan wani kafirin mota take ja haka da kanta a garin nan ya mamud ne daga inda yake zaune ya dago yana fadin ina ruwan ki ko jirgi a yanzu sai zainab taja wanan ba abin mamaki bane ai. A mota nake ba fadila rabarin yadda mukayi da Aisha da amsan dana bata ni kuma . Fadila tace kin min daidai wallahi don raga masu baida wani amfani ko kadan gara su san yanzu ke din ba sa,an su bace ai. Mun isa asibitin ban wani sha wuyaba muka gane inda mami take muka shiga kamar yadda ka,idan shigan su yake a kasan. Don sukan ba,a barsu sun shiga ba don sunyi yawa kuma ba time din duba mara lafiya bane lokacin. Muna shiga muka samu jamal da jafar a zaune shiru a dakin mukai sallama bai dago kai ya kallemu ba yana dakilan wayan shi. Jamal ne yayi muna sannu da zuwa muka kara gaidasu tare da yiwa mami sannu da jiki ta dan dago tana amsawa. Abinci da muka zo dashine muka aje a gabanta nace mami ga abinci munzo maki dashi. Godiya tayi muna sai lokacin jafar yayi magana yake fadin fadila ki taimaka mata ta tashi zuwa bandaki ta dan gyara. No ta bari zan iya mami ta fada a karo nabiyu da tayi magana ke nan tun zuwan mu dakin da take kwance din. Da kyat ta yun kura ta mike ta shiga bayin haka yasa dakin shiru babu mai magana a cikin mu har ta fito ta hau gadon da niyar kwantawa. Abincin nake kokarin zubawa muryan mami ya dakatar dani tana fadin dakata zainab kada ki zuba don bazanci abincin gidan ku ba. Wani irin kallon mamaki kowa na dakin yai mata lokaci guda sai fadilace mai karfin halin fadin mami kiyi hakkuri ki danci wani abu don Allah. Jamal ta kalla inda yake tana fadin akwai kudin kasan nan a hannun ka ka sayo min abinda zanci a waje. A sanyayye dan nata ya amsa mata yana fadin akwai mami amma da kici wanan din don gurin sayar da abincin yana da nisa sosai. Jeka ka sayo min zan jiraka hakanan har ka dawo ta fada tana kawar da fuskanta daga kallon mu cikin dakewa. Jamal na fita jafar din ya mike tare da fadin mami zan koma wurin aiki sai anjima zan dawo insha Allahu. Ko motsi batayi ba balle yasa ran amsawa ga sallaman da yayi mata haka yasa kai ya fice daga dakin duk wanda ke wajen saida yaji wani abu a ransa lokacin. Munyi shiru dukkan mu mami ke fadin kada ki damu zainab badon ke nayi haka ba wanan karon donshi mara hankali da tunane na aikata hakan don haka kada ki dauki wanan don ke nayi hakan dama. Babu komai mami Allah ya shirya tsakanin ku na fada ina mikewa tsaye da sauri suka mike suma nace su jirani a waje ina zuwa. Suna fita fadila ta rufo kofan hakan ya bani daman karasawa bakin gadon da mami din take kwance. Ka nakai gurfane ina fadin mami kiyi hakkuri ki gafarce ni ban auri jafar don wani manufa da kuke fadi ba. Asalima shi jafar di ne ya turasasa iyayyena ya aureni da wani manufa da yake dashi a zuciyar shi don cinma burin shi. Kimarki da martaban ki hade irin kaunar da kika nuna min yasa iyayyena basu tsaya dogon bincike ba suka bayar dani ga danki. Kuka ne yazo min na dakata na dan lokaci saida nayi mai isata naci gaba da fadin Alhamdullahi mami tunda yau kin gane waye jafar da abinda yake aikatawa na fasadi a doron kasa. Don haka nake rokon ki a matsayin ki na uwa a gare mu mami ki tursasa jafar ya sakeni in koma wurin iyayyena tunda Allah bai nufa burin shi ya cika ba a kaina. ZAINAB IDRIS MAKAWA ALHAMDULLILAHI RABIL ALAMIN AR RAHAMANIN RAHIM, , , , YAR UWA WANAN NOVEL NA KUDINE DON GIRMAN ALLAH IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA DON KADA KI SHIGA HAKKIN WATA ALLAH YA BAMU CIKAWA DA IMANI AMIN, , , , , , Ido kawai mami ta zuba min har na gama na barke da kuka lokaci guda mai tsuma zuciya mami bata juyo ba. Sai da ya jamal ya turo kofan ya shigo dakin da sauri ya karaso yana fadin subbahanallahi lfy haka zainab ? Mami me ya farune take wanan kukan haka don Allah ko wani abin kuma ya jafar yai mata kafin ya fita. Gata nan ai katambayeta kaji abinda takewa kukan don ni ban fahinci inda ta dosa ba don ni yanzu bashi ke gaba . Zaune yakai yana fadin zainab me ya farune haka kike kuka don Allah ? Ya jamal a taimakeni ya jafar ya sakeni in koma gidan mu don Allah na gaji da wanan auren wasan da mukeyi. Kiyi hakkuri mami taji sauki za a kai ga wanan don kowa yasan yana cutawa rayuwan ki ai yanzu zee. Sai dai ke din wani baiwane a cikin ahalin don zancen rabuwa da yaya yanzu bai taso a gareki ba zainab. Kukane ya kubce min yasa nabar dakin da sauri don jin abinda jamal din ya fada game dani don ni yanzu banda wani buri dayafi naga ya sahale min wanan auren dake kaina in hutu da bakin cikin shi a zuciyana. A mota fadilace take ta ban baki duk da bata san abinda ya faru ba amma haka tayi ta ban baki kan hakkuri. Mun shigo gida yamma yayi a lokacin don haka kai tsaye kowa dakin sa ya nufa direct don yin sallah . Koda na idar ban shigo ba ina part dina don yadda nake jin zuciyana a lokacin sai suka dauka hakan wani wullakancine kuma dana samu yanzu gare su. Ban fito ba sai washegari don a ranan zamu rufe school zuwa hutun examas daya kawo jiki lokacin. Na sauko na nufi falon suna zaune ana hira har hjy tafito a lokacin wurin ta na nufa nakai har kasa ina gaida ita da kwana take fadin. Niko kawata wanan karon sam ban gane maki ba don bakya son shiga mutane yanzu sam ? Zanyi magana naji muryan Nuriya na fadin kai hjy da wani abu kike ina zata shigo mutane a yanzu bayan tana ganin tafi aji da matsayi a yanzun. Take annutin fuskan hjy ya sauya take fadin wanan wani irin magana kikeyi yar nan yarinyar nan idan ba wani abu ba me zaisa tayi hakan. Ai munzo munga halinta a nan din ba hakan take ba ai yanzu ma din dai kila wani abin ne dai ya taso mata na uzuri. Kara maimaita gaida ita nayi da kwana ta dan amsa da sauran hasalan a tare da ita nace zan leka makaranta in dawo. Shi mijin naki fa ta tambaya tana kallona nace ya na ciki yana shiri shima zai fito yanzu don ni ina rigashi fita kullun. Tace owoo Allah ya taimaka yasa a amfana ga abinda ake nema bayan ni dana amsa da amin babu mutum daya daya amsa mata wanan addu,an da tayi min. Na juya inda suke a cikin jam,i ina ina kwanan ku ya bakunta ban jira amsan su ba nace na tafi sai na dawo. Sai Na,ima ce tace tace min a dawo lafiya zee nace amin na leka dakin su Fadila na sallame su na fice gidan . A waje na samu su yaya suna kallon gari daga dan wurin da suke nayi masu sallama na bude motana na tafi. Na wuce ban dade ba jalal ya shiga ciki yana fadin ashe gaskiyan masu karin magana da sukace idan baka mutu ba ba debe tsammani a gareka. Wai yau zee din mami ce take tuka motar da Nigeria sai dan wani dan kasuwa a lagos yake tukata wai yau ga zee a cikin shi tana ja. Zee kan ai ta barmu da mamaki Na,ima ta fada sukan sauran shiru sukayi kamar basuji me ya fada ba a lokacin. Hjy daga gefe tace Allah ke nan dare daya Allah kanyi bature dama abin haka yake wurin ubangiji ai. Zaka ga dan mai kudi bai dace ba sai dan tallaka yazo shi ya bada mamaki baiwane na ubangiji hakan ai. But Nuriya ta mike daga inda take zaune tana fadin muma din ai ba fin mu dai akayi ba dadin abin idan gidan miji sun kasa dakai ai iyayyen ka nada shi ko ? Kaiya yar nan ai samun miji ga ya mace yafi na mahaifa don abin miji naka na kaima na iyayye kuma na sauran yan uwankane yanzu. Har ta juyo kamar ta bada amsa sai kuma ta juya taci gaba da tafiya rai bace zuwa dakin da aka sauke su a ciki. Yanzu kan zama gida ya kamani tare dasu dole na toshe kunnuwana akan irin maganganun da ake sake min a fakaice idan an zauna. Ga mami an sallamo ta daga asibitin taki sake jiki da kowa a gidan tana daki ko yaushe ita kadai a ciki. Ta fito da zancen komawa Nigeria hjy ta fatatake da fada don me take hakane tazo ne dama don ta dagawa yara hankali. Don haka ba za a koma ba sai idan lokacin da suka diba din yayi hakan yasa mami din yin fushi da kowa a gidan babu ruwanta da kowa sai wanda ya shiga su dan gaisa sama sama kowa fushin ya same shi a gidan. Ranan da suka cika sati daya a gidan suka shirya fita zuwa zagaya gari sun so mu tafi tare amma sai yaya yace na zauna suna sin ganina dama fadila da sadiya su rakasu. Jin hakan da Nuriya tayi tace itama ta fasa fitan idan bada ni zasu fita ba nan kan ranan yaya yai mata jan ido akan lalai sai sun fita tunda da ita aka shirya fitan dama. Badon taso ba ta shirya ta bisu suka fita bisa jagorancin jalal don jamal yaki shigowa gidan balle su leke mai. Jin haka yasa na koma dakina ina zaman jiran tsamanin su basu dade da fita ba yaya jamal yazo ya kwankwasa min na bude. Gaidashi nayi bayan ya amsa yake fadin kizo mami ke magana dake yanzu na amsa da to tare da komawa ciki na sako hijjabina na fito. Ina shiga dakin ya mamud nagani a zaune yayi shiru kamar me tunane na gaidashi ya dan juyo yana amsa min. Na gaida mami da jiki shiya nuna min wuri in zauna ban yarda na zauna saman kujeran da ya nuna min din ba. Na samu wuri a kasa na zauna dan shiru ne kafin ya mamud ya kawar da shirun da fafmfin zainab tambayan ki muke son yi don Allah. Kada ki fassara wanan abin da wani manufa ko ma,ana na daban ki tuna kema kamar mune kike a wurun mami. Duk abinda yashafi dayan mu kamar ya shafeki ke ma don bayan kina diya a wurunta ga alaka na aurataya ya kara hadaki da mami din kuma a yanzu. Don haka yarda da amana ya kara shiga a tsakanin mu ke nan ta ko ina yanzu don haka don Allah ki bamu amsa daudai abinda kika sani a game da mijin ki kada ki boye muna komai a game da rayuwan jafar a yanzu ? Kaina gyada a hankali ba tare dana dago kai ba na kalli kowa daga cikin su yaci gaba da fadin don Allah zainab ki fada muna iya abinda kika sani akan jafar din dan zaman da kikayi nan dashi. Don mun fahinci akwai sautin rayuwa wanda addini mu da al,ada bai amincewa ko wani dan musulmi dashi ba ya kasance yana aikata haka a rayuwan . Ya jamal ya amsa da fadin kinga boye muna ko rufa mai asiri kamar kinfi kowa cutawa ne a hakan don asan ta inda za a fara taro wanan matsalan a tsanake. Wani kuka ne yazo min ina kokarin dannewa saidai hakan bai yuyu ba gareni don saida hawayen ya zobo daga cikin idanuwana zuwa saman fuskana. Kada kiyi kuka don Allah zainab don a wurin kine kawai zamu samu abinda muke son ji a yanzu kafin shi mu tunkare shi muji dalilin yin hakan garesh. Nan ma dai shiru nayi masu don ban san mezan fara dashi ba a lokacin to tunda bata magana ai sai ku tambayeta muji don wanan ba abinda za a tsaya wani boye boye bane don mu fita daga zargin da zukatan mu ke ciki mami ta fada. Hakane mami don na kula nima ba zata iya fadan komai yadda muke so ba a wirin ta ya gyara zama da kyau tare da fadin. Zainab shin tunda kika auri jafar har zuwan ku nan akwai wani mu,a mulan aure dake shiga tsakani ku kamar yadda addini ya tanadar muna ? Ma,ana yana kwanciyan aure dake yadda musulunci yace mata da miji suyi a tsakani ko kuma a, a wani hanya yake bi ya biya bukatanshi a gareki idan bukatan hakan ya taso a gare ku. Kai na kara sadawa kasa don tambayan yai min nauyi da amsa hakan koda kuwa yaya jamal da yake kanin sane a wurin shi kadai. Zainab ki fada mana mafita akeson a nema maku ga baki dayan ku do koba jafar kike aure ba yau hakan ke faruwa dole mu dage mu nema maki hakkin ki ga ko waye . Don hakan yin shirun ki kamar kara dulmiyashi kike son yi ga aikata haramun a yanzu don baida kamarmu a fadin duniyan nan kaf da zasu tsaya akansa a yanzu. Ki daure mun san wanan tambayan yana da nauyi ki fada muna kai tsaye amma kuma ya zama dole a gareki damu mu san gaskiya. Kaina girgiza har lokacin kuka nakeyi da sauti a hankali mami tace kiyi magana mana kin tsaya kina girgiza kai kawai. Mami kinsan sai anbi a hankali ba zata iya fadi kai tsaye yadda akeso ji ba sai dai a cikin fahinta za a gane komai jamal ya fada. Kuna kwanciyan aure dai dashi ya mamud ya fada na sake girgiza kaina kamar yadda nayi da farko. Wai kina nufin wani abu na aure bai taba shiga tsakanin ku ba tunda ya aure ki tun a can gida har zuwa nan ke nan ? Na gyada kai innalillahi suka dauka dukan su mami kan kuka tasa saida suka bata baki suna fadin idan tayi haka ai ba za a gane komai ba karshe ma ya karta mu. Ya juyo gareni ya sake fadin zainab ta yaya kuka zauna haka ba tare da wani ya san da wanan zancen ba kinsan kuwa kina cutuwa ? Na girgiza kai yace wa iyazu billahi kuma ke baki taba masa maganan meya kawo haka ba don yanzu dai babu kurciya a tare dake ai ? Sai lokacin na bude baki cikin muryan kuka ina fadin ban masa magana ba kan hakan saida nayi masa magana kan irin rayuwan da ya keyi a nan wanda bai dace ba. Sai yace maki me ya mamud ya tambaya da sauri ya fada min kada in sa mashi ido ga duk abinda nagani yanayi idan ina son in tsira da mutunci na . Kinsan yana mu,amula da maza yan uwan shi dan jim nayi nadan lokaci na kasa furta amsa ga wanan tambayan. Muryan jamal ne yake fadin kinsan hakan ko baki sani ba na gyada kai alaman na sani kin dauki mataki a hakan ? Nace yace shi mace bata ta burgeshi ba asalima asalima idan munga yayi hurda da mace eather yar uwar shi ko abokiyar aikin shi ko wani abin amma bada sunan so ba. Wani irin kuka mai gumji mami tasa tana fadin na shiga uku jafar ya halakani jama,a ina zan saka kaina a duniyan nan ? Tsakanina da jafar sai Allah , , , , a, a mami don Allah kada ki masa baki kuma ya kara lalacewa fiye da hakan Jamal ya fada a cikin damuwa. Yana kuma sha har yanzu ko yaya mamud ya tambaya na gyada kai shiru ya biyo baya na dauka suna nazari ne kan zancen. Ashe duk kuka suke a dakin sai da naji sheshekan kukan yaya mamud yasa na dan dago kai hakan yasa nima na kara sake sautin kukana sosai a lokacin. Karshe dai ya mamud ne yace zainab koma dakin ki ko hakan ya wadatar damu kuma ba zamu nuna mashi munyi wanan zancen dake ba don gudun jefa ki a wani fitina kuma na daban . Kaina gyada na mike jiki ba karfi cikin sanyin gwiwa na fice zuwa dakina a can na dasa wani sabon kuka saida lokacin sallah yayi na mike zuwa hin sallah. Idarwa na yayi daidai da shigowan sadiya dakin tana fada min dawowan su nan ta zauna tana ban labari wanda ni a cikin zancen ta dain banhinci komai ba a lokacin. Tare da sadiya muka kwana a dakina don yanzu Aisha tun ranan da muka samu matsala ta daina shiga dakin karshema daukan jskkar kayan ta tayi ta mayar dakin mami. Zuwa safe ne jikin mami ya motsa aka kaita asibiti saidai ba a kwantar da ita ba magani kawai aka bata suka dawo gida. Ashe a cikin daren suka zauna dashi tare da zayano mai laifin shi kaf yaso mussa masu saidai hakan bai samu ba. Mami tace jafar ka cuce ni ka cuci rayuwana na na baya saidai ka sani ba zan bar zainab a gidan nan ba gaskiya tashi na tashin wanan yarinya. Daga yau kuma jafar na sallame ka a cikin yayana tunda ka dauki turban shedan da ka yafa wa kanka ka zama abin kyama cikin mu. Kai bamu kadai ba duk wani wanda ya sami wanan labarin dole ya kyamace ka a rayuwan shi. Don haka bazan yarda ka cutawa yar mutane ba ka sallami yarinyar nan tunda ba aure a tsakanin ku tun kafin iyayyen ta suji su dauki mataki. Sai lokacin da yaji mami ta kara maimaita zancenta kan tare dani zasu tafi ya dago kai ga idanuwan shi sunyi ja jajir don tashin hankali yace. Mami akan me zan saki matana laifi daine nine na aikata ba ita kuma baiyi aune ba yaji saukan hannun mami a jikin shi. Ya dago ta kara wanka mashi wani marin sai kuma ta kara fashewa da kuka tana fadin ka tashi ka bace min da gani . Kuma dakata kaji daga yau sai yau idan ka kara nuna ka sanni ko wani nawa jafar muddin bakabar wanan halin ba sai na tsine ma. Zaiyi magana mamud ya tare shi yace ka fice muna banza mara tunane da lissafi wawa kabi fudin duniya ka batawa zurian mu suna. Ba mami dake duniya ba har daddy yana Allah wadai da samuwan ka a cikin zurian shi kayi gagawan tuba ga Allah tun kan ka wullakanta a duniya don karshen mai wanan dabi,an bai taba kyau tun a duniya. Idan kana ganin kayiwa mutane wayau ne ai ba zakaiwa Allahn daya halice ka ba don yana nan madakata yana jiran kowa. Dama manufar da kake fadin kana dashi ga auran yarinyar nan ke nan da muka kasa ganewa ashe abinda kake aikatawa ke nan a rayuwan ka. Kana dan musulmai har ka iya mantawa da Allah zai iya daukan ranka akowani lokaci wata kila ma kana kan aikata wanan sabon ko kana shirin aikatawa Allah ya daukeka da wanan niyar. In ma baka sani ba ka sani in ka mutu babu musulmin kwarai da zai halarci jana,izan ka wallahi. Maganganun su kamar saukan garwashi yake jin shi a zuciyar shi saidai yadda yaga sun hau yau babu sauki a tare dasu . Do bai taba zaton zata kwabe mashi da wuri haka ba shima sai gashi abu ya kwabe mai a lkkacin da bai shiryawa hakan ba. Kalman mami gareshi da take ta nanata ta tsane shi ta tsaneshi ga baki daya tana kuma data sanin haihuwan shi datayi a yanzu. Karshema tace datasan shi zata haifa da cikin shi ya bare bata haifeshi ba tun lokacin da wanan abin kunyan daya ja masu a duniya yanzu. Lalai zainab yar albarkace don da watace da tuni an dade da jin wanan halin nasa gashi ta rufe ko su iyayyen shi bata fadawa wanan zancen ba tana zaune dakai a hakan. Dole nema ka sallami yar mutane taje can tayi auren ta a cikin sallama idan ranshi yayi dubu ya baci a ranan don tashin hankalin da yake ciki. Karshe ya mike ya fita daga dakin mami din ranshi bacd ya barsu ba don sun gama fada mai maganganh masu zafi ba. Falo ya samu sisters din shi haka ya wuce su suna gaida shi bai karba masu ba ya fice daga gidan badon yasan inda ya dosa ba a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KAFIN KI KARANTA DA GUJEWA DAUKAN HAKKIN WANI, , , , Duk wanda ke gidan yasan akwai rikici a tsakanin sai dai ba wanda zaice ga dalilin daya faru a tsakanin su ba. Sai hakan ya jefa kowa a cikin duhu akabar su da wasi wasin a zuciyar su don suna son sanin meke faruwa haka a gidan. Sai dai sunfi karkata zuciyar su akan rashin kaunar da mami batayiwa auren mune ta tayar da wanan fitinan a tsakanin mu . Har hakan ya jawo wani fitina da akeyi a lokacin wanda ya dagawa kowa hankali a cikin mu. Nuriya har zancen ta tsare ya mamud dashi a dakin su ya hauta da fada yana fadin shi sam bai sam ma wani abu yana faruwa a gidan ba in ba data fadi hakan ba yanzu a gaban shi. Bata gane komai ba dole ta bar zancen ga gulma kuma yana cinta akan sanin ko rikicin me akeyi a tsakanin su. Gashi mami ta fada masu su shirya zasu koma gida tun lokacin tafiyan da suka debo baiyi ba na komawan su gida. Da safene ina daki zaune wayana yai kara na dauka layin ya jafar ne ke kirana a take mamakin hakan ya kamani. Saida naja aji na daga wayan da sallama a bakina naji muryan shi kasa kasa yana fadin kizo dakina ki sameni yanzu. Ya kashe wayan nabi wayan da kallon mamaki a raina don mawuyacin abune zaisa ya nemeni a part din shi haka kai tsaye don ni har na saba da hakan. Saida na dan dauki lokaci na mike na fito tare da rufo kofana na nufi part din nasa don ba nisa ke garemu sosai ba. Dama kuma zamu bar wanan gidan mu koma wani unguwa dake can nisa da inda muke a yanzu . Sanin hakan ranan yake waya a gaban mu muke jin yace wurin sabon gidan shi da zai koma da family din shi za a kai wanan dalilin yasa muka san zamu tashi a gidan. Na dauka yana falon shi saidai ban sameshi a falon ba haka yasa na nufi dakin kwanan shi kai tsaye. Saida na danyi nocking din kofan kafin in tura in shiga bawai zanji amsawan shi bane in har ya amsa din ma. Can na hango tsaye a gaban widow dakin yana kallon haraban gidan na tako a hankali har zuwa inda yake tare da fadin gani yaya. Ya juyo lokaci guda tare da dan kura min ido na dan lokaci kafin yace dani rufo kofa magana zamuyi dake. Na juya zuwa kofan na rufo koda na juyo a lokacin ya dawo saman gado ya zauna wuri ya nuna min na samu a kusa dashi na dan zauna a cikin tsarguwa. Zainab me kika fadawa mahaifiyata da yan uwana game dani ya fada ba tare da ya dago kai ba har lokacin kanshi na a duke ya harde hannayen shi biyu saman gwiwan kafan shi. Da sauri na dan kallo shi don nima fuskana yana kallon kasan dakin dama a cikin mamaki karara a fuskana nake kallon shi. Ya dago kai ya dan kalleni sai lokacin naga yadda idanuwan shi suka sauya sun rikede kamar ba nasa ba lokaci guda. Nace mena fada masu ko sun fada ma na fada masu wani abu a game da kai zuwan su ? Duk da nake yarinya ai nasan mutuncin kai na da kuma darajan aurena don haka bana cikin irin matan dake fallasa sirin gidan su. Ido ya kura min kamar yana nazarina kafin ya sauke ajiyan zuciya yace idan bake kika fada masu ga yadda nake ba banyi zaton akwai wani wanda zai fadi hakan ba garesu. Amma ai abinka ba a boye yake ba kowa ya sani idan ka boyewa wa mutane ai ba zaka boyewa Allah ba dole wata rana asan ko kai waye . Saidai ranan ai mami ta shigo dakin kuma ta ganka tare da wanan abokin fasadin naka koka manta da hakan ne ? Don ni ban san a yanayin data riskeka a ciki ba nadai ganta tayi baya acikin tashin hankali wanda hakan yai dadai da zuwana wurin na tareta zuwa dakina. Bayan haka kuma ta wayi gari a cikin ciwon da har ta kwanta asibiti don haka ba ni zance da kawai na sani ke nan a gidan nan. Humm kada ki mayar dani karamin yaro zainab idan baki fada masu ba abinda ke shiga tsakanina dake ba a matsayin mu na miji da mata yaya za ayi su san hakan su ? Wanan ni ba matsala bane tunda zaman hakan bai dameni idan kana son jin komai ai zaka iya zuwa ka tuntubesu su fada ma wanda ya fada masu hakan. Don ni ba a wurin mutum zan kai kukana ba sai wurin mahalicina don shine mai maganin kowa ba wani ba don haka meye amfanin fada masu komai. Rashin kunyar nawa ai baikai in fada masu ga yadda muke zama dakai ba don na matsu ko me zaisa har in fadi hakan. Na fahince ki zainab kina kokarin nuna min yanzu kinsan komai na dade da kula da hakan gareki don hakane kike son a rabaki dani yanzu ko ? Idan anyi hakan an taimakeni ne yaya don ko ba a rabamu yanzu ba nan gaba dole a rabani dakai ai. Kamar yadda nasan ka a dan musulmai a asali haka nima nake diyar musulmai a zahiri don haka ba zan zauna na yarda mu kone tare da kai ba tunda ka sani kake take sanin ka . Tunda nakan fada mai magana ban taba gasa mai mai zafi irin wanan ba don haka hakkurin shi a ranan ya kai karshe dani. A harzuke sai dana razana daya daka min wani tsawa ke enough kada ki daukeni mara hankali ko rashin wayau. Naji mami na fadin zata wuce dake Nigeria bari kiji idan ma ke kika hada wanan zancen ki koma ki fada mata kin fasa tafiya don hakan zaifi maki sauki. Don kafi ki tafi sai na halaki a kasan nan idan kin kafe akan zaki bisu ba tsoro duk da na tsorata da maganan nace. Nasan zaka iya don imanin ka nada rauni ba Allah ka sani ba ai da baka kwana da dan uwanka namiji ba kabar , , , Marin daya daukeni dashi yasa naga wani irin duhu ya gitta min har na manta da abida zan fada lokacin. Dafe wurin nayi na dan lokaci kafin na mike cikin karfin hali ina fadin ka mareni yaya ? An mareki kada ki manta tun farko saidana fada maki auren mu na taimakon junane nida ke. Don me yanzu zaki bijiro da wani zancen saki a baya ko kin dauka kinfi karfinane da kike min abinda kikaga dama ina kyaleki. Akwai abinda nake duba nake raga maki sosai kada ki dauka hakan ba yana damuna bane don kawai banda abinda zanyi dake. Wani kallo nayi mai wanda ban taba mai itin sa ba na raini na juya na fara tafiya don barin dakin. Zaka san ka mareni don wanda bai sani ba yanzu zai sani bazan zauna da fasiki mai aikata fasadin mafi muni ba a duniya na fada dana kai kofan dakin. Ya bini da kallo yana jin kansa kamar ya hade ranshi don wani irin takaicin da yake ji a zuciyar shi yana fadin. Shi yarinyar nan zatayiwa tonon asiri irin haka duk ingata mata rayuwan danayi kada takai zuciyar ta ga hakan ? Kafin wani lokaci wurin ya nuna alaman yatsun hannun shi don ya fito radau a fuskana abu ga farin mutum sai idanuwa na duk suka rikede sukai ja. Kin fita nayi ina daki a kwance don ban gaida kowa na gidan ba da kwana a ranan haka yasa hjy aiko sadiya ta dubani ta same a wanan halin. Komawa tayi ta fada mata ta samu kamar banda lafiyane ina kwance. Sai ga hjy ta taso da kyar zuwa dakin take tambayan meya sameni ina kokarin boye mata take tambayana. Wanan kamar shedan mari a fuskan ki nayi kasa da kaina ina hawaye jafiri ne ko shi yai maki wanan haka ? A garin yaya haka ya faru ko uwar tasa tasa ya dokeki haka har tsanan yakai tasa dan ta gaba yai maki haka ? Na samu na bude baki da kyar ina fadin hjy ki taimakeni ki rabani da ya jafar don ba cikkaken musulmi bane shi. Innalillahi take fada tana taba hannayen ta a cikin mamaki kafin tace sallah ne baya cikawa ko azumine bayayi ? Kaina girgiza mata a hankali ina maijin yadda zan bude bakina nayi maganan da ita a lokacin. Saiga fadila ta turo kofan ta shigo dauke da abinci a hannun ta don tana da wanan dabi,an na kula dani idan ta fahinci bana cikin dadin rai. Yanzu sadiya ke fada min bakya jin dadin jikin ki ta fada tana aje abincin tana kallona idon ta yi arba da shartin yatsun shi a fuskana . Da sauri ta dago tana fadin subbahanallahi meya faru kuma haka madam wa yai maki wanan aikin haka ? Wa zai mata banda mijinta mara tunane koma me tayima ai sai kayi hakkuri tunda baku kadai bane yanzu a gidan nan. Wanan ai sai kabar mata abin fade idan yana dukanta bama kusa yanzu ma da muke nan akace ya duketa don bai san ciwon kansa ba. Ina jafari ina dukan wanan yarinyar haka tunda ba karfin su daya ba wanan me zubin samudawa ina wanan yar zata dauki dukan shi haka ? Hjy tunda nake zaune dasu a nan ko fada basa yi gaskiya a tsakanin su don zainab yarinya ce mai biyayya . Yau daine hakan ya faru tsakanin su har abin yai muni to idan uwarshi tasa ya dukeki ai ya daki auren shi ke nan a gidan nan. Jin haka na kara marairaicewa ina fadin don Allah hjy ki ceci rayuwana ban iya zama da yaya jafar a maysayin miji don ba dukiya nake aure ba. Shiru sukayi suna kallo na kafin fadila tayi karfin halin fadin haba zainab ai addu,a bai bar komai ba ki dinga masa adduan nan dai da kika saba har Allah yasa ya daina wanan abubuwan da yakeyi din. Amma zancen a rabaku wanan wani sabin tonon asirine a tsakanin ku zai taso maku har duniya ta jiku. Bayan ana ganin ke din mai sa,a ce da kika samu miji da gidan hutu irin wanan kinga mutane basu gane halinda kike ciki ai. Dakata yar nan kuna makana kun nuke ni ta baibai kun barni a duhu kai zancen ku yana nuna akwai mumunan zama a tsakanin auren nan da bamu sani ba. Wallahi hjy a kwaishi kan sai dai tayi hakkuri data saba amma zainab tayi kankanta da irin wanan rayuwan haka da takeyi a gidan nan tunda da kurciyar ta. Ace miji ba ruwan sa dakai ba zaya kalleka da sunan mata ba a idon sa saidai ayi ta labta ma kayan alatu kana hasaka gari ? Tsohuwar ta gyara zama a rude tana fadin nikan kun barni a cikin duhu har yanzu don na kasa fahintar inda kuka dosa. Sai ta mike tsaye wanan zancen bana kyalewa bane barin samu uwar nasa idan itace me sakashi cutawa yar nan haka a zaman su. Duk kiran da fadila kewa hjy ta fice bata juyo ba gashi da kyat take tafiya yanzu ajiyan zuciya na sauke don nasan ko banza yanzu za ayita ta kare tunda har hjy taji wanan zancen duk da bataji duka ba ma. Fadila ke fadin banso tsohuwar nan tafita haka a cikin fushi ba don yanzu komai zai iya faruwa har wa yan nan yaran su ji. Dakin da mami ke ciki hjy ta dosa suka hade da ya jamal a kofa ta wuce shi tana fada haka kawai ka tasa yar mutane a gaba da duka . Gara dai a kashe wanan auren kamar yadda iyami ke so tun farko kowa ma ya huta da wanan alkakan hakana. Aure ba haihu bada ba jika amma fitinan shi har yau yaki karewa mutane a rayuwa gara akashe kowa ya huta. Jin hakan yabi bayan ta zuwa dakin kusan a tare suka shiga mami na zaune ta jingina bayan ta da gado kafafuwan ta a mike da gani ba sai an tambaya ba tana cikin damuwa ko tashin hankali walau ciwo kuma. Yau dai ayita ta kare a gidan nan ku sakarwa yar mutane mara ta huta mami ta dago kai da sauri tana fadin hjy kedawa kuma ? Ni da dan nan naki jafari ya kama yar mutane da duka haka duk ya bata mata fuska da shartin yatsun shi ina yar nan ina daukan dukan bawan Allah nan. Ko ya fara shaye shaye ni kan don sai magana take min bayani a dunkule mai nuna ABU A CIKIN DUHU SIRINE. Mu muna mata kallon ta samu gida tana yadda ranta keso jiya jiyan nan na gama ji yaran nan wanda basu da aiki sai hassada da kyashi suna fadan haka da kunnuwana naji su sai gashi yau Allah ya nuna muna sirin dake boye. To gara dai kisa ya sallami yar nan tunda abin ya kai ga duka haka tun muna nan ke nan inaga bama nan Allah kadai yasan ukuban da yake nuna mata tunda kin riga da kin masa huduban shedan ya dauka gara dai kowa ya huta da wanan auren itama ta kama gaban ta taje ta samu daidai da ita a can. Saida ta kai aya ta dago kai don duban mami data kyaleta tana ta zuba haka sai taga mami din na hawaye mawuyacin abu ga mami din duk yadda ranta yakai ga baci kuwa. Cikin muryan kuka mami ke fadin hjy jafar kasheni yake son yi ya huta a yanzu ina dana sanin ma haihuwan jafar a duniyan nan . Hjy tayi tsaye sororo tana kallon mami din cikin mamaki don ganin yanayin ta dakuma abinda take fadi din don yadda tasan tana son dan nata fiye da duk yan uwan shi. Haba mami ki daina fadan haka ki masa addua jamal ya fada daga bayan hjy inda yake tsaye a kofa ranshi bace. Jamal dole in fada don jafar so yake ya konani a duniya bayan ya kona kansa saboda rudin duniya. Fita yayi zuwa waje ashe ya mamud zai kira a waya ya kirashi ba a jima ba sai gashi yazo da saurin sa suka shigo tare. Har lokacin mami kuka takeyi sosai itama hjy sai ta kama kuka duk da bata san abinda ya saka mami din kuka ba haka ? Da sauri ya turo kofan ya shigo jamal na bayan shi ya maida kofan ya rufe don ma ginan su irin na kasan da wani bsijin wani da dole sauran mutanen gidan hankalin su ya dauku garesu. Wai me kuma ya faru ni wanan abin gara mu koma gida zaifi mami fon wallahi hankalin kowa dai a tashe yake da wanan maganan. Shi kanshi jafar din ai in kin kula baya cikin kwanciyan hankali duk tsiyat shi yanzu da yasan an gane me yakeyi ana nuna mai kyama. Haka yasa ya tozarta ga baki daya baya cikin walwala duk da karfin halin shi kuwa wanan karon ya sare don bai zaci haka abin zaizo mai lokaci guda ba tunda ya maida mutane wawaye, Yanzu ba wanan ba ya mamud zainab ya kama ya doka waya sani ko yayi shaye shayen nasa ne kuma ko ta kamashi yana harkan banza. Sam ya manta da hjy tana dakin don idon shi ya rufe a lokacin yake faman dake maganan da ba a son taji din taji sai ji sukayi ta fadi saman gado Allah ya taimaka a zaune take lokacin. Ihun kiran sunan ta da sukeyi yasa hankalin a gidan ya koma kansu da gudu aka nufo dakin mami din. Gaba daya dakin suke shiga dan ihun da mami din keyi ina daki ban leko inda suke ba don hutun nasu ya zama muna tashin hankali ga baki dayan mu daga mu harsu a yanzu. Ya mamud ya kira jafar a waya yana fadin kana inane kazo ga hjy ta some muna bata numfashi. What hjy din meya same ta kuma yanzu muka gaisa da ita na fita to kazo dai yanzu ya fada ya kashe wayan. Shike nan kun kashe min uwa kun huta saura ni ku kasheni mami ta fada a cikin kuka goran ruwa mai sanyi jalal ya dauko a fridge ya bulbula ma tsohuwan ta sauke ajiyan zuciya saidai bata bude ido ba. Lokacin ne jafar ya shigo gidan a rude yana fadin ku dauko ta ga motab asibiti nan waje yanzu zasu karaso . Yana kokarin daukan tsohuwan kakan tasu uwar ta daka mai tsawa da fadin kada ka taba min tsohuwa. Tsayawa yayi cak bashi ba da wanan zancen ya daki zuciyar shi duk wanda ke wurin saida zancen ya taba mai zuciya. Ya mamud ne ya matso ya sukuci tsohuwan dake kwance zuwa waje sauran suka mara mashi baya a cikin sanyi jiki. Allah ya gyara daga Nuriya har yaran ta babu kowa a wurin lokacin suna part din su sun kulle don har yanzu bata bari yaran su sake jiki a cikin yan uwa. Muna daki bamu san wainar da ake toyawa a gidan ba fadila tana ban hakkuri har muka koma hiran hjy da take nuna min kauna kamar ni din jinin tace. Na,imace ta shigo part dina tana fadin hjy fa ba lafiya an tafi da ita salati muka saka fadila na fadin yanzu fa muke nan tare da ita. Falon muka fito muka samesu zaune zugun zugun anan suke labarta muna dan abinda ya faru muna jimame tare da tamtaman hakan. Allah ya taimaka ba a kwantar da ita ba bayan yan aune da sukai mata suka bata magani da sallama. Bayan sun dawone kula da hjy ya dawo kaina nake kula da ita da komai dani da fadila yayin da shi kuma bai zama gidan sai dare sosai yake dawowa. Ranan naji yaya mamud na fadawa hjy zasu koma Nigeria jibi jin hakan danayi yasa nima na fara shirya muna tafiya. Fadila ta fahinci hakan ta sameshi ta fada mai don kada tayi laifi a wurin shi bai iya min magana ba don abinda ya faru mami ta kara daukan fushi dashi sosai da bai taba tsamani ba don ko ya gaida ita yakai bata karbawa yanzu ko gaban waye. Don haka yaje ya samu yaya mamud don yai min magana ina daki zaune sai ga ya mamud din yazo nan dai yake ban hakkuri yana fadin. Tunda yace da zaran na gama karatu zai zo damu Nageria don haka nayi hakkuri idona ya kawo hawaye nake fadin ya mamud kasan ya dai fada ne kawai . Sau nawa yake zuwa gida bai je damu ba sai ya dawo muke sanin gida ya tafi ai dolen shi yazo gida don mami dake fushi dashi yace . Muddin yana son albarka ya gama da duniyan nan lafiya dole yazo su shirya da mami din. Dole ba don na yarda ba na bar zancen tafiyan muna kallo suka kwasa suka koma bayan ya cika yan uwan shi da abin arziki kaf da suka zo sai mami da jamal ne sukaki karban komai nasa. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN NAN NA KUDINE DON ALLAH KI BIYA MU FITA HAKKIN JUNA DANI DA KE YAR UWA, , , , , Gidan shiru kamar ba kowa tun bayan tafiyan su ashe mutum rahamane sosai don duk yadda nake dasu sai gashi na koma ina kewan su. Ina dakina kwance don tafiyan dare sukayi ranan tunda muka dawo daga rakiyan su na shige daki ban kara lekowa waje ba har dayan rana. Yunwa ya fitar dani na sauko nan ma babu kowa wurin a lokacin dakin su na nufa na tura na shiga. Na hangosu saman gado kwance ba barci sukeyi ba sai dai sun kwanta shiru a lokacin ba wai hira sukeyi ba. Sadiya tana kallo a wayana ita kuma fadila tana kwance ta kurawa rufin dakin ido tana tunane. Kin tashi Fadila ta fada tana dagowa daga kwancen da take nake fadin eh dama ba barci nakeyi ba ina dai kwance ne. Abinci fa ta tambayeni nace shina sauko ci zama nayi a dakin ta kawo min abincin na dan ci muna hira. Itace ta sako zancen su tana tuna yadda hankali ya tashi da ciwon hjy kafin ta koma hiran yadda hankalin mami ya daga akan su koma gida alhalin basu gama kwanakin da zasuyi ba a nan. Bandai yi magana ba sai murmushin da nakeyi kawai ina jin raina yana matukar baci sosai ga hiran da take min din a lokacin. Nan dai na zauna a dakin har lokacin sallah yayi na mike na koma dakina bayan na idar da sallah kuma ba sake fitowa ba falon saida dare da zamuci abincin dare. A takaice dai bamu hadu da yaya ba sai bayan kwana biyu da tafiyan su ranan ya samemu a falo zaune duk suka shiga mai sannu da zuwa. Yanayin shi kawai na kalla nasan a buge yake yashawo maye don ko wurin hawa sama saida ya dan tsaya kadan kafin ya daure ya hau sama din. Binshi nayi da kallo zuciyana tana wani irin tafasa kafin in mike zuwa part din na sameshi a yadda ya shigo din kwance shame shame saman kujera yana barci. Saida na kare mai kallo na duka wurin kafan shi ina cire mai takalman dake kafan shi saye baiko tsaya ciresu ba. Ya dan bude idanun shi a daidai lokacin dana fara cire mai takalman a kafan shi yana fadin wai meye hakane kin dameni fa yarinyar nan. Kai na girgiza ina zare mai safan kafafuwan shi na mike dasu zuwa inda yake aje takalman daya saka kafin a goge mai a mayar. Wanan ba aikina bane yana da mai gyaran dakuna a gidan yasa ban wani damu da inje in masa wani aiki ba a dakin nasa. Na sake mai gudun AC din falon don yayi saurin farfadowa da wuri sanan na ja masa kofan na fita zuciyana na cike da tsanar sa. Daki na na shiga ina tunanen zancen hjy a gareni da take fadin yar nan ki taimakawa mijin ki don Allah badon mu ba ko uwarshi dake nuna maki rashin kauna taimako zakiwa addini ki zauna dashi. Zan samu lokaci mu zauna dashi kan matsalolin ku saidai hakan ba zai samu ba sai kin hada da hakkuri cikin al,amarin. Hawaye ne yazo min dana tuna da wanan nauyin data dora min wanda ta rantse datun farko tasan da halin sa ba zata taba yarda ya aureni ba. Yanzun kuma data sani din iya taimakon da zamuyi mai shine addua da saka ido ga wasu abubuwan da yake aikatawa koda yin hakan zai ja mana matsala a tsakanin mu. Shine dalilin gwada hakan da nayi yanzu bayan na fahinci a buge ya shigo gidan ke nan don baida niyar daina hakan alama ya nuna. Haka na kwana a cikin bakin ciki washegari inda na idar da sallah nan na kwanta sai barci don ban samu barci da dare ba saboda da tunane. Haka ya shigo dakin ya sameno kwance kasa ina barci a takure ya dan dade tsaye yana kallona kafin ya juya zai fice daga dakin. A lokacin na bude idanuna don nauyin mutum danaji a kaina tare da gyara kwanciyana shi nagani zai fita jin motsina yasa shi juyowa. Baiyi magana ba ya sa kai ya fice dakin da sauri kamar wanda aka kora yayin da ya barni da mamakin abinda ya kawo shi dakin lokacin. Saida naga fitan shi na mike da sauri na zauna ina dan dube dube a dakin banga komai ba na sauke ajiyan zuciya. Wayana dake saman gadone ya dauki kara lokaci guda na mike zuwa inda wayan ke ruri na dauka bakon lamba daga Nigeria ake kirana dashi da mamaki nakai wayan a kunne na. Muryan mami ne ya daki kunuwan nawa tana amsa sallaman da nayi saida na dan daga wayan daga kunne na a cikin mamaki. Na mayar ina sauraren ta tana fadin mun sauka lafiya zainab nace Alhamdullahi mami ya gajiya ya sauran yan uwa da gajiya ta amsa a sake da lafiya lau zainab. Ya kowa nan wurin ku kuna dai lafiya ko nace a cikin dan dari dari da ita lafiya muke to ki kara hannkuri don Allah zan kara kiran ki idan mun huta muyi magana a kan mijin naki kiji ko ? Nace to mami nagode kiyi hakkuri kinji komai yai farko yana da iyaka insha Allahu ta fada a sanyaye na kara fadin na gode mami. Bayan ta kashe nabi wayan da kallon mamaki ina rayawa a zuciyana yau ni mami kewa magana a tsigar lalashi haka ? Nan ta barni da tunane barkatai a raina karshe na mike na shiga bandaki na watsa ma jikina ruwa cike da mamakin mami a zuciyana. Don koda zata wuce wanan kalman ne muka rabu dashi na don Allah na kula na kara daure koma zai zo da sauki insha Allahu. Ina zaune gaban mirrow nake wanan tunanen sai ga wasu hawaye masu dumi suna gangaro min a fuskana nasa gefen hannu na share a hankali. Ina ayyanawa a raina cewa ni kuma nawa kaddaran ke nan auren dan luwadi mai bin jinsin shi ya gane me a hakan da yakeyi wai. A take naji wani itin ysanarshi ya kara mamaye min zuciyana na mike zuwa wurin kayana ina dauka naji an shigo dakin. Dan juyowa nayi shine ya shigo dakin a cikin shirin shi yayi wanka yasa tufafi a jikin shi yayi wani irin kyau da kamala zakace wani musulmine da tsoron Allah ya gama ratsashi. Kallo daya nayi mai na kawar da kai daga kallon shi hakan bai hanashi karasowa inda nake tsaye ba. Saida yazo gab dani ya ja ya tsaya yana fadin zuwa gobe ku shirya zamu bar gidan nan mu koma wani unguwa. A raina nace at list ai zaka fada min da wuri don mu shirya amma ba haka kwatsam na inji wai gobe zamu bar wanan gidan zuwa wani wurin. Saidai a fili ce mai nayi Allah ya kaimu kawai ya juya zai tafi sai kuma ya kara juyowa yana fadin uafin ku kawai da kuke so zaku dauka . Naji na fada yasa kai ya bar min dakin na sauke ajiyan zuciya ina mai godewa Allah dayasa na rage kayana da yawa na tura gida. Don hjy nabawa ta kai min gun innan mu don ita sakon zaifi saukin kaiwa a wurin don a kaduna take zaune. Saida na gama shirina na fito falon zama nayi don inci abinci na samu irin girkin mu na yan Africane aka girka don girkin fadila daban yake da nasu idan tayi. Zama nayi naci abincin sosai na turo ban kai ga dagawa ba fadila ta fito daga daki su tana fadin ashe kin fito yanzun nake zancen ki a raina ai ko kin tashi ? Na tashi na bata amsa, sai ta dago kai ta dan saci kallon idanuwana da sukasha kuka tun a dare don tana saurin gane hakan idan har nayi kukan . Zama tayi a gefena tana fadin kuka dai ya zama maki sana,a madam ya kamata zuwa yanzu kin saba da halin mijin na ki ai don shi bai dauki abinda yakeyi yanzu a bakin komai ba tunda yana cikin masu irin wanan dabi,an. Da ace a gida Nigeria yakw rayuwan shi don dole yabar wani abin daga ciki saidai kash yanzu kan taro shi sai Allah gaskiya don yayi nisa sosai a cikin bata. Ba yaya yasani kuka ba mamice mukai waya da ita da safen nan da sauri tace ba dai laifi kikai mata ba kuma na girgiza kai kawai tare da fadin hakkuri tabani kawai kanshi. Anzo wurin ke nan ashe yanzu ta daina ganin laifin ki kan danta tunda ta gane gaskiya dama ai tasan gaskiya tunda ita ta haifi abinta. Na mike tsaye don barin wajen ban son zancen yayi nisa kafin na juyo ina fadin yace gobe zamu bar gidan nan fa don haka mu shirya kayan mu a yau. Gobe goben nan dai ta fada da mamaki nace haka ya fada dazun da zai fita tace ikon Allah shidai haka rayuwan shi take daban dana kowa . Bahagon rayuwa dai ko dan wani abin da sani yakeyin shi don bai dauki mutane da muhinmanci ba a rayuwan. Sadiya da aka fada mata sai murna da farin cikin komawa sabon wuri takeyi a fili da murrnan ta tacin min daki na rasa meke min dadi a lokacin. Don Allah ya gani nasan wanan komawa gidan da zamuyi da biyu da uku zai canza wurin don wanan din ma da muke cikinsa ba laifi don in a Nigeria muke cikin sa sai ya zama gidan kwatance a gari. Yayan mu ashe mu bar gidan nan cikin washe baki take tambayana haka na kallota ina fadin kinji dadin hakan ke nan ke ? To ai abin murna ne ya samemu baki daya tana kaiwa kwance take wanan maganan nace eh abin murna kan ya samemu sadiya dake da maigidan ko ? Don zamu koma can yayi bushashan da yake so yanzu idan nan na saka mai ido haka na damun shi. Sam na manta da sadiya nake wanan maganan sai naji tace dani ba gidan sa bane yaya komai zaiyi yaje yai tayi balle ni banga wani abinda yakeyi ba ma. Sadiya ki fice min daki tun kan ranki yakai ga baci yanzu na fada a hasale ina shirin sauke haushin daba nata ba a kanta kamar yadda uwa wani lokaci takan sauke haushi kan diyan ta idan ranta ya baci. Falo ta koma ta zauna tana fushi har ya dawo ya sameta a wurin yanayin ta ya kalla kawai ya gane akwau abinda ke damun ta. Ciki ciki ta gaidashi tana kawar da kai ya amsa har ya wuce ya dawo yana fadin sadiya yau ya akayine na ganki zaune ke kadai ? Ba komai ta fada ciki ciki ya tako har inda take ya zauna kusa da ita ya sake fadin fada min mana yar kanwata waya taba min ke a gidan nan kuma ? Yayan muce ta fada a sanyayye tana son yin kuka mai kikai mata kuma kukai fada ta sake fadan ba komai don kawai naji anty na fadin wai gobe zamu bar gidan nan shine shine ta kasa fada. Shine me ya riko hannun ta yana tambaya shine tace wai ina murna don kawai zamu bar nan don na taya ka yin bushasha da kake so a can ? Meye bushasha kuma ya tambaya da mamaki ta dago kai tana fadin nima ban sani ba haka dai ta fada ta koroni wai zata bata min rai. Mikewa yayi ba tare dayayi magana ba zuwa part dina ya turo kofan ina zaune bakin gado na tsurawa kasa ido ina tunane. Na rasa meye damuwan ki zainab duk yadda nake son mu rabu lafiya dake naga baki fatan hakan ke ? Kai na dago ina mamakin dalilin wanan maganan yaci gaba da fadin meye bushasha a canza gida da har zaki zauna kina fadawa yarinya kamar sadiya wanan maganan ? Ita ta fadama nace hakan nacene don bansan uban da takewa farin cikin don za ka canza gida ba ? Idan ke baki farin ciki da hakan ki bari ita tayi don naga sadiyan tafiki wayau ma tunda ita yadda aka ajeta haka take bin abu. Bazan taba bin karya da halaka ba saidai idan kasheni zakayi don ka fada dama zan saka kaina ga halaka idan nace sai nabi su mami ai. Kai ya girgiza tare da fadin ni ban taba kashe ko dabba ba balle mutum idan ma haka kike tunane gareni. Rashin inmani ai yana saka bawa yayi komai a rayuwan shi matukar ya fara kaucewa maliccinshi komai ma zai iya yi ai. Shirme ke gareki zainab ina daukan ki yarinya da tasan kanta ga hakkuri da juriya ashe ba hakan kike ba ke ? Zan iya jurewa a kan komai amma ba akai laifin da Allah zai tambayeni ba ranan hisabi wanda bani na aikata hakan ba kawai laifin wani ya shafeni. Wani kallo yayi min na dan kasheshi da idon rashin kunya na dan lokaci kafin in dukar da kaina kasa . Nasan da ace ba ya jafar bane nakewa wanan rashin kunyar haka da andade da jin mu da mai shi ko. Amma sai inyi mamaki zan masa abinda bai dace ba saidai ya kalleni ya kyaleni hakana ya fice don a kullun muka hadu sai munyi fitina kan abu daya kuma yaki dainawa shi. Yanzu kan tunda na kara dab shekaru na fahinci waye jafar din na daina tsoron shi sam a raina duk da ina dan dari darin shi ga wani abu idan bai shafi irin halaiyan rayuwan shi ba wani lokaci. Yana fita na kuta don sadiya ta kaini iyaka yanzu banda daman yi mata fada sai tayi dalilin daya sani yaji yayi magana a kansa don hakane na shirya mata tsiya kan hakan. Yan tufafina kawai na hada a cikin jakkunan tafiyana sai takardun karatuna dana dauka baya gasu ban dauki ko cibi ba a gidan kuma ? Don nasan ko gida zan koma iya abinda zan bukata ke nan a yanzu don haka banba kaina wahala ba . Sai dai da safe da yace idan akwai wani abinda zamu so zamu iya dauka don duk fitar dasu za,ayi don wani ne zai zauna a gidan na kasa dashi a wurin aikin su. Nan na fahinci wanan sauyin gidan daga ma,aikatansu ya taso ke nan don haka na yanke shawaran kiran Maya da take kawata don na fahinci itama irin mune masu karamin karfi a kasan. Kwatance nayi mata tazo gidan ta dauki duk abinda ranta keso tana murna ita kan da farin cikin hakan mota guda ta hada na kayan zuwa kauyen su da baida nisa da cikin garin sosai. Sai da yamma yazo muka dauki hanya tafiya mai dan nisa da unguwar da muka baro din ya kaimu wani hatsabibin gida na zamani wanda kamar ba hannune ya gina shi ba. Tsayawa fadin tsarin gidan bata lokacine don kowa yasan yadda chaina suka kwarai a wurin ginan su komai na zamani akwaishi a wanan gidan don ni abin har tsoro ya bani sosai. Kamar yadda na zarga haka dinne ya faru don part din mu daban nasa daban a wanan gidan don haka zaici kareshi ba babbaka a wanan gidan. Don ko kattai goma ya kawo ba zamu taba ganin su ba sai idan wani abu yakai mutum ya gani ga filin parking babba ga motoci a je a wurin. Ga swimming pol mai kyau dashi ga wurin kiwon dabbobi can daga gefen gidan ganin haka sai kawai shima kanshi jafar din ban yarda da rayuwan shi ba gaba daya yanzu. Har wani aiki yake masu yake samun wanan mahaukatan kudin haka a kasan mutane don ni in an barni zance wanan arzikin gaskiya da biyu. Ban kara tsorata ba sai da muka shiga part din da yace shine namu ana saka muna kayan mu tsoro ya kara kamani sosai. Haka muka kwana sabon gidan namu mai cike da abin aljabi a cikin sa wai matashi mai shekarun jafar ne mamalakin wanan katafaren gina irin haka. Komai na gidan kan sai masha Allah ba a maganan wani bincike don fadan daya fi karfin ka sai ido don haka na raya dare ina kai kukana ga mahakicina Allah don neman tsari ga wanan gidan dashi kanshi mamalakin gidan a yanzu. Da part din mu da nasa akwai katon falone gidan ne dayaji kayan alatu a tsakiya namu da nasa shima mai hawa biyu ne ginan saidai akwai bambaci sosai a tsakanin mu da wancan da muka baro. Sannu sannu har muka fara sabawa da wanan gidan mai girma da ban tsoro duk da akwai tsaro sosai ba wani abin daga hankali a gidan. Mu kanmu in ma cigaba ya samu ko wani daukaka mun sani don daula kan muna cikin sa sosai saidai hakan duk ragage ne a wurina. Na daya da ace a gida muke cikin yan uwa hakan zai fi muna dadi don ko banza zaka taimakawa wanda ma baka da alaka dashi a can sabanin nan da kowa ta kasa yakeyi ba ruwan wani da wani don makwabtaka duk da unguwar da alama ba mabukata sam. Sai na biyu wanda duk wannan daulan bai tsone min ido har in manta da addinina ba da al,adana na malam bahaushe don kullun zaka ganni saye da dan abinda zai rufe min tsiraicina wanda hakan ke min kariya ga duk narazana da iya shegen yan kasan da suke fama dashi. Zan iyacewa Maya ce kadai wace nake hurda mai zurfi da ita don akwai yadda sosai a tsakanin koshi don mun karewa juna hakkin addinin mune tun farko wani bai shiga harkan addinin wani idan dan uwa na ibandan shi. Maya kan da ace musulmace gaskiya da akwaita da rikon addini sosai sai dai kash ta kasance mai addinin suce na gargajiya ita. A haka har hutu ya kare muka koma makaranta don ci gaba da darasin mu ba wani sokuni ko walwala a tare dani wanda yasa mayan ta kula da hakan. Har yakai tana tambayana nake ce mata babu komai don ita a zaton ta ni ba matar aure bace saboda zata girme min sosai ga shekaru. Ranan dai nake fada mata cewa nidin ai matar aure ce ta tsaya tana mamakin hakan don bata taba kowo hakan ba a fanta. Take fadin babu wani alaman daya nuna ina da aure ai don komai nawa ya nuna still ni budurwace ai. Da yake akwai yadda a tsakanin mu nan dai na dan bata labarina sama sama muka rabu tana cike da tunen halin da nake ciki din. Na dawo gidane na tar da Fadila kuma a cikin tashin hankali wai danta daya mota ya bugeshi a hanyar zuwa makaranta ya rasu. Ranan mun kwana cikin tashin hankali sosai a gidan don har ya jafar saida ya tausaya mata yana zaune a part din mu yana bata hakkuri. Haka yasa tafiya zuwa Nugeria ya kama fadila din zata tafi ta barmu ke nan na dan wani lokaci kilama ra tafi ke nan ba zata dawo ba kuma. Yanzu kam hankalina ya kara tashi sosai dason komawa gida dama itace mai debe muna kewa gashi itama din zata koma gida. A cikin sati biyu ya gama mata shirin tafiya rana kan nayi kuka sosai ina ji dama ace nice zan tafi gida ba wani ba. Baki ta fara bani tana fadin inyi hakkuri kada hakan yasa in sare in hakkura nagama karatuna kamar yadda yace tunda saura kadan ingama ai. Don yanzu idan na koma gida ban karasa ba duk wahalan danayi ya tashi a banza amma a kalla in na kare karatun in ma rabuwa zamuyi ina da riban dana samu a wurin shi ai. Tace nasan kina cutuwa da yawa zainab amma hakkuri baibar komai ba da rokon Allah nima nayi maki alkawarin zan dinga maki adduan akan wanan matsalan naku insha Allahu. Da irin wanan ban bakin ta kwantar min da hankalina yasa aka kaita airport sai Nigeria ta barmu da halin mu a chaina mu kadai sai Allah. Sam na manta da muyi wani zance da maya ranan muna hira take cewa dani tana son in samu lokaci in kai mata ziyara kauyen su don akwai abinda take son tataunawa dani a can amma fa idan na yarda. Don tana son ta hadani da wasu kakanintane akan matsalana da mijina wanda tana son ta taimakeni a rayuwan ta itama kamar yadda nake taimakonta tun haduwan mu. Shiru na danyi kafin ince ta bari in fadawa mijina zan kai mata ziyara tunda yasan muna tare da ita sosai a school. Tace ba matsala idan naga hakan ba matsala zan iya fada mai niko hikimar yin hakan kada inzo in tafi bada sanin shi ba wani abu yaje can ya sameni bai sanda zuwana ba can. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE YAR UWA DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA PLEASE, , , , , , . Duk da gakiyan data shana hanya hakan bai hanata shiryawa don zuwa garin zaria ba don da ba wani lalura a gabanta yadda tayi wanan tafiya da tana kwance a wanan lokacin tana hutawa. Saidai wanan tafiyan yasha bambam da sauran tafiyan data sabayi a kullun don tafiyane na bashiri da ya risketa zuwa zaria din unguwar kusfa. Gidan wani dadtijo data samu labarin shi a wurin sharan aikin sosai kamar yankar yuka don da wuya yayi aiki ba ai nasara ba akace. Shine dalilin daya tayar da mami tazo kaduna cikin gagawa don hankalinta a tashe yake har wanan lokacin da tazo kaduna din. Duk da mutanen da suka cika mata gida hakan bai hanata fita zuwa inda tayi niyar zuwa ba saidai wanan tafiyan daga ita sai yayan ta zasuyi shi bata yarda kowa ya bita cikin makarabanta ba don tafitane na shiri zasuyi kan abinda ya shafi rayuwanta da iyalin ta. Haka ta fito tana ba mutane hakkuri uzuri ya kamata zata tafi unguwa sai ta dawo zata gansu kafin ta wuce. Dole kowa ya hakkuru sai kalilan daga cikin danginta yan naci suka tsaya don akwai abinci da abin sha wadattace da aka girka don zuwan nasu. Nan suka zauna a cikin radhin damuwa suna ci da sha da raha a tsakanin su masu kyashin juna kuma daga cikin su sunayi kamar yadda ake samun hakan a ko wani gidan mai akwai idan mutanen sa sun taru. Tafiya sukayi na dan lokaci tsakanin kaduna da zaria sai gasu garin zaria din da bin kwatance har suka gano gidan malamin da dama yasan da zuwan su garin. Basu tsaya wani bin layi ba don sha,anine na kudi akai masu iso suka shiga inda yake ganawa da mutanen sa. Tare take da ya mamud sai jamal dasu kawai tayi wanan tafiyan don ko jalal da Aisha basu san abinda ke faruwa ba har wanan lokacin. Bayan dan bayanin daya biyo baya yayi shiru kamar yana nazari a cikin ranshi yana kallon kasan da ke gaban shi zube a cikin wani katon katako. Ga tasbaha a dayan hannun shi yana wani irin ja a cikin sauri yana kada kai suna gefe zaune sun kura ma abinda yakeyi idanu. A sanyayye ya dago kai yana fadin lalai kunzo da babban al,amari mai wuyan sha,ani don gaskiya abinda nagani abune mai wuyan magancewa da sauri. Saidai shi addua da sadaka baibar komai ba don duk yadda abu yake wanan suna rage karfin abu don ba abinda ya gagari ubangiji balle an hada da addu,a ga sadaka. Musamman ke uwa kece ya kamata ki dage a wurin nemawa wanan yaron mafita daga fitutunun nan na duniya da suka taru sukai mai yawa a kanshi. A yanzu mu maluma mun daina fadan sanadin abu don irin rigiman da abinda muka gani yake haifarwa daga baya. Saidai wani hanzari ba gudu ba a wanan zancen ga wata yarinya dake tsaye fiye da kowa ga wanan zancen yar fara mara jiki sosai . Don tafi kowa shiga damuwa da kuma yawaita yin addua a kullun kan wanan dan naki wanda a yanzu ma kiris take da samuwan warakan wanan al,amarin . Saidai akwai dan tsaiko da wasi wasin yin hakan a zuciyar ta amma dai bari mu gani ya kara share kasan dake gaban shi yana dan wani tabe tabe a cikin kasan kafin ya nisa yace. Bari dai mu gwada wanan dinbdon zan iya cewa ba tabbas a cikin lamarin yarinyar a yanzu don haka akwai yadda za ayi aike yaje gareshi.. Allah gafarta malam bamu dade da dawowa can kasan ba duk bamufi sati daya da dawo ba wurinsa yanzu. Zaiyi wuya yanzu wani ya koma can din tunda har kasan chaina yake zaune tare da iyalin shi. Tsohon yace na,am to idan har hakane yanzu sai dai aiyi aiki mai kama da aike a gurin shi zan baki addu,oi da zaki dinga yima safe da marance . Zaifi kyau ace yasha wani abu daga cikin abinda zamu hada mai ya shiga cikin sa don ya ratsa jikin sa. Ya mamud ya karbe da fadin malam zaizo nan kasan saidai ba lokaci amma munyi dashi zaizo ba dada dadewa ba in Allah ya yarda. To duk lokacin da yazo din zaku iya kawo shi nan don akwai maganan da nake son muyi dashi ido da ido dashi. Nan dai ya basu abinda zai basu suka fito suna godiya har lokacin ran mami ba dadi don ita tafi son ayi aikin gagawa wanda zai dakatar mata da dan nata daga aikata duk wani abin alfasha. Ga tsohon kamar yana da magana a bakin shi don yace ba zai fada mata dalilin shigan dan nata wanan halin ba yayi mata magana ta baibai data kasa fahinta sai juya zancen take a cikin ranta har suka shigo garin kaduna. Ta samu gidan nata a cike da mutane kamar yadda ta barsu kan ta tafi yanzu ma haka ta samu gidan saidai yau yan zuwa wurin nata sam basu ganewa hjyn tasu ba don fuskanta babu walwala. Haka take amsa masu gaisuwan su tana wucewa don jin kanta takeyi kamar ba ita bace saboda damuwa da yayi mata yawa sosai a lokacin. Saidai ganin anty Safiya tare da yar uwanta yasa ta dan ja ta tsaya tana fadin Safiya ina kika shige kwana biyu bamu haduwa ? Jin hakan da gani da anty safiya tayi mami tayi mata magana cikin sakin fuska da hahaba a cikin mutane wanda rabon data samu ganin sakin fuskan mami wurin ta tun faruwan rikicin auren mu da jafar ta daina sake masu fuska haka yasa mijin ta cewa ai ba dole bane ta rabu da ita mana idan ta sauya mata. Basu daddara ba yanzu ma suka zo yi mata sannu da zuwa don kawai wai tana gaba dasu suke mata biyayya a cewan su. Don mami ta kasace mace ce mai yawan aikata alheri shiyasa ake yawan zuwa wurinta da zaran anji tana gari har wanda bata sani ba suna zuwa da koken su. Har ta wuce kowa sai kuma ta juyo don ganin anty safiya da hannu ta nunata tana fadin ke wai kina kasan nan dama. Ba anty safiya ba kowa dake wurin yayi makmakin hanka a yadda ta shigo bata kula kowa ba sai ganin anty din ta dan ja ta tsaya. Ita ko anty safiya mamakine ya kamata sosai ganin yau yadda ta tsaya ta kulata a bainan jama,a sabani tun lokacin auren mu da ya jafar data tsani kowa nawa harda anty din data kawoni wurin ta. Tana ganin itace sanadin komai a lokacin yasa ta rufe da ita gaba daya wullakanci iri iri sun sha shi wirin mami har suka gaji suka dauke kafansu a wurinta. Yanzu dai di sunzo ne don cewa da akayi bata da lafiya tunda ta dawo chaina gashi kuma tazo garin kaduna sukace bari suzo su gaida ita kunsan abu ga maishi. Da hannu ta yafutu ta tana ci gaba da tafiya da sauri anty din ta mike tabi bayan mami din suka shiga part din ta tare. Safiya kin dauke kafan ki ko nazo garin nan yanzu baki zuwa ko wani abin ne ya faru tana zama take fadan hakan tare da cire gyalen data yafa a jikinta lokacin. Anty safiya tace bawai hakana bane aiko ina zuwa wani lokaci dai bama ganin kine ko munzo. Ok ta fada tana daukan wayan ta tace Ramatu akawo min abinci mana su mamud ma na part din shi akai masu nasu ta dago bayan ta aje wayan tana fadin. Diyarki ce ko kanwar ki tana can yanzu idan kinganta ai ba zaki ganeta ba ma don gaba daya ta canza wallahi . Ikon Allah suna dai lafiya anty ta fada tana gudun ta fadi wani magana tayi baranbarama a gaban mami din. Mami ta amsa a kasalance lafiya kalau halan baku waya da itane yanzu ta fada tana dago ido don kallon anty din . Ina ganin bata da layina nima haka don tunda suka tafi bamuyi waya ba gaskiya don yadda na falfale ta akan auren kamar yadda kika umurceni in mata din. Kai ai komai ya wuce yanzu suna can zaune kalau abinsu sai karatun da takeyi tana gab da gamawa yanzu haka da munzo tare ai taga gida don sun dade basu zo gida ba, har kanwarta da suke tare a can. Au da yarinyar ta tafi ashe gaskiya jafar yayi kokari sosai Allah dai ya saka da alherin sa don ba karamin kokari yayi ba yin hakan. Aka toro kofan mai abinci ta shigo da abincin mama Ramatu na biye da ita a baya suka sauke abincin saman dan table din dake karamin falon. Tare aka zuba masu da anty sai wani kallo mama Ramatu ke bin anty Safiya dashi duk da tagani bata damu da hakan ba. Kowa yayi mamakin jin a ranan zasu koma ashe karfe nakwai na dare saida ta gana da wasu daga cikin jama,an wasu kuma aka basu hakuri sai gaba. ANCHAU Gidan namu yana nan har yau da fitinan shi kamar kullun duk da an raba shiya yanzu amma haka bai hana Lantana takowa har wurin inna yin fada . Abban mu yayi warning dinta kan hakan bata daina ba ya kawo ido ya saka mata, dan gara ma yanzu don Sa,adatu na taka mata burki sosai idan tana gida. Saidai duk da raba shiyan bai hana lantana saka ido ga shige da fice a sashen inna din ba don takan dawo barandanta ta zauna tana kallon abindake wakana a gidan . Don yanzu inna nada katon fridge har biyu da take sana,a dashi kankara a wurinta ko wani lokaci mutum yazo zai samu dayan kuma ruwane da zobo mai sanyi da sukeyi dan kobon kashi na shigo masu . Duk wanan aikin nasa ne da yakeyo masu aike a kai akai ba tare da sanina ba saidai inna ta fada min ko sa,adatu a waya nake sanin yayi masu aike wani ma banji sai daga baya acikin hira da mukeyi dasu a waya wani lokaci. Motan su hjy ne ya tsaya a kofan gidan da sauri lantana tacewa karamin danta kai dan baba jeka kofan gida ka duba ko Abban kune yayi baki don naji mota ya tsaya a kofan gidan nan. Yaron ya ruga da gudu zuwa dubawa ya dawo yana hakki yana fadin motace mai kyau mama wata tsohuwa ce a ciki tafito. Ta mike da sauri tana fadin ina kuma muka samu tsohuwa mai mota kodai wani gidan suke nema sukazo nan din don bata sai sallaman hjy sukaji ta shigo tana tafiya da kyar don kafanta. Kicibis sukayi da Lantana a kofa dake sabe da diyarta datake goyo don yaranta mata biyu yanzu data haifa bayan wancan da namiji din na farko data haifa. Tana da namiji daya innan mu nada maza biyu yanzu itama saidai inna ta fara kiran auta kan wanda ta yaye din. Tsaye tayi sororo tana kallon tsohuwar dake kwada sallama tana fadin gidan ne kuwa don gaba daya wurin ya sake mun ? Asbe dake can tana jin tun lokacin da lantana ta tura yaron ta ta fito tana fadin maraban ku ku karaso daga ciki. Lantana sai fadi take kina ta karaso kinsan wanda tazo nema kilafa ba gidan nan sukazo ba ai ko ba nan bane mutum ya shigo ka taresa ko ? Hjy ta taka har zuwa cikin part din Asabe din suka gaisa bayan tayi mata taro na arziki saida hjy ta dan sha ruwan da Asabe ta kawo mata ta aje kwanon take fadin daga wurin su zainabu nake takwara na dake kasan wajen. Asabe batayi saurin gane wa hjy ke nufi ba saida ta kara mata bayani da cewa yar gidan nan dake aure a Abuja nake nufi yanzu suna zaune a kasan waje ita da kanwarta uwarsu nake nema ? A, a daga wurin su Abu kike ashe tana gyara zama tana tambaya kafin tace madalla da wanan zuwan naki kuwa ga gari ya dauka mun sayar da. Abune da kanwarta wa mai kudi. Yanzun hakama basa raye an kashesu su biyun, ba kowa ya yayata hakan a garin nan ba nan ne Lantana duk tabi garin nan ta bata muna suna da wanan zancen saboda bakin kishinta na banza. Zainabu kan tana raye karatune ya tsayar da ita yasa baku ganta ba kwanan nan muka dawo daga wurin su duk tace a gaishe ku. Ai haihuwan diya mace ke nan babban arzikine a yanzu don aure ba inda baikai mace a duniyan nan sai kinyi kwana biyu a jirgi kafin kikai garin su. Tana kokarin mikewa don kukan da taga Asabe ta fara take fadin kaini naga uwarsu bana son tafiyan dare shiyasa muka dako safiyan nan haka. Asabe ta mike suka fito har lokacin lantana tana labe sai bakar magana takeyi dun kawo tsakar gida take fadin indai da kwadai da wullakanci . Da anga bakin yan birni sai hankali ya gushewa mutum wurin kwadai kai kawai hjy ta girgiza duk Labarin lantana da nake yawan bata ba karya a cikin sa ko kadan don ta sheda hakan yanzu. Sun shiga wurin inna sin samesu a falon su zaune ga dakin na kamshin turaren wutan kajiji da karo data saka don sanyin damana da akeyi. Wanda yana cikin sirin mata da can baya wanda mata a yanzu suka daina amfani dashi don rashin sanin muhinmancin hakan . Akwai wani sirin boye da ke akwai a cikin kajiji da karo wanda ba kowa yasan da wanan sirin ba sai matan da suka amsa sunan su ko a baya suke yawan amfani da wanan sirin a dakunan su. Akwai haske da kwar jini ga kariya ga both uwa da yaranta wurin amfani da kajiji da garin karo da mata keyi a da can baya. Don mace mai amfani da wanan gaskiya idan kin tambaya ba wani farmakin kishiya ko dangin miji ko makwabta da zai iya farma ki ko danki don akwa kariya sosai a wanan sirin . A wurin miji kikan zama mowar mata do zaki zama zara a duk inda kika dosa balle ga mijin ki na sunna. Hjy na shiga dakin ta dan sake murmushi tana girgiza kai don ganin inda na koyo tsabta da hakuri da sanin wasu sirika da take gani a wurina. Sun zauna an gaisa sa,adatu ce ta fara tambayana take fadin muna lafiya satin nan daya wuce suka dawo daga wurin mu ai. Nan dai ta shiga basu labarin mu da karatun da mukeyi a can chaina din a karshe tace a fita waje a shigo da sako na nan dana bayar akawo masu. Lantana na ganin ana shigo da manyan kumshin kaya zuwa wurin innan mu sai zama ya gagareta ta shiga sintiri tana leken kayan da ake shiga dasu din har kumshi uku gasu dirka dirkan kumshi dasu. Duk da inna bata sanda zuwan hjy ba hakan bai hana ta dan bata abin motsa baki ba gashi dan wake tayi da mai da yaji hjy ta sake taci sosai aka kaiwa driver da jikanta daya daya rakota nasu. Bayan tafiyan hjy ne sa,adatu ta matsu a bude kayan suga abinda ke ciki dole dai saida inna ta bude suka shiga ihun ganin kayan. Sun kira waya basu sameni ba ina school lokacin don ina kashe wayana idan zan shiga lectures bana shiga dashi a kunne. Nan dai Abban mu ya dawo ya sakesu suna murnan sakon dana aiko masu din wanda tufafi ne sai zannuwan gado da sauran tarkacen mata. Shima Abba har lantana sun samu nasu rabon don na rubuta sunan kowa a cikin sakon sai gashi lantana baki ya mutu a lokacin. CHAINA Zancen mu da maya ya tsaya min a rai don ina tsoro ban san abinda zanje inji ba ko ya kasance sha,anin su na tsafine. Gashi ina ji daga chaina sai indiya a wurin tsafi ni kuma ban son inyi abinda zan kaucewa ubangijina gaskiya. Itama a nata bangaren maya bata kara yi min maganan ba daya shafi wani zancena dashi tun wanan lokacin. Inda shi kuma gogan yanzu ya samu saukin fitina tun bayan dawowan mu wanan gida akwai kofa ta bayan ko wani part ta baya yake yawan bi da mutanen sa tunda ba fasawa zaiyi ba ga halinshi. Wanan ya kara kawo ko in kula ga zaman mu sai dai yana kokarin duk rana zai dan shigo sama sama ya duba lafiyan mu iyakan mu dashi ke nan yanzu. Sai hakan ya kara kawo min kwanciyan hankali duk da rashin Fadila da mukayi mafi yawan lokaci zaman kadaici yakan dame mu don dama da tana nan da ita muke debe kewa ayi ta hira har wani lokaci. Yanzu ko matan da muke tare dasu ba launin mu ba don haka ba ruwan mu dasu iyakan mu dasu sai gaisuwa idan mun hadu saidai akwasu da girmamawa sosai gaskiya. Ga arzikin shi kamar ana zuba mai taki gaskiya ni har abin watarana yana ban tsoro idan ina tunane ni kadai. Ga sadiya baki babu halin in zauna da ita muyi wani magana kamar yadda mukeyi da fadila don sai ince ma tafi daukan shi dan uwa yanzu bisa gani. Shima yana yawan kulata sosai komai ya gani daya dace da ita zai sayo ya kawo mata shi ta dinga murna har nakanyi tunanen wa sadiya ta biyone a cikin iyayyen mu wai ? Abin mamaki ranan safiyan asabar duk muna gida bamu fita ba har shi saidai ba lalai bane ai ya shigo wurin mu don mun saba da hakan dama. Muna zaune falo zaman daki ya isheni ya dawo falon gidan dake tsakiya inda ya samemu ya zauna. Da dan takardan daya shafi karatuna a hannu na dake nazari ya zauna a kusa da sadiya yana fadin yau dai sai ku shiya zamu tafi wani shakatawa tare daku. Hakan da ya fada bausa na dago kaina ba tun bayan gaisuwan danayi masa daya shigo naci gaba da karatuna daya samu inayi. Murna sosai sadiya keyi lokacin ganin ban dago kaina ba yasa shi fadin ina fatan kinji abindana fada ai ? Ina da test ba zan samu zuwa ba itama din tace tana da pratical da zasuyi ai ranan mondaya na bashi amsa ina kallon shi. Fitan da zamuyi din na dan lokaci zai hanaku yin test ko pratical don haka ku shirya karfe uku zamu bar gidan nan ya fada a dake yana mikewa. Kallon mamaki na bi bayan shi dashi har ya shige part din shi Allah yasa ya kaimu irin wurun da mukaje ranan nan mu hau doki. Muryan sadiyace ke fadin haka a gefena na juyo a cikin fushi ina fadin yanzu in mare bakin nan naki sakaran yarinya kawai. Da sauri ta make a wuri daya don in akwai abindata tsana shine duka ganin haka na mike zuwa dakina na barta a wurin zaune. Ina shiga dakin wayana yana kara da sauri na karasa na dauki wayan innan muce ke kirana nasan safiyace a wanan lokacin Nigeria . Dauka nayi da sallama muryan Sa,adatune tana fadin inna na sameta ta dauka naji innan mu na bani wayan nan. Mun gaisa take fadin saiga sako tsohuwan nan ta kawo muna ta shiga saka min albarka wasu hawayene suka zo min lokaci guda har inna ta gane kuka nakeyi. A rude take fadin subbahanallahi meku ya faru dake ko baki da lafiya ne da kyar na iya budan bakina nace inna kalau nake. Gida nake sin dawowa yanzu kuma yaki bari hakan don naso na biyo yan uwanshi da sukazo bai yarda ba. Kanki daya kuwa naji inna ta fada keda ke aure inake ina bin wasu kuma kull na kara jin wanan zancen haka ranki zai baci sosai. Kuka na sakawa inna cikin wayan ina fadin inna na gajine ya jafar ba abokin zama bane wallahi dabi,un shi da halaiyan shi sam ba na mutumin , , , Innace ta kashe layin bata tsaya ta karasa sauraren abinda zan fada ba a lokacin takaicin hakan yasa na fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA DON ALLAH KAFIN KI KARANTA DON SAUKE HAKKIN WANI A KANKI ALLAH YA BADA IKON BIYA, , , , Ba don na soba haka na shirya sai dai ba wani make-up danayi a fuskana riga kawai na zura a jikina na fito falon na samu har sun fita waje ko da uwar zumudi sadiya. A mota na samesu zaune na bude baya da nufin shiga ba tare daya dago kai ya kallon in da nake ba yace dani. Amma kinga ni zan tukaku ai da zaki shiga baya yafada yana gyara zaman shi cikin ko in kulla na dawo gaban motan na zauna na rufo kofan a hasale. Don ni harga Allah wanan fitan haka kawai zuciyana naji baison fitan da zamuyi dashi a lokacin. Juyowa yayi yadan kalloni ya girgiza kanshi don shigan nawa bai mai ba a lokacin sai kuma naji ya furzo iska daga bakin shi tare da shafo suman kanshi da hannu daya ya tayar da mota muka fice gidan. Kida ya saka a motan kamar na yare bandai saurari mai ake fada ba balle na gane haka muke tafiyan har wurin wani taro don na gane hakan ne saboda motacin dana gani a wurin . Saida ya tsayar da mota yake fadin zamu shiga wurin tarom nan ba zamu dade ba don abokinane ke bukin zagayowan haihuwan shi yau. Kai na dan gyada ba tare da in kula dako ya kalloni ba muka fito daga cikin motan zuwa cikin inda ake taron . Sune yan kasan birjit a wurin tun daga waje zaka gane hakan sadiya dake wani shige mai na finciko da karfi tayo baya duk da yajimu bai juyo ya kalle mu ba nace a hankali wallahi ki natsu ki kama kanki a wurin nan kin dai san kasan nan naman mutum sukeci. Sai mu nemeki mu rasa a wirin sun daukeki sun yanka ba wani aiki bane a wurin su don haka kafana kafan ki idan kinji. Na fadi hakane do yadda naga tana zumudin shiga ga wurin sam ban yarda dashi ba tun daga ganin irin mutanen dake wajen da nayi. Take ido ya dawo a wurin mu nasan ba komai ya jawo hakan ba sai kasancewan mu bakaken fata kuma musulmai don abaya na saka sama na rufe kaina da gyalen shi shigar musulunci nayi kamar nasan hakan zai kasance idon ta ya jafar ne baiki na fito kamar sauran matan dake wurin suna shiga kamar tsirara dasu. Tun a kofa aka fara bashi hannu wani irin gaisuwa da akeyi wurin zai daurewa mutum kai don in dane sai ince gaisuwan kasan ke nan a hakan . Amma yanzu na fahinci komai ba wai dabi,an yan kasan bane wanan gaisuwan haka muke tafiya har zuwa inda taron yake duk wanda nayi katari ya gaida mu sai dai na dan dukar da kai yadda naga yan garin na gaisuwan su. Idanuwa a kanmu sai kuskus da keyi kan shigowan mu din hannu philip ya miko wai mu gaisa na girgiza kai tare da mai gasuwan su na koma bayan yaya na labe sai ya bini da kallo. Duk inda ya saka kafan shi muna biye dashi a baya har wani yazo ya jaye shi ina hangen su suna gaisawa da wasu da nake ganin kamar bakine suka zo saidai shigan su tantiran yan iskane ga sarka ga dankune duk sun saka a jikin su kamar mata. Ganin hakan na kara shan jinin jikina ga sadiya tana makale a hannu na ban yarda na saketa ba. Wani ne ke nufo mu a cikin murmushi har ya karaso inda muke ya miko min hannu yana fadin sunan shi Sam hannun nasa na kalla nace mai thanks kawai ina kokarin kawar da kai sai ji kawai nayi ya rungumoni a jikinshi. Ban tsaya jiran komai ba na daga hannu na kwasheshi da mari kayauuu a fuska Allah ya ban sa,a na samu fuskanshi da kyau ya dafe wurin yana kallona. Haka ya dawo da hankalin mutanen taron kan mu yana fadin pretty kika mareni do kinyi sa,a na kulaki kina mace ? Sai zaran idanu nake a hasale nace dashi how dear torch me ina musulma zaka rungumeni haka kaiba mijina ba ba wani dan uwana ba ? J dinnne ya karaso inda muke wanan maganan ya kalli mutumin yace me ke faruwa ne a nan ? Ya dago idanun shi da sukai ja yana fadin don kawai ta burgeni nazo mata shine ta daga hannu ta mareni kawai yana murza wurin da alama marin ya shigeshi sosai. J din yace kasani ai ita ba karuwa bane ko wata mai zaman kanta addinin mu kuma bai yarda dayin hakan ba don me zaka rungume ta ? Just a hug nayi niyar mata don tana pretty girl ta burgeni kawai amma ban san hakan zai bata mata rai ba ai har ta mareni ? Zuwan abokan shi su uku wurin ya hana J din bashi amsa don har ya dago idon shi jajaye da niyar fadin wani abu suka iso suna rungumar shi. Tare da fadin mai zai sa kayi mata haka kaiko ai kaga shiganta kasan su musulmai ne basu yarda da hakan ba ai dakayi. Yace naga J din kamar shi bai damu da addinin nasu ba don naga baya abinda sukeyi na dauka itama yar hannuce ya dauko . Wani irin hawayen nadama ne suka zo min lokaci guda a idona a hankali na juya na fara tafiya da hannun sadiya dake makale da nawa har lokacin. Fita mukayi daga cikin dakin da ake birthday din ba tare da nasan inda muka dosa ba a lokacin sai tafiya mukeyi babu ko waigawa. Nake jiyo horn din mota a bayan mu sai sadiyane ta iya juyawa naji tace ga yaya nan a bayan mu da mota shi. Hakan baisa na tsaya ba saida naji yace ina zaku tafine ana maki magana kina wucewa naja na tsaya . Ya tsayar da motan yana fadin ku shiga mu koma gida sannan na taka na zagaya na shiga motan ba tare dana kalleshi ba muka fara tafiya bamu san yadda suka karasa a wurin taron ba . Ga wayan shi nata ruri tun dauka daya dayayi ya duba bai kara duba mai kiran nasa ba lokacin sai tsukin da yakeyi kawai lokaci lokaci. A wani babban shago ya tsaya tare da waigawa inda sadiya take zaune yake fadin ku fita kowa ya dauki duk abinda yake so a nan . Shiru motan yayi ba wanda ya motsa a cikin mu ya kara fadin ku fita mu shiga nace daku ko bakuji bane ya fada a dake. Bana son komai gida nake son zuwa kawai na bashi amsa ba tare da juyo inda yake ba sadiya fito mu shiga ciki. Da sauri sadiyan ta girgiza kai tana fadin a, a yaya muje gida kawai nima ban son komai . Kallon mamaki yayi mata kafin yace tsoro kike jine har yanzu sadiya ta gyada mai kai alaman eh. Dama tunda bakiso fita ba nasan fitan ba zai muna dadi ba don kamar na tursasakine kika fito ai da sai ka barmu gida zaifi tunda ka fahinci hakan. Na fada a hankali wasu hawaye na zo min a idona kai ya girgiza tare da bude motan yana fadin da zai fita ko ku fito ko kuma na mayar daku wurin taron nan don ba zaki hanani zama ba . Kizo nan kuma ki tauye yar uwanki dani zabi ya saura gareki yanzu ya fada yana karasa fita daga cikin motan. Dole na fito don ranan ji nake kamar duk zunubi a kaina ya kare don abinda dan arnen nan yayi mun a wurin. Yana gaba muna biye dashi har muka hau lifter zuwa sama ya juyo yana fadin yau kan Sadiya ba zan tayaki zaben komai ba don fushi nake dake. Kayi hakkuri ya jafar tsoro naji kada su kashemu a wurin kaga su arnaku ne duka wurin cewa da abinda na fada mata da zamu shiga wurin birthday din dazun shi ya tsorata ta ashe ta natsu badon Allah ba. Balle taga abinda ya faru dani a wurin ya kara daga mata hankali take ganin kamar gaskiyane abinda na fada mata din. Naji yace tsoron may kike ji kuma Sadiya ba gani ba ba abinda zai same ki ai muna tare kinji. Mun shiga wurin ban dauki komai ba a shoprite din sai faman yawatawa da sadiya sukeyi karshe ma na dawo na samu wuri na zauna har suka gaji suka fito lokacin dare yayi sosai koda muka shigo gida. Sallah nayi bayan nayi wanka nayi ta darazan jikina don ina jin kamar har lokacin indaya tabani wurin yatsunshi dun manne mun a kafada na. Ko a school haka nake komai sukuku dani ba sakin jiki yasa har maya ta fahinci hakan gareni ina zaune cikin zurfin tunane . Naji an dafa min kafada na nayi firgigit na zabura ina sauke ajiyan zuciya ta zauna gab dani tana fadin meke damuwan ki haka zee ? Tun da safe ina hankale dake baki cikin hayacin ki ko kun kara hadewa da mutumin naki ne kuma har kike tunanen hakan ? Kaina girgiza tare da dan dago kai ina fadin abinne ba dadi sister nan dai na labarta mata duk abinda ya faru dani a weekend din . Dan guntun murmushi tayi tare da fadin matsalanki sai kinga native doctor din mu na gargajiya suke da herbal medicine dake kawo karshen wanan case din nasu da sauri harma a manta mutum yayi shi a baya indan an dace. Amma yana da mata kai da zakubi don kada maganin ya baci amma nasan idan kinga kakata akwai yadda za ayi don wani dan uwan mu ya taba fadawa irin case din nan a baya yanzu kuma ya daina ko cigari baya kaunan gani balle giya. Case din homosexual kuma sai dai idan kinje don na bata labarin ki tunkan kizo tana dakon ki a ko wani lokaci don ta tausaya maki sosai kan hakan. Nagode maya da kullawan ki a kaina zanyi kokari na samu time da zamu tafi kauyen tare dake amma sai idan na shiryawa hakan zan fada maki. Haka muka rabu na dawo gida da wanan maganan a raina ba abokin shawara fadila na kira da dare bayan mun gaisa na kwashe yadda mukayi da maya din na fada mata. Saida ta nisa kafin tace zainab wanan damane sosai Allah ya baki kan hakan sai dai gaskiya akwai matsala ga hakan baki ganin idan aka samu akasin hakan abin zai iya dawowa kan ki ? Kindan fa yadda kike da uwar mijin nan naki don haka nake shawarta ki da kidai kara tunane akan hakan gaskiya. Anty ta yaya zan fara tunkaran mami da wanan zancen ai saita dauka ni din watace data iya irin wanan abubuwan tun a gida kamar yadda takan fada min cewa . Nida iyayyena mun iya shige shige muna kammale mutum da dan sa tun kan mu shigo birni wanan zancen ba zan taba mantawa dashi ba a raina don ido da ido tasha fada min hakan. Idan na tuna yana min zafi sosai wanan kalman yanzu kuma in fito mata da wanan zancen ai sai tace hakan gaskiyane dama. To yanzu ke wani shawara kika yanke ga hakan don gaskiya kada wanan daman ya wuce ki yanzu zainab . Don idan kika baro kasan baki gwada sa,an ki ba daga baya hakan zai dameki sosai kuma kinga abin nasa sai gaba gaba yakeyi yanzu. Na sauke ajiyan zuciya tare da fadin zan kara tunane in gani abinda zai yuyu zan kiraki in fada maki abinda zuciyana ya yanke min kan zancen. Dan tsuki nayi don wanan shawaran da fadila ta bani din din kamar ta famamin wani miki dake zuciyana ne lokacin. Don sam ban kawo wanan tunanen ba da farko sai yanzu da ta fito min da zancen fadawa mami din nake tunanen hakan. Kawai banda mafita saina share zancen a zuciyana naci gaba da abindake gaba na. Kowa sai harkan gaban shi yakeyi don ba ganin shi nakeyi ba shima baya ganina sai idan zamu gaisa da safe bayan hakan sai kuma wata safiyan kuma idan yayi zamu gaisa. Ranan ba school don haka na fito don nasha iska saman benen part din mu ina zaune a gurin wanda ba kowa ne zai sanda hakan ba. Da takarda a hannuna wayana na gefe daya aje sai cup din drink's dana aje daga dayan gefen ina dan kurba kadan kadan. Na dauki cup din drinks din na dan kurba kadan na aje kamar ance na dago kaina na kalli kasa sai na hango ya je suna fitowa da Taju daga cikin gidan. Wani irin faduwa gabana yayi yaba da ras ras lokaci guda ban san lokacin dana mike tsaye ba ina mai furta innalillahi wa inna alaihim raju,un. Allahuma Ajirni fi basibati wa,akalillif hairan min ha , . Ina mai runtse idanuwa na kafin in bude in kara fadin La,illah ha illa anta subbahanaka inni kuntun minal zalumin har ban san lokacin da hannuna yakai saman cup din dana aje saman table din ba ya fado ya tarwatse a wurin. Kai ya J ya dago daga inda yake tsaye yana kokarin shiga mota ya hangoni ina shigewa ciki hannuna yana dafe a bakina don kuka. Sam shima baiji dadin hakan ba don bai kaunan in ganshi yana aikata wani aikin da bai dace ba shiyasa ma raba part din da akayi yanzu yai mashi dadi sosai don mun rage samun rikici dashi yanzu. Motan ya fasa shiga ya juya zuwa cikin gida da sauri taju wanda ya riga ya shiga mota ya bishi da kallo kafin ya dago yana kallon saman benen part din mu baiga kowa ba. Haka yasashi mamakin mai kuma ya mayar dashi cikin gidan a wanan lokacin bayan yasan inda zasu a yanzu yana da muhinmanci a garesu sosai. Nikan ina shiga dakin na fada saman gado kife na fara rusa kuka mai tsuma zuciya naji an turo kofan da karfi an shigo dakin nawa. Hakan baisa na dago don ganin wanda ya shigo min saima kamshin turaren shi mai mugun tashi daya ziyarci hancina a lokacin daya yasa na gane shine a dakin. Zainab meke damun kine har zaki so halaka kanki da glass haka baki da hankaline kome ? Ban dago ba sai kukan da nakeyi naji yaja wani irin uban tsuki yana tako zuwa inda nake kwance ina rusa kuka. Jinayi kawai gaba daya ya ficikoni na kwanto a jikin shi lokaci guda nayi saurin kokarin jayewa ina fadi cikin muryan kuka. Kada ka tabani don kai ba cikakken musulmi bane har abokan hurdan ka sun sanda hakan don sun fada a gaban ka suma. Ni din ya nuna kamshi cikin mamaki yana kallona nace kai mana Allah ya kara min tsari da duk abinda kake nufi da daukoni dakayi zuwa wanan kasan na kafirai. Idan har kana tunanen zaka iya juyani na koma kamar yadda kake fasiki ne Allah ba zai taba yarda kaga hakan ba a rayuwan ka, , , Wani irin mari yaso kaimun Allah ya taimakeni na kauce bai sameni ba na samu na kwace a jikin shi ina ja da baya baya. Zainab ni kike kallon idona kina fada min haka ya fada kamar zaiyi kuka ba tsoro nace mene marabinka dasu yaya ? Ai gara fasikin dake neman mata da kai yaya wanda ke fasadi da namiji dan uwan shi ta inda Allah mahalici mu ya hanemuyi koda matayen kuna aurene kuwa. Amma kai don rashin tsoron Allah da karancin addini dake yawo akanka shine ka mayar abin tunkaho a gurin ka kamar ba zaka mutu ka koma ga mahalicin ka ba saboda rudin duniya dake damun ka. Ya kara kaimu cafka a hasale na kara ja baya har na samu na sauka daga saman gadon muka fara zagayan dakin muna fadawa juna bakaken maganganu. Ranan kan yayi mamakina matuka don idan wani ya bashi labarin hakan zai iya karyatawa don ban raga mai komai ba ban kuma ji tsoron shi ba. Karshe nace dashi zan bugawa mami waya tazo ta daukeni don duk abinda ya sameni kaine na kuma riga da na fadawa iyayyena hakan da yan uwanka . Don nasan gab kake daka kasheni a kasan nan don kawai kana ganin ina takura maka kan harkan ka. Ido waje yake kallona yana nunani da yatsan shi yana kallona ido waje ya iya furta zainab ashe dama haka kike baki da hankali da wayau. Ina maki komai da kike so ban ga na rageki da komai ba don kema ki amfana daga gareni tunda nasan kinyi hakkuri da ba kowa zai iya irin sa ba. Ka daina idan ma kana mun ne don yaudara don ni na dade dagane manufan ka a hakan don ka auroni ne nan don ka kawar da idon mutane akanka ace duk zargin da ake fada akanka karyane tunda kana da mata tare dakai ko ? Saida ya kalloni yace cikin girgiza kai tabbas hakane wanda ya fada maki hakan baiyi karya ba zainab . Haka dinne ba wai ba amma sai na dauka zaben ki danayi ga hakan kamar ke din mai rufamin asirine ga wanan kaddaran da kowa ke gudu akansa . Saidai ashe banyi tunane ba don ashe duk mata kalan ku daya da tsohuwa da babba duk daya kuke a wurin tunanen ku. Ke kanki idan kinsan kanki ai abun kunyane ace mijin da kike aure yana hakan don ko ke bazaki tsira a bakunan mutanen da suka sanda hakan ba. Kowa yasan tursasani kayi ka aureni don ko hjy da ace tasan hakan da farko bazata taba mara maka baya in zauna dakai ba zaman da baida amfani a garemu sai tarin zunubi ga Allah. Ya sake girgiza kai ya kalleni zuwa lokacin idanuwann sun kade sunyi ja jajir niko ina tsaye daga kofa ina jiran naga yayo kaina in gudu. Don a tsorace nake sosai dashi lokacin kiris ya rage na ruga da gudu da naga ya haruni din. Shiru yayi ya koma ya zauna yana tunane sam ya manta da zancen wani taju na jiranshi a waje sai can ya dago ya kalleni yana fadin . Babu wanda ya taba mi cin fuska irin wanan a gabana zainab yauni kike kira da kazami fasiki ido da ido. Yo idan ba kazami kake ba me kake fada min sunan ka wanda ke wasa da gidan najasan da yafi ko ina wari a jikin mutum kaga aiko ka bata sosai wallahi kuma da kato namiji dan uwan ka fa. Kina son ayi da kene din in gwada tir tir wallahi dakai ya jafar ka kuna baka tsoron kauri saidai irin ku karshen ku baya kyau don kun kama talala da yawa a duniya. ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GAREKU MAKARANTA WANAN NOVEL TARE DA FATAN SAKON DAKE CIKI NA ISA GAREKU YADDA YA KAMATA ALLAH YA TSARE MUNA ZURI,A AMIN. LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KAFIN KI KARANTA DON SAUKE NAUYI DA FATAN ZAKI FAHINCENI YAR UWA, , , , Fitan da basuyi ba ke nan ranan don zuwa wurin likitan su ya duba taju dake fama da lalura kwana biyu ke nan na wani katon kurji a duburan shi few days ke nan yana fama da wanan cutar. Akwai wani magani da likitan su na musaman yake basu idan sun samu irin wanan matsalan bayan kwana biyu sai abin ya bace wurin ya koma normal. Shine zai kaishi wurin likitan ya dubashi ya bashi yan taimakon da ake basu don kariya saboda shi taju kamar shine mace a wurin J din shi kuma ya J din yana zaman namiji a garesu haka yake wanan rayuwan kazantar dasu shekara da shekaru. Wanda idan baiyi hakan ba da maza yan uwan shi ba baya jin dadin rayuwan shi sam . Zai iya rantsewa bai taba jin sha,awan wata ya mace ba a rayuwan shi da sunan taraiya sai dai ya kalli ya mace da abokiyar shawara ko wani abu. Haka yaso rayuwan shi ya kasance da zainab din don shi Allah yasa mai tausayin diya mace a rayuwan shi don hakane itama zainab din yake matukar tausaya mata sosai ga duk wani lamari nata. Saidai kash bai samu zainab din maiyin biyayya a yadda yaso ta kasance mai saidai ya fahinci yarinyar addini ya ratsa zuciyar ta sosai irin masu ra,ayin rikau din nan ne da kudi baya rudasu ko wani abin. Yanzu ma kalaman ta ya rudashi don yana son ta kwantar da hankalinta ta zauna suyi magana na fahinta don baison abinda zai kara tayarwa mahaifiyar su da hankali. Shiyasa yake son ya bata lokaci ta sauko sunyi magana na tsanake yadda zata fahince shi ta dan jaye wanan furicin nata na fada a gida da tace tayi din don kafa shedan hakan din garesu. Nan ya zauna shiru kanshi na duke a kasa ni kuma ina tsaye a firgice kofan dakin ina jiran tsamani. Har na kai tsugune daga kofan na hade kaina da gwiwa na ina rusan kuka a tsanake cikin tashin hankali bamai sauti ba sosai. Don hakane banji tasowan shi ba zuwa inda nake din sai jin shi nayi ya dafa min kafada na cikin murya mai taushi yake fadin zainab. Kiwa Allah ki daina wanan kukan haka don Allah ke wai kuka baya isan kine ni dake cikin wanan jerabawan yanzu nace me idan ke kina kuka haka ? Kada ki manta a gaban idon ki fa mami ta bar kasan nan tana fushi dani cikin bacin rai ta barmu fa ? Amma kina ganin na kasa daina wanan abin da kuke ganin laifina a kanshi don sabo zainab ya kamata yanzu kifi kowa fahintar matsalana ai zainab. Keda zaki zauna dani muyi shawaran mafita kan fushin da mami keyi dani shine kuma zaki kara hadani da ita kuma a yanzu. Kaina na dago a cikin mamaki nace nice kuma zan hadaka da mami naku bai hadaku ba a yanzu. Indon tanice kayi hakkuri don Allah ka taimakeni ka mayar damu gida yaya kada nima wanan abin ya shafeni don Allah ai muna dauka daya dakai. Wani kallo yai min kafin ya hade yawu masu daci a bakin shi yana fadin cikin karfin hali don me za ai muna dauka daya dake kuma ? Duk yana daurewa ne yaga hankalina ya kwanta kawai yasa shi tsayawa rarashina din da yakeyi a yanzu. Wanan mutumin nefa ya kara dawowa gidan nan mutumin da tun ban sanshi ba nake ganun shi a mafarkina har yakai na waye dashi a idona. Da irin barazanan son daukan raina da yake yaya don Allah ka tausaya min tunda har abin yakai mutanen naka yanzu raina suke nema kuma ka sani. Yaya ka duba irin wullakacin da arnen nan yayi min a wuri dakaje damu ranan a gaban bainar jama,a . Idan ba Allah ya gyara ba yaya me kasan zai faru a wurin damu wurin mashaya fa ka kaimu tsundun masu aikata masha,a da alfasha a bainan jama, a . Har yai muna sauka daya da sauran matan dake wuri wanda har yau duk na rufe idona ina ganin wanan bakar ranan yana min gizo kamar yanzu ne yake kokarin rungumana. Isanuwan shi ya runtse don jin zafin abin shima a cikin wani tsawa tare da daga hannu yake fadin enough zainab bana son kina tuno min da wanan abin don Allah. Komai lalacewa na aiba zan taba son inga wani ya wullakata ku ba koda kuwa bana kusa daku zan dage sai inda karfina ya kare. Kamata yayi ace kin tayani addu,a ba irin wanan masifan da kike mun ba koda yaushe instead ki jawoni a jiki sai bakar magana kike fada min ko yaushe. Kina tunanen wanan halin da kikeyi yanzu shine zai sa nabar duk wani abinda nakeyi din. Na dauka kurciyane ke sakaki hakan baki gane ni din mai so kine da gaskiya bawai don manufan da kike tunane ina dashi ba a kanki. Nasan da farko bana aureki bane don so ko kauna amma a yadda iyayyen ki suka banke a cikin mutunci da girmamawa hakan yasa min kaunar ku na gaskiya a raina daga ke har kanwarki sadiya. Jin abinda ya fada yasa ni sake hawaye wani na bin wani na kasa fadan komai a lokacin kinsan mace da raunin zuciya lokaci guda . A take zancen shi ya kashe min zuciya na nadan dago kai na kalleshi shima kai ya gyada min alaman eh abinda ya fada har zuciyar shi ya fada min shi. Na dukar da kai kasa sai ruwan hawaye nakeyi ya ciro hankaci daga cikin aljihun rigan shi ya miko min ban karba ba haka yasa ya fara goge min fuska da kanshi. Kitayani addu,a na daina duk wani sabon Allah danakeyi yafi mun wanan yawan kukan da kikeyi a yanzu. Duk wani addu,an da zan ma idan kayi da kanka Allah zaifi karba maka amma sai idan zuciyar ka da gangan jikin ka suna da tsarki Allah zai karbama addu,an ka tare dana mahaifiyar ka. Yanzu ki tashi ki koma saman gado ki dan kwanta ko zaki samu barci natsuwa yazo maki tunda naga kin tsorata da ganin taju gidan nan tare dani. Banyi magana ba na mike da zumar fita yake fadin ina kuma zaki haka falo zan koma in kwanta na basa amsa. No kada ki fita haka ki tayarwa kanwaki da hankali don Allah ki zauna a nan nima ba inda zan tafi ai na fasa fitan yau. Ance mutum rana gareshi sai gashi kan wanan dalilin mun wuni a dakin dashi duk da ba hira mukeyi ba kowa da abinda keci masa zuciya. Dan gara shima yana kallon wayan shi lokaci lokaci yana shiga ciki nikan tunda na bashi baya ban juyo ba ina faman tunanen zuci. Ranan taju kan ai mutuwa ne baiyi ba don ya gaji da jira har ya fito daga cikin motan lokaci lokaci yake kallon agogon hannun shi. Ya dago ya kallo kofan gidan shiru baiga fitowan shi ba haka yasa shi yanke shawaran binsa ciki yaga halin da yake ciki din. Nan ma ya samu part din a rufe kamar yadda ya rufe kafin su fito ga kuma ciwon nasa yana damun sa ranan sosai da zafi haka ya daure ya fita waje yana mai cizon yatsa don yasan yana wurina ke nan . Ji yayi kamar ya bishi can part din namu sai dai yasan abinda zai iya fitowa bayan hakan saboda yasan irin alkawarin da yasha a kaina na, don kafin J din ya yarda ya dawo alaka dashi saida yai mai warning sosai a kaina kuma ya yarda zai kiyaye din. Shine tunanen da yayi yasa bai nufi can part din mu da yake zaton J din na ciki ba a lokacin saidai daga inda yake zaune cikin furani yana dago kanshi lokaci lokaci yana kallon part din namu a fakaice. Sallah da akayi naga baida niyar tashi yasa nayi magana dashi zaman shi a dakin nawa kamar an kafeshi dole a wurin . Nake fadin azahar yayi fa tun dazun yaya lokacin yana dakilan wayan shi babu kakautawa ban san dai da wanda yake charting ba a wayan. Dan kalloni yayi yana fadin OK kafin ya mike na zata fita zaiyi sai naga ya nufi hanyar ban dakina da nufin kewayawa a can don dauro alwala. Da mamaki nabishi da kallo har ya shige don zan iya rantsewa da cewa tun zuwan mu gidan nan bai fi uku ko biyu ba daya taba shiga dakin kwanana a wanan gidan. Sai gashi ya gane ina bandakina yake a dakin koda yake hakan ba abin mamaki bane don ginan mu da nasa iri dayane a gidan sai dan bambanci kadan daba a rasa ba kila. Yana shiga yabi ban dakin da kallo yadda yake gyare tsab sai kamshi yakeyi haka ya sa ya sake jiki ya dauro alwalan shi ya fito ina zaune yace kiyi alwala muyi sallah yanzu. Da dan mamaki na kalle shi don jin abinda ya fada a zuciya nace kadaiyi kai kadai wa zanbi sallah haka kana mashayi mai luwadi kuma ? Yadda ya tsareni da ido yasa na mike na shiga da kyamkyami bandakin na dauro alwala nasame shi zaune bakin gado yana jiran fitowana. Nayi mamakin jin yadda yake karatun sallah a tsanake yana bada hakkin ko wani aya yadda ya dace sai abin ya tsaya min a rai. Nake mamaki har a fili mutum ya san kur,ani haka yake sakaci da daman shi ga wani can shi kimtsatsene a rayuwan shi amma Allah bai bashi ikon haddace alkur,ani maigirma ba a rayuwan shi. Idarwan mu yayi daidai da rurin da wayana yakeyi ban dauka ba don adduan da nakeyi lokacin har kiran ya katse na farko. Wani kira ya sake shigo min na dauka sunan maya na gani tana kirana ashe na dauka gaisuwa muka fara take fada min ai suna asibiti da mahaifiyar ta tun ranan Friday amma kila yau za a sallamesu. Sannu nayi mata tare da tausayawa a yadda ta dan ban labarin rashin lafiyan mahaifiyar nata a wayan. Duk yana jin mu tunda a kusa muke da juna lokacin har na kashe wayan na mike ina nade abin sallah don bana barin shi a wurin duk da ni kadaice a dakin nake amfani dashi. Kawo mun abinci naci ya fada na sake kallon shi ina mamakin sauyin shi na dan lokaci guda tare da rashin fahintar shi kan hakan. Ban taba shigo da abinci a part dina ba amma ranan sanadin shi saida ya saka na shigo dashi tare da kira mai sadiya muka zauna akaci tare , duk da ni a tsarge nake a cikin su don ban fahinci sallon yaudaran daya bullo min dashi din ba na zama min a daki yau. Kiran dayan wayan da akayine yasa shi barin dakin ya fita yana waya sai lokacin sadiya ke fadin yau kan yaya ya bamu lokacin shi a gidan nan sosai . Sau biyu ina lekowa zan shigo dakin nan sai na samu yana dakin a zaune na koma nace akwai dalilin zaman shi dakin ai tunda kika ganshi zaune yau. Bansan ya suka kare da taju ba daya fita don dai ban kara ganin shi ba sai kashe gari da muka hadu zai fita office nima mun fito da shirin makaranta zamu fita. Muka gaisa ya wuce muma muka fito na sauke Sadiya a nasu school din kafin in karasa makaranta. Naso makara don traffic da ya tsayar damu saidai tunda na doso wurin maya bata a sit din mu na tuna da wayan mu na jiya da ita da take fada min zancen rashin lafiyan mahaifiyar ta. Har aka tashi ban sake jikina ba saida na idar da sallah na kira maya din naji jikin maman ta? Nan take fada min ai basu bar asibitin ba suna nan nake cewa gani zuwa insha Allahu ban tsaya school din ba na shiga mota na bar cikin school din . Na fara zuwa don in dauko sadiya a can na dan bata lokaci wurin jiran sadiya din har muka samu an sallami su Maya daga asibitin sai banji dadin hakan ba sam. Shiyasa washe gari na roki yaya ya barni na je kauyen na gaida maman nata don mutuncin dake tsakanina da ita. Baiso barin mu ba don ya soma fada yana fadin meye nawana zuwa wani kauyen su na dan kara marairaicewa ina fadin. Kayi hakuri yaya don mutuncin dake tsakanina da ita ba dadewa zamuyi ba idan munje na dago kai ina kallon shi sai cin abincin shi yake kamar bada shi nakeyi magana ba. Idon dana zuba maine yasa shi dago kai ya dan kalleni yaci gaba da breakfast din shi a gurguje sai can ya dauko waya ya kira wani layi sukai magana. Nan na fahinci driver ne zai kaimu kauyen da iyayyen mayan suke zaune din sai can ya dago yana fadin ki shirya wanda yasan wurin zai kaiku kada ku dade idan kunje banson kuna nisa da garin nan ba tare dani ba. Insha Allahu zan kulla da kan mu har mu dawo lafiya na fada ya mike mukai mai a dawo lafiya bai amsa ba ya fita da tafiyan shi mai kama da sauri ko yaushe. Tun fitan shi na fara shiri tare da tanadar dan abinda zamu kai masu a kauyen idan mun je. Driver yazo muka dauki hanya ikon Allah ban taba zaton akwai masu talauci irin hakaba a wanan kasan . Sai gashi naga abinda ban taba zato ba idona na ganan min irin yadda tallakawan su ke cikin wahala da yunwa. Dama maya tana fada min irin yadda suke rayuwa don su basu yarda sa zamani ba sai gargajiya suka rike yasa basu faye samun cigaba a rayuwan su din. Da wayan da mukeyi da maya har muka iso dan kauyen nasu wanda gidan su yake da dan nisa daga titin kauyen don suna cikin duwatsune su . Maya tayi murnan ganin mu sosai don bata zaci hakan ba ta dauka kawai ina fully din tane b zuwa zanyi don duba mahaifiyar nata ba. Mun shiga dan karamin gidan nasu mai ginan al,ajabi a wurin mu har dakin da mahaifiyar nata take kwance. Mun dade a dakin kafin mu fito dan karamin falon su maya din mu zauna muna hira take fadin ai yakamata naje mu gaisa da kakannin ta da suka haifi mahaifiyar ta wace take bani labarin ta koda yaushe. Dole na mike don mu taka zuwa gidan yaran suka fito suna kallon mu kamae dai yadda yaran kauye sukeyi idan sunga bako. Dan gidane wanda bai kai wancen kyau ba da yan tsufin biyu suke rayuwa a cikin sa saidai akwai bambamci sosai dana su maya da muka baro a baya. Tsohuwace sosai matar yadda maya ke ban labari sun dade kafin su samu mahaifiyar ta itama haka kafin a haifeta an dauki lokaci mai tsawo da auren mahaifan ta din. Dalilin hakane wuri;yawon neman mahaifiyar maya din kakanin nata suka zama masu bada magani don shige shigen da sukeyi a dajin su don neman maganin haihuwa suka koyi wanan sana,an. Tsohuwan nada kirki sosai bayan dan bayanin da maya tayi mata da yare game dani sai take min sannu da zuwa wurin hada hannayen ta biyu hakan yasa na gane me take nufi da hakan da takeyi din. A duduke ta tashi ta dauko wani ganyen magani fresh ta fara dakawa a gabana kafin ta tace ta mikowa maya ta bani insha. Saida nayi bissmillah na karbi ruwan ganyen na kurba baida bauri ko daci saidai kamshin itaciya da yakeyi na kurbe na mika mata cup din ina mata godiya da kai irin na kurame. Dan murmushi ta sake a fuskan ta na tsufa kafin maya ta dauko wani zance sunayi sai ga fuskan tsohuwar ya sauya daga fara,an da takeyi lokaci guda. Yaren su sukeyi kafin maya din ta juyo gareni tana fadin tshohuwar tace idan ina son zata taimaka min don ta yaba da hankalina sosai. Na gyada kai alaman eh ba tare da wani tunane ba sai ga shi tsohuwan ta mike a duduke zuwa wani dan karamin kabat dake falon tsoho tana tono wani abu a cikin tarkacen ta cikin wani jakkar fata ta ciro abin. Ta dawo ta zauna ta kalli maya ta fara mata bayani itama tana min da turanci ina fahintar ta dan abin bai kai wani abuba don dan garin maganine . Sai wani abu kamar sayen ice yana wani kamshi tana bayani tare da nuna yadda zanyi yayin da niko gabana sai faduwa yakeyi don tsoro da fargaba. Yadda tsohuwar ke bayani zaka gane wuth full confidence take akan abinda ta bani din nasa hannu bibiyu na karba da take miko mi gwiwa har kasa da alaman taji dadin hakan danayi sosai. Dan kudin dana bata da zamu tafine yasa tsohuwar ta rungumeni a jikin ta tana dan taba bayana a hankali mukai mata sallama muka fito. A hanyar komawa gidan su maya inda sadiya da driver suke jiran dawowana mu tafine take kara min bayanin akan maganin don bata fadi ainihin aikin da zaiyi ba a lokacin tadai ce nayi mai amfani dashi yasha ko sau dayane zanga amfanin shi. Tare da fadin zan iya yiwa wani amfani dashi ma nan gaba idan naga yana cikin matsala irin na yaya din zan iya yi mai amfani dashi. Maya ta matsa da nanata min kan inyi amfani dashi ko za a dace muka kara sallama da mahaufiyarta muka tafi. Har muka zo gida ina faman tunane abu biyu na farko yanayin rayuwan su maya din a kauye sai kuma wanan maganin da tsohuwan ta bani yanzu yana a ciikin jakkar hannuna. Mun dawo a gajiye na wurgar da jakkan saman gado ban daki na shiga don dauro alwala har wanka nayi don ban san a inda na zauna ba a gidan su maya din su basu sallah. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN NAN NA KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA CIKIN SALAMA YAR UWA MU GUJI ABINDA ZAI KAIMU GA FADAWA HAKKIN WANI, , , , , Kwana biyu ina faman tunane a raina na yadda zan samu daman bashi wanan abin ya sha na rasa dabara yin hakan sai tunane nake a raina. Kai karshe dai na barzancen har na fara mantawa da wani zancen magani can a kanshi don nazo nayi tunane uwarshi ma da ta haifeshi ta barshi a haka balle ni. Iyaka dai na samu hanyar tsirewa daga gareshi da zaran na gama karatuna shike nan na fita wanan sarkekeniyar na auren shi ai. Na sani sarai bai daina halin nan ba don babu abinda ya fasa daga cikin halaiyar nasa shiyasa na yiwa kaina alkawarin ko a gabana yake mugayen halinsa iyaka na ido sai kuma addua ga musulmi da zanyi tsakanina dashi. Ashe abin ba haka bane idan ance miji abin yafi da nan duk da auren namu na wasan tamola ne ba kamar sauran auren da aka sani bane da farko. Matsalan abin banda abokin shawara a rayuwana ga zurfin ciki dake damuna ko banza balle wanan din da ban yarda kowa yaji wanan zancen a gurina ba . Ko abu yana damuna haka zai tsaya min a rai har lokacin da Allah zai gusar min da tunanena na manta da zancen ga baki daya . Don ina da saurin mantuwa a rayuwana ban faye rike abu a raina na tsawon lokaci ba bai fita mun a raiba. A bangaren mami kuma mu dai dan gaisawa yanzu a kai akai akala sau uku da ko sau biyu a sati zata kirani ta tambayeni muna lafiya dai ko ? Idan na bata amsa zata sake tambayana yaya mijin naki zainab saidai nayi murmushi bazan bata amsa ba akan komai. Zakaji tace kiyi hakkuri insha Allahu komai zai dawo daidai insha Allahu tare da kara kwantar min da hankalina. Saidai duk yadda na iya daure da hakkuri saida yaya ya kaini kull har ya kawo muna matsala don yanzu kan kamar kara masa iskanci akeyi don dawowan taju gidan ya kara maidashi ruwa sosai. Don yasan na sani yanzu ba zancen boyo a tsakanin mu a fili yake abinsa don ba mai kwaba masa yake gani. Ranan na dawo school da wuri daga makaranta don haka kawai nake jin ba dadi a jikina muna fitowa darasin farko na shigo mutana na dawo gida don in dan kwanta. Saboda ina jin kamar barcine ke damuna ko zazzabi ke son kamani a irin hakan kawai na yanke shawara in dawo gida. Nayi mamakin ganin falon a bude don ban tsanmanin dawowan yaya gida a wanan lokacin daya dace ace yana wurin aikin sa. Haka na bude falon cikin karfin hali na shiga har na rufo kofan na shigo kai tsaye tsakan falon na samesu kamar wasu karnuka suna romace a tsakanin su kamar wani miji da mata ko saurayi da budurwa. Inna lillahi na fada da karfi ina sake yar hand bag dina dana sako tarkacena a cikkn sa. Salatin danayi ne ya dawo dasu hankalinsu suka mike lokaci daya tare da sakin junan su ga maballan rigansu duk sun balle sun shagala da hakan. Tashin hankali iya tashin hankali na shigeshi a ranan yadda gaba daya idona ya rufe na ke fadin stupid, idiot noses mazinata fasikai ku fice min a falo kafin na tona maku asiri a nan. Ido rufe kamar gidana suke sheke ayan su din a ciki don yadda idona ya rufe da ganin su baro baro danayi a lokacin. Wani kallon tsana taju din yai min don yadda yaga abokin fasadin nasa yayi laushi sosai yana fadin wai meye haka me ya dawo dake gida wanan lokacin ana karatu. Ban iya magana ba don duhun da idona ya fara yi mun a lokacin na kara fadin ku fice min nan nace kada fushin ku ya shafeni a wurin Allah. Ke ki natsu ki san abinda kike fadi mana da irin wanan kalaman naki ya mike da kyar yana mai gyara rigansa yake wanan maganan tare da nufo inda nake tsaye. Na fara ja da dan baya kadan bai daina nufo inda nake ja da baya din ba naci karo da wani abu a bayana na fadi kafin in kai kasa na some don tsoro a wurin. Da sauri ya karaso ya tareni na fada a jikin shi sai lokacin yaga ai a some nake ma ashe ya fara kiran sunana da karfi yana jijigani ban farfado ba. Yasa ya juya inda taju din yake cikin daka tsawa dauko min ruwan sanyi a fridge mana da sauri baka ganin ta somane. Haka taju din ya nufi kitchen da sauri ya dauko goran ruwan da har ya fara kankara ya kawo mashi bai tsaya kulawa ba kawai ya watsa min a jikina . Na sauke wani ajiyan zuciya tare da dan bude idona kafin na mayar na rufe na kara sakewa lokaci guda kuma. Ya subbanallah ya fada tare da dan jijigani yana kiran sunana a hankali kuma a rude ka barta zata farfado ai tunda ta falka taju ya fada. Shout,up ya fada da karfi duk waya jawo hakan yanzu saida na fada ma ka bari zan dawo don jaraba ka manne min saida hakan ya faru. Na fada ma yarinyar nan yar gargajiyace da rikon addini kayi duk wani taka tsatsan dasu don komai yanzu a cikin tako nakeyin shi don su. Taju din yace I am sorry boss ban san zata dawo yanzu bane ni kuma ina son jinka a jikina wanan lokacin. Yace yasa kayi min karyan baka da lafiya na bar aikina zuwa gida yanzu ga abinda ka jawo min yanzu wanan abu baka san iya inda zai tsaya ba . Duk zancen da sukeyi ina jin su don na fara farfadowa lokacin zancen su yana shiga kunnena bandai bude idona kawai bane don ban son ganin su sam a rayuwa na. Ji kawai nayi ya cicibene zuwa sama bai ajeni ba sai saman gadona ya shifideni ya juya wurin AC ya kunna tare da sake volume din AC din. Ya dawo inda nakw yana dan murza min goshi tare da kiran sunana a hankali da zainab kina jina don Allah ki kwantar da hankalin ki mana ki natsu. Don Allah ka fita yaya bana son ganin ka a rayuwana kai din shedan ya gama ma fitsari a zuciyar ka bama iya kanka ba. Yaya a gidan ka ? Gidan da iyalin ka suke zaune anan kake shimfida fasadi irin wanan kamar kai din ba musulmi ba haihuwan musulmai ? Enough zainab ya isheki kin dai san koni waye don haka ki kyaleni yadda kika ganni a haka na fada maki. Wayo ni Allah na na shiga ukku na lalace a rayuwana. Ni zainab naga ta kaina ya Allah na tuba ka yafe min da wanan jerabawan dakake jarabbata na dashi idan laifi nayi ma ka jefoni a wanan rayuwan. Tsuki yayi ya mike bai tsaya ba ya rufo kofan da karfi ya fice na kara kurma ihu kamar an tsikareni kuma na mike tsaye ina saukowa daga saman gadon. Dan jakkana na dauko na nufi kofan fita nima da sauri sai dai ina zuwa bakin get din security din kofan ya rufo kofan da sauri yana min wani yare da ban sani ba. Duk yadda naso fita daga gidan sun hana hakan dolw na koma cikin gidan rai bace ina hawaye. Tashin hankali ranan na shige shi ga tunane kala kala da nakeyi a zuciyana sai can Sadiya ta fado min a rai don lokacin dawowan ta da yayi har ya wuce yasa na kara mikewa tsaye na nufi hanyar waje . Ban kai ga fita daga falon ba sai ga sadiya din ta fito daga dakin tana fadin . Yau yayan mu kin barni ina jiran ki saida ya jafar ya turo aka dauko ni a makaranta ya din yace driver ya fada min kina gida baki da lafiya wai . Hannu na warewa sadiyan tare da fadin yar kanwata zo gareni don Allah ki rungumeni ko zanji dadi a rayuwana kada in mutu. Da sauri ta karaso ta rugumeni din tare da fadin yayan mu meke damun ki baki da lafiyane ko wani abu ya sameki. Saidana runtse idona ina jin dadin dumin ta a jikina kafin ince da ita ya jafar daine yake son kasheni Sadiya. Kai ta dago tana zare jikinta daga nawa tana fadi a razane zai kasheki yayan mu me kikai masa nace nima ban sani ba Sadiya ya daice zai kasheni yau a garin nan. Daga haka naja hannunta zuwa saman kujera wayan dake hannuna na fara neman lamban mami ina kiranta. Kira biyu saiga mami ta daga wayan murya a raunane nake fadin mami na shiga uku yau a garin nan wallahi. A rude mami ke fadin meya faru zainab ina jafar din yake ko wani abu ya sameshi take tambaya a rude. Mami ba abinda ya sameshi kawai dai na kamshine yana abinda ba daidai shine yai min dukan tsiya ya ce zai kasheni ba zai barni da raiba tunda na saka mai ido da yawa. Innalillahi shi jafar din baibar wanan dabi,an bane zainab ko kwayance ta fara tabashi yanzu har yake furta hakan ? Sai kawai naji ta fashe da kuka nima kukan nakeyi na daukan hankali ina tausayawa kaina kan wanan rayuwan dana samu kaina a ciki. Yayan mu mu gudu mana idan yaya a zama mugu kada ya dawo ya kashe ki din a gidan nan sadiya ta fada a tsorace don taji wayan mu da mami din. Ni kuma na fadi hakan ne don labarin da Maya ta bani daya taba faruwa da wata inda take cewa zasu iya kashe mutum idan ya faye saka masu ido basu da yadda zasuyi dashi . Sai kawai su kashe mutum su huta kuma ba ai masu komai idan an kwana biyu kigansu a gari suna yawon su. Do suna da daurin gindi sosai a wurin manyan gwaunati da sauran jami,ai don haka ba ai masu komai ko an kamasu. Jin hakan yasa nake tsoron hakan don nasan shima yaya din dole yana da wanan halin data fada min don bai rasa daurin gindi yadda naga yana shanawa a kasan son ransa. Wanan dalilin yasa na fadawa mahaifiyar nasa haka don riga kafi a yadda na ganesa yau din kafin ya fita don zai iya aikata min komai tunda na gansa din yau ido da ido. Sai gashi a rude ya dawo gidan tun kan ya hawo sama yake kwala min kira ina zaune sama ina jin yadda yake kwala min kiran a gigice muna tare da sadiya a dakina na tashi na rufe kofan da sauri a tsorace. Don nasan sunyi waya da mami ke nan akan wayan da mukayi da ita dazun kan wanan zancen yasa ya dawo a hasale yake min wanan kiran na tashin hankali. Muna jin lokacin da yakw dukan kofan a haukace muka rike junan mu a dakin a tsorace kamar zai shigo muna dakin ne, bayan a rufe dakin yake. Har ya gaji da haukan sa ya tafi kilama dama a buge yake zo ya sauke haushi a kaina waya sanar mashi mudai muna ciki lokacin. Haka muka kwana tsorace rai kuma bace damu don ko sadiya da take karama a tsorace ta kwana makake dani ranan. Tunda safe na sake kiran manmi duk da nasan a lokacin sauran darene a can Nigeria ina kuka na tayar mata da hankali akan ta saka baki ya turo mu zuwa gida don na gama zama dashi ni. Mami hankali tashe ta tayar da ya mamud tana fada mai abindake faruwa a waya duk da ban fito fili na fada masu gaskiyan maganan ba amma hankalinta yayi matukar tashi a lokacin. Wanan wayan ne ya tayarwa kowa hankali tunda safe sai kiran shi akeyi aka daga mai hankali don mami ta fada mai har in ya yarda ya turoni nageria a haka asirin su ya gama tonuwa ke nan a kasan nan. Tayi rantsuwa duk abinda ya sameni wallahi sai tayi sanadin da za a kashe shi shima kafin ya bata mata sunan zuria a duniya. Yabi wayan da kallon mamaki bayan sun gama waya da mami yana mamakin yadda a shekaru na iya jefashi cikin wanan rikicin haka. Don kalaman mami sunyi tsauri sosai a gareshi hankalin shi ya tashi sosai gashi ranan ya kori taju bai kwana dashi a dakin ba. Don yana ganin duk shine ya jawo mashi wanan fitinan daya faru yana zaman shi a office din shi tajun ya daga mai hankali. Yayin da shi kuma tajun ya kwana yana neman mafitan hanyan da zai ga ya raba tsakanina da jafar din gaba daya don tun haduwan mu da jafar din gaba daya komai ya jagule masa ba yadda abubuwa suke tafiya masu ba a baya. Don yanzu jafar din ya canza kamar bashi bane mai yawan sha,awa a kansa a baya yanzu bai faye damuwa da hakan ba sai yaga dama tunda har yana iya koran sa a yanzu. Shiyasa ya zama mai dole ya dauki mataki a kan zainab din da yakewa kallon karaman yarinya da farko sai fashi yarinya nason rabashi da farin cikin ga baki daya. Matakin daya yanke a ransa shine yayi min silent kill ba tare da wani ya gane hakan ba har jafar amma ta yaya zaiyi hakan ba, a fahince shi ba. Don idan ba raba yarinyar nan yayi da duniyan ga baki daya ba wanan karin kan yasan ba zai taba samun kan jafar din ba kuma. Da ire iren wanan mafarkin ya kwana a ranshi har safe bai kai ga mafita ba yana falkawa wayan shi ya jawo yana neman layin jafar din saidai wayan yawan busy yayi yawa a ranan. Shiko jafar daya gaji da tunane mikewa yayi ya shiga bandaki ya watsa ruwa tare da dauro alwala yazo ya tayar da sallah kafin ya fara samun natsuwa na zuwa mashi lokaci guda. Saida ya shrya tsaf kafin ya fito part din namu ya nufa kai tsaye ya samu dakin har lokacin yana rufe bamu bude ba. Mami ya kira itace ta sakamu mu bude kofan ya shigo don sadiyace ta bude mai kofan ta rabe a gefe a tsorace har ya shigo dakin yana mata kallon mamaki. Kafin ya dago ya kalli inda nake zaune rakube saman sallaya a wurin danayi sallah har lokacin ban daga ba ina zaune. Sadiya ya kara kallo yana fadin jeki kiyi wanka ki shirya na saukeki school tace to a tsorace ta fice daki da sauri zuwa abinda ya umurce ta yi din tana waigena a tsorace. Sai take ganin kafin ta dawo dakin ya gama halakani ga kuma tsoro da biyyaya yasa ta barni dashi a dakin ta fita. A hankali ya tako zuwa inda nake a dakin ya zo gab dani ya tsunguna a gabana ya kura min ido na dan lokaci. Kafin ya furta a hankali zainab a zatona ke yar uwatace da zata iya rufa min asiri a duk irin halin da muka tsunci kan mu a cikin sa. Sai gashi ke din ce a yanzu ke neman hadani fada da mahaifiyata da yan uwana har kina ikirarin zan kashe ki in rabaki da rayuwan ki. Ban kawo ki kasan nan don na tozarta ki ba cin zarafin ki sai kawai don wani bukatana na daban wanda a baya na zata zaki iya daurewa da irin rayuwana. Ashe abin ba haka bane ke a wurin ki tunane bai barni na gane irin ra,ayin ki na rikau da kike dashi ba a lokacin. Ban taba zaton hakan ba a wurun ki don na dauka ke din ma a dan uwa na jini kike dauka na kamar yadda yasa na zaboki kan tayin mami na aure a kaina. Nayi zaton idan na biyo ta wanan hanyar komai zaizo min da sauki a rayuwana ashe abin ba haka yake ba kece ma zaki min fiye da abinda na guda a gurin wata. Don ke din na kula abin duniya gaba daya baya gaban ki kin nausa a wata duniyan na daban. Ban iya cutar da wani ba zainab balle na fara a kanki a yanzu don haka ina rokom ki da kibar kiran mahaifiyana akan rikicin mu don Allah. Banda ra,ayin rabuwa dake ko nan gaba balle wanan yasa na mayar dake Nigeria kamar yadda kike so nayi maku. Idan zaki kwantar da hankalinki wuri daya saura kiris ki karasa karatun ki idan naga hankalin ki ya kwanta na kaiki gida kiga iyayyen ki idan kuma haka zamuci gaba da zama zaki tabbata a kasan nan baki je gida ba din zuwan ki a haka illa ne garemu baki daya. Da sauri na dago kai ido tab da hawaye don ban so ma ganin sa na kalleshi ina son yi magana kuka ya rinjayi zuciyana har bakina bai iya buduwa a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN NAN NA KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA NA FITAR DA HAKKI NA FADA MAKI YAR UWA ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMAN SA AMIN. Maza mutanen mu da irin hikimarsu ta maza badan yaso ba sai dole don yanzu shima yana dana sanin kakabowa kanshi aure daya yarda yayi don kawai ya farautawa mamin shi rai. A yanzu yana dana sanin yin haka dayan san duk mata daya suke a wurin hali da bai yarda yayi wanan auren ba yake rayawa a ranshi. Yarinyar daya dauka bagidajiya zai iya yaudaran ta da kudi da wasu kyalkyal din duniya duk da yana zube matasu kamar ba gobe amma tana son zame mashi ciwon idon rayuwa. Sam bai taba zaton hakan ba da sauri ya dauka koda zan fahinci hakan sai bayan shekaru sun ja san nan zata iya fahintar rayuwan da sukeyi dashi a gidan. Sai gashi a cikin yan shekaru ta nuna mashi halin mata a wurin wayau da hikima har ta iya hadashi da mahaifiyan shi haka. Hadi na zargi da kake har mami na zubar da hawaye da bata taba irin saba tana ikirarin cewa zata sa a kashe shi shima duk inda ya shiga a duniyan nan. Tabbas mami zata iya tunda ta furta hakan har in yayi gigin aikata hakan kan zainab din da kanwaera. Shi ta yaya ma zai aikata hakan wai da har mami ta yarda da hakan da sauri don zainab din ta fada mata kawai zatayi amfani da wanan zancen. Yana gama wanan tunanen ya dago kanshi dake duke ya kurama zainab din ido na dan lokaci . Yarinyar ta rame sosai tayi wani hasken dake daukan ido tausayi ta bashi sosai don tana a tsorace ne ko damuwa har lokacin. Baisan irin kalaman da zai mata amfani dashi ba a bakin shi ta yadda zata fahince shi a yanzu ta kwantar da hankalinta. Don karyama ko yaudara bai taso ba gareshi yanzu tunda da idon ta ta ganshi bawai zato ba ko jiji da takeyi da farko. Yanzu kan idanun ta ya gane mata koshi waye don haka babu sauran wani zancen dadin baki a kan hakan daya rage a bakin shi saidai hikima. Muryan shi naji yana fadin wai yaushene zaku samu hutun makaranta ya fada yana kallo na ? Jin abinda ya fadane yasa na dago kai da sauri don a zatona yana tambaya ne don ya mayar damu gida lokacin. One month coming zamu samu saidai ita sadiya zata rigani samun hutu na fada mai a sanyayye don jikina da baida karfi sosai. Ina son in kun samu hutu zamu tafi Dubai mu dan huta a can sai kunyi hutun naku can ga baki daya don nima zan dauki hutu a lokacin. Fuska na bata ina kawar da kai daga kallon shi don jin abinda ya fada tunda ba gida zai kaimu ba a lokacin . Ashe ya fahinci hakan danayi naji ya sake fada a daidai lokacin sadiya na fitowa daga daki yace ko Dubai din bai maki ba na kaiku America ko wani kasa kuyi hutun a can ? Ni ba inda zan tafi na fadi hakan ina murgada baki kafin yace wani abu sadiya ta cabe da fadin yaya mune zamu tafi Dubai din ? Eh sadiya a can nake son kuyi hutun ku wanan karon don ku dan ga garin tunda baku taba zuwa ba ko ? Yayan mu shine bamu zuwa Dubai din don Allah karkice ba zamu can din ba ina son zuwa naga Dubai din nan da friends dina ke bada labarin sa. Iyayyen su masu kudine idan kinji suna zance ke ko yar waye da zaki matsawa rayuwan ki zuwa can ? Amma ai kanwan jafar ce ita din ko, ko anfada maki kani baya tunkaho da dukiyan wanshi ne ? Wani kallo nayiwa sadiya din kafin nace tabi dai duniya a sannu irin haka ke kai mutum ga halaka karshe har mutum ya bar addinin sa ya fada sabon Allah. Murmushi yayi tare da dan shafan gefen fuskan shi ya mike tare da fadin while sadiya saiki fara shiri ko ? Don mukan Dubai zamu tafi mu huta ko ta daga kai tana satan kallona nidai nawa ido kawai na zuba masu ban iya furta komai ba garesu. Haka muke samun kulawa daga gareshi a wanan lokacin don gaba daya yanzu ya sakawa duk wani motsi namu a gidan idanu idan yana gida. Banda sakewa don kullun a cikin farga nake haka kuma yanzu nasakawa raina zaman dakin don falon da na riskesu a cikin sa suna fasadin su ya fita raina gaba daya. Dana kalli daidai wurin dana gansu din a ranan sai naga kamar a lokacin ne suke aikata alfashan su . Dakina ne ya koma min wurin zama muddin ina gidan saidai sadiya ta sameni a ciki muci abinci muyi hira ko kallo a nan. Har wanan lokacin Maya bata tambayeni zancen magani ba nima ban tayar da zancen ba gareta don na manta da wanan zancen don abin yaya yayi nisa sosai. Saima nake ganin ina wanan tsohuwar zata iya da taimakon kan haka al,amarin shi sai addu a kawai. Ko banza sai nake ganin ai su din ba musulmai bane kuma ba Allah ma suka sani ba don haka ai abinsu ba zama dole a amsa masu ba a wurin Allah. Kawai saina dinga addu,a da kyauta idan na biyo hanya naga marasa galihu saina tsaya na dan masu alheri. Jerabawa ya sakamu a gaba hakan yasa ban ma da lokacin kowa a yanzu saina karatuna don ina son in fito da sakamako mai kyawo idan na gama. Kwanan mu hudu da hutu muka daga zuwa Dubai inda mukaiwa dubai din saukan dare kafin mu kai hotel din da zamu sauka an fara kiraye kirayen sallah asuba. Wani tsadden hotel ya sauke mu a kusa da ruwa muke duk da darene amma hakan bai hanamu gane kyau garin ba. Dakin da aka saukemu shike kusa da nasa wurin dai sai kingani gwanin ban sha,a sallah nayi na haye gado sai barci ko abincin da yai odar akawo muna na karyawa ban tashi naci ba sai karfe daya na rana. Sadiya bata dakin wanka na kara yi don naji dadin jikina bayan nafito na zauna ina gyara fuskana duk daba makeup nakayi ba a fuskana yau sai na samu kaina da shafa poweder kadan a fuskan nawa. Gurin mayarwa ne naci karo da wanan maganin da kakan Maya ta bani don da wanan jakkar na tafi kauyen su maya din a ranan da naje can din. Nayi mamaki kwarai dana ga wanan abin ashe ban cireshi a jakkar ba har nazo nan dashi uwar duniya. Riga na mike na dauko na saka a jikina duk da bawasu kaya muka dauko ba don yaya ya hana hakan wanda zamu canza idan munyi wanka sai na jikin mu kadai muka dauko. Kofan aka turo sadiyace a gaba yana binta a baya suna dauke da kaya niki niki a hannayen su haka yasani juyowa ina kallon su. A saman gadon dakin suka zube kayan shi bai tsaya ba sannu kawai nayi mai ya juya ya fita bayan ya amsa min. Baiko karasa fita daga dakin ba sadiya ke fada min yau yayan mu naga garin nan ashe haka wanan garin yake cike da musulmai ? Ina kukaje na tsare ta da tambaya yayan mu ya shigo ya sameni zaune kina barci yace nazo muje unguwa. Kada ki kara fita da kowa idan baki fada min ba na fada fuska daure Allah ya taimakeni tana matukar tsorona sosai don fada nakan mata idan tayi ba daidai ba. Zama nayi na fara bude kayan suturu ne irin na mata yan duniya da suka amsa sunan su a ciki sai kuma na sadiya din leda daban ita sun kai kusan kala goma. Ikon Allah na fada a fili a raina kuma rayawa nayi yanzu shi yaya bai gajiya da labto mana kaya haka ko a gida can chaina bazance ga yawan tufafina ba yanzu. Sai kayan kwalama wanda ko ban tambaya ba na san saboda sadiyace ya sayo su haka kala kala. Yunwa ne ya fara ziyarana sai lokacin na daga ido na hango abin karyawana saman table din cin abincin dake dakin mai kama da karamin palace. Mikewa nayi zuwa kan table don na zauna tare da bude abincin irin cimarsu ne na larabawa aka shirya saman table din. Dan kadan na tsakura na barshi don tafarnuwan da yai yawa a ciki duk da suma chaina suna cin tafarnu amma basu kai nan ci sosai ba. Bayan karfe biyar shi ya shigo dakin da kansa yace muzo mu fita mu sha iska a waje munga kifaye suna wasa a ruwa wanda suka dauke min hankali sosai wurin kallo gwanin ban sha,awa; Mun baza ido munyi kallo sosai ranan sai kusan magariba muka dawo cikin masaukin mu a gajiye. Dadi kan muna shan shi zuwan mu dubai har yakai na kasa fahintar wanan daulan yadda yake kashe muna kudi don zuwa hutu kawai da mukayi a nan din. Ban tashi sanin taju yana garin ba sai ranan da dare na fito daki kamar wace akacewa na fito wajen a cikin daren . Na kama hanya zuwa waje don kawai iskan dake kadawa mai dadi a wajen dana shaka ta tagan dakin. Kwatsam na gashi a gaba saida nayi wani irin kaduwa mai ban tsoro kafin na jawo karfin hali insa a rayuwana na dake na watsa mai harara kamar yadda shima yake min kallon rainin wayaun. Shamlace man kaji kunya kato dakai kana bin karamin yaro kuna lalata dashi don taushewan kwakwalwa da batan basira. In dai J ne insha Allahu sai ka zama abin kyama a gareshi nan gaba don ko kallon kare ba zai ma ba a duniyan nan indai akwai Allah na daga hannuna sama ina nuna saman alaman Allah na nan. Na wuce shi ba tare da yai min magana ba naji mamakin hakan kwarai da yayi don sai murmushin mugunta ya sake kawai. Ina tsaye rai a bace ina tunane wanan irun bala,in da yake tunkarana haka koda yaushe na jafar din. Karama dani mai karancin shekaru a wanan halin haka ni yanzu ma na rasa abinda zanyi saidai kawai na barwa Allah lamarin sa. Don abin ya wuce gaban mamaki sai la haula wala kuwati kawai za a ce ma lamarin nasa tunda har naga wanan katon kuma a nan. Rasa abinda zanyi nayi a wurin na kunna wayana ina daukan hoton wurun don ya debe min kewa da bakin cikin dake cina a rai. Don wanan karon nayi alkawarin bazan wa J din magana ba kan hakan saidai in bar abin a cikina kawai Allah yayi min maganin su da kanshi Jimana naji an fada a bayana nayi saurin juyowa inga ko waye ke magana haka dani a wurin . Taju ne tsaye ya saka hannayen shi a cikin aljihun wandon shi yace kada kiga kin fada min magana na kyaleki. Yanzu dai nasan kin san ko wayw ni a gurin J din a tunane ki kina ganin har J din na iya rayuwa badani ba ? Don haka yanzu ki ba kanki amsa a nan ya juya ya fara dan tafiya sai kuma ya juyo yace ku mata wawaye ne koda yake kwadayine ke damun ki keda iyayyen ki shiya kawo hakan. Ya sake wani shu,umin murmushi a fuskan shi ya juya ya tafi ya barni tsaye a wurin ina binshi da kallo cike da kunan rai. Har na dawo dakine ba tuna da wayana a kunne yake don ba kiran kowa nakeyi ba a nan tunda banda layin kasan a wayana. Gado na fada sadiya na kwance tana kallon a system dina wanda aikinta ke nan sai sallah kawai ke tayar da ita lokacin. Yaya kin fitane nace eh na sha iska ne a wajen bayan haka bamu kara magana ba don kwance nakai rigingine fuskana yana kallon saman dakin ina faman tunane. Barci ya daukeni a hakan itama ashe tayi barci tabar sytem na aiki waya na kuma shima ya nuna a kunne yake don dan wutan da yake nunowa yana aki aiki. Ya dawo ya shigo dakin don ganin wutan mu a kunne dayayi sai ya samu duk barci mukeyi a dakin dukan mu ga naurorin mu a kune a kusa damu. Yayi niyar ya tayar damu daga barcin sai kuma ya barmu ya fara kashe system din dake wurun kan ta a yashe. Bayan ya kashe system din ya mika hannu ya dauki wayana zai kashe ya ga video ne na dauka ya dan tsaya yana kallo. Forwarding din shi yayi abin ya bashi mamaki don hotunan wajen hotel ne ya bayana yana magana sai dai baya jin me ake fada don ba kara. Girgiza kai yayi yana murmushi ya dago ya kalleni ina kwance nayi barcina bansan inda nake ba ma a lokacin ya kashe wutan dakin ya fita. Sai cikin dare na falka naga yadda muka kwanta tashi nayi da sauri na nufi kofan don in rufe sai na samu kofan a rufe ba key a wurin haka yasa na gane ta baya aka rufe mu. Da tsoro na dawo cikin dakin ban kwanta ba abandaki na shiga nayi alwala nazo na tayar da sallah na dade a zaune ina addu,a da rokon Allah kan ya tsaremu ya karemu daga halaka. Zancena da taju ne yake dawo min sabo saka sunan iyayyena da yayi yafi komai tsaya min a zuciyana. A karshe wani dabara ya fado min a raina a hakan har aka kira sallan asuba na mike na gabatar sai lokacin na koma barci. Da yake na sa abu a zuciyana sai banyi wani barcin sosai ba don kada yaya ya shigo ban sani ba. Dakin ya shigo kuwa bayan mun gaisa dashine yanawa sadiya sherin wai ta fara zama yar lukuti tana dariya. Yaya yau ina son shiga ruwan can don haka idan ka fita kada ka dade ka dawo mu shiga na fada kai tsaye ba tare da shakkan komai ba. Bashi ba har sadiya tayi mamakin jin wanan maganan daya fito a bakina lokacin yace a cikin mamaki dama kin taba shiga ruwane ke nan ? Ban taba ba yau dai nake son in fara na bashi amsa da hakan ya gyara tsayuwa yana fadin idan aiki ya barni zan dawo din Allah dawo dakai lafiya . Yana fita na bishi da kallo tare da mamakin kaina nayin wanan karfin halin haka da nake son gwadawa a yanzu. Tun lokacin na fara shiri na na fita har zuwa bakin shagunan dake layin hotel din na sayo wasu irin kaya masu matukar kyau ga tsada. Kwalliya mai daukan hankali na tsarawa kaina don ban taba sanin na iya ba haka tun dan koyon da nayi zamanin zama da yan matan mami a gidan ta ina jin zancen su a wurin yin kwaliyan su zakaji suna gardama wanan yayi yawa wanan bai ji ba. Kodana dauko rigan zan saka saida na runtse idanuwana kafin na bude na daure na saka kayan hakanan sai gani na koma kamar wace zata wurin fashion. Ni kaina saida na gigiza dan ganina haka ba komai bane yasani hakan sai daukan irin shawarwarun fadila da yau nayi a zuciyana. Don ina son in gwada in gwada sa,ata da hikimana na diya mace da fadila ke yawan fada min ko yaushe da takace. Mu mata makamine gun da namiji komai taurin da namiji da cijewa ko gagara a duniya sai mace ta juya shi a wata tsigar nata wata rana. Ta hanyar yaudarar ta ko kisa ko kuma kisisina da kutungwila irin na mata da maza basu taba gano hakan sai mace yar uwarta zata gane mai take shiryawa. Wanan baiwa ne irin na mata da Allah ya halicci diya mace wanda su matan bayan addu,a wanan ne makami na biyu da suke amfani dashi a wajen mazanjen auren su ko hurda. Ranan turare yasha kashi don duk wanda na gani har wanda ke cikin jakkana nayi amfani dashi a irin hakane na dauko wanda idan baki matan ba fadilace ta banshi da dadewa lokacin da zamu zo chaina tace ta karbo min nayi amfani dashi. Uku da rabi na fara wanan shirin kafin karfe hudu don saida nayi sallah la,asar na zauna yin kwalliyan nawa na kammala komai daidai lokacin daya dace in kammala din. A nasa bangaren kuwa yana tune da hakan yasa ya baro abin da yakeyi zuwa masaukin namu don shi ba mutum bane mai saba alkawari duk halin turawa shine akidar shi. Don da hakan bai samuwa da bai mun alkawari ba tun farko dakin shi ya fara yadda zango yayi wanka ya shirya already yayi booking din wani haddaden jirgin hotel din da zamu shiga ruwan dashi. Dakin ya turo wanda kamshi ne ta ko ina ya fara taron hancin shi ya fara raba ido a kan mu Allah ya taimake mu ina zaune saman gado ina zaman jiran tsamani ya shigo. Duk da kusan wata biyun da suke shige idan ya kalleni gaban shi sai ya fadi ko yaji wani bakon yanayi a kaina yana ziyartan shi . Wanda hakan yakan daukeshi don kawai yasaba da mune kwarai a yanzu yasa tausayine ko wani abu yakan ziyarci zuciyar a kaina don yasan badai feeling bane wanda maza kanji akan wata mace. Shiya dauka hakan sabone kawai da tausayina da yake ji ayanzu ne don yasan bayai min daidai yasa yana jin wanan akaina idan ya kalleni wani lokacin. Don saboda wani lokacin yakan zauna yana yin tunane mai zurfi kan matsalan namu tunda mami ta sakashi gaba yanzu don da kyat take daukan wayan shi koshi sai ya bi ta hanyar ya mamud yake samu su gaisa saboda Allah ya aza mai son mahaifiyarsu a ranshi. Don hakane yakan zauna yana neman way out kan matsalan nasa da yake da wuya ya bari shima ya sani saboda yasha gwada barin ya kasa yin hakan. Sai yanzune yasan ya fada tarko mai wuyan fita a cikin rayuwan shi wanda zaice kurciyane da zugin abokai sukai tasiri a ranshi a lokacin don kawai duniya ya fada halaka. Gashi arziki da suna duk sun samu a duniya saidai shi gareshi a yanzu wanan duk banzane a wurin shi tunda har mahaifiyar shi da uwar cikin shi suna kyamarshi saboda halin shi. Da wanan ya shigo dakin namu sai dai yau din muna hada ido dashi daga inda nake zaune nayi wani irin zama kamar wata Queen of manshion saman gadon. Wanda nima dai haka kawai yanayin zaman yazo min bawai nayine da ganganba don kawai kada kayan jikina ya baci ne na zauna hakana. Ras ras yaji a gaban shi wani abinda bai taba ji ko hangowa a gareni bane ya hango tare dani yau din daya shigo ya tsinkayeni hakan. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA KAFIN KI KARANTA A CIKIN SALAMA NA FITA HAKKIN KI NA FADA MAKI YAR UWA ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMIN SA AMIN, , , , Ina zaune saman gado nayi zaman balance irin na goggagun mata yan duniya na wani harde kafa rabin cinyana duk a waje yake. Na bude baki a hankali cikin wani yauki da yatsune ina fadin sannu da dawo tare da kawar da kai kamar shigowan shi ba dameni ba yadda na nuna. Amsawa yayi da mamaki karara a fuskanshi yana kare min kallon irin shigan da nayi a lokacin don fitan da zamuyi din dashi. Yayan mu na shirya muryan sadiya ya daki kunnuwan mu lokaci daya tana fitowa wani dan lungu dake dakin don dakin babbane an masa part part kamar kana cikin babban gida mai dakuna da yawa. Mayar da hankalin shi yayi gareta har ta kara fitowa yake fadin Wa, Wooo wai wanan sadiyace kanwata dai dana sani ko idona ne ke mun gizo haka ? Dan murmushin jin dadi ta sake a fuskanta ya mika mata hannu tazo gareshi yace kanwata kinyi kyau sosai wallahi . Tace har na kai yayan mu yin kyau kuwa ya J har kin fita ya furta tare da jawota yana mata rada a kunnen ta kafin ta juyo ta kalleni a inda nake zaune bakin gado. Idan kun gama gulman sai mu tafi na fada ina mikewa tsaye na dauko handbag dina dake gefen inda na zauna. Ina gyara gyalen dana yafa saman hullar daya rufe min kaina da kyau ido ya kara bina dashi na turu baki ina fadin wanan kallon ai sai mutum ya kware haka. Ina mamakin wanan kwalliyan ne haka don ban taba ganin kiyi irin sa ba duk da ruwa zamu shiga amma kika chaba ado haka dake ? Nayi ne don daga ni sai kai sai Sadiya zamuyi tafiyan da ace wurin mutane da yawa zamu shiga bazanyi shi ba. Hanya ya nuna min da hannu na kalli sadiya ina fadin shige mu tafi ta fara hanya na mara mata baya ya rufo dakin da makulli bayan mun fita. Dan tafiya ne ya sadamu da wurin ina bin ko ina da kallo sai gamu bakin ruwa nidai har cikin raina dama ina son shiga ruwa koda bai kai haka yawa ba a rayuwa . Sai gashi yau zan shiga ruwa irun wanan jiragene a wurin jere da juna muka tun kari wurin nomban da aka bashi. Bamu sha wahala ba don jirgin yana da matakala kamar a tudu muke a wurin shiga cikin jirgin kuma a kwai komai kamar yadda muke ganin sun shiga a cikin film. Bayan shigan mune kamar ance in daga ido sama ina dagawa na hango taju a tsaye saman bene yana kallon mu. Dan murmushi na sake tare da daga mashi hannu alaman bye kafin na karasa shiga cikin jirgin ga baki daya a lokacin har jirgin ya soma tafiya damu ko. A gaskiya masu kudi suna jin dadin su sosai a duniyan nan don idan ka dace da rahaman ubangiji gaskiya ka huta . Allah yasa mu cika da imani na fada a raina kafin na kai zaune ina mayar da idona rufe ba komai ya sani haka sai tunawan da nayi da irin rayuwan da yaya yake ciki. Ya haka kuma keda kikace jirgi kike son shiga kika rufe idanun ki yanzu kuma ? Jin hakan da nayi yasani bude idanun nawa na sauke a kanshi yana zaune ya bude system ko har ya fara aiki a cikin sa yake wanan maganan. Duniya nake tunane yaya na bashi amsa don nasha alwashin sakewa dashi yanzu a kan taju duk yadda zanyi sai naga na raba wanan alakan nasu koda kuwa yin hakan bazai sa yaya ya daina ba sai dai ya canza wani katon bashi ba. Tunanen me kikeyi na duniya nace a daidai lokacin da nayi wani irin zama na yan barikin mata ina dora kafana daya saman daya. Wanda yin hakan har ya baiyanar da rabin cinyana a waje wanda dama rigan nada tsaga har kasa idan mutum yayi irin hakan zai baiyana sosai a gani. Duniya aljanan kafiri lahira kuma ta mai rabo duk wanan jin dadin naga iyakar shi duniya za a barshi ba a zuwa lahira dashi nagani. Yaji maganan sosai har cikin ranshi sai dai bai kara magana ba yaci gaba da abinda yakeyi a cikin computer din shi ya kyaleni. Tsawon wani lokaci wurin yana shiru jirgin sai tafiya yake damu a cikin ruwa hannu na mika na dauki dayan cup din dake saman table din dake tsakiyan mu ina tsiyayya ruwan enabi na fara kurbawa a hankali. Yana sane da sabon halin dana tsiro dashi don yasan ba haka nake ba da rashin kunya sai dai yana bina yaga iya guduna kawai. Daga inda nake zaune na kara daukan kofi na tsiyaya drinks din na mike a hankali zuwa gefen da yake zaune na zauna gab dashi ina mika mai abin sha. Dan juyowa yayi ta miko min bakin shi da zuman wai in bashi don shi wanan ba komai bane a gareshi. Don ko Aisha da take kanwarsa watarana ina gani itace ke basa a baki yana sha tun ina zagin su har na saba da ganin hakan na daina. Tunawa da hakan da nayi banyi sanyi a gwiwa ba na mika masa ya kurba a hakan har ya shaye cup din. Na aje na dan jiginu da jikin shi tare da daukan jaridan dake saman table din wanda aka aje don mu na fara karantawa. Matane sexy girls gasu nan iri iri ko wace da irin nata shigan ciki computer ya rufe tare da fadin ki tashi mu leka waje kuga ruwa. Don ita sadiya tana nata aikin kallo a cikin wayan ya dauke mata hankalin ta garemu tana jin hakan tayi saurin dago kanta tana son jin amsan da zan bashi. Batare da yin magana ba na mike zaune shima mikewa yayi muka fita sosai muke jin dadin wanan fitan namu don sai da gari yai duhu muka dawo masaukin mu a cikin an,nashuwa. Tun fitan shi dakin ko washe gari bamu kara jin duriyan shi ba saida yamma ya shigo muna ruwan saman da akeyi a garin ya dan dukeshi. Don ni a lokacin har zuciyana ya fara wasi wasin din ko dai taju shima ya nuna fushin shi kan fitan mune yasa bai shigo dakin namu ba yau ya fita . Tunda taju din da ire iren su sune kishiyoyina a yanzu wurin shi yasa na fara wanan tunanen haka sai gashi ya shigo dakin da yamma. Gaidashi din dai mukayi yake tambayan sadiya ko zamu koma ruwa ne yau din ma Sadiya mu kwana a cikin ruwan. Da sauri tace a,a yaya j bazan koma ba jiya ma banyi barci da dadi ba wallahi don da zaran na rufe idona ruwan nake gani saina bude. Matsoraciya yace yana juyawa ya fita dakin yakan shigo da dare kafin mu kwanta sai gashi bai shigo dakin ba ranan. Hakama washe gari bai lekomu ba sai wajajen karfe biyu aji wayan dakin na ringing na dauka. Muryan shine a cikin wani irin yanayi yake fadin zainab sun kawo maku breakfast ki hado min ruwan zafi ? Nace eh yace ok black tea kawai zaki hada min ki kawo min yau ban fita ba bana jin dadin jikina ne kadan. Subbahanallahi nace hope dai da sauki yace ciwon kaine kawai ke damuna har nakai wurin kayan breakfast din sai wani tunane yazo min a rai. Da sauri na koma na dauko wanan maganin ba tare da nabari sadiya ta kula da abinda nakeyi ba na nufi wurin da zan hada mai tea din da jakkata. Na hada kamar yadda maya tayi min bayani na dauka na kai mai dakin da shine farkon shigana tun zuwan mu Dubai din duk da bamu da nisa dashi. Yana kwance saman mamakeken gadon dakin jikin shi saye da dogon wando ash colour sai farar singlet daya saka a saman jiki ya kife cikin saman gadon yana kwance na shigo dakin. A hankali na taka zuwa bakin gadon saida na kai zaune nake fadin ga ruwan tea din nan yaya na gado maka gaba sai faman faduwa yakeyi kamar nayi laifi za a kamani. Dan dagowa yayi sai ya koma kwance yana tsuki kafin kuma ya dago da karfi ya tashi gaba daya yana fadin a daidai lokacin da nake mashi sannu, da jiki yace. Ina ganin ruwan daya dan dukeni ne jiya yaja min ciwon kai dama jikina bai shiri da dukan ruwa ko kadan. Kasha magani yace nasha don dashi nazo ban faye yarda da magani su nan ba shiyasa nake tafiya dashi duk inda zani. Ya shiga ban daki ina ganin baki ta wanko ya fito har lokacin ina zaune a wurin dana zauna din ya dauki ruwan shayin yana kurbawa daga tsaye. Dan kai na dago na saci kallon shi na dukar da kai shiru muke bayan ya gama kurban ruwan tea din ya aje cup . Ganin hakan na mike na dauki cup din na fita dashi da zan fita nace Allah ya sauwa yake fadin ai barci zanyi na dan lokaci ko zan tashi inji saukin shi. Nakoma daki da fargaba a ciki zuciya do dai kam na kada na bashi ya kuma sha saura in jiran hukuncin ubangijin mu yanzu kam a kan wanan lamarin. A cikin wanan tunanen ne har barci ya daukeni ban sani ba barci sosai na samu nayi a lokacin a can cikin barci nake jin wayan dakin yana ringing alaman kira yana shigo min lokacin . Da kyar na iya bude idanuwana da sukai nauyi saboda barcin na mike da kyat din kuma na jawo kan wayan dake gefen gadon. Muryan yayane baya fita da ji yana cikin tsananin ciwo a lokacin yana fadin zainab kizo kada in mutu . Gabana ya bada ras ras lokaci guda da sauri na sauko saman gadon ban tsaya jiran komai ba na nufi hanyar fita waje zuwa dakin nasa. Ina shiga yana wani irin nishi da kakari kamar zai mutu ya dafe cikin shi da hannun shi daya yana mulmula a kasa. Da sauri na karasa inda yake kwance saman ties din yana wanan gurjin kamar karimin yaro. Gaba sai faduwa yakeyi don tsoro don ni su maya basu fada min zaiyi wanan wahalan ba haka. Tsugunne nakai saman kamshi ina dan kiran sunan shi da yaya yaya me ya sameka haka ina fadi a rude tare da kai hannuna saman jiki shi ina taba shi. Bai iya dago kai ba ba kuma magana sai kokarin nuna min cikin shi da yakeyi da hannun shi na kara rudewa sosai. Magana yake son yi ya kasa haka yasa na mike a rude ina kuka zan fita daga dakin naji ya rike min hannu na a cikin nasa. Na dawo inda yake din yana son kara yin magana yai wani irin yunkuri sai ga amai yazo mai lokaci guda wani irin bakin amai da ban taba ganin irin saba a duniya. Amai yayi sosai a wurin na kara rudewa kamar rayuwan shi zai dauke a lokacin duk ya fita cikin yanayin sa lokaci guda har halittan shi ya dan sauyawa ganina. Nishi yakeyi sama sama can ya samu magana yazo mai da karfi yana fadin dauko wayana ki kira a kaini asibiti don Allah kada in mutu. Da sauri na mike na nufi wurin gadon dakin ina neman wayan nashi a karkashin filo naga wayan na dauko ina tambayan shi wani nomba zan kira. Mai 00 karshe ya fadi yana mayar da kanshi a kasa da alama sayin yake so sosai a lokacin ya ban tausayi matuka. Kamar jira suke a kirasa baifi minti biyu ba sai gasu dakin da gagawan su suka daukemu zuwa asibitin. Likitoci sunyi aune aune a kan aman da yake yi din basu gane dalilin aman ba, yan magunguna suka bashi tare da karin ruwa muka dawo masaukin mu dashi. Duk ya zabge lokaci daya yayi wani irin rama mara ma,ana a jikin shi ko don ban taba ganin wani a irin wanan halin bane oho ? Aman bawai ya tsaya bane ga baki daya don yana yinsa lokaci lokaci idan ya taso mai da kyat mukaga safe ranan dashi don a dakin nasa na kwana. Washegari ya dan tashi da dama amma duk jikin shi ya sake bai ko iya tafiya sai da kyat da bin bango yake iya zuwa ban daki ya kewaya. Har na gane yana tsunguni ranan ya dawo ya kwanta ina zaune na zuba mai ido cikin tashin hankali da tsoron abinda zai biyo bayan hakan a kanshi. Wayan shi dake gefe yayi kuka na dan kalleshi idon shi a rufe baida niyar budewa balle ya dauka. Har kiran ya katse wani ya kara shigowa sai nakai hannu na dauka sunan mami na gani da sauri nayi recieve kada ya kare katsewa irin na dazun. Jafar lafiya banji ka kira ba tun jiya ta fada mami bashi bane gashi kwance baida lafiya tun jiya din na bata amsa . A rude tace meya sameshi kuma zainab injin dai ba abin bane ya fara bashi matsala har muryan ta yana sarkewa a lokacin don rudewa. Mami daga ciwon kaine sai ya koma amai da tsugunni a yau din jiya dai aman yakeyi kawai. Yanzu kuna ina ne wai ta tambaya, nace muna nan Dubai munzo hutu ne last week kunje asibiti ko nace jiyan munje sun bashi magani muka dawo. Barin fadawa mamud ko zai iya tasowa yau yazo idan zai samu jirgi a lokacin naji ya dan yi magana na juyo gareshi yana fadin Kice ta barshi zamu koma chaina ne inje asibiti can likitana ya ganni a can din ba sai yazo ba. Na fadawa mami din abinda yace nan ta fara fada hankali tashe nayi shiru ina saurarenta tana fadin zai dauki ciwo tundaga Dubai har zuwa chaina nan babu likitocine da zasu dubashi ? Nikan karshe wayan na kara mashi a kunnen shi yana jin fadan da mami din takeyi a wayan yace a karshe mami na riga nayi booking ko zai gani da zaran mun isa can din. Yau zamu koma insha Allah anyi booking din jirgin tafiyan mu a yau din don likitan shi yasan matsalana. Ba zainab din waya muyi magana ta fada ya miko min wayan tace zainab don Allah idan kun isa kinga abin bai tsaya ba ki kira mu ki fada muna halin da ake ciki . Murya na rawa nace tau mami insha Allahu ki kula dashi sosai don Allah zainab nasan halin jafar da gardama kada ki daka ta nasa don Allah. Ni yanzu idan mami tana min magana sai abin ya dinga ban mamaki balle yanzu da har mami din taji wai muna dubai da danta bansha zagi da sheri ba. Wai har da danka min kula da dan nata a hannuna tana wani hadani da Allah can bayan ta gama min cin fuska a baya. Don darajana da kima baikai na wace zata shiga cikin wanan daulan ba na danta iya abinda mami ke nufi dani ke nan ba wani abu ba. Amma yanzu data ga dan nata yana da mugun tabo masu yawa da kyama a rayuwan shi shine take kokarin nuna min cewa tana sona a cikin ahalin ta a yanzu. Idona na runtse wasu hawaye masu dumi suna zobo min meta fada maki daya sakaki kuka a yanzu muryan shine cikin sanyin murya yake min wanan tambayan. Ban iya bashi amsa ba sai mikewa da nayi don barin dakin da sauri kada ki fita ki barni haka a cikin wanan halin da nake ya fada. Ja nayi na tsaya wuri daya ban kara gusawa ba daga inda nake tsaye din yaci gaba da fadin banji ta fada maki wani abinda zai sakaki kuka haka har ki fushi ki fita ba ki barni ni kadai ina cikin wanan halin. Don koma ta fada maki bazan yarda da hakan ba kema kin sani don haka ki dawo ki zauna har na dan kara jin karfin jikin nawa. Zan je na fara shiri ne na bashi amsa ba tare dana juyo inda yake ba nake magana ina kokarin fita duk da ya hanani ina son kebewa inda zanyi kuka ma,ishina ba wanda zai hanani a yanzu. Bina yayi da kallo har na bace mai da gani kafin ya sauke ajiyan zuciya yana runtse ido cikin takaici don shidai ya rasa meyasa ni kuka a cikin wanan maganan kuma ? Ban iya zama dakin ba don halin dana barshi a ciki koda na koma na samu ya fito ban daki ya zauna a kofan don bai iya karasowa cikin dakin da kafafun shi a lokacin. Nan kan hankalina ya tashi sosai don sai dana kamashi ya koma saman gado ya kwanta na shiga fadi a raina shike nan nine zanyi ajalin yaya ke nan ashe ? Kofa aka buga don shigowa na mike na bude kofan wasu mutum biyu ne na sama a wurin tsaye suke tambayana shi na nuna masu ciki da hannu suka shiga. Ashe likitane da wani abokin shi suka shigo basu fita ba saida aka daura mai ruwa da sauran magani sai gashi ya samu karfi har sallah naga yayi a tsaye bayan fitan su. A lokacin hankalina ya fara dan kwantawa don ganin ya soma samun lafiya a jikin shi yanzu dama ni tsorona shine kada ya halaka a sanadiyar maganin da na zuba mai wani abu yazo ya same shi kuma. Karfe takwas na dare muka bar cikin hotel din mun dan jira kafin jirgin ya tashi zuwa tara na dare muka bar kasan zuwa chaina. Muna isa asibiti aka wuce dashi daga can duk gwaji likitan yace shi baiga courses din ciwon nasa ba sai dai idan wani abu yasha na daban da ya jawo mashi hakan. Sai dai nan din sun kwatar dashi na kwana biyu kafin su sallamoshi ya dawo gida ya karasa jinya a gida kuma yana shan magani. Bashi dake jinyar ba koni na rame sosai don ciwon nasa ya daga mi hankali amma yanzu da naga ya dawo normal na fara sake jikina nima. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DON SAUKE HAKKIN WANI A KANKI, , , Alhamdullahi zan iya cewa don jikin yaya yayi sauki sosai kuma ina bashi kulawan daya dace sosai a matsayina na sunan matar shi. Yar uwan shi kuma mafi kusa dashi a yanzu haka yasa na zage sosai wurin kula dashi din don shima a iya yin shi gaskiya yana nasa kokarin damu tankar yan uwansa na jini. Don haka naba kaina shawara dama kuma kinsan mace ga rauni da sanyi hali a wurin namiji nima hakan ne yaci don shi kanshi saida yayi mamakin yadda nake bashi kulan a lokacin. Ba tare da wani jin komai ba tsakani da Allah nake masa komai yadda ya kamata don shi kanshi ya fahinci hakan. Safiyane yau na shirya cikin wani riga ja na daure kaina da ribon mai ja shima da farin duwatsu. Dan gyale ja na dora saman kaina sai dai bawai rufe kai din nayi ba sosai sai kamshi da jikina keyi a lokacin . Dakin na part din shi na nufa don gaida shi da kwana akwance na hango shi ya kurawa silling din dakin ido kamar mai tunane. Kamar yadda na saba idan ni nazo gaidashi da kwana bashi ya sameni a zaune part dina ba. Jin motsina baisa ya motsa a yadda na riskeshi ba har nakai bakin gadon na gurfa gwiwa bibiyu ina fadin yaya ina kwana ya karfin jikin kuma ? Zainab na dago kai na kallo shi sai kuma naga ya danyi gajeren murmushi ya kawar da kanshi daga inda yake kallo. Haka sai yasani tsarguwa da yadda yai min din ina a yadda nake ban motsa ba nayi shiru shima hakan baiko amsa min gaisuwan da nayi masa ba na safen dana saba zuwa part din in gaida shi don da sadiya mukan zo gaidashi din ranan kuma ni daya nazo. Sai can nace dashi a hada ruwan wankane ka watsa yanzu na fada ina kallon shi don jin amsan da zan bashi. Ki hada nima ina son inyi wanka yau in dan fita tunda naji sauki sosai mikewa nayi zuwa ban dakin na hada mai ruwa kamar yadda yake son yi dashi tun ranan farko daya fada min yadda zan hada mai din. Na hado ruwan na dawo na fada mai zan bar part din tunda ba wai wani hira mai tsawone irin na mata da miji a tsakanin mu ba dama. Muryan shi ke fadin sai ki fitar min da tufafin da zan saka idan na fito tunda yanzu naga zaki fara aikin ki na mata a gareni. Wani irin juyowa nayi ina kallon shi a cikin mamaki a fuskana don jin abinda ya fada din gareni. Ba matsayin mata ya saka nake maka wanan ba a matsayi kanwa a gareka da kuma Allah nake maka komai don ka cancanci hakan a gareni . Ina fadan hakan na sa kai na fice daga dakin don jin da nayi yace fita zaiyi a lokacin da ba haka ba idan na shigo bana fita haka zan zauna a wurin shi. Duk da ba wani magana mai tsawo ko hira a tsakanin mu saidai kowa yayi sha,anin gaban shi a dakin ko ina tunane ko taba waya wanda hakan yakan daukeni wani lokaci mai tsawo a wurin shi. Wanda bai sani ba sai ya dauka wani hiran arzikine ko wani abin miji da mata ya tsayar damu a cikin dakin lokacin. Alhamdullahi gaskiya don jikin nasa yayi sauki sosai saidai da alama har yanzu baya jin karfin jikin nasa ko kadan. Karfin hali irin na mazane kawai yakeyi yana fita don kada ya zauna don da mace ce nasan har lokacin nan tana kwance tana fama da jikin ta. Saidai wani abin dana dan kula dashi a yanzu shine irin kallon da yaya yakan min wani lokaci kallo ne mai tare da ma,ana iri daban daban. Na kasa fahintar dalilin hakan da yake min wani lokaci idan zamu hada ido dashi zaiyi saurin kawar da idon shi gareni. Gashi a yanzu ya dora min nauyin hada mai ruwan wankan shi duk safiya duk da komai a hade yake amma dole sai naje na hada mai zai tashi yayi. Haka cin abincin sa dole ina wurin har ya gama zamu tashi duk da ba wani hira tsakanin mu a lokacin. Ga mami da ke kira yanzu kamar ta bude ido ta ganta a kasan takeji don zata kira akalla sau uku a rana tana jin halin da muke ciki a nan. Wanda wanan kiran har ya soma samin zarginta kan dan nata watay ita duk abinda yakeyi ma bata ganin laifin shi ashe ga hakan don yadda naga ta damu da halin da yake a yanzu. Har take fadin idan azumi yazo zasu shigo su ganshi su danyi azumi tare damu suna jiran Aisha ta karasa karatun tane aiyi bukin yayye su yasa basu zo a yanzu ba. Tabdi ba zuwan mami din ba sai irin takura min da sukeyi idan sun zo da fanin laifina ko kyashin da baya boyuwa a fuskokin su. Shiko cewa yayi yana farin cikin da zuwan su indai zasu zo din suyi azumin a tare damu zaiji dadin hakan.. A raina nace tunda kai da uwarka baku da matsala duk tudun laifin ka bata ganin hakan gareka sai ma so da take nuna maka zallah ai kace kana farin ciki da hakan . Muryan shine ke fadi yana kallona yace zainab na san kema zaki fini jin dadin hakan tunda yanzu naga naku da mami din yanzo daya har tana maki sako a boye ko ? Ban sani ba don wani aiki sai mami na sani da sauri na dago kai na kalleshi tare da fadi cikin mamaki sako kuma ? Daga wurin mami yaushe mami tayi min sako dana zo kasan nan idan ma har mami zata aiko min wani abu ai ta hannun ka abin zai fito. Hakane fa kuma ya fada yana murmushi yana batun mikewa tsaye na sake fadin sai dai idan ka manta baka ban sakon ba yana hannun ka ? Banjin yana a hannu na gaskiya sai dai idan na manta nima nake ganin kamar ke ra aikowa anywhere forget it ba damuwa. Bayan shi nabi da kallo har ya fice kafin in tabe baki ina mayar da kaina ga kujeran da nake zaune tare da lumshe idanuwa na nadan lokaci. Tunda mami ta furta zata zo yake shirin zuwan su din duk da bai fads ba nasan abinda yasa ake wasu yan gyare gyare a gidan wanda ya dace. Dare ne naga bai shigo ba yasa na shiga part din shi tunda nasan yana gidan bai fitan nan da yakeyi a baya yanzu ya daina tunda yayi ciwo baya yawan fita koda rana da ya dawo office yana gida sai kuma gobe idan ya fita. Wando ne da riga tie a jikina baki rigar kuma yellow mai dan fadi wuyan shi ma da fadi sosai. Sai dai rigan ya dan sauka ya rufe min mazauna na rabi kayan sun matukar karban jikina sosai sun dane min jiki da kyau. A falon shi na saneshi zaune da kwalba da cup a gaban shi ya zauna ya mike kafafun shi saman karamin table din dake gabab shi . Yayin da dukkan maballeyan riganshi suke bude mashi duk chest din shi a waje ya dafe kanshi da hannun shi daya kamar mai barci. A hankali na tako zuwa inda yake zaune ganin kamar yana barci yasa dana kare mai kallo nake batun juyawa na bar dakin. Ina zaki kin shigo kuma zaki fita yana sauke hannun shi data dafe goshin shi yake fadin hakan . Kallon kwalban da cup nayi na turo baki kafin nace naga kamar yau dakin yafi karfin shigana ai don naga kamar ka gama warkewa yanzu. Dan murmushi yayi yana gyara zama tare da fadin zoki zauna a nan mu sha tare don na yau din tare zamu sha dake ai. Wa ni na fada har ina nuna kaina da hannuna nace Allah ya tsare ya kareni don ni na zabi na Allah da wanan na nuna da bakina inda kwalban yake. Kanshi ya dan mayar ga makarin kujeran ya lumshe idanun shi a hankali yace yana taba wurin da yake zaune ta gefe zo zauna a nan nace maki ko ? Kallin shi nayi kamar in tafi nake ji sai kuma wata zuciya tace min naga iya gudun shi ga hakan sai na tako na zauna kamar yadda yace min din. Na zauna a dan takure ban sake jikina ba da zaman ya dago yana zuba abin a cikin kofi ya miko min yana fadin karba ki dan sha. Wani kallo nayi mai ina kawar da kaina gefe daya nake fadin har abin yakai can yaya ka koya min shan wanan haramiyan abin ? Dauki kwalban ki karanta idan na cutarwane na baki yana komawa yadda na sameshi da farko saman kujeran. Ban karba sai mikewan da nayi na fice part din ga baki daya raina a bace ina tunanen irin halin yaya da abin haram ba komai bane a gareshi shi ?. Har ni yakecewa yau wai nasha giya a tare dashi don kawai ya mayar dani yarinya ko me ? Ko wawiya ya daukeni ko bakyauya har yanzu ban san komai ba kan hakan har yake kokarin juyani ga halaka. Ranan banyi barci ba sai na daman sanin sa da nayi ga baki daya ina jin wani irin tsanar shi yana karuwa a zuciyana lokaci guda. Washe gari ma kin shiga nayi wuri shi don karya shigo mi part sai naki bude ko ina da safe na lafe a dakina kawai. Don ranan bamu zuwa makaranta daga ni har sadiya muna gida a kwance abin mu shidai ne mai fita baya dadewa koshi a irin wanan ranan. Ganin bamu bude kofan mu ba yasa shi fita bai ganmu ba sai text da yayi min a waya dan guntu da cewa nina fita sai na dawo. Na tabe baki ina jefa da wayan saman gado don haushi tare da fadin dan iskan mutum kawai ka fara bata kanwar ka kafin ka bata ni mana Daya dawo din ma bai nememu ba part din shi ya nufa ya rage kayan jikin shi ya shiga ban daki ya watsa ruwa a jikin shi don yaji sanyi.. Sai bayan da yayi sallah isha,i ne ya fito zuwa part din ya samemu zaune a falon mu muna kallo sadiya ce ta fara gaidashi da dawowa. Sadiya yau ba assignmemt din ke nan kika tsaya kallo a nan tace yaya ba test saidai zamu fara exam bada dadewa ba. Ya kai zaune tare da kallon inda nake yana fadin ya zainab kuna lafiya dai ko yau banji duriyan ki ba gidan nan. Baki na turo gaba ina fadin lafiya nake bagani ba yanzu a zaune au har yanzu fushi kikeyi kan wanan maganan ? Dan dagowa nayi tare da kallon shi watau shi baima dauki hakan komai ba ke nan har yana tambayana yanzu. Amma ke zaki iya bani abu insha ba tare dana sani ba koda abin zai wahalal dani a rayuwana idan nasha in dai bukatan ki zai biya ban damu da hakan ba ? Wani kallo nayi mai na mamaki sai na dukar da kaina kasa kafin na dago nace nasan ko na baka ba wanda zai cutar dakai bane sai dai ya taimaki rayuwan ka ai. Umm,humm haka kike tunane ko a naki zaton ban tunanen komai don nasan daidai nake ga abinda nayi balle ma banyi ba din sai abin da zuciyar ka ya baka kan hakan. Mikewa yayi tsaye ya fara tafiya ina kule dashi a dan kwanakin nan idan yana tafiya wani lokaci sai ya dafe gefen cikin shi da hannu daya yakan iya tafiya da kyau. Bin shi nayi da kallo har ya fice kodana juyo sadiya ta mayar da hankalinta gareni tana kallona. Da sauri ta duka kamar bani take kallo ba nabi lafiyan kujera na kwanta ina tunane a raina kardai ace yaya ya fahinci na saka mai magani a dubai ? Idan ko hakane na shugo uku ashe nawa ya sameni ke nan dashi tunda gashi ya fara sake min magana a fakaice kan hakan. Kamar maya tasan halinda muke ciki sai gashi washe gari ta fito min da zancen tana tambayana ko nayi amfani da wanan maganin kamar yadda akace nayi din. Ajiyan zuciya na sauke kafin na fara bata labarin abinda ya faru sai kawai naga tana tafawa tare da fadin ki godewa wanda kike bautawa da yasha wanan abin zee. Don na yarda da aikin kakata hundred pacent kan wanan da wuya ya kara kallon wani abin da zaisha har ya fita hankalin shi. Shi dayan fa kikai ga amfani dashi ta tambayeni nace ai lokaci guda duk na hada nayi amfani dashi tace Budah da cewan wai abin bautan su. Baki tsoron hakan zai iya tabashi don karfi ke ga maganin sosai ashe da gaske da ake fadin ku bakaken fata kuna da karfin hali sosai haka. Tsoro naji wani tunane yazo min dana tuna da yana yawan dafe gefen cikin a yanzu saidai ban san dalilin da yasa yake hakan ba da yake yi ? A maraice na bata labari irin yadda yakeyi a yanzu tun bayan ciwon da yayi na fita hayacin shi a Dubai. Dan tunane ta tsaya tayi kafin tace ina ganin sai mun koma wurin kaka muji ko akwai wani abinda yasa yake hakan. Zamu iya zuwa yanzu na tambayeta don na riga da na tsorace a yadda ta nuna min illan abinda nayi lokaci daya ba daidai bane. Dan duban lokaci tayi da dan tunane tace zamu iya don zamu iya zuwa mu dawo lojacin tashi ma baiyi ba a yanzu. Mota muka shiga tafiya mai dan tsawo ya kaimu kauyen nasu dake da dan nisa da cikin garin mun samu kakan a waje tana shanya wasu ganyayyaki tayi muna taro na arziki. Mun zauna an gagaisa ne maya ta kora mata bayani kamar yadda na fada mata tana mamulan baki irin nasu na tsofi take fadin . Kinyi aikin yarinta yarinya amma yanzu shan maganin yakai kamar sati nawa a jikin shi na dan yi tunane tare da dago kai na bata amsa baikai wata daya ba ina gani. Duduke ta mike zuwa cikin dan gidan ta ta dan dade ciki ta fito da wani abu kamar kankara da wasu dai maganin kala biyu a hannun ta ta miko min. Karba nayi da hannu bibiyu cikin girmamawa take fadin ki masa amfani da wanan zai daina jin abinda yake ji din da yardan mai duka. Don su basu yarda su ambaci Allah ba don basu san shi ba basu bauta mashi na karba ina istigifar ni dai bukatana kada ya halaka a sanadiya na shine fatana ban yarda da abin bautan ta ba tunda na fada tarko ko. Mun dawo yamma yayi sosai don haka ina sauke maya gida na nufo don nasan yanzu sadiya tana gida zai turo a dauke ta . A falon gidan gaba daya na samesu zaune tare dashi suna zaune shi yana waya ita kuma tana kallon tv na shigo a gajiye. Da sauri sadiya ta taso tana rungumeni tare da fadin I miss you sister tun safe na shafo kanta dake bude ina fadin bakya ji baki son saka hula a kanki sadiya. Na nufi inda yake zaune yana waya amma hankalin shi yana gareni tunda na shigo yana waya da hannu ya yafuto ni nazo dan hugging dinsa nayi ina fadin miss you. Ya dan rungumoni na dago zan juya muryan shine ke tambayana me kika jeyi sea side yau da mamaki na dago ina kallon shi. Na yadda har yasan inda naje na wayance da fadin munje duba wani projects ne a can bakin ruwan yaya baki kirani zaki tafi can ba saida na gani. Da wasu course mate dina muka tafi ban san zamu dade a can haka ba na dauka zamu dawo da wuri na bashi amsa yace take time next time. Bana son kuna zuwa nisa a garin nan don akwaisu da nuna wariyan fata wani lokaci kada wani abu ya samu mutum. Nace insha Allahu a raina kuma sai mamaki nakeyi yadda yau kawai har ya gane na tafi wani wuri na daban ba cikin school ba. Na dai samu na shige ciki don duk na gaji don na dan watsa ruwa don wani irun yunwa nake ji sosai a lokacin saboda banda ruwa ban iya cin komai a waje ko ruwan sai shanshi ya kama dole zan sha idan na fita. Don kasan kafirai ne ba zan yarda ko bread din su inci ko snacks din su ba don amfani da man alade ba komai bane a wurin su su yasa nake kiyayye hakan. Duk da yunwan da nake ji saida na rama sallolin dake kaina har isha,i saida nayi kafin na fito na nemi abincin da zanci. Shine ya shigo ina zaune ya saka wani jallabiya blue a jikin shi tafiyan shi kawai zaka gane cikin karfin hali yake a yanzu duk ya rame ya zube har duhu ya danyi. Zama ma da kyat ya kai zaune na dago kai na dan kalle shi cikin tausayi tare da sada kaina a kasa ina ci gaba da cin abinci don ba a dining na zauna ba. Jin abincin ya fita min rai nayi tunda naga yanayin da yake ciki din zuciyana naji ba dadi lokaci guda. Ban san lokacin da bakina ya furta mashi baka da lafiya har yanzu yaya don yanayin ka ya nuna hakan na fada ina ture abincin a gabana. Hannu ya mika ya jawo plate din zuwa gaban shi ya dan diba ya fara ci ba tare da yayi magana ba saida yayi kamar cibi uku ya koma ya kwantar da jikin shi saman kujera yana dafe goshin shi yace. Ban san meke damuna ba zainab kwata kwata na rasa gane kaina ga baki daya bana jin dadin komai a yanzu tunda ciwon nan ya kamani wallahi. Komai gaba daya ya fice min a rai haka bakina bana son ko kadan in saka abu a cikina sai naji shi kamar wuta na saka indan naci. Kaje asibiti na tambaya da sauri naje sunyi gwaje gwaje sunce basuga komai a tare dani ba har yanzu. Innalillahi nace ko mami zamu fadawa ta san halin da ake ciki da sauri yace No kada ki fada mata tunda zasu zo ai ki barshi ki dai tayani da addua kawai shinafi bukata a yanzu. Rabin addua na a kan kane ne ko yaushe yaya sai dai idan banyi sallah ba aiko na gode da wanan taimakon ke alherice zainab a gareni na sani ke sakon Allah ce zuwa wurina yanzu na gane hakan. Dago kai nayi na kalle shi yace kwarai nasan da hakan ba yau ba zainab ke din kin kasance a yadda banyi tsamani ba. Da farko wani sashe na zuciyana yakan min tambaya a kanki amma yanzu ta haska min matsayin ku a gareni daga ke har sadiya . Ban kara gaskanta zuciyana ba sai wanan lokacin da na kwanta ciwo na samu taimakon da ban taba zato ba a wurin ku. Zanma ce ke don kece mai komai da yadda hankalin ku ya tashi a kan hakan ya nuna min matsayin dan uwa ko mace a kusa da kai a yanzu. ZAINAB IDRIS MAKAWA LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA YAR UWA DON GUJEWA FADAWA HAKKIN WANI NA SAUKE NAUYI NA FADA ALLAH YA BADA IKON TSAREWA ALLAHUMA AMIN. Bayan mun dan gama zaman da zamuyine ya samu ya mike da kyar muna mai sannu da jikin yana dafe da cikin nasa ta gefe haka ya bar falon ya tafi. Na sauke ajiyan zuciya bayan fitan shi daga part din ina mikewa tsaye kallon sadiya nayi ina fadin shige ki kwanta dare yayi yanzu. Ta mike ba don taso ba ta shige tana turo baki gaba na kashe wutan falon na shige ciki don in kwanta saboda gajiyan dana debo a ranan. Saidai kodana kwanta barci ya gagareni sai faman tunanen abinda ya wakana a falon tsakanin mikewa nayi zaune don kwancin ya gagare ni a lokacin. Tabsa yaya yana ji jiki don iyanzu yakai ga fadi da bakin shi ga alaman hakan kuma ina gani shawara na fara yi a zuciyana na yadda zan bashi wanan abin da tsohuwar ta kara bani yasha a yanzu. Abinda ban sani ba shine ashe yana can daki yana mukurkusa shi kadai yayi amai tun yana iya tashi yaje yayi har tashin ya gagareshi. Da kyat ya iya daga waya ya kirani muryan shi kawai ya isa ya sanar ma da halin da yake ciki a rude na mike dagani sai rigan barci zuwa dakin nasa a rude. Kai ba dadi a yadda na same shi a kwance kaca kaca a cikin amai dan ihu na saka a cikin gigicewa yayi saurin bude idanun shi ya sauke su a kaina yana fadin. Kada kiyi kuka zainab nasan nina jawa kaina wanan kila giyan da nake sha ne yake min haka a yanzu . Ka bari in baka wani magani da nake dashi kila zai taimaka ma kafin mu kira muje asibiti dan murmushin karfin hali ya sake a fuskan shi. Haka yasa na juya da sauri na nufi dakin na tsaban rudewa ma baisa naga maganin da farko ba sai na dauka nayar dashi ne wurin sauri. Baki yar ba zuciyana ya bani hakan na tsaya nema a tsanake na ganshi can kasan jakkana dana jefa. Da sauri na dauki na nufi kitchen din mu na hada na kai mashi baiki sha ba da taimakona ya mike ya shanye ga baki daya ya koma ya kwanta. Kallon gadon daya baci nayi cikin dabara da hikima na gyara ko ina cikin ikon Allah sai gashi ya mike wai zai kewaya shine na samu daman gyara ko ina yadda nake so. Da alama ya samu sauki sosai don har ruwa ya watsa a jikin shi kafin ya fito don yaji dadin jikin nasa daya sake mai. Nina taimka mai ya saka tufafi a jikin shi can kuma ya yunkura kamar zai kara amai da ban san lokacin dana tallaboshi ba sa sauri. Yana ta kokarin kakarun aman bai samu fitowa ba ya koma ya kwanta sai barci ganin haka na dauki wayan shi na nemi layin mami na kurata. Tana dauka take fadin jafar ya akayine ya jikin da sauki ko nace a dan maraice mami bashi bane nine gashi kwance yau jikin ba dadi sosai. Innalillahi tace a rude yanzu kuna asibiti ne ko gida muke mami idan na masa maganan asibiti baya son zuwa ne. Ke wata irin yarinyace da har yanzu baki waye ba zainab idan kin masa magana baiji ba baki kaisa ko ki fadawa abokan sa suzo su kai shi mana. Ban san abokan sa ba mami kuma yakan ce dani ai yaje asibitin idan na matsa mashi din. Zainab idan kika bar min da ya halaka a kasan mutane ba zan yafe maki ba wallahi. Mamaki da rudewa ne ya kamani lokaci guda na rasa amsan da zan bata sai kawai na kashe wayan gaba daya na aje a gefen shi don kunnuwa ba zaici gaba da iya sauraren wanan matar ba a yanzu. Juyawa nayi inda yake kwance na dan kalleshi barci yakeyi har lokacin nima na dan kwanta a gefen har barci ya dauke ni ban sani ba a wurin. Washe gari abin mamaki ko daya tashi sai naga ya mike da kansa saidai rashin karfin jikin da baida shi a lokacin. Ya dan dade a cikin ban dakin kafin ya fito ya tayar da sallah a tsaye nan nasan yaji saukin jikin sosai mamaki karfin magani irin nasu nakeyi a raina. Ya dade zaune yana addu,a kafin ya mike ya koma ya kwanta saman gadon ya koma barci ranan dai ban fita ba don yanayin da yake ciki din. Yakai wani lokaci mai tsawo yana barci kafin ya tashi yana neman abinci yaci ya sake yin wanka ya fito a lokacin ya kunna wayan shi dake kashe. Kamar jira ake ya kunna kira ya kama shigo mai wanda kiran daga nan chaina ne abokai da wuri aiki suke kiran shi. Ban fada mai komai kan zancen wayana da mami ba saida ta kira shi da kanta tana fada wai haka kawai don keta na barshi gida ina kallon zai halaka ban kira a kaishi asibiti ba. Haba haba mami yarinyar nan fa tayi kokari sosai a kaina kuma ko yanzu tana ciki yin sa ne. Kaima ai kana kokari akan su don me ita bazatayi ba har tana fada min wai kana gidane a kwance. Haba mami zainab bata cancanci wanan kalamin ba a gurin ki don nasani ta tare shi da fadin ta yata zata biyewa rashin hankalin ka ta barka a gida. Ko dai meye ai mami zainab mata tace tasan zafina tasan ciwona don haka yarinyar nan tayi duk yadda akeso fa bai yarda uwar tayi wani magana ba kuma. Suka dan dai taba hira akan ciwon nasa tana tambayan shi ainihin abinda ke damun shi tare da kara nuna mai bakin cikin ta kan halaiyan da yake yi wanda take zaton shi yaja mai wanan ciwon haka a yanzu. Har dare yana duban yanayina ko zan nuna wani bacin rai kan abinda mami din ta fada mai nayi mata baiga alaman hakan a wurina ba shima sai ya share zancen baice dani komai ba. Da dare na shigo na gaidashi tare da bashi abinci ban fita ba saida ya gama na mike zan bar dakin naji ya ambaci sunana da fadin . Zainab haka yasa na juyo da sauri baiyi magana ba yasa na dan kara matsowa inda yake ban dai zauna ba amma na tsaya a cikin ladabi yake fadin. A lokacin daya lumshe ido idon shi a rufe zainab me kika bani nasha jiya ne naji sauki haka da sauri ? Magani oh wanan maganin ya dade a wurina dama dashi nazo tun daga gida na waraka ne kan cututuka ko wani iri na bashi amsa. Ya bude ido yana kallona kamar me nazarin wani abu ya ce dama kina dashi tare dake baki bani nasha ba nake ta wanan wahalan haka naji dadin magani sosai ina shan sa kamar an zare mi ciwon naji lokaci guda. Ban taba amfani dashi ba na fada ina juya don na matsu in bar wurin a lokacin kada ya kureni har ya gane ba gaskiya na fada mai ba. Kwana biyu kwatsam su mami suka diro garin shi kanshi bai san da zuwan su ba ban nuna mata komai ba don tun lokacin da mukai wayan nan da ita wani abu bai kara shiga tsakanin mu ba kuma koda wayane. Don sai naga kamar kwata kwata dai mami bata yi danine a rayuwan ta don banga laifin da za a dora min kan mutum mai shekaru kamar ya j ace wai nice zan matsa mai ya kula da kansa bayan shine ya kawo mu kasan ai. Nan muka shiga dawai niya da su kamar ba komai a zuciyana sai dai a gaskiya na barwa kaina duk wani abu da nake shiryawa a yanzu game da kowan su gidan. Lafiya kalau zan shiya masu abinci idan masu aiki sun gama ba zan fita ba sai na gama dasu don wanan tafiyan ba irin wancan bane da sukazo da yawan su . Wanan daga mami sai samarinta biyu da Aisha kawai suka zo part daya aka bar masu don hakane ba wani takura a tsakanin mu yanzu. A yadda mami take matukar son diyan ta wanda a yanzu na kara gane hakan sosai yadda duk da ya J yaji sauki a yanzu. Amma hakan bai sa wai mami ta nuna wai ita jinyar jafar din takeyi ba a fili tana nuna tafi kowa sanin zafin dan ta da sanin abinda yake damun shi . Wanda banyi tunanen cewa jafar din zai fada mata ba don da zai iya fadiawa wani nasan nice ta farko da zai fadawa hakan. Kawar da ido da kai ga komai yasa mami din bata samu wani kafan yi min wani rashin mutunci ba don haka muka zauna lafiya da kowa a cikin har azumi yazo suna kasan tare damu. Ranan a na zaune da safe samarin basa ciki suna waje sai shi da mami da Aisha ne sai ni da na shigo gaida mami din da safe zan fita zuwa school. Baki fita ba ke nan har yanzu kina gidan nan ya fada yana zaune a kasa kusa da kafan mami din abinda ban taba ganin yayi ba tun zuwan mu kasan zama a kasa. Karatun ai ba wai ta saka a ranta bane nake ganin mami ta fada ya dan gyara zama yana fadin ai mami zainab ta saka karatun nan a ranta sosai kuwa. Zainab din zaka ban labarin halinta a yanzu kuma jafar don ta zama matar ka komai ko ta canza ne ban sani ba ? Sorry ma na mance kin fini sanin halinta ai tana nan har yanzu da sanyin halin nan nata ai sai mami din taja wani tsuki tana kawar da kai. Aisha tace ya j ai yanzu ba zaiso a fadi wani kalma a kan zee ba koda tayi laifin ma balle yana ganin batayi ba . Aisha ke nan ki bar ganin mami da zainab suna abin su na uwa da yarta kice zaki saka baki tsakanin su har yanzu sai Allah ni zan baki labarin hakan. Ni dai ina zaune a inda nake ban ce da kowa kala ba a cikin su naji yaci gaba da fadin a daidai lokacin dana mike tsaye yana cewa. Har sako fa mami zata aiko dashi tun daga can ba zan san da hakan ba sai idan tunanena ya bani haka. Sako kuma naji mami ta fada da dan mamaki ni dai fita nayi ban karasa jin zancen su ba. Sai bayab na dawo ne na shiga gaida ita ta tsareni tana tambayana da fadin zainab jafar ya gaya min kece kika bashi magabin da yai sanadin barin shan giyar sa ko ? Na dago kai da mamaki tace ya fada min komai don shi a nasa zaton ko nice na aiko da abinda kika bashi din har yaji sha ya fice masa a rai ina tsaye ne a lokacin sai nakai zaune. Kafin ta kara fadan wani abu jalal ya shigo dakin yana fadin mami garin nan yana da dadin azumi sosai don basu da zafi irin namu can Nigeria gaskiya. Jekiki huta zamuyi maganan daga baya mami ta fada don ganin jalal din ya kai zaune a lokacin . Ya dago ya kalleni yana fadin dama magana ake irin na uwa da yarta nima dai ina ganin irin auren ya j zanyi mami in samu mata kamar zainab din ki don bana son mace irin Nuriya gaskiya. Fita nayi daga dakin ina dan murmushi don abinda ya jalal di ya fada saidai zuciyana cike da zargin maganan mami yake alokacin Bata kara min maganan ba nima haka banwa ko J din maganan ba saida akai azumi ashirin suka tattaro suka dawo Nigeria. Munyi sallah lafiya wanan sallah har idi muka tafi wanda hakan bai taba faruwa damu ba tun zuwan mu a gida zamu dai zauna . Sai dai mu kalla yadda ake bukukuwan sallah a kasashen duniya wanda mu nan cikin gida muke babu wani celebration da mukeyi. Sai gashi a wanan shekaran tun da daren muka bar gidan mu muka kwana a wani hotel a cikin wani unguwa ashe a can ne masallacin su yake da suke sallah a garin. Bayan an sauko ne motocin mu suna jiran mu muka dawo namu gidan wanan kan mun san ayi sallah don yadda yaya ya nuna muna har kwana biyu muna shagalin da murna da kai ziyara a gidajen yan uwa musulmai dake kusa don suna da musulmai tsararu a cikin kasan sosai ashe. Hutun sallah ba yawa ga ma,aikata don haka sati daya mukayi ana shagalin muka koma makaranta don ci gaba da karatun mu. Yaya kan a bangaren shi jiki yayi sauki sosai don bai wanan dafan cikin da yake yawan yi a baya yanzu. Gashi yayi wani kyau raman da yayi don zafin ciwo a baya duk yanzu yana shigewa ba a ganin wanan sosai a jikin shi don dan cikowan da yakeyi yanzu ba wannan kaman. Sai dai ina yawan tuna halaiyan mami na nuna kiri kiri son danta akan komai da take min don na lura nami ba ganin laifin dan nata takeyi ba asalima tana kokarin dora komai ne a kaina a ganina. Don ko dan zaman da mukayi dasu anan duk da da farko taso nuna hakan a fili amma daga baya sai naga kuma ta canza ta daina nuna min wani abu. Nima sai na dauka a hakan nake nuna ba komai a raina don haka kowa ya aje a ranshi da ba komai din dai. Ganin yadda yanzu yaya ya koma wani silent bai son hayani duk da dama can din shi din ba mai hayaniya bane sosai amma dai sai na yanzu din yayi yawa sosai. Don zai iya zama a wuri duk abunda zamuyi ba zai ko daga kai ya kalli mutum ba balle mu saka ran zaiyi magana kan kiriniyar mu har ya gaji da zaman shi ya tashi a wurin zuwa part din shi. Gama sadiya da har rawa da marming zata dinga yi koda yana zaune don ba karamin sabawa sukayi ba dashi sosai a yanzu. Wanda tun ina zargi a kan hakan har yakai na debe komai a raina nima mai dan girman bai damu dani ba balle ita da keda sha uku yanzu cif a duniya. Yau ma kamar kullun ya dawo wirin aiki da yanzu mun saba dashi idan ma ya dora dan dakiku a kai mun sani zamu fara fadin yau yaya bai dawo in time ba. Shiko da ya dawo baya zuwa part din shi kamar yadda yakeyi a baya nan wurin mu zai shigo direct mu gaisa ya dan zauna damu na lokaci kafin ya shige part din shi sai kuma bayan sallah isha,i zai fito aci abincin dare a tare tun bayan zuwan su mami wanan ya zama muna dabi,a a gidan yanzu. Zaune nake na tasa laptop a gaba ina aiki ban san shigowan shi part din namu ba don itama sadiya ta shiga ciki dauko littafin da take assigment kan shi. Muryan shi ne daya duka bayan kujeran dana zauna na mike kafa ina aiki a cikin system din na shagala ga karanta abinda nake sercheing a computer din. Naji muryan kamar daga sama yana fadin wanan ai da wuyan fanhinta da kin bi ta cikin Google direct zaifi ki fahinta ai. Ganin yadda na dan kadu ne yasa ya dan shafo kaina yana fadin kin cika tsoro da yawa duk security din dake gidan nan amma kike tsoro haka zainab ? Ban ji fitowan ka bane yaya sai muryan ka danaji a kaina yasa na tsorata da hakan. Zagayowa yayi ta gabana ya zauna yana fadin when last kukayi waya da mami tun bayan komawan su gidane wai ? Da sallah ma ai munyi waya sau biyu dasu na bashi amsa ina dagowa daga duken da nake ina kallon shi don jin dalili tambayan nasa. But tace dani mana yanzu kin daina kiran ta duk da na fada mata kin fara exam a yanzu baki da lokacin komai saidai tayi fada cewa exam ai ba zai hana ki kirasu ba . Zan kira na bashi amsa ina tagumi don nasan wani abin ke shirin tasowa kuma a kan wanan maganan da mami din tayi yanzu. ZAINAB IDRIS MAKAWA BARKAN MU DA SHIGA WANAN WATAN MAI ALBARKA YAN UWA UBANGIJI ALLAH YA SADA MU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN WATAN ALLAHUMA AMIN, , , , LITTAFIN KUDINE YAR UWA KADA KI MANTA DA HAKKAN DON KAUCEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , , Akwana a tashi ba wuya a wurin Allah yau gashi har na kamala karatuna a ta fannin fasahar kimiya a kasan chaina inda na fito da sakamoko mai kyau wanda yaya jafar ya nuna jin dadin hakan a fili har ya kasa boye farin cikin shi ga hakan. Yayin da sadiya take matakin yar gaba da primary a shekara na biyu zata shiga na uku a yanzu daidai lokacin dani na kare nawa karatun . Har lokacin muna matsayin kannesa ne ga ya J da muke zaune a gidan shi wanda kuma ta dalilin shi muka samu wanan matakin na ci gaba da muka samu a rayuwan mu. Eh ba zance ya j ya daina duk wasu mugayen halaiyan sa dana san su a baya yana yi ba don a yanzu in ma har yana yine saidai in a boye yake wanan rayuwan do banga hakan a gare shi ba gaskiya. Asalima a yanzu ga baki daya ya koma kamar ba ya J din da muka sani a baya bane don ga baki daya ya canza gaba daya . Ya koma wani irin mutum mai taushi da tausayi ga ibada da kula a tare dashi ga natsuwa da kamala da kullun yake kara sauka masa. Banga wani shirin da yaya yakeyi don zuwan mu gida ba asalima ni yanzu da zaman gida kawai nakeyi yasa wanan damuwan yake damuna a raina har karshe na kasa boye hakan a zuciyana. Yau tun safe na tashi da wanan damuwan a raina gashi ni kadai ne a gida haka zan wuni daga kallo sai in shiga interneat ina searching shine kawai aikina. Ina zaune a babban falon mu tv na aiki saidai ba kallon nakeyi ba hankalina yana gun computer na dake gabana ina hada wani kimiyan da nake tunanen hadawa danaga ana tallan shi ko ina a kasan. Pretty me kikeyi haka ya fada a bayana na dan dago kai na kalleshi tare da dan sake murmushi a fuskana ina fadin yau ka dawo da wuri haka yaya ? Na dawo ne don nasan ke kadai ce zaune a gida yanzu yasa naga ya dace ba dawo ba dubaki ashe ma na manta kina da abokin hira gashi a gaban ki. Wanan bai rage min komai yaya sai kewan gida da yanzu yake damuna sosai ina son zuwa gida na ga Inna ta da yan uwana yaya . Wani kallo yayi min daga inda ya zagayo ya zauna a gefena gida a yanzu baki ganin yin hakan zai taba karatun sadiya ? Ai ba don karatun ta muke nan ba na fada a dan hasale OK tunda ke kin karasa naki zaki fadi haka ko ? Ba hakana bane yaya gani nayi kayi alkwarin hakan a baya don Allah yaya ka kaimu gida mu duba su yanzu kusan shekara biyar ke nan muke nema rabin mu da gida fa. Ba yanzu ba zainab gaskiya don so nake kici gaba da karatun ki a cikin shekaran nan in Allah ya yarda. Ba zan tsaya karatu ba a nan gida zan koma karatun ya isheni haka yaya nima fa haifana akayi zanso na samu ladan da ko wani da ke samu ga hakan. Bai min magana ba sai mikewan da yayi lokaci guda ba tare da yai min magana ba ya fice a falon na bi shi da kallon mamaki. Wanan dan maganan ya jawo muna dan tashin hankali a tsakanin mu har yakai munyi dan kwanaki baya kula wani harkana a gidan yana shan kamshi dani. Ban shiga harkan shi ba duk da hakan yana damuna sosai don sai yanzu na san ashe ba karamin sabone tsakanin mu a yanzu. Tun ina daurewa har ya kai na kasa hakan ina shawara kan na same shi na bashi hakkuri sai dai nakan tambayi kaina idan naje ince masa me ? Ban san ya ake abi sallon ba miji hakkuri ba indan irin haka ya faru a tsakanin su balle mu dake zama irun na wacin gadi da juna kinga hakan ashe zai min wuyan fahinta don nawa kaddaran auren yana daban dana sauran mata gaskiya. Don haka ban kara gigin wanan shawaran a raina ba don haka na kawo ido na zuba mai kawai na bisa a hakan kowa yana harkan gaban shi a tsakanin mu. Ina kallo sai dai ya dan shigo yai magana da sadiya ba zai dade ba ko ya zauna zai fita sai kuma gobe. Saidai hakan ni bai hana in ya shigo da safe na gaidashi ba ya amsa min a dakile gashi ba inda zan kaishi kara inji sanyi . Wurin mamine nasan ko nakai goya masa baya zata yi kan hakan karshe ma ta kara min wani zafin da yafi wanda nake ciki a yanzu din. Don kanshi ko me ya gani ranan muna zaune falo da dare da sadiyan ba wani hira mukeyi ba sai rage dare a tsakanin mu ya shigo. Ga hasken kwan falon na wuta ya haska mu tar ina zauna a cikin wani riga mai shara shara a jikina rigan baida hannu sune irin kayan dana sakawa a kasan don yana sauka min har kasa . Gasu su ba jallabiya bane ba kuma abaya ba haka suke kamar kayan yan brazil da sukafi amfani dashi wurin wani bukukuwan su na shahara. Sai dai ni da ba bukin nake zuwa ba a gida nakan saka abina ko shi ba don kwaliya ba don dai kawai ina dasune da yawa nake amfani haka dasu. Kayan suna min kyau sosai a jikina idan na saka saidai ba wanan a raina nidai zan saka kawai don ba wanda zan burge ga hakan idan ma nayi ne don shi din ba wai burgeshi zanyi ko jan ra,ayin shi ba a kaina. Sadiya yau kuna wani show ne a nan banda labari ya meka gani ta fada tana dagowa daga kwancen da take tayi rub da ciki saman kujera. Gani nayi dai yau kunyi wani kyau daku ko zamu fitane ku ga gari ko kada wanan kwalliyan haka ya tafi a banza. Ba a banza bane yaya tunda ka gani har ka yaba ai idan mace tayi kwalliya a mijin ta tayi akace . Daga inda nake zaunw na watsa wa sadiyan wani kallo mai harara don abinda ta fada din nake fadin. Miji sadiya yaushe nayi auren har zan wa mijin kwaliya ya gani dani da wance bata da aure babu bambanci a tsakanin mu a gun wasu daine nake matar aure kamar su inna da sauran yan garin mu. Maimakon yai fushi da abinda na fada sai gashi ya wasance yana fadin sadiya kin yarda dav zancen nan nata wai ? Gaskiyane yaya duba ga har yanzu bata haihu ba tana da wanan hujjan don burin su inna a kullun tayi waya damu zanji tana tambaya wai har yanzu shiru babu labarin haihuwa gareta ? Killa shiyasa ta fadi hakan yanzu duba ga sauran yan kauyen mu sa,annin auren ta ai duk suna da haihuwa biyu ko ukku wasun su ? Sadiya naso ace kin girma a gaban su inna da wanan wayau naki bazai dauki garin naku ba mema sunan kauyen naku ? Lah yaya har ka manta da sunan garin namu niko ko barci na tashi akace min meye sunan garun mu zan ce Anchau da gudu. Yau hausa suke a tsakanin su sosai don bai faye mata magana a cikin yaren hausa ba nice dai koda yaushe hausa nake mata a tsakanin mu don kada mu manta da yaren mu mu koma gida ai muna dariya wata rana. Idan ba haka ba sai ince da yanzu sai turanci da yaren yan garin da take ji a yanzu don saurin daukan yare dake ga yaro ko ni ba a barni a baya ba wurun daukan yaren su don ina jin wasu masu saukin dauka a yanzu duk da ban mu,amula da kowa sosai kamar maya da yanzu naje gidan su yafi a kirga don kaina . Gashi duk zuwa kakan maya din sai ta hada min maganin irin nasu ta ban wanda ban san irin amfanin su ba a gareni ina dai karba ina sha don sanin ba masu cuta min bane. A zancen da yakeyi da sadiya din kuwa raina yakai kololuwar baci a lokacin dashi don fadin wai ya manta da sunan garin mu a cewan shi yanzu. Ba abin mamaki bane don ka manta da sunan mahaifan mu ai yanzu tunda ka biya bukatan da kake dashi akan mu. Murmushi ya sake tare da fadin ai ban isa in manta dasu ba a rayuwana sunan garin kawai na manta kuma sadiya nake tambaya ta fada min ba wani ba. Ai gata nan sai ta fada ma da bakin ta kafin ma na rufe baki sadiya tace dashi ANCHAU ne sunan garin mu yaya. Gaskiya sunan garin akwai dadi sosai kuma gashi garine da ya tara manyan yan boko da suka san kansu a tahirin kaduna kaf. Yanzun ma ga wasu karin an samu harda yan scientic a cikin su mata masu kera fasaha da kansu don wanan matar tawa nan gaba . Sai lokacin na gane zolaya yazo dashi akaina na neman jin bakina kawai yasa ya fadi haka akan garin mu. Nace gara dani nasan asalin garin mu wasu ko kauyen su basu san hanyar shi ba har yanzu sai kame kamen garin wasu sukeyi da sunan nasu. Sadiya ke kinji akwai wanda zaice bai san asalin garin su ba ko ga suna idan ba karya ba. To idan nan sani din a tafi mana in ba tsoro ba na fada ina kwashe kafafuwana ina dorawa saman kujera tare da kawar da kai a gare su. To zamu gani idan mun je Nigeria idan wani zai nuna min hanyar asalin garin mu lokacin da nake zuwa ke kina ina ?. Zamu gani idan an tafin ai in ba burgan aiki ake muna ba a nan don banga alaman an sanda yan kauyen ba sai yan birni. Wai yaushe zamu tafi gidane yaya sadiya ta tambaye shi da saurin don jin yace idan mun tafi Nigeria zai kaimu garin nasu. Zamu tafi idan ki samu hutu sadiya har in yayi daidai da lokacin banda aiki sosai zamu tafi. Ko yanzu dai ba wani amsa mai karfi na fada a raina ina dan tunane kafin naji sun buge da hiran gida shi da sadiya din fitan da basuyi ba ke nan a ranan sai washe gari muka samu fita dashi ya kaimu yawo cikin gari tare da yin sayyaya mai yawa muka dawo gida dashi a cikin farin ciki iyakar abinda ke tsakanin mu ke nan dashi ko yaushe. Da irin wanan har muka shirya fada ya kare a tsakanin mu a yanzu mun koma daidai a tsakanin mu yakan shigo mu dan taba hira da yakan yi kamar na dole wani lokaci. Wani lokaci zanyi zargin bai daina komai ba a cikin halaiyar shi don ba wani canji da nake gani dake nuna ya daina din. Abinda ban sani ba shine abune mai wuya ashe koda mutum ya daina wasu halaiyar shi ya dawo daidai lokaci guda kamar yadda nake tunane ni. Abin ba haka yake ba don shima yaya din yana fama da kansa ne sosai boye hakan yakeyi kada mu fahinta da hakan. Haka zai ta fama da ciwon ciki wanda bai san kanshi ba sai da kyar zai samu ya lafa mai ko kuma wani kumfa mai kauri ya dinga fita mai a baki zai wuni yana fama da wanan laluran yana faman shaye shayen abinda zai lafa mai da ciwon . Ranan ya fita wurin aiki sai gashi zuwa karfe daya sai gashi ya dawo ina dakina kwance ina barci . Dakin shi ya nufa a gigice ya fada saman gado a yadda ya shigo din ko takalman kafan shi bai cire ba don zafin ciwo. Kamar a mafalki nake jin wayana yana ringing da kyat na bude idona na kai ga wayan na dauka muryan shi babu dadi yake fadin. Wanan maganin da kika taba bani nake son ki bani yanzu idan akwashi a wurin ki har yanzu ? Kana ina yanzu yace part dina kwance banda lafiya tun daren jiya da kyat na samu na fita yau dama. Maganin na dauka na jika kamar yadda tace na nufi wurun shi wani irin juyi na sameshi yana yi shi kadai a dakin da sauri na karasa inda yake din ina mashi sannu. Ya tashi da kyat yana karban maganin ya kafa kan shi saida ya shanye ya cire baki sa yana miko min cup din daya sha maganin. Zaune nakai gefen shi tare da kura mashi idanu na dan lokaci sannu a hankali na fara ganin yana karya zufa a goshin shi sai barci. A cikin dabara na cire mai takakman kafan shi sai ya bude idanu shi ya sauke a kaina tare da fadin nayi barci ne ko ? Wai da takalman zan cire ma ko zaka ji dadin barcin nan wurin ne yake yawan damuna sosai sai yayi kamar ya bari kwana biyu kuma sai naji ya motsa min ba dadi wallahi ya fada yana bata fuskan shi. Da zaka daure ka sha maganin na yan kwanaki mu gani ko Allah zai sa a dace a hakan zan sha ya fada a dan maraice yana lumshe idanun shi a haka barci ya daukeshi yana sake ajiyan zuciya kamar karamin yaro. Tagumi nayi ina tunane ni kadai a dakin sai bin ko ina na dakin nakeyi da kallo amma a can kasan zuciyana sai tunanen kada fa wanan abin ya halaka wanan mutumin ta dalili na. Don yanzu kan na yarda da cewa maganin kakar maya ce ke bashi wanan matsalan haka yake hanashi sukuni da sakashi yawan ciwon mara da ciki da yake complain ko yaushe . Lalai idan haka din ne kuwa ya zama dole in koma wurin kakar maya in mata bayanin komai dake faruwa kan abinda ta bani na bashi din yasha . Don ni har yanzu ba wai naga wani canji bane a gurin shi banda wanan matsalan dake taso mashi na yawan ciwon mara din. Gashi har shi kanshi ya fara zargin hakan don wanan zancen daya taba fada min a gaban mami din ya nuna yasan na bashi wani abu yasha da yake zargin hakan. Kwana biyu yana shan wanan dan abin mai kama da kankara da nake jika masa yasha yana kuma dada kara samun sauki don idan ya sha sai wani irin zufa ne zai dinga karyo mashi a duk kafofin jikin shi lokavi guda sai ya tube yana neman sanyi a jikin shi. Haka yakanyi duk tsawon kwanakin nan da yake shan wanan maganin dan hakane ma baya sha yanzu sai da dare idan zai kwanta. Na gama bashi maganin na juya zan fitane naji yana fadinn wai zainab waya baki wanan maganin da kike bani ne ? Na tambayeki ranan baki ban amsa gamsashiya har nake zaton ko mami ce ta aiko maki dashi ki bani tace bata san zancen ba ? Dan shiru nayi kafin na dago kai nace mai na fada ma dashi nazo garin nan dama ina dashi a wurina nakan yi amfani dashi idan cikina yana ciwo. A zaton ki zan yarda da wanan maganan da kike fada ne ko kin mata farkon zuwan mu kasan nan kiyi ciwo mara saida aka kaiki asibiti ? Baka yarda ba ke nan dani ai da kada kasha tunda zuciyar ka yana baka zan iya cutama ne da maganin . Ban ce hakan ba amma kin san dalilin da yasa kike min amfani dashi wanda yasa nake zargin hakan a kanki sai yanzu na kara tabbatar da hakan. Kada ki dauke ni karamin yaro da baisan abinda yakeyi ba zainab na kallo shi da sauri don jin abinda ya fada yace eh. Na dade da sanin komai shiya har da farko nake zargin ko mami ce ta baki kiyi min amfani dashi ashe tunanena bai bani daidai ba. Kece don kanki kika ga daman yi min amfani dashi ai da saiki fada min tun a Dubai da kika fara saka min nasha wahala kamar zan mutu. Kin ko san kwana na kawai ke gaba a wanan lokacin dan da zan iya mutuwa a wanan lokacin. Hawaye ne yazo min masu dumi kan maganan da yake fada min din na kasa furta komai sai hawayen da nake zubarwa kawai. Babu abinda zan iya fada tunda har ya gano hakan a yanzu nace dashi don kawai yana wanan halin na bashi magani ya daina ko don ina son shi nayi masa hakan bai sani ba tunda gashi yana fadi da bakin sa ya san na bashi wanan maganin kan wani dalili nayi hakan zan bashi amsa. ZAINAB IDRIS MAKAWA YAN UWA MUSULMAI BARKAN MU DA SHAN RUWA UBANGIJI ALLAH KA YANTA MU CIKIN YANTATTUN WANAN WATAN MAI ALBARKA AMIN YA ALLAHU. ALLAH KA KARFAFA MUNA ZUKATUN MU MU ZAMO MASU KASKANTAR DA KAI A GARE KA AMIN YA ALLAHU, , , , , LITTAFIN KUDINE YAR UWA DON SAYA SAIKI KIRA WANAN LAYIN 08036959257 KO 09026931792 DARI UKUNE KAWAI KUDIN SA ALLAH YA BADA IKON BIYA YAR UWA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA YARDAN UBANGIJI, , , , Rayuwa haka ya kasan ce ba tabbas a tsakani da yaya akan cewa ya daina duk wani halaiya nasa mara kyau a yanzu. Ni dai tunda yace yace ya daina na dauka din ya daina ko ya rage don ba yarda nayi da hakan har kasan zuciyana ba. Sai dai ba wanan zancen a tsakanin mu ban sani ba ashe yaya yana nan yana shirin tafiyan mu zuwa Nigeria a asrince. Don daga gyaran gidan da zamu zauna har suturo da duk wani abinda zamuci ko amfani dashi an gama hada komai a can Nigeria din ya tura wasu daga nan wasu kuma an saye a wani kasan an tura can Nigeria din. Ko mami bata san da wanan shirin nasa ba balle wani dan uwansa ya sani dama dai jamal ne wanda nasu yazo daya da jafar din . Yanzu ko sun raba gari a tsakanin su do ma mahaifiyar su na tsaye a kansu ne yasa basu kai inda ba,a so ba a tsakanin su din. Don shi jamal din ga baki daya ya tsani jafar gaba daya a rayuwan shi ya tsani duk wani abinda ma ya fito daga hannun jafar din. Tun yana iya boye hakan a zuciyar shi har yakai mami ta kai ga fahintar hakan duk abinda ya fito daga jafar din shi jamal baya amsa baya ko kallon abin. Ranan a gaban kowa mami ke masa fadan hakan sam ta manta da cewa sauran yaran basu san halin da dan uwan nasu ke ciki ba a lokacin. Take fadin Jamal ina kula da take taken ka kan dan uwanka kana nuna kyama da tsana akan komai nasa. Duk halin da jafar ke ciki a yau ko ma ya zama abin kyama ne a gun wasu banyi tsammanin ku zaku iya guje masa ba ai. Tsit sukayi falon kowa na kallon su kafin shi jamal din yace mami nifa ba tsanan shi nayi ba ina dai koyi ga abinda sunna ya koyar da mune ga masu wanan halin kawai. Hali wani hali kuma kega ya J da har zai fadi haka mami kawai kila hassada ya jamal ya fara a kan dan uwan shi . Amma meye matsalan da har zai fadwa dan uwan shi haka ni dai a gareni banga wani abin kushewa gun ya j din ba sai dai wanan bakauyiyar yarinyar da yake aure kawai wace bata san kanta ba balle na wasu . I realy totally hate dis zainab yanzu wallahi ji irin dukiyar da shegiya ke ciki amma bata san yadda zata juyashi ba dan gidadancin dake damun yar iska. Wani kallo jamal din ya watsa mata tare da fadin dan Allah gafara can ki rufawa mutane baki gada na balla ki a wurin nan. Tunda bakya son ta ba sai ki kasheta ba ko ki fitar da ita cikin daulan da kike kyashin zaman ta din a yanzu. Zainab da kike gani tafiki hankali da wayau sau dubu dan ita tasan ya kamata ba wai daula ko arzikin shi ke gaban ta ba ita. A,a,a ke Aisha ki kyale bakin ki fa akan zainab don bata taba laifi a gaban bros tun asali kin sani . Ta sani mana tunda yafi son ta sama ga dan uwan shi tunda ta iya makirci har ta gaji a rayuwa har yana wani son ririta ta yanzu a gaban kowa. Mikewa yayi tsaye don fita daga falon yana fadin gaskiyane dai baki so mami amma yarinyar nan ai bata cancanci irin wanan ba a wurin ku yanzu tunda kunsan zaman da takeyi dashi itama. Sakarai kawai mara hankali zanga yaushe zakayi hankali ka daina wanan halin wai kai mai ra,ayin rikau hakan. Fita yayi bai juyo ba yana fita jalal ke fadin mami wai me ya J yakeyi ne da kullun jamal ke nuna baya son shi haka ? Kyale mara hankali da baisan me yakeyi ba dan kawai dan uwanka na wani hali mara kyau zaka nuna masa tsana haka ? Ni dana haifeshi ince me yanzu don yanzu dani duniya zatayi kwatancen shi idan an tashi fada ai. Wani irin kallo yaran kewa uwar cikin rashin fahintar inda maganan nasu ya dosa a lokacin kafin Aisha tace wai mami nafa kula kamar akwai wani hali da ya J din keyi wanda ba a son mu sani. Wata kila dai mata yake nema ko tunda naji jamal na fadin ko zainab na hakkuri dashi ai. No kai ina ba dai ya J ba kan akan mata don da munga alaman hakan tuni a gareshi ba wanan bane mami basa son muji daine nake gani. Dan Allah ku rufa min baki koma me yakeyi ku tayashi addu,a Allah yasa ya daina ta fada a cikin bacin rai tana kawar da kai a garesu baki daya. Ranan wanan zancen da yaran sukayi ya hana mami din shakat a rayuwan ta dashi ta kwanta can dare kamar yadda ta saba tashi a cikin dare tayi nafila hakama ranan ta tashi tana mika kukan ta ga Allah. Tun tana yi a cikin zuciyar ta har yakai ta fashe da kuka a fili tana rokanwa dan nata sauki a wurin Allah. Tare da kaskantar da kanta ga Allah ta daga hannayen ta sama duka biyu tana hawaye tana addu,a tare da mika kukanta a kaskance wurin ubangiji. Zaune nake ina bitan kur,anina da yanzu na koma gare shi sosai fiye da komai da nakeyi don ina son na kara saukewa duk da banda wanda zai karani a lokacin. Sadiya ta fito daga dakinta tana saye a cikin dan wando pink daya tsaya mata iya gwaiwan kafanta sai yan aninaiya biyu da akaiwa wandon ado dashi sama rigace fara mai shaka shaka da rigan ta fito dashi a jikin ta. Zama tayi kusa dani tana kokarin lalaban wayana dake gefena ajiye sai lokacin na dago kai na kalleta na tsayar da karatun da nake ina fadin . Amma dai kinga abinda nake zaki zo min kai babu hula ko dan kwali ki zauna a kusa dani haka ? Ba zama zanyi ba ai waya nake son dauka dama ta fada a cikin harshen turancin da yanzu dashi take iya magana ko a gida sosai. Kallon ta nayi mai kama da harara ina kawar da kaina gefe ta gane may nake nufi yasa ta juya ta koma dakin. Naci gaba da abinda nakeyi ban tsaya bin ta kanta ba sai can ta fito saye da hula a kanta ta zauna nisa dani tana kumbure kumbure na fita batun ta. Shine ya shigo part din saye da farar jallabiya zakace balarabe ne shi din yadda rigan ya karbi jikin shi kusa dani ya zauna daya shigo . Sai dai hankalin shi yana gun sadiya yake fadin Sady ya na ganki a haka kamar an bata maki rai ko ? Shafawa nayi tare da dago kai ina fadin fushin banza takeyi tunda bata son a fada mata gaskiya don tana kokarin kwasan dabi,an nasara ta dorawa kanta yanzu niko ba yarda zanyi da hakan ba. Me tayi ya fada yana kallon sadiya din ai gatanan ta fada da bakin ta ina mikewa don dauko mai ruwa don nasan ko ban dauko ba zai tambaya idan zai tsshi. Ina zaki ya tambayeni ruwa zan dauko ma a fridge na fada naci gaba da tafiya na dan dade a kicin din don adduan dana tsaya yi a cikin ruwan ba wani addu,a bane sai fatiha dana tsiri karanta mai kafa goma sha daya a ruwan wanda kafin nasa nakan karanta na aje mai ya danyi sanyi daya tambaya na dauko mai shi. Sai ranan na manta ban karanta masa ba har ya shigo part din namu haka yasa na dan tsaya ina karantawa har na bata lokaci a karamin kitchen din namu na part din. Wai ke zainab tunda yarinyar nan tana son waya don me baki bata wayan can dana ce ki bata ba tun farko. Tiren Ruwan da cup na aje a gaban shi cikin ladabi ina kokarin budewa yace min barshi sai na tashi zansha a cikin muryan shin nan me kamar na rowa ga mutum idan bashi yaso magana ba. Wayar tana inane tunda kin hana mata naki ya sake maimaitawa nace tana nan aje wanan ma ai ya ishe mu amfani banda mutanen gida wa muke kira dashi. Naki ma ai wani za a saya tunda ba zaki gida da wayar data sha hannu ba sai ki bata ta ci gaba da gamen dinta a zauna lafiya ko gimbiyar game ? Sai lokacin tayi murmushi a fuskanta jin abinda ya fada din yace to koke fa sadiya kin zauna kin hade rai haka kamar wata matar soja can dake ? Ni da naga sa,adatu hade fuskanta ai baiban tsoro na fada ina zama a inda na tashi muryan shine ya sake fadin akwai wani abinda kuke son sayane zaku tafi dashi gida duk da dai ba dadewa zamuyi ba zamu dawo ? Don hutun nasu na tambaya baida yawa kwarai akace wanan karon saboda sadiya sai mu dawo da wuri yaya nikan sai na gama koda zan dawo na bashi amsa. Tunda kece mai shirya tafiyan ya fada a dan hasale amma yaya kasan dai mun dade rabo mu da gida ai na fada ina kallom shi. To idan hakane sai a fasa tafiyan in hakan bai maki ba wata daya na yanke zamuyi a can zuwa lokacin nasan kin gama dai abinda ya kaiki ai. Duk da naji dadin zancen a raina amma a fili cewa nayi wata daya kuma yaya ina laifin dai wata biyu zuwa uku haka ? Karatun nata fa wai zainab bana son wasa da abinda ya shafi karatun ku ga baki daya kema na saya maki form da mun dawo zaki koma karatu ne nan gaba. Ko hakan bai maki bane zaki tsaya batawa kanki lokaci zanso ace kin hada karatun ki kaf a nan kafin mu tattara mu koma Nigeria gaba daya da zama can don hakan nake planning nan gaba don mami ta fara fadin mu koma gida hakana. Mami tana da gaskiya yaya zama acan kusa da yan uwa zaifi ma tana ganin ka a kusa da ita hankali zaifi kwanciya ai balle ni wa yanan abokan naka yaya basu min ba sam. Zainab yaushe kika san abokaina da har kika san basuyi maki ba ya tambaya da mamaki yana kallona . Nasan su tunda sune mahalakan ka a yanzu na fada a hankali sai naji ya sake dan murmushi kawai yana kada kai . Can yace zainab da kinfi haka bansan inda wayau ki zai tsaya min ba don kallon da nake maki kin wuce haka a wurina. Abi ma dariya ya bani na kai bayana saman kujera ina dan murmusawa tare da fadin ni di kuma yaya sadiya karya na fada matar da take zaune a gida take fadin abokaina. Yanzu da nayi magana yayan mu laifina zata gani yaya ta fada tana nokewa ga maganan ruwan dake gaban sa ya bude ya zuba a cup din tare da dan kurba a hankali yana kada kai kafin yace ina ganin ranan Friday mai zuwa muna Nigeria. Don haka idan akwai abinda kowan ku keso sai ya fada ko ku fita ku sayo da kanku zaifi min sauki saidai bana son kaya masu nauyi da yawa kin sani ga tafiya. Duk iya abinda zan rika yaya tufafine ko dan wani abin amfanin mu na bashi amsa ina cikin farin ciki da jin zamu wuce gida dabai fi an kwanaki ba a lokacin ashe . Tu wanan ranan sosai muke busy yawon fita sayayya duk ban san cewa ya riga da yai muna sayayyan da ban taba zato ba don wanan tafiyan. Kafin ranan duk mun gama wani shiri na tafiyan mu inda nikan shiri nakeyi sosai na barin kasan gaba daya a raina don haka duk wani abunda zan tuna nayi dana sani bukatan shi a can na tanada don komawa dashi gida duk ya yaya yace baya son muyi tarkacen kaya da yawa ga tafiyan. Ranan daya bukaci mu fitar a tafi da kayan airport yasha mamakina sosai don bai iya boye bacin ranshi a zuciyar shi ba don ganin yawan kayan da yayi dana fitar. Haka ya daure akai muna packed din shi zuwa airport inda kayan da alaman zasu rigamu isa ga nawa tunanen. Shiri sosai mukayi daga gyaran jiki zuwa duk wani abinda ya kamata ace munyi don ban yarda na bar kasan ba saida naje har kauyen su maya mukai sallama da ita da iyayyen ta kan na tafi na tafi ke nan ba zamu sake haduwa da suba idan na tafi. Kamar yadda duk wani sabo yake udan za a rabu haka muka rabu da maya da yan uwan ta kakarta bata barni haka ba saida ta ban wasu abunuwa datace na zanka amfani dasu har yayana nan gaba muka rabu cikin kewa da juna ina kuka maya ma tanayi. Washe gari da daren ranan muka bar kasan chaina zuwa Nigeria sai dai naji haushin tsayawan mu a kasan Dubai da muka kanceqa da yayi wani aiki ya taso mashi a can da zai tsaya ya dan yi. Ba laifi mun tsaya a Dubai mun kuma sha dadi sosai duk da shikan baida lokacin mu kullun sai dare yake dawowa masaukin da muka sauka wani lokacin ma kafin ya dawo zai samu munyi barci ko. Wasa wasa kwanan mu biyar a dubai din wanda ni dai nayisu ba a cikkn dadin rai bane do na matsu na bufe ido na ganni a kasata Nigeria a lokacin. Shiko hakan ko a jikin shi don ba abinda ya dameshi a zamanu din sai ranan da yake fadin gobe zamu bar kasan ya danga walwalana kadan. Alhamdullahi mun sauka Nigeria da dare amma ta kano ba kamar ta Abuja ba kamar yadda ya tsara muna. Nasan maganan hauka zanyi idan nace ya barmu mu fara zuwa gida don gamu a kano don yafi muna kusa da gida a lokacin. Amma nasan zuciyana hauka take ban don ba zai taba yarda da hakan ba sai idan mun danganta da wurin mami da yanzu zaman ta ya koma garin Abujane kamcankan duk da an sauke su a lokacin. Don lokacin har waya tayo min kan wai ban kirata na mata jajen saukan su a mulki ba ta fada don takanas ta kirani a waya ta balbaleni ni dai sai hakkurin dana bata kawai a lokacin. Duk da an sauke su bata kwaso ta dawo kadana da zama ba sai suka zauna can ga baki daya tunda dama gidan su na kansu suke zaune a cikin sa yanzu ba na gwaunati ba. Duk wani gyaran gidan da aka kara yi yaya J ne ya kara gyara masu shi suke zaune a cikin sa yanzu. Karfe goman safe duk muna Abuja ba zance ga unguwar da muke shiga ba don garin gaba daya ya kara sauya min ga dan sanin danayi mai a baya. Duk da rudewan sauyawan wurin hakan bai hanani gane ba wancan gidan da muka zauna a farkon aurena dashi bane kafin mu wuce zuwa chaina. Wanan gidan na yanzu yaci uban wancan sosai ga fasali da keruwa komai na gidan sabone ba sai an fadawa mutum haka ba. Motocine a haraban gidan gasunan birjit a cikin rigunan su rurufe sai shuke shuke da zai tarbe ka. Tun saukan mu kano ya sauya layin wayan shi naga ya aje wancan wayan da mukai tafiya dashi haka kuma ya miko min nima waya sabuwa a kwalin ta kiran samsung full ita kuma sadiya iphone karama mai kyau da su. Zakace duk biyun ba zaka gane bambancin su ba don kyau godiya nayi a fili a zuciyana kuma fadi nake kyautan karshe ke nan tsakanina dakai baka sani ba. Don yanzu sai lalabashi kawai nakeyi in samu naga mun sauka ya mika mu gida lokacin zan tayar da balli na a garesu. Don duk wani rudi da abin duniya da yake min yanzu ni bashine a gabana ba kaina kawai nake son na kwata a garesu naga na fita hannun shi baki alaikum ba tare da duniya ta zargi komai a hakan ba. Kinga gidan ki na abuja ke nan da fatan tsarin ginan yayi maki kyau sosai ya fada kamar mai rada a lokacin. Don naga kina da sha,awan ruwa wancan kuma babu swimming poll a cikin sa yasa na fadada wanan din aka gyara makushi sosai. Dan murmushi yake na sake tare da fadin gidan yayi kyau sosai wallahi ballw ni yar tallaka ina ni ina wani zabem gida mai kyau gareni. Bana son kina kiran kanki da hakan don yanzu a matata kike a idon kowa don haka wanan kallaman ya fita a bakin ki. Donke din matar jafar kankia ce ba yar anchau ne ko meye sunan garin naku ba na manta ya fada yana kawar da kanshi don motar data tsaya gab da kofan shiga gidan. Innalillahi zakace wasu basu tunanen lahira idan suna hada duniyan su kamar ba zasu barshi ba don tsarin gidan kamar ba gobe. Haka muka fito muna bin gidan da kallon mamaki zuwa cikin gidan saidai duk hakan bai hanani addua a bakina duk da na rude da ganin wanan gidan haka. Sai tambayan kaina nake wai ya jafar ne mai mahaukacin kudin nan haka kamar wani mai shekaru a duniyan nan daya tara kudi irin haka. Oyyoyo da uwar dakina muryan fadilace ya daki kunnena lokaci guda sun fito tare da wasu daga cikin gidan. You again muryan sadiya ta fada da dan karfi ta nufi wurin ta da gudu don murnan ganin ta a lokacin. A hankali nake takowa cikin dan murmushi zuwa gareta ta hadamu ta rugume ga baki daya kafin sauran mata su shiga gaida mu suna muna sannu da zuwa cikin nuna kulawa a gare mu. Na dago ina fadin mun sameku lafiya suka amsa a cikin fara,a da murna kamar sun taba sani mu da farko. Shine ke waya da bansan wanda yake wayan dashi ba a bayan mu yake fadin mun iso a kawo mai abinda yace azo dashi din. A raina nace giya ke nan ko wani katon tun da naji ya fadi hakan yayin da matan suka shiga gaidashi da zuwa da sauran yan aikin gidan. Muna shiga wani katon hoton mu da muka dauka a chaina dashi ranan sallah ne ya tareni don nasha kwaliya a photon zakace ko balarabiyace ta asili yadda na fito a photon. Da murmushi na sake tare da tambayan kaina yaushe har ya yi wanan aikin haka kai yaya ya iya duk wani abinda zai kawar da zargi a zukatan mutane shikan . Ai wanan photon sai a dauka ni din matarshice ta gaskiya yadda photon ya karbi falom kamar kai magana damu mu amsa ma a fili. A falo muka zauna aka shiga gaisawa da masu aiki sai kuma wasu biyu da ban sani ba na dai ga suna zirga zirga a gidan kamar yan uwan shi. Kafin shi ya fara mikewa a daidai lokacin da Fadila ke fadin ai maza a kara gyara table din abincin don muna da gajiya kafim mu shige ciki mu huta. No saidai su nikan zan shiga na watsa ruwa ya bada amsa yana kallon agogon hannun shi kafin ya juyo yana fadin mami bata san da zuwan mu na fa nasan zaku kwasa da ita karshe. Da nayi laifin me tunda tasan bani bace mai tafiyan a raina kuma fadi nayi saidai tayi da wanda ta gani don ni goben nan zan bar gidan nan idan ma ba kasani ba ka sani. Don a kage nake ko zuwa abujan duk bat da saune kawai nayi mai kada mu raba hali tun a hanya shiko sai wani nuna jiji damu da yakeyi a gaban kowa yadda kasan auren gaskiya muke a tsakani mu dashi. ZAINAB IDRIS MAKAWA YA ALLAH KASA MUNA CIKIN YANTTATUN BAYIN KA UBANGIJI KA KARBA MUNA IBADUN MU KA GAFARTAWA DUKKAN MAGABATAN MU KA BAMU CIKAWA DA IMANI A ZUKATAN MU ALLAHUMA AMIN, , , , , LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA AKANKI BA YAR UWA, , , , DON SAMUN LITTAFIN NAN ZAKI KIRA 08036959257 KO 09026931792 DARI UKU NE KACAL KUDIN SHI, , , Dakin namu nabi da kallo komai ansaka na jin dadin rayuwa dan Adam a dakin kamar ba gobe a wurin bawa. Wanka na shiga na fito na samu an shigo mun da kayana dana zo dashi ranan na bude wardrobe da niyar aje jakkar kayan gaba daya ba tare dana zazzage kayan ba don idan zan tafi gida dauka kawai zanyi na tafi dashi. Saidai abinda nagani a cikin wardrobe din shi ya girgizani lokaci guda don kayane ciki shake nau,i nau,i na mata irin namu na kasan Africa. Wanan ko a wata dayan da yace zamuyi mu koma yaushe zan saka su a jikina duk a cikin wata dayan balle su kare. Don sun kai kala hamsin ko fiye da hakan a cikin wardrobe din idan ma basufi hakan ba ga lissafin. Nan na karewa kayan kallo ina sauke ajiyan zuciya kasa daukan ko daya daga cikin kayan wardrobe din na zari guda a cikin jakkana na saka na koma bakin gado na zauna ina tunanen wanan halin na yaya J. Na kasa fassara wanan halin na yaya J gaskiya don wani sahu zan saka shi a yanzu shin zan iya kiransa da mai yawan alheri ko kuma mai iya yaudara ne ? Don wanan halin nasa idan ba wani akasi ba sai mace tace ta dace da miji gaskiya don irin halaiyar nan nasa. Salaman sadiya dakin yasa na dago kai ina kallon ta fuskanta da fara,a take tafe tana fadin wai yayan mu kinga yadda aka cika min wardrone da kaya. Nuna mata nawa nayi da hannu ina fadin duba can ki gani sadiya wanan ai haukane ko ? Ta nufi wurin wardrobe din tana fadin a,a yayan mu zamu saka mu ji dadi wallahi gaskiya yaya j mutum ne yasan harkan arziki sosai wallahi. Tana budewa taci gaba da fadin da har ina kallon ina karawa g wanda muka sayo a can da zamu zo ashe ga wanda yaci uban wanan din a nan. Wani irin ihu ta sake lokacin data bude wardrobe taga kayan shine ta sake wanan ihun a firgice tana taba kayan da ta gani din a ciki . Yaushe duk zaki saka wanan kayan haka masu yawa yayan mu, gasu nan dai na bata amsa ina mikewa take fadin zan saka sau uku ko biyu a wuni nikan duk sai na saka su a jikina kafin mu koma. Ta gama daddaga kayan ta juyo da nufin ganina a inda ta barni zaune bana wurin ina tsaye bakin mirrow dina ina kallon kayan shafen dake wurin. Wani dan turare ne ya dauki hankalina na mika hannu na dauko ina karanta sunan shi sunan da larabci aka rubata shi aswad. Jin hannun sadiya nayi a kafadana tana fadin wai amma yana da kyau sosai nace sadiya meye baida kyau a wurin nan. Mun gama kallo muka koma kan waya zube muke saman gadon tana danne danne a wayan nikan barci ne ya fara daukana a wurin. Fadila ta shigo dauke da tire da sauran tarkace tana fadin na dauka kunyi barci don gajiya kasan nan akwai nisa sosai da nan duk ka sauka sai ka yi hutun gajiya wallahi. Bude idona nayi da suke a lumshe ina fadin saukin abin mun dan huta a Dubai kafin mu karaso nan din shine saukin mu ai. Zama tayi daga gefe tana fadin ya bayan rabon mu ni kuma ina fadin ya jikin mama da sauki ko ? Mama ta samu sauki sosai kafin na iso na samu baban yaran nan ya kaita asibiti an kula da ita nace kin fada min a waya yanzu dai jikin da sauki ko ? Tace da sauki sosai uwar dakina ya wajen ku da alama abubuwa a yanzu kamar sun kamkama don alama ya nuna hakan. Gaba dayan ku kunyi wani irin kyau kun kara haske kamar mutum ya sace ku wallahi nikan gaskiya da badon na san kuba sai nace baku bane gaskiya. Dan murmushi na sake kafin nace kai anty ke nan wanan zuzutawan haka tace gaskiya na fada ance alaman kwanciyan hankali yana ga mai kiba . Don wallahi kun sauya sosai a yadda na san ku don haka abubuwa a yanzu suna tafiya da sauki ga alama. Bandai fadi komai ba sai murmushin da nakeyi sadiya ce ke fadin bayan ki kan ai munji dadin yaya fiye ma da yadda kika barmu anty. Ke kan akace ko shekara nawa kayi baka ga mutum ba kada ka tambayi halinsa don hali na nan bai canza ba sadiya har yanzu. Sadiya kan ai sai abinda ya karu na bata amsa ina mikewa tare da bude fruits salad din da ta shigo muna dashi na fara zubawa a hankali. Naga kamar kun kasa cin abincin nace bari na hada maku wanan din ku dan ji nauyi yayane zaiso shan wanan din a yanzu don naga baici abincin sosai ba shi. Mun zuba mai sadai bamu da halin shiga part din shi a yanzu sai dai idan ya fito barin gama na kai masa na bata amsa ta bini da kallo saidai ban san me haka ke nufi ba. Kadan nasha na mike muka fito tare a dakin ina karewa gidan kallo a tsanake babban gidane kan wanan gidan sai dai part din mu yana kallon juna da nasa a sama amma akwai wani irin falo babba a rsakanin mu dashi. Na karbi kayan da ta dauko a hannu ta na nufi part din data nuna min nasa sai dana kwankwasa na tura kofan na shiga dan karamin falone na wuce sai dakin kwanan shi ko ina yana kamshi a part din Yana kwance saman gado ga sytem din shi a gefen kanshi bude sai dai ba aiki yake a ciki ba da alama yana aikin barci ya dauke shi. Ganin halin da yake ciki yasa nayi shawaran juyawa kada in tayar dashi daga barcin sai dai hakan baikai ga samuwa ba naji ya motsa yana fadin. Meke sa idan kin shigo kin samu ina kwance kike saurin juyawa ki fitane kin dauka zanyi barci mai nauyin da har za a shigo min ban sani ba ? Banson in tayar da kaine daga barci don naga kamar ka samu barci a yanzu idon shi ya bude gaba daya ya sauke a kaina yana fadin. Na dauka kina zaton ko zaki samu ina abinda baki kaunan ganin inayi ne yasa zaki koma don kin ganin a kwance. Wanan yanzu ai ba damuwa na bane yaya tsakanin ka da mahalicin ka Allah ne wanan ka daina ko kayi wanan ya saura gareka kuma ? Haka zaki fada yanzu ko ya fada yana kallon cikin idanuna sai ban yarda mun hada ido dashi ba na aje mai tiren a saman dan karamin table din dakin da yake kala daya da gadon nasa ina jawo table din zuwa gaban shi. Don na kawar da zancen nace ga wanan ko zaka sha don naga bakaci abincin ba sosai dazun. Naci mana ya fada yana mikewa kinsan bana cin irin wanan abincin kada ya saka jikina budewa sosai. Da jikin ka zai budewa ai daya dade da budewa yaya don ruwan kwalban da kake durawa cikin ka sosai. Zainab bana son jin wanan zancen a bakin ki don sanin kankine a yanzu na daina wanan harkan don haka bana son a tayar min da wanan zancen kuma . Kayi hakkuri idan hakan dana fada laifine na barka lafiya na fada ina kokarin ficewa dakin yake fadin bakiji ba ko ? Na juyo ina dan kallon shi yake fadin zuwa dare zamu fita zuwa gidan mami mu gaidasu idan zaku iya fita a yau din ko kuma a barshi da safe sai mu tafi. Zaifi kyau yau din mu tafi na bashi amsa daga inda nake na rungume hannayena a jikina eh hakan zaifi don mamud ya fada mata muna garin tun safe. Tayi fadan hakan ke nan na tambaya badan na shiryawa hakan ba fadan me zatayi tunda mun shigo kasan ko ? Zo ki zauna ya fada yana gyara zaman shi da kyau tare da fadin idan bake ba wata mace ce zata shigo wurin mijinta aga ta fita haka da sauri. Ai sai a dauka akwai rashin jittuwa a tsakanin mune kila kinkoga hakan ba zanji dadin shi ba daga zuwan mu ki bada mu haka ? Yaya ke nan ka dauka ba,a san zaman da mukeyi da kai bane a hakan kana dauka kowane zaka iya wasa da hankalin shi a hakan. Sai dai idan kin fadawa wani wanda ban debe tsamani fadilace ko zaki iya fadawa ban taba ki kamar sauran maza. Wani kallo na watsa mashi da sauri tare da fadin kada ka daukeni yarinya kamar da bansan kaina ba har yanzu. Ko a da can ban fada mat komai game da zaman mu da kai ba balle yanzu da hankalina ya kara zo min na fahinci me kake nufi dani. Me nake nufi dake zainab ya fada a daidai lokacin da yakai cibin mix fruits din a bakin shi tare da bissimila a fili na dan kalleshi. Don a kwaishi da wanan akidar na fadan bissimila ga duk abinda zaikai a bakin shi ko wani lokaci idan zaici abu. Niko nasan kin kara girma a yanzu zainab don nasan kin fara kiyasta wasu abubuwa a tare dake . Ban fara kiyasta komai ba saidai a yanzu din zan fara mutukar wanan halaiyar naka munana suna tare dakai yaya don ba zan zauna da wanda ke sabon Allah a fili ba haka gaskiya. Da nai maki me a cikin zaman namu dan dama ina zargin hakan a gareki tuntuni saidai ki sani ba kowa zaki fadawa wanan zancen a yanzu ba ya yarda da zancen da zaki fada. Saboda basu gani a jikina ba kome yasa ka fadi hakan ai jikin shike nuna kana cikin wani hali keko naki bai nuna hakan ba. Shine hikimar ka a kaina banda wani hikima ko basira a yanzu da da can baya wanda yafi in ganki cikin farin ciki kamar haka ? Da alama dai dadin zancen yake yana kuma bugun cikina da wayaun manyan yaji wani shiri nake a kansa yanzu da mukazo gida. Farin ciki a haka yaya farin ciki zuciya tana cike da damuwa da tashin hankali akan mutum kullun ? Zainab meye matsalan ki a yanzu dani kallo shi nayi da mamaki kamar zanyi magana sai kuma naja bakina nayi shiru ina kallon shi ban iya furta kai din kaine matsalata ba a yanzu kamar yadda na bashi amsa a zuciyana da hakan. Bakinane yai subul da baka nace ina ko naga matsala dakai kana da irin su Taju dake debe maka kewa duk lokacin da bukatan hakan ya taso maka. Na sani zainab nasani banda wanan din da kike ganin shine matsalan ki a yanzu dani baki da sauran matsalan komai bayan wanan. Koshi din ai zaki iya idan kina so sai ki gwada ki gani ko zakici nasara a kaina har ki samu yadda kike so din. Ka dauka yaya ina da feeling a kanka ne kamar yadda baka da wanan feeling din a kaina haka nima haka kwata kwata ban taba jin wani feeling akan kaba irin wanan. Take naga annurin fuskanshi ya canza lokaci guda yace kina nufin baki da feeling kamar sauran mata akan mijin ki ? Miji miji fa kace yaya ko yau bakin ka ya mantane har ka furta hakan a gabana bayan zaman kanwar ka nake ga idon kowa. Haka dai kika fada zainab wanan zancen ai ya dade da wuce ko ga idon kowa don wayau ki yafi nawa yawa zainab. Banda wayau bayan hakanndin haka ka tsawa zamana da kai yanzu kuma lokaci yayi da hakan zai kawo karshe na fada ina barin dakin. Dakina koma raina na min zafi don wanan maganan da mukayi a yanzu watau yaya daukan jarababba yake min ko me ?. Shiko na fita na barshi da tunane na a zuciya don abinda yake zargine ke shirin faruwa wanan yarinyar gab take da daukan wani mataki a kansa yanzu. Me zanwa zainab na wake kaina kada ta kasa hakkuri ta fasa abinda ke tsakanin mu ne? Wata zuciya tace mai baka saba da wanan halin nata bane a baya babu abinda zatayi duk hakan barazanane kawai na mata ka riga da ka gama da ita ko don babu inda ka ragota a yanzu kan wurin zamantakewa ya fada. Sai kawai ya shafe zancen da basarwa don yasan haka dinne ba wani abinda zanyu inma zanyi din nice dai a kasa bashi ba. Don babu mai yarda da duk wani abinda zan fada a yanzu don za a dauka sherine kawai na mata a hakan. Hannun shi yakai ya shafo gaban shi da kusan wata da watani ke nan yake fama da wanan matsalan yaji shi a lankwas kamar kullun. Hannun ya mayar a fuskan shi yana shafowa a hankali shi yanzun ma ba zaice ga ta inda matsalan ya fara mashi ba. Don dai yasan cewa da farko bayan maganin dana basa a Dubai yana tare da lafiyan shi na mazakuta sai daga bayane ya fara fuskantar wanan matsalan da yake ji a yanzu tare dashi. Gashi ya kasa fadawa kowa bayan likitan shi da yagani kan wanan zancen a chaina ya kuma dubashi yace lafiya komai nasa yake. To a ina wanan matsalan ya taso masa shi dai ba zaice zainab din bane da wanan matsalan sai kawai yake danganta kansa da kawai don yanzu baijin sha,awan ko wani irin jinsi don jin dadin rayuwan shi ya kawo masa hakan. Da kyat ya mike ya shiga bathroom don ya watsawa jikin shi ruwa sai dai har ya fito zuciyar shi yana cike da tunane kala kala daya kasa fahinta. Nikan sallah nayi sai a lokacin na samu barci ya daukeni sosai don na samu barci har lokacin sallah la,asar ya wuce ni sosai. Bayan na samu na tashi da kyat na shiga bandaki na dauro alwala nayi sallah ban fito ba dakin na zauna ina dan dube dube a cikin wayata sabuwa daya saya min. Sosai nake jin dadin wayan don komao na wayan yana da kyau sosai kafin hankalina ya dauko ga tunane ba abinda yazo min a rai sai zancen zuwa gidan mami daya ce zamuyi da yammanan nake tunanen yadda mami din zata karbe ni . Dukda mun shirya sama sama a yanzu da ita sai dai ina tsoron halin dan adam tunda har yanzu bawai na kwanta mata a rai bane. Koma meye wanan karon kam nasan ba zan yarda daduk wani rainin wayau kowa ba a kaina don ga kura mai laifi basu gani saini da banci ban sha za a dinga dora laifi a kaina ? Sadiya na tuna tun fitana dazun ban kara ganin ta ba hakan yasa na mike zuwa dakin da take tana ciki da waya tana faman yin game hankalinta ya dauku a wayan. Jin motsina yasata dago kai tana kallona tare da fadin ashe kin tashi yayan mu na shiga dazun na samu kina barci. Ke wai me yasa bakya jin magana sadiya wanan yasa nake hanaki rike waya don sai ya canza maki akidar ki ga baki daya wallahi. Ina fara magana tayi saurin lkashe wayan tana ajewa gefen filonta da sauri zaune nakai cikin bacin rai ina fadin kinga akan wayan nan zamu samu matsala babba dake don akan wanan hali zan mayar dake na dauko binta mu zauna tare don ita ban taba jin tayi wani abin rashin ji ba . Ina kokarin yi mata wanan nasihan ne don gujewa gurbacewan rayuwan ta nan gaba a kan waya duba ga yadda naga daga shi har kannen sa basu da lokacin kowa akan wanan nauran a rayuwan su don zai iya zama dakai na tsawon awan ni ba tare da yai magana dakai ba hankalinshi naga waya yana tabawa kawai. Duba ga hakan nake tsoron kada ta tashi da wanan akidar nan gaba ya zame mata hitina a rayuwa gashi mu ba diyan wasu a tarihin mu. Idan na fara irin wanan fadan taka natsu sosai ta daina duk wani abinda takeyi ko yanzuma din da nake magana hakane ya kasance a tsakanin mu. Kuma ina son ki saurareni da kyau kiji duk wani tambayan da fadila ko wani zai maki akan rayuwan mu kada ki yarda inji ance ga abinda kika fada don idan naji da Inna zan hadaki wanan karon. Bazan fada mata komai duk tambayan da zatayi min idan kinyi hakan kin kyautawa kanki na bata amsa ina mikewa don barin dakin. Shiru tayi tana bin lafiyan filo ta kwanta tana kallona har fice dakin ta sauke ajiyan zuciya tare da fadi ta rasa meya sa nake yawan tsanan ta mata hakane ? Daki na koma har lokacin banjin dadi a kasan zuciyana kawai naji na tsani komai sai bacin rai dake kara min yawa nakeji . Duk a kan dan maganan da mukayi da yaya J a ranan kawai nake jin raina yana wanan bacin da yake min. Allah ya taimaka har tara na dare ya wuce banji yace mu fito zuwa gidan mami din ba daya fada zamu shiga da dare. Hakan yasa na fara shirin kwamciya kafin Fadila tayi min sallama ta shigo dakin tana fadin taga fitan mijina a cikin daren nan ko lafiya ya fita a wanan lokacin. Tabbas tunane na ya fara zama min gaskiya akan fadila shiyasa yanzu nake taka tsantsan da ita wani lokaci. Don na fara zargin wani abu akanta da yanzu wayau na da hankalina suka fara kawo min haske akanshi don yawan tambayayin da take min lokaci lokaci koda a wayane kuwa idan muna wayan. Har yakai hankalina da tunanena sun fara hasko min wasu abu a kanta ko yanzun ma tambayan data jefo min ya kara rikitani tana fadin. Ko dai mijin naki bai bar wanan harkan bane har yanzu a cikin mamaki na juyo ina fadin harka wani harka ke nan fa ? Sai kuma ta rasa abinda zata fada min kan hakan tace wai irin dai halaiyar nan da yakeyi a baya. Ance mutum mai yawan murmushi baka fahintar bacin ranshi lokaci guda sai dai ya jefaka a cikin kwankwanto da zargin kanka kaida yakewa wanan murmushin a lokacin. Hakan ne ya faru da fadila dani sai kuma ta fara dan kame kame tana fadin a yanzu kan ai komai ya wuce da alama akwai fahinta a tsakanin ku a yanzu. Dama babu ne na tambaye ta cikin alaman mamaki a fuskana naci gaba da fadin ban taba fada dashi ko wani rashin yarda wanda ya shafi ni dashi har wani ya sani na bata amsa. Tare da karewa da fadin bana shiga harkan shi hakan ya kara jawo mana zaman lafiya a tsakanin mu wanda ko wace mace ke fata da mijinta. Itama din kallon mamaki ta bini dashi lokaci guda tana dan murmushi a fuskanta nima hakan nakeyi. ZAINAB IDRIS MAKAWA YA HAIYYU YA KAIYUMU YA ALLAH KA KARBI IBADUN MU KASA MUNA CIKIN YAN TATTUN BAYIN KA A WANAN WATAN MAI RAHAMA DA DAUKAKA ALLAHUMA AMIN, , , , LITTAFIN KUDINE KI BIYA DARI UKU KI KARANTA YAR UWA DON ALLAH KI GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI YAR UWA KAN ABIN DUNIYA, , , , Na san mai karatu zakiyi mamaki jin abinda na fada akan fadila hakan kuma ya samo asaline tun ranan dana fara gane waye fadila a gurin mu. Ranan kishin ruwa kawai ya tayar dani a cikin dare na fito don neman ruwan da zan sha a lokacin. Banyi amfani da ko wani irin haske ba don nasan inda ruwan yake sauri kuma ya hanani tsaya na dauki ko wayana in haska. Har na dauko ruwan zan fito naga kamar gittawan mutum a falon namu karami. Naji tsoro iya tsorata nayi shi don haka na samu wuri na lafe a bayan kofan kitchen din muryan fadila naji tana waya a hankali. Tana fadin wallahi duk dabaran da zanyi in gane wani abu a gareta nayi shi har yanzu ban gane komai ba a wurin ta . Don yarinyar akwaita da shegen wayau tsiya don wayau ta yafi karfin shekarunta sosai wallahi. Na saka ido sosai don in fahinci wani abu a gurin shi na kasa fahintar hakan duk da janta danayi a jiki sosai abu daya na sani shine. Yana shan cocaine din amma baya harkan sayarwa don aikin sa a nan yana jawo mai babban riba da samu fiye da zaton me zaton hakan. Shiru tayi tana sauraren me ake fada mata a wayan kafin tace zan saka ido kafin tafiyana yazo sosai zan kara gano wani abu a hakan. Kara lafewa nayi sosai inda nake boye ina mamakin ta a raina kafin naji tayi sallama da maishi tana kashe wayan ta dan haska ko ina ta koma daki. Sai dana dan dade ban fito daga inda nake boye ba kafin na fito na koma daki cikin tunanen wacece fadila din ? Haba abin mamaki ne ace mace wayayya kamar fadila tana aiki irin wanan haka sai dai mutum ya duba ga irin yanayin da kasan mu ke ciki na rashin aikin yi zaisa mutum yayi duk wani aikin daya samu don dogaro dakai. Tun wanan ranan na kara tsorata sadiya a kanta ta kuma tsorata duk tambayan da tayi mata takan zo ta fada min da amsan da ta bata a lokacin. Sai gashi bayan kwana biyu tana fada muna gida zata wai mahaifiyar tace ba lafiya a lokacin. Yanzu yana da wuya kayi saurin yarda da mutum farat daya irin haka Allah ya taimakeni ga zurfin cikina. Nidin na kasance irin mutanen ne da basu da yawan sake magana ga kowa idan hakan ba ya kama dole bane. Idan zan tuna duk hiran mu ko sakewan da zanyi sai dai ita din ta kasance mai ban shawara ko tayi magana akan abinda tagani da idon ta tana bugun cikina. Kinji dalilin daya sa yanzu nake ja baya da zancen fadila din duk da bansan dalilin kasancewar ta a cikin mu ba har wanan lokacin. Bamu hadu da yaya J ba sai washe gari misalin sha biyun rana da nake ganin fitowan shi ke nan daga barci. A falo ya same mu na gaji da kwanci na fito muna zaune da sadiya fadila ta bar wurin zuwa kitchen duba masu aiki a can. A daidai lokacin tana dawowa yake fadin pretty ya kike na dan dago kai na kalle shi tare da fadi cikin wani yanayi lafiya ya gajiya ? Akwaishi wallahi sai yanzu na tashi ki bani abinci na danci zan fitane yanzu ya fada yana zama a gefena kaina dago kafin inyi magana ta juya zuwa wurin da za, a shirya mashi abincin kamar yadda ta saba yi. Yadda muke zaune zaka dauka mu din wasu ma,aurata masoyan juna a lokacin don ya zauna ya dan kwanto min a jikina . Fadin an hada table da tayi yasa na rigashi mikewa na nufi dinning din ina duba abincin ya biyoni a baya. Zama yayi na fara zuba mai abincin bayan na gama na samu wuri na zauna a gefen shi zakace zaman arziki mukeyi dashi a lokacin yadda muke nunawa. Yana ci muna dan hira har lokacin daya kare ya goge bakin shi ya mike ya danyi hugging dina yana fadin sai na dawo. A dawo lafiya nayi masa na mike na bar wurin cin abincin nan koma inda na tashi ba da farko dakina na nufa. Ina shiga daki take cewa sadiya da alama dai yanzu sun daidaita tsakanin su ko take tambayan sadiya din ? Dama ba daidaitane a tsakanin su anty ta tambayi fadila din cikin mamaki sanin halin sadiya yasa ta basar da zancen itama sadiyace data shigo take fada min yadda sukayin. Bani da wani buri a yanzu illa inji ya kawo zancem zuwan mu gida wurin iyayyen mu duk da ko gidan mami ma da yake garin bamu je ba suma basu leko inda muken ba har yau kwanan mu biyu da zuwa kasan. Tunane nayi dan ganin dacewan hakan ya dawo da yamma nake fadin yaushe ne zamu gidan mami mu gaida su din duk da nasan kai ka tafi ko kun gaisa ko. Ko yau ina can tunda na fita muna tare dasu idan kun huta sai mu tafi lokacin da kuka shirya hakan ya bani amsa. An jima zamu idan Allah ya kaimu na fada ina shirin barin dakin naji yace sai ki fitar da tsaraban da zaku kai masu idan zaku tafi. A cikin mamaki nace ba wani tsara dama dai turarene sai wasu jewels dana sayo da zamu zo na fada ina kallon shi. Tsara yana dayan dakin nan sai ki duba kiga abin daya dace ku kai masu a ciki da duk wani wanda ya dace aba shi tsaraban. Ba mamaki don sanin halin sa nace angode kawai na fita zuwa dakin don duba kayan suna daure har lokacin ba a bude su ba. Don haka ban san ko meye a cikin kayan ba na juya na fita na koma daki da niyar fara shirya fitan da zamuyi din. Ban fadawa kowa zancen fitan ba ko sadiya don gudun ta fadawa wani hakan sai bayan sallah magariba nace taje ta shirya inji yaya zamu fita. Ta juya da murna ta fita nima na zauna ina idar da isha,i na shirya wanan dakin na koma na samu an bude kayan a lokacin na shiga duba ina zaba. Kayane irin na tsaraban mata da maza sai wasu abubuwan da ban sani ba na dai dauki wanda zan dauka na fito. Shiyasa aka kwasa zuwa cikin mota da zamu fita da muka fito na rufo kofan da key din dana gani a wurin na zare key din har kofan da zai sada mutum da part din mu da nasa sai da na rufo na jefa key din a jakkata. Wani iska ne mai dadi ya daki jikina har hanci mai dadi muka tako a hankali zuwa wurin motan dan shi a baya muka barshi bai fito ba. A hankali motar ke tafiya muryan sadiyane ke fadin anty tace bata san zamu fita ba wai. Baki fada mata zaku fita bane ya tambayeni daga gefena nace ban fadawa kowa ba ya sake fadin har fadilan ? Ban fada mata ba don ta canza yanzu a sanin da nayi mata a baya ke sai yanzu kika san da hakan ya tambayeni ? Na juyo na dan kalleshi yake fadin na sani ita din yar sandan ciki ce bincike takeyi a kaina sai dai tana dauka ban sani bane . Sai dai ya akayi ke kika san hakan ya tambaye ni cikin son jin amsa nace zuciyana ne ya bani hakan ban fada mai komai dana sani game da ita ba. Amma kina da abin mamaki zainab yadda har kika gano hakan da sauri da kanki game da fadila din ? Idan ina zaune da mutum tsakani da Allah nake zama dashi shiyasa Allah ke nuna min ko waye maishi da sauri haka ban taba zama da wani mutum da wani manufa saidai kai ka da muke zaune ka munafunceni.YA HAIYYU YA KAIYUMU YA ALLAH KA KARBI IBADUN MU KASA MUNA CIKIN YAN TATTUN BAYIN KA A WANAN WATAN MAI RAHAMA DA DAUKAKA ALLAHUMA AMIN, , , , LITTAFIN KUDINE KI BIYA DARI UKU KI KARANTA YAR UWA DON ALLAH KI GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI YAR UWA KAN ABIN DUNIYA, , , , Na san mai karatu zakiyi mamaki jin abinda na fada akan fadila hakan kuma ya samo asaline tun ranan dana fara gane waye fadila a gurin mu. Ranan kishin ruwa kawai ya tayar dani a cikin dare na fito don neman ruwan da zan sha a lokacin. Banyi amfani da ko wani irin haske ba don nasan inda ruwan yake sauri kuma ya hanani tsaya na dauki ko wayana in haska. Har na dauko ruwan zan fito naga kamar gittawan mutum a falon namu karami. Naji tsoro iya tsorata nayi shi don haka na samu wuri na lafe a bayan kofan kitchen din muryan fadila naji tana waya a hankali. Tana fadin wallahi duk dabaran da zanyi in gane wani abu a gareta nayi shi har yanzu ban gane komai ba a wurin ta . Don yarinyar akwaita da shegen wayau tsiya don wayau ta yafi karfin shekarunta sosai wallahi. Na saka ido sosai don in fahinci wani abu a gurin shi na kasa fahintar hakan duk da janta danayi a jiki sosai abu daya na sani shine. Yana shan cocaine din amma baya harkan sayarwa don aikin sa a nan yana jawo mai babban riba da samu fiye da zaton me zaton hakan. Shiru tayi tana sauraren me ake fada mata a wayan kafin tace zan saka ido kafin tafiyana yazo sosai zan kara gano wani abu a hakan. Kara lafewa nayi sosai inda nake boye ina mamakin ta a raina kafin naji tayi sallama da maishi tana kashe wayan ta dan haska ko ina ta koma daki. Sai dana dan dade ban fito daga inda nake boye ba kafin na fito na koma daki cikin tunanen wacece fadila din ? Haba abin mamaki ne ace mace wayayya kamar fadila tana aiki irin wanan haka sai dai mutum ya duba ga irin yanayin da kasan mu ke ciki na rashin aikin yi zaisa mutum yayi duk wani aikin daya samu don dogaro dakai. Tun wanan ranan na kara tsorata sadiya a kanta ta kuma tsorata duk tambayan da tayi mata takan zo ta fada min da amsan da ta bata a lokacin. Sai gashi bayan kwana biyu tana fada muna gida zata wai mahaifiyar tace ba lafiya a lokacin. Yanzu yana da wuya kayi saurin yarda da mutum farat daya irin haka Allah ya taimakeni ga zurfin cikina. Nidin na kasance irin mutanen ne da basu da yawan sake magana ga kowa idan hakan ba ya kama dole bane. Idan zan tuna duk hiran mu ko sakewan da zanyi sai dai ita din ta kasance mai ban shawara ko tayi magana akan abinda tagani da idon ta tana bugun cikina. Kinji dalilin daya sa yanzu nake ja baya da zancen fadila din duk da bansan dalilin kasancewar ta a cikin mu ba har wanan lokacin. Bamu hadu da yaya J ba sai washe gari misalin sha biyun rana da nake ganin fitowan shi ke nan daga barci. A falo ya same mu na gaji da kwanci na fito muna zaune da sadiya fadila ta bar wurin zuwa kitchen duba masu aiki a can. A daidai lokacin tana dawowa yake fadin pretty ya kike na dan dago kai na kalle shi tare da fadi cikin wani yanayi lafiya ya gajiya ? Akwaishi wallahi sai yanzu na tashi ki bani abinci na danci zan fitane yanzu ya fada yana zama a gefena kaina dago kafin inyi magana ta juya zuwa wurin da za, a shirya mashi abincin kamar yadda ta saba yi. Yadda muke zaune zaka dauka mu din wasu ma,aurata masoyan juna a lokacin don ya zauna ya dan kwanto min a jikina . Fadin an hada table da tayi yasa na rigashi mikewa na nufi dinning din ina duba abincin ya biyoni a baya. Zama yayi na fara zuba mai abincin bayan na gama na samu wuri na zauna a gefen shi zakace zaman arziki mukeyi dashi a lokacin yadda muke nunawa. Yana ci muna dan hira har lokacin daya kare ya goge bakin shi ya mike ya danyi hugging dina yana fadin sai na dawo. A dawo lafiya nayi masa na mike na bar wurin cin abincin nan koma inda na tashi ba da farko dakina na nufa. Ina shiga daki take cewa sadiya da alama dai yanzu sun daidaita tsakanin su ko take tambayan sadiya din ? Dama ba daidaitane a tsakanin su anty ta tambayi fadila din cikin mamaki sanin halin sadiya yasa ta basar da zancen itama sadiyace data shigo take fada min yadda sukayin. Bani da wani buri a yanzu illa inji ya kawo zancem zuwan mu gida wurin iyayyen mu duk da ko gidan mami ma da yake garin bamu je ba suma basu leko inda muken ba har yau kwanan mu biyu da zuwa kasan. Tunane nayi dan ganin dacewan hakan ya dawo da yamma nake fadin yaushe ne zamu gidan mami mu gaida su din duk da nasan kai ka tafi ko kun gaisa ko. Ko yau ina can tunda na fita muna tare dasu idan kun huta sai mu tafi lokacin da kuka shirya hakan ya bani amsa. An jima zamu idan Allah ya kaimu na fada ina shirin barin dakin naji yace sai ki fitar da tsaraban da zaku kai masu idan zaku tafi. A cikin mamaki nace ba wani tsara dama dai turarene sai wasu jewels dana sayo da zamu zo na fada ina kallon shi. Tsara yana dayan dakin nan sai ki duba kiga abin daya dace ku kai masu a ciki da duk wani wanda ya dace aba shi tsaraban. Ba mamaki don sanin halin sa nace angode kawai na fita zuwa dakin don duba kayan suna daure har lokacin ba a bude su ba. Don haka ban san ko meye a cikin kayan ba na juya na fita na koma daki da niyar fara shirya fitan da zamuyi din. Ban fadawa kowa zancen fitan ba ko sadiya don gudun ta fadawa wani hakan sai bayan sallah magariba nace taje ta shirya inji yaya zamu fita. Ta juya da murna ta fita nima na zauna ina idar da isha,i na shirya wanan dakin na koma na samu an bude kayan a lokacin na shiga duba ina zaba. Kayane irin na tsaraban mata da maza sai wasu abubuwan da ban sani ba na dai dauki wanda zan dauka na fito. Shiyasa aka kwasa zuwa cikin mota da zamu fita da muka fito na rufo kofan da key din dana gani a wurin na zare key din har kofan da zai sada mutum da part din mu da nasa sai da na rufo na jefa key din a jakkata. Wani iska ne mai dadi ya daki jikina har hanci mai dadi muka tako a hankali zuwa wurin motan dan shi a baya muka barshi bai fito ba. A hankali motar ke tafiya muryan sadiyane ke fadin anty tace bata san zamu fita ba wai. Baki fada mata zaku fita bane ya tambayeni daga gefena nace ban fadawa kowa ba ya sake fadin har fadilan ? Ban fada mata ba don ta canza yanzu a sanin da nayi mata a baya ke sai yanzu kika san da hakan ya tambayeni ? Na juyo na dan kalleshi yake fadin na sani ita din yar sandan ciki ce bincike takeyi a kaina sai dai tana dauka ban sani bane . Sai dai ya akayi ke kika san hakan ya tambaye ni cikin son jin amsa nace zuciyana ne ya bani hakan ban fada mai komai dana sani game da ita ba. Amma kina da abin mamaki zainab yadda har kika gano hakan da sauri da kanki game da fadila din ? Idan ina zaune da mutum tsakani da Allah nake zama dashi shiyasa Allah ke nuna min ko waye maishi da sauri haka ban taba zama da wani mutum da wani manufa saidai kai da muke zaune ka munafunceni. Oh really ? Ya fada kanshi na duke yana duban wani takardan dake hannun shi hankalina na mayar ga titi da muke tafiya. Har motan ya sha kwanan da zai sada mu da gidan mami din dake wani katon unguwa mai gine gine masu kyau da daukan hankali. Gaba daya sai gidan ya canzawa sanin danayi mai a baya saida muka fito ne a cikin mota na tabbatar da ba wancan gidan bane da muka zauna dasu a baya. Allah ya gani ban shiga gidan da wani manufa a zuciyana ba lpkacin sai gashi muna shiga komai ya canza a lokaci daya. Da farko mun shiga da sallama mun jero tare da yaya sai sadiya dake dan bayan mu kadan tana biye damu a bayan mu. Ko kaine wa dole mu baka sha,awa yadda muka shigo gidan a lokacin gaba dayan su suna falon mami din a zaune har Nuriya da yaran ta kamar wani abu sukeyi a lokacin. Jalal kan ya amsa muna sallama da nuna murshin da ganin mu yana fadin a, a mutanen chaina ne yau a gidan namu haka ? Sai ya jamal daya dago cikin mamaki yana fadin a, a zainab kuma kun zone ashe sannun ku da zuwa a cikin fara,a. Ya jalal mun sameku lafiya na fada tun a tsaye kafin na juya wurin ya jamal ina fadin ya jamal ya gida ya aiki ? Zainab ai sai mutum ya dauka kema yar chaina din ce ko yar wani nahiyar larabawa yadda kika koma din nan inji ya mamud ya fada cikin yar fara,a. A daidai lokacin dana zube gaban mami itama sadiya ta zube kamar yadda taga na zube din muna gaida mami. Sai ji nayi ya jafar shima ya zube a kusa dani yana fadin kamar yadda na fada mami ina wuni mun samuku lafiya. Duk suka kwashe da dariya banda mami data daure fuska tana fadin kai yanzu bakaji kunya ba ace kuna kasan nan tun shekaran jiya amma sai yanzu matar ka zata shigo gidan gaishe mu ? Haba mami kin san suna tare da gajiya nine nace ta bari su huta sai na kawo su na kuma fada maki ai a waya. Kaina yana sade a kasa koda take wanan maganan can na dago na dan kalli inda yan matan gidan da ya mamud da matar shi suke zaune nace yaya mun same ku lafiya anty ya gida ya yara ? Kafin nace kuma anty mun sameku lafiya ya gida ya aiki da karatu duk a lokaci guda na jera masu gaisuwan a tare. Sai ya mamud ne da anty Na,ima suka amsa mun da fara,a suna fadin munzo lafiya ya can ni sai lokacin ma nasan ashe Nuriya matar ya mamud ta kara haihuwa ashe . Don na ganta da yarinya karama dauke a jikin ta da alaman har an yayye yarinyar ma a lokacin . Muryan mami naji tana fadin sarauta dai da jin kai irin na samun wuri har zainab ce yau za a ce wai tana hutun gajiya irin haka a rayuwan ta. Da sauri na juyo na dan kalli mami din kafin naji ya jalal yace haba mami sai kace ita din ba mutum bane naga ke idan mun dawo har karin ruwa ake maki fa. Gasu dai gwanin ban sha,awa kamar ace da yara suke tafe shine abin zaifi burge mutane ai ba a tafi uwar duniya a dawo haka babu ko kwai ba. Nuriya ta fada tana wani irin dariyan shu,umanci a fuskanta wanan kuma sai idan da Allah kike jayayya don shine mai bada haihuwa lokacin da yaso kuma a inda yaga dama. Zainab tashi muje ya J ya fada yana mikewa fuskan shi a daure da sauri ya mamud yace ku tafi ina yanzu kuna shigowa zaku tafi kuma. Dole mu tafi don ba zan lamunci cin fuska irin haka ga iyalina ba ga kowa duk wanda yace zai taba min mata kamar ni ya taba don haka ba zan dauki wanan ba. Kayiwa matan ka iyaka kan sake zancen daya shafeni idan ma haihuwan takewa zainab gori dashi ai ba zainab bane mai laifi don nine raggon namijin dana kasa bata cikin ta haifa. Falon yayi tsit a lokacin kamar babu kowa a cikin sa sai Nuriyan ne tayi karfin halin fadin yo ni ai da wasa kuma naga dacewan hakan na fada don yaci ace yanzu kun fara aje iyali ai. Kai wanan halin baiyi ba wallahi kamar kuna jirace da yarinyar nan tazo ku gasa mata magana haka. Duk da dai mami ke kika fara bada hanyar yin hakan sai dai ku sani a yanzu kuna falon kaf banda mami babu wace ta kama kafar zainanb ko mijin da komai da har zaku tare ta da wanan zancen haka. Kema mai haihuwan aiba rawa ko kida kikayi gaban Allah ba ya baki su da kika tareta da wanan zancen mara dadin ji jamal ya fada yana jan tsuki ya bar falon a fusace. Nuriya ke nan yanzu dai kinji idan ma dama kina jiran inxo ki gasa min wanan maganan ne haka daga shigowa na kamar kina jirace dani. Na fada a daidai lokacin dana mike tsaye sadiya ma ta mike tana manne dani kamar taga abin tsoro a falon. Gaskiya haka baiyi ba Nuriya at,list ai kya bari ta huta kafin ma ki fadi abinda ke ranki ai Aisha ta fada. Ballwma ko an raina dan tsuntsu ba acin shi da gashi don anyi sake dan zaki ya girma ko gaskiyar jamal ne Nuriya zainab dai ba abin yarwa bane yanzu don muje ta muna goma na arziki gaba dayan mu nan Na,ima ta fada tana mikewa. Saida safe mami na fada ina bin bayan ya j din daya fara tafiya a lokacin kafin na juyo ina fadin ga tsaraba nan mami da muka zo dashi ayi hakkuri dashi ba yawa. Na sa kai nabi bayan shi ins jin ya mamud na fadin kin gani mami saida nace kada kiyi wanan zancen a gaban su tunda ya fadi uzurin shi kika yi a gaban wanan mara hankali da tunane. ZAINAB IDRIS MAKAWA YAN UWA DA FATAN MUN WUNI LAFIYA YA IBADA ALLAH YA BAMU KARFI DA LAFIYAN BAUTA MASHI BAUTA TSAKAKAKE A RAYUWAN MU ALLAHUMA AMIN LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA SAUKIN FAHINTA BA TARE DA DAUKAN HAKKIN KOWA BA A KANKI, , , , DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACCOUNT 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , Babu wanda yai magana da dan uwa tun fitowan mu cikin gidan mami din sai tafiya yake damu a guje a haka har muka karasa bakinn wani plaza ya juyo inda sadiya take yana fadin ya sadiya mu tsaya a sai wani abune a nan ? Da sauri ta girgiza kai tare da yaya muje gida kwai hakan ya nuna itama din a tsorace take a lokacin da abinda ya faru. Ya mike zuwa hanyar gidan namu horn ya danna saiga masu get sun bude da sauri don sheda horn din motan da sukayi. Motan na tsaya nayi saurin fita daga motan na dauka shima fita zaiyi a lokacin saidai muna fita sai naga ya juya ya fita daga gidan. Muna shiga falon fadilace ta tare tana muna sannu da dawowa na amsa take fadin ai ta dauka zamu dade ashe yanzu zamu dawo. Eh na bata amsa dashi don ina ganinta zancen ta da mukayi ya fado min a rai lokaci guda ina ganin ta na tuna wai ashe ita din yar sandan ciki ce take zaman leken asiri a gidan mu to akan me na tambayi kaina ? Maimakon na zauna a falo kamar yadda muka saba nake fadin bari kawai na rage kayan jikina sai na nufi hayar dakin inda sadiya ma take biye dani bata zauna ba a falon itama. Mun wuce munbar fadila da mamakin mu a fili kafin ta sauya tunanen ta da cewa wata kila gidan mami muka je aka bata muna rai a can. Tsoranta nake ji yanzu sadiya ta fada a bayana yasa na juyo ina fadin tsoron wa ke nan anty mana naji yaya yace ita din yar sandace wai . To kinga kada ki soma yin wani abinda zata gane kin san komai a wurin ta tunda har mun gane ta sai mu bita da hakan shike nan. Wa zata kama a gidan nan anty da take zaune a nan nima tunanen da nakeyi ke nan sadiya saidai nasan don yaya take wanan aikin a nan mukan meye ruwan mu a ciki tunda bamuyiwa kowa laifi ba . In ma har mamice ta turota nasan ba zata taba kamani da laifin komai ba tunda banyi ba insha Allahu. A dakin muka kwana tare da kanwata da barci ya daukemu bamu ma sanda hakan ba tun muna hiran abinda ya faru a gidan mami har mukai shiru muka fara barci. A cikin dare na falka a dan tsorace na tuna ban rufe kofa ba lokacin bayan na rufene na shiga bandaki na dauro alwala ba abinda nake tunane sai kalamin Nuriya wanda nasan dani take wanan maganan . Ba komai yasa haka ba sai hangen nesa da take min tana ganin kanar duk dadin duniya da daula ya kare a gareni yanzu. Wanda ita bata san ABU CIKIN DUHU SIRINE BA ba ko wani dadi yakan daure a dadin da take zato ba ba tare da kalubalin rayuwa a bawa ba. Hawayen takaici da bakin ciki suka fara zubo min masu zafi daga idanuwana a daidai lokacin da wani tunane ya ziyarci zuciyana na mike lokaci guda na fara ibada sai bayan na dauki lokaci na shafa tare da waigawa inda naji motsin sadiya ina kallon ta sai barcinta take a tsanake hankali kwance nace kin huta baki da damuwa sadiya. Washe gari tun bayan idar da sallah mu da asubah sadiya ta koma dakinta ta kwanta nasan tayi gudune don kada ince ta tsaya muyi tulawan safe da mukanyi wani lokaci idan ta kwana dakina da safe. Nima din ranan ban iya tabuka komai ba gado na koma na kwanta tare da dunkulewa wuri daya a haka barci ya daukeni kuma. Tun daren jiyan ya kasa tsayar da tunanen shi wuri daya har zuwa wayewan garin da bai samu sukuni a tare dashi ba. A gaskiya ya jefa yarinyar nan a cikin wani hali yasan shikan da badon Allah yai mai zabin mata irin zainab ba a rayuwan shi da yanzu kila ya auri mata sun fi a kirga yana sakin su don halin shi. Shidai yasan bai iya tsinanawa mace komai na abinda ya shafi jin dadin aurataiya har ya kai ga an samu ciki don tara zuria. Sam irim wanan tunanen baizo mashi a raiba da farko sam ya manta babu wani babban buri ga dan Afirca kamar ya ga ya tara iyali a karshen rayuwan shi. Yau sai gashi tun ba,aje ko ina a gaban shi an fara suka na da zance mafi tayar da hankalin wanda ake fadawa hakan. Nuriya why zaki shigo cikin lamarina haka da gagawa ki bata min tsarin komai da nake shiryawa a kan mu. Yasan wanan zancen ba waiba zai iya jawo masu matsala a tsakanin shi shida zainab din komai hakkurin ta kuwa. Don komai hakkurin ka akai ma gori akan haihuwa kuma laifin ba naka bane dole ranka ya baci ga hakan. Balle shidin da zainab da ba wani irin wanan mu,amulan a tsakanin su da har zai kai ga tunanen haihuwa nan gaba. Idon shi ya lumshe a hankali yana sauke ajiyan zuciya don numfashin shi da yake ji yana harde mai lokaci guda daga inda yake kwance saman gadon dakin nasa. A hankali ya fara tunu abubuwan da suka faru dashi tun farko har ya tsunci kanshi cikin wanan harkan duk da ba zai iya cewa ga dalilin fara hakan ba gareshi. Da idan akwai wanda ya tsani wanan halaiyar a bayan shi yake sai gashi dumu dumu yau a cikin wanan harkan daya tsana din yana yi. Wani irin nauyi yaji zuciyar shi na mashi lokaci guda da har bai iya sauke numfashi ya sauka mai yadda ya dace. Da kyat ya dago daga kwancen yana dafe da zuciyar shi ya kai zaune har lokacin hannun shi na saman chest din shi kafin ya samu ya sauke numfashi da karfi yana runtse idanun shi . Ya dade zaune a hakan kafin ya mike cikin rashin jin dadin komai a lokacin ya nufi hanyar fita daga dakin nasa. Direct part dina ya nufa kai tsaye ya tura kofan dakin ya jishi a bude duk da safiyane sosai a lokacin yayi mamakin ganin kofana a bude. Kai tsaye yasa kai ya shiga babu kowa a falon ya nufi uwar dakin da yake tunanen ina ciki a lokacin. Can ya hangoni kwance tsakiyan gado na dunkule a wuri daya ina barci kamar a wahalce nake yadda na kwanta din. Ya dan dade tsaye yana kallona yasan dalilin maganan jiyane daya faru a gidan mami din ne ya kawo min rashin barci a daren jiyan. Kamar zai fita sai kuma kawai ya nufi gadon ya hawo a hankali har zuwa inda nake kwance din ya kwanta ya rungumeni a jikin shi. Ga mamakin shi sai yaga na gyara kwanciya ina kara shigewa cikin jikin nasa duk a ciki barcin da nakeyi nayi hakan . Shima ajiyan zuciya ya sauke a nasa bangaren yana jin tausayin kanmu a karo na farko da nadama a rayuwan shi. Ga kamshin bodyspray din da nake amfani dashi yana shiga mai hancin tare da saukar mai da wani irin yanayi a zuciyar shi da ba zaice ga irin abinda yake ji ba lokacin sai kara rungumeni a jikin shi dayayi a hakan. Mun kai wani lokaci yana shakan kamashin man gashin da nake amfani dashi wanda har yakai ga daukan hannun shi a hankali ya cusa a tsakiyan gashin kaina dake kwance lub yasha gyara yadda na kamashi wuri daya da zan kwanta tunda ba kitso muke samun yi ba. Can a cikin barcina nake ji nauyin mutum a jikina sai nake gani kamar mafalkin haka nakeyi kafi hakan ya fara hanani barci don wasan da yakeyi a kaina din. A tsorace na bude idona tare da dan zabura a firgice a cikin razana ina kokarin yin ihu don tsoro . Sai nake gani abin kamar a mafalki don bude idanun da sukai min nauyi don barci da nake ji a lokacin ga kuma mutum a tare dani da ban kawo cewa shine ba sam a raina. Common relax zainab its me jafar kin faye tsoro da yawa now jin hakan bai hanani yunkurin kwance kaina daga gareshi ba a cikin tsoro. Sai kara rikoni da yayi a jikin nasa babu yadda zanyi in kwace kaina a lokacin don irin rikon da yai min din. Meye haka yaya zaka shigo min daki ina barci har ka hau min gado ka rike ni kuma ? Baiyi magana ba sai dan murmushin da naji ya sake da baikai ciki ba dayayi a lokacin. Kafin can inji yace zainab zuciyana kamar zai fashe nakejin sa na kasa rike kaina da kaina ina neman inda zan raba naji sanyi ne a rayuwana. Ba tare da na juyo ba don babu daman hakan saboda irin rikon da yai min ba daman na kaucewa hakan. Amma a cikin karfin hali irin namu na mata nace mai babu sanyi ko sauki a tare dani yaya don babu abinda zan ma a hakan ka sani. Nima din da ka sani da baka nufoni ba don a hakan yadda kake ka sameni a yanzu don ba kai kadai ke cikin bacin rai ba yau. Na sani zainab ya fada kamar wani karami yaro dashi yana kara cusa kanshi a kaina yadda muke kwancen. A cikin wanan yanayin fadila ta fado dakin ta samemu ta koma baya da sauri tana dafe kirjin ta do abinda idon ta ya gane mata a lokacin. Wanan wani irin mutum ne da ba,a gane gaban sa sai da ina gab da hada komai dana samu gareshi yanzu kuma zai canza min lissafi ? Idab na bada shedan shi din guy ne bai aikata wani abu da matar shi fa yanzun ga idona kai haba ashe malam biri yai kama da mutum na kasa gane gaskiyar yarinyar nan tun farko. Ashe akwai abinda ke wakana a tsakanin sune wani lokaci yasa take kin fada mi komai idan na tuntube ta da zancen nasa. A dakin kuma shiru ne ya biyo baya kamar ba zai yi magana ba sai can yace a naki ganin ke nan zainab ? Amma at list ko wanan rikon da nayi maki naji sanyi a raina ba kamar yadda na shigo dakin da kumci ba a zuciyana da farko ba. Da karfin gaske na kwace kaina a jikin shi jin abunda ya fada din ina fadin duk wani jin dadi ko walwala ka haramtashi a zukatan mu yaya. Yau sanadin ka har ake daukan laifin da banawa ba ana dora mi duk da bansan yadda ubangiji ya halicceni ba tun farko ko ni din mai haihuwace ko akasin hakan . Amma a yanzu kam laifin hakan yana wurin ka yaya don dama na dade ina tsoron wanan ranan duba ga yadda mutanen mu suke nan akan aure. Tareni yayi da fadin na fiki sanin duk wanan matsalan yana tafe muna komai dadin dadewa watarana za a samu wanda zai muna wanan korafin na haihuwa a tsakanin duba ga yadda muka dauki shekaru a tare dake. Amma sam banyi tsamani hakan zai fito daga bangarena ba sai dai daga gun yan uwan ki nafi zaton hakan. Zainab nasan kinyi hakkuri ga komai game da zama dani a hakan don banda abinda zan iya saka maki dashi a rayuwana da zan maki na ga na saka maki ga hakkurin ki. Nima din a yanzu nakan yi nadaman hakan saidai ba kowa bane zai yadda da hakan sanin ni ko waye ke tare dake kuma kikai hakkuri kika zauna dani hakana. Duk da nasan Nuriya ta yi wanan zancen tana daukan kece mai laifin rashin haihuwan a tsakanin mu duba ga irin rayuwan da kike ciki a gidana. Wanda nasan zafi da kishi irin naku na mata yasa ta fada muna wanan maganan haka a gaban kowa don dai kawai taga ta bata maki rayuwan ki. Saidai da tasan abinda kalamin nata zai jawo a gareta da bata furta hakan da nufin tozarci a gareki ba don ba iya ita wanan kalaman zai shafa har mijin ta da kowa a yanzu hakan zai shafa. Kara matsawa nayi dan nisa dashi a cikin murmushi nace kaiyya idan kai hakan ga yaya mamud baka kyauta ba kuwa . Don baka da dan uwa mafi soyuwa a gareka bayan shi da jamal duk da ban zauna dasu ba munyi wanan zancen amma naga damuwa karara a tare dasu kan sanin ko kai waye da sukayi. Shiru yayi gashi yana son bani hakkuri saidai ya rasa kalman da zaiyi amfani dashi wurin bani hakkuri a bakin shi don shi a nasa ganin tsaya a bata lokaci wurin ba mace hakkuri wani abune can na daban . Gyara kwanciya naga yayi ya mike saman gadon tare da lumshe idanuwan shi sai hakan da yayi min a daki ya zama min wani bakon al,amari kuma tunda ban saba ganin hakan ba ni. Sai mukai shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunane a ransa sai da na jefo mai tambayan da baiso ne ya bude idanun sa lokaci guda da nace. Yaushe ne zamu gida muga su inna na tambaya cikin kallon shi inji amsan da zai bani lokacin sai cewa yayi dani sai idan kun kara hutawa zan shiryawa zuwan ku din. Ba wani hutu don ba aikin komai nakeyi ba ko wani abu a nan yanzu don haka gida muke son zuwa mu ganesu. Zaku tafi amma ba yanzu ba ya fada yana kara gyara kwanciya vikin dan kara lafewa saman gadon kamar mai shirin yin barci a dakin. Iya kuluwa na kulu da jin amsan daya bani a lokacin don haka ban ko iya bude baki na ce dashi wani abu ba sai faman tunane da nakeyi a can kasan zuciyana wanda na kasa tsayar da zance guda kan hakan. A hankali nake ji saukan numfashin sa dake nuna min ya samu barci ne a hakan na sauka saman gado a hankali zuwa bandaki don i kewa ya daga nan na tsaya yin wanka. Har na fito yana a inda na barshi a kwance yana barci bai tashi ba balle in sa ran fitan shi daga dakin nawa sai abin nasa yake ban mamaki. Haka na daure na karasa bakin mirrow ina shafa mai a jikkina da sauran al,adun mu na mata idan munyi wanka. Kamar ance in daga kai yana kwance ya lafe a inda yake din ya kura min ido yana kallona nayi sauri kawar da kai daga hada idon da mukayi dashi da sauri. Mikewa nayi zuwa wardrobe dina na bude sai lokacin nace dashi an lodawa mutum kaya haka kamar wanda zaiyi wani abu dasu ba sakawa ba. Idan basuyi maki ba sai ki kyautar ya fada yana juyawa daga barin da yake kwance din nace har yaushe zamuyi amfani da wanan kaya haka wai ? Har na gama na shirya a boboye duk yana dakin banu abinda nake ji sai haushi da takaici nasa na yadda ya zauna min a dakin da bansan dalilin hakan ba. Bai fita dakin ba nima kamar an dasani a dakin haka muka zauna sai wuraren sha biyun rana ya bar dakin ya nufi part din shi. Nima daki na gyara duk da wata tazo wai itace mai gyara amma ban yarda da hakan ba dana tashi kafin tazo na gyara dakina tsab balle yanzu da nake jin tsoron duk wanda ke gidan tare damu zaune sai nake masu bugu daya gaba dayan su ma aikatan gidan. Ban fito ba saida sadiya ta shigo dakin tana fadin yayan mu kun tashi ke nan dazun nazo zan shiga anty ke fada min yaya yana ciki kwance. Fadila fa na fada da mamaki tace eh ita ke fada mi hakan sai na koma barci yanzu na tashi yunwa nake ji sosai tana shafan ciki ta. Ina mamakin fadila a raina nace ke nan bakici abinci ba kema tun dazun jin hakan yasa na mike muka fito falon tare ganin fadila dake mazurai yasa nace barin duba yaya ya fito mu karya na nufi part din nasa. Na samu yayi wanka har ya saka tufafi a jikin shi a cikin daure nake fadin wai sadiya bataci abinci ba tun dazun tana jiran mu fadila ke fada mata kana dakina. Bakiji lokacin da ta shigo dakin bane muna kwance ya fada na zaro ido waje a cikin mamaki yace eh ai hakan yayi kyau don zata shiga duhu kan abinda take hadawa yanxu. Haka dai muka fito suka shiga gaidashi yana amsawa cikin basarwa har ya zauna yana fadin kanwata ya akayi baki ci abinci ba kika tsaya jiran mu ? Haka dai muka zauna duk abin yana daurewa fadila kai don ta kasa fasara matsayin da yaya j yake ciki a yanzu don bayanin data tara nata yanzu ya bayar da ita kuma. Wayan shi ne ya shiga kuka alaman kira na shigo mashi a lokacin ya basar kamar bai ga kiran ba haka yasa na duba ya mamud ne na dan dube shi sai ya dauki wayan ba don yaso ba sun gaisa yake tambayan shi naji yace bana gida na fita tunda safe. Haka yasa na dago ido ina kallon shi vikin mamaki don da alama abinda ya fadi yake shiri sikatawa don laifin daba nasu ba ya shafi kowa a yanzu ke nan. To meye laifin su ma akan wanan maganan dashi ya jawa kanshi hakan kome aka fada ai naga shiya jawa kansa dai hakam. ZAINAB IDRIS MAKAWA HASBUNALLAHU WANI IMAL, WAKIL YA HAIYU YA KAIYUMU BIN RAHAMATIKA YA ASTAGIS , , , , LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA SAUKIN FAHINTA BA TARE DA DAUKAN HAKKIN KOWA BA A KAN KI YAR UWA, , , , , DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACCOUNT ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , , , , Kwana biyar rabon mu da gidan mami har ranan ya J bai leka gidan ba tun mami na boye zafin hakan da take ji har ya kai ranan ta zauna a falo suna magana da yaranta ta sako zancen rashin zuwan shi gidan da baiyi ba. Kowa yai shiru a falon sai jamal ne ya bata amsa ba tare da ya dago kaiba yake fadin mami ya zaizo kuna masu cin fuska irin haka ko waye ma ai dole yaji zafin hakan. Shike nan kada a fadi gaskiya don kawai ya dauki yarinyar tafi kowa ko me zaice tayi laifi kada a fada. Harni zainab zata ce saita huta zata zo gaidani da ace matsiyatan mahaifan ta ne garin nan har zata kwana uku bata gansu ba ? Haba haba mami wanan abin fa ke batawa ya j rai daku ko ya iyayyen zee suke ai yanzu an zama daya dasu mami jalal ya fada. Ji wani maganan banza da wa suka zama daya wa yan nan kaskantattun mutanen Aisha ta fada tana wani kauda kai. Ke ni kike fadawa maganan banza haka ku mi shiru mami ta fasa a hasale tana zarewa kowan su idanu lokaci guda. A daidai lokacin ya mamud ya shigo falon ganin yadda ya samesu kowa ranshi a bace yake fadi tun kan ya zauna. Ba wanda ya bashi amsa sai ya juya wurin mami yana fadin mami mai ya faru kuma na ganku rai a bace ? Barsu da batun banza kasan su jamal da jalal kamar wa yanda yarinyar nan zainab ta asirice su basu son ayi zancen ta ko kadan. Zancen me kuma mami ina dai anyi wanan zancen ya tafi waya tayar da maganan kuma yanzu ? Nice na tayar kan zancen rashin zuwan shi gidan nan yau kwana biyar ke nan da yin wanan zancen bai leko ba. Zaizo mana mami abinda akai masu ne ba a kyauta ba idan ke kin fada masu ita wanan mara hankalin ina ruwanta da rashin haihuwan su har yanzu ? Ko ita din da take haihuwan yaushe ta iya kula da yaran da har take fadawa wani bai haihu ba ? Ta samu wurine a wurin mami don taga mami ta saka yar mutane a gaba akan danta yasa itama ta fadi hakana jalal ya fada . Ya salam yaran nan me kuke son mayar dani ne yanzu bari kuje dukkan ku rayukan ku zai baci dani wallahi kan wanan zancen. Kiyi hakkuri mami ya mamud ya fada yana kaiwa zaune kafin yace barin gwada kiran jafar din yanzu muji in lafiya yake don na kirashi yake ce min yana wani aikine. Ya kira shi saidai bai dauki wayan ba har ya katse ya kara kiranshi wayan ya nuna yana busy. Yace kin gani duk na kira busy yake saka min harni fushin ya shafeni ke nan ya fada yana kallon uwar tasu. Yayi fushi mana indai don kan yarinyar nan ne zainab mai shegen bakin wayau su na yan kauye yarinya kwarkwar da shegen bakin wayau zanyi maganin ta ai don ba zan yarda ya kara barin kasan nan ba tare da kara aure ba. Da sauri duk wanda ke falon ya dago kai yana kallon ta don jin abinda ta fada din . Kai haba mami kada ki soma wanan abin don zai zama tonun asiri a garemu baki daya tunda kinga ko zainab din dai hakkuri takeyi dashi ai. Hakkurin me mamud kune baku gane wanan yarinyar ba tun farko ni yanzu na dawo daga rakiyan ta ai. Tunda na gane me take hadawa kan dan uwan ku idan da baida amfani a gareta zata zauna dashi tsawon wanan shekarun hakane ? Tunda ta kasa shawo kanshi ai gara a auro wace zata zama silar barin komai nasa zaifi ta fada tana kawar da kai gefe daya a hasale. Wanan shawaran naki baiyi ba mami sam wallahi don ya j din ba zai taba yarda da hakan bama wallahi . Ke dai ki barshi a yadda ya zabawa kanshi illa dai a tayashi da addua shine abin yi a yanzu don wallahi tonawa kai asiri kawai za ayi ga hakan. Ya mamud na shiru jamal ya dauka yace kai mami ina kika samu wanan shawaran kuma yanzu ? Ya fada yana kallon ta yace kindai san waye ya jafar ai kin kuma san haiinsa idan zainab ta zauna ta rufa maku asiri duniya bata jiku ba wanan da zaki aura masa itace zata zama silar tona maku asiri a duniya . Wai kanshine farau wanan halin idan na kara masa aure ai ita yarinyar da zan aura masa ba wata bace ta daban a cikin yan uwa zan aura masa wace ta waye ta san kanta har ta taimaka masa ya daina wanan halin da ake masa zaton yana yi. Au mami yanzu baki yarda yana komai ba ke nan ya jamal ya tambaya cikin mamakin jin abinda mahaifiyar tasu ta fada. Idan ma yanayi sai ka dauki laspeaker kayi shela zai fi ma sauki idan da har na yarda da zancen ku yanxu ban yarda da hakan ba. Lalai mami akwai abinda ke damun ki ya mamud ya fada tare da fadin ke da kanki ba wani ya fada maki wanan abinba duk da mun san da haka amma ke kika gani fa da idanuwan ki. Nayi da kai na gansa a wani halin a lokacin ko wani ya fada ma hakan cewa yaga yana aikata wanan abin . In ma har zargi ake masa a bari ya kara auren sai mu tabbatar da hakan daga bakin wata ba a bakin wanan yar sherin yarinyar ba zainab. Duk shiru sukayi sai can Aisha da har lokacin bata sanda zancen ba tace wai ma har me yake aikatawa haka mai muni da ake ta wanan zancen wai ? Iyaka dai zainab tace yana neman mata ko ba a nema ita aka nemeta ne wai da ake wani tarewa kada a kara masa aure . Waya gane me take samu ina gidan su da yan uwanta kawai take aikawa inba wanan karon data kawo muna wanan tsaraban ba haka ? Ya jamal daya mike ya watsa mata wani irin harara daga inda yake kafin ya juya ya fice falon suka bishi da kallo cikin mamaki. Yana zaune dan falon dake part din shi saidai wanan karon ba komai yake yi ba zama yayi kamar mai tunanen wani abu a zuciyan shi. Kafin wayan shi dake gefe ya dauki kara ya kalli wayan saida ba sunan mai kiran nasa wanda hakan ya bashi mamaki waye zai kirashi da bakon lanba ne ? Ya raya a ranshi yayan shi mamud ne ya canza layi don kin daga mai kira da yakeyi a kwanan kin nan. Ya dai daure ya daga kiran ba tare da yin magana ba muryan jalal yaji a wayan yana gaidashi ya amsa yake fadin bros kwana biyu gashi har yau mami tana zancen ka. Ya J rashin zuwan ka yasa mami tana shirin karayi ma aure don ta dauka laifin zainab ne hakan . Wani murmushi ya sake a fuskan shi yana fadin aure fa jalal ita mami din ta fadi hakan yace wallahi yau take fadin hakan a gaban kowa dake falon . Nan dai ya kwashe komai ya fada mai a cikin bacin rai har yana fadin ni bansan meyasa mami take kin zainab dinka ba yaya ga Nuriya da take mata iskanci amma bata ganin hakan. Kada ka damu jalal ta dai fadi hakan ne kawai amma tasan ai banda ra,ayin mata biyu a rayuwana. Bai tsaya jin ta kanin nasa dake fadin kada ka bari ta san ni na fadama don tayi warning din mu kada wanda ya sanar ma da hakan. Ya kashe wayan ya mike tsaye cikin hasala zuwa dakin shi don ya watsawa jikin shi ruwa kafin nan ya fito. Ya fito ya samu miscal har uku a ciki hardana jalal din daya kara kiranshi sai na ya mamud bai kira kowa a cikin su ba don yasan zance dayane dai suke kiranshi a kai. Fitowan shi yayi daidai da shigowan ya mamud gidan muna gaisawa sai gashi taro na musanman aka hadawa yaya din a babban falon gidan da akayi don karban baki maza. Sun gaisa yake tambayan shi ko lafiya kwana biyu bai shigo ba yake fadin lafiya kalau yake yana hutu ne a gida kawai. Kana ganin rashin shigan ka gida wurin mami hakan da kayi shine mafita a gareka yanzu. Dan murmushi ya sake tare da fadin mamud ya kake son nayi da mami meye laifin yarinyar nan zainab mamud ? Idan mami bata godewa zainab ba ba kuwa zata hattare ta ba haka tana kokarin maida mun mata abin tsana a gareta. Shima mamud din dan murmushi ya sake ma dan uwan nasa yana fadin duk mun san da hakan mun fadawa mami din komai. Amma ta nuna ba hakan ba ni yanzu hukuncin da take son dauka a kanku don kawai maganan wanan mara hankalin Nuriya da mami ta hau shine matsalan dake shirin kunno muna kai a yanzu. Wani matsala ke nan ya tambaya kamar bai san komai ba a kai sai mamud din ya dan dukar da kai kasa yana fadi a sanyaye mun dai fada mata zatayi kuskure idan tayi hakan don zai shafi gaba dayan mu gaskiya. Duk zancen da sukeyi a kunnen fadila sukeyin shi kafin J din yace dashi ku barta duk wance zata aura min taje ta aura zata gane true colour dina lokacin. Dan kallon fargaban jin abinda ya fada da fadila tayi mai yasa shi fadin fadila live dis place please. Da sauri ta mike daga zuba ruwan juice din da takewa ya mamud ta koma ciki da sauri cike da biyayya a gareshi don bin umurnin shi. Hakan baisa ya je gun mami din ba saida aka dauki kwanaki ya tafi bai wani tsaya ba suna gaisawa ya juya ya fito fuska a daure. Nikan a lokacin ba abinda nakeyi sai sha hakkuri don mu samu ya sallameni zuwa gida gashi a bangaren fadila gulman abinda taji yana cin ta don a gaskiya duk da tana aiki akan shi ne hakan bai hanata sona a cikin ranta ba duk da ta kulla da ina ja baya da zancen ta a yanzu don ba kamar da muke ba sai mu zauna ba wani zance mai tsawo kamar yadda muka saba a baya da ita. Satin mu biyu da zuwa Nigeria sai ga wayan sa,adatu take fadin ai gata ta hanya zuwa wurun mu inna ta aiko ta ta duba lafiyan mu. Sam banji dadin hakan ba duk da hakan yana cikin karamawan iyayye a gare mu don asan mu din muna da gata yin hakan kamar al,adane na malam ba haushe. Don inna tayi tayi da Abba a samu wanda zaizo ya dubamu da saukan mu amma sai Abba din ya hau fada kan hakan dole inna taja bakin ta tayi shiru. Shine karshe suka yanke shawara a daki da yaranta kan sa,adatu ce zata zo Abuja ta dubamu da dan tsaraban da inna din ta hada muna kamar su dambun nama datayi mai yawa sai man shanu da kwai da dubula. Duk a gidan malam mijin mai zube inna ta bada kudi aka hada komai a can da tare zasu zo da maizube din sai aka tashi ranan da zasu zo din wani a cikin yan uwan maizube din ya fadi ya rasu da asuba. Shine dalilin da sa,adatu ta biyo hanya ita kadai duk da bata taba zuwa Abuja ko wani wuri mai nisa irin hakan ba sai wanan ranan. Jin haka yasa na bugawa yaya waya ina sheda mai zancen zuwan sa,adatu din dake hanya tafe shima yayi mamakin hakan yake tambaya tana ina yanzu nace tace sun kusa shigowa gari don motan safe ta biyo zuwa Abuja din. Bai dawo gidan ba sai tare da ita sukaje tssha aka dauko ta niki niki da robobi tsaraban da tazo muna dashi din. Munyi murnan ganin juna da yar uwan mu har mun manta da duk wanda ke wajen a lokacin yadda muka makalewa juna don daukin ganin . Sai cewa ya j yayi kuyi a hankali kada ku kayar min da matana don Allah duk aka kwashe da dariya a wurin yadda mukeyi saida ya ba kowa sha,awa don hakan na nuna akwai shakuwa da kaunan juna a gare mu. Daki muka shiga bayan gama murna sai mamakin yadda muka canza take yi har ta kasa boye hakan. Fadilace ta kawo mata abinci har dakin don gaskiya ina gani kokarinta wuri kaskantar da kai da takeyi don aikin ta wurin boye ko ita waye gare mu ta nuna aikin da ya kawota garemu shine takeyi a gidan. Yau dai naga sa,adatun nan da nake yawan jin labarin ta gun ku ta fada tana aje turen abincin a gaban mu nace ga anty fadila sa,adatu. Ta juyo tana fadin ayo itace ashe gaskiya yayan mu tana yawan ban labarin ki anty sannu da dawainiya an gode fa. Ni kaina naji dadin hakan da sa,adatun ta fadawa anty din sai na karbe da fadin wallahi sa,adatu ko ya j yana fadin banda kamar anty a rayuwana shi kanshi yafi yarda da ita sama da kowa a rayuwan shi. Yana daukan ta tankar yar uwa a garemu yanzu don ya wuce zaman aiki a tsakanin mu sai zumunci da rufawa juna asiri a yanzu don shi yanzu bai san abinda zai saka mata dashi ba. Wani irin yanayi ta nuna a fuskanta lokacin da nake fadin hakan ta dan sake dariyan yake kawai tana dagawa a sanyayye ta bar gurin. Tana fita na bita da kallo a fakaice kafin muryan sa,adatu ya dawo dani daga kallon fadila din tana fadin . Anty wanan gidan naku kamar a turai mutum yake ni ai ban gama kallo ba don kawai kada na bar abin kunya na shigo. Ki gama mu fita sadiya ta fada da take kwance rub da ciki tana jagulan wayan sa,adatu din dake hannun ta tana dubawa. Munyi hira sosai ranan a daki muka wuni sai bayan la,asar yaya Jafar ya shigo dakin ya same mu zaune mun baje tana muna hiran Asabe da Lantana na fafatawan da ake tsakanin su yanzu. Sai dariya muke kwasa ina kwance a gurin dana sallame sallah ita kuma sa,adatu tana saman rogh din dake tsakiyan dakin sadiya na saman gado kwance. Gaida shi sa,adatun keyi ya amsa tare da karasa shigowa dakin ya nufi bakin gado ya zauna yana tambayan ta mutanen gida ? Tace duk suna gaida shi su inna sunce ai masu godiya kafin su hadu na alherin daya aika masu shekaran jiya dashi . Dago kai nayi da sauri na dan kalleshi bai nuna komai ba yi yayi kamar bai ganni ba ma na kallon da nake masa. Yanzu karatun ki yayi nisa ko ya tambaye ta tace insha Allah muna two hundred level ke nan yace ashe kun fara nisa sosai . To ya zancen ku da baba yanzu dai ya amince ki karasa karatun naki kafin zancen auren naki ko mu tsaya mu sha buki kafim mu koma ne ? Ya tambayeta a cikin zolaya tace Abba ai case ne wallahi ni ba do kai ba yaya ai ba zai yarda naci gaba da karatuna ba a yadda ya dage din nan . Yanzu ko shiru baya zancen ma sam idan ba nayi masa wani laifi ba kuma a kan lantana ce dake zugashi zakaji yace yar abu kaza aure zan maki in huta ai. Ya kwashe da dariya zakace ba ya j bane ya sake haka a gabanta yana kwasan dariya nice na katse su da fadin ga sako nan inna ta aiko ma dashi ina nuna masa kayan da tazo dasu din. Abinka da wanda bai saba da hakan ba ya dago kai yana fadin wanan meye haka da yawa aka aiko muna kuma ? Sadiya ce ta sauko saman gadon da take ta fara bude mai roban dake cike da dambun nama kafin ta koma gana kwai dana man shanu . Yake fadin kai wanan duk namune haka amma inna tayi dawainiya da yawa gaskiya. Ai kaima kana dawai niya dasu sosai har su rasa bakin godiya sa,adatu ta fada yake tambayan sadiya cikin basarwa wanan din da kika bude da farko meye shi sady ? Tace barin debo ma kaci kaji dambu ne na nama aka soya yace a hakan na tuna mami idan tazo ana kawo muna shi muci muna US. Ta debo mai a lokaci nace sai a dibarwa su mami a kai masu don wanan dai yayi muna yawa kan a nan. Bai ban amsa ba sai diba da yayi ya fara ci wanda hakannda yayi yai muna dadi sai godiya yake daids ya danci sosai muna hiran mu da sa,adatu bai ce komai ya mike yana fadin zaki kwana biyu a nan ke nan ko ? Eh to kwana biyu din innan mu tace nayi na koma kada Abban mu yayi fada idan na dade yace ba zai yi fada ba ai a wuri mu kike ba wani wuri ba. Mu yaushe zamu tafi ina tare zamu koma da ita idan zamu tafi na tambaya yayi kamar bai ji me nake fadi ba yasa kai ya fita. Wai mu ba zamu gida bane yayan mu sadiya ta tambaye ni nace sadiya ban san me yake nufi da tafiyan mu ba har yanzu sai ja muna rai yake yi. Kai wai meye a zuwa gidan da kuka matsa dayine ina dai dole ku tafi kafin ku koma ai . Ki bari kawai sa,adatu bafa komai muke mashi a nan din ba kawai kuntatawa iri na mazane kawai. Anty a gaskiya kinyi dacen mijin aure ga hankali ga natsuwa gashi da son yan uwanki kamar nasa kowa yana fadin hakan gaskiya ki godewa Allah da wanan rufin asirin da yai maki ke kan. Wani iri naji a raina sa,adatu ke nan ke fadin haka ina ga iyayyen mu da ya riga ya saye nasan akwai aiki a gabana kan abinda nake kokarin shiryawa nan gaba ke nan. Don su ba zasu gane ABU A CIKIN DUHU SIRI NE BA ni kadai nasan irin rayuwan da nake yi da ya jafar din don ko sadiya dake zaune damu nasan kirkin shi zata fada a gida idan hakan ya taso . ZAINAB IDRIS MAKAWA ALLAH YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YASA MUNA CIKIN YAN TANTUN BAYIN SA YA NUFEMU DA AIKATA ALHERI A RAYUWAN MU AMIN, , , , , , LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKI SALAMA DA AMINCEWA DON ALLAH DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACOUNT 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , , Washegari mun tashi lafiya tare da kannena dashi mukai breakfast a cikin raha yana zolayan su har muka gama. Ya mike zai tashi nake cewa dashi zancen tsaraban da za a kaiwa su mami din sa,adatu tace dayani sai naje na gaida mami tunda ba dadewa zanyi a nan ba idan za,a kai masu. Allah ya gani banda niyar zuwa gidan mami kuma kan abinda sukai mun a ranan yasa na tsani sake zuwa da niyar gaida mami din gidan ta kuma. Duk da nasan hakan abune mai wuya a wuri amma ba yadda na iya dole na amsa da hakan na dakyau sai naga ya dan kalleni a falaice baidai yi magana ba ya barmu a wurin. Kamar yadda muka tsara hakan muka shirya da yamma bayan sallah la,asar don fita zuwa gidan mami din a karo na biyu da zuwan mu garin duk da nasan akwai kalubalin da ba za,a rasa ba ga zuwan namu gidan dake jiran mu. Tunda a yanzu na gane dai ba zan taba haske a wurin mami ba don ta nuna min hakan a zahiri bata dai kaunana a yanzu sam. Amma don kada kanwar tawa ta gane akwai wani abu a tsakanin mu da mami din yasa na daure don na kaita ta gaida mami din wanda ita take ganin hakan girmamawa ne a wurin ta. Driver ne ya kaimu a cikin wani haddaden jeep dake fake a gidan tun zuwan mu nake ganin motan a jiye sai gashi yau da moka fito naga itace zamu fita da ita wanda hakan umurnine daga maigidan nasan. Dukkan mu ukun mun gama haduwa wurin tara kwalliya da kure adaka inji bahaushiya wuri kwalliya muka dauki hanya har da fadila a wanan tafiyan sai da tayi mamakin jin cewa ta shirya zamu fita tare da ita. Zaune take dakinta tana waya da yar uwanta dake fada mata hjyn su jikin ta ya dan motsa a ranan amma sun kaita asibiti taji sauki a lokacin tana dai kwance. Bayan sun gama magana ne da yar uwan take tambayan mami din da cewa ashe jafar tare yazo da matar shi kasan wanan karon dazun nake jin haka da suke waya da yaya a falon hjy. Dan wani basarwa mami tayi kafin tace tare sukazo ai yar rainin wayau yarinya da take ganin yanzu daidai take da kowa tunda ya maida ita wani abu a idon duniya. A dama haka zata gani yanzu ai yaya tunda ta samu tsuntsu daga sama gasshe a hannun ta ba dole ta dauka tafi kowa ba. Wai ki duba yarinyar nan saida ta kwana kusan biyar a kasan nan kuma a garin nan fa wai kafin zainab tazo gaidani . Da sauri mama Ramatu din tace ita zainab din lalai yanzu wuyan ta ya isa yanka ke nan inda uwarta ce a garin zata iya hakkuri har kwanakin bata zo ta ganta ba. Shina fadi nima Ramatu har yaran nan da basu san ciwon kansu ba suke ganin laifina kan hakan don nayi magana Nuriya kuma take fadin . Ai bata burge ba tunda basu zo ganin mu da kama hannu ba da zasu zo shine fa wai jafar din har da daukan fushi dani don hakan. Shi jafar din ta tambaya da mamaki tare da fadin kai yaro kamar wanda aka shanye da asiri kan yarnan wanan abubuwan da yakeyi akanta ? Barni da mara mutunci zanyi magani su daga shi har ita don ba zai bar kasan nan ba sai da auren wata matar wanan karon . Ta san cewa ban haifa mata dan ita kadai ba don su juya shi yadda suke so ita da iyayyen nata da yakewa bauta. Wai yaya kina ganin zai yarda da hakan yanzu dama can bai yarda ba balle yanzu din kuma ya yarda ? Zan tsaya sauraren shine Ramatu ai wanan karon umurni kawai zan bashi bawai rarashi ba daga shi har ita ai basu fi karfina ba Ramatu. Zan zauna ne in saka masu ido tsawon wanan shekarun ba haihuwa ko batan wata tare dasu sai bakin kazafi da sheri da suke kokarin kulawa yaro ko yaushe shiko idon shi ya rufe baya ganin hakan ko kadan ? Ai gara kan a gwada don shi bai sanin dadin hakan sai idan anyi zai gane gata akai masa da yin auren. Shidai nagani Ramatu amma yaran nan da yake kansu daya duk basu ban goyon bayan hakan ba ai ni zan tsaya bin ta kansune halan. Aisha ce ta shigo dakin a fusace tana fadin nifa mami ban ganewa wanan mai aikin naki ba fa duk akace tayi min gyaran daki sai wani abina ya bace a dakina. Wayan ta katse tana kallon yar nata kafin tace wai bata daina wanan halin ba har yanzu kawai wanan karon idan zargina ya zamo gaskiya zan koreta ne don na gaji da zanbar yan aiki a gidan nan. Kwanaki ina fada maku daga cire agogo in shaga ban daki sama ko kasa na nemeshi ban gashi ba a gidan nan. Wazai dauka mami banda ita mudai tun barin mu da zee wallahi bamu kara samun yar aikin kwarai ba a gidan nan abu kamar da sa hannu a hakan. Ita ma din aka sani ko hakan take wanan mai iya kilibibin tsiya da takom saka wa zai sani idan ma tanayin hakan ? Kai haba mami gaskiya bata taba hakan ba ida ba dai wanan case na yaya j da ita ai zainab mutunce a wanan lokacin. Tsuki mami din taja tana mikewa ta fito daga dakin tana kwalawa mai aikin kira da tantano tantano hat tana sarkewa wurin daga murya. Matar ta fito da sauri tana amsawa da akala zatayi haihuwa bakwai ko shidda da haihuwa don dai ta dan manyanta kadan. Tana fadin gani hjy mami ba tsaya jiran komai ba take fadin wai saunawa zanyi warning dinki kan taba muna kayane idan bamu baki ba. Ni hjy mai kuma akace na dauka yanzu karya za ai maki muna tare da wasu a gidan nan bayan ke da za ace sune suke daukan muna kaya. Wallahi sunma tallahi ban daukar maku komai ba hjy ta fada a cikin wani yanayi na bacin rai da rudewa lokaci guda. A wanan lokacin mukayi sallama muka shigo gidan duk abinda suke fadi a kunnen mu wanda shigowan mu bai hana matar cigaba da magana ba tana fadin. Hjy mezai sa na dauki abinda ba nawa ba idan ba a banba sai dai idan ba a duba bane da kyau. Ban duba ba na nema banga dankune dana cire ba na aje saman side drower dina yanzu kuma na nema kaf dakin ban gani ba. Da mamaki muka karaso tsakiyan falon inda suke matar tace nikan ban dauki dan kunne ba wallahi kuma ban maga yan kunne a wurin ba gaskiya. Don Allah rufawa mutane baki mutanen banza duk haka kuke sai an yarda daku kwana biyu ku yaudari mutum mami ta fada a cikin takaici. Wanda nasan gugan zana ce akai muna gaba daya lokaci guda harni dana shigo da yan uwana a gidan lokacin yasa mami fadin hakan don ta sokeni kawai. Sallama na kara yi don kawai su bar zancen tunda mun shigo muzanci bada kyau a yadda sukewa matan . Aisha ce ta amsa tana fadin kune a gidan sannun ku da zuwa tana yar sake yake a fuskanta muka karaso mami na fadin. Ni dai ban taba dace da yan aikin kwarai ba a gidan nan kowa ka yarda dashi sai ya ha,ince ka a karshe ya nuna ma halin yan duniya. Ta sake fadi a fusace jeki wallahi kifoto mata da dankunen ta kafin na hadaki da security ranki ya baci. Ta juya zuwa wurin kujera ta zauna muma zama mukayi saman kujerum muna gaida ita . A cikin mamaki ta dago kai tana amsawa tare da mamakin hakan don bata iya boye mamakin taba na zaman da mukayi akan kujera tana zaune sama itama a lokacin muke gaida ita. Wanda ta dauki hakan a raini ne sosai a wurin ta, don kamar zaman tsara da tsara ne mukayi da ita a falon a ganin mami din. Saidai ta daure ta amsa muna da kyat tana wani jan kamshi a tare da ita a daidai lokacin da wani yaron gidan yake shigo da roban da fadila tayi siling din kayan tsaraban Sa,adatu da tazo dashi. Can ta juyo tana kallon shi tare da fadin wanan fa daga ina haka kuma tana kallon shi tana son karin bayani kan kayan da taga ana shigowa dashi falon. fadila ke fadin hjy tsarabane da akazo dashi daga anchau shine aka kawo maki. Inane haka kuma ta fada a wullakance tana dan bata fuska , a cikin dan murmushi fadilan tace mahaifan uwar dakin mu zainab ga kanwata nan da tazo jiya tazo dashi. Ta dago ido ta dan kalli sa,adatu da mamaki ya fara kasheta a zaune tana fadin owo tazone ashe ? Babu ko ya mutanen gida sai cewa tayi lafiya dai tazo ko wani abu tazo yi nan din da tazo tare da tsure mu da idanuwan ta tana karewa sa,adatun da mukai matukar kama da ita sai dai hanci da dan dogon fuska da haske kadan dana darata dashi wanda hakan yasa na fita kyau a gani da kuma wayewa shine kawai bambamcin mu. Kai tsaye wanan karon na bata amsa da fadin duba mu tazo tayi taga saukan mu ta duba lafiyan mu. Sai ta kawar da kai gefe can Aisha tace meye a cikin roban tana kallona ki duba ki gani mana da idanun ki na fada cikin dakewa. Mami tayi saurin dago kai tana kallona don jin abinda na fadawa yar nata kai tsaye ta kasa danne zuciyar ta tace koma meye ai ba abinda baki taba gani bane da zai dameki har kina tambaya. Wayana yai kara daga cikin jakka na sa hannu na dauko sunan ya j na gani a screem din wayan na dauka yake fadin kuna ina nace gidan mami. Badai matsalan komai ya fada da sauri na ce a wayence babu don kada a gane tambayan da yai min din a lokacin sauran yan matan suka fito dakunan su. Da yanzu dai ina ganin zaman su ya dawo Abuja ne suma bayan gama karatun su saidai ba wace tayi aure har yanzu a cikin su. Rufaida ke fadin ba tare data kulamu ba ko tayi muna sannu da shigowa take cewa mami naji kina fada da wanan matar mai shegen baki. Bari Rufaida macutan mutane ne yan aikin nan dukkan su ka basu amana sai sun yaudare ka maha,inta sai mutum.ya kwaso talaucin shi daga kawai yazo ya sameka da abinka yace zai cuceka har gida. Af mami ai kin saba da halin su dama wahala ke koro su ai suzo birni aiki kome suka gani sai su dauka a banza ka sameshi kai wasu har su so hada kansu da yan gida su nuna sun fi mutane a karshe. Dan murmushi na sake kadan ina fadin wanan kuma in kinga haka dama can mutum ba wullakntace bane da baiwan sa yazo . Wasu ba sunan aikin suke zuwa ba cin arzikine sai kiga sun fi masu gidan iya shege don kawai haye daga sama ba a san kan arzikin ba. Ai abin ke dai daga Allah ne da yake tsarawa kowa rayuwan shi yadda yaso mu zamu koma mami dama na kawo sa,adatune ta gaida ke. Ban jira me mami zata fada ba na mike tare da kallon inda su Aisha suke ina fadin mun barku lafiya mun tafi. Idan mijim ki na gida zan shigo don ina son ganin sa ki fada mai ban ko tsaya ta kanta ba na karasa gaban mami tare dan dukawa ina sallaman ta muka fita. Shiru motan ba wanda yai magana a cikin mu kowa da irin tunanen da yakeyi a lokaci a zuciyar shi. Mami kamar bata son ganin mu gidan ta kullun mukazo sai ta dinga daure fuska tana nuna bata son ganin mu. Babu yadda zatayi ai dole ta ganku tunda danta ya dauko ku gidan shi bai kuma gaza da ku ba a rayuwan shi . Don haka tayi a banza tunda bata sadai ya sake ki sai dai tace zata kara mashi aure don ki don kawai ta bata maki rai don kiyayya. Aure kuma aishi yaya din ba zai yarda ba sai dai idan yana ra,ayin hakan dama zai yarda da shawaran nata sa,adatu ta fada . Nidai ina jinsu ban tanka masu ba ina tunanen wanan maganan da fadila ta fada yanzu don tabbas hakan zai iya faruwa ba wai bs. Gashi a bakin fadila nake jin zancen don nasanta nasan halin ta idan ta fadi magana kamar ta auna ne kafin ta fada. Mun tsaya wani shago don sayen yan abubuwan motsa baki da zamu gida dashi har lokacin banda walwala a tare dani har muka koma gida. Zaune muke a falona muna hira ya shigo da waya a hannun shi yana yi shiru mukayi don shigowan nasa ga waya da yakeyi. Yana fadin yanzu dai me ya kawo wanan zancen nasan zainab nasan abinda zata iya mami don haka ban yarda da wanan zancen ba. Na fada maku ban son irin wanan zancen akan yarinyar nan matatace fa zainab don haka yan uwanta nada daman zuwa dubata duk lokacin da sukaga dama. A hasale yake magana don ranshi daya baci kan abinda mami din ta fada mashi ya karasa zancen da fadin bana son irin hakan . Wanan dalilin yasa bana son zuwan su nan din tun farko don bana son irin abinda naga anayi din nan gaskiya. Shiru yayi yana sauraren su kafin muga ya kashe wayan ya tura a aljihun rigan shi ta gaba ya juyo yana fadin meya faru ne da kuka je gaida mami dazun. Nima da mamaki nace wani abin kuma akace munyi da mukaje ya ja tsuki tare da fadin yanzu mami ta kirani tana fadin wai naja maki kunne kan abinda taga kina son yi mata yanzu. Ni din bana fatan ranan da zanwa wani babba rashin kunya ko wani abinda bai dace ba don nasan darajan iyayyena da manya na tun kan nakai haka. Nasan neman bakine kawai sukeyi kan hakan yasa na dauki matakin da ya dace a yanzu kan hakan. Indai nice su bar bata lokacin su ai na fada ina kawar da kaina gefe don raina da yake a bace. Ya juya ya fita sai lokacin Sa,adatu ke fadin amma matar nan bata da hali ashe har me akayi bayan sune suke gasa muna magana ba a kula su ba. Ni yau da nice da sun san suna sake min magana don wallahi ba zan kyale suba su dinga daukana kaskantata koda yaushe bayan Allah ya daukakani a cikin su su nuna min bakin ciki. Haka kawai zasu azawa mutum tsana da kiyayya don kawai hassada da bakin ciki irin na dan adam me suka rasa a rayuwan su da zasu kyashe da baiwan da Allah yai maki yanzu. Da nace daku kada mu tafi ai zaku ga kamar banson zuwan kune gidan amma yanzu da kuka gane wa idon ku komai ko na fada nan gaba zaku yarda dani. Ai itama tana da yara mata a gaban ta bata san inda Allah zai jefa rayuwan su ba nan gaba shi tallaka ba abin rainawa bane sam a duniya. Ranan sa,adatu tayi fada har ta gaji ta kyale don kanta nidai ba wanan ne a gabana ba don inda sabo na saba da halin mami da yaranta tun kan na auri danta a baya. Fadila ko cewa tayi idan bata so ai sai ta dawo da tsaraban karshen kiyayya ke nan ai da zata nuna min sa,adatu tace shine ai. Sai na dauka zasu dawo da tsaraban da muka kai na sa,adatu din sai gashi naji shiru banga an dawo dashi ba har tsawon kwanaki shima bai kara zancen ba. Sai dai bai kara zancen mami din ko wani na gidan su ba a gaban mu sai mazan ne kan shigo su dubamu jefi jefi zamu gaisa a cikin mutunci dasu. Nakan yi mamaki sosai yadda mami wai ta manta da komai na halin yaya take kokarin daukan laifi ta dora min koda yaushe sam bata kokarin maganan kan zancen halaiyar nasa balle a san mafita a kan dan nata. A kan wanan tunanen na tsaya a zuciyana cewa duk ranan da wani zance ya kara hada mu zan fito fili in fada mata hakan don tasan dan da take min kyashin zama dashi fa ba cikakken namiji yake kamar kowa ba. Sai dai me kuma a bangaren shi yaya Jafar din gaskiya yanzu yana jefa min wasi wasin akan shi ko da yaushe. Don a gaskiya yana tsayuwan sosai akaina kan yadda mami din take kokarin nuna min zai tsaya ko a gaban kowa ya nuna shi bai yarda da hakan ba sam wanan ya kawo saukin wasu halaiyan da mami din ta dauko nuna min. Wasa wasa saida sa,adatu ta shafe sati da kwanaki a wurin mu kafin ya shirya zancen zuwa gidan mu a lokacin. Nayi mamakin irin tsaraban daya shiryawa tafiyan mu din da zan kaiwa iyayyena da yan uwa a gida. Ga kuma kudi daya ban don kawai wanan tafiyan da har na rasa me zanyi dasu idan naje gida din don yawan su. Lalai ka bar wanda yafika da wayaushi da hikima a kanka don sai Allah zai iya kwato ka gareshi gaskiya . Don nikan yaya Jafar ya nuna min ya fini hikima da wayau tare da sanin duniya a yadda yake nuna min kamar babu gobe a kan mu wurin kulawa. Saidai hakan bai hanani matawa da irin zaman da mukeyi dashi ba duk da yana rudina da abin duniyan da yake gani zai iya matar dani ga komai dake tsakanin din dashi na basajan da yakeyi wa mutane dani. Wanda ya samu hakan ne ta dalilin hakkurina da zurfi ciki da Allah yai min wanda sam ban nunawa mutane sai idan kana da kula sosai zaka iya gane hakan. Don ko zuwan sa,adatu wuri mu ban yarda ta fahinci irin rayuwan da mukeyi dashi din ba don yawan shakuwan dake tsakanin mu dashi zaka dauka wani zamane najin dadi akeyi tunda ba a daki daya nake kwana dasu ba. Muka dauki hanyan garin mu a safiyan tafiyan cike da dauki da ka,idan zamuyi sati daya a gida mu dawo Abuja lokacin. Na dauki duk wani abinda nake bukata har takarduna da bazan iya bari su a yanzu ba a matsayin riban da naci a zama gidan yaya jafar din danayi dashi. Tafiyan mota masu lafiya karfe biyu da yan kai muna cikin gidan mu da mukai masu zuwan bazata a ranan do ba wanda yasan da zuwan mu a ranan sak ganin mu sukayi kawai ana muna sannu da zuwa. ZAINAB IDRIS MAKAWA HASBUNALLAHU WANI IMAL WAKEEL YA HAIYYU YA KAIYUMU BINRAHAMATIKA YA ASTAGIS, , , , BARKAN MU DA SHAN RUWA UBANGIJI ALLAH YA KARBA MUNA IBADUN MU YASA MUNA CIKIN YANTTANTUN BAYIN SA YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YA GAFARATAWA MAGABATAN MU YASA MU GAMA DA DUNIYA YA TSARE MUNA ZURI,AN MU DAGA FITUNTUNUN DUNIYA ALLAHUMA AMIN, , , , Yan uwa nayi rashin kanwar mahaifiyata hjy hazeena Ahmed dake aure a garin zuru matar Ahmed jolly provose na yauri. Allah ya karbi ranta bayan gajeren jinya datayi anshan ruwa lafiya da ita ranan asabar ciwon kai da ulcer yayi sanadiyan barin ta duniya a ranan ta rasu tabar yara biyu a duniya da fatan zakuyi mata addu,a irin na addinin musulcin nagode. Ba wanda yasan da zuwan mu ranan sai gani mu akayi mota ta tsaya da baki a kofan gidan mu idon mutane dake shawagi a lokacin ya dawo gare mu. Sai ganin Sa,adatu data fito farko daga motan ya dawo da hankalin su sanin cewa bakin gidan mune wanan. Saida na dan dade ban fito a motar ba ina daukan jakkata da sauram kayan dana rike a hannuna kafin na zuru kafata farare da suka canza dan samun daula a yanzu waje. Kafin gaba daya na fito daga cikin motan nida sadiya kusan lokaci guda muka fito daga motan kallo ya koma garemu nan kowa ke fadin albarkacin bakin shi a kan mu. Don wasu na tambayan ina sa,adatu ta samo turawa wasu na fadin yartane da yar uwanta da akace suna turai zaune an sayar dasu ga wani mai kudi sai kudi yake turowa iyayyen su ba a san ko suna raye ba daga cikin irin maganganun da Lantana ke yadawa a garin game damu. Na juya ina magana da driver kafin na juyo na fuskanci shagon tsoho baba iro wanda na bari ds kaya cike a ciki a baya inda mafi yawan mazan unguwan mu ke zama da can amma yanzu banga kayan ba . Ba kuma jama,a da yawa a wurin basu fi su biyar zaune wurin ba a ranan na dan daga masu hannu tare da fadin baba iro mun sameku lafiya ? Da sauri suke amsa min tare da fadin cewan wani a cikin su kungaji aina fada maku itace don bata da girman kai kaf a cikin su. Nidai na shige ina jin su ban tsaya kula su ba don maganan da suke fadi a lokacin game damu din. Sa,adatu ce a gaba muna bayan ta muka shiga da sallama Lantana na wanki a part din ta ta dago kai don ganin wanda ya shigo don sai ka shiga ta cikin tsohon part din mu zaka shiga kofan da zai sadaka dana innan mu a yanzu tunda basu bude kofan su na baya da aikai masi Abban mu ya hana hakan duk cikin dokan lantana a lokacin. Wanda ba don komai tayi hakan ba sai don duk wanda zai shigo wurin inna mu tana gani da kuma abinda za a shigo gidan dashi din. Sa,adatu bata tsaya bin ta nata ba duk da ta dago tana muna kalon mamakin data kasa boyeshi a lokacin a fuskanta don zaka gane a rude take da gani mu din. Wurinta na nufa da yar fara,a a fuskana ina fadin anty Lantana mun sameku lafiya tunda ita ta kasa magana sai idon data waro a bude a lokacin. Can kamar a firgice take fadin ai Abu kune tafe ashe sannun ku da zuwa a yadda ta tareni wanan karon naji mamaki matuka tankar ba Lantana bace. Na duka ina daukan yarta dake zaune tana kuka ga yarinyar ko wanka safe ba ai mata ba sai tsamin dauda da ke fita a jikin ta . Uwar ke fadin kada ta bata maki kaya Abu fitina take ji dashi halinta ke nan kukan banza ko yaushe. Bayan na dauki yarinyar na juyo ina fadin mun sameku lafiya ya bayan rabo cikin kame kame har lokacin take fadin ahe zaku zo yau bankoji ana fada ba. Nace ba wanda yasan da zuwan mu a yau din shiyasa ina Asabe da cewa kakan mu tana wurin ta ta ban amsa sai bina da kallon mamaki da takeyi. Ihun kanne da suka fito daga part din innan mune ya dauke muna hankali duk suka zo suka kankame muna a jiki nida sadiya dake makale dani duk inda na saka kafata. Lah yaya kika dauki wanan mai dattin haka ta bata maki jiki kanwata ta fada a cikin gatse don lantana taji haushi. An dauke ta din ai ita ba irin ku bace da kuke raba daya biyu a gidan nan an dai ji din a ajeta kada ta bata mata jiki. Ban tsaya ta kansu ba don zasu iya rikidiwa a wurin nake gani don haka na nufi part din asabe kakan mu ina tambayan su hanyan part din. A wurin asabe din sun tsaya suna wagala tsohuwar da tsokana wai mu din bakin turawane mun zo muyi mata alluran riga kafin tsufa ne. Ita kuma ta yarda da maganan su ta shiga yin bare bare ban taba riga kafi ba tun zamanin shagari da akai muna lamba a hannu ina lafiya sai yanzu za a zo min wani allura can. Asabe wai baki gani ni bane Abuce fa na fada ina kallon ta ina murmushi tace tana kallo a cikin mamaki. Abu dai Abun dana sani sai kawai ta fashe da kuka tana fadin hakan ta rungumeni tana fadin. Abu ashe zan ganki kafin na mutu Allah na godema da ka nuna min yaran nan sun dawo garemu lafiya. Ana ta fadin mun sayar daku ga mutumin da bamu sani ba don munga kudi ya rude mu sai gashi mutumin arziki da alherin sa yana ta turo muna da abin arziki a gidan nan kai da kai. Sai da muka dan dade a part din na asabe tana faman bamu dariya kafi mu taso zuwa part din innan mu har lokacin yaran lantana suna biye damu a baya har lokacin. Asamau kanwata ta juyo cikin hattara tana fadin ku kuma ina zaku haka kuna wani bin mu a baya ? Da sauri na juyo ina fadin haba asma,u ki daina hattaran su haka mana jin muryan Lantana mukayi daga bayan mu tana dauke da ruwan pure water da ta sayo muna tana fadin. Haka suke masu ai komai bakin cikin ku kuwa sai kun gansu a cikin gidan nan wa yanda sukai gadon mugun abu a zuciya. Duk da zancen nata ya dakeni a zuciya don nasan gun innan mu take nufin sun gado bakin halin ta manta da nata halin ita garesu. Ko taga yadda na danyi da fuskane sai cewa tayi ga ruwa mai sanyi kusha na juya wurin asamu din ina fadin karba an gode anty lantana. A waje na samu innan mu bakin baranda tana jiran shigowan mu da sauri na karasa jikin inna din sai hawaye suka zubo min lokaci guda don murna. Sa,adatu na shiga part din mu take fadin inna bani makulin kofan nan na baya a bude a shigo da kaya ta mika mata a daidai lokacin ne aka fara shigo da kayan da muka zu dashi din na tsaraba da ya sayo muna. Yayin da lantana ta koma ta kasa ta tsare a kofanta taga an shigo da abinda muka zowa inna dashi gidan zuwan mu. Drivers din basu tsaya ba kamar yadda ya umurce su da sun sauke mu su juyo da mota daya zasu bar daya a gurina a nan don zirga zirgan mu a garin. Haka yasa suna gama sauke kayan sukai muna sallama duk da nasan ya sallamesu hakan bai hana na kara masu alheri ba da zasu tafi. Falon na inna ya hargitse da hayaniya lokaci guda kowa sai fadin albarkacin bakin sa yakeyi a lokacin kan mu. Gyaran muryan da Abba yayi yasa kowa natsuwa a falon nan aka shiga gaida shi da dawowa gida yana amsawa sadiya ce ta taso ta rungume shi. Farin cikin Abba bai boyu ba ga ganin yadda muka sauya gaba dayan mu yake fadin wai sadiya ce wanan ko yar gidan gwaunan jahan nan ? Duk aka kwashe da dariya a falon sai lokacin na fito daga cikin daki ina fadin Abba sannu da dawowa ya washe baki don gani na yana fadin a, a Abu kune haka tafe ? Yaya shi maigidan naki da mahaifiyar shi tare da yan uwan shi shine tambayan Abba a gareni cikin nuna jin dadi da rikon da suke min a can. Allah sarki ABU CIKIN DUHU SIRRINE yanzu shi Abba yana tunanen zaman mutunci muke dasu a baki daya har nayi wanannsauyin da yake gani a tare dani a yanzu. Muryan Abban ne yake saka masu albarka kan kokarin da sukeyi damu a can hakan yana fadin wa yan nan mutanen sai godiya kawai Asiya. Da cewan innan mu ya fadi sunan ta kai tsaye don jin dadin abinda idon shi ya gane mashi bai san na badinin dake a boye ba a lokacin. An dan taba hira kafin ya mike don fita yana fadin bari je a nemo abinda za ai masu kafin yamma yayi ya fita. Har kwana biyu ina gida iyakata na fito daga part din mu zuwa wurin Asabe da lantana mu gaisa in dawo dakin mu bazan kara fita ba sai kuma washe gari. A rana ta uku da zuwan mune na shirya zuwa gidan su maizube don mu gaida su tunda mun saba sosai yanzu dan zaman mu da ita a abuja kafin mu koma chaina akwai shakuwa sosai a tsakanin mu da ita yanzu don lokaci lokaci muna waya dasu. Don idan nabi ta mutanen dake shigowa ba zan fita zuwa ko ina ba garin nan don tsaraban da ina ta zauna ta rabawa mutane unguwa da yan uwa yasa suke shigowa gaishe mu. Cikin wani dinkin yan mali na shdda marron colour dinkin har gwiwa yakai min ga farin lace da akai mai kwaliya dashi duk jikin kayan. Duk da ba dadin daura zanin nake ji a yanzu ba haka dai na daure na daura don sanin gidan da zan tafi wurin malam ne mu gaisa amma da abinda zai kaini kuma a kasan zuciyana. Mun fito a cikin shiri na tsaya da inna muna magana take fadin idan mun fito mu gangara mu gaida wasu yan uwanta nace to inna. Ni da sa,adatu ne a gaban motan tana nuna min wasu sabbin gina har na dauki hanyar da zai kaimu gidan malam din. Muk tsaya a kofan gidan malam din da mota na bude muka fito suka kwaso kayan muka shiga ciki. Farko munci karo da kishiyar su wace itace amarya a gidan tana ganin mu take fadin shike nan ma yaya ga wace zamu gaidawa anjima tazo har gida. Nan suka fara fitowa suna muna sannu da zuwa muna amsawa kafin mu zube a dakin maizube ana sabom gaisawa da yaushe rabo ? Munyi hira sosai dasu kafin kafin su watse suh bar daki ya rage sai mu da ita take tambayana ya bayan rabo ? Na danyi murmushi kafin nace wallahi maizube sai alheri saidai har yanzu muna nan kamar yadda kika sani. Ta dafe kirji tana fadin ban fahince ki ba zainab kina nufin har yanzu ba wani abu a tsakanin ku dashi ko me ? Kallon sa,adatu dake zaune nayi sai na kawar da kai da sauri ta gyara zancen ta da fadin har yanzu ace ba shiri dake da yan uwan shi haka ? Sa,adatu ta cabe da fadin wallahi maizube nima shedane kan hakan dan zuwan nan da nayi kwana biyu sai dana sheda hakan. Nan ta shiga ba maizube labarin abinda ya faru tsakanin mu da mami a gidan ta ranan tace ikon Allah wanan matar da karfin hali take ashe. Zamani na abinda dan ka ya kwaso har idan baida illa akaima sai ka ruguma da hannu biyu tunda ba Allah ya hana hakan ba. Saidai idan da illa ga abin zaka nuna kinsa gareshi har sai ya gane abinda kake nufi da hakan. Amma wanan kamar tana jayayya da ikon Allahne hakan shiyasa nake son na bar masu gidan har danta na fada a sanyayye ina dukar da kai kasa duk suka kaleni. Ki bar mata danta anty ai sai taji dadin hakan tayi nasara ke nan a kanki wallahi ke suka samu sukewa hakan da nice da duk sun gane kuren su har wa yan nan yan matan gidan nata masu yiwa mutane kallon raini din. Amma kice zaki bar mata danta dama ai haka take so ita ki barshi din tunda dama ba zaman ku a tare take so ba dashi. Tana fadin hakan ta mike tsaye tare da fadin ni barin kewaya kinji fitsari ya cika min mara tun dazun wallahi ta fita daga dakin. Maizube ta kalleni tana fadin amma yanzu kun daidaita da mijin naki a tsakanin ku nan ma kaina iya kada mata alaman a,a takaice na dan fada mata abinda zan iya don ta fahinceni. Hankalin maizube yai matukar tashi a lokacin sai maimaita cewa takai har wanan lokacin kana zaune da mutum kamar dutse ba abinda ke gudana a tsakanin ku haka ? Gaskiya wanan ba abinda za a kyaleki bane zainabu don a gaskiya kina cutuwa da yawa sai dai dole ki san yadda zaki bulowa mutane da maganan a yanzu. Maizube wanan ba wani abu bane illa ranshi daya fita ga mata sai yan uwan shi maza yake bi shine matsalanshi kawai. Jam jam wa,iyazu billahi wanan abin da muke ji dauri a jakkar magori shine ya kawo garemu yanzu ? Shigowan sa,adatu dakin yasa mukai shiru kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi cikin mu a lokacin. Anty muje kinsan ba nan kawai zamu tsaya ba gashi malam bai dawo gida ba har yanzu. Zan dawo na yini a nan na fada ina mikewa don nasan maizube din zata fahinci mai nake nufi da hakan dana fada ai. Mukai masu sallama muka fito daga gidan zuwa gidajen da inna ta umurce mu da mu tafi idan mun fito gidan malam din har gidan mahaifiyar Lantana nasa muka je mukai mata alheri bayan mun gaida ita sa,adatu ta cika fam dani kan zuwan mu gidan. Sai bayan la,asar muka dawo gida a gajiye mun samu wai anyi fada da innan mu da anty lantana wai an fake da zuwan mu Abban mu yana shiga lungun inna ko wani lokaci yanzu. Wanan maganan shi ya kawo fitina har suka kaure da fada a tsakanin su don kishiya bata raina abin fada kullun. Ana hakane muka shigo gidan a daidai lokacin da Lantana ke fadin mijin yae taki dake yankan kai yana turo maku kudin jini kuna kashewa keda ubansu. Muka karasa shigowa muka samu ko wace na tsaye cirko cirko rayukan su a bace sunyi shiru don ganin mu. Kamar ba zan tanka masu ba har na dan wuce na juyo ina fadin haba innan hakan ba girman ki bane yanzu ai shi kadai na fada na shige part din inna abina. Saidai ina tunanen a raina wanan maganan ke nan ina ga sun san gaskiyan ko waye mijina a gaba me Lantana zata fadawa innan mu ke nan ? Dakuwan da muka dawo dashi daga gidan wata yar uwan inna na bude ina rabawa kannen mu kan na fara ci na dibarwa yayan lantana nasu akai masu. Nan sa,adatu ta hau fada ba za a basu ba ai yanzu muna ji ta gama zagin innan mu da mijina tana masa kazafin da ba shi ba a tsakar gida. Nace naki ne ko nawa sa,adatu duk me tayi don kanta ai itama ta haifa kuma zasu girma ai taji idan da dadi abinda takeyi din. Inna ta shigo nake mata maganan don Allah ta bar biyewa haukan lantana suna zama daya haka a gaban mu. Dama shi me son fada maka magana yakan jaka fadane ya samu kafan fada ma magana a cikin fada din. Yar nan bar wanan matar mara hali ko yaushe ita burin ta shine taga ba, a zauna lafiya ba a gidan nan. Nan dai na bawa innan mu hakkuri aka bar zancen kowa ranshi ba dadi ga abinda ya faru din ranan. Sai bayan kwana biyu ina kuryan dakin inna kwance da dare bayan kowa yayi barci inna ta sameni ta zauna a bakin gado inda nake kwance. Na dago da sauri ganin ta shigo ta zauna a wanan lokacin nasan magana ya kawo ta wurina ke nan. Yar baba meye damuwan ki da har kika kasa fada min kike shiti yankewa kanki hukuncin da bai dace ba badon sa,adatu taji kudirin ki ba kan hakan. Wani abu ta fada maki nayi inna na tambaya cikin mamaki don na manta da munyi wanan zancen a gabanta. Hukuncin da kike shirin dauka don kawai mahaifiyar mutymin nan bata kaunarki da danta har yanzu. Wani dan murmushi na sake a fuskana kafin na fara silalo da hawayen takaici na dago kai na kalli inna cikin karfin hali na toshe bakina ina fadin . Inna ba don mahaifiyar shi nake son rabuwa dashi ba don akidarshi ce daya kaucewa addini nake son barin shi. Wani ka)on mamaki inna tayi min kafin tace dani kin ko san abinda kike fada yar nan mutum kamili kamar wanan zakiwa sheri don kawai bakya son shi ko me zaki mai wanan kazafin ? Kallon ina nayi nan dan lokaci kafin na girgiza kai ina hade wani kololon bakin ciki daya tokare min makogorona dama nasan za a rina idan na fito masu da wanan zancen ai. ZAINAB IDRIS MAKAWA YA ALLAH ALLAH KA JIKAN MAGABATAN MU KA GAFARTA MASU KURAKUREN SU KASA ALJANNAN MAKOMAR MUSULMAI YASA ALJANNA MAKUMAR WANDA YA FURTA KAMAL LA,ILLAH HA,ILLAH MOHAMMADAN RASULULILAH, , , , , , , YAN UWA MUSULMAI YA SHAGALGULAN SALLAH DA BANKWANA DA RAMADANA DA FATAN RAMADAN DIN BANA YAZO DA KARA MUNA IMANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , Ganin da inna tayi na kasa magana sai hawaye ke zuba a fuskana sai kuma ta shiga damuwa lokaci guda ta rude. Hankalinta ya tashi ta koma fadin ki rufa muna asiri ki rufa min idan da wani abu ki fada min mu san inda zamu bullo ma ko meye matsalan ki da mijin ki yar nan ? Da kyar na iya budan bakina da yai min nauyi ina fadin inna da matsala a cikin auren mu babba sai dai idan kince na koma mu zauna a hakan zan koma don ke . Menene matsalan dake akwai tsakanin ki dashi inna ta sake tambaya tana kallona don son jin mezan fada. Bakina yai nauyi da abinda zan fadawa innan sai kawai naja filo na mayar da kaina tare da sake wani irin kuka lokaci guda mai ban tausayi. In don matsalan kice da uwar mijin ki wanan ba kanki bane farau ai naji muryan innan na fadi,don da wayau ki kinga irin zaman da mukayi da kakar ku a gidan nan. Yanzu fa da nayi hakkuri komai ya wuce sai abinda ba,a rasa ba tunda yanzu ta gane gaskiya ita da kanta. Cikin kukan da nake nayi karfin halin fadi inna matsala ba irin taki bace tawa matsalan daban yake dana ko wace mace inna. Subbahanallahi wanan maganan babba ke nan ta fada sai kuma tayi shiru na wani dan lokaci can naji ta mike zata bar dakin . Ta kai kofa ta juyo tana fadin kiyi tunane kafin ki san abinda zaki fadawa mahaifin ku don kin san shi kin san halin sa ta fita. Ban daina kuka ba sai ma karawa da nayi kan wanda nakeyi da farko don nasan za a rina kan hakan. Don ba kowane zai yarda da abinda zan fada ba gashi ma ban fada din ba a fahinceni asan akwai matsala akan hakan dana ce. Haka na kwana ranan tare da dinbin tunane a raina ina nemawa kaina mafita da naga zai dace dani. Washe gari koda muka tashi inna ta dauki zafi dani sosai ko gaisuwan da nayi mata da kyar ta iya amsa min shi ba cikin dadin rai ba. Ganin haka yasa nima na nisance ta na koma kuryan daki ban zauna a falo ba yadda muka saba gaba dayan mu. Kanne na sai shigowa dakin suke suna tambaya ko lafiya nake na zauna a dakin har tsawon kwana biyu muna haka da inna ba wani sakewa a tsakanin mu ni da ita. Ranan na uku na shirya nake fadin zan je naga maizube tayi min sai mun dawo wanan tafiyan ban yarda na tafi da kowa ba sai karamar kanwa daya dana dauka muka fita tare da ita. Nayi sa,a na samu malam a gida muka gaisa da matan shi maizube tayi min jegora zuwa wurin malam din. Ya tareni sosai yana saka min albarka tare da kara ban hakkuri irin na manya kafin maizube tace dashi barin baku wuri ku gana ayi yaushe rabo ko ta fada cikin hikima . Nace ba sai kin fita ba ai tunda kin san komai tun farko kamar dai yadda kika barmu har yanzu hakan muke dashi. Ta amsa da fadin eh malam gaskiya kamar yadda dai na fara fada mane zaman nasu ba dadi sai hakkuri. Ga kuma fannin uwar mijin nata shima dai babu dadi har yanzun din don kiyayyan nata da ita yana nan bai gushe ba. Nan malam din ya danyi murmushi yana fadin halin ku mata sai ku wallahi mace ko tayi shekaru kamar me bata taba canza halinta na mata. Ita bata san ke din alheri bace a garesu ke maizube na fada na kara fada maki tun farkon auren yarinyar nan ita din alheri ne a cikin su. Duk sanda zanyi istihara akan matsalan su ni haske nake gani a lamarin nan banga wani abin aibu ba a cikin auren ta da yaron nan . Sai dai dan matsala na rayuwa da ba a rasa ba can da ake samu gun ko wasu maurata da suke tare na rayuwa. Dakin yayi tsit babu mai motsi a tsakanin mu sai can na gyara zama ina sharce zufan dake zubo min a goshina lokaci guda jin abinda malam din ya fada. A raina ina fadin ta yaya malam zai fadi hakan har in ance malamai suna ganin abinda ke faruwa ga mutum . Ni tayaya malam zai kira min wani alheri bayan halin da nake ciki muryan malam din ne ya dawo dani daga tunanen dana tafi yana fadin. Maizube ki bamu wuri in kara ganawa da ita akwai abinda nake son ji a bakin ta don naga akwai nauyi a tare da ita har yanzu. Take maizube ta mike don bin umurnin mijin nata tana fadin nima dai haka naga yafi don matsalan kawar tawa babba ne don gaskiya malam sai anyi bicike sosai ga matsalan nan. Ace mace na zaune gidan miji har tsawon wanan shekarun yana kallon ta photo malam ba ko wace mace bace zata iya wanan hakkurin haka. Hannu malam din ya dagawa mai zube din alaman ya isa tare da fadin ke kuma yanzu zaki zama babban banza ko makin ki yabe ta kan hakan sai kuma ki tunzura ta. Malam abinne keda daure kai wallahi koma meye Allah na maganin sa ai tana kokari tunda har takai haka dashi yanzu riban ta ya rage ta girba da yarda ubangiji ya fada yana daukan tasbahan dake aje a gefen shi. Maizube ta sa kai ta fita tana fadin Allah yasa haka malam muma ai hakan muke fata wallahi. Ki daure kinji malam ya fada bayan fitan maizube dakin yana fadin koma meye matsalan da yarda Allah saukin shi na zuwa. Kinyi kaifin basiran zama hakan ansani an takura da yawa idan hakan gaskiyane sai na tare shi da fadin. Malam ba zan mashi kazafi ba ko kadan kalar rayuwan shi shi daban ne dana sauran mutane don da bakin shi yasha fada min shida mace sai zaman mutunci da yan uwan taka a tsakanin su. Malam ya kada kai nace kuma ko acan da muke ya sha ya fada a gabana da cewa nidin kanwarshi ce ta jini. Jam malam ya fada da sauri a cikin mamaki kafin yaci gaba da fadin dole akwai abinda ke damun shi a rayuwa daya kawo hakan. Malam ba wani abu bane illa masifan daya fada rayuwan shi a ciki na bashi amsa daga inda nake zaune a gefen shi. Ya dago kai tare da tambayana ko kin san duk wani halaiya nasa zuwa yanzu bana son ki boye min komai da kika sani game dashi . Ki dauka nan kamar yadda zaki sake da iyayyen ki ki bani amsan komai a bayane ta yadda zamu san mafita akan lamarin. Dan dukar dakai nayi na dan wani lokaci kafin na dago na fara fadawa malam din komai dana sani a game dashi. Har maganin dana amso mashi a wurin kakan maya da yadda mukayi dashi a lokacin har abinda ya fada min zuwan mu nan ban boyewa malam din komai ba na fada mai. Sai dai kafin in gama fada mai idanuna sun cika da hawaye a lokacin haka na karasa a cikin kuka da bacin rai. Shiko malam babu abinda yake fadi sai wa,iyazu billahi har na kai karshe yana girgiza kai cikin mamakin abinda nake fada mai. Dan shirune ya biyo a dakin kafin inji muryan shi yana fadin Allah kai muna tsari da sherin zamanin nan. Sai dai ko akwai wanda kika fadawa a cikin yan uwan ki ko iyayyen ki wanan zancen da kika zo ? Kaina girgiza mai kafin na iya budan bakina da kyat nace dashi a, a malam ko kanwata da muke tare a can bata san da zancen nan ba. Kin kyauta kwarai da kina karaman na har kika iya rikewa mijin ki siri irin wanan nace to amma malam. Sai dai yan uwan haihuwan shi da mahaifiyar shi sun sani suma din banice na fada masu ba halin yau da gobe ne yasa suka gane hakan. Amma mahaifiyar suce nake ganin bata yarda da zancen ba duk da taga makamancin hakan tare dashi amma laifina take gani na ma danta sheri. Malam ya tare da fadin mata ke nan ga gaskiya sai su baude soboda son zuciya da diya da Allah ya dora masu. Babu uwar da zata yarda da sherin danta idan bata gani da idon ta ba saidai dan wani haka kuke mata wurin son kai. Ita yanzu ba abin ta gode maki bane a irin kokarin da kikayiwa rayuwan su da badon Allah ya taimaka kin hadu da wanan kawar data taimaka maki ba wa yasan inda abin zai tsaya mai tunda masiface wanan Allah ya jerabi rayuwan shi dashi. Nayi shiru shima din dai shirun yayi har na dan wani lokaci kafin na dago kai ina fadin ni yanzu malam so nake kawai a rabani dashi ba zan iya wanan zaman dashi ba. Da sauri ya dago kai ya tsura min ido kafin ya sake murmushi yana fadin kayya yaro dai yarone ashe ? Ke abu baki tashi rabuwa dashi ba sai yanzu da tafiya ta kawo ga gangara a tsakanin ku kada ki zoje ladan ki wurin gajin hakkuri irin na dan adam. Ai tunda kika ji ya fada da bakin shi ya daina haka din ne ya daina sai dai yanzu mu nemo mafita ga zancen kawai. Yanzu abinda nake so dake ki ban kwana biyu nayi ustihara naga inda bakin zaren yake don mu san daga inda zamu fara aiki a kai. Ina fatan dai kina da sauran kwanaki kafin ki koma ko ya tambaya yana kallona don jin abinda zan fada. Sai dana gyara nace dashi malam akwai don kwana goma ya ban nayi a nan yau muna da kwana shidda da zuwa garin nan. Yace masha Allah kafin sauran kwanakin su cika mun san dan abinda za a gwada a gani ko Allah zaisa mu dace da hakan . Amma ba zan ce dake komai ba a yanzu sai idan mun duba mun gani duk abinda ya dace sai ayi sai ki matsa da addu,a a naki bangaren don addu,an ki yana da tasiri a gareshi sosai. Mun dan dade yana min yan nasihohi su na manya kafin in fito in masu sallama na dawo gida. A gidan kuma bayan barina gida inna da sa,adatu sun tasa sadiya a gaba suna mata tambaya. Sai fasin take bamu da matsalan komai da yaya din nan take kara basu labarin irin rayuwan da mukeyi a can har zuwa lokacin dana dawo gida . Gaida inna nayi na shige dakina kai tsaye ban tsaya a falon da suke zaune ba don ban jin dadin yanayina a lokacin. Sa,adatuce ta dauko abincin ta shigo dashi dakin ta samu na ina rage kayan jikina don zafin daya dameni tunda na faita. Ga abincin ki anty ta fada na dan kallo ta ina fadin nagode zan kewaya nayi alwala kafin naci don naga lokacin azahar ya gabato. Kodana idar da sallah ban tsaya bin ta abinci ba na koma saman gado na lafe ina faman tunanen zancen mu da malam da muka fara. Har inna ta shigo ta sameni a hakan take fadin au abincin ma da aka kawo maki bakici ke nan ko ? Na dan dago a yadda nake kwance nace zanci anjima inna ta juya tana neman abinda zata dauka a dakin daya shigo da ita. Zata fita take fadin ya zancen ku na zuwa fambeguwa da kuyi wurin yar inna dake aure a can . Sai lokacin nadan dago da kyau ina fadin zamu tafi inna akwai abinda nake jira na karba ne zuwa jibi sai mu tafi. Daga hakan tasa kai ta fice a dakin bata kara magana ba wanan zancen da mukayi da inna ne zuciyar ta ya bata taje wurin malam din koshi yasan irin matsalan da nake fuskanta tunda na kasa fada mata ita. Da yamma naji tana sallaman mu cewa ta unguwa wanda tun zuwa mu banga ta fita ba sai wanan ranan. Sai dai duk da hakan ban kawo komai a rai na ba kan hakan sai ta dawo da mukai mata nan kanne suka sameni a dakin muna hira duk da ba dadin hiran nake ji ba a lokacin. Taje wurin malam din sun gaisa take fada masa damuwan ta a kaina tare da yadda mukayi da ita din. Malam din yace koda baki zo ba a yau ni zan aika kizo ai don yarki na cikin gagarumin matsalan rayuwa da ko ke din nan mahaifiyar ta ba lalai bane ki iya daukan hakan. Sai dai ki godewa Allah da ya baki ya irin wanan a rayuwan ki don ita di abin alfaharine ga kowa idan ya samu yaro irin hakan. A matsayin ki na uwa a gareta ke ya dace ta fadawa wanan damuwan nata ki san irin matsalan da yarki ke ciki na rayuwa. Amma sai kika kasa yin hakan gareta kikai aikin jahilci baki tsaya kin san damuwar yar ki a gidan auren ta ba. Yau da ace ba yarki bane dakeda zurfin ciki da tunane wanan zancen ya fita a garin nan ke kanki da fita waje ya gagareki koda rdarene kuwa. Gaban inna dake faduwa ya kara bugawa sosai don jin abinda kanin mahaifin nata ya fada a kaina. Ta dago kai a cikin tsoro tana fadin malam ban san abin yakai girman haka ba na dauka irin shirmen yaran yanzu ne kawai take son ta aikata. Koma shirmene Asiya ai sai ki saurareta kafin ki balbale ta da fada ki kara tayar mata da hankali haka. Idan ma baki sani a yanzu yarinyar nan Abu tana bukatan taimakon mu akan rayuwan da takeyi a gidan mijin ta din matsalan ba karami matsala bane a yadda kike tunane. Na shiga ukku inna ta fada tana kyarma tare da fadin meye matsalan da yai girma haka malam ? Kin ga ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Allah zai muna mafita ga wanan zancen nan inna ta fara kyarma tana magiya ga malam din ya dan fada mata wani abu do hankalin ta ya tashi sosai. Na fada maki ki kwantar da hankalin ki ya zama dole ai ki san wani abin don ki taya ta da addu,a don ba zamu kyale yarinya ba ta zauna haka har tsawon shekarun nan babu abinda ya taba shiga tsakanin ta da miji na aure. Innalillahi wa inna alaihim raji,un malan matsalan da yar nan ke ciki ke nan ban sani ba kadan dai kikaji Asiya daga abubuwan dake gudana. Saidai abinda nike so dake wanan maganan yanzu ya tsaya iyamu don ko mahaifin ta ban son yaji wanan zancen yanzu sai in har abin ya gagare mu. To ya zama dole ya sani a lokacin don ba zamu yarda yarinya ta koma tana zama haka ba shekaru kurewa shigewa suke ga bawa. Malam nagode Allah ya bar zumunci inna ta fada dolene muyi maki Asiya don kema baki yarda mu ba ai, ko banza ai dole muyi maki tunda muna raye daku. Haka inna tayi sallama da malam din cikin tashin hankali ta dawo gida yanayin ta kawai zaka kalla ka san cewa tana cikin tashin hankali. Kallon juna mukayi nida sa,adatu sai sa,adatu din ta tashi ta bita zuwa cikin dakin sukai kus kus naga itama ta fito a cikin damuwa a fuskanta sai dai ta zauna ta dan wayen ce kawai. Tun wanan ranan inna ta koma rarashi na tana jana a jiki dama akwai akidar yar farko da takan nuna min wani lokaci don sunfi shakuwa da sa,adatu gaskiya sama da ni. A cikin hikima da dabara takan sameni a daki mu danyi hira tana dan jefo min zancen zaman mu wani nakan bata amsa wani ko na yi shiru kawai don amsan bai faduwa. Da haka har inna ta fahinci wani abu take dan ban hakkuri na daure in kara hakkuri don haka zama ya gada wani lokaci mata da hakkuri aka san su dama. A raina nakance wani hakkuri ba inna nawa kan yafi gaban yin hakkurin da kike nufi nayi. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA DA FATAN MUN WUNI LAFIYA ALLAH YA SADA MU DA AHERIN SA AMIN YA ALLAHU, , , , YAR UWA KADA KI MANTA NOVEL DIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA, , , , Sannu a hankali har inna ta fahinci irin zaman da nakeyi da ya jafar tun bayan auren mu dashi ba abinda ya taba shiga tsakanin mu har zuwa wanan lokacin. Kalman hakkuri kawai da ban baki yake fita daga bakin ta na kara hakkuri na dan lokaci kamar yadda malam ya fada. Na kancewa inna naji kawai amma amma a zuciyana ba haka abin yake ba din ni ba zancen gyara nake so a tsakani mu ba illa iyaka dai naga na barshi har abada. Kwana biyu ya cika a haka na shirya zuwa gidan malam din kamar yadda mukai alkawari dashi zanzo bayan gama binciken shi. Inda na samu ni yake jira na iso daman zai tafi wani unguwa shi bayan mun gaisa da iyalin malam din mun dan taba raha kamar yadda muka saba da iyalinshi idan mun shigo a matsayin su na matan kakan mu din. Na nufi wurin malam din ni kadai nabar kanne dana zo dasu tare dasu maizube suna hira a tsakar gida. Muka gaisa dashi yake tambayana lafiyan inna nace suna can lafiya ya dan dade yaja dan dube dube yana jawo ledoji a cikin kayan shi. Kafin ya dago kai yana fadin kamar yadda na fada maki zanyi istihara kafin nace wani abu sai idan na bincika naga abinda ke nan. To a gaskiya nayi din kuma naga akwai matsalan da duk kika fada ba karya a cikin sa ko kadan. Ya dago kai ya kalleni na dukar da kaina a cikin damu a lokacin da yake fadin sai dai abinda nake so dake yanzu na farko ki kwantar da hankalin ki . Komai yana bukatan natsu a cikin sa dolene mu bishi a sannu kafin mu kai ga nasara ga abinda muke nema. Bai fada maki karya ba kamar yadda yace maki ya daina ya daina wanan harkan din saidai kawai matsalan da karfin maganin nan da tsohuwar nan tabaki da yaso yai mai yawa a jikin shi saboda abin ya bugeshi sosai. Ki godewa Allah yar nan da Allah ya taimakeki ya hau dake kan masu bibiyan ki da sheri akan mijin naki. Mafarkin ki da kikeyi a baya ya baiyana a gareni yanzu na fahinci dalilin mafarkin naki akan wanda kike yawan gani ya shiga tsakanin ki da mijin ki a cikin mafalkin ki. Ba wani bane illa wanan harkan da sukeyi ne Allah ke son ya baina muna tun baya ba a gane hakan ba sai yanzu da lokacin da baiyanan yazo muna. Don haka ya zama dole ki daure ki kara jajircewa akan wanda kikeyi tun farko kada su ga kasawan ki ga hakan. Babban kokarin da zamuyi shine muga mun shawo kan matsalolin nasa a baki daya har in son samune ya rabu da abokan harkan nasa har abada. Saidai gaskiya wanan tsohuwar data baki magani tasan kanta a wirin aiki don tasan magani sosai. Don mawuyacin abune mutum ya iya daina wanan dabi,an haka kai tsaye ba tare da ansha wani wahala sosai ba dashi. Don abin nasa ya hade masa da yawa akwai sa hannun makiya dana muggan abokai a cikin lamarin shi . Shi yasa abubuwan suka taru sukai mai yawa a lokaci guda don Allah yayi yaron nada karfin arziki mai yawa a rayuwan shi dan ba haka akaso ya kasance ba. So akayi ga baki daya ya lalace a rayuwan shi tun farko an haska anga cigaban shi dana sauran yan uwan shi akwai rinjaye mai tazara a tsakanin shin da duk wani na family din su baki daya tun wanan lokacin aka jefa masa wani rayuwa na daban a cikin lamarin shi don ba haka mai sakon yaso ya kasance ba. Kuma an basa abin yacine tunda kurciyan shi na yarinta akaso ya soma lalacewa don mahaifinsa yana tsaye da lamarin yanyan sane abin bai samu tasiri sosai a jikin saba wanan lokacin sai bayan mutuwan mahaifin nasa ne abubuwan suka fara aiki a jikinsa yanzu. Gareku iyayyen zamani kalubali ne wanan zancen a gareku mu kula da wa yanda muke mu,amula dasu a rayuwan mu don wasu a fuskane kawai soyayyan su garemu. Baikai ciki ba yadda kike zaton kekaki bazaki iya cutawa dan wani ba wani nacan ya kyashewa naki yana kai masu hari a fakaice sai mu yawaita addua gun yayayen mu don nema masu kariya daga shedanun mutane kamar yadda malam ya fada mahaifin su jafar yana tsaye ga addua a gun yayan shi. Shine dalilin dayasa abubuwan jafar din sukai sanyi basu samu aiki a gareshi yadda maishi yaso ya gani ba. Ga kuma abokai dake canza rayuwan yaro lokaci guda ya zama dole garemu wanan zamanin musan dawa diyan mu suke mu,amula a kullun don kawaicewa fadawa halakan zamanin Allah ya tsare ya kare muna zuri,a amin. Har malam ya gama bayanin sa jikina ya mutu a lokacin ina tunanen waye zai jefosa haka da mugun abu don ya koma hakan. Don masu kishiya nake jin iri wanan kalamin na faruwa a tsakanin su idan a hadu da mai raunin imani. To amma gashi ita mami bata da kishiyan kuma hakan ya sameta ga zurian ta yanzu. Muryan malam ne ya dawo dani ga tunanen da nakeyi da yake fadin kinga akwai aiki babba a nan don sai mun wareware kulin zamu san aikin mu na kyau akansa. Na gyada kai kawai alaman eh malam don jikina ni lokacin ya gama mutuwa da zancen daya fada min din. Zaki iya turarara wanan hayakin ta yadda zai kai ga hancin sa ya shaka na kwana uku malam ya tambayeni. Na dago da kai da sauri a dan razane don sanin kwanan wasan don wancan karon da kakar maya ta ban magani yadda muka kwashe dashi. Malam bai tsaya jin ta bakina ba don ya fahinci irin tunanen da nakeyi a lokacin sai cewa yayi dani zaki iya mana sai kace ke din ba mace bane. Yana fadan hakan yake miko min maganin dake kulle a cikin wani dan kyale ja na karba kafin ya juya yana dauko wani a haka dai duk yai min bayanin ko wani maganin da amfanin sa gareshi. Nabar gidan malam a hanya wayan ya jafar ya shigo min na dauka da kyar bayan mun gaisa yake fada min yaso shigowa satin nan don mu dawo amma yafiya ya kamashi zai fita ba zai dade ba zai dawo sai yazo ya dauke mu mu dawo. Jin hakan take wani tunane yazo min a zuciyana don na gama yanke shawara a kansa ko yanzu. Do duk abinda zanyi karshe nice mai laifi a wurin mami ba zata ga hakan ba sai laufin da zata dora min da banji ban gani ba. Haka na dawo zuciyana cike da zargi iri iri a lokacin don ni abin har tsoro ya fara ban don mutum ba abin yarda bane ashe haka. Don ko waye lalai na jikin sune don yadda mami take kafa kafa da yayan ta nake gani ashe hakan bashi ya dace tayi kawai ba a rayuwan ta a kan yayanta. Don bayan sa ido irin wanan da takeyi ya zama dole kuma uwa ta dage da addu,a da neman tsari gun yayayen ta ashe . Koda ta hanyar yawan yin sadaka ko alheri da sunan yayanta Allah ya tsare mata su don sherin zamani. Amma da yake ita mami yanzu irin rayuwan turawa ne gareta duk ta mance da wanan a rayuwanta batayi sadaka ba zuwa garesu don hakan balle wani neman taimako gun malamai a kansu don abin yanzu saida hakan . Saidai kada mutum ya zure don gudun fadawa ga halakan ubangiji don yadda da irin abubuwan nan gaba daya yana juya kan mutum ya manta da Allah watarana. Sai mu kula mu dinga sadaka da sunan yayayen mu da yawaita alheri ga marayuwa da masu karamin karfin shine mafita. Washegari kawai na tashi ina fadawa inna zan tafi fambeguwa tayi mamakin hakan saidai bata hana mu zuwa ba sai ta fadawa Abban mu shima ya yarda. Da sa,adatu da sadiya mukai tafiyan inda Allah ya taimakeni shine mun tafi washe gari sai ga waya ana neman su sa,a datu makaranta nace su tafi tare da sadiya don naga bata sake jiki ba. Suna tafiya nima na tsiri tafiya kan zanje na duba wata kawata na dawo kafin su dawo haka na samu hanya na balle ba wanda yasan inda na nufa. Ni kaina ban san inda zan nufa ba na juyo zuwa kaduna kawai gidan wata kawata da mukai yayin zuwa makaranta a tare lokacin can dabaran zuwa ya fado min don su din gidan sune na kansu bana wani ba. Ban sha wani wahala ba sosai wurin gane gidan saidai itace da farko bata gane ni ba saida nayi mata kwatance da kyau tace ta ganoni ta rungumeni. Mun zauna ana yaushe rabo a nan take ban labarin ai mahaifin su ya rasu bayan rabuwan mu bada dadewa ba. Na tausaya masu sosai don ni kaina naga sauyi sosai a gidan maganane kawai ban yi ba tun shigowana. Gidan da yake da yawan arziki ga yan aiki da jama, a amma yanzu shiru babu kowa tun wajen gidan shara da tulin ganyen bishiya zasu tareka a waje shiyasa da farko harna zata ko ba kowa a gidan ne yanzu. Mun kai wani lokaci muna hira kafi mu ci abinci mu kwanta barci na kashe wayana gaba daya tun shigowana garin kaduna na jefa a jakana. Ya jafar ya kira layin nawa yafi a kirga da safe zuwa rana don hakane ya nemi layin Abban mu yake tambayana. Abban yake fadin bata fadama zasu ziyara nan fambeguwa wurin yan uwan mahaifiyarsu ba yace ok kila ta fada min na mantane ya kashe wayan bayan sunyi sallama da Abban yace masa bari ya samo lamban da za a samemu dashi a can. Abba ya shigo gida ranshi a bace yana wa innan mu fada kan zuwana wuri mijina bai sani ba gashi yanzu ya bugo waya yana tambayana. Itama inna hankalin ta ya tashi nan ta buga waya sai dai wayan baya shiga hankalin inna ya tashi take tambayan sadiya ko ba service a garin tace sun baro services a can lafiya kafin su dawo. Hankalin innan mu ya kara tashi gashi yarta di ba waya ke gareta ba balle su kira nata layin suji ko lafiya nake. Har dare inna na kokarin kiran layina shiru babu layin hankalinta kuma yaki kwanci da hakan har sadiya ta dawo daga zari,a ta samesu a hakana itama ta gwada layin nawa bai shiga. Sai cewa ake layin yana kashe idan sun kira sadiya dake gefe tace aiko anty mu bata kashe wayan ta haka idan dai ba wani matsala ne ya faru da wayan ba. Har washe gari basu sameni ba haka yasa sa,adatu fita ta samo layin wata yar garin data sani ta kira akan taje gidan ta duba in lafiya nake ta fada min na kunna wayana ya jafar nason magana dani. Basu akace wa kawar babu wata bakuwa a gidan wace suka zo duk sun wuce koda ta kira sa,adatu dare yayi lokacin don haka saidaf safe sa,adatu ta sameta take fadin abinda aka fada mata. Sai hankalin su ya tashi sosai nan inna hankalin ta ya kawo cewa akwai matsala ta bangarena ke nan lalai wanan abin da nayi yana da alaka da zance da yaya jafar di nan hankalin ta ya kara tashi sosai. Sai gashi ya jafar din ya kara kiran Abban sun gaisa yake tambaya ko na dawo dan layina baya shiga ana fadin layin yana rufe har lokacin. Mamaki ya kama Abba yake fadin bata kira kaba ke nan danace su sanar mata bayan sunyi sallama ne Abban ya shigo gida ya hau inna da fada ta inda yake shiga banan yake fita ba. Dole washe gari sa,adatu tayi asubancin zuwa fambeguwa da kanta ta duboni ko taji inda nace dasu zan tafi daga can don hankali su ya kwanta. Saidai tana zuwa din kamar ta karo tashin hankalime gare su don ta dawo da labarin ba wanda yasan inda na tafi sai innan mu ta fashe da kuka. Dole ba yadda za ayi aka fadawa Abban mu komai shima nan hankalin shi ya tashi ya fara fada inna cewa komai ya sameni itace don itace ta kirkiro da surfan aje gun yan uwanta ai. Daba haka ba ai da ina gida asirin su rufe yanzun me zasu fadawa mijina cewa nayi tafiya na bata ba a san inda nake ba ko me ? Daga shi sai inna da yan uwana ake kumbiya kumbiyan maganan a tsakanin su har karshe dai saida Asabe ta san da zancen itama hankalin ta ya tashi sosai. Inna taje gidan malam tana kuka take zayana masa komai malam din yai murmushi tare da fadin nasan za a rina don yarku na cikin wani hali wallahi. Sai dai kada ku damu sosai za a san abin da akayi ta dawo gida lafiya kada abin ya kai ko ina amma hankalin ta ne ya tashi sosai da mijin nata har mahaifiyar shi. Nan dai malam di yace za ayi rokon Allah duk inda na shige na dawo gida lafiya ba tare da wani abu ya faru dani ba insha Allahu. Abba kan ya saka inna a gaba har ya kai inna itama ta hasa ta mayar mashi da amsa a cikin zafin rai ta fadin shin malam kana ganin laifina a nan. Kai tunda yarka tazo garin nan ka taba zama da ita ta fada ma halin da take ciki a gidan auren ta daudai da rana daya malam a gidan nan. Abba yace owwoo yanzu kika fito mi a mutum sak watau duk abinda yar nan tayi da sanin kine Asiya boye min kawai kikeyi dama ? Tace wallahi bada sanina bane malam don babu uwar da zata koyawa yarta mugun abu haka tabar dakin mijin ta da mutane suke hangen tana a cikin daula ne ita. Saidai mu iyayyen mun kayi sakaci wani lokaci har abu ya girma ba tare da mun maida hankalin da halin da yaro ke ciki ba sai abu ya lalace. Shike nan Asiya kin sai komai dai da yarinyar nan tayi ke nan to wallahi bari kuji baku isa ku kunyatani ba a idon jama,a. Duk inda taje koma wani iya shege take ji dashi a zuciyar ta zata dawo nan ta sameni sai ta koma gidan mijin ta bata mai dani mutumin banza a garin nan ta tona min asiri ko watau kunga Allah ya rufa min asiri ta tsatson ku ? Kaiya kaiyya ina ta fada har sau biyu kafin tace shine matsalan malam bahaushe wallahi kaji na fada ma yarinya tana cikin matsala watau kai ko a jikin ka malam don kawai dan abim duniyan da kake samu daga wanan mutumin ko ? Ya rufe maka ido ba zaka dawo da hankalin ka wuri daya ka natsu kaji ko meye matsalan yar taka ba da miji nata kadai kawai burin ka ta dawo ta koma koma meye ta karata can dashi ko ? To ban yarda yata ta halaka a haka ba don kawai kana kwasayin abin duniya kai yanzu idanuwan ka sun rufe ba zaka nemawa yarka manufa ba. Nan Abba shima ya taso kamar zai daki inna a ranan kan wanan maganan har yana fadin idan ta kuskura ta kashe aure na da ya jafar a bakin auren su ke nan itama. Ran inna ya baci matuka tana mayar mashi da martani har yakai saida su sa,adatu suka ja inna zuwa daki sannan Abban ya fita . A waje ya hadu da lantana dake labe tana saurare ta rasa gane zancen da akeyi da farko amma ta dan tsuntsunci wasu daga cikin maganan inda ta fahinci akwai matsala ke nan ga aurena dama tana neman sanadin da zata katse duka jin dadin daulan data hangomu a cikin sa ni da innan mu da kowa a dakin mu da wanan bakin cikin take kwana take tashi dashi a kullun. Abban mu yana fita gidan malam ya nufa don ya kai karan inna a can ya sa ai masa iso a wurin malam din nan ya samu wuri a waje ya tsaya yana cika yana batsewa har malam din ya fito ya sameshi a wurin. Bayan sun gaisa ne ya koro magana ya fadawa malam din komai saida malam din ya gama jin Abba ya nisa tare da fadin. Bello ka ban mamaki matuka duk da matar ka ta baka haske a cikin zancen auren yarka zuciya ya hana ka gane hakan ? Malam wani matsala take kira wa yarinyan nam fisabililah duk wanda yaga yar nan yasan tana a cikin daula ai. Malam ya katse shi da fadin kaiya amma bakai tunane ba bello a nan ka yanzu barin fito maka baro baro ka sani yar ka na cikin matsalan aure a rayuwa ta a gidan mijin ta don haka ka daina wanan kumfan bakin da kake yi a yanzu. Kamata yayi ka natsu a sama ma yarinya mafita ga rayuwan ta ayi abinda zai kawo zaman lafiya garesu da kwanciyan hankali . Don babu auren da za ayi tsaon wata daya ko biyu zuwa uku ace babu wani abinda ya taba shiga tsakanin mata da miji irin na aureta a tsakanin har wanan lokacin. Bale yarka dake neman shekara shidda yanzu a gidan mijin ta ya kake ganin wanan abin zai kasance komai hakkurin yar ka kuwa ? Jikin Abban mu yayi sanyi wani zufa ya fara keto mai lokaci guda ya kara gyara zama yana cire hulan kanshi. Kafin ya nisa yana fadin yanzun malam kana ganin hakan yana yuyuwa a tsakanin su kadafa yarinyar nan taiwa mutumin nan sheri kuma kan hakan ? Malam yace malam Bello ke nan ka godewa Allah daya baka ya kamar wanan yar mai hakkuri da sanin ya kamata do sauran zancen ba zai fadu ba. Abba yace wa iyazu billahi ban samu zama da ita ba gaskiya malam ban san da wanan zancen ba sam wallahi. Ya dan dade suna tautanawa da Abban kafin suyi sallama da juna ya nufo gida gwiwan da sanyi sai tunane yake a ransa. Yana hanya bai karasa gida ba kiran ya j din ya shigo mai haka ya bar wayan har kiran ya katse don ko ya dauka baisan amsan da zai bashi ba a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAN UWA DAFA MUN WUNI LAFIYA ALLAH YA GAFARTA MUNA KURA KUREN MU AMIN. LITTAFIN KUDINE YAR UWA DON ALLAH IDAN BAKI BIYA BA KADA MU SHIGA HAKKIN JUNA PLEASE, , , , Ina kwance ina barci dakin da muke kwana nida kawata nake jin suna kus kus kus da mahaifiyanta a waje. Matar na fadin yanzu yaya zamuyi da bakuwan nan gashi gidan nan haka muke babu abinda zamu dafa balle ai mata abin karyawa. Wani irin tausayin sune ya kamani lokaci guda na tuno sanin da nai masu a baya can da irin daulan da suke a cikin sa. Lafewa nayi kamar ina kan barcin har lokacin sai ta shigo ta zauna a bakin gado bayana tayi zugun tana tunane. Nima tunanen nake a raina bandai rasa komai a gidan mijina ba na rayuwan duniya sai kwanciyan hankali kawai dana rasa a tare dani. Wanda ko wace mace ke burin tayi aure ta kai gareshi watau ko wani gida da mutum yake ganin ana rayuwa da nasu kalan kalubalin rayuwa da suke fuskanta. Sai can na motsa kamar a lokacin na falka daga barcin take fadi daga bayana a sanyaye zainab kin tashi nace eh besty na mun tashi lafiya ya gajiyan dawainiya ? Tayi dan murmushi tana fadin haba dai wani dawainiya kuma besty kinfi haka a gareni ai kin sani. Gaakiya ta fada don lokacin gaskiya ta tsare min komai a makarantar da muke zuwa din don ko yanzu ban nuna mata ni din wata tsiya bace saidai ta gane hakan kawai a wurin yanayina. Mikewa nayi daga saman gadon na kewaya bandaki bayan na fitone na dawo na zauna a bakin gadon. Jakkar hannu na na dauka daga inda yake aje a kasa na dauko kudi masu yawa a ciki ba tare da nasan ko nawa bane na mikawa Nafisa din ina fadin. Kiba umma wanan kudin banyi tsaraba da zanzo ba don ina tamtama koba zan sameku har yanzu a gidan nan ba. Kallon mamaki tayi min tana zatgin ko naji shawaran su da mahaifiyar tane da sukayi na tare da fadin don Allah ki bata kice tayi hakkuri dashi ba yawa. Haka ta fita cike da mamakina a ranta na irin kudin dana debo mata din ko a ina na samesu haka sai sheki sukeyi a hannun ta. Uwar ba irin makwadaitan matan nan bane don haka ta taso yar nata a gaba zuwa dakin nata tana fadin ke yar nan wanan kudi haka masu yawa ? Ta samu na idar da sallah nafila ina addua na dago kai ina fadin wallahi umma ba komai ban samu yo maki tsaraba bane shi yasa. Umma tace ba zan karbi kudin nan ba don gudun fadawa ga halaka kin gani nan na tsaya a matsayin da Allah ya zaunar dani da diyana a gidan nan. Don tun lokacin da mahaifin su ya kwanta dama yan uwan shi da abokan aikin shi suka wawashe abinda ya bari sai gidan nan da mota daya muka tsira dashi nake tsorin duk wani abin haram da zai fado a hannun mu. Lah umma don Allah kada kimin mumunan zato a gareni ina nan a yadda kuka sanni har yanzu ba canzawa nayi ba umma. Ina da aurena a kaina tunkafin na karasa karatuna igiyan aure ya hau kaina muna kasan chaina ne zaune da mijina tun wanan lokacin . Sai naga sun kalli juna ina da yarta tana fadin haba nikan na sani zainab don kamanin ki da yanayin ki kawai mutum zai kalla ya gane ke din bata wasa bace yanzu nayi murmushi da jin hakan. Kafin na dago kai ina fadin umma dan matsala muka samu da mijina nazo nan na karasa ina hawaye. Subbahanallahi umma ta fada don jin abindana fada na zancen mijina take fadin keko yar nan Allah ya rufa maki asiri da gani me zai kaiki wanan kasadan kuma ?. Umma ba wanda zai taba gane irin rayuwan da nakeyi a gidan sa nayi haka don kawai ya gyara wasu halaye nasa da ban so. Mijin naki dan gari nan ne ko wani kasa yake umma ta tambaya na gyada kai alaman eh tare da fadin gidan danayi aiki ne a baya can garin nan. Nafisa ce ta dafe kirji tana fadin dan minister kike nufin kin aure ba dai last done din nan dake zaune a chaina ba ? Ta fada tana kallona don son jin amsan da za bata a lokacin na gyada mata kai a hankali alaman eh shi nake nufi. Sai naga ta wani rungumoni a jikinta tana fadin kawata kice kece mai sa,an da kikayi dace da wanan hadaden guy din da ake maganan sa dama . Wai ya auri wata yar kauye da ba ajinsa ba shiyasa bukin sa ba wanda yasan anyi a kasan nan don ba kowa yasan da zancen auren sa ba. Kinga diyata yanzu hankalina ya fara kwanciya da zancen ki bari naje a hada maku abin karyawa na dawo mu zauna mu san abinda ake ciki. Don ba zai yuyu na barki haka gida ba a san inda kike ba hankalinsu yana a tashe yanzu duk inda suke na rashin sanin inda kike. Umma daga wurin yayan maman mu na wuto nan amma baki kyauta ba yar nan a zaton ki ba zasu san baki can gurin ta ba yanzu ? Nayi shiru tare da dukar da kaina kasa na dan wani lokaci har umman ta gama min fada mai kama da nasiha ta fita daga dakin. Nafisa tace dani kiyi hakkuri besty kowa hakkuri yake a gidan shi ba zaki gane bane nafisa na fada ina share hawayen dake zuba a idona. Duk da haka ki godewa Allah daya baki irin mijin da ko wace mace take fatan samu a rayuwan ta nidai jinta nake kawai don na kula su mutane basu san abu cikin duhu sirine ba. Ka bar mutum inda ka ganshi kawai kada kayi amfani da zahirin shi don baka san zuciyar shi ba can abinda ke cikin rayuwan shi da zai baiyana ba zaka kara kallon shi sau biyu ba. Har mahaifiyarta ta kawo muna abin karywa tana kan bakin ta kafin ta juye zancen da ban labarin irin halin da suka shiga a baya.da yadda yan uwan su suka cuce su. Wanka nayi na sauya kayan jikina na saka dogon riga wanan karon tare da yafa gyalen shi a kaina a lokacin Nafisa ta gama gyara dakin nata. Kwana na biyu a gidan su Nafisa yayin da can gida aka tsanan ta nemana ta ko ina dole ya jafar ya sanda bana gida kuma ba a san inda na nufa ba. Tambayan dayane kowa keyi duk da ba kowa yasan da zancen batan nawa ba shine dama akwai wani abu a tsakanin mune dashi na rashin zaman lafiya ? Hjy ya fara nufa da zancen batan nawa daya shigo kasan kaduna ya nufo direct ya samu hjy da zancen take tambayan shi ko akwai wani abu a tsakanin mu na sabani daya hadamu ? Yace shidai a nasa sani baisan da zancen ba don lafiya muka rabu kuma muna waya dashi lafiya babu komai daya hadamu dashi. Anya jafari ka canza halin ka kuwa a kan yarinyar nan dana san ku dashi a baya hjy ta jefo mashi tambayan ? Yace a lokacin da yake cire hular dake saye a kanshi hjy wani haline nawa zainab bata sani ba da zaisa ta bata haka wa mutane. Duk wani kyautatawan daya dace nasan inawa zainab shi hjy a daidai lokacin ne hjy ta dakatar dashi da fadi kai tsaya kada ka mayar damu mutanen banza. Nasan halin yarinyar nan haka kawai ba zata saka kafa tabar gida ba haka kai tsaye ba tare da wani abuna faruwa a tsakani ku ba. Saida ya gogo zufa a goshin shi kafin yace hjy me take so bayan irin kulawan da nake bata a gidana ? Wai kai kuwa kasan me ake nufi da kalman aure a addinance ko a rayuwan malam bahaushe dole akwai wani abinda kakewa yarinyar nan wanda ba daide ba . Kasa fadan komai yayi ga hjyn don kalamin ta ya dawo dashi hanya lokaci guda yasa ya fara zargin kansa da kansa kan hakan. Amma hjy duk da nasan na auri zainab ne don rufin asirina ina iya baki kokari na wurin ganin na kyautata mata ta hanyar inganta rayuwan ta don ci gaban ta kada ta zauna hakana. Hjy tace bn fahince ka ba dan nan wani irin rufin asirine kake magana a kanshi kullun haka duk zancen auren ka da yarinyar nan ya taso ? Wanan matsalana ne dani da ita ba lalaine kowa ya san da shi ba ya bata amsa kai tsaye a cikin ko in kula irin na akidan yan turai. Ta fara tafa hannayen ta wuri daya tana salati kafin tace dole ni nasan da akwai abinda kake boyewa mutane kan auren ka da yarinyar nan tun farko. Shike nan idan na auri mace don wani bukatana hjy sai jama, a sun gama jin dalilina shine matsalana da kasan nan wallahi ya fada a dan hasale. Itama hjy a cikin hasala take fadin duk yadda akayi baka da gaskiya akan zancen nan tunda yarinyar nan har hakkurin ta ya kare a kanka, Hakkurin me hjy illa iyaka tace bana kwana da ita nasan wanan shine damuwan ta a yanzu kawai. Innalillahi hjy ta fada a cikin rawan jiki tana kallon shi shima din kallon ta yakeyi cikin halin ko in kula kafi cikin karfin hali hjy ta iya budan bakin ta tace dashi. Ka dauka kawai ka rasa auren ka jafari har in wanan zancen daka fada ya tabbata hakan gaskiyane ? Kafin ta juya tana fadin kai me ya sameka da har baka kwana da matar ka tana yarinya karama ka barta a hakan. Kako san nauyin abinda ka aikata a addini gareka ko so kake yar mutane ta fada ga halaka idan hakkurin ta ya kare ? Hakkurin me hjy zai kare ga zainab karamar yarinya da ita har yaushe wanan abin zai dameta a yanzu don namiji baya tabata ya fada with full comfidence babu wani damuwa a tare dashi. Hjy bata san lokacin data fashe da kuka ba tana fadin ya tashi ya fita yaje can ya samu uwarshi su san yadda zasu gyara wanan zancen da kansu. Ganin da gaske hjy keyi yasa ya koma lalashin ta yana fadib bana son mami ta san wanan zancen don kinsan tsakanin su da zainab din dama. Shine dalilin dayasa na nufo nan wurin ki don ki ban shawaran da zau dace kafin a farga da hakan kowa yasan zancen batan nata don nasan da manufa tayi hakan gareni. Hjy kan bata tsaya sauraran shi ba sai salatin da take sakewa tana fadin boyar Allah an hada kai dani an cuta maki a cikin rashin sani wallahi. Don wanan kan ba musulunci a zuciyar shi sam don duk dabi,un kafirai ne a zuciyar ka karara wallahi. Ya dade zaune a wurin shiru kafin ya mike ya bar falon tsohuwar ba tare da yi mata sallama ranshi a bace kai tsaye kauyen mu ya nufa. A can ma bai sha da dadi ba a gurin Abba sai dai godiyan shi ga Allah shine iya abinda na fadawa iyayyena ke nan ga yadda ya fahinta. Hakkuri ya basu akan zai gyara insha Allahu shidai burin shi shine ansan inda nake muyi ido biyu dashi kawai yasan zan amin in koma. Don bai dauki wanan matsalan dana gabatar a gaban iyayyena wani babban matsala ba can don shi a ganin sa aini mutane zasu zaga kan hakan. Abuja ya nufa da yamman nan kai tsaye gidan mami ya nufa bai boye mata komai ba game da rashin ganina da ba, a yi ba. Sai cewa mami tayi idan ma na tafine in tafi mana ba sai a aura mashi wata ba a cikin gata dama ba yarda tayi da kasancewan mu tare ba ita. Don dan tallaka bai iya samun wuri ba duk gatan da ake muna nida iyayyena bamu gani ba muna neman mu tonawa mutane asiri a gari. Ya mamud yace asha mami bai kamata ki fadi haka ba wallahi duk hakkurin da yarinyar nan tayi ba a gane mata ba har ake fadin haka gareta. Hakkuri hakkurin me wani riba ya samu ga auren ta dama banda barnab suna ni hakan yafi mun nono fari wallahi. Sai ji tayi ya jafar na fadin mami bafa bana son zainab bane ina son matana don haka ki daina fadan wanan kalamin a gareta. Ana neman hanyar da zata dawo gidana kina kokarin sako wani sabon matsala kuma yanzu ni sam bazan taba yarda da hakan da kike son yi mun ba. Ka rufa min baki mara hankali kawai me kake tsunta gun wanan yarinyar ne wai a rayuwan ka ? Mami ba zaki fadi hakan ga zainab ba yarinyar da tayi min tsaye kan duk wani al,amarin da wani ya kasa min har ta samu na daina wasu abubuwan a rayuwana. Ka daina fadan wanan shirmen jafar a gaba har me zainab zata iya ma wanan bagidajiyar yarinyar mara hankali da wayau. Mami ke kike ganin hakan ga yarinyar da tayi min tsaye da addua ga komai har na daina harkan da kowa yake tsana na dashi. Idan baki sani ba ki sani mami zainab ce sillar daina shangiya da har kan guy da nakeyi a baya. Wani irin zabura mami tayi tana kallon shi tarre da dafe kirjin ta tana fadin wai dama da gaskiya kana wanan harkan jafar. Ya kalli mahaifiyar nasa ido da ido yace kwarai kuwa mami kuma a haka yarinyar nan ta zauna dani hakana. Wa kike tunanen zan zauna da ita tsawon wanan shekarun ina kallon ta ba tare da duniya taji mu ba. Don haka ni bani da kamar zainab a rayuwana banda wance tafi min ita mutunci a idona so ki daina bata yarinyar mutane haka idan ma laifine ni nayi ba ita ba kuma tayi hakkuri ta zauna dani hakana. Shot up mami ta fada a hasale cikin wani irin tsawa da bata taba yiwa kowa ba a cikin su. Don baka da kunya jafar kake fadan wanan maganan haka kai tsaye kasan girman laifin da kayi a wurin Allah ? Hukuncin kissa ne fa ya hau a kan ka har zaka zauna kana fadawa mutane wanan maganan haka ? Kai idan ka san ciwon kanka ashe har zaka tsaya kana wanan maganan a yanzu ita yarinyar da kake magana a kanta kana wani neman kareta a gaban mu ai kwadiyine ya zaunar da ita har tsawon wanan shekarun bata damu ba sai yanzu ? Don kudi ya rufe mata ido ita da iyayyen nata yasa basu ga laifin ka a farko sai yanzu zata zo tana wani neman mafita a yanzu ? Mami laifine don ta zauna dani a hakan ashe haka din laifine gareta a wurin ki na dauka ai babu kamar zainab a gurin ki yanzu. Yarinyar data kwatoni a cikin halakan dake kanki kika kasa kwatoni a cikin sa sai ido da aka zuba min ina kara shiga cikin halaka. Badon zainab ba da ban san iya inda rayuwa zai fada ga halaka ba da ke kanki ba zaki so a kirani da dan ki ba mami. Saidai haduwana da zainab shiya kawo min sauyawan rayuwa har na koma kamar ko wani mutum a yau. Daga tsaye yake wanan maganan sai da yayi tako kamar biyu ya tsaya yana fadin na fada maki a nemo man matana idan ba haka ba nima ku rasani kamar yadda zainab ta bata. Daga hakan ya sa kai ya fita kowa ya bishi da ido kafin mami ta fashe da wani irin kukan bakin ciki daya tokare mata makoshi a lokacin. Suma yan uwan nasa kukan sukeyi don gaba daya ya basu mamaki ya kuma zarewa sanin da sukai mai a baya. Yau ya koma kamar ba jafar di da suka sani ba idanuwan shi ga maganganun daya fada masu tsauri da nauyin fada shiko baiji nauyi ko kunyan idanuwan su ba yada ya fita abin shi. Gidan shi ya nufa kai tsaye duk da darene bai hana ya samu yan gidan wasu na aiyukan su ba a lokacin. Gaidashi sukeyi yana amsawa da kyat har ya shige part din shi kowa ya ganshi a lokacin yasan yana cikin bacin rai sosai. Wanka ya fada ya dade tsaye a bayin ruwa kawai ke sauka masa a jiki ya dafa hannun shi a bango ba abinda yakeyi sai aikin tunane. A iya tunanen shi ya rasa me yayiwa zainab din ta dauki wanan matakin a garesu don bai taba zaton hakan ba a yanzu a wurin ta. Tayi hakkuri ta zauna dashima a lokacin da yake cikin ganuwan shakiyancin shi balle yanzu da bata ganin komai a tare dashi. Menene bukatan zainab a yanzune ya tambayi kansa can ya runtse idanun shi na dan lokaci kafin ya kai hannun shi ya shafo gaban shi yaji a yadda yake mai duk tsawon watanin nan. Wani iska ya furzu a bakin shi kafin yayi wani tunane ya zabura da sauri ya kai hannun shi ya kashe ruwan dake zuba mai a jikin sa yana sauke ajiyan zuciya. Ya fito ya shirya a gurguje ya nufo falon shi ya samu fadila na kwashe kayan abincin da suka jera mai don tasan tunda yakai wanan lokacin ba zai ci abincin ba. Sam bata san da fitowan shi ba a lokacin sai muryan shi da taji a bayan ta yana fadin Fadila wani shiri kukayi da zainab akan tafiyan ta ? A dan tsorace fadila ta juyo tana rawan jiki tare da fadin sir ban fahince ka ba yayi mata wani irin kallo mai kama da tsana kafin yace me kika fada mata ranan a kaina. Jikin fadila ya fara rawa ta mayar da kayan data dauka a hannu ta tana fadin sir ban fada mata komai ba believe me ba muyi wani magana a kan ka ba tunda tazo. Kin tabbatar baki fada mata zancen da kikaji ranan munayi da dan uwana ba a falon nan ya tambaya cikin tsare ta da idanun shi. Da sauri fadilan tace believe me ban fada mata komai a kan wanan zancen ta yaya ma zan fada mata wanan maganan idan har ina kaunan ta da farin ciki ? Idan har na binciko na gane da hannun ki a cikin tafiyan nan nata duk hukuncin dana yanke a kanki ke kika jawa kan ki kowa kike kuwa bai dameni ba don kina yar sandan ciki. Wani irin faduwan gabane ya ziyarci zuciyar fadila lokaci guda hankalinta yai mungun tashi ya juya ya barta a wurin tsaye cikin farga ba da tsoron . Na sanin ashe ita din yar sandace yasan aikin da takeyi a gidan sa ke nan amma kuma bai koreta ba ga hakan. Haka yasa ta kai zaune saman kujeran dinning din tana tunane to idan shi ya sani ita zainab fa tasan da wanan zancen ke nan ko me ? ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI DA FATAN MUN WUNI LAFIYA ALLAH YA SADA MU DA ALHERIN SA AMIN LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA AMINCI YAFI. Irin samakon da yayi ne ya ba malam mamaki matuka har ya kasa boye hakan a zuciyan shi yakewa ya jafar din ba, daya fito yana fadin. Kai ka dauka zan sace ma matar takane kayo min wanan samakon hakan a gida ya fada yana dan dariya tare da mikawa jafar din hannu kafin ya juya wurin kanwata da ta rako ya jafar din gidan malam din yana fadin kece yar rakiya ko kika nuna mai gidana. A cikin dan kunya ya jafar yake fadin malam an tashi lafiya ya kwanan iyali ya amsa da lafiya tare da fadin mu karasa ciki ko malam jafar ya fada yana nuna mai kofan shiga zauren nasa kai tsaye. Bayan sun zauna suka kara gaisuwa da malam din kafin malam ya fara magana yana fadin ka kyauta da ka amsa kirana da gagawa don mu samu mukai karshen zancen ba tare da kowa yasan meke gudana ba a tsakanin ku. Don ko yanzu an fara sake zancen a gari saidai wasu basu yarda da hakan ba gaskiya kaga ko a kai karshen abin zai fi. Gaskiyane malam ya fada cikin dan kunya da dukar da kanshi kasa malam yaci gaba da fadin gaskiya sam baji dadin hakan daya kasance a tsakanin ku ba tun farko. Ya sake dukar da kanshi kasa don kunya da nauyin malam din da yake ji har cikin ranshi a lokacin. Nasan fashewan wanan zancen yanzu a gare ka babban nauyi ne da kunya ace dan musulmi ke aikata wanan sabon a doron kasa hakan . Dan adam yakan manta da irin azaban da Allah ya tahadar mashi tun a nan duniya kafin aje ga lahira ya koma a makomar da Allah ya tanadar masa. Duk wani jin dadi sabo da bawa zai aikata a cikin sabon shi na dan lokaci ne don yanzu duniyan rayuwan cikin sa kalilan ne. Ka godewa Allah daya hadaka da wanan yarinyar mai zuciya irin na manya da sanin ya kamata da dogaro ga ubangiji. Yau da ace watace ba zainab bace na tabbatar da wanan rikicin sai yafi hakan a gareku ya dan dago kai a lokacin tare da fadin gaskiyane malam. Nasan zainab yarinyace mai karanci da kara agareni wanan yasa nake jin ba zan iya rabuwa da duk wani abinda zatai min ba na tozarci. Baza a kai ga hakan ba da yardan Allah don yanzu haka zainab tasan abinda kai da iyayyen ka baku sani ba a zancen nan naku. Ya dago kai da sauri ya kallo malam, malam din yace eh haka zancen yake don abinda bincike na ya nuna min mun tatauna shi da ita nan ranan . A yadda nasan zainab da tausayi da karamci a rayuwan ta zata duba ma kan hakan sai dai da yake shi dan Adam ajizine ba a yanke mai hukunci ga abinda zuciyar shi ke nasa mai don haka ban san dalilin zainab na aikata hakan da tayi ba a yanzu. A sanina nasan zainab tayi hakan ne bisa wani dalili nata da ba lalaine mu iyayyenta mu san hakan ba tunda har ta iya boye ma iyayyen ta sirin dake tsakanin ka da ita don har gobe basu san mai kake aikatawa yarsu ba na asha. Ya dago kai ya kalli malam malam din yace kwarai ko wanan hujan da suka rike ninan na fada masu hakan don kawai a fitar da wani tuhuma ko zargi a tsakanin ku. Kuma na tabbatar da zainab ba zata taba fada masu sirin nan ba don kawai kare mutuncin ka a idanun su. Dukar da kanshi yayi yana hawaye don jin abinda malam din ya fada kafin malam din yace na kirakane nan kafin kazo da iyayyen ka a zauna ya kamata in ganka mu zauna a tsara komai a mutunce. Malam dai bai boye mai ba duk yadda mukayi dashi ya fadawa jafar din komai har makarin daya ba zainab ta bashi sai daya fada mai. Cikin mamaki jafar din ke tambaya malam kana ganin jifana wani yayi da wanan mumunan akidar yace kwarai kuwa. Bakai akaso ya shafa ba mahaifinka akai wa da farko sai abin ya dawo gareka kai din anyima naka don duk inda zasu su duba kan iyalin shi farko sunan kane zai haska. Wanan dalilin yasa suka juyo a kanka suka saki kowa da komai a cikin iyayyen ka don ganin taurarin ka sunfi na iyayyen naka haskawa nan gaba. Allah ya kawo saukin abin ta sanadiyar zainab data dauki mataki akan ka da wuri wanda ba kowa ne zai iya tsayawa yai maka hakan ba kai tsaye. Yanzu duk mu manta da wanan mafita shine abin nema a gareka ya zama dole gareka ka tsaya kasha magani sosai ka dawo mutum kamar kowa. Tare da kuma neman tsari don kasan mai neman naka na gidan kune ba fasa jifan ka zasu yi ba tunda sun dauki niyar hakan a zuciyar su sai sunga bayan iyalin ku kaf. Sun dauki lokaci suna tataunawa da malam din kan matsalan nasa da kuma irin matakin da zai dauka don zaman mu ya dore dashi nan gaba. Nan dai yayiwa malam sallama tare da ajemai alheri amma malam din yaki amsa ko daya daga cikin abinda ya bashi din. Karshe jafar din yace ai masa sadaka dashi a inda ya dace da niyar Allah ya rabashi da abinda ke damun sa a rayuwan shi. Nan dai ya kama hanyar airport bai ko leka gidan mami din ba don gaba daya yaji gidan nasu da yan uwan shi sun fita ranshi a lokaci daya. Sai tunane yake ko mai yaiwa wani da zai masa wanan karen aikin hakan na zancen abokan sa kuma zai yi kokari ya nisanta kanshi dasu in Allah ya yarda. Ya iso Abuja a gajiye don gaba daya wani irin zazzabine ya rufe shi lokaci guda jan jin wanan maganan da yayi daga bakin malam din mai nauyi haka da kunya. Dakin shi ya shige ya kwanta ya rufe kanshi kwanan shi biyu bai leko waje ba ya mamud yana zuwa neman shi ace yana ciki bai fito ba . Ga kuma wayoyin shi duk a rufe lokacin hakan ya tayar da hankalin mamud din zuwa na karshe da yayine ya dawo gida hankali tashi ya samu mami data dau zafi dasu baki daya kan zancen dan uwan nasa don sun mara masa baya kan maganan yana fadawa mami din. Itama hankalinta ne ya tashi sosai ta mike ba bata lokaci zuwa gidan jafar din da yaranta gaba daya suka tafi hankalinsu a tashi dukan su. Sunyi dukan kofan da kyar ya taso ya iya budan kofan a lokacin har mami taba da shawaran a balla kofan aga halinda yake ciki a cikin dakin. Sai gashi ya bude masu da kyar duk ya rame ya fita hayacin sa yayi wani irin baki lokaci guda mami na shiga tana gani yadda dan nata ya koma ta hau fada tana fadin. Wanan yarinyar ta zama min masifa a rayuwa yanzu a kan wan yar kake kokarin halaka kanka jafar da sauri ya mamud din yace haba mami ba lokacin wanan zancen bane ai . A samu a ceto rayuwan sa tukun kafin a fadi wani maganan da za, aimai yanzu don yadda ya koma din nan ya kamata yaga likita gaskiya. No ku barshi ba sai naga likita ba ai na samu sauki sosai ya fada yana gyara zama saman kujeran da ya hau din. Mami da sai binshi da wani irin kallo takeyi tana mamakin wai jafar ne ke son halaka kan shi akan mace haka ? Tambayan da jafar din ya jefo matane yasa kowa ya kadu a falon don cewa yayi mami ko zaki tuna ina karami gidan da mukaje akan ban abinci naci har ya zama min matsala a lokacin ? Abinci a kasan nan ko a can US din ta tambaye shi yace a nan dai mami don ance nayi ciwo sosai a lokacin kan cin wanan abincin da nayi ? Wanan kuma wani zance ke nan yaushe mami zata iya tuna hakan abinda ya dade dayi ba yanzu ba . No ni zan tuna jafar ya fada don har ni nayi ciwo a lokacin ai gidan uncle musane mana mahaifin Rufaida daddy yaje damu ranan anty ta bamu abincin daddy bai ci ba yace mu muci tun a gidan mukai ta amai. Kwarai kuwa ta fada ainayi fada da daddy ku a lokacin kan hakan tunda ba sabawa da irin abincin nan kukayi ba da yasa kukuci. Ido jafar din ya lumshe na dan lokaci kamar yana tunane kafin ya bude su ya sauke ga yan uwan nasa a daidai lokacin mami ta jefo masa wani tambaya da cewa . Mai ya faru kake tambaya yanzu babu komai ya bata amsa yana kawar da kanshi gefe daya kowa falon yai shiru yana nasa tunanen a zuciyar shi. Ita kanta mami abinda ya farune a wanan lokacin yake dawo mata a rai gaban tane ya fadi ta kura dan nata ido a lokacin ne likitan da suka kira don ya duba shi ya shigo dakin. Bayan yan aune aune yake fadin ya kamata ka huta don jinin ka gab yake da ya hau a wanan lokacin ya kamata ka fitar komai a ranka yanzu don samawa kanka lafiya. Dan murmushi ya sakewa likitan ba tare daya furta masa komai ba yans gyara kwanciyar da yayi a lokacin. Kwance nake ringingine ina tunane umma ta shigo dakin ta sameni a hakan take fadin tun kan ta karaso yata kin fara kewan gida ko ? Jin hakan da nayi yasa na dago kai da sauri ina dan murmushi tare da fadin kai umma ina dai tuna wani abune daya daure min kai umma. Nan na bata labarin abinda malam ya fada min ranan na kare da fadin umma shi nake tunane wa zai masa wanan aikin haka a cikin yan uwan nasu ? Kai duniya ai in fada maki yata haka duniyan nan ta koma yanzu wallahi sam mutane basu da imani a zukatan su yanzu ko kadan. Wanda bakai tsamanin ko tunanen zai iya cuta maka ba shine zai cutama din don haka ne akeso a kullun mutum ya mayar da hankalinsa sosai kan iyalin shi. Zakiga mutum ya nuna maki so da kauna kamar ya hadeki a ransa don kauna amma shine zai koma baya yai maka sheri bari ma in maki na mahaukaci yan ciki daya ma a zamani nan sai su cutawa junan su fa. In har hakan da kakan ki ya fada maki gaskiyane bai kamata yanzu a ce kin bar mijin ki a cikin wanan halin da yake ba a yanzu kinzo nan kin zauna haka zainab . Saura kiris ki cin ma nasaran ki sai dai kuma shedan ya rudeki yayi maki huduban tsiya da kika bi kina kokarin goge ladan ki kan hakan. Zainab ba zan cuta dake ba ko kadan yadda na dauki nafisa a gareni yanzu haka nake jin ki a zuciyana. Don ke din yarinyace mai hankaki da sanin ya kamata don haka hakkuri zakiyi na mayar dake gun iyayyen ki ayita ya kare a tsakanin ku dasu da mijin naki. Don zama da boyon ki a nan yanzu baida wani fa,ida a gareki zainab hakkuri ya kamata kiyi da mijin ki koda kin koma gida kici gaba da daurewan da kikeyi da farko a kansa kina masa addu,a . In Allah ya yarda ubangiji ba zai bar wahalan ki ya tafi a banza ba zainab Allah yaga zuciyar ki da niyar ki a kanshi. Shima kuma din nasan ya sani abu daine idan ka riga daka saba shi a rayuwan ka yana da wuyan bari ko kuma ki masa uzuri wata kila wani lalurane yake damun rayuwan shi har ya kasa kaiwa gareki zainab Allah masani. Hawaye nake yi duk da nasan gaskiya umma take fada min duk a cikin zancem nata ya zama dole di inyi biyayya gun umma in koma gidan mu gaban iyayyena ayita ta kare din kamar yadda umman tace din. Bakina na bude da kyar nace umma ba wai wanan zaman da mukeyi dashi bane matsala a gareni sai yadda mahaifiyar shi har yanzu ta kasa gane hakan a nata bangaren . Take tsanana ni da iyayyena kan zamana da dan nata wanan shi ya saka bana kaunar komawa gidan shi a yanzu. Ina ruwan ki da ita zainab ina tana gidan ta kina naki sai kun hadu ko kunje zata ganki kuma duk abinda zata fada shi ba zai taba daukan hakan ba tunda yasan hakkurin da kikeyi dashi ai. Shike nan umma zan koma koda baizo din ba zan nuna masu nidin diyace idan Allah ya yarda da sauri umma ta riko min hannu tana saka min albarka ina amsawa a kasan zuciyana . Haka nafisa data fita zuwa kasuwa ta dawo ta samemu da umman tana ban baki itama ta zauna sunayi tare a gaskiya nafisa da mahaifiyar ta mutanen arziki ne matuka. Don yayan tane yayi kokarin neman mota don nasi yana ajiyene a gidan kamar photo kawai baya aikin komai suna kallon shi. Motar abokin shi ya dauko mukai tafiyan dashi samako mukayi muka bar kaduna dan lokaci kadan muna anchau. Sai ganin mu akayi kamar daga sama don ba wanda yasan da zuwan mu a wanan ranan. Wanan dawowan yayiwa innan mu dadi sosai don nan take ta nuna cewa ai dama ba wani wuri na tafi ba gidan yan uwan ta naje ganin su . Wanda hakan baiwa Lantana da tabi makwabta tana fada masu ai yaji nayi na gudu ba,a san inda na tafi ba . Sai gashi na dawo gida a cikin salama sai hakan kuma yai mata zafi a ranta har ta kasa boye bacin ranta. Taro na sosai su umma suka samu daga innan mu da yan uwana inda suke nuna su din yan uwan innane ga mutanen gidan mu din. A nan suka wuni don umma basu tafi ba sai data gana da Abban mu suka dan tatauna kan matsalan mu Abba yace zasu zauna dashi ai suji dalili hakan daga bakin shi. Malam kuma godiya yayiwa umma sosai bisa irin kokarin da tayi na dawo dani gida a cikin salama ba tare da rayuka sunkai ga baci ba. Don Abbana shi kan bai boye yana goyon bayan jafar ba har lokacin don nunawa yayi na koma naci gaba da hakurin da nakeyi da mijina. Tunda hakan sirin mune baki daya dani dashi yanzu ai tunda bai rageni da komai ba bayan wanan matsalan kuma yace yana neman maganin hakan don kawo karshen matsalan dake damun shi din. Kafin su umma su tafine kuma sai ga Abban ya canza shawara ya samu su umma a falon inna yana fadin ni hjy naga tunda yarinyar nan ganin mu dai tazo yi dama . Ya kamata ta shirya ta koma dakinta kawai tunda dama lafiya suka rabu da mijin ta ai yin hakan kamar zai kara muna girmane a idon sa. Da sauri inna tace a, a, a dai tsaya har yazo din aji ta bakin sa zaifi da sauri umma da ta fahinci hakan zai iya kawo masu matsala a tsakanin su tace hakan zaifi gaskiya. Don haka basu bar garin ba aka saka ranan komawa na muna daki muna jinsu lokacin mutuwace kawai banyi ba don ta kaicin abinda abba din yayi min. Shike nan ni nasan yanzu banda baki a wurin mami don wanan zai jawo min abin fada sosai a wurin su . An aje umma zata dawo su rakani har abujan idan ranan yayi ita da maizube zamu tafi haka aka aje zancen komawan nawa. ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI FATAN ALHERI A GAREKU KO YAUSHE ALLAH YA BAMU IKON BAUTA MASA AMIN, , , LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA YAR UWA ALLAH YA BADA IKON SAUKE NAUYI AMIN, , , , , Duk wani motsi da yunkuri da naso yi don daukarwa kaina fansa kan wanan halin na ya jafar iyayyena sun hanani motsawa . Daga mai fadin yin hakan kamar tozarcine ai a gareshi sai mai fadin may ya ragani dashi da zan gujeshi ko don yadda ya dauki dawainiyar karatuna dana kanwata ai zan hakkura na zauna in rufa mai asiri ba tare da wani ya jimu ba. Magana dayace ya karya min gwiwana shine maganan innan mu da tayi min tana fadin ki kara basa dama kiyi hakkuri ki koma ko Allah zaisa ya gyara nan gaba. Idan kinga bai gyara halinsa ba kinga kina iya daukan mataki a lokacin ke nan don gaskiya ba zanso ace ki rabu da wanan bawan Allah ba ko dan kiyi sanadin kubutoshi daga halakan da yake ciki a yanzu ma. Haka kuma mahaifiyar shi data sa ido taga karshen zaman ku dashi ko dan haka ba zan so ace kinbar shi a yanzu ba a daidai lokacin da yafi bukatan ki a kusa dashi ke nan yanzu . Sai gashi kina kokarin goge ladan da ya kusa zama rabon ki a wurin Allah don ba karamin jahadi kike kokarin yi ba tunda har Allah ya fara kwatoshi daga halaka ta dalilin ki a yanzu. Wanan kalaman na inba ne suka kashe min jikina sosai har na dinga zubar da hawaye don tausayin kaina da sauran yan uwan da suka samu kansu a irin halin da nake ciki a lokacin nan . Ba wanda yasan irin yadda zuciyar ka yake ji a irin wanan zaman da mutum keyi da mai iri halin nan sai ma mutane ko sun sani din suyi kokarin dora maka laifi don kawai kayi kara na dan lokaci guda. Don wata ko na sati daya ba zata iya daukan hakkurin da kai kakeyi a gidan auren irin wanan ba . Irin yadda inna ta nuna min yasa na tattara komai na barwa Allah zan koma nayi hakkuri don abubuwa biyu zuwa uku don kwadayin na zama silar shiruwan shi. Na biyu kuma don farin cikin iyayyen da naga komawan nawa suke bukata kawai gidan yaya jafar a yanzu. Sai kuma uwa uba don mami da yan matanta da inna da umma suka nusar dani yadda komawan nawa gidan ya jafar din zai zafafa masu rai idan na koma don su burin sune suga nabar shi ga baki daya . Sai kuma irin su Lantana yan bayan fage a garin mu dake da yawa wurin saka ido suga nabar gidan jafar din a samu abinfada a karshe. Ire iren tunanen da nakeyi ke nan a raina har na amince da zuciyana zan koma gidan na rugumi hakkuri a zuciyana. Ana gobe zan koma bayan magariba mukaji sallaman malam mijin maizube a kofa innan mu zan iya cewa a iya wayau na wanan ne karo na farko da malam din ya tako har gidan mu. Bayan gausuwa da dan barkwancin da akayine ya bukaci kowa ya barmu a falon dani dashi a lokacin a haka suka fice suka barmu dani dashi sai dan shiru ya biyo baya bayan fitan kowa falon kafin ya kira sunana a lokacin. Na dago kai na amsa a dan kunyace ya fara fadin duk da nasan sherin shedan ne daya rudeki har kika kai ga aikata hakan don kina ganin mu bamu damu da damuwan ki ba ko wani abu haka ? Sai dai zainab ina son ki sani shi hakkuri bai taba faduwa kasa banza a rayuwan bawa duk mai hakkuri mawadaci ne watarana. Don haka zainab ki koma dakin ki ki kara hakkuri na dan lokaci muga abinda Allah zai maki sakaiya dashi ga hakan. Don yanzu insha Allahu kina kiris ne da ki cinye jerabawan ki fa Allah ya dora maki a gidan shi na kirashi yazo munyi magana dashi ta fahinta. Jin hakan yasa na dago kai da sauri na kalleshi kafin in mayar da kan ina mamakin hakan . Malam yace kwarai na kirashi ba tare da kowa ya san da hakan ba kuma yazo mun zauna munyi magana dashi ta fahinta ya fada min komai yadda ya daxe na kuma fahinci inda matsalan yake yanzu. Basa wani a nan gidan yasan da zuwan shi ba garin nan ko a gidan nan naku bani tsamanin wani yasan da zuwan shi din. Don haka yanzu sai kin kara jajircewa kan wanda kikeyi a baya zainab nasan kina kokari sosai amma ki kara a kan wanda kikeyi a baya. Insha Allahu muna sa ran abunuwan zasu zo da sauki don mawuyacin abune mutum ya shiga wani kungiya su barshi ya fita a ckkin shi salin alin ba tare da wani tangarda ba. Balle shi din da suke ganin kamar samun shi a cikin su wani babban kamu sukayi a hakan yanzu kuma yace zai fice cikin su ba tare da ansha wahala ba. Jin hakan na dan dago kai a tsorace na kalli malam yace kwarai nasan ke baki san da wanan zancen ba ai burin ki kawai shine kiga ya bar aikata abubuwan da yakeyi ko ? Kamar yadda mahaifiyar shi da yan uwan shi duk basu san da wanan zancen ba suma a wuri su. Ba abin mamaki bane a wanan zamanin idan kaga mutum yana wandakan shi ka dauka ya samu damane kawai a banza kabar mutum kawai a yadda ka ganshi don bakasan zuciyar shi ba. Tsorone ya kara kamani lokaci guda amma sai malam din ya kara wayar min da kai yadda zan fahinta. A karshen maganan nasa ne na gane wa yan nan abokan nasa na chaina shi dasu kamar wani gungiya suke cikin sa da yasa ya jafar din kara fadawa a cikin halaka. Ga kuma nan gida mai binshi da sheri da son ganin komawa bayan shi a kullun sun masa aiki tun yana karami da iyayyen shi basu farga da hakan ba. Malam din yaci gaba da fadin don haka yanzu aikine ja a wurun ki ko kun koma din ba zaki zauna hakan ba ki kara komawa wuri wanan matar koda abinda zata kara baki a hakan . Duk da nasan insha Allahu har in kinyi aiki da wa yan nan abubuwan da muka hada mai abubuwan zasu zo da sauki sosai kema kanki sai kinsha na tsarin jikin ki din zasu iya waiwayan ki a ko wani lokacin kan hakan. Ya miko min wani dan ruwa daga cikin aljihun babban rigan jikin shi yace karbi wanan ki shanye duk yanzu. Da yardab ubangiji saidai ta Allah ba nasu ba don wanan makaru ne sosai majarabi ne kwarai na sani. Ina hawaye na karba da hannu biyu na bude dan goran nayi bissimillah na kafa kai na shanye kamar yadda yace inyi din. Ya kara miko min wasu kulli da zanyi wanka da hayaki tare da wasu addu ,a da aka rubuta min zan dinga yu safe da yamma don tsari. Da wanan tunane na zancen mu da malam na kwana a raina ina faman tunane a raina watau a zamanin nan ko wani gida da kalan nasu matsalan ke nan na rayuwa. Zama haka kai sakw bayayi ke nan sai mutum ya hada da neman tsari a wurin Allah da yawaita sadaka da kyautatawa gun mabukata shine zaman lafiya ga bawa. Washe gari karfe goma na safe muka bar garin mu cike da bacin ran rabuwa da gida da zamu sakeyi na tsawon wani lokaci kuma don ban sa rau yaya zai kara bari nazo gida kuma ba nan maza. Wasa wasa har abu yakai ga karawa yaya jafar ruwa don rshin karfin jikin shi da bayayi a wanan lokacin dole mami ta tsareshi saida aka kara mai ruwa don ya dan samu karfi. Duk suna falo gaba dayan su sun sakashi a tsakiya sai ya dan ci abincin da mami tazo dashi don ta fahinci rashin cin abincin sa a yanzu. Mami na fadin kawai zaka halaka kan ka kan wata yarinya can da bata damu dakai ba kana kokarin jefa kanka a cikin halaka haka. Kai haba mami na fada maki bafa wani wuri ta tafi ba tana gidan yar uwan maman suce ashe a kaduna . Nayi mamakin ma rashin dawowan su jiya da basuyi ba don kwanakin dana bata ya cika jiya ya fada yana bata fuskan shi. Kaiya yanzu kuma hakan suka tsarama cewa zata dawo din bayan ka gama fadin ta bata har kana batun yiwa mutane hauka. Mami ai dole ya damu rashin jin ta a waya da baiyi ba na kwanaki kin san yadda kasan nan ya koma fa a yanzu ya mamud ya fada daga gefen shi. Tama bata din mana Aisha ta fada waya damu da ita idan ta bata tunda ita bata san ciwon kanta ba ta tashi taje wuri ba tare da fadawa mutane ba. A cikin wani murya yake fadin AISHA ya kalleta kawai ya kawar da kanshi tare da gyara kwanciyan shi saman kujera. Kai haba Aisha wanan wani irin maganane haka kuma ku kullun baku son gaskiya wallahi Na,ima ta fada tana kawar da kanta gefe. Kaji kuma Na,ima da wani zance ai gaskiya aka fada rufaida tace kawai ta tayawa mutane da hankalin a banza. Do kawai taga kamar yanzu din daya take da kowa har zata tafi wuri haka ta share mutane don kawai ta dagawa mutane hankali ta karasa kasa kasa don tasan kwanan wasan. Nifa ku bar wani kame kame a gaban shi mami ta fada idan ma zata tafi ne ta tafi din aini har na fara murna tafiyan ta sai ga mamud na fada min wai rudun jafar ne taje wurin yar uwar maman sune ashe. A daidai wanan lokacin suka ganmu kwatsam a bazata daga ni sai sadiya da hjy umma muka shigo don a dakatar da zuwan mu da maizube don kada su dauka wani abinne hakan. Ashe ko hakan yai muna daidai do yadda muka samesu gaba dayan su a gidan zaune a falo lokacin. Da wani irin mamaki suke kallon sadiya dake shigowa gidan jaye da dan troler kayan ta kai tsaye. Da sauri ya dan dago daga kwancen yana fadin sadiya kune tafe ashe ina yayar taki take duk wanda suke zaune a falon suka kalli juna lokaci daya. Sadiya tana fadin gasu shigowa suna baya tare da gwaggo data rako su da zamu dawo a daidai lokacin muka shigo ni da umma da Nafisa. Basu ba duk mun dan kadu muma da ganin su sai dai mun dake mun shigo kamar babu komai a rayukan mu lokacin. Nayi wani haske fayau dani don dan raman danayi a lokacin saidai hakan kuma bai hana kyauna ya kara fitowa fili ba sosai a lokacin. Gaba dayan su idanuwan su ya koma a kanmu sai Na,imace da su ya jalal ke muna sannu da zuwa don mami ta ma kasa magana a lokacin . Saboda bata yarda da abinda suka fada ba ta dauka shirine kawai don su batar mata da hankali suka shirya hakan. Muna amsawa ya dago shima don ganin mu tare da umma yana mata sannu da zuwa dole yana kallon gefen shi su Aisha da sauran sukai saurin mikewa suka bamu wuri muka zauna. Gaisuwa aka fara a tsakani su da umma bayan mun zauna din kafin umma tace ashe kuma bayan tafiyan yar nan jikin maigidan nata ya kiya haka ? Ya mamud ya saurin fadin eh wallahi da zazzabi ya dawo kasan da yai tafiya kuma sai gashi ya kira layin ita zainab baya shiga gida kuma sunce basu sameta ba a lokacin ya dada tayar mai da hankali. Kai ai zainab bata bata a kasan nan in ba wani ikon Allah ba hikiman ta dai na yarinyane zakaje wuri ba ka fadawa mijin ka ba ya sani don hakane ma da akace ya bugo bata nan . Yasa nace ai sai muzo tare nida taje wurina in bashi hakkuri kan hakan da tayi kasan yaran yanzu basu daukan irin wanan da muhinmanci su. Kai haha mama aida baki taso ba ko ita dayan ma ta dawo ai yasan gida taje gashi an dade ba ahadu ba dole ta dan zaga ta gaida ku ai. Hakane amma zuwan zai sakashi jin dadin hakan don yasan an mutuntashi kaga gaba sai ya bata bakin zuwa ko ina ta duba mu ko ? Shi dai yana gefe sai dan murmushi yakewa umma din ba tare da yayi magana ba a lokacin . Kallon tsab mami takewa umma tunda ta fara magana sam batayi kama da irin yan uwana da take daukan sune gareni ba kawai. Don umma dai in ba don da duniya ya basu baya ba a yanzu tana cikin matan da a zamanin baya suke fada a kaduna aji. Ya jafar ya dan kalleni cikin kulawa yana fadin ki shiga dasu ciki su huta ko kuna da gajiyan tafiya a yanzu zaka dauka wani zancen soyayya mukeyi dashi a lokacin duk suka zubo muna ido duk da basu jin me yake fadi. Ganin hakan na mike tsam daga inda nake zaune ina fadin Nafisa mu shiga daga ciki ina daukan jakkar umma dake gefen ta aje inda ta zauna. Duk suka bimu da kallo bayan mun mike din don basu so hakan ba a rayukan su gaskiya jin karin bayanin da umma din tayi masu don kwana uku na kara ga kwanakin daya bamu din muyi a gida ke nan. Wanan ita din wacece mami ta tambaya bayan mun shige ciki yan aikin gidan kuma suna shigo da kayan mu a cikin gidan har lokacin zuwa dakunanan mu . Ai ba lalai bane ya san yan uwanta duka duba ga yadda aikai auren su din kinga ba wai ansan yan uwan zainab din bane duka. Bata daiyi kama da yan kauyen nan ba ita kila a wani birni take zaune Aisha ta fada. Amma kema dai kina da yan uwa a kauye ko don ba kowane zaune a birni ba ina su hjy dasu mama Ramatu duk a kauye suke zaune. Jamal ke fadin hakan ba tare daya dago kanshi ba daga latsan wayan da yake yi tun zaman shi a falon bai furta komai ba tunzuwan su sai yanzu. Mami tace cikin tsawa zaka fara ko tun dazu nake kule daku kuna kokarin hana yarinyar nan shan ruwa ya fada mata. Bata da kunyane mami ana magana sai ta dinga saka baki a maganan wataga ya saka baki a cikin zancen cikin mu ? A daki kan muna shiga umma tana zama take fadin ikon Allah gaskiya dai tayi halinta don wanan matar bata iya boye bakin cikin ta ba sam. Haka muke umma na fada ina kokarin cire lafayan dake jikina daga sama ina juyawa Nafisa ke fadin aini umma ban ko tsaya kallon su ba ni mamakin gidan nan nakeyi kamar ba a cikin kasan nan ba. Ita da tasan kanta ai kinga wanan bai rudeta ba ko umma ta fada ai idan ranka ya baci ko ka hango abinda ba daidai ba har kana da zuciyar kwarai abin duniya baya rufe ma ido sam. Hakane umma don mai daki shiyasan inda ruwa ke masa yoyo akace ita da ke zaune cikon su tasan irin rayuwan da take yi a nan. Sallaman Fadilace ya katse muna zancen mu ta shigo da dan fara,a a fuskanta kadan tana fadin ina baya tun zuwan mutanen gidan su oga sai yanzu ake fada min kin dawo ashe. Nan dai ta juya tana gaisawa dasu umma tare da tambayan lafiyan su inna tana tambayan sadiya sai gata ta shigo dakin tana fadin. Anty wai yaya yace ga bakon mu ya shigo shima a kawo masa abinci da abin sha a falo. Sai dai ganin anty fadila yasa ta dakatar da maganan da takeyi ta makaleta don murna a lokacin nake fadin bakin falin sun tafine ko suna nan. Tace babu kowa yanzu a falon ina ga sun tafine don basu falo sai fadila ke fadin ai sun tafi yanzu ina shigowa dakin nan. Nikan wanka na shiga don hakan ya zama min kamar dabi,a na yanzu ance zama da madaukin kanwa don haka shima yaya din yake da tsabta dole nima na iya hakan. Abinci lafiyayye Fadila da a yanzu nake ganin sauyi a wurin ta suka gabatar muna tare da sauran yan aikin dake shigowa muna gaisawa dasu a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM WAHAMATULLAH YAN UWA MUSULMAI BARKAN MU DA WANAN LOKACIN ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN, , , , , YAR UWA BA DAMUWA BANE TUNINE HAKAN KADA KI MANTA KI SHIGA HAKKIN WANI IDAN BAKI BIYA BA DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA, , , , , Mutunci da daraja bako ranan sun ganshi a gidan wurin mu don har sai da suka gaji daci don kansu daki na daban aka kai ko wani su. Amma karshe a dakin umma da aka sauke ta a nan muka taru gaba dayan mu dakin wurin ta ana hira inda a karshe hiran ya koma na daulan duniya da sauran su. Muna cikin hira misalin hudu da rabi ne yaya ya shigo dakin don gaida umma da gajiyan hanya gaba daya dakin kowa ya shiga kama kanshi a lokacin. Nayi mamakin ganin wai ya jafar ya iya ladabi gun sarakan shi irin na malam ba haushe ashe don har kasa yakai yana gaida ita abinda ban taba gani ba a wurin shi ko dan bamu taba hadewa a gaban iyayyena bane dashi oho ? Umma ta amsa itama a cikin dan kunya take kara yi mashi nasiha kan zama da iyali sai hakkuri don mu mata haka muke kaman yara wurin tunane. Ya daga yana godiya ya fita daga dakin kafin umma ta juyo tana fadin ke ko yan nan kije gunshi tunda muka iso gaein nan kuwa ? Kasa nayi da kaina lokacin data fadi hakan don ban tafi ba kuma ba zanyi karyan hakan ba gaskiya. Assha zainab baki kyauta ba gaskiya kema kina da naki matsalan ke nan a nan don ba aiwa maza hakan ai kome ko ke tsakanin ki dashi. Ya kamata ace kinje kun gaisa ba wanan da kukayi ba a bainan jamma,a dashi kinga a hakane zaku samu fahintar juna a tsakanin ku har ku warware matsalan dake akwai ba tare da kun shirya hakan ba. Ya zama dole ki dinga bashi hakkin shi a naki bangaren bawai ki biye masa ki dinga share shi ba haka ban san lokacin dana bude baki ina fadin ummz bawai ban zuwa bane. Shi din ne yayi warning dina tun farkon auren mu kan hakan ya kance shi mace bata gaban shi asalima shida mace sai dai mutunci da zaman yan uwantaka a tsakanin su. Badake matarsa ba kan ko ya fadi hakan don kece mace mafi kusanci yanzu a duniyan nan gareshi kinfi ko uwarshi kusanci a wurin shi. Hakama kinfi duk wata yar uwa tasa mafi kusanci a yanzu gareshi kefa mace ce zainab kina da hanyoyin da zaki sauya duk wani akidar shi wanda bai maki ba a cikin ruwan sanyi. Na marairaice murya ina fadin umma yaya zanyi nikan yace baya son mace a kusa dashi ko dakinsa dokar shiga yasa min a lokacin idan bashi ya bukaci naje nayi wani abuba bana shiga part din shi sam. Ikon Allah sai kace wanda baya hurda da mata su nake jin haka a garesu Nafisa ta fada a bayana inda take zaune. Wanan wani irin maganane Nafisa ko kin manta shi din tashin American ne wai bakin akidarsune kawai ya kwasa a zuciyar shi na rashin daukan abu da muhinmaci . Ki bar wanda bai tashi a cikin al,adan malam bahaushe ba kawai don shi hakan da yakeyi ba komai ya daukeshi ba a wurin shi. Gyara ya zama dole yanzu gareki ba wai rashin kunya bane yasa nake fadan hakan gaskiyan maganan a nan kema kina da naki laifi zainab. Dolene ya zamo makwancin ku daya dashi koda hakan ba zai kasance kullun ba haka kuma duk wani bukatan shi ko laluran gida ya zamo kece mai masa shi. Kyautatawa fa yana daga cikin abinda namiji yafi so a rayuwan shi koda kuwa yarone kankani yana son hakan gareshi. Wanka ki zamato kece mai tayar dashi kafin ya tashi kin hada mai ruwa ya shiga kin tsaya dakin ki gyara kafin ya fito kin feshe dakin da kanshi kin fitar mai da kayan da zai saka a ranan. Ya fara shiri idan akwai lokaci ki tsaya har ya shirya kafin ki fita zuwa hada masa dinning da already kin gama abincin kafin ki tayar dashi daga barcin don gudun makara. Kina zaune kin tsare shi har ya gama ki rakashi idan fita zaiyi kina masa fatan alheri da addu,an kariya a gareshi har ya fice gidan . Zainan ki fada min cikin wa yan nan halaiyar wani kikewa miji ki a ciki na dukar da kaina kasa tace kin gani . Inda ake fara samun matsala ke nan a wurin mu, mu mata ana fadin ni mijina bayai min kaza baya min kaza. Kinga a nan ai matsalan na mace ce don itace tayi sakaci da hakan ba zance ki matsa dole sai ya kwana dake ba a,a. Wanan kawai idan kin tsare ya isa shi kanshi yaji kunyar kanshi da kanshi yasan abinda yake maki bai dace ba ya gyara wasu daga cikin halin da yake nuna maki din. Kwanciya a kullun kusa da miji wani sirine da Allah ya boye hakan a zukatan ma,aurata wanda su kadai suka san feeling din hakan. Amma dake dashi kuna zaune haka a cikin jahilci kowa na ganin laifin wani alhalin dukkan kune masu laifin gaba dayan ku. Din haka ya zama dole ki gyara kema a naki bangaren a gani ko za a samu nasara a wanan bangaren. Don Allah zainab kiyiwa Allah kema kiji tsoron Allah ki gyara kada kiyi tsamanin Allah ba zai iya kamaki da laifin wanan sakacin ba. Irin wanan har sai mutum ya shiga wani hali ma dan uwa shi bai sanda hakan ba sai azo ana ganin laifi mutum daya. Hawaye nakeyi kawai zuwa yanzu nasiha sosai umma ta zaunar dani tayi min sosai a karshe tace in tashi in tafi gurin mijina mu gaisa. Hakana mike ba don naso ba na nufi hanyar fita daga dakin gwiwa duk sunyi sanyi sai faman sake saken yadda zamuyi arba dashi nakeyi bayan abinda na aikata masa din nagudu . Daki na shiga na dan kara gyara jikina kafin na fito zuwa kasa babu kowa a falon sai na,uran wuta dake aiki a lokacin. Dan fita nayi na hango su can a gaban gidan zaune su ukku saman fararen kujerun roba dashi da ya Uzaifa da mukazo tare sai wani da ban san kowaye shi din ba tare dasu lokacin. Gabana ne ya fadi naji tsoron hakan don ban amice da imanin shi ba har lokacin nan don tsoro nake jin kasancewar su tare da wani namiji dan uwana ko wani musulmi a yanzu. Wata zuciyane tazo min da magana tana fada min haba ya zai aikata hakan kan dan uwan ki komai abinsa ai yasan kunya. Tunanen hakan yasa na danji sanyi a raina na juya ba koma part dina ba tare dana je inda suke din zaune ba suna shan iska din. Zama nayi a daki ni kadai ina tunane ta yaya zan fara tunkaran yaya din kamar yadda umma ta umurceni dayi yanzu. Kawar da kunya da nauyi zanyi in sameshi kai tsaye cikin dakewa don haka ya zama dole in koyi yin hakan in jeraba in gani ko zan samu sauki a hakan . Kafin na koma tunane su mami kuma ta wani hanya zan bulo masu a yanzu don dai na kawar da irin tsana da bakin cikin da suke gwada min a fili. Shawaran umma dai din zan bi da tace in nuna ban ma san sunayi ba in dinga wayen cewa kawai idan sun min abu in daina nuna damuwana a kai. In nuna masu hakan bai dameni bani da dansu nake zaune bada su ba hakan zai kara jefasu cikin shakku da fargabana. A haka ina faman tunane har lokacin sallah magariba yayi na mike na gabatar da alwala na tayar da sallah. Ban fito dakin ba sai da nayi sallah insha,i na yi wanka na fito daga dakin dakin umma na fara shiga na gaida ita inda na samu an kawo masu abincin dare. Ban wani tsaya ba don tana zaune har lokacin tana lazumi na fita bayan mun gaisa kai tsaye part din shi na nufa . Gabana sai faduwa yakeyi haka na daure na shiga dakin baya falo na nufi kuryan dakin ban hango shi ba ma nan nabi dakin da kallo na dan lokaci yana gyare tsab kafin in juya zan fice daga dakin naji ance dani. Ki karaso mana zaki koma kuma nayi mamakin daga ina yake magana sai gashi ya juyo saman kujeran dake kallon window dakin nasa irin sofa din nan mai laushi yana kwance sama da tasbaha a hannun shi yana ja. Saida na dan kadu kafin in samu courage din fadin dama ba wani abu nazo yi ba zuwa nayi na gaishe ka da wuni naji ya jikin naka kuma ? Ina magana ina karasowa inda yake zaune din gefen kafan shi na samu na zauna ya dan ja kafan nasa kadan yana fadin. Naji sauki dama ba wani ciwo bane ai kinsan halin mami da rudewa ciwon kaine dole ta saka saida akai min karin ruwa jiya. Tafika damuwane da jikin ka don kai baka dauki hakan serious ba shiya sa su inna suna gaida kai sunce ace sun gode. Ni zan gode masu ai da suka dawo min dake lafiya aina dauka zaki dawo tare da Asabe ne ta kwana muna biyu nan ? Asabe kuma na tambaya a cikin mamaki yace eh ai yanzu irin su kin san hutu suke so da kulawa kullun naga tsohuwan tana ban tausayi wallahi. Ni kan ka rufa min asiri na dauko asabe gidan nan ace kuma na cika gida da yan uwana haka sa,adatu ma tazo da sunan kwana biyu hakan ya zama abin magana. Shiru yayi na dan lokaci bai ban amsa ba sai can yace amma nan dai gidanane ko ba gidan wani ba kuma yan uwan matane suka zo muna ai. To idan kana son tazo sai ka aika a dauko ta zaifi tunda yanzu ban zo da ita ba yace zan dauko su din ai ita da hjy su kwana muna biyu kafin tafiyan mu. Na kawar da zancen da fadin abinci fa yace tea na umurce su su hado min kafin in kwanta karfe tara na dare. Ba sai sun kawo ba tunda na dawo wanan aikinane yanzu ai na fada ina mikewa tare da fadin wani nau,i za a hada ma yace black tea na jinger. Na juya yake fadin bakya son hutu yanzu ke nan nace ai wanan aikin lada zanyi don nayiwa dan uwana dawainiya. Na fita ya bini da kallo kamar wace ya fara gani a ranan ko yana kallon wani abu a jikina. Kai tsaye kitchen na nufa a karo na farko inda na samu yan aikin suna gyaran kitchen din cikin girmamawa suka shiga gaidani . Na amsa ina fadin ruwa nake son hadawa oga shayi da sauri namijin ya taso yana fadin dama oga yace a hada mai zuwa nine akai masa. Ka barshi akwai hadin da zanyi mai na fada tare da juyawa zuwa dakina dauko abinda nakeson zubawa tunda Allah ya ban sa,an wanan ranan ke nan a kanshi duk da malam ya fada min ba matsala wurin hada mai din. Kamshi sosai na zuba sai ganyen shayin daya biyo baya ina tsaye har ruwan ya tafasa sosai kafin na juye na tace shi, na mayar a cikin flask.. Dakina na nufa da flask din wanka nayi na zauna tsab na gyara jikina na kawo hijab na saka na shiga wurin umma na samesu suna hira nake fadin idan akwai abinda suke so a tambayi fadila za a kawo masu. Na fito na kara gyaran jikina tsab da turaruruka a cikin hikima na shafa wani da malam ya bani dan mitsitsi dashi a jikina kamar yadda yace a ko wani sako na jikina din. Na gama na sanya wani rigan baci mai silk mai dan hannu pink clour da dan filawa a gaban rigan sai dan wandon shi iya gwiwa da dan tsaga a gefen kasan wandon. A haka na dauki kayan shayin zuwa part din shi na samu ya fito daga wanka yana saka jallabiya a jikin shi na aje kayan bayan nayi sallama ya amsa min . Ina ajewa wayan shi na kara ya dauka kai tsaye saman gadon shi na nufa na zauna ina hangoshi daga inda yake tsaye bakin seif din shi yana amsa wayan . A hankali na kwashi kafana dake zube na haye gadon da kyau gabana sai faduwa yakeyi don ban san abinda zai iya biyowa bayan hakan danayi mai ba. A yadda nasan ya tsanin hakan a baya in ba lokacin da baida lafiya ba har ya nemi taimakona a ranan bayan hakan ban taba yin gigin kawo kaina wurin shi ba haka. Idona na mayar na lumahe na fara jero addua a bakina ban masan wanda zan karanta ba ina dai yin duk wanda yazo min a lokacin ne. A haka yana karba wayoyin dake faman shigo mai a tsaye har ya hada tea din yana sha duk a tsaye din kafin ya koma bakin window dakin ya zuge ya mayar da hankalinshi waje. Idona na mayar na rufe wani tunane yazo min nasan a lokacin ji yake kamar yayi ihun ganina haka saman gadon shi ya san da manufa nayi mai hakan. Saidai a yanzu babu yadda zaiyi tunda yasan neman magana nake wurin shi kawai don yin hakan. A daidai lokaci cikin wanan tunanen ne barci ya soma satana don akwai gajiya a tare dani na tafiyan da mukayi a mota ranan . Kamar a mafalki nake jin muryab shi yana fadin zainab a nan zaki kwana ne ki tashi kafin barci ya dauke ki mana. Maimakon in tashi kamar yadda yace sai na gyara kwanciyana da kyau na fita batun shi dama nasan za a rina ga yin hakan. Saida ya dan dade tsaye a kaina yana kallona kamar yana nazarina kafin inji ya taka zuwa dayan bangaren gadon ya hau a hankali kamar mai tsoro ya da kwanta rabin kafafuwan shi a kasa. Kamar an zabureshi naji ya mike zaune na dan lokaci can kuma ya koma ya kwanta tare da daukan dayan hannun shi ya dora saman fuskanshi. A haka har barci ya dauke mu kowa da irin tunanen da yake a ranshi a lokacin nikan cike nake da tsoro da mamaki shi a lokacin. Tabbas malam yayi gaskiya don wanan abin nasa bana kai sake bane irin yadda naga yanayi a lokacin don kawai na zo inda yake a ranan na kwanta a kusa dashi yake nuna wasu irin halaiya na daban. Da a yan shekarun baya da suka wuce ne ina tsoron shi sosai gaskiya ba zan iya kwanciya a dakin ba ganin yadda yakeyi din nan. Amma a yanzu dana dan kara shekaru a tare dashi abubuwan nasa sun daina firgitani haka kai tsaye. Can a cikin barci nake jin kamar ana kokawa dashi na bude idona da sauri don gani meke faruwa dashi. Barcin shi yakeyi amma kuma kamar a wahalce yake a cikin barcin nasa sai dai yana faman juyi kamar yana faman fada da wani a lokacin. Allah ya taimakeni dabaran yin addu,a yazo min tun ina addua har na fara karatun kur,ani da karfi a fili. Sannu a hankali naga ya fara sakewa numfashin shi yana dawowa normal can ya sauke ajiyan zuciya kafin ya juya yana gyara kwanciyan shi. Tsoron kan naji shi a ranan gaskiya barci kuma ya kaurace min a idona gaskiya sai addua da tunane nakeyi lokaci guda. Kafin asuba barci ya dan daukeni sai dai abin mamaki har mukai sallah ya koma min kamar bashi bane yayi wanan abin a cikin dare sai gashi ya koma normal dinshi. Nikan sai ya barni cike da tunane a raina sai faman satan kallon shi da nakeyi har na fice daga dakin na koma dakina . Da kyat na samu nayi wanka don barcin da nakeji a lokacin riga na saka na fada saman gadon sai barci haka ya jawo ban samu fitowa da wuri ba ranan sai wajajen sha dayan rana na falka. Saidana shirya ne na fito don gaida umma sai na samu sun shirya wai dama ni suke jira un fito muyi sallama su zasu tafi. Da mamaki nake kallon umma tare da tambayan umma wani abu ya faru ne kuma take fadi cikin mamaki itama . Zainab mun dawo dake dakin ki lafiya kuma alhamdullahi ba, a samu matsalan komai ba a gun mijin ki to me kuma zamu tsaya yi yanzu ? Ai sai ya zama muna rashin hankali ko gamu har mu uku da yaran nan ai sai mijin naki ya daukemu mutanen banza kuma. Kedai ki daure kiyi duk abindana fada maki a naki bangaren da yardan Allah koma meye Allah zai sama maki mafita a nan. Umma zanyi kamar yadda kikace dani insha Allahu amma zancen tafiyan ku yau don Allah a fasa har zuwa gobe ko jibi sai ku tafi. Sam umma din bata yarda ba a karshe saina roketa su dakata har ya fito suyi sallama dashi don Allah bata soba dole dai ta yarda da hakan. Hira mukeyi niko sai tunanen abubuwa nakeyi a raina akan halin danaga yaya a ciki a daren jiya din nakeyi. Na tambayi kaina koshi yasa malam yake fada min sai na kara dagewa da addua da neman tsari nima a jikina ? Kuma har yake fadin yanzu kabar mutum a yadda kasan shi don bakasan ciki zuciyar shi ba ke nan ya tabbata dai yaya yana cikin wani kungiya kenan dai na asiri ko ? Sai misalin sha biyu ya shigo dakin suka gaisa nan umma ke fada mai zasu tafi dama shi suke jira ya shigo suyi sallama dashi su tafi. Bai boye mamakin hakan ba yake fadin haba mama aikwa bari zuwa jibi dai sai ku tafi din idan an shirya tafiyan naku ko ? Kai haba munzo munyi yadda ya dace tsayawan me kuma zamuyi a yanzu ko hakan ma mun gode kwarai da mutantamun da akayi. Ina gefe babu abinda nakeyi sai satan kallon shi ina zargin shi a raina tare da fadin watau shi dai ya tara abu goma da goma ke nan a rayuwan shi. Kai zama cikin kafirai baiyi ba wallahi don komai kama kanka idan ba Allah ya kareka ba sai ka bace hanya ke nan. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YA YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN YA ALLAH KA SADAMU DA RAHAMOMIN KA KA KAREMU DAGA DUK WANI ABIN KI ALLAHUMA AMIN, , , , YAR UWA KADA KI MANTA DA LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA AMIN BA TARE DA DAUKAN HAKKIN KOWA BA A KANKI, , , , , , Kamar yadda ya roki umma hakan ne yafaru don sun dage tafiyan nasu sai washe gari da safe zasu tafi din. Ina dakina kiran wayan shi ya shigo min na dauka yake fadin in sameshi a falon shi na sama. Banyi nawa ba ga hakan na sameshi shi kadai zaune ya tasa computer a gaban shi yana aiki ga cup din ruwan a gefen shi da yake sha. Idona na akanshi bayan nayi sallama ya amsa min ba tare daya dago kan shi ba har na karaso inda yake zaune din idona yana akanshi. Alokacin na kula da jikin shi daya tashi kamar yayi fada da wani yajin mai ciwo a haka nagaida shi da aiki na samu wuri na zauna daga gefenshi sai lokacin ya dago kai ya kalleni yana fadin. Gobe din zasu tafi ko nace eh baka basu hakkuri su dage tafiyan nasu ba dazun yace hakan zaifi kyau ai ga kudi nan ki dauka a basu dubu dari uku. Wanan kuma ku fita idan zaki iya ko kuma ki hadasu da fadila taje ta rakasu su sai tsaraba dashi. Na dago kai a cikin mamaki nake fadin an ko gode wallahi amma dai ban tsamani zasu iya kashe wanan kudin duka saidai su gyara motan su da ya uzaifa ke neman kudi dashi ya lalace. Jin haka yasa ya dago kai da sauri ya kalleni saina dan tsargu da kallon da yai min din naci gaba da fadin . Ina nufin tunda mahaifin su Nafisa ya rasu yan uwan shi da abokan shi suka kwashe abinda ya bar masu suke cikin halin wahala motan daya da aka bar masune yaya uzaifa ke dan haya suna samun abinci yanzu kuma motar ta baci sun shiga wani hali ko abinci yana masu wuya a yanzu. Zainab ke mai kikai msu akan hakan na dago kai da mamaki ina kallon shi don jin abinda ya fada din yace eh a matsayin ki na wace tafisu zarafi a yanzu wani taimako ya kamata ace kinyi masu. Nan ma dai shiru nayi ganin ya tsureni da idanun shi yasa nayi karfin halin fadin ni me zan masu kuwa nadai taimaka masu dana abinci a lokacin da nake gidan su. Nafisa kawatace ba yar uwata ta jini ba a makarantan da mami ta sakani a kaduna kafin mu dawo abuja muka hadu da ita ta taimaka min sosai a lokacin. Tun wanan lokacin take a raina don bazan iya mantawa da karancin da taimin ba a lokacin shine dalilina nazuwa gidan su a yanzu na nemeta. Ko a yanzun ma sun min karcin da ko wani dan uwana ba zai iya min haka ba don umma ta nuna tankar nice nafisa a wurinta ta sakani a hanyar daya dace kuma. Nasan da hakan ko baki fada ba don ba zai yuyu matana ta tafi surun da banyi bincike a kanshi ba in kyale ta. Na bincika nasan komai a kai don haka nake tambayan ki ai ya kamata ire iren su dake cikin wani hali kuma kina tare dasu in dinga sani don a taimaka masu ga rayuwa. Ba wai ki shiru a kyale mutum a cikin wahala ba haka irin su ba zan san da halin da suke ciki na bukatan taimako ba ai ga kuma suna a cikin bukatan suna kuma cikin makusantan mu a yanzu. Irin wanan alheri nakan so inyi shi saidai rashin sanin wa zan tunkara da hakan tunda bawai kusantan mu irun su sukayi ba. Bayan hakan ma ai banda wani lokaci a yanzu da zan san hakan har insan wani na cikin irin wanan halin. Yanzu ki basu wanan din ki bar ni zangana dashi yaron a waje inji abinda za a taimaka mashi dashi kafin su tafi. Da wanan ya duka yaci gaba da aikin da yakeyi a cikin laptop dinshi kawai bai sake magana ba kuma bayan wanan din. Kara dago kaina nayi idona ya sauka akan wuyan shi daya fi yin miki da yawa yana nuna kokawa yayi da wani ko wasu. Sai abin ya ban mamaki sosai don a iya sanina dashi dai bansan shi da fada ba ko daga murya saidai idan ranshi ya baci bai iya nunawa mutum hakan ba a lokacin da ranshi ya bacin . Har na mike ban bar tunane ba akan jin ciwon nasa sai faman tunanen inda ya samu miki hakan a jikin shi. Dakin da umma din take na koma suna zaune nima na samu wuri na zauna a gefen ta tare da aje mata sunjin kudin duka a gefen ta. Ta dago kai da sauri tana fadin na meye wanan kuma nace umma shi yace abaku kowa dari dari har yaya uzaifa. Wanan kuma wai ku shirya fadila ta rakaku kasuwa ku sayo tsaraba dashi na bata amsa duk suka kalloni kafin su juya kuma su kalli juna ita da yarta. Kai umma ta fara girgizawa kafin tace dani haba zainab ai wanan ya zama lalura kuma mu da mukazo neman lada za, a bamu wanan kudi haka ? Don haka dauki kudin nan ki mayar mashi kice mun gode don Allah da zumunci muka kawo masa ke badon wani abin hannun shi ba. Da sauri na tare da fadin a, a umma ko na mayar masa ba zai karba ba fada zai min kan hakan ko yanzu saida yayi min fada sosai kan zancen motan ya uzaifa dana fada mai ta baci. Kai ta dago ta kalli Nafisa dake daga gefe zaune itama Nafisa din da sauri tace wallahi umma bada wani manufa na fada mata motan yaya din ya baci ba a cikin hirane har muka dauko zancen lalacewar motar tashi. Yanzun dai na fahince ku so kuke ko mayar dani tsohuwar banza a cikin ku, ku bata min ladana da kimana a idon mijin ki ko ? Wallahi umma ba yadda kike tunane zancen yake ba sam ban roke shi akan hakan ba sai don kawai ya tambayani zancen uzaifa nake dan fada mai abindana sani game dashi kawai . Shine yake fada don me ban fada mai tun jiya ba yasan da hakan sai yanzu nake fada mashi zancen . Amma wallahi ba rokon shi nayi ba akan hakan na dan marairaice mata ta bini da kallo kafin tayi ajiyan zuciya tana kawar da kai gefe daya. Dakin yayi tsit a tsakani mu kafin ta dago tana fadin gaskiya hakan bai mun dadi ba wanan ai sai yaga kamar roko mukazo yi dama gunsa. Umma yadda fa kike zato sam ba haka abin yake ba Allah sam umma ban rokeshi ba ko kadan yadda na fada maki haka zancen yake. Idon ta ta kara saukewa kan kudin dana aje din a gabanta tace wanan kudin a gaskiya yayi yawa zainab don haka ki raba biyu ki mayar mai da rabi. Murmushi nayi na mike tsaye tare da fadin Nafisa nasan umma ba zata fita ba ki shirya mu fita anjima karfe hudu. Ina fadin haka na koma dakina don indan huta saidai tunane ya hanani hakan don a gaskiya zancen lamarin yaya ya fara daure min kai yanzu kuma. Tunanen irin fada da naga yanayi a cikin mafalkine ya dawo min a raina zubur na mike daga kwancen da nake tare da wani irin tsoro da ya ziyarci zuciyana a lokacin. Cikin kaduwa na mika hannuna inda wayana yake aje na fara neman layin malam kakana don in kirshi nayi sa, a wayan yana shiga don shi yace duk abinda na gani wanda ya fara daure min kai na kirashi don asan abin yi. Bayan mun gaisa ne yake tambayan ya muka isa nace lafiya kalau ya sake tambaya to ya muka kwashe nace baiyi wani magana a kai ba har yanzu malam. Saidai gaskiya naga wani abinda ya daure min kai dashine nan na koro mashi komai duk yadda abubuwan da yayi a barcin sa. Sai da na gama fada mai komai ya danyi shiru kafin yace dani dama na fada maki sai kin jajirce don iri abubuwan da zaki gani a yanzu . Don ko ke idan sun fahinci wani abu zasu iya juyowa gareki su farmakeki insha Allahu har in kin dage da addua ba zasu taba galaba a kanki ba da yardan ubangiji. Dasu yake fada a mafalkin don ga zahiri kin gani da idon ki idan zaki tuna a baya irin yawan mafalkin da kika dingayi a lokacin yanzu shine ya fara baiyana maki a fili zakiga zahiri saidai irin kallon da kike ganin mutumin na maki yanzu din kece zaki masa da yardan Allah. Mun kai wani lokaci da malan din yana min bayani kafin muyi sallama dashi ina masa godiya. Ajiyan zuciya na sauke tare da lumshe idanuwana lokaci guda abubuwan da nasha gani a cikin mafalkina a baya ke dawo min a raina. Dakin su umma kuma ina fita sadiyama dake kwance gefe ta daga tana fadin zanje in kwanta umma tunda ance za, a fita anjima. Sadiya na fita dakin Nafisa ta kalli umma din tana fadin umma hakan da ki kaiwa zainab baiyi ba sai ta dauka kamar da wani abu ai. Dole inyi fada Nafisa don na rasa abinda zan fada kan hakan iya gaskiyana ke nan don a yanzu kusan daya na daukeku a wurina don yarinyar nada hankali sosai wallahi. Ita din a yanzu wani haskene ubanguji ya kawo muna a rayuwan mu a yanzu ban san kalman da zanwa yarinyar nan godiya dashi ba a yanzu. Don ko wanan kudin kawai ya isa ya taimakawa uzaifa a halin yanzu na yarda alheri danko ne baya faduwa kasa banza. Kin taimaka mata a baya yanzun kuma itace take taimakon ki a yanzu da abinda yafi wanda ke kika taimake ta din. Umma a lokacin fa ba ma wani abu bane nake taimaka mata dashi sai dan abincin tara na da muke ci tare kuma in saya muna wani abu muci tare. Don haka kawai yanayin ta yake ban tausayi yasa naja ta a jiki muna yawo tare ko ina tare zaka ganmu har dai sukazo suka koma abuja da zama ga baki daya. Alheri Nafisa kona kwayan dabino ne sai ya rikede wata rana ya zama maka kamar girman zinari. Haka muka fita da yamma ina a cikin damuwa har umma na tambaya ko dan abinda tayi min ne na koma haka kuma ? Dan murmshi nayi tare da fadin umma ai ba afushi da zancen ku don kome kuka fada idan mutum ya kwatar da hankalin shi mai amfanine a garemu. Abubuwane dai kawai suke ban mamaki dan dawowan nan namu umma a game da yaya jafar din yanzu. Ina dai ba wanda zai iya illanta muna ke bane yar nan umma ta fada a dan razane. A, a umma lamarin fa dai ya shafe shi ne ni bai shafeni ba tace to Allah ya sauwaka daga haka kowa yai shiru a motan. Mun zaga sun sayo abinda suke so sai dai ba sosai ba don a karshe duk abinda suka nuna suna so basu saya ba nakan saya nace ya ban sha,awa nima. Mun dawo a gaji lokacin magariba ya yi mun samu ana sallah magariba bamu tsatsaya ba muma muka gabatar da sallah kafin mu shirya masu kayan su a wuri daya. Yau ma kamar ince yaya jafar yafi shan wuya a cikin barcin ko ince mafalkin shi don dambe sosai yayi a mafalkin nashi da kuma surutu da banjin abinda yake fada har saida na tayar dashi daga barcin nasa. Yana falkwa da kyat ya fara fadin bani ruwa in sha zainab ki taimaka min da ruwa sai kuma zufa da yake karyo mashi a lokaci guda ya jiki sharkaf duk da sanyin AC dake akwai a dakin lokacin. A cijin gigita na falka na nufi inda goran ruwa yake na dauko mashi ya kafa kai zuka daya ya zuke ruwan goran duka kamar wani mai cutar masha ruwa. Ni dai ina tsaye gefe na rugume hannaye ina kallon shi a cikin mamaki na rasa abinda zanyi mai a lokacin . Kamar an tuna min na shiga karanta mashi Amanal rasulu har zuwa karshe kafin naga ya koma ya kwanta lankwasa saman gadon yana sauke numfashi guda guda ya dafe goshin shi da hannun shi. Ranan kan naji tsoro kwarai da wanan abin dayayi a gabana gashi kuma na dauki alkawarin duk wani abinda ya sake faruwa dashi ba zan sake kiran mami in fada mata ba . Tunda tace kazafi nake son na kullawa danta don kawai in bata mata sunan zuri,anta a duniya nake fadin haka . Shiru ne ya biyu dakin na dan lokaci ina tsaye a kanshi na kura mai ido kafin inga ya sauke wani ajiyan zuciya ya gyara hannun shi dake saman goshin shi da alama kanshi ke masa ciwo sosai a lokacin. Hannuna nakai a hankali saman kafada shi jin hakan yasa ya sauke hannun nasa da sauri ya kallo inda nake tsaye ya sauke idon shi akaina. Meke damun ka hakane yaya ko baka da lafiya ne baka fadawa kowa ba matsalan dake damun ka kada yai ma yawa a hakan. Murmushin karfin hali naga yayi tare da dan jan jikin shi ya koma baya yana fadin koma ki kwanta abinki ba abunda ke damuna mafalkine kawai nayi. Ka dinga addua idan zaka kwanta zaifi akasari idan mutum ya kwanta ba tare da addu,a ba hakan ne yake faruwa dashi. Nagode ya fada tare da juyawa kamar wanda baison ganina a lokacin don haka na gane na zama mai karfe kafa a yanzu ke nan. Juyawa nayi side din da nake kwance da farko na koma na kwanta ina karanto muna addua a fili ta yarda har yake iya jin abinda nake karantawa. Haka dai muke kwance ba wanda ya iya komawa barci a lokacin ganin shirun yai yawa na mike na shiga bandaki na dauro alwala na fara gabatar da Nafila. Ko me ya gani yakai kusan rabin awa naga shima din ya mike ya nufi ban dakin ya dan dade a ciki kafin ya fito daga ciki da alama alwala yayi shima yazo ya fara sallah. Saida akai kiran sallah muna zaune shiya fara mikewa ya sake dauro alwala kafin nima nabi bayan shi . Ina idarwa ban tsaya gaidashi ba na mike zuwa dakina na kwanta don barcin da nake ji sosai a lokacin. Barci ne mai nauyi ya daukeni can cikin barcin nake jin ana ja min kafa hakan yasa na bude idanuwana da kyar don ganin mai tayar dani din. Da kyar na iya bude idona shine tsaye a kaina yana saye cikin kaya irin na motsa jiki kamar bashi bane ya wahala a daren jiya din haka ? Ki tashi kada kisa su makara rana ya soma yi ya fada yana tsaye a kaina zan tashi na fada ina gyara kwanciyana don barcin bai sakeni ba. Ya kara fadin zaki tashi ne fa don sun shirya nake ganin tun dazun haka yasa dole na mike ina mamakin shi a raina har lokacin kamar bashi ba . Mota nan waje da zasu tafi dashi munyi magana da yaron zai kawo min takardun shi in duba inda ya kamata a sashi ya fara aiki. Da sauri na mike zaune don jin abinda ya fada nace a cikin mamaki mota yaya eh ya tafi dashi ya fara amfani dashi. Ganin na tashi yasa shi ya juya ya fita daga dakin nabi bayan shi da kallon mamaki ga mutum har mutum a fili amma ya samu rauni ga imanin shi. Yanzu wa zan fadawa wanan maganan ya yarda dani a yadda muka kwana dashi a daren jiya a wahalce dashi har a yarda da abinda na fada yadda ya mike haka da safe. Gashi gari ya waye ya mike tangararam kamar wani abu bai faru dashi ba haka a daren jiya din don haka yanzu dai ya tabbata a zuciyana shi din yana wani kungiya ke nan na asiri ko wani abu na boye da mutane basu sani ba ? Wanka na shiga na fito na shirya tsab kafin inje dakin umma din na samu har sun karya fitowan mu kawai suke jira a lokacin. A, a wai har kun shirya kome na fada ina kallon nafisa dake zaune a cikin shirin ta . Tace fitowan ki kawai muke jira mu da yanzu munyi nisa kinsan yau umma nada ganin likitan ta ai. Gaskiyane na fada ina kawai tsugune kasa don gaida umma din a cikin ladabi da biyayya ta amsa min da dan fara,anta a fuska don jin dadi. Ita a zaton umma din abubuwa sun fara kamkama a tsakani da yaya yanzu don haka takw ganin hikimar ta yayi na cusani a gareshi datasa inyi don dole. Saidai da ace a lokacin umma tasan kusantan shi da nakeyi yana sashi shiga cikin ukuba a kullun na kwanta a kusa dashi da bata umurceni da yin hakan ba a lokacin. Don wanan zuwan da nake daki shi ina kwana a kusa dashi da nakeyi ashe yana cikin dokan su yin hakan garesu su kusanci mace ko numfashin mace a makwanci daya su da mace dokane a gare su Wa, iyazu billahi asirin ma kanshi wahalane kawai a cikin sa ga dan mami na cikin fitina da masifa daya jefa kanshi. Amma ita mami din mulki da giyan duniya ya hana mami ta kwantar da hankalinta ta fahinci komai a lokacin. Bayan mun gaisane nake fadin umma yace in fada maki mota na nan da zakuyi tafiya dashi ga makulin motar yace abawa yaya uzaifa ita nasa ne yabashi. Yar nan me kike fada kuma bayan wanan alherin da kuka cika mu dashi a baya sai kawai ta fashe da kuka lokaci guda. Dakin yai shiru haka ya sakamu muma dake dakin a lokacin sake hawayen daga idanuwan mu sai umma ta bude baki kamar zatayi magana sai kuma ta kara fashewa da kuka mai ban tausayi. Fadilace da a yanzu take wani ja da baya damu bata sakewa tun dawowan mu na kula da hakan a gareta ta shigo dakin don ta fada muna yaya Uzaifa yaja falon yana jiran fitowa su umma. Ta samemu a cikin wanan halin na kuka ba maiwa wani magana taja ta tsaya tana kallon mu a cikin mamaki. Kafin ta bude baki tace haba hjy koma mene ai bai kamata ke ki sare masu gwiwa ba don kukan ki dole ya sakasu a wani hali haka. Yar nan dole in kuka wanan alheri haka kamar kaika haifi mutum banda baki godiya kukan nan kawai zan iyayi a yanzu. Mama kiyi hakkuri don Allah haihuwane mai akbarka kukayi shi ya jawo maku wanan yanzu. Da ace kun haifi wata ba zainab dake da sanin ya kamata ba da duk wanan alheri baku sameshi ba hakkurin ta da dauriya ne ya jawo mata hakan. Hakane yar nan dadin haihuwa mai albarka ke nan gun iyayye duk wata uwa tsakanin ta da danta tun yana ciki shine adduan samun mai albarka dama. Haka dai ta samu ta lalashi umma har suka fara shirin tafiya a falo suka tsaya jira shi ya fito suyi ban kwana dashi. Sai gashi ya fito a cikin shirin shi na bakaken suith a jikin shi yana cikin ujula yana sauri ganin su yasa yaja ya tsaya suka gaisa. Nan umma ta shiga mashi godiya bai tsaya ba yace haba ba komai umma na fadawa uzaifa ya dawo wani sati ya sameni nan kafin mu koma. Kai Alhaji dawainiyar yayi yawa ba mu kadai bane wanan irin alherin haka ubangiji Allah ya saka da alheri kuma ya baku masu rama maku nan gaba ya hadaku da zuri,a masu albarka aka amsa da amin nikan a cikin zuciya na amasa hakan. Yan uwa ina mika sakon ta,aziyana a gun yan uwan da sukai rashi a cikin satin nan ubangiji Allah ya gafartawa musulmi yakai hasken rahama a kabarin su amin ya gafartawa duk wani musulmi daya kwanta daman shi Allahuma amin. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMUTULLAH YAN UWA FATAN ALHERI A GAREMU BAKI DAYA ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN, , , LITTAFIN KUFINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA YAR UWA DON GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , , , Naga maki da al,ajabu a cikin yan kwanakin nan don ranan dasu umma suka tafi ranan munyi barci a tsaye a dakin don ni kaina tsoro aka fara bani ina tsaye da kiran Allah. Saidai abinda ke ban mamaki a yanzu shine a lokaci yaya zai koma kamar bashi ba amma in gari ya waye sai ya dawo min mutum daidai kamar bashi bane muka kwana a raye yana min saddabarun a cikin dare. Sai gashi gari ya waye ya koma kamar bashi ba da zarah biyar tayi daidai lokacin da za,a fara kiran sallah ya fara samun sauki lokacin gari ya fara wayewa ke nan. Ina kula da hakan tun fara kwanana a dakin shi a daidai wanan lokacin ne yake samun natsuwa ya koma normal kamar kowa. Kamar kullun dakina na nufa ina idar da sallah ban tsaya jiran wani abu ba na haye gado sai barci a ranan nayi barci sosai. Don ban tashi ba sai after one na rana koshi nasan don sabo da lokacin sallah ne duk inda musulmi yake da zaran wanan lokacin yayi zai fara ji a jikin shi. Wanka na fada kodana fito time din yayi har ya gwauta a gurguje na tayar da sallah din don makaran da nayi. Ina zaune ina shafa mao a gaban mirrow dakina ya shigo dakin a cikin madubi muka hada ido dashi nayi saurin dukar da kaina a kasa. Kin tashi ke nan ai na zata har yanzu din barci kikeyi baki tashi ba da zance dake kada ki kwana a dakin sai ki dauki hakab da wani manifa a zuciyar ki. Ko yanzu din da idona ya gane min gaskiya bashi zaisa in fasa kwana a dakin ba komai shedancin mutum dai ai Allah ya fishi. Gaskiyane amma kuma Allah baice ki kusanci abinda zai iya ja maki illa ba ai zuwana biyu dakin nan kina ta barci baki tashi ba. Idan har zan samu barcin da rana inyi na daren ba damuwa bane matukar addua akan hakan zai muna tasiri ai. OK ina maki fatan alheri ga hakan na ce amin kamar a fusace ya sake dan murmushi ya juya zai fita daga dakin sai kuma yaja ya dakata yana fadin. Zan so tunda kin fara fahintar hakan kiyi nisa dani kamar yadda na umurce ki dayi tun farko kada ki jefa kanki ga halaka. Ban fahinta ba nace a cikin mamaki na juyo da sauri ina kallon shi kafin in ce dashi. Ke nan hakan na nufi in barka har abada ko me don magana kayi min a dunkule wanda na kasa fassara ma,anan shi yanzu ? Da zaki dauki shawaran da zan baki zaifi maki sauki a rayuwan ki ki zauna kamar yadda na umurce ki da nisantana tun farko. Saida na sake wani irin laulausan murmushi a fuskana na mike tsaye na fuskan ce shi a lokacin saboda tsaban rudewa na manta da daura gaba nake tsaye a gaban shi don yadda nake ji nace. A yanzu idan har zanyi hakan dayan biyune zai biyo baya kodai na nisance ka har abada ko kuma kai din da kanka ka rubuta min takarda shedan ka sakeni in koma wurin iyayyena da zama. Shima murmushin ya mayar min kamar yadda nayi masa da farko yace kina ban mamaki a yanzu da wanan taurin kan naki zainab. Idan wani ya fada min ke din zaki iya hakan a baya zan iya mussanta masa hakan akan bai fahince ki bane ya fadi hakan. Zaka iya fadan komai saidai amsan bukatana nake saurare a yanzu don hakan nima ya isheni don ban san a matsayin da nake a zuciyar ka ba har yanzu. Zaki iya fadan komai a yanzu zainab mutukar ba zaki daukeni a matsayin makiyin ki ba dai yana fadin haka ya juya ya fice rai bace. Na bishi da kallo ban san lokacin da wani irin kuka yanzo min ba lokaci guda don takaici bakin gado na koma na zauna ina hawaye ni kaidai. Sai faman tunane da nakeyi na yadda mutane su a wajen su suke min kallon wace ta dace da mijin aure . Basu san cewa ABU A CIKIN DUHU SIRINE BA da ace zan zauna in fada wa wata irin rayuwan tashin hankalin da nake ciki tun shigana gidan sa da mata da yawa sun gane ba daula ne arzkin da mace ke cikin shine zamana jin dadin aure ba a yanzu. Eh nasan da yawa kan sun dace amma akwai irin mu da ke cikin jarabtan aure ta hanyoyi daban daban a duniyan nan. Sai dai muce ubangji Allah ya kawo muna dauki ya fitar damu da ma wa yanda basu shiga ba amma yana zane a kundin kaddaran rayuwan su sauki. Na gaji da kukana ni kadai na kuma ba kaina hakkuri na mike na saka dogon riga haka kawai naji zuciyana yana son kiran maya a ranan. Duk da zuwana Nigeria na kirata sau biyu mun gaisa take fada min cewa ta samu aiki a wani karamin company yanzu ta fara aiki a nan. Saida kiran ya kusa katsewa ta daga tana fadin inyi hakkuri bata kusan da wayan ne a lokacin. Mun gaisa nake tambayan ta aikin ta da iyayyen ta ta amsa da kowa lafiya aiki kuma tana nan tanayi saidai wurin bai mata ba idan ta samu wani zata canza. Nake dan bata hakkuri akan tayi hakkuri dashi for now don ta rage zaman banza hakana tace hakane. Ya kuke ina mijin ki da sady nace suna lafiya ta kara jefo min tambayan dake cina a raina tace muryan ki ya nuna min cewa kinyi kuka yau zeey ? Dan murmushi na sauke har tana iya jina a lokacin naji tace why zeey why da zaki zauna kina kuka akan abu daya kullun. Nasan dai a kan halin sane kike kukan naki ko zee nace a cikin muryan kuka maya kasheni yake son yi kawai nan dai na fara kora mata labarin komai da ya faru zuwan mu gida. A karshe ta ban hakkuri tana fadin in bari idan taje gida zata kirani muyi magana yanzu tana wurin aikintane. Mukai sallama da ita na kashe wayan ina ajiyan zuciya na mike na nufi hanyar fita daga dakin dakin sadiya na fara lekawa bata cikin dakin . Na nufi falo kai tsaye don nasan tunda ban ganta a dakin ba tana falo ke nan a nan na sameta zaune tana kallon wani film. Kallon ta nayi watau sadiya dai sai gyara Allah ranan da wanan daulan ya subce muna muka koma gida da zama. Don duk dabi,un ta na diyan masu kudine ita ba zakace gidan mu ta taso ba a lokacin saboda irin rayuwan da na hango a gareta. Har na karaso kusa da ita bata sani ba jin takon mutum ta juyo da sauri tana fadin lah anty ashe kin tashi na shiga daki kinata barci. Remote na duka na dauka saman table na kashe tv ina fadin tashi kije kiyi sallah kada in saba maki yanzu na fada rai bace. Ganin ba wasa a fuskana don wani lokaci mukanyi wasa har da kokawa a tsakanin mu idan mun bushi iska a tsakanin mu. Wanan karon kan babu wanan sakin fuskan a gareni don haka ta mike tsam tana turo baki ta bar falon. A hankali na juyo bayan na gama binta da harara ina sake ajiyan zuciya na kai zaune dan table din dake kofan na jawo na dora kafana . Ko zanji dadin zama a hakan ta hanyar mike kafafuwana saman dan stole din na dora hannuna saman fuskana . Ina zaune shiru ban motsa ba ban kuma kunna tv ba don komai bana jin dadin shi a lokacin sai wani tunane yazo min. Tambayan kaina nayi wani makusamcin shi zan fadawa damuwana ne da zai duba min wanan zancen Amsa naba kaina da fadin ya mamud shi ya cancanci in fadawa don yasan halin da dan uwan shi yake ciki a yanzu. Na dawo naba kaina amsa da kaina da fadin in kuma na fada mai ai kamar na tonawa kaina asirine kuma. Hujja dai iyayyena suke so a gareni ko yanzun kuma ina da babban hujan da zan basu ai akanshi. Zancen mu da innan mu ya fado min a rai da take fadin nayi hakkuri na zauna dashi ko dan mahaifiyar shi da basu sona dashi ya nace min. Da wanan bakin nacin ai gara shima ya kini din zaifi min dadi na bawa kaina amsa ni kadai muryan fadilace ya katseni tana fadin . Ashe kin tashi lafiya dai kike ko nayi mayawa da mayanni don mu gaisa kina kwance. Hannuna na sauke ina fadin lafiya kalau nake take fadin an wuni lafiya abinci har yayi sanyi baki karya ba. Barci ne ban samu sosai ba a dareb jiya yasakani wanan barcin dan ruwan zafi zan kurba ya isheni koshi hanjina nake son ya bude. Ta juya da sauri bata jima ba sai gata da kayan shayi ta hado min ita da kanta ta hada min komai nace nagode har ta juya zata wuce nake fadin. Ya yaran ki kin samu lekasu kuwa jin haka yasa ta juyo tana fadin ko gafarceni don Allah nasan kinsan komai a kaina don oga ya fada min maganan daya girgizani a ranan. Na dago da sauri ina tambayan ta akan mefa don bansan abinda kike magana a kaiba yanzu ? Kai ta dukar kasa sai naji wani iri naci gaba da fadin indai akan matsalan mune ki barshi kawai dani don yanzu ba da bane nasan ciwon kaina a yanzu. A hankali ta dawo inda nake tana zama take fadin zan fada maki magana daya zainab ko ki yarda ko kada ki yarda Allah ya sheda har cikin raina gaskiya daya nake fada maki. Sai tayi shiru kafin tace dani duk yadda kike ganin munin halim mijin ki zainab ki hakkuri ki zauna dashi hakana da halinsa. Duk da nasan a yanzu ba lalai bane ki yarda da zancen da zan fada maki din don kin san koni waye a wuri ku yanzu tynda mijin ki ya sani ya kuma fada min yasan zamanan aikin da nakeyi gidan nan tare daku. Jin hakan na dago kai na dan kalleta da mamaki don jin abinda ta fada din a lokacin a raina nace ke nan ya jafar ya sanar da ita mun san zaman da takeyi a tare damu ke nan. Tace haka ba zai hana ni zama daku tsakani da Allah ba zainab don ni musulmace kamar ku ba zan taba bada shedan karya akan abinda banga makamancin shi a wurin ku ba gaskiya. Nazo nan aikine bisa zargin da akewa mijin naki da yin fasa kwari da sauran abubuwa na rayuwa don gani shi da da mahaukacin kudin da kasa suke zargin shi dashi. Sai dai zamana din don bincike a cikin ku zainab na gano mijin ki tsayayyen mutum ne wanda ya tsaya da kafan shi wurin nema ya kuma dage da aikin shi kuma da kafafun shi yana neman na kasa ba kamar yadda ake tuhumar shi din ba. Yawan kyautatawan ku gareni yasa ni kaina na fara zargin hakan kafin in binciko komai na gane gaskiya . Yanzu nazo maki nan ne a matsayin yar uwa kuma aminiya kamar yadda kika rikeni a baya a matsayin yar uwa kuma aminiya saidai yanzun da kika san koni din wacece ba ki dauke hakan ba ayanzu sai dai duk da hakan. Zanso kiyi hakkuri ki kuma kara hakkuri ki zauna da Jafar har abada a rayuwan ki don shine kawai yanzu mafita a gareki da rufin asirin ki. Zainab abinda baki sani ba shine kina fita gidan jafar kema kanki mutane zasu kyamace ki idan kowa yasan irin rayuwan da kika guda a gareshi har ki barshi. Sai zargi ya fara yawo a zukatan mutane a kanki cewa ta yaya kika zauna dashi na tsawon wanan shekurun a cikin wanan halin nasa ? Kaina dago da sauri na kalle ta tare da zuba mata ido don jin abinda ta fada zai iya faru game dani nan gaba idan nace zan bar gidan shi tace eh haka zancen yake gaskiya a wurin mutane. Shi mutum dan tara ne bai cika goma ba kowa da kike gani yana da nasa kalar jerabawan rayuwa da Allah ke dora mashi sai idan Allah na son kane . Karshe sai ya yaye maka wanan jerabawan ta hanyar sauki da lumana Allah ya jefoki a rayuwan mijin kine do ki taimaka masa kuma kina taimakawan ba laifi. Don ba ko wace mace bace zata zauna tayi hakkurin shekaru kamar yadda kikayi zainab don koni din da nake magana ba lalai bane na iya hakan. Nasan jafar yana da rauni duk da baki fada min ba nasan komai don kin san aikin mu bawai kawai saka ido bane ga binciken da mukeyi akan mutum ba kawai mu leki asirin aikin daya kawo mu wurin mutum mu barshi. A, a komai daya shafeka sai mun gane a lokaci guda a irin hakane na gano mijin ki ba mai sha,awan mata bane shi a rayuwan shi. Zaman turai da kuma miyagun abokai ya bata rayuwan mijin naki da kuma asiri irin namu na bakaken mutane ya bata rayuwan shi duk da hali irin na kyautatawa nasa. Sai da ya samu akasi a rayuwa yana wanan aikin da ko wani addini da al,ada bai yarda da irin wanan fasadin ba a doron kasa. Ki godewa Allah daya nufi mijin ki da samun rayun shi a yanzu ga daina wasu halaiya nasa masu muni da yakeyi a baya can . Duk da mahaifiyar shi ce ya dace tayi hakan amma ta kasa tsayawa ta duba rayuwan dan nata sai shirme da zugan mutane da ke rudin hankalin ta. Hakkuri gareki zainab shine mafita a yanzu don ki girbi wahalan ki da hannun ki idan kinyi sake kinaji kina gani sai watace zata zo daga baya taci gajiyan wanan hakkurin naki a gaba. Nasani zainab mahaifiyar mijin ki na kokarin shirya yi mai aure don a ganin ta ke din baki cancanci zama da danta ba haka matsayin ki dana iyayyen ki baikai na yadda take son matan diyan ta su kasance ba. Na dago kai da sauri na dan kalleta again tace yes zainab wlh bawai hjy mami bata son ki bane a, a wanan ne kawai ya kawo maku rashin jittuwa a tsakanin ku da ita . A gabana gidan nan kwanaki dan uwan mijin ki yazo da wanan zancen gidan nan yana fadawa mijiki abinda mahaifiyar tasu take kulla mai wai zata aura mai wata a dole don kare martaban shi. Sai dai amsan da ya bayar a lokacin shi ya wadatar dani a lokacin na kara sanin kina da tasiri matuka a zuciyar shi. Sai gashi daga baya kuma kina neman ki bada wanan kafan a garesu suyi yadda suke so a kanki. Don duk da sanin halin danta da tayi kin san ance uwa bata taba ganin laifin danta kome akace ya aikata zataga sheri ake masa don tarbiyan data bashi ita kadai tasan halin shi. Wanan matsalan ke damun wasu uwaye a yanzu da basu tsayawa su natsu su san yanzu da zamani komai ke tafiya a yanzu. Duk da nasan sheri shedan ne da har ya rudeki kike ganin bari gidan nan shine mafita a gare ki da har zaki iya gudu ki bar dakin ki wata tazo ta gaje daga baya. Kada kiyi mamakin yadda nasan hakan duba da irin shakuwan dake tsakanina dake a baya yakai har mijin ki yake zargin nasan wani abu a game da tafiyan naki . Shine ranan ya titsiyeni a nan falon yake min warning kan na fada mai inda kika shiga a kasan nan kika boye ? A lokacin gaskiya hankalina ya tashi sosai da jin haka da nasan zaki aikata hakan da na baki shawaran karki soma yin hakan a yanzu. Inda na kara tsorata da zancen sai nake ganin suna yawan shigowa gidan nan akai akai na gane hakan da takeyi na son cusa mashi wani manufane na daban a lokacin. Sai gashi Allah ya gyara kin dawo kwatsam a lokacin da kowa bai tsamaci hakan ba da zaki dawo a kan lokaci ba tare dana waje sun fahinci komai ba. Ko suma na gidan kansu ya daure da ganin kin dawo salin alin duk da akarshe hjy mami cewa tayi kwadayine ya dawo dake gidan nan ai. Ido na lumshe dama nasan zata fadi hakan a kaina koda banji haka a bakin fadila ba din nasan abinda mami zata fada ke nan kan dawowa na din a lokacin. Ta dan motso kadan daga inda take zaune takai kai hannun ta saman gwiwana ta dafa haka yasani bude idanuna dana runtse a lokaci guda don takaicin kalami mami a gareni da nake ji a lokacin har kasan raina. Hakkuri zakiyi zainab kowa da irin tasa kaddaran a rayuwa wata kila Allah ya jefoki a cikin sune don ki zamo masu haske a nan gaba ita bata sani ba ta tsaya tana hauka a yanzu. Ki nuna komai bai dameki ba zainab kibar nuna bacin ranki haka a fili don ko zaman da kikayi nan na fahinci abinda ke damun ki ke nan yasa kikaji ina maki wanan bayanin haka a yanzu. Nasha fada maki ke di mace ce zainab kin kuma nunawa duniya ke mace ce don kinyi amfani da iliminki na mata gashi yau har kin kai ga taka nasara akan shi kin rabashi da wasu halaiya masu muni a rayuwan shi. Koya sani a yanzu ko bai sani ba shi da duk wani nasa dole a karshe zasu san hakan da cewa ke din ce haske a garesu kinyi namiji kokari sosai kiris ya rage ki kai ga in ma nasara ki akan komai da yardan ubangiji. Tana fadin haka ta mike tare da fadin ni zan tafi don yan kwanaki ya rage min a gidan nan zamana ya kusa karewa daku tynda na gama hada abinda nazo samu a wurin ku din. Sai dai ina fatan zaki bi shawaran dana baki din kiyi amfani dashi don Allah kada ki bari kowa yasan zaman da kikeyi a gidan nan yanzu a bar ABU A CIKIN DUHU YA ZAMA SIRIN KA KAI KADAI. Tana fadin haka ta juya zata tafi da kyar na iya budan bakina nace mata nagode anty bayan hakan ban kara furta komai ba akanshi. Hanyar kitchen ta nufa na bita da kallo a inda nake zaune ina mamakin wasu zantuka da tai min yanzu din a karshe. Tabbas ABU A CIKIN DUHU din ne kuwa zama a gidan yaya jafar din don mutane na min kallon jin dadi da samun duniya a gidan shi yanzu. Ni kuma ina zaman hakkuri da danne zuciya akan tayuwan wani don duk wanan hangen da mutane suke min bashine a gabana ba yanzu. Zakaji duk wani na tare dani zai ga kamar don abinda mami din take min ne nake son barin gidan a lokacin har iyayyena da suke ganin wanan ne ya tayar min da hankali har nake son yiwa jafar din sheri akan wai baya kwana dani. Kwana dani ba shine a gabana ba mutane sun ki su gane hakan a gareni maganan fadila din ne don ya zama dole inyi hakkuri in bar zancen a raina koda hakan shine ajalina a gidan nasa. ZAINAB IDRIS MAKAWA JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMI UBANGIJI ALLAH YA SADA MU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMIN. YAR UWA LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA VIKIN SALAMA DON KARUWAN KANKI DA KANKI YAR UWA, , , Kamar yadda maya tayi min alkawarin kirana karfe takwas na dare ina daki zaune saman sallaya ta kira layina din. Na dauka muka gaisa take fadin yanzu haka tana gidan kakarta don yadda tajini a dazun bata ji dadin haka ba. Da yake video call mukeyi da ita ta nuna min fuskan kakar nata a screen din wayan ta tsohuwar take murmushi ba yaren su nake ji ba don haka na daga mata hannu alaman gaisuwa a gareta . Bayan mun gaisa din takewa maya yare mayan ta kalloni tana fadin wai me ye damuwana a yanzu ido na dan lumshe kafin na sauke ajiyan zuciya na fara ba maya din bayani ita kuma tanawa tsohuwar kamar yadda nake fada mata. Daga ta bata fuska sai ta dan kada kai tsohuwar keyi don jin bayanin da nakewa maya din. Saida na gama ta fara magana tana dan tafiya a duduke zuwa wurin da take aje maganin ta ta dauko ta juya tanawa maya magana. Maganin naga maya ta amsa a hannun ta tana nuno min tare da fadin wai ki duba irin wanan maganin ta baki irin sa kwanaki. Shi zaki dauko kiyi amfani dashi a yanzu ta bude maganin tare da nuna min shi sosai a screen din wayan ta nace nagane. Ta sake fadin zaki jika mai a ruwa har sau uku daga nan ki bar bashi sai tsohuwar ta katse ta da bayanin da takeyi din ta fara magana tana nuna mata wani farin garin magani dake hannunta. Nan dai sukayi min bayanin komai na yadda zanyi amfani da magugunan data bani a kwanaki da na tafi masu sallama zamu dawo Nigeria. Don ni na barsu kenan a nufina bazan sake komawa kasan chaina din ba kuma a yadda na yanke a zuciyana. Bayan mun gama wayan ne dasu ba nufi wardrobe dina ina binciken inda na aje maganin da tsohuwar ta bani din. Suna ajiye kamar yadda na ajesu daya bayan daya na duba ko wani na dauko na dawo bakin gado na zauna ina kallon maganin. Can kasan zuciyana nace Allah kaga nufi a kan hakan banyi don na raina ma yin ka ba ya Allah ka gafarceni akan hakan idan na saba maka . Kasa wanan karon iyakar wahalance ga hakan kasa mu dace da nasarorin ka ya Allah na fada ina shafa hannuna a fuskana. Tashi nayi daga inda nake zaune din na nufi inda wasu cup suke ajiye na dauko tare da goran ruwa na zauna a inda na tashi din. Ruwan na fara zubawa a kofin na daga tare da karanta fatiha kafa bakwai a cikin sa don ance kome ke damun ka fatiha na maganin sa da yardan ubangiji. Na kawo garin farin maganin na dan zuba a cikin sa kadan na fara karkadawa kafin in daga in kai bakina da bissimillah. Na gama duk yadda ta fada min din inyi bayan na kamallah na koma na kwanta saman gadona ina mayar da numfashina a hankali. Ina nan kwance ido a rufe naji an turo kofan dakin an shigo na bude idona a hankali sadiyace ta shigo tana fadin anty kin kwantane da wuri haka yau. Zan tashi yanzu na bata amsa ina mikewa tare da fadin kin ci abincine tace min bata ciba muje yanzu muci na fada a daidai lokacin dana sauko saman gadon. Mun zauna falon ke nan ya shigo fuska a daure nice na fara mashi sannu da zuwa wanda hakan ya bashi mamaki don ya dauka a yadda muka rabu da rana ina cike dashi a ranan. Haka yasa yaje gidan mami ya zauna abinsa ya yini a can bai dawo ba sai wanan lokacin daya shigo gidan. Duk da hakan bai tsaya a falon ba ya nufi part din shi kai tsaye bayan ya dan tsaya yana amsawa sadiya gaisuwa tare da tambayan ta tana lafiya ? Baifi yan mintuna a tsakani ba na mike tsam ina fadin sadiya ina zuwa na nufi part din nasa nima. Na sameshi tsaye a tsakar dakin yana cire rigan jikin shi na karaso inda yake ina fadin yau ina ka shiga har wanan lokacin ? Ina gidan mami ya bani amsa kai tsaye a yadda yake amsa min din naji ba dadi gaskiya saidai na hade hakan a raina na kara takowa har inda yake ina fadin . Suna lafiya ya yaran ya mamud basu zo badai gidan nan har na tambaye shi don rasa na fadi a lokacin . Kema kinsan uwarsu ba zata bari suzo gidan nan ba din har yanzu fushi takeyi dani bata zuwa ko naje gidan. Ikon Allah me yai zafi haka a tsakanin ku ta dauki fushi dakai haka hummm kawai yace yana kokarin wuceni ya shiga bayi. Ya kai kofan bayin duk a cikin daurewa nake fadin mu jirakane ka fito muci abinci na tambayeshi don karfin hali don kawai in nuna mai yanzu ba haka zancen yake ba a guna. Naci abinci gidan mami a koshe nake ya fada yana shigewa bayin kai tsaye nabi bayan shi da kallo. Kafin ajiyan zuciya ina mai jin zafi a raina tare da tunane nabar dakin nasa watau mu mata a zalunce mu kuma mu koma bi da biyayya garesu Allah sarki diya mace ubangiji Allah kaiwa mata rahama albarkacin Annabi Mohammadu sallalahu alaihin wasallam. Falo na dawo na zauna a dinning muka fara cin abincin da aka shirya na dare don mu a gida. Mun gama hira muka danyi kafin kowan mu ya mike zuwa part di shi har lokacin banga ya leko mu ba . Haka yasa na gane cewa bazai fito di ba ke nan yake nufi ina shiga daki na fada bandaki nayi wanka na fito na shirya tsam kafin in saka rigan barci na dauki abinda kakan maya tace min in shafa bukata kawai ko bai shafa bashi yaji kakshin shi dab a hancin shi dai kawai ko hakan ya wadatar. Sosai na mulke jikina da maganin nabi da dan turare a sama saboda kar kamshin maganin ya tashi sosai. Na dan dade a zaune ina tunanen hanyar da zabibsakon ya isa a hancin shi duk da nasan abune mawuyaci yin hakan garemu a yanzu. Can dai na daure na mike na dauki hijab din sallah na na dora saman jikina kamar yadda na saba yi idan zan shiga part din. Bakina tab da addua kamar kullun na nufi part din nasa kofan yana bude har lokacin na shiga jna rufo kofan a hankali nasaka key narufo kofan. Kwance na hango shi rigingine ya na saye da jallabiya a jikin shi ya dora hannu a fuskan shi kafaduwab shi suna a harde yana dan kada su a hankali. Duk da nasan ba barci yakeyi ba a lokacin hakan bai hanani tafiya a hankali ba motsi ba na karaso har baki gadon da yake kwance din sama. hankali nakai zaune saman gadon har lokacin ina kan adduan da nakeyi a lokacin na gama na tofa tare da shafawa a jikina nayi bissimillah na hau gadon da kyau tare da dan jawo jikina zuw inda yake kwance duk da ban taba masa hakan ba sai wanan ranan. Kaina nakai saman kirjin na dora lokaci guda yayi wani irin zabura yana fadin kanki daya kuwa zainab ? Sau nawa nake fada maki idan har bukatan hakan ya taso min da kaina zan nemeki da hakan. Ikon Allah na fada a raina kafin a fili ince dashi ban kwanta a nan don wani feeling ko wani abuba na kwantane kawai don in dan samu sauki a zuciyana a wurin dan uwana don kawai naji dumin wani ajikina. Ba tare da yai magana ba ya kai hannun shi da zuman bambareni a jikin shi na kara lafewa kamar da gaske a jikin nasa. Da karfi ya fincikoni zuwa gefeb shi ya juya yana wani irin mayar da numfashin sa da dan sauri kafin can inga ya mike zuwa ban dakin. Shiru shiru bai fito ba sai zuwa can ya fito da alaman ruwa a jikin shi yayi wanka ke nan a lokacin don kawai na dan taba shi din ya watsa ma jikin shi ruwa a lokacin. A hankali na mayar da idona na lumshi jin bai hawo gadon ba a lokacin yasa na bude idona yana tsaye gaban mirrow yana faman goge jikin shi. Tabdi jam ashe abin bana wasa bane na fada a raina ina kara gyara kwanciya har barci ya daukeni ban sani ba lokacin. Kodana falko a cikin dare na hangoshi can saman kujera kwance kuma har lokacin baiyi barci ba idanun shi biyu da waya a hannu shi. Tashi nayi zuwa bandaki na dauro alwala kamar yadda na saba yi a kullun don Nafilan dare. Sai zuwa can ya shiga ban dakin nan ma dai irin abinda yake ji yaji a ban dakin ga kanshi yayi wani irin daure mashi lokaci guda haka dai yaja kafan har ya fito. Yau ba mafalkin asalima tsorone kawai daya ziyarci zuciyar shi haka kawai yake jin kamar tsoro yake ji saidai baisan na meye ba a lokacin. Saida yai sallah raka,a hudu ya dan samu saukin abinda yake ji a zuciyar shi muna wurin har akai kiran sallah asuba . Nayi sallah kamar kullun nabar dakin zuwa dakina sai dai abin mamaki ba kamar yadda ya saba tashi a cikin kuzarin shi ya tashi ba a yau. Gashi nan so wick dashi bai son magana da kowa a ranan karshe ma ya kwanta yana barcin rana abinda bai taba yi ba ke nan a sanina dashi . Koda kuwa baida lafiya baya barci da rana saidai ya rufe idon shi kawai na dan lokaci ya bude . Allah ka tsare muna rayuwan mu daga fadawa a cikin halaka saboda duniya ko neman wani abu makamancin hakan. Duk da irin halin da nakw ganin shi baisa na fasa shafa wanab magani ba insha kuma a nasa bangaren kuma sam ya rasa gane lafiyan jikin shi sam. Shidai yasan cewa lafiyan shi kalau baya jin ciwon jikin shi tako ina amma kuma yawan kasala da damuwa ya hanashi sukuni ko kadan. Ban dada ba ban kara ba a yadda aka ban lokaci da zanyi amfani da magani in bari daga nan kuma aka sake dorani kan wani da zan fara. Nikan garin ceton wani naga ta kaina yar uwa sai dai abinda zance yanzu gaskiya kamar yadda malam ya fada min ne naga sauki sosai ga harkokin ya jafar a yanzu. Ranan ya shigo da rana yake fadin in shirya zamu Samunaka mu duba hjy bata jin dadin jikin ta su mami sun tafi mu zuwa yamma jirgin mu zai tashi. A rude na dago ina fadin subbahanallahi har ciwon yayi serious hakane sosai yace ance sosai ne ciwon suna can dai sun tafi su dubo. Ya na fadin haka ya juya ya fita daga dakin nan ya barni ina jimame akan tsohuwar har wani lokaci kafin in mike in fara shirin tafiya . Bayan sallah la,asar ya shigo yana fadin ba zamu tafi din ba mami tace mu dakata zasu zo da ita nan Abuja yau din nan. Sai naji hankalina ya kara tashi sosai ba abinda nakeji sai rashi zuwa ganin ta da banyi ba gani har kaduna amma ban samu leka wurinta ba har na dawo. Tunda ya fita bai dawo ba ranan har dare sosai haka yasa nasan yana can wurin su hjyn ke nan a lokacin nasan sun iso da ita Abujan kenan tunda yakai wanan lokacin haka a waje. Har na gama komai na shiriya zuwa dakin shi na kwanta ni kadai a dakin ina addu,in dana iya a bakina. Barci ne ya daukeni na dan lokaci sai gashi ina mafalkin wasu mutane masu bakaken kaya duk jikin su sun saka hulunan kayan saman kawunan su. Wanda duk yazo ya wuni a inda nake tsaye ina kallon su din cikin mamakin me ya kawo ni nan kuma su din su waye ? Fuskan dayan abokain shi philis na gani na gane a lokacin ya daga hannu kamar yana warning dina Allah ya taimakeni na furta Au,zubikalamati min sheri min halak .Lah illa ha in,llah anta subahanaka inni kuntun minal zalumin ya wani yanka ihu duk sauran suka kallo mu sai na juya da sauri nabar wurin. A daidai lokacin kuma na falka daga barcin sai wani irin zufa dake fita a jikina don wahala na mike zaune a firgice ina bin dakin da kallo a tsorace. A daidai lokacin kuma kiran wayan jafar din ya shigo wayata saida na dan zabura don tsoron da nake ciki a lokacin. Na kai hannu da kyar na dauki wayan yana fadin kina inane haka nace dakin ka na kwanta ki koma dakin ki yanzu har in dawo ya fada a cikin comand ya kashe wayan. Wayan nabi da kallo tare da kallon lokaci karfe biyu na dare da wasu yan mintina a lokacin. Na mike da sauri zuwa dakina banko rufo kofan dakin da kyau ba wurin sauri don ba karamin tsorata nayi ba a lokacin gaskiya. Ban kwanta ba na shiga ban daki na dauro alwala na tayar da sallah na dade zaune ina karatun kur,ani naji dawowan shi gidan uku da darabi koda ya shigo. Dakina ya fara shigowa tun daga kofa yake jin kira,a na har ya karaso tsakiyan dakin inda nake zaune yana fadin. Mesaya kikaje dakina ke kadai a wanan lokacin na dan dago kai na kalleshi na mayar naci gaba da abinda nakeyi shima ya juya ya fice a dakin da saurin shi. Kafin asuba wani irin zazzabi mai karfi ya rufeni lokaci daya haka nayi sallah a dadafe na koma saman gado na kwanta. Rufe nake ina nishi da kyar sadiyace ta shigo ta sameni a wanan halin hankalinta ya tashi sosai ta juya da sauri zuwa part din shi ta fada mai halinda nake ciki. Tare suka dawo dashi yana tambayan ya nake ji nace zazzabine kawai nakeji a lokacin ya fita sai gashi da magani ya kawo min nasha yana zaune har ya dan fada min. Sai lokacin nake tambayan shi jikim haji yace taji sauki daya barsu jiya da dare yanzu zai koma yaga jikin nata kuma. Wani asibiti take na tambaya a cikin karfin hali ya fada min tare da fadin kada kice zaki a wanan halin ki bari sai kinji sauki ya fita. Bayan fitan shi zazzabin ya taso min sosai na ce sadiya ta ban ruwa na karanta fatiha a ciki nasha sai barci ya dan daukeni a lokacin. Mafalki marasa kyau na dinga yi a wahalce dai nayi barci sosai a lokacin koda na tashi na dan samu sauki har nayi wanka. Na fito na shirya don zuwa duba hjy don tana raina a lokacin sosai mu uku muka tafi da sadiya da fadila zuwa duban ta sai abinci da kayan marmari da muka saye a hanya don mu kai mata. Kusan kowa na asibitin a lokacin don bayan sallah la,asarne lokacin mun shiga mun gaisa dasu tana kwance an daura mata ruwa ana kara mata. Mama Ramatu ke fadin dazun mijin ki ke fada muna baki da lafiya ai nace naji sauki ne na taso gashi a lokacin wani zazzabi nakeji da sanyi a jikina. Mami dake gefe zaune tace ya dai fadane kawai don ya kareta wani zazzabi kika gani a nan don Allah. Kai haba yayan mu kika sani ko alherine ya samemu ake wanan zazzabin yanzu haka ai wasu haka suke laulayin cikin su dama. Dakin yai shiru ba wanda yai magana a lokacin mamice ta sake fadin ai bata da niyar baku jika ta zauna suna jin dadi idan suka hadu da fushina watarana maganin su zanyi ai. Da yafi mami tunda ita bata iya haihuwa ai hara a kawo wace zata haihu muna Aisha ta fada fadila ta karba da fadin Allah ne bai kawo ba hjy komai dan lokacine ai. Wanan kina min shishigi da yawa mami ta fada abin mamaki a lokacin hjy akaji muryanta tana fadin iyami ko bayan raina kikasa jafari sakin yarinyar nan ban yafe maki ba. Dakin yayi tsit ana sauraren hjy kafin Aisha tace dama na fada maku ai ji wanan tsohuwar da kowa ya rude a kanta tun jiya batayi magana ba yanzu take fadin haka. Sai aka kwashe da dariya hjyn da take kwance take fadi cikin karfin hali zo nan kiji kawata inji dumin ki kusa dani tana kokarin mika hannun da ake mata karin ruwa dashi gareni. Kai hjy da zainab sai Allah a tsakanin ku Na,ima ta fada tana fadin to mu din da baki damu da jin dumin mu ba sai mu tafi tunda zuwan mu baida amfani a wurin ki. Ni dai na taka zuwa bakin gadon na riko hannun tsohuwar ta rike gam tana fadin zauna a nan kinji ko suna so ko basu so kin shigo cikin mu ke nan. Muna zaune a haka sunawa junan su sheri suke fadin albarkacin bakin su kan hjy mazan suka shigo ya jafar yana ganin mu a dakin yake fadin. Zainab kin iya tasowa ne yanzu naje gida bakwacen ake fada min kunzo asibiti ya mamud ne ke min sannu da jiki yana gaida ni har su jamal din kasa nayi su lokaci guda akaga na sunkuya kawai dama ni kadai nasan yadda nake ji a lokacin karfin haline kawai nakeyi a hakan. Tsale daya ya jafar yayi ya kai gareni ya rungumoni na some a lokacin ban sab inda nake ba kuma sai hankalin su ya fara tashi. Da sun dauka pretending nakeyi a lokacin har mami tana jan tsuki jamal ya fita da sauri ya kira likita yazo dashi dakin likitan ya duba yake fadin dama bata da lafiya ne haka har jinin jikin ta yana batun konewa duka. Lokaci daya mami ta mike tsaye cikin furgicin jin abinda likita ya fada a game dani yana kiran nurse da sauri yana fadin a shirya daki a kaini ciki nan hankalin kowa ya tashi kuma. Mami da kanta ta rikeni har dakin da aka kwantar dani duk bansan wainar da ake toyawa ba a lokacin sadiya kan kuka ta saka masu tana ihu ganin halin da nake ciki. ZAINAB IDRIS MAKAWA FATAN ALHERI GARE KU DUKKA MASOYANA NAGAISHE TARE DA FATAN NASARA GA DUKKAN AL,AMURAN KU NA YAU DA KULLUN, , , KISAYA YAR UWA KI KARANTA A CIKIN LAMUNA KADA KIJI KYASHIN BIYAN DARI UKU DON KARUWAN DA ZAKI SAMU A CIKI YAFI KARFIN HAKAN ALLAH YASA MU GANE HAKAN AMIN, , , , A rude suke sama kaina saida likita ya zo ya rokesu dasu fice a dakin su dubani suka fara fita daya bayan daya tare da tarin tambayoyi a zukatan su. A bangaren ya jafar sai fuci yake yana fitar da iska a baki da hanci don takaici irin yadda yake ji a zuciyan shi lokacin don yasan abinda ke damuna a lokacin. A bangaren mami kuma ita a nata zaton tunane takeyi kodai jafar din ya samu lafiyan da har na samu ciki a yanzu ne . Hakama yan uwanshi da suka san da zancen suke zargi suma sai dai ya jamal ne da hankalin shi bai kwanta ba sam don zargin bai dauke shi da muhinmanci ba sam. A karshe fita yaya jafar din yayi zuwa bayan don yai waya a kuma daidai lokacin Aisha taji tausayin sadiyana dake ta rusan kuka ta jata zuwa bayan. Da farko bata dauka shi bane yana fadin na fada maku tun farko kada ku taba min yarinyar nan kuma kun sani. Ta dan dago daga inda take zaune ta hango shi din daine ke magana a waya a hasale saidai bata san da wanda yake wayan ba a lokacin . Yaci gaba da fadin duk wanda ya tabi lafiyan ta na rantse maku gaba daya dangin shi sai naga bayan su haka yai ta fadin maganganu kafin ya juya ya bar wurin bayab ya kashe wayan nasa. Jinkin kanwar tasa Aisha har wani irin bari yake a lokacin ta mike tsam tare da jan hannun sadiya suka bar wurin ta hanyar canza hanya. Kasa zama tayi asibitin take cewa mami ita zata koma gida a lokacin mami tayi mamakin hakan kuma ga yar nata a rude yanayin ta ya canza lokaci guda sai ta dauki hakan ga tsorone kawai yasata hakan yadda ta ga nayi a gaban su. Har ta fara tafiya ta juyo tana fadin mami kema zanso kizo muje gida akwai abinda nake so zan fada maki . Aisha kanki daya kuwa ya zan bar asibitu muna cikin wanan halin haka ai saiki sa a zageni idan na wuce. Haka Aishan ta tafi tabar sadiya tare da fadila a asibitin hankalin kowa a tashe lokacin likita yayi iya binciken shi baigano ciwon komai da yaja min konewan jini ba haka lokaci guda . Dole wai sai an kara min jini akace a lokacin yace aje a dibi nasa mami tace kai har yaushe ka tashi a ciwo a dai duba na sayarwa a gani. Kai sam mami ba za,, a kara mata jinin sayarwa ba gaskiya ya fada daga inda yake tsaye cikin tashin hankali kafafuwan shi a harde ya dora hannayen shi saman weast din shi duka biyu. Jamal yace a je a dibi nawa ai zan iyabawa kowa jini na mami ta kalleshi ta rasa abinda zata fada dole ta kyalesu kawai suka tafi. A can ma jafar din yaki yarda sai nasa aka diba aka kara min mami tayi fadan hakan sosai don ta nuna mashi bacin rai akan haka har tana fadin idan shi baisan ciwon kanshi bane yake neman kashe kanshi saboda mace su sun dani Likitan da ya shigone yasa su fita ya fara kara min jinin a jikina sai lokacin na dan farfado har ina gane inda nake ina bin mutane da kallo. Har dare sosai su mami basu je gida ba sai sha biyu saura na dare suka sauketa a gida don tunda Aisha ta tafi da motan driver bai dawo ba. Ga mamakin mami ta zata Aisha ta dade da barci a lokacin sai ta iske su a falo zaune suna kallo da yan uwanta. Tana ganin mami ta mike suka shiga daki tare a gurguje mami tana sauri tana cire kaya a jikin ta zata shiga bayi. Aishs tace mami ya jikin zainab din da sauki ko tace tana shigewa ban dakin da sauki zainab zaki tambaya banda hjy. Mami na fada maki da magana wlh kin ki ki saurareni tun dazun wallahi mami akwai matsala akan ciwon zainab din nan. Ja mami tayi ta tsaya tana fadin wai ban gane ba me kike nufine da magana sai ta kalli kofan dake bude ta mike ta rufo kofan kamar wani zai ji abinda take fadi a lokacin. Ta zauna ta kurawa mami dake tsaye kofan bayi ido fadi mana ina sauraren ki mami tace ga mamakin mami sai taji yar nata na fadin mami kizo kusa don Allah kiji kada wani yaji mu a waje. Ikon Allah Aisha meke damuwan ki hakane yau bayan kin rufe kofa wa kike tunanen zaiji kine wai yanzu. Me kike son fada min har jikin ki ke kyar ma hakane wai tace mami is something serious daya shafe ki wallahi. Jin haka mami din ta karaso gaban ta yana faduwa don gani yadda yar nata ta tsoroce a lokacin. Zama tayi a gefen yar nata tana fadin ki fada min gani nazo kusa dake Aisha sai Aishan ta dago kai ta kalli mami din gaban mami ya kara faduwa ganin idanun yar nata tab da hawaye lokaci guda gaba daya hankalin ta ya tashi Mami ko kinsan ya j yana cikin kungiyan asiri kuwa what mami ta fada da karfi kafin ta fara girgiza kai tana fadin No No No Aisha kin san abinda bakin ki ke fada game da dan uwanki kuwa ? Kai Aisha ta fara dagawa kafin tace a cikin kuka mami na sani ba zanwa ya J sheri ba ko da kuwa ba dan uwana bane shi. Wallahi mami ciwon nan na zainab da sanin ya j wallahi ke Aisha mami ta fada da dan karfi ki san abinda kike fada kada in saba maki yanzu a wurun nan. Wallahi mami naji abinda yake fada a waya da kunnuwana da banji wanan bakin abinba bazan taba fadin hakan ba mami. Nan ta fara bata labarin yadda abin ya faru har zuwan shi yana waya da abinda taji ya fada a wurin lokacin game da zainab din. Innalillahi mami kawai ke fadi kafin kuma tazo ta fashe da kuka tana fadin jafar sai kuma ta girgiza kai a cikin takaici. Can ta juyo kamar tababa tana fadin bayan kanwar zainab din ke dawa ke wurin mu kadai ne ta bata amsa. Ita kanwar zainab din fa taji abinda yake fada tace ban tsamani taji don kukan da takeyi a lokacin saboda shi najata zuwa bayan wurin filawowi. Innalillahi Aisha jafar ya kasheni idan wanan maganan gaskiya don ko mu ba zai bari ba wata rana. Wallahi mami najine ya fada exactly abinda naji na fada maki mami ban kara masa ba ni yanzu tsoron da nake ji shine kada su kashe ta a sanadiyar shi fa. Ki bar wanan zancen Aisha zanga mamud mu tatauna a kai zuwa safe don yanzu nasan ya shiga gida ko tunda ya saukeni. Mami a nan zan kwana tsoro nakeji wallahi ba zan iya kwana dakina ba yau ta fada a cikin dan shagwaba. Mami bata tsaya ba ta wuce zuwa ban dakin da tayi niya kai tsaye zuciyar ta cike da tunanen dan nata. Har ta fito bata bar jin abinda take ji ba a lokacin don haka ta samu wuri takai kwance Aisha na gefe kwance taji mami din ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya. Haka yasa ta mike zaune tana fadin mami ki bar kuka please kada ki jawa kanki matsala don Allah addua ya kama ayi masa yanzu please. Aisha jafar yana son ya kasheni me yar mutane tayi masa yake son bada jinin ta a sh haka ? Mami ni godiyana ga Allah daba zarah bace yake aure haka ya faru da kinsan iyayyen ta ba zasu taba yarda da hakan ba sam. Tunanen da nakeyi ke nan yanzu Aisha da ace itace a gidan nasa yau ina zan sa kaina a kasan nan inji dadi. Yanzu ne na kara tabbatar da kalami da ya keyi idan nayi mai maganan aure sai yace zainab ce daidai dashi ya aura. Ashe abinda yaron nan yake nufi ke nan ban fahinta ba har hjy tsohuwa ta rigani fahintar manufar sa din . Haka suka kwana sai kusan asuba mami din ta tashi ta fara nafila ana fitowa sallah ta kira wayan mamud tana neman shi idan ya tashi. Hankalin ya mamud ya tashi yana zaton ko hjy ko nice wani abu ya faru damu. Ya amsa da fadin mami gani zuwa yanzu Nuriya dake gefen shi ta dago da sauri tana fadin lafiya dai ko yace ban sani ba sai na tafi. Kodai zainab din ce ta cika ta tambaye shi tana kure shi da ido don jin amsan da zai bata a lokacin yace itace damuwan ki a duniya dama ? Kai ba a maganan arziki dakai dama ta fada tana kawar da kai gefe cikin jan tsuki da jin haushi shi a lokacin. Rigan shi dake gefe ya dauka ya zura ya fice dakin da sauri zuwa part din mami din hankalin shi a tashe. Yana shiga part din mami din ya nufa babu kowa a wajen sai yan aiki dake ta aikin su a gidan suna gaudashi yana amsawa a gurguje ya kai kofan ya kwankwasa. Aisha ta amsa mai da fadin shigo yaya ya sakai da sallama ya shiga yana shiga ya hango mami zaune a kasa ta jingina jikin ta ga bangon dakin kamar tana tunane. Mami lafiya ya tambaya yana kallonta jin ba amsa a wurin ta ya juya wurin Aisha yana fadin Aisha meke farune haka ? Ka zauna yaya ta fada itama a sanyaye tana kallon mami din ya samu wuri ya kai zaune a hankali gefen gadon yana maimaita tambayan shi har lokacin ba amsa. Shiru ne ya dan biyo a dakin kafin mami din tace mamud kasan wana ciwon da yarinyar nan zainab keyi a yanzu Jafar ne silar shi kuwa. Jafar kuma mami ya tambaya a cikin mamaki yana kallon mahaifiyar tasu don son karin bayani a wurin taba Eh jafar ki fada mai abinda kikaji yana fada tacewa Aisha dakw gefen shi zaune a takure cikin damuwa karara a fuskan ta. Jine da kanwarta ke kuka bayan ta some din nan sai na jata zuwa baya ko zatayi shiru nan ta kora mai komaai wanda kafin ta gama ya kira sunan Allah yafi a kirga. Saida Aishan tagama magana har lokacin kai yake gitgiza yana jin ta aje ya amsa da fadin mami na fada maki ina zargin haka gare shi kice in bar zancen nan kada in kara fadab haka a bakina. Subbahanallahi wlh biri yayi kama da mutum mami duba da wasu halayen jafar na rashin son raban mutane da baiyi kuma a haka harkokin shi suke ci gaba kullun. Ya kara fadin hasbunallahi wani imal, wakeel wallahi in har wanan maganan gaskiyane jafar ya cuci yarinyar nan don a tsaye take wallahi mami kan al,amarin shi . Don shi da bakin shi wallahi yake fada min irin kokarin da yarinyar nan tayi a kanshi har ya daina shan giya da neman maza yan uwanshi a yanzu. Ita zainab din mami ta tambaya cikin dago kai tana kallon shi yace wallahi mami ya fada min komai amma bai fada min yana cikin wani kungiya ba haka. Ai ba zai fadama ba tunda yasan bai shuka gaskiya ba mana yarinyar da tayima wanan har zaka iya bada jinin ta ga tsafi. A dai bincika mami don bamu san inda zancen nan yanufa ba kai tsaye kar muzo mu yanke kasa hukuncin da bashi ba a nan. Idan ba gaskiya bane me zaisa ya fadi haka yana warning din su kada su kashe ta dashi suke da matsala ba ita ba. Mami jamal yasan da wanan zacen ya mamud ya fada yana kallon fuskan mami din tace kai kadai na fadawa yanzu. Don tun jiya ta fada min da dare na kasa barci a gidan nan sam ban runtsa ba tun jiya di data fada min zancen. Bari mu tambayi jamal ko yana da wani masaniya ga hakan da sauri mami tace kada ka fada mai komai yanzu sai in hakan ya kama a fada mai din. Kasan jamal da bakin zuciya wallahi zai iya kawo hatsaniy tsakanin ka dashi yanzu menene kada a fada min jamal din ya fada yana shigowa dakin. Don tun shigowan ya mamud ya ganshi ya koma daki ya saka riga tare dayin brush yabiyo bayan dan uwan nashi hankali tashe. Asibiti kusan a zaune yaya ya kwana a dakin sai can ya daga ya je dakin da aka kwantar da hjy ya leka ya samu suna barci ya dawo. Ya kafa sintiri a tsakiyan ward din yana dan buga hannayen shi a cikin damuwa ya kuma koma ya zauna ya tsura min idanu na wani lokaci. Zuwa asuba na dan motsa ya taso da sauri yana dan kiran sunana na dan bude ido na kalleshi na mayar na rufe kuma kamar ina barci a lokacin kuma idona biyu ba barcin na koma ba. Saidai dakin da naga yana juya min yasa na kulle idanuna dan in ji saukin hakan . Kai kai ya fada yana naushin hannu shi cikin dan uwa tare da fadin idan kuka cutawa yarinyar nan i will not spear any one in dat crimme. A hankali hawaye dake idona suke silalowa gefen fuskana sai yanzu na dan gane abinda ke damuwa na a lokacin wani irin kukane yazo mi har yana dan jin sautin na a lokacin. A hankali ya tako zuwa inda nake kwancen ya dan sunkuya daidai gadon yana fadin baki barci ba ke nan zainab. Abinda nake gudan maki kenan ya faru dake tun farko ki gafarce ni zainab nasan na cuta maki da ban fada maki wanan tsarin nawa ba. Ba a shiga dakina a kwanta saman gadona idan bana cikin dakin wanan dokane hakan shiyasa tun farko ban saba maki da shiga dakin nawa ba ma. Don irin hakan nake maki gudu duk da nasan ba zasu iya maki komai ba a yanzu warning din ki kawai sukeyi a hakan . Jin maganan da yakeyi a lokacin kamar almara nakeyi kafin in mayar da idona in rufe ina mai jin wani irin tsanar shi na shiga zuciyana lokaci guda. Ba zan taba yarda a cuta maki ta bangare na ba zainab ko waye kuwa sai inda karfina ya kare don ke din amanace gareni zainab. Insha Allahu zakiji sauki ki dawo gare da yardab ubangiji don na fada masu kowa ba zan bari ba idan sun taba min ke wallahi. A hankali na bude bakina cikin muryan dake nuna zafin ciwo ga mutum don muryan bai fitawa mutum sosai a lokacin da yake son fadan wani abu ga wanda ke kusa dashi a lokacin irin hakane a lokacin nace dashi su waye wayan nan yaya ? Meye hadin ka dasu har suke bibiyan rayuwan ka dani ya shafeni a yanzu wani laifi nayi masu suke son kasheni ? Sai lokacin ya dago kai da sauri yana fadin ba zasu taba iya kashe ki ba zainab Allah ba zai basu ikon hakan ba don ya fimu sanin komai. Ke din ba jinin daya halatta bane a garesu sun sani in ma wani abu suke so sukai maki haka ni zanyi maganin ko menene da yardan ubangiji. Idona na runtse a hankali don jin abindaya fada tabbas akwai wani kulli tsakanin shi da wasu da ban sani ba amma kuma ai fuskan phlips abokin shi nagani a mafarkin. Da budan bakina nace dashi your friends philips and others ko don shi nagani a wani wuri a cikin mafalki da ban san ko ina bane wanan wurin. Kingashi ko zainab na gyada mai kai a hankali ina kawar da kaina gefe daya wasu hawaye na gangarowa daga idona a hankali. Naji yace good zai gane baida wayau kuwa ido na mayar na kulle a hankali don nikan a zuciya nasan na gama da duniya ke nan tunda na shiga hannun wa yan nan mutane a yanzu. Yanzu nasan kin fahinci ko meke gudana dani zainab saidai ina son don Allah idan zaki min hukunci kiyi min adalci a cikin sa don ni kaina a haka na tsuci kaina a cikin su badan nasa kaina ba. Wanan yana cikin abinda bature ke kira da trust person yarda da shakuwan dake tsakanina dasu a baya yasa suka jefani a cikin su . Don su a wurin su mutum bai zama dan baiwa bai kasance a cikin wani kungiya ba haka wanan shine dalilin kawai da suka halaka min rayuwa a yanzu. Zakiyi mamaki idan nace dake su a wurin su hakan shine iya kaunan da zasu nuna min na zama tare da mukeyi. Saidai ina son ki sani duk da sunan ina cikin su ban yarda da dokokin su ba da ake shimfidawa mutum inda na samu dama shine bani na saka kaina a cikin kungiyan ba sakani sukayi da kansu. Don shi bature yana baka hakkin ka akan ka,ida komai ritsi kuwa ga abu dole sai sun ba mutum hakkin sa a kai. Duk yadda suke sona a cikin su hakan baisa na yarda na sake ibadana ba don su kamar yadda da dama suke hakan idan sun shiga sai dai rauni dana samu wurun addinin nawa wanda ni kaina na sani kuma abin yana damuna sometimes. Ina fada maki wanan ne badon ki yarda da abinda nake fadi din ba iya kuma gaskiyan ke nan nake fada maki a yanzu. Haduwana dake shine sillar tabarbarewan komai a wurina wanda su basu so hakan ba don addinin da na juya yanzu ina yi akai akai yasa mun samu rauni sosai dasu a hakan. Karshe kuma sai rabuwana da su taju da nabil daya kara tun zurasu suka sake jin haushin hakan da takaicina gashi a yanzu a kullun zasu ganin a kwance tare dakene a kuss dani wanda hakan yana cikin dokan mu. Ba zamu kwanta da mace don muji dadin ta ba don su a ganin su mace haramtaciyace a wurin su dokane hakan. Yawan adduan ki idan zaki kwanta yasa basu iya maki komai a lokacin ko jiyan dama suka samu har hakan ya faru dake wanda nasan kuma ba zasu maki komai ba sai tsorata kin da suke son suyi a hakan. Nasan da ba wanda yasan da wanan zancen duk a kasan nan sai ke a yanzu ke din ma na yarda da sone yasa na fada maki komai don ki sani ki kuma kwantar da hankalin ki kada kiyi tunanen komai kan hakan. Kuka nake a hankali ya mike don kiran sallah da yakeji a lokacin ko ina a cikin asibitin yana tashi yake fadin ki yi barci a yanzu idan na dawo sallah sai in kamaki kije kiyi taki sallah kada kice zaki tashi fa please ya fada yana fita daga dakin. ZAINAB IDRIS MAKAWA. FATAN ALHERI GAREKU MASU KARATU MARASA LAFIYAN MU UBANGIJI ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYA ALLAH YA KARA MASU LAFIYA DA WADATAN ZUCI ALLAHUMA AMIN, , , , ANTY COROFFE UBANGIJI ALLAH YASA KAFFARA NE WANAN JARABTAN DA ALLAH YA AIKO MAKI DASHI ALLAH YA BADA IKON CIN JERABAWAN SA AMIN. AKWAI WATA BOYAR ALLAH TANA BUKATAN ADDU,OIN KU DA BAKUNAN KU MASU ALBARKA ALLAH YA BADA IKON MATA DAMU DA ITA DUKA ALLAHUMA AMIN, , , , Tunda na runtse idanuwana ban budesu ba ashe har barci ya daukeni ina tunane a hakan. Hayaniyan da naji a saman kaina yana tashi a dakin yasani bude idadanu na a lokacin naga har hasken rana ya haska gari a lokacin alaman dai gari ya dade da wayewa ko . Muryan ya mamud ne naji a saman kaina yana min sannu tare da fadin kin tashi ke nan zainab ya karfin jikin naki ? Na bude idona tare da kakaro murmushin dole a lokacin a fuska ina dan amsawa a hankali. Yawa na soma yi da idona ina bin wa yanda ke cikin dakin da kallo na sauke idona a kan mami dana gani can daga gefe ta tsura min idanun ta kuri tana kallona. A hankali naga ta tako zuwa bakin gadon tana fadin ya jikin zainab da sauki ko min shigo mun samu kina barci. Da sauki mami na fada ina yunkurin tashi zaune take fadi a cikin sauri kwanta mana ina kuma zaki yanzu ? Cikin daurewa na soma fadin sallah zanyi mami banyi sallah ba tun dazun na fada ina mikewa zaune. A take na mayar da idona na rufe dan jiwan da nake gani idon nawa nayi lokacin dana tashi din zaune. Lafiya mami da jamal suka fada lokaci guda ban iya basu amsa ba sai komawan da nayi na kwanta a lokacin da sauri ina zatane mami jamal ya tambaya. Wai sallah zatayi ta bashi amsa yake fadin ta bari mana har taji karfin jikin zuwa dan ajima sai ta tashi tayi. Lokaci yana shigewa idan zata iya a barta tayi ya fada yana karasowa wurin duk suka bishi da kallon mamaki a zukatan su. Zata iya mana idan basu samu galaba a kanta ba kamar yadda suke son halaka yar mutane batai masu komai ba ya fada a hasale yana juyawa. Duk da mamakin da yayi da abinda kanin nasa ya fada baisa ya nuna ko gezau ba a hakan sai ma kokarin dukawa da yayi yana tambayana abinda nakeji dana tashi din. Ban bashi amsa ba sai yunkurawan da nayi da karfi Allah ya taimakeni na tashi da addua a bakina ina sauke kafafuna kasan gadon na sauka . Kamani yayi da sauri zuwa ban daki da taimakon shi har na samu nakai yafito tare da rufo min kofan na tsugunna da kyar kami nayi sarki. Ina fitowa a kofan yake tsaye saidai duk wa yanda ke dakin a lokacin sun fita shiya kamani zuwa wurin daya shimfida sallay a dakin nayi sallah a zaune yana gefe saman kujera tare da wayan shi a hannu yana dakila. Fadilace da sadiya sukai sallama suka shigo dakin da gudu sadiya tayo kaina ya daka mata tsawa kada ta fada min a jikina. Fadila ko tun a kofa take fadin alhamdullahi jiki yayi sauki tunda mun sameki zaune haka kafin ta juya wurin shi tana gaidashi bai wani amsa mata a sake ba. Bayan sun gaidani ne ya mike tsaye yana fadin barin leka likitan koya fito kada ki zuba abincin kar taci sai munji abinda likitan zai fada. Daga haka ya mike ya fice a dakin ya barni dasu yana fita nace fadila kamani in koma saman gadon zan kwanta. Ta rikeni na tashi muka nufi gadon saidana kwanta tana min sannu ta koma ta zauna saman kujeran daya tashi sama. Ina nan kwance a wurin suka shigo su ukku da likita sai ya mamud da suke tare likitan ya dan duba yayi rubutun shi yake fadin ba wani matsala har yanzu saidai za a bari har anjima aga yadda na kara ji sai a sallameni mu tafi gida. Bayan fitan likitan ya kalki fadila yana fadin zaki iya bata abincin yanzu taci tace ok oga tana mikewa tsaye don zubawa . Da sauri nake fadin bazanci ba don Allah ruwan zafi kawai zan sha na fada ina kawar da fuskana nan ya kama min fada don me ba zanci ko kadan ba inji karfin jikina. Rabon ki da abinci tun jiya bakici komai ba sai lokacin ya mamud yai magana a dakin yana fadin ka barta ba aiwa mai ciwo hakana a sannu ake bin shi ai. Ruwan zafin ta hada min nace kada tasa madara haka zan sha tana dan juyawa ta dago kai tana fadin oga kaje gida tunda munzo ka huta. Ya mamud yace lalai kan zai fi kada kaima ka rafke muna da ciwo kuma ya dan yi murmushi kadan tare da dubana kafin yace. Mamud mu tafi wurin hjy na kara dubanta kafin na wuce gida suka fita daga dakin ya rage mu kadai a dakin na kalli inda suke zaune sunyi shiru ina fadin. Kunzo min da wayana suka amsa da eh yana a jakkan ki da muka tafi dashi jiya gashi sadiya tasa hannu ta dauko wayan a ciki ta miko min. A hankali na bude wayan don malam nake son kira na kalli fadila ina fadin ku dan fita ku ban wuri na min ti uku don Allah. Da sauri suka mike suka fita na danna kiran malam din ya dauka yana fadin yau uwar gidan jafaru ce da kira da safe . Maimakon inyi magana saina fashe da kuka inajin yana fadin subbahanallahi me kuma ya faru dake zainab bar kuka kiyi min bayani a tsanake kukan nan naki yana daga min hankali sosai wallahi. A cikin karfin hali nace dashi malam ina cikin wani hali yanzu haka ina asibiti a kwance tun jiya ance wai banda jini. Subbahanallahi malam ya fada a kidime tare da fadin meya kawo hakan gareki nan ma wani kuka na sake kafin in koro maganan na fara fada mai tiryan tiryan har karshe. Wa iyazu billahi ya fada tare da fadi cikin sauri ina zuwa ki kashe wayan nace to malam nagode na kashe wayan. Banji malam din ya kirani ba har zuwa rana hankalina kuma yana wurin kiran malam din don sai ina ganin shi keda maganin a hannun shi. Yasa na damu da in fadawa malam din a lokacin karfe hudu likita yace ina iya zuwa gida a lokacin ban bar asibitin ba saida na shiga na sallami hjy itama din ba laifi ta samu lafiya a lokacin. Mun dawo gida dakina nashiga nayi wanka har lokacin ina jin jikina ba karfi kamar nayi watani a kwance ina jinya nake jin jikin nawa. Karfe shida sai ga maizube da malam an shigo dasu gidan wanan ya ban mamaki don ban san zasu zo garin ba a lokacin. Basu huta ba malam ke fadin a kaishi wurina yana son ya ganni a lokacin aka kaisu har dakin ina kwance duk da yamma yayi a lokacin na kwantane don zama bai mun dadi a lokacin . Yana shigo da sallama a bakin shi bai min magana ba ya fara bin dakin da addua kuswa kuswa na dakin kafin ya dawo ta kofan dakin ya tsaya ya dade yana adduan da bamu ji abinda yake fadi a lokacin. Yasa hannu ya ciro wani dan gora da rubutu a cikin aljihun babban rigan shi tare da wani fifiken wani dabba mai dan girma yana bin ko ina yana dan yayyayafawa a dakin ko ina har zuwa wurin gado. Sai daya gama yazo inda nake zaune din ya mikowa maizube wani gora yana fadin ku shiga bayi ki mata wanka da wanan zamu samu abin yin hayaki ko a gidan nan ? Burner muke dashi na bashi amsa tare da yimai bayanin yadda yake yace zaiyi ai tunda yana fitar da hayakin a jikin shi. Nayi duk yadda yai min bayanin ayi min koda muka fito basu dakin shi da yaya jafar din hakan ya bamu daman yin yadda yace ayi din maizube na fadin ai da yardab ubangiji komai zaizo karshe ke nan yanzu don sai da malam din yaje Damau yaga aminin shi kafin muzo nan. Ni da kaina nace aban abinci inci a lokacin ina ci sai barci mai nauyi ya daukeni ban falka ba sai cikin dare sosai koshi fitsarine ya tayar dani a lokacin. Da safe koda na tashi jiki wasai dashi kamar bani bace a jiya ban ko iya daga hannuwana a lokacin. Kwanan malam ukku a gidan mu yana burgan gidan damai gidan gaba dayab mu har mami da ya mamud sunzo ya zauna dasu sunyi maganan siri da jafar din dasu . Wanda ban san abinda suka tatauna ba a lokacin nidai naga mami ta canza min yanzu tun a asibiti naga wani canji a gareta a yanzu gareni. Washe gari su malam sukai min sallama suka tafi bayab yaja mun kunne koda wasa kada in fada wa wani a gida cewa sunzo nan Abuja . Kuma haka din nayi duk da inna na kirana mu gaisa ban fada mata ai malam yana wurina a abuja ba. Duk da malam ya tafi haka baisa mun daina maganin daya bamu inayi ba a kulun har kwanakin daya diban muna din muyi a tare dashi mukeyin maganin kullun kafin mu kwanta barci zamuyi wanka da hayaki sai adduan kwanciya din daya bamu safe da yamma. Alhamdullahi zance a yanzu banda wani damuwa a jikina ko na tsoro a yanzu tun bayan zuwa malam wurin mu din. Ana sallamo Hjy gidan mu akayo da ita don can tace a kaita kafin ta koma gida idan ta dan murmure jikin nata. Mami bata so hakan ba saidai ba yadda ta iya da hakan dole ta barta taje gidan namu ta zauna hakana yayin da mu kuma hakan yai muna dadi sosai don son da mukewa tsohuwar. Sabon zancen daya taso muna kuma a kan zuwan hjy gidab mu shine dawo da kwanan mu wuri daya da yaya a yanzu don zuwan hjy. Don tun faruwan hakan ban kara komawa dakin na kwana ba sai yanzun da hjy tazo gidan namu zata kwana biyu damu. Don sa idon tsohuwar duk da a daki take zama nan take wuni bata fitowa ko falon gidan sai dai kuma suna tare da mama Ramatu a gidan namu. Wace mami tasa ta biyo mahaifiyan nasu su zauna nan tare da ita don halin jikin nata da take ciki a yanzu. Hakan yasa a yau dole mu hada daki da yaya din wanda kowan mu na cike da tsoron hakan a cikin zuciyar shi tunda bamu san mai hakan zai haifar muna daga baya. Na shiga dakin da sallama yana kwance yadda ya saba kwanci wani lokaci ya daga kafa daya ya dora hannu saman fuskanshi ya kare da hannu daya. Yana jin sallamana ya dan dago kadan ya kalleni ya mayar da kanshi a yadda yaken na tako a hankali zuwa bakin gadon kamar a tsorace nake.a lokacin. Zama na danyi a baki gadon ban karasa hawa ba gaba daya yake fadin idan kina ganin hakan da matsala ki koma part din ki ko hankalin ki zai kwanta nima ina dauting din hakan a yanzu ban son a kara samun matsala again. Kada su mami su kara zargina don mun kwasa dasu wacan satin suke fadin wai nine na bayar da jinin ki a wurin tsafina. Jin hakan yasa na juyo da sauri ina kallo inda yake kwance din yana nan yadda yake yake maganan shi hankali kwance. Waya fada mata hakan na tambayeshi da mamaki a fuskana shine abinda ya ban mamaki don maganan yana kama da wanda muka sani din don haka yaya akayi suka san da zancen. Nasan baki fada masu komai ba kan hakan saidai idan zargi sukeyi ko kuma sunji a wurin malaman su don nasan kowa na shige shige a kaina a yanzu. Wanda ni nasan da hakan ba yau ba sai dai duk bata lokacin su sukeyi ga hakan don hanya fita ciki dayane nina sani idan lokaci kuma yayi zan daina din da yardan Allah. Wani irin kallo nayi masa na tuhuma duk da bai kalloni ba yasan nayi masa sai naji yace yes matakin da basu so zan dauka shi zai rabani dasu lafiya. A hankali na jingina bayana saman filon dake gefena nakai kwance ba tare dana iya furta mashi komai ba a lokacin. Don a yanzu ya daina bani tsoro ko mamaki don sai nake ganin a gadarance yakeyin abinsa kai tsaye duk da yasan hakan ya sabawa addinin mu sosai. Sai dai maganan malam ce da yake fadin in bishi a sannu don bayin kansa bane hakan zanga kamar komai yana yinsa a cikin sani ne saidai asirine dake aiki a kansa kawai ba a gane hakan ne ko shi kanshi bai gane hakan kai tsaye. Sai idan an bishi a sannu zai zo ya daina komai wanan ne suka tatauna da mami da malam din ashe da zasu tafi bayan malam din ya fada mata komai akan dan nata da a yanzu ta yarda da komai da ake fada akanshi. Ba wanda ya sake wani magana a cikin mu har barci ya dauke mu a hakan ko dadin barci ne ya kawo mu kusa da juna kowan mu ya dora hannu saman jikin dan uwa oho. Sai dai mun tashi da asuba mun samemu a hakan nice ta farkon falkowa nayi mamakin gani shi rungume dani yau abinda bai taha faruwa a tarhin mu cikin jin dadi irin hakan. Ban gama mamaki hakan ba ya falka shima da sauri ya dan ja baya ya zabura wanda hakan yasani na kara mirginawa gefe daya. Ganin na matsa yasa shi sauka da sauri ya zauna a bakin gadon na dan wani lokaci kafin ya mike ya shiga ban daki nabi shi da kallon mamakin yin hakan. Bai dade ba ya fito daga bayin na shiga wanka nayi na daura alwala ina mamakin wanan bakon yanayin yau da nagani a garemu. Har na fito ban daina mamaki hakan ba ina idar da sallah na koma na kwanta don gari bai gama waye ba a lokacin. A cikin barcin ne nayi mafalkin ga wasu nata kwasan kayan su suna tafiya kamar masu barin gari ina tsaye ina kallo su sai da suka gama suke dago hannayen su na duba sai banga kowa ba kuma. Kakan maya na gani tsaye da abu kamar sanda a hannun ta tana min murmushi na mayar mata itama din tabi bayan su suka bace mi tare. Tashi nayi firgigit ina kallon ko ina na dakin sai lokaci na gane inda nake kwance a dakin yaya nake har lokacin kwance . Juyawa nayi shine zaune yana aiki a cikin laptop din shi ga tea a gefen shi yana tashin turin hayaki. Na mike na saka hijab gaidashi nayi na nufi hanyar fita daga dakin naji ya dakatar dani yana fadin mafalkin me kikeyi kuma haka da safen nan. Dan kallin shi nayi ban furta mai komai ba nasa kai na fice daga dakin kai tsaye zuwa dakina . Idan ka ganni a yanzu zaka gane ina a cikjn damuwa don yadda na rame na danyi duhu ba sosai ba dai. Don Allah ayi hakkuri da wanan din ba yawa sosai yar uwa dare yayi sosai ba zan samu karasa shafin nan ba yau. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI UBANGIJI ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA MARASA LAFIYAN MU ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYA ALLAH YA KARA MASU LAFIYA . YAN UWA MUSULMI DA SUKA RIGAMU GIDAN GASKIYA UBANGIJI ALLAH YAI MASU RAHAMA ALBARKACIN KALMAN LA, ILLAH HA,ILLAH MUHAMMADUN RASULILLAH ALLAHUMA AMIN. NOVEL DIN KUDINE NA FADA BA HAKKI A TSAKSNINA DAKE RANAN TAMBAYA NAGODE ALLAH BADA IKON BIYA A KATANTA LAFIYA, , , , Zaman hjy a gidan mu zance kamar alherine a garemu baki daya don tsohuwar duk da tsufa da yai mata yawa a yanzu haka baisa ta barkace ba ga komai. Wanan shi ake kira da tsufan mutunci zakaga tsofo a kamile komai nasa a cikin mutumci da addine yakeyin sa ubangiji Allah kabamu irin tsufan nan idan tamu tazo Allahuma amin. Yau ma ina fitowa mukai kicibis da mama Ramatu da tafito kitchen yiwa mai aiki magana ta kawowa hjy ruwan zafi tasha shayi kafin tasha maganin ta. Tana dawowa ina bude kofan yaya jafar din zan fito a lokacin mukai kicibis da ita jin karan kofan yasa ta dago ta kalli part din . Nice ina rufe kofan ta dan sake dan murmushi a fuskanta daga can nisa inda take tana fadin har kin tashi ashe. Ban iya bata amsa ba don nauyi da kunyan hakan a gareni ashe shigan ta take cewa hjy din ikon Allah koda ake cewa yaran nan basu damu da junan su ba auren nasu na gashi nayi kane sukayi ashe zancen ba haka yake ba hjy. Nikan nasan cewa lokacin haihuwan nasu ne baiyi ba koda yaya ke fadin dama dai ai auren yinsa yayi don kada a matsa mai yarinyar ba sonta yakeyi ba har yanzu. Tunda babu soyayya a tsakanin su da yarinyar yasa bai kulata har su samu fahinta nikan nayi mamakin hakan da yaya take fadi ai. Dan murmushin manya hjy ta sake kafin tace da yar nata shin Ramatu kin taba ganin inda akai sharia kan mata da miji irin haka ? Kyake yar ku kawai da halinta nina dauka kawai lokacine baiyi ba don Allah ba ai masa dole sai lokacin daya dibarwa mutum yayi. Yaran nan duk kansu hankali ke garesu don basu fita fili suna fitsara irin na yaran yanzu yasa take fadin hakan amma ai mai hankali yana gane wani abu a tsakanin su shi. Ina nan kuke hiran yadda ya rude da ciwon ta a asibiti har kuna masa sherin hakan kawai dai ku barta da halinta jinin sune bai hadu da yarinyar ba a yadda na dauka. Sun dauki lokaci mai tsawo suna tataunawa akan mu da mami kafin su juya hiran zuwa hiran Nuriya matar ya mamud. Nafito wanka na shirya kafin in fito dakin na nufi dakin da hjy take don in gaidasu da kwana a zaune na samesu suna hira ga abin karyawa da suka karya dashi a gefe daya. Da sallama a bakina na shiga dakin suka amsa min nakai zaune ina fadin hjy ina kwana ya karfin jiki take fadin lafiya yar nan . Ya naki jikin ina da sauki i yanzu nace Alhandullahi hjy na juya wurin mama Ramatu ina gaida ita ta amsa min a cikin fara tana fadin ya dare zainan an tashi lafiya Alhamdullahi na bata amsa. Daga haka nakai zaune a gefen carper din da suke zaune suna hiran ga abinci nan ki karya hjy tayi min tayi. Kafin inyi magana mama ke fadin a, a hjy da mijin ta suke karyawa fa yanzun kuma kyace ta zauna nan tace aiko zaku hadu dashi idan ya fito. A daidai wanan lokacin yayi sallama ya shigo dakin saida ya kalli hjy kafin ya juyo ya kafeni da idanun shi har saida na tsargu. Mama ya fara gaidawa sabanin ni dana fara gaida hjyn a lokacin dana shigo din dakin hjy ce tace kin gani idan na nuwa yar nan so da kauna kuga laifina a hakan kuna fadin wai nafi son ta da kowa. Yanzu ki duba ina zaune amma dan nan keya fara gaiyarwa daya shigo shi dakin nan matar shi ko datafishi sanin muhinmanci na ai kinga ni ta fara gaidawa data shigo. Bai bata amsa ba sai da yakai zaune kusa dani yake fadin wai mama mai wanam tsohuwar take fada ne haka tun dazun ? Fada takeyi da kai ka fara gaidani kafin ita ya juyo inda take zaune yana fadin da me kike nufi in bar uwata da take zaune in fara gaida ke ? Ai idan ina da rana ka fada randa babu ni yace baga iyayyena ba ina gani ta mere bakin ta tana fadin ke dai kawata kada ki biyewa wanan butulun mijin naki nayi murmushi kawai ina dukar da kai kasa ina dan wasa da hannuna. Ta sake nunani tana fadin ka gani Allah ya baka mata mai.alkunya ba irin ka fitsarare ba mara kunya. Haka ma wancan kanin naka mai irin zubin ka yazo jiya yana min huci kamar wani tsohon kimarci wai am bata masa rai. Wa ke nan keda zubina ya tambaye ta take cewa masu suna irin dayan nan wanda yaso kwaso farin ka da tsayi. Mama Ramatu tace jamal take nufi fa kasan ita hjy bata da gwani a wurinta jiya kuma kai aka yaba akan jamal din gashi yau kuma ana kushema. Barta kawai ai idan mun tashi tafiya chaina da ita zamu tafi wanan karon hjy na fadin kadai je da uwarka gata zaune ni kuma ina dago kai ina kallon shi. Don jin zancen komawa chaina da yayi a lokacin don na tsani inji zancen tafiyan nan namu a bakin kowa a yanzu. Balle yanzu da nake ganin can din yake da babban matsalam rayuwa data shafi halin da yake ciki a yanzu yasa gaba daya na kara tsanar kasan a rayuwana. Amma kai kadai zaka tafi wanan karon ko hjy ta tambaye shi ya kai hannu ya dauki wayanta dake gefe yana bin shi da kallo kamar yana nazarin wayan. Ba tare da ya dago kaiba yace ita matar tawa gunki zan barta idan ban tafi da ita ba can din ? Ni dai in tawa ce kabar yarinyar nan a kasan nan kusa da gida zaifi idan ka tashi kazo ka ganta yafi sauki wallahi. Wayan dake hannun shi din ya aje mata a gefe inda ya dauka da farko yana fadin wanan sabon zance kike son dauko min hjy. Yaushe zan iya zuwa in wani dawo nan kasan kuma yanzu banda wanan lokacin gara dai muna can din hankalina zaifi kwantawa ai. Budan bakin mama Ramatu sai cewa tayi nima abindana fadawa yayan mu ke nan da take wanan maganan wai ba zaka koma da zainab din ba wanan karon. Kamar ba hjy ce ta tsokalo maganan ba a yanzu dana dauka zata goyi bayan zaman nawa a nan sai ji nayi tana fadin. Ku barshi ya koma da matarsa yafi mai kwanciyan hankali hakan ita lokacin da mijin ta yake raye ina can suke da zama gaba daya shekara da shekuru kuwa. Ai kawai ku barta tabi mijin ta shi yafi, na fadawa mami hakan ba zai yuyu ba tun ranan don haka abar wanan zancen don Allah ya fada yana bata rai ya mike don barin dakin a lokacin. Mama Ramatune ta tsayar dashi tana fadin nace ko zaka leka gidan yayane da safen nan ina son zuwa yau din akwai sakon da zan bayar akai min gida a can. Haka yasa yaja ya tsaya yana sauraren ta kafin yace da ita ba yanzu zan tafi ba mama amma idan zaki tafi akwai driver a waje sai ya kaiki ai. A lokacin na mike don barin dakin nima don idanuna ya riga da ya cika da hawayen takaici a lokacin nakai kofa yaja ya ban wuri tare da bina da kallo. Yaki kawata hjy ta fada ban iya juyoba a lokacin kuma nasan dani take maganan sai dai naja na tsaya daga kofa kadan. Au kardai ince kema din baki son bin mijin naki can ne yanzu mama Ramatu ta fada tana kallona. A, a kada kuyi mata fassaran daba shi ba babu wanda zaiso yabar gida irin haka shekara da shekaru mutum naizo gida ba fa . Tazo din kuma bai barta ta gama bin dangi ba ya tayarwa mutane da hankali kamar gareshi farau yin mata . Yaki nan kinji kyale shi idan ba zaki koma ba yanzu sai ya tafi ya barki nan har ki kara ganin mu ai muma nan bamu gaji dake ba. Baiyi magana ba sai fita da yayi daga dakin ya barni tare dasu baki hjy ta fara ban kan nayi hakkuri ai dama haka aure ya gada. A cikin zancen su ne na fahinci tafiyan mu a yanzu bai da wani nisa ke nan duk da ni bai min zancen tafiya ba har lokacin. Duk dana dan sake jiki munyi hira da hjy a dakin nata haka baisa na sake zuciyana kan zancen tafiyan namu ba a lokacin. Tambayan da hjy din ta sako min ne ya dawo da hankalina gareta tana fadin ina dai kawata ba kin biyewa mijin ki bane kuna tsarin iyali nan da sukeyi na kafirai. Lah hjy wallahi bai taba min wanan zancen ba tun zamana dashi kawai dai bama rayuwa irin na sauran ma,aurata dashine har yanzu , na fadi hakan don na kawo hanyar da tafiyan mu zai fasa a lokacin na fadi hakan. Kamar ya ban gane hakan ba da kika fada yanzu don magana kikai min a dunkule hjy haka maganan yake dana fada. Na fada ina dukar da kaina kasa lokaci guda ido hjy ta kura min na dan lokaci kafin tace ki min bayani yadda zan fahinta don wanan ba karamin magana bane kike fadi a yanzu zainab. Shin kina nufin bai taba tabaki a matsayin aurataya ba zainab ko dai kina nufin bai gamsar dake ne yadda ya dace. Zainab ki kwantar da hanlinki ki fada min gaskiyan komai yadda ya dace jafari ba fin karfina yayi ba dagashi har uwantasa zan iya daukan mataki a kansu kan hakan. Jin ta ambaci sunana na sake fadin hjy haka maganan yake har yanzu bawai wani zama mukeyi dashi ba yadda ya dace haka. Wai zancen nan gaskiyane ko al,mara nake ji don na dade da zargin hakan a gareku har in wanan zancen ya zamo gaskiya gaba dayan ku zan dauki mataki a gareku har uwan naku data boye min hakan. Ba laifin mami a nan hjy don ina ganin bata san da wanan zancen ba har yanzu innalillahi hjy ta fada hankali tashe tana fadin shike nan yaron nan ya cuce mu a rayuwa. Me yake nufi da hakan daya aikata ya tauye maki hakki yana daukan alhakin ki haka yar nan ko baida lafiyane ba a sani ba haka ? Lafiyan shi kalau hjy kawai dai bai sha,awan mata ne yace na fada kai tsaye har ina mamakin kaina banda malam kakana ban taba irin wanan maganan da kowa ba a duniyan nan sai ita hjy da nake fadawa ranan. Yau na shiga uku ni zainabu Abu kuna da wanan matsalan haka akai shiru aka saka maku ido a cikin sa. A kira min mijin naki ta fada hankali tashe na mike da sauri na tashi zuwa kiran nasa inda nabar tsohuwar a zaune. A falon shi yake zaune yana shan coffee mai zafi sai turiri yake tashi a cup din daga gefen shi ya bude laptop din shi yana aiki a cikin sa. Na shigo ya dan dago ya amsa sallaman nake fadin hjyce tace na kiraka yace me kuma zan mata yanzu ya fada yana dan jan tsuki dagani aikine mai muhinmanci yakeyi a lokacin. Akan zaman mune da kai na fada mata komai yau take kiran ka akanshi wani irin dago kai yayi yana fadin what da karfi tare da fadin me kika fadawa hjyn ? Kanki daya kuwa zainab ko kin samu matsalane na dan kalleshi ina murguda baki kafin ince kaina daya wallahi. Nadai fada matane don ba zan yarda in koma wurin wa yan nan muggan abokan naka ba a kashe ni a banza wanan kasan ba . Ko a nan din sukaso kashe ki kina ganin ba zasu iya bane idan ma wasa kikeyi a hakan kinyi kuskure wallahi zainab ya fada yana ture computer shi a gefe daya ya mike tsaye. Talkaman shi dake aje gefe daya ya zura a kafan shi ya fita nabi bayan shi ina kallon yadda hankalin shi ya tashi lokaci guda. Har mun kai kofa yaja ya tsaya ya jiyo a hasale yana fadin ki gagauta gyara duk abinda kika fada a yanzu don kinsan condition din da hjy take a ciki yanzu . Idan maganan ki ya kara ja mata matsala a yanzu ta kara kwantawa ciwo ki kuka da kanki ga duk abinda zai iya biyowa baya gun yayanta dake. Baki da hankaki ne ko ina wayau ki ya shiga da zaki zauna kina wanan zancen da hjy at her age baki tunanen komai da zai iya biyowa baya ba. Ya juya ya fara tafiya ina biye dashi har lokacin a bayan shi ba tare da jin komai ba na warning din da yai min din kan hjyn a raina ni dai kawai mafita nake nema a yanzu. A tare muka shiga dakin dashi mun samu hjy tabar kasa inda na barta zaune tana jin mun shigo ta dago kai ta kalle mu . Yanayinta gaba daya ya canza a lokacin kallon shi tayi ba tare data yi magana ba ta nuna muna kujera mu zauna. Shi yakai zaune saman kujeran yana kallon ta na samu wuri a kasa na zauna sai dan shiru ya biyo a dakin . Can ta dago kai ta kallemi tana fadin yanzun muna hira da kawata nake bugun cikin ta a haka naji wani maganan daya daure min kai a tare daku jafari. Me kikaji hjy ya tambaya ta kalleni tace takwara sake maimaita abinda kika fada min yanzu a nan. Na dukar da kai kafin na sake dagowa ina fadin cewa nayi a matsayin budurwa nake da kike tambayana ko nasha maganin haihuwane ban haihu ba har yanzu. Hjy ya tare da fadi nasan zainab a yanzu zata iya fadin komai da zai kawo rashin komawan ta can tare dani . Nagodewa Allah dake ta fadawa wanan maganan haka ba wani ba ai gata a zaune me na rage ta dashi na zaman takewan aure da akeso namiji yaiwa iyalin shi. Duk mai hankali dai ya dubi zainab a yanzu yasan bata tare da wani damuwa a gidana shi haihuwa ba Allah ke kawo shi ba idan lokacin hakan yayi. Nasan ina da rauni kwarai wurin mu,amula da taraiya da ita a yanzu na kuma sha bata hakkuri a kan hakan tun da ni din ba mazauni gida bane ko yaushe. Hjy tace a, a takwara wai haka maganan yake dama kika barni ina tunanen wani abu har hankalina ya daga haka ? Hjy ni dai ki masa magana gaskiya bana son komawa kasan nan wallahi na fada kamar zanyi kuka a lokacin. Don ga daman magana ya samu a gareni kuma hakan yanzu ba zai yuyu ba don ya samu wurin fakewa akan ciwon hjy din wanda gaskiya ne ya fada kuma. Wani abu zai iya samun hjy din a dalilin maganan mu din gaba daya zasu dawo su tsaneni kan hakan danayi tunane. Sai kawai naja bakina nayi shiru ban fasa kwan gaba daya gun hjy ban da nasan zata dauki mataki a kanshi. Sai ga hjyn ta koma fadin nasan maza da yawa a zamanin nan suna irin haka ga iyalin su wanda hakan ba daidai bane sam wallahi. Kuna shiga hakkin iyalan ku da yawa akan aiki da iyakarshi a wanan duniyan zaku barshi yau ina mahaifin ka yake ya rasu ta ba kanta amsa. Duk ko son aikin ka ina ganin bakai na balarabe ba shi da ko yaushe kaje gidan sa baka masa ganin daya kai uku ko biyu ko yaushe yana kashen duniya yana aiki. Kuma hakan bai hana shi zama da iyalin shi ba ai har a sameku don haka ina kara tuna maka a yanzu tunda har kaji yarinyar nan ta fadi haka. A gaskiya tauyewan yayi yawa a gareta ke nan tunda har yana cikin korafin da zata iya fada . Kada ka manta da yadda auren ku ya kasance da yar nan a baya don haka ka guji duk wani abinda zai kawo matsala a tsakanin ku yanzu. Hjy indai wanan shine matsalan za a gyara da yardan Allah ya fada har lokacin bai tare da walwala a jikin shi. Tun daya fita dakin ya barmu hjy tana saman bakin ta dani har akai azahar muka mike don zuwa sallah. A inda na idar da sallah naji kawai nayi amfani da kayan kakar maya a ranan ya kamata in gwada ko wani kamar yadda tace min inyi dasu. Nayi din ko wani har sha da shafawa da dai sauran su don su ba hayaki a cikkn maganin su sai dai sha da shafawa kawai zanyi a jikina. Tun dana shafa ban fito ba duk da baka sanin nayi amfani dashi ma don haka na shige daki abina shima bai leko dakin ba kamar yadda ya saba idan yana gida. Ban kuma kara ganin shi ba sai da dare da zamu kwanta barci na shiga dakin na sameshi yayi zaune ya daga kai sama yana tunane har nayi sallama bai amsa min ba. Nima idona ya bushe a yanzu game dashi don haka ban damu da amsawan shi ba a lokacin na gama abinda zanyi na kwamciya na kwanta abina ba tare dana tanka mashi ba. Ban sani ba ashe maganin yana aiki a kanshi a lokacin ya fara jin wani irin bakon yanayi yana sauka a gareshi a hankali har bai san lokacin da magana yazo mai ba. Ina hawa gadon naji muryan shi yana fadin ke wani irin abu kika shafa haka mai kamshi ya sawa mutum kasala da hawa kan mutum ya fada yana dan lumshe idanun shi kafin ya sake fadin yayi min karfi a kai. Ba tare dana kallo shi ba nace ban shafa komai ba sai turaren dana saba amfani dashi kullun na shafa na fada ina jan bargo zuwa jikina. Banji takowan shi ba sai ganin shi da nayi a kusa dani tsaye gaba daya idanuwan shi sun canza kala kamar ba nasa ba yana fadin ina tambayan ki kina kokarin kwanciya ki kyaleni. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAN UWA FATAN ALHERI GARE KU KO YAUSHE UBANGIJI ALLAH YA SA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA DAMU DA IYAYYEN MU DA ZURI,AN BAKI DA TARE DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA AMIN, , , , YAR UWA KADA KI MANTA DA NOVEL DIN KUDINE KI SHAGALA BAKI BIYA BA AKWAI NAUYI A HAKAN KIN SANI, , , , Allah sarki yar uwa novel dina bana soyayya bane ko wani jin dadin duniya ina novel ne don fadakarwa a yadda rayuwa ke tafiya a yanzu don ki gyara da kanki ko ki gyara wasu ta hanyar novel dina ubangiji Allah yasa mu karu da juna anan duniya ranan lahira ke shedace akan duk abinda na rubuta a ciki. Bana fata ko in yarda alkalamina ya kaini wuta don kawai in gyara maki rai in saka zuciyoyin ku a cikin wani yanayin dana san za,a tambayeni a kansa gobe kiyama. Novel dina kan abinda ke faruwane a cikin gidajen mu na hausawa a yanzu da kuma yadda zaki fitar da yar ki ko kanwarki a cikin kangin rayuwa don haka idan zaki karanta ki karanta a hakan don idan kin lura wanan rayuwan na yanzu bawai don kayi aure zuciyar ka ya huta bane da itun kalubalin dake baya. Allah ya iya muna yasa mufi karfin zukatan mu a rayuwan mu na zaman duniya Allahuma amin Allah. Zaune yakai bakin gadon tare da dafe kanshi na tsawon wani lokaci yayin da gaba ya shiga faduwa don basan halin da yake jin kasa kusa ba. Sanin shi din ba cikakken mutum bane kamar kowa a yanzu kallon da nake mai ke nan a zuciyana karfin addu,an iyayyene da ikon Allah dake aiki a kaina na tabbatar ya zaunar dani a yanzu gidan shi. Don wani lokaci idan ina tunane zanji zuciyana yana raya min na gudu na tafi can duniyan da ba,a sanni ba inyi rayuwana acan da zama a gidan wanan munafukin Allah a yanzu. Amma koda zan tashi sai naji zuciyana ya canza min shawara akan hakan zanjini wani lokaci wasai ko kuma ina tausayin shi. Kinsan zama na hana mutum ganin laifin wanda kake zama dashi ko yaushe wani lokacin zaka san ba a daidai mutum yake ba kuma ka kasa rabuwa dashi a hakan. Idona biyu dai a lokacin ina sauraren shi dan filin dana bari a gefen dana kwanta naji ya kai kwance a wurin hakan ya sani dan bude idanuna ina kallon shi a fakaice. Kwanciya yayi a rigingine tare da daga kafanshi daya ya tokare na dan kada shi kadan ya jingina bayan shi da kan gadon yana kallon saman dakin. Zainab a tunane a yanzu ba zaki iya fadawa kowa matsalan ki na zama tare dani ba duba a yadda na rikeki a zuciyana nake gani. Sai dai kash a she yadda na dauka abin ba haka yake ba ke a wurin ki a zuciyar ki kuma kuma koda yake kinyi kokari a hakan ma don sam banga laifin ki ba ko kadan zainab. Nasan wanan kwarai ban cancanci wata mace ta zauna dani ba a hakan sam don yadda rayuwana yake da akasin da mu hausawa mukafi tsana a duniya. Allah yasan nasan kinyi hakkuri kan hakan amma ki kara dora hakkurin ki akan wanan din don ni kaina jikina yana ban zan bar wanan harkan nan gaba kadan insha Allahu. Sai lokacin na samu magana don hakkurina ya kai karshe a lokacin na fara fadin ka daina ka daina shan giya ko ka daina kwana da maza yan uwan ka ko kuma tsafin zaka daina ? Naji yace hummm zainab ke nan a yanzu nasan kinsan komai don haka kome zaki kirani dashi ki kirani dashi a yanzu din ya fada yana runtse idanuwan shi a hankali. Wani iri naji a raina ba dadi don hakan ya zama kamar gori nayi mai a yanzu din ban san lokacin dana bude bakina ina fadin Nasan jarabtane hakan a gareka don Allah kan jarabci imanin bawan sa tako wani hanya don yaga karfin imanin shi to amma yaya tunda ka gane hakan ka yaki zuciyar ka ka mayar da lamarin ka ga ubangiji ka Allah shine mafita. Ka dauka ba mai iya yiwa bawa komai a duniyan nan sai Allah shike kashewa ya raya kuma aduk lokacin daya so hakan ga bawan sa. A jiyan zuciya naji ya sauke daga inda yake kwance din a gefena naci gaba da fadin yau yaya baka zama kayiwa kanka tunane akan wanan rayuwan naka. Idan akace yau babu kai dukiyan naka da kake nema ya zama ganima da abin wasoso ga duk ahalin ka . Tunda ba zuria ko wani ka aje a duniya da zai gajeka ba a yanzu a kadara kana da zuria din yaya yaya ka ke son su kasance a cikin al,umma da rayuwan su. Ni kaina a yanzu a kunyace nake shiga yan uwan ka tunda ina ganin kowa yasan irin rayuwan kyaman da kakeyi a yanzu balle yayan ka na cikin ka da kowa ke maka fatan samu a duniyan nan. Ina maganan nan ne badon kwadayin abinda kake dashi ba ko dan nagada a,a ina magana ne don tsakanin mu dakai ba a san gawan fari ba a wurin Allah . Kadara kai namiji ne a kullun mami tana maka fatan samun wata macen wayayya wace ta dace da rayuwa irin naka. Ya kake tunanen zataji idan ta riskeka a cikin wanan halin baka tuba ka koma ga ubangijin ka Allah ba kana zaton zata kyale duniya bata jiku ba ke nan. Hannun shi naji ya dora a saman kaina lokaci guda ya dafa min kai yana gyara kwanciyan shi a yadda yake kwancen da farko. Zai,nab naji ya fada a hankali tare da sauke numfashi a cikin wani irin yanayi ya fara magana a hankali yana fadin . Nima a kullun akai zancen haihuwa gareki ina mai jin zafin hakan don nasan laifin ba naki bane nine mai laifin ga baki daya kuma ake dorawa a kanki. Nasan ba ko wace mace bace zata iya daga min kafa a hakan koda kuwa duniyan nan da abin cikin sa nake bata alherin shi a kullun. Sai a asirina ya tono ga jamma,an duniya zuwa yanzu din kowa ya gama sanin koni waye a hakan nayi nadama ina fada maki ko yaushe kan shigana wanan harkan duk da ba zance ga lokacin dana tsinci kaina a hakan ba duk da nasan ko nayi rantsuwa ba mai taba yarda da zancena a yanzu. Tsam naji a duk kan ilahirin jikina don jin saukan hannun ya jafar da nayi ya sauka a jikina wanda hakan ya sani dan razana da yin hakan da yai min din a daidai lokacin da ban taba tsamanin hakan ba a gareshi. Dan tsoratan da nayi din yayi daidai da runtse idanuwan shi a daidai lokacin yana jin wani bakon yanayi yana sauka mai wanda hakan yake ganin sa kamar zai aikata wani sabone gayin rikon da yai min din a lokacin. Sai dai kuma duk da hakan ya kasa cire hannun shi daya riko ni dashi a jikina din a lokacin maimakon ya cire din kamar yadda zuciyar shi take gargadin shi da yi saima kara rikoni da yayi a lokacin ya matseni sosai a jikin shi . A daidai saitin kunne yake magana yana fadin kamar mai rada kin san me zainab ban samu ko fadin a, a ba gareshi a yadda nake razane dashi a lokacin. Tsorona daya shine kada ya matseni yace zai min dole ta baya wanda hakan tun lokacin da umma ta umurceni da zuwa dakin shi koda bana son hakan idan nazo na saba zanji duk abinda nake ji a kanshi ya gushe min a zuciyana. Wanda ni ba komai nakewa tsoron haka ba sai gujewa bacin rana irin wanan yaga kamar ni din irin mazan da suka saba mu,amula da sune yazo ya halakani a banza banji ba ban gani ba. Kaduwa sosai jikina keyi naji yana fadin ko kowa bai yarda da rantsuwana ba aduniyan nan ke zainab nasan zaki yarda da abindana fadi a kaina a ko inane kuwa zaki shedeni a kan wasu halaiyana da kika sani a baya da yanzun da nake fadin na daina din a yanzu. Duk da tsoron da nake ji a lokacin nasa hakan baisa hankalina ya gushe har na kasa fadin yardan Allah da amincewan shi a yanzu gareka yafi na kowa da zaima ka. Don Allah subbahanahu kaiwa sabo kuma yafiyan shi zaka nema a yanzu don ya yafe maka kurakuran ka yaya. Komawa ga Allah gareka a yanzu shine babban abinda ke gaban ka duk na mutane mai saukine . Allah zai iya sa mantuwa ga zukatan wasu su manta da ka taba aikata hakan a baya, tuban ka zai iya sa Allah ya shafar dasu komai a kanka ga baki daya. Banyi aune ba a wanan lokacin da nake maganan sai ji alaman kukan nadama da naji yana yi a lokacin. Nima kukan ne yazo min don ko banza naga wani na kuka haka nake nima sai hawaye yazo min balle wanan da yake shakikina a yanzu mafi kusa dani da kowa a duniyan nan yana cikin wani hali na rayuwa. Da kyat yayi shiru koshi wayan shi dake ta ringing ne a lokacin ya sa ya mika hannu ya dauka ba tare da yayi magana ba sai sauraren mai magana a lokacin da yayi. Yana gama wayan ya kashe ya aje a gefe daya ya rufo hannayen shi gaba daya a saman jikina lokaci guda ya matseni ta yadda muke iya jin numfashin juna a lokacin a haka kowa da nasa kalan tunanen barci ya daukeni a jikin shi . Misalin ukun dare ina barcin kamar a wahalce acan cikin barcin nake jin wani irin nisi a kusa dani wanda tun kan na bude idanu nasan inda nishin yake fitowa . Shine duk da yana cikin wani irin yanayi hakan baisa ya raba jikina da nasa ba yana rike dani da hannun shi daya a jikin shi. Yayin daya dafe maran shi da hannun na hagu yana yanka wani irin gumi tun daga kafan shi har zuwa kanshi . Na tashi a rude ina kokarin kwacewa don na samu na taimaka mai a halin da yake ciki yake fadin kada ki daga nan zainab . A wahalce yake magana a lokacin duk da na saba da ganin hakan wani lokaci wanan yanayin yafi na duk wanda yayi a baya muni sosai. Can yakai ga wani irin zabura kafin ya kai ban daki ya fara wani irin kakarin amai kamar zai zubo mai kafin yakai bayin a lokacin. Ganin hakan yasa dole na mike zaune ina binshi da kallo a cikin yanayin da yake din na ban tausayi da al,ajabi. Don nasan wanan halin da yake ciki a yanzu yana da nasaba da rikon da yai min muka kwanta a tare ya jawo mai wanan wahalan haka. Raina naji yayi wani irin baci lokaci daya na gyara zama ina hada kaida gwiwa na takure a wuri daya na dinga kuka a hankali. Yafito bayin dafe da maran shi yana tafiya dakyat yazo bakin gadon ya dan zauna a gefe ya dukar da kanshi kasa kamar mai tunane. Sauka nayi zuwa ban daki na dan dauki lokaci na gyara ko ina koda na fito na samu yana sallah a zaune na bishi da kallo. Muna zaune ba wanda yai magana a cikin mu kowa na lazumin shi motsin da naji daga bayan mu yasa na dan firgita kamar anyi tsoki an fita daga dakin nashi lokacin naji da kunnuwana sai dai Allah ya gyara ban yarda na juya ba . Wani irin iskane aka fara yi a wajan gidan kamar hadari ya yaso a garin ko guguwa mai karfi cikin dan lokaci kuma muka daina jin hakan. A daidai lokacin ne na kula da yanayin da yaya da ke zaune a kusa dani yake ciki yana wani irin kaduwa kamar mai jin sanyi ko zazzabi mai karfi a lokacin. Ni kan naga ta kaina a wanan rayuwan yau nice auren dan giya dan luwadi dan mafia kuma ashe shiga kungiyan ma bala,ine kala kala a rayuwan mutum irin haka. A dadafe mukaga safiya dashi saidai wanan karon akwai bambamci ga yadda na saba ganin shi a baya idan yayi ciwon shi gari yawaye sai ya mike tamgararan. Wanan karo kan yasha bamabam da wacan din don zuwa safe kamar ciwon karuwa yakeyi a lokaci. Sai amai da gudawa yakeyi sosai wanda hakan ya tayar min da hankalina ya mamud na kira a boye don yayi min kashedin fadawa kowa halin da yake ciki din a ranan. Ba bata lokaci ya iso gidan layina ya kira na fada mai ina sama wurin shi ya sameni a nan saman dakin shi do ban fito ba har lokacin. Yana ganin yanayjn da dan uwan nasa yake cikine ya rude tare da tambayana zainab yaushe ya fara hakan nace dashi. Lafiya lau muka kwanta dashi zuwa rabin darene hakan ya faru dashi har wanan lokacin wanan kan ba abin kyalewa bane dole mu sanarwa mami taji ya mamud din ya fada . Layin mami ya fara nema ya fada mata nan ta hau fada don me ba a wuto dashi asibiti ba tun dazun ko so muke ya halaka a gida. Mami kizo fa wanan kan ba abin kaiwa asibiti bane gaskiya sai jikinta yayi sanyi ta koma magana a hankali tana fadin . Wani irin yanayi ne mamud kuyi wani abu don Allah kafin na karaso ta fada hankali tashe me zamu iyayi ga hakan mami sai kawai ta fashe da kuka ya kashe wayan. Ina jin haka nace yaya ina zuwa na fita zuwa dakina bincike na fara yi kafin ingane maganin da tsohuwa kakan maya tayi min bayani ranan idan naga irin yanayin nan tare dashi. Na fito da sauri zuwa kitchen na jona heater dan kankanin lokaci ruwan ya tafasa na hada komai na nufi dakin yan aikin gidan sai faman gaidani sukeyi da kwana ban tsaya binta kansu ba yadda na saba sama sama nake amsawa idan sun gaida ni din. Dakin na nufa na samu yaya ya kamashi zuwa bandaki sun fito na shigo dauke da cup din maganin ina mashi sannu. Saidana aje cup din nake fadin ya ko zaisha wanan maganin kafin mami tazo mu gani yace zaisha mana zainab kin hadane ya fara sha agani. Na dan zauna ina fifitawa har yayi sanyi don ta fada min sai yayi sanyi sosai zaisha kamar yadda tace din haka nayi komai daki daki. Yana kurbawa na farko ya saki wani irin gyatsa mai karfi lokaci guda sai kuma ya fara hamma ba kakautawa muna tsaye muna kallon shi nida ya mamud din . Ya kara sake wani irin gyatsa har mai warin tsiya saida muka kawar da kanun mu ga kallon shi da sauri anan kasan ya leme sai barci . Dan uwan na fadin ka hau gado idan barci zakayi zaifi ma dadi jafar ina har barcin ya kwashe shi ko a lokacin. Daga inda nake na sauke ajiyan zuciyar da har ya fito fili ban sanda hakan ba sai ji nayi ya mamud na fadin . Zainab kiyi hakkuri da wanan jerabawan da Allah ya aiko maki dashi haka tun ran gini ran zane Allah ya rubuto kece zaki shiga a cikin wanan wahalan haka. Godiyan mu ga Allah da hakan ya kasance kece a gidan shi a matsyin matar shi a yanzu da wata ce ko wace mami ke gani a lokacin itace ta dace da jafar din ai da tuni zancen ya wuce nan ko. Amma yanzu kinga tun mami naganin kwadayine har yanzu ita da bakinta ta gane gaskiya tana godiya da haka ya kasance kece a matsayin mata a gareshi. Nasani zainab watarana mami zata rokeki gafara da bakin ta kan hakan tunda yanzu tasan abunda Allah ya shirya a zaman ki dashi haka. Hakuri yana da dadi zainab don hakkurin ki yayi muna amfani kowa yanzu ya sani Aisha kanta jiyan nan nake jin tana fadin bata san da wani ido zata kalleki ba a yanzu. Ko yanzu na sani maganin da kika bashine Allah ya taimakeshi ya samu barcin nan da yayi a yanzu don wallahi da badon Allah ya gyara ba yasha wanan abin da bansan me zai faru ba zuwa yanzu gareshi. Hawaye ke fito min a idona na kurawa inda yaya din yake kwance ido kawai ina kallon shi ga mutum har mutum idan ka ganshi amma ya samu akasin rayuwa a tare dashi. Muryan ya mamud din ne yake fadin ni nasan babu yarinyar da zata zauna da jafar ko na tsawon wata daya a wanan hakin haka da yake ciki. Yanzu ne kowa zai gane shi mutum yana da ranan shi ta hanyar da baka taba zato ba don ance ke yar tallakane baki cancanci auren shi ba a lokacin. Sai Allah ya nuna muna tallaka yana da ranan sa sosai don zaiyi abinda kudi baya iyayiwa mutum shi a rayuwa don na tabvatar da zabin mami din ya aura a lokacin da yanzu wallahi duniya ta gama sanin komai a yanzu. Sallaman mami da su jamal ne da suka shigo hankali tashe dakin ya katse shi ga maganan da yakeyi a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH JUMMA,AT MU BARAK YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN AMIN, , , , , Bin yadda yake kwance a cikin wahala kowan su keyi jamal ke fadin yana numfashi kuwa ? Yanayi ya mamud ya bashi amsa ai don zainan ma ta taimaka ta bashi wani magani dazun ya sha shine har yake hakan. Da sauri mami ta juyo ta sauke kallon ta gareni tana fadin me kika bashi ya koma haka zainanb me kika shirya kike son ganin bayan shi a yanzu. Wallahi idan wani abu ya samu dana bazan taba yafe maki ba kema sai naga bayan ki har iyayyen ki. Kai haba mami wanan maganan bai dace ba haka dan Allah ba don yarinyar nan data take tsaye a kanshi ba ai bamu san halin da yake ciki ba. Wa yasan hanlin da suka tsunci kan su zuwa wanan lokacin da badon ita data bashi wanan maganin ba dazun da wallahi kila da yanzu mun rashi ga baki daya har abada. Itace tafi kusan dashi take zaune dashi tasan irin laluran shi a yanzu don haka ba zamu zargeta ba mami, kan halin da yake bayan duk munsan da abinda yake damun shi a nan. Jamal ne ya fara fadin gashi kuma mami kai brother asibiti haka kamar tonon asirine a wurin ki a garin nan sai nake ganin kamar a samo yarddaden likita a dauko shi gida yazo ya dubashi a nan. Nima haka nagani ya mamud ya fada daga gefe mami kan ta koma ta zauna saman kujera ta kurawa dan nata dake kwance a kasa cikin wani hali sai hawaye take sakewa a lokacin. Bata iya furta komai a wanan lokacin don bakin ciki da takaici da yai mata yawa a zuciyar ta ina zata kai wanan abin kunyar da jafar ya dauko mata a cikin iyalin ta yanzu . Kai kome zasu fada a kaishi asibiti kawai wallahi a dubashi a san halin da yake ciki zaifi jalal ya fada. Nima dai abinda naga yafi ke nan Aisha ta sake fada daga inda take zaune a takure a lokacin na dago kai da sauri tare da fadin . Don Allah kada ku kai shi asibiti a cikin wanan halin da yake ciki haka ku taimaka ku rufa mai asiri da akaishi asibiti gara dai likitan yazo gida ya duba shi don Allah. Ya mutu kike so Aisha ta fada a hasale tana kallona kamar zata cinyeni danya a lokacin da take wanan maganan cikin kunan rai take tambaya na hakan . Mami ta dagp kai tana fadin gaskiya zainab ta fada fitar dashi haka zuwa asibiti tonan asirine kamar yadda kuka fada da farko. Don haka kai mamud wani likita kake ganin zamu nemo a wanan case din nasa yanzu har lokacin idon ta na kansa inda yake kwance tana kallon shi. Ina gefe ina sauraren shawaran nasu kai mutum dai ba abakin komai yake ba lafiya itace jarin ga mutum da ya kumce ma ka rasa komai, komai arzikin ka kuwa. Wani likita ya mamud din ya kira yace a bashi dan lokaci yana tafe duk zaman da nakeyi wurin bakina na dauke da addua a lokacin. Tun ina yi a boye har na fara fitar da sauti ina karatun a fili duk suka bini da kallo kamar kullun amanal rasulu nake karanta mashi sai yasin haka ma wanan lokacin shinakeyi a hankali suna saurarona. Dakin yayi tsit sai muryana dake tashi a lokacin can ya dan motsa hannun shi kadan alaman yana son ya falka a lokacin. Gaba dayan mu ido muka zuba mai kafin can ya bude idanun shi da kyat yana fadin zainab bani ruwa in sha don Allah ba wanda zai gane me yake fadi a lokacin don muryan shi daya dakushe bai fita sosai. Na dago kai na dan kalli ya mamud dake kusa damu ina fadin wai ruwa yake son sha. Bashi wanan can da kika rufe dazun ya sha tunda a kwai sauki sosai daya sha shi dazun na tashi a daidai lokacin da mami ke fadin ruwan meye wanan din sauran kuma duk suka bini da idanu har na dauko ruwan dake rufe a gefen gado cikin cup din glass. Na kawo mai tare da dan kiran sunan shi ina fadin yaya ga ruwan ya bude idanun shi da kyat ya sauke a kaina. Dan yun kurawa yayi don ya sha ruwan dake hannuna ya kafa kai yaja sosai kafin kuma ya dakata na dan lokaci ya dago kai ya kalleni. Muryan ya mamud din ne yake fadin shanye mana jafar don Allah yana da amfani a gareka sosai. Ya dan daga kai ya kalli inda ya mamud din yake kafin ya mayar da kanshi ga kallon dakin ga baki daya sai a lokacin yasan a kasa saman ties yake kwance don neman wa jikin sanyi a lokacin. Muryan mami da yaji tana fadin kasha maganin mana jafar ka tsaya kana kallo kuma da sauri ya juya inda take tana zaune tana magana saman kujeran dakin nasa. Sannun da yan uwan ke masa ne ya kara juyawa wurin su yana kallon su kamar bai ganesu ba a lokacin. Karbi ruwan kasha yaya na fada daga inda nake tsungune ina bashi ruwan da zai sha ya juyo a hankali ya karbi ruwan daga hannuna. Tunda ya kafa kai bai cire a cup din ba sai daya shanye ruwan ga baki daya ya miko min cup din na karba daga hannun shi. Ki kamani in koma saman gado ya fada a hankali don haka sai na aje cup din sa sauri har yana faduwa kasa . Ban damu da hakan ba nayi saurin kai hannu ina kamashi ya mike a hankali muke tafiya har zuwa bakin gadon ya dan zaunan kannen nasa suka kara mashi sannu ya amsa da kai kawai. Har saida ya kwanta sannan na dago ina sauke ajiyan zuciya ya jamal dake tsaye ya tokare jikin shi da mirrow dakin yace dani sannu zainab da kokari. Nayi dan murmushi na juya inda na aje cup din na dauka tare da nufan kofan fita daga dakin kai tsaye. Fitana daga daki yayi daidai da mikewan mami ta nufi bakin gadon da yake kwance ta zauna a gefen shi a hankali jin hakan yasa ya dan juyo kai ya dan kalli wurin. Ganin mami ne ta zauna a kysa dashi yasa ya dan juyo gareta yana fadin yaushe kuka shigo mami ina barci ko na dan samu barci ke nan ashe. Don jiya bamuyi barci da dadi ba dagani har zainab a wahalce muka kwana a gidan nan amma yanzu naji sauki sosao barci kawai nake ji da kasala ya fada yana gyara kwanciyan shi. A falo na samu su fadila da sauran yan aikin gidan suna zaune a cikin jimamen meke faruwa ne sunga su mami sunzo rai bace. Gashi kuma har lokacin basu ga na fito part din ba hjy tana ta aika sadiya a duba ko lafiya anace mata ban fito ba. Suna ganin fitowa na fadila tare da mai aikin wanke wanke da shara su kayo kaina suna gaidani sauran ma suka biyo bayan su suna gaidani. Na amsa ina wucewa har na dan taka nake fadin anty in ganki mana ta biyo bayana da sauri sauran ma suka watse a lokacin. Tunda basu ga wani alaman komai a tare dani ba muna shiga dakina a tare tana bayana nake fadin ko za,a samu freash meat da milki a gasawa oga yau baya jin dadin jikin shi tun daren jiya. Aiya da sauki ko ta tambaya nace yaji sauki yanzu sosai yana can tare da su mami da yan uwan shi don Allah a gasa mai idan za a samu a aika da wuri na fito da kudi ina mika mata. Take fadin jiya an bada kudin da za ayi sayayya barin aika a ciki a sayo komai yanzu ta fada da sauri tana fita na dan bita da kallo. Wanka na shiga don a matse nake a lokacin ina shiga na sakewa kaina ruwan zafi sosai don har saida naji ya kama min jiki na goga sabulu na fito . A gurguje na shirya duk da barcin daya cika ni a lokacinn don har idona sun fara nauyi a lokacin don barcin da nake ji. Saidai babu daman yin hakan gareni don su mami dake gidan a lokacin dole in koma in sallamesu kafin su tafi. Saidai ina shiga dakin ban samu mami da Aisha har jalal a dakin ba sun fita zuwa dakin hjy su gaisa da ita . Sai ya mamud da jamal tare da wani likitan da aka kira shi ya jafar din yana zaune ya dan jingina jikin shi da gado. Ina shigowa suka dan kalloni sai na dan tsargu da hakan na daburce ina tambayan mami su har sun fitane ? Ya mamud ke fadin sun shiga wurin hjy yanzun nan da likita ya shigo zai duba jafar din na dan juyo ina gaida likitan kafin na sake juyawa zan fita daga dakin. Muryan ya makud ke fadin ki tsaya zainab ga maganin da likita ya bashi da lokacin da zaisha idan time yayi na dan dakata likitan yana yi min bayanin komai. Na tsargu da irin kallon da yaya jafar din ke min yasa ban ko tsaya fahinta ba na juya na fice daga dakin, wanan halin da yaya jafar yake nuna min na kishi a gaban wasu. Dakin hjy na nufa a nan na samesu zaune nake gaida hjyn da kwana bata amsa ba take fadin ke yar nan ashe abinda ke faruwa ke nan har wa yanda basu kwana a gidan ba sunji sunzo mu bamu sani ba. Kiyi hakkuri hjy ban fito bane sai yanzu ya mamud ne ya kira ya fada masu bani bace na kira na fada a ladabce. Yanzu ya jikin nasa da sauki ko nace yana ma zaune suna hira na fada sai ga fadila ta shigo tana fasin madam an gama komai kamar yadda kika ce ayi. Na amsa da godiya ina fadin gani fitowa in duba mami ke fadin bari su leka ta ji me likitan ya fada game da jikin nasa ni dai kafin su fito na bar dakin kai tsaye. Na samu sun shirya komai yadda ya dace na dan duba kafin na dauka na nufi dakin nasa dashi suna cikin dakin dukkan su a lokacin na samu likitan ya mike yana tsaye suna magana da mami na shigo dakin. Kai tsaye na kai gaban shi na aje na dauko dan stole na dora akai ban kai ga mikewa ba mami ke fadin wanan meye kuma aka kawo mashi ? Duk idanuwan su yana kan abincin na bude va tare dana bata amsa ba kamshine ya game dakin lokaci guda da tururin abincin yana tashi sama. Gurfane nakai a gaban shi tare da dan dago kai ina fadin a zuba da yawa zakaci ko ya dan kada kanshi kadan ba tare dayayi magana ba na fara zuba mai a hankali saida ya dan kai yadda yake tunanen zai iya ci yace ya isa. Good likitan ya fada yace wanan ya dace dashi a yanzu yadda yaji jikin nan dole sai irin wanan abincin dama normal milk danye na tsiyayya mai tare da ajewa gefe na mike tsaye duk suna kallon abinda nakeyi a lokacin. Juyawa nayi zan fita yake fadin ina kuma zaki ki zauna muci don nasan kema baki karya ba har yanzu zan tafi in duba sadiyace ban gata ba tun dazun na bashi amsa na fita. Gaskiya zainab tana da kokari wallahi tasan duk abinda ya kamata ba sai an fada mata ba jalal ya fada Aisha ta amsa da gadkiya kan . Da gaskiya gun sadiya din zan tafi don duk abinda nakeyi hankalina yana gareta na rashin ganin ta da banyi ba din. Tana kwance ta rufe jikinta wai sanyi take ji alaman dai bata da lafiya ke nan na karasa wurin ta hankali tashe. Ina kware abi rufan tare da dan kiran sunan ta ina tambayan ta meya sameta ta nuna min kanta ke ciwo. Fadila ce ta shigo dauke da abinci a ture take fadin dama yanzu nake fadin kila baki san bata da lafiya ba haka ashe kina nan ma. Ta aje kayan tana fadin dama ina son in fada maki daren jiya bamuyi barci ba a gidan nan duk wanda ya kwana a gidan nan a jiya yaji tsoroa gidan nan da bamu san dalili ba. Allah ya taimaka daga hira sadiya tayi barci a wurina nan muka kwana a dakina a tsorace sai kusan asuba muka daina jin tsoro . Basar da zancen nayi ta fadin kai kodai iskan da kukaji anyi jiuan ne kuke jin kamar motsine anty tace wata kila ko hakan ne wallahi. Nan dai muka zauna a tare mukayi break fast a daki mu uku muna hira wayana ne ke ringing a lokacin na dauka . Malam ne kakana jin na ambaci sunan malam din yasa su kallona muna gaisawa na mike na fice a dakin . Mun dade muna magana dashi yana ban labarin artabu shi da bakin shi a daren jiya din inda yai nssaran koran su fata fata ta yadda ba zasu kara tunkaranshi ba da yardan Allah. Nan ya fada min wasu abubuwan da zanwa jafar din nayi mai godiya bayan munyi sallama na fito zuwa dakin hjy na samu tana sallah a lokacin. Na juya na fita daga dakin fafila ke fada min su mami sun tafi ya mamud yace naje na duba jafar din da suka bari shi kadai a dakin shi. Na shiga na samu ya dan mike zai watsa ruwa shigowana ya jiyo yana fadin wanka nake son inyi ko zan kara jin karfin jikin nawa a yanzu Bari na gyaro ban dakim na fada ina kallon shi jikin shi yayi wani irin radau radau kamar yasha duka ko sunyi fada da wani a lokacin. Bi jikin nasa da yaga inayi da kallo yasa ya dan juyo yana kallln jikin nasa yace wanan kike kallo aiba komai bane tunda sun barni da raina. Ke nan su din ne suke baka wanan wahalan na tambaye shi ina kallon shi yace ya zasu dani tunda yanzu na daina duk wani abinda suke so na taka masu doka suke gani Zaman lafiya shine kabi tsarain su da dokan su a zauna lafiya ko kinsan kwamciyan kinan a tare danine dalilin wanan azaban da nake sha a yanzu. Na zargi hakan dama tunda naga wanan wahalan naka yayi yawa a yanzu idan har shiga dakin zai saka su dinga baka wahala haka zan daina shigowa yaya don su daina. Kina tsoron hakan ne ya tambaye ni nace ba wai tsoro hakan nakeji ba tun farko yaya ka riga da kashiga kungiyan su yanzun ko ya zama dole a bisu a sannu don ka zauna lafiya dasu din . Dan murmushi ya sake a fuskan shi tare da fadin koma me zasuyi min a yanzu sai dai suyi don na daina wanan harkan har abada ke nan insha Allah. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM FATAN ALHERI GAREKU DUKKA MASOYA ALLAH YA TAIMAKA YA BADA SA,A A RAYUWA AMIN LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KIBBIYA DARI UKU KI KARANTA A CIKIN SALAMA YAR UWA. Idan na tsaya fadan irin wahalan da yasha a wanan lokacin zamu bata lokaci a labarin don amai da gudawa yayi shi yafi a kirga tun yana iya tashi yaje da kanshi har yakai baya iya tashi a lokacin. Kuma ban daina mashi amfani da maganin wurin malam da kakan maya da suka bamu ai amfani dashi don matsalan. Duk da nasan maganin suna da karfi suna daya daga cikin abinda ke karasashi zama weak a yanzu saidai hakan baisa na tsorata ba don malam dake kara min kwarin gwiwa da shi da maya a ko wani lokaci. Har yan uwan shi ba,a bari sun san da zancen wanan rashin lafiyan nasa ba cewa ake ya yayi tafiya a lokacin. Haka kuma ya mamud ya gargadi duk wani wanda ke gidan a lokacin idan azo nemasa yayi tafiya dazun da asuba duk da sunyi mamakin jin ogan nasu yayi tafiya ba tare da sanin su ba. Don ya saba idan zaiyi tafiya ya tarasu ya dan raba masu dan kudin kashewa a hannun su sai sukaji ya tafi bai samu ganin su ba hakan sai bai masu dadi ba a zukatan su. Sannu a hankali jikin ya fara dawo mashi daidai duk da hakan kuma ba a leka asibiti dashi ba nice sai yan uwan shi muke fama dashi haka a gida har Allah ya kawo mai sauki a hankali ya fara fitowa falo yana shan iska idan ya gaji ya koma daki kuma. Yau da kanshi ya fito dan karamin falon shi ya zauna ya dan mike kafan shi a saman dan karamin stol dake wurin. Ya dafe goshin shi da hannun shi daya tare da kurawa kasan dakin ido yana tunane. Yayana yau da kanka kafito na fada abinda yasa shi dan dagowa ke nan daga yanayin da yake zaune din, ya dan dago kanshi ya dan kalleni tare da dan sake murmushi ta gefe fuskan shi. Aje dan cup din da na shigo dashi a hannuna nayi daga gefen shi ya kalla ya wani bata rai kamar karamin yaro a lokacin. Dan murmushi nayi na koma gefen shi na zauna ina kallon shi kafin ince sauki ya samu ke nan tunda har ka fara tsanar magani a yanzu. Bana jin dadin sha sa a yanzu ya fada yana kawar da kanshi gefe daya nace hakkuri zakayi kasha daga gobe shike nan ya kare ai. Zama ya gyara a irin yanayin dana riskeshi a ciki da farko sai dan shiru daya biyo falon tsakanin mu na dan lokaci. Kafin muryan shi ya maye shirun da fadin zainab nasan kina kokari dani ba kowa bane zaiyi wanan abinda kike min duk da kinsan makasudin matsala kika zauna dani haka kuma kika yi jinyana a hakan . Duk da irin halin da mami da yan uwana suke nuna maki a kaina hakan baisa kin gujeni da halina ba duk nasan abin yana damun ki a cikin zuciyar ki kuma. Kiyi hakkuri ki yafe min duk wani abinda nayi maki tun haduwana dake zainab ina rokon ki da kiyafe min don Alla. Da sauri nakai hannu saman bakin shi ina rufe bakin nasa da hannu ina fadi cikin murya mai nuna alaman kuka a lokacin . Ka daina fadin haka yaya ko nayi aurena nayiwa kuma wa mijina nayi don ance aljannan mu mata yana karkashin kafan mazajen mu. Kai din kuma koba aure a tsakanin mu kacancanci hakan a gareni ya don kaimun komai a rayuwana yaya ka ingata rayuwana ka taimakawa kanwa da yan uwana ashe nima din ba zan saka ma da irin alherin da kake min ba a kullun. Taimako a tsakanin mu Allah ya hada zaman rayuwan mu a wuri daya hakan na nufin mun zama daya da kai a yanzu. Idan kana cikin farin ciki ko akasin hakan nima hakan ya shafeni don nayi ma abu ba sai ka gode min ba kaina nayiwa hakan. Wasu hawaye masu zafine suke zubo min na kasa magana naji ya jawoni zuwa jikim shi yana dan buga min baya kamar karamar yarinya a lokacin. Zainab ki godewa Allah da ya sa kika zama silar shiryuwana a duniya dana mutu a cikin wanan halin da ko uwata ta kasa fitar dani a ciki sa ya zanyi me zan fadawa ubangijina a wanan halin. Ke din zainab alherice ga duk wanda kika zauna dashi ke haske gun duk na tare dake zainab farin cikine ya dace dake a yanzu ba kuka duk da wani farin ciki sai a kuka bawa ke iya nuna hakan. Don haka kiyi kokan ki a yanzu don kukane ya dace damu a yanzu don godiya gun ubangijin mu. Ina son ki sani ni jafar nayi maki alkwari a yanzu duk wasu munanan halaiyan da nakeyi a baya na daina su har abada kuma inawa masu irin halina na baya da Allah ya fitar dasu a cikin sa kamar yadda yai min sanadi dana barshi nima a yanzu. Yakai yanzu kunyan kaina nake ji da duk wani na tare dani dayasan hakan a kaina ina bakin ciki a yau dana wayi gari ina tuna nayi wanan halin dabbobin a baya zainab. Sai kawai naji ya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya a lokaci daya , rudewa nayi na rasa abinyi sai can na koma fadi in girgiza kai don Allah yaya ka daina wanan kukan bashine yanzu a gaban kaba. Dacewa yayi ka koma ga Allah har idan kasan akwai wani sauran abin haramun a tare dakai har yanzu kayi gagawan fitar dashi a gare ka . Ta hanyar yin sadaka ko ka tambayi malamai abinda ya dace kayi da wanan abin shine nake ganin abinda yanzu ya saura kayi . Ma,ana a cikin dukiyan ka ko wani kaddara daka aje da kudin hharamun sai kayi gagawab fitar dashi a hannun ka don a yanzu ya haramta a hannun ka tunda ba ta hanyar halal aka sameshi ba. Ajiyan zuciya naji ya sauke tare da lumshe idanuwan shi yana gyara zaman shi tare da mike kafafuwan shi duka biyu kafin yace. Duk ba wanan bane damuwa na zainab don nasan dukiyana na zufanane na sameshi a kashin kaina ga baki daya. Elimenatis din mu kawai na wayewa ne da harkan homo bawai don arziki bane ko wani abu kawai dai hakan wayewa ne a garemu duniya ta dauki mutum da tsoro ko wani abu can. Ai akwai wa yanda basu da komai kuma suna ciki kungiyan tare da kowa kawai ni yanzu abinda ke damuna shine. Sai ya dan ja numfashi yana girgiza kai kafin ya bude ido ya kalleni yana nunani yace damuwa na shine zaman mu dake zainab a yanzu. Ban san a wani matsayi aurena dake yake gun malamai idan zasuyi bayani zainab ina tsoron kada su fada min ke din ai kin haramta a gareni yanzu . Don tsawon dadewan da mukayi a tare ban sauke hakkina a kanki ba da kuma manufan da na aure ki akai a yanzu wani matsayi aurena dake yake ga Allah ? Da sauri na daga na kalleshi kafin na mayar da kaina na dukar a sanyayye wani irin harbawa kitjina keyi lokaci guda don sam wanan tunanen banyi a lokacin ba. Tunanen hakan sam bai taba zo min ba don ban dauki hakan a wani matsayi ba can na daban da zai iya kawo shamaki a tsakanin mu. Tsam na mike daga yadda muke zaunen na dan gusa nisa dashi ina jin faduwan gaban nawa na tsanan ta. A yanzu wani iri nake ji azuciyana da yayi wanan maganan dan jinyasa kawai ya kara saka shakuwa sosai a tsakanin mu wanan lokacin. Shima din da alaman hakan ke damun shi cikin zuciyan shi a lokacin na sameshi yayi shiru dana shigo yana tunane. Karshe mikewa nayi don ba zan iya jure zama a falon ba a lokacin bina yayi da kallo har na fice ya mayar da idanun shi yadda suke yana maijin tausayin mu a zuciyan shi . Ina shiga daki na fada saman gado na sake wani irin kuka lokaci guda kukan da bazan ce ga dalilin yin shi ba a lokacin shin kukan bakin cikine koko na murna nakeyi a lokacin. Abin mamaki nida na dawo Nigeria da zuman rabuwa dashi har abada a zuciya sai gashi yau abin mamaki ina sake hawaye akan ya furta zaman wata kila dashi a yanzu ya haramta. Don wasu dalilai dabai cika ba na sharia tun yin aurena dashi dana zauna a tare dashi a matsayin nazo aure gare shi. Ni kadai a dakin na kasa samun natsuwa a tare dani zuciyana ina jin ba dadi a yanzun tun bayan wanan maganan da mukayi dashi a part din shi din. Haka na wuni sukuku dani da damuwa cike tare dani na rasa sukuni a wanan wunin ba abinda ke min dadi a zuciyana. Bayan na sallame sallah isha,i ne na jawo wayana na tasa a gabana ina kallon lokaci a wayana ina dakon time din da nake tunanen malam ya shiga gidab shi a lokacin karfe tara ke nan na dare. Saida na dan bada lokaci kafin na dauki kiran na danna maaa kira kamar kiran zai katse ya daga da sallama muka fara gaisawa dashi. Yake tambayana jikin jafar din na fada mai yadda yanayin jikin nasa yake a lokacin yayi masa fatan samun sauki a tare dashi har abada. Kafin nace da dashi malam tambaya nake dashi yace na,am ina sauraren ki zainab nan na jefo mashi tambayan sai naji yayi murmushi ya fata min bayani tiryan tiryan yadda zan fahinci yadda maganan yake a addinance. Saida ya gama min bayanin nayi mai godiya mukai sallama na kashe wayan a hankali na kai kwance a wurin ina lumshe idanuna. Dare yayi ban iya lekowa ko falo ba balle nace zan tafi na duba shi don yanayina ya koma kamar na mara lafiya yin yau. Ina kwance a kasa a inda nayi sallah kuma nayi waya da malam ya wayar min da kai kan maganan kamahin turaten jikin shi ne ya ziyatci hanncina a lokacin. Jin hakan duk dana gane shine ya shigo dakin a lokacin amma hakan baisa na daga ba daga yadda nake kwance a kasan dakin saman salayan. Tun da ya shigo idon shi yake a kaina ya karaso yana dan kiran sunana da zainab ko barci kikeyi ne wai ? Na dan daga tare da fadin idona biyo banyi barci ba ya kalleni ya dan sake murmushi a fuskan shi yaja jikin shi zuwa bakin mirrow ya tsaya tare da jingina da jikin mirrow din yana face dina. Sake ambatar sunana yayi yana fadin zainab meke damuwan kine yau ko bakya jin dadin jikin ki ne yau din ? Sai lokacin na dan dago na zauna a hankali ina kallon shi kafin na mayar da kaina na duka ina fadin lafiya ta kalau nake. Kin manta da kina jinya ne baki lekani ba tun dazun ya sake tambayan yana hakan sai dan sake murmushin dole ina dan gyara hijabin dake jikina nace. Ban manta saidai naga majinyacin nawane a yanzu ya samu sauki yasa na nisanta kaina dashi har zuwa lokacin da za a warware matsayin zamana da kai. Shima dai dan murmushin yayi ya gyara tsayi yana fadin au kan wanan maganan yau yasa ban samu kula yadda aka saba min ba kullun ? Ko kema bakya son rabuwan namu ne a yanzu kamar yadda nima nakeji idan hukuncin hakan ya hau kanmu ? Na danyi murmushi tare da girgiza masa kai ina fadin a, a ko daya saidai kawai ina jiwa sabone da juna da mukayi da kai a yanzu. Amma nasan ko mun tafi kai baka da wani kewa ko damuwa ai irin wanda mu zamuji na rabuwa dakai a yanzu. Don dama a shirye ake da a aura maka wace ta dace dakai a rayuwan ka don farin cikin kowan ka koni a yanzu nasa ba sa,an ka nake ba. Ya dan kalloni da mamaki a fuskan shi kafin yace wanan shine tunanen ki a kaina zainab ? Har kina tunanen akwai wata macen data dace dani a yanzu kuma bayan ke ? ke dince zabin da Allah yayi min koda akadara hukuncin rabuwa a yanzu ya hau kaina sai dai in zauna hakana ba tare da aure ba a gareni. Aiba kai zaka aurawa kan ka ba wanan karon aure za aima kamar kowani da dan gata a duniya irin naku na yayan attajirai a kasan nan don duniya tasan da auren ka. Murmushi kawai yayi ya dago tare da fadin idan kin gama fadin abinda ke zuciyar ki yanzu saiki hado min magani nasha na kwanta. Daga haka bai tsaya ba ya fice daga dakin na sauke ajiyan zuciya ina maijin daci a kasan zuciyana kamar ya fashe a lokacin. Ban bita yadda nake ji a zuciyana ba na mike na hada mai maganin nakai masa na samu har ya kwanta saidai ba barci yakeyi ba a lokacin. Ina tsaye har ya mike zaune yasha ya miko min cup din na juya na fita daga dakin bai kara ganina ba sai washe gari dana kai masa maganin yasha ba tare da yai min magana ba har na fita. Yasan dai dalilin hakan a yanzu kan wanan maganance da yayi min da yanzu yake daya sanin furta hakan a garebi. Don ya fahinci zan juya maganan ya zama wani manufa ta daban a gareshi saboda ya fahinci kawai wani aure nake zato a gareshi a yanzu. Ya tambayi kanshi dama ina jin shi a zuciya har hakane ashe don gashi na fara nuna kishin shi da wata mace a duniya a fili. Niko ina komawa dakin hjy na nufa na samu tana zaune tana dan kirga kudin ta tana jin na shigo dakin tayi maza zata boye kudin sai kuma ta fasa tana fadin . Ai kece na zata ai wanine zai shigo dakin bake ba har abin yaso ban dariya na dan dara kadan ina fadin. Hjy duk wanan kudin nakine haka tace ba kaji ba shiyasa bana son a gane su haka kada a saka min baki tana kokarin daure kudin cikin jikinta. Sai kuma ta fasa tana fadin ko na dan baki wani abune ki rika dama dan kudin da bayin Allah dake zuwa gaida nine nake tarawa kinga dana koma sai in taimakawa kawun ku Amadu dana cefane kome kika gani yar nan. Kinsan shi Amadu baidashi kuma ga tarin iyali Allah ya bashi kullun a cikin wahala yake na iyali shiyasa nake dan tausayin shi a cikin su. Kaina girgiza jin takai aya ina fadin hjy bar kudin ki kaiwa kawu ya fini bukatan kudi a yanzu ni nan babu abindana nema na rasa a rayuwa. Tace wanan nake maki fata yar nan ko yaushe gashi har kina fadi da bakinki a yanzu hakan shine shedan kwarai wurun mace ga mijinta. Ni kaina naga alaman hakan a tare dake a yadda kika koma din nan kamar a tabaki jini ya fita din nan hakkuri ke nan idan ka yishi kana da riba sosai a wurin Alllah tun a nan duniya. Ki kara rike mijin ki dakyau yar nan irin mazan ku yanzu tsadane dasu a duniya ba kowane ke samun su ba a rayuwa na dan murmusa na ciki na ciki ina fadi a zuciyana. Kedai tsohuwa ayi sha,ani an cuci na kauye baki san komai ba don ABU CIKIN DUHU SIRINE namiji ko tallakane indai halinsa yana da kyau shine dace. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAR UWA ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA ALLAHUMA AMIN ALLAH YA TAIMAKI MUSULMI A DUK INDA YAKE AMIN YA ALLAH, , , , Yanzu sai kuma zaman namu ya dan sauya don wanan kalman daya furta min din sai nake ganin ai kawai a yanzu na haramta a gare shi . Zuwa wurin shi din bai zama wajibi a gareni ba kada muzo mu aikata wani zunubi a hakan do gashi yanzun da dabi,an son rugumeni a jikin shi ko yaushe . Wanda hakan nakewa tsoro tunda ban san matsayina a zuciyar shi ba kamar yadda malam din yayi min bayani. Don haka a yanzu ya zama dole a gareni na nisanta kaina dashi don ina ganin rashin dacewan hakan a garemu baki daya gujewa afkawa ga fushin ubangiji a kan mu. Gashi a yanzu duk wani laifi nasa dake zuciyana a baya na daina ganin hakan illa zalla tausayin shi dake cikin raina a yanzu. Ba komai nakewa tausayin ba na farko dai ko dadin bakin mazane da yaimin daya nuna shima kamshi baisan lokacin daya fara wanan harkan ba. Haka zalika badon kudi yake irin rayuwan ba kawai dai don giyar kurciyane dake diban mutum a ganuwan kurciyar sa. Malam kuma ya fada min cewa akwai asiri a kanshin tunda kurciya akaso ya lalace saidai da yake a lokacin mahaifin su yana nan bai zauna hakana ba yasa asirin a lokacin baiyi tasiri a kanshi ba. Amma yanzu da uwar suce kawai wace tafi maida hankali ga aiki da neman duniya kawai bata da lokacin tambaya da neman taimako akan zuri,anta a yanzu. Sai uwa uba irin nuna min da yayi shi a yanzu ko ance ba auren mu don irin dadewan da mukayi da taimakon dana bashi baiga wata macen da zai kara zama da ita da sunan aure ba a duniyan nan bayan ni. Wanan hujojin yasa na hauna zauna a kai ina jin tausayin mu a zuciyana don yanzu in ma haushine nafi jin haushin mami fiye dashi don ganin da nake kamar ita duk munanan halaiyar sgi ba dame ta ba ita. Bata dauki hakan abin kyama a gareta ba kodan rayuwan turai da tayi ta saba da ganin hakan har yasa take daukan abinda karamin zunubi a wurinta oho ? Idan nace bata damu ba ba laifi bane duba ga yadda wasu mata a yanzu suka ba aikin su muhinmanci sama ga zama su ba yayan su tarbiya da kansu inganttace . Nasan wasu na da lokacin hakan saidai kosu ba yadda ya dace din bane akeyi a yanzu don ya zama dole a gareki ke uwa kisan a ina kike barin yayan ki idan zaki fita koda kuwa ba wuein aiki bane a yanzu. Cusawa yaro tsoron Allah tun yana karami a zuciya da irin azabobin da Allah ya shimfida ga wanda ke masa sabo. Wanan idan uwa tana hakan yana kawo yaro ya tashi da tsoro a cikin zuciyar shi sabanin wasu uwayen na yanzu da yaro zai ga abin asha a tv yana kwakwayo uwaye su zauna suna dariya ga abinda yaron ke koyo na bata tarbiyan shi. Zama da dan ki walau namiji ko mace kuna hiran abokan sa tanan zaki fahinci dawa danki ke mu,amula a bayan ki. Yawan dafa kai ko a cikin wasa kina sakawa dankin albarka tare da adduan kariya yana sa yaro ya kara imani yaji tsoro da tausayin ki ke uwa azuciyar shi koda bayan kine kalan irin yabon da kike masa zai tuna ya fasa aikata wani abin. Idan kinga da ko yar wata ta lalace bakin ki ya saba da fadin ubangiji Allah ya shirya muna ku kiyi shi a cikin jam,i kada a zauna dake ana gulman dan wani dan sheri jifane dawo kan maishi yakeyi komai dadewa ubangiji ka bamu ikon gyara halayen mu da zurian mu Amin. Naga abinda nakeyi tsab na shirya kamar yadda na saba samun shi a dakinshi in mashi ina kwana idan yana bukatan wani taimako nayi mai a gurguje in fito. Yau ma hakan nayi na nufi dakin sai kamshin oud din jikina ke tashi duk inda nabi don a cikin gida nake nakan shafa abina son raina don gasu nan aje kala da kala a dakin wani ma ban taba amfani dashi ba. Da sallama a bakina na shiga dakin nasa zaune na hangoshi saman gado ya mike kafafun shi ya harde su a wuri daya tare da hade hannayen shi suma ya saka a tsakiyan cinyar shi yana aikin tunane. Kallo daya za kai mai ka gane yana a cikin wani yanayi na damuwa a lokacin duk gaba daya ya fita a hayacin shi a yanzu. Kai ya dago a hankali yana kallon kofan tare da amsa min sallaman ya mayar da idon shi kasa wurin kafafun shi yana kallo. Ina kwana yaya na fada tare da jan in tsaya daga dan abin zaman bakin gado da ake ajewa a yanzu gaban gadajen kasan waje a yanzu. Ba tare da ya amsa min ba Kai ya sake dagowa a hankali ya kalleni da kyau kafin inga ya dan sake murmushi a fuskan shi can kuma ya girgizan kan nasa a hankali. Zainab na gane yanzu guduna kikeyi bakya kaunan zama a kusa dani ko kadan a yanzu ko kema kin koma kyama nane a yanzu abinda bakiyi min ba lokacin da nake cikin aikata sabon da nayi a baya. Ko kuwa har yanzu kina zargina a rankine akan ban daina abubuwan da nayi a baya bane a yanzu ? Idona kura mai a inda nake tsaye ina kallon shi tare da sauraren abinda yake fadi a lokacin har sai daya dakata na dan gyara tsayuwana ina fadin. Ba haka bane yaya ina gudun mu fadawa fushin Allah ne ga hakan tunda kayi wanan furcin a gareni nake tsoro da taka tsantsan a zaman mu yanzu. Me zaisa na gujeka a da can ban guje maka ba balle yanzu da nasan kafi bukatan a zauna dakai zan fara gudun ka kuma ? Laifi Allah kawai ai yaya yanzu tsakanin kane da ubangijin ka kanemi gafara a aurin shi mu kuma na tare dakai mu taya ka. Murmushin da yanzu ya kara zama dabi,an shi ko yanzu shiya sake min din don abindana fada a lokacin gefen shi ya dan bubuga alaman in zauna a wurin. Kallon wurin nayi kamar mai nazari kafin nayi ajiyan zuciya na kai zaune a hankali kamar mai tsoron hakan. Zamana dan shiru dakin yayi kafin yace dani banyi tsamanin za a samu matsala a kan zaman namu ba a yanzu sai dai shi tambaya yana da amfani don yanzu ban kaunan wani abu da zanyu wanda zan sabawa ubangjji na a yanzu. Wanan yasa nake son nayi tambaya akai dan kada muzo mu tabka sabon Allah kema in jefaki a cikin fushin ubangiji. Ni kaina zainab nasan na cuta maki na tauye maki hakkin ki daya rataya a kaina kuma kikayi hakkuri ga hakan bawai don abin hannu yasa kikai hakkurin zama dani di ba a a . A yanzu na kara fahintar kawai dai Allah yayo ki mai tausayine da jin kai na tare da ita tun a zamanin zaman ki gidan mami na fara fahintar haka. Saidai ban gaskantan hakan ba sai zamana dake a yanzu na kara fahintar hakan akanki any way anjima ki shirya zamu fita sha biyu zuwa gidan mami akwai malamin da za a kira jan matsalan namu a can yau. Gabana ne naji ya fadi lokaci guda har yakai ba dan dago da sauri ina kallon shi ido ya dan lumshe tare da kada min kai alaman eh. Nayi karfin halin fadin Allah ya kaimu a sanyayye ko dan ya kawar da zancen ne a lokacin ya jefo min tambaya da maganin nawa ya kare ke nan naga kin daina ban. Ajiyan zuciya na sauke tare da fadin iya adadin da akace ayi amfani dashi ke nan na fada ba tare dana dago kaina ba. Hjy fa ta fito yau kuwa ya sake jefo min tambaya nace yau banji motsin ta a falo ba ta fito ba tukun na dai je mun gaisa da ita dazun tana lafiya. Yunkurawa yayi yana fadin muje dakin don da ita zamu tafi gidan mami din an jima ya fada yana tashi zaune kafin ya mike nabishi da kallo. Kada kiji wani abu zata kai masu ziyarane ita ba abinda zai kaimu zai kaita ba ya fada yana tsaye. Ban bishi dakin hjy dakina na wuce ina tunane kafin na kira layin inna na labarta mata abinda ke faru sama sama. Sai ji hankalin ta ya tashi lokacin kuma nayi dana sanin sanar da inna din duk da ban fito fili na fada mata ga dalili ba amma sai ta rude . Har na dan fara zargin iyayyena a raina ina fadi cikin zuciyana wai ko sun damu da damuwana kuwa ? Sai nake ganin kamar dan abin duniyan da ya jafar ke basu akai akai yasa basu ganin laifin shi a kan komai . Saida abinda ban sani a lokacin shine komai munin aure ga diya babu uwa ko uban da zasu so auren yarsu ya kare sai in hakan mukaddari a wurin Allah dama akai rabuwa a cikin auren . Sai dai kuruciya ya hana in gane hakan a lokacin nake ganin laifin iyayyena kan son na zauna gidan jafar don abin duniya da ya rufe masu ido a lokacin. Kafin sha biyu har na shirya shi kawai nake jiran fitowan shi don bani da kwanciyan hankali a lokacin son har na fara yanke hukuncin abinda zanyi idan na bar gidan nasa don kada rayuwana dana iyayyena ya wahala gaba. Sai gashi ya shigo dakin nawa a cikin shirin shi yasa wasu shadda masu ruwan sky clour dinkin su ya tsaya masa iya gwiwan shi hannun rigan karami shima iya gwiwan hannu ya tsaya mashi sai kamshi ture ke tashi a jikin ranan har yar hula baka mai kyau ya saka a kanshi sai hakan ya kara fito mashi da kyawon shi fili duk da ya rame a lokacin. A falo muka samu hjy zaune tana jiran mu yake fadin lalai hjy kina jin fita yau din nan har kin rigamu fitowa ke nan suka dan taba wasan jika da kaka kafin mu fita daga gidan. A gida nabar sadiya don tace bazata gidan mami ba ita dataji can zamu tafi duk da fadila nasan tasan komai dake faruwa a gidan sabanin sauran yan aikin da basu san abinda ke faruwa ba sai aikin gaban su da sukeyi. Amma ita kan nasan ta san komai dake faruwa a lokacin nuna kawai take bata sani ba nima kuma ban mata wanan maganan ba sam. Ko lokacin da muka fito zamu fita din dagani akwai magana a bakin ta saida babu idon yin maganan ne a gareni balle ta tambayi abinda take son ji din. Mota daya mukai amfani dashi zuwa gidan mami din shine gaba zaune da driver muna baya nida hjy. Dan tafiya muka shigo unguwar su mami din ban dago kaina ba daga yadda nake zaune a bayan mota nayi tagumi sai faman sake saken da nakeyi a cikin raina . Tsayawan motan yasa na dago kai ina kallon get din gidan da maigadi ya bude a lokacin a raina nace kila zuwan karshe kenan da zanyiwa gidan nan a hankali na mayar da idona na rufe har muka karasa shiga cikin gidan. Muryan jalal yasani bude ido don jin yana fadin a, a bros kune tafe ashe gara da ban fita ashe tun dazun ya fada yana karasowa bakin motan. Ganin hjy yasa ya koma kanta yana janta da ba,a har dai muka shiga cikin gidan yana wani ja mata hannu suna tafiya a hankali ina bayan su nima tare da yaya dake waya daga gefena. Gaba dayan su kowa na falon zaune kasancewa ranan ba aiki duk suna gida ga baki dayan su har mami tana falon tare dasu. Sallaman suka amsa na jalal amma sai idon su ya dawo a kaina sun kasa boye kyashin su a zukatan su a kaina. Gaida hjy sukeyi da yayan su sai Na,imace take ce min zainab sannu da zuwa na danyi murmushi ina amsa mata a cikin dan fara, a har take fadin ga wuri kizo ki zauna tana kokarin tashi ta ban wuri. Da sauri nace a,a anty ki barshi in zauna a nan na nuna kasa yace No cikin dakewa ya kalli Rufaida yace ke bata wuri ta zauna. Saida tayi wani iri kafin ta mike a cikin fushi zata bar falon mami tace keko tsiyana dake ke nan wallahi saurin fushi Rufaida. Tace to mami sai kuma tayi shiru ta kasa karasawa don wani irin kallo daya watsa mata yasa tayi shiru. Dole ta dawo ta zauna a gefen mami din tana wani irin shagwaba mami tace kedai zuciyar nan naki zata wahal dake wallahi . Ni kan zaune nakai a bina duk ina kule dasu irun yadda kowan su ke satan kallona tundaga kafa zuwa samana. Na fara gaida mami bayan na zauna ta dan juyo da dan fushin fadan da takewa Rufaida ta amsa min tare da fadin ya gidan ya dawainiya da hjy. Nayi dan murmushi na gyara zama bayan haka ba wace muka gaisa da ita a cikkn in bayan Na,ima da tun shigowan mu tayi min magana. Sai suka wayen ce hakan da hira da hjy na nuna ban masan suna hakan ba gareni ina dakalan wayata daya dauke masu kuma hankali ga ganin ta. Jamal ya shigo shima da alama baisan da zuwan mu ba sai lokacin suka gaisa da dan uwan shi nice na fara gaidashi yake fadin. Zainab kun sha Nageria fa nasan ba don ciwon yaya ba da yanzun kun koma ai jalal ya karba a bayan shi daga inda yake tsaye. Me zaisa ta damu ta koma tunda ba karatu takeyi ba yanzu Aisha da tun shigowan mu batayi magana ba ta fada a yanzu. Ke lokacin da aka dawo kasan nan ai kuka keyi zafi ya isheki zaki koma jalal ya fada budan bakin ta sai cewa tayi aini a lokacin na tashi cikin jin dadi na sai kawai a daukoni a kawoni nan. Amma kuma a yanzu kinsan zainab ta fiki samun dadin da kike fadin kin samuba can don haka ai ba abin mamaki bane don tace zaman Nigeria ya ishe ta a yanzu. Wani tabe baki tayi tana kawar da kai gareshi bata ji dadi amsan daya bata ba daga inda mami take zaune tace koma dai meye a yanzu ba zaka taba hada Aisha da zainab ba ko ku ke nan kullun cikin gwatsale yar uwan ku a gaban kowa. Look ba nazo nan da mata na bane don a riga challangen din ta haka koma meye a yanzu zainab zamana takeyi bana son jin wani zancen bataci a gareta again. Falon yayi shiru kafin hjy tace dasu banda abinku ai ka zama matar mai hali yafi ace ai yar me halice ke a wanan zamanin. Kafin wani yayi wani magaba akai sallama aka shigo ya mamud ne a gaba sai wani mutum mai cikar kamala a bayan shi suka shigo. Nan aka shiga gaidashi sai lokacin na gane shine wanda zai warwale matsalan zaman mu da yaya din da mukazowa jin abinda hukuncin ya tanadar muna yanzu. An dan taba hira kafin su mazan su fita su barmu a falon kamad kada yaya ya fita duk sai naji na tsawala a lokacin cikin su sai dai da yake hjy na wurin ba halin wani yai min wani maganan banza. An dan dauki lokaci kafin yaya mamud ya shigo yana fadin zainab dan zo mijin ki na magana dake a waje. Duk suka bishi da kallo ya fita na dan daga nabi bayan shi nima nasan kallona sukeyi a lokacin ba mamakin hakan a garesu. A can na tsinkaye su zaune saman fararen kujerun roba su hudu na isa wurin da sallama a bakina suka amsa min. Kusan a tare suke nuna min wuri in zauna na danja kafa a hankali nakai zaune a takure nake cikin su din kafin naji mutumin ya fara jan dogon addua tare da godiya ga Allah daya hadamu a wanan wurin. Kafin yace ina gida zaune dazun malam gashi ya nuna ya mamud ya sameni da wani zance wanda ya daure maku kai . Sai dai Alhamdullahi don addinin islama yazo da wayen kaine ga al,umman Annabi ga baki daya Annabin rahama bai bar duniyan nan ba saida ya warware muna irin matsalolin nan idan zun taso gare mu. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI FATAN ANTASHI LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA MARASA LAFIYA ALLAH YA BASU LAFIYA MASU LAFIYAN ALLAH YA KARA MASU LAFIYA AMIN. YAR UWA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA KADA MU SHIGA HAKKIN JUNAN MU. Zowan mami da ta biyo bayan mu ta samu muna zazaune malam na bayani hakan baisa malam din yayi shiru ba a lokacin har saida ya tsaya don kan shi. Malam ya kare bayanin shi a lokacin jikin kowa yayi sanyi a wurin don irin bayanin dayayi a lokacin kan addinin Allah. Ya dago tare da fadin kada in katse ku da bayani haka zan so wanda suke da alhakin zaman mu wanan wuri suyi min bayanin komai a tsare yadda zan fahinci zancen. Sai lokacin mami ta samu bakin magana tana fadin akan meye akai wanan zaman ya mamud ne ya bata amsa da fadin kan matsalan matsayin auren su da kika fara magana ranan muke son malam ya warware muna. Sai ta dan bimu da wani irin lalattacen kallo tana kawar da kanta gefe daya ba tare datayi magana ba a lokacin. Sai ya mamud yayi sauri fadin dama watau malam kamar yadda na fada ma dan matsalane aka samu tun farkon auren har yakai an kwashi tsawon shekarun nan, ana zaune ba wani abinda ya taba shiga tsakanin su shiyasa muke son a warware muna matsayin wanan auren a yanzu. Saboda mahaifiyan mu ta fara furta wanan kalamin wai an dade an dauki lokaci a yanzu kan ba sauran aure a tsakanin su. Da sauri mami ta dan dago kai ta kalli ya mamud din tana fadin au don hakan dana furta kuka kira malam a kanshi to ai gaskiya na fada dan aure ko watani masu tsawo ya diba ba saduwa a tsakani ai akwai bincike a kai. Malam din cikin murmushi ya karkada kai ba tare dayayi magana ba sai murmushin da yakeyi a lokacin. Ya jafar yace dakata mamud jin haka kowa yayi shiru a wurin a lokacin ina faman tunanen zancen ya mamud din da yace mami ne tazo da wanan zancen ke nan haka na nufin mami dai har yanzu tana son in bar mata danta kota halin kaka ke nan yasa take wasu tsire tsire zance a yanzu din. Sai gashi kuma yanzun din ma ta kara maimaita hakan a gaban kowa ba tare da jin komai ba a zuciyan ta. Wani dan iska ya furzo mai cike da sautin zafi da takaici irin yadda yake jin kanshi din a lokacin nan dai ya bude bakin shi da yai mashi nauyi a lokacin kafin ya fara fadin . Watau malam bayanin da zan ma ba akan wanan zaman bane kawai kamar yadda dan uwana daya gaiyace ka yayi maka bayani a yanzu. Duk kallon shi mukayi kafin yaci gaba da fadin malam ni din dai na kasance mai aikata sabo a baya, da sauri malam yace wa,iyazu billah. Yace kwarai malam a kuma cikin irin wanan halin na auri matata zainab gata nan zaune a gaban kowa . wanda da farko nayi wanan auren ne don in fake a gareta da sunan aure a kaina ga idon mutane don kowa ya san ina da aure kada mutane su kawo wani zargi a gareni. Duk kallon shi sukeyi har ni din da yanzu na kara gaskanta manufarshi a kaina a baya daya aureni din sai naji wani irin bakin ciki ya kara tokare min makoshina lokaci guda kafin sauti muryan shi ya dawo dani a daidai lokacin da yaci gaba da fadin. Watau malam bayan auren namu da ita hakan baisa na bar aikata fasadi a doron kasa ba wai don ina da mata sai na dauki abin kamar yadda na tsara zaizo min a baya yadda nake so A gaskiya na auri zainab ne akan zan samu rufin asirina a wurinta don tana yar tallakawa zata zauna dani ko don talaucin ta dana iyayyenta alokacin a yadda nake hange. Saidai kuma nima ba wai haka kawai wanan tunanen yazo min ba sai bayan nayi nazarinta da irin hakkurin ta naga ya kamata in taimaka mata ta wanan hanyan kaga kenan zamu taimaki juna a takaice dani da ita amma ba cikin ta sanda hakan ba saboda tana da karancin shekaru sosai a lokacin. A lokacin mami bata gane hakan ba don tana ganin na bijirewa zabin tane don tana ganin zainab din bata cancanceni ba ga aure. Malam ya dago kai ya dan kalleni a hankali ya mayar da kanshi kasa yaci gaba da fadin. Sai dai kakata da take jin ina yawan fadin zainab ce ta dace da rayuwana a lokacin duk da bata san mugun halina na boye ba da nake aikatawa a lokacin. Amma hjyn ta bani goyon baya dari bisa dari ga wanan auren da nake son yi da zainab din. Inda a karshe da mami din taki jin magana da shawaran mahaifiyan nata muka yanke shawara da hjyn da yayana mamud gashi a zaune kan naje na nemi auren zainab din a boye tunda mahaifiyarmu ta kafe kan sai zabin ta a lokacin. Wanda ni kuma nake hangen zabin nata a gareni kamar wani hanyar tonon asirinane a wurin jama, a wanan auren na mami, don zai iya jawo min ga duniya don nasan koni waye. Saidai ashe wanan zaben da nake ganin nayishi ne kawai don bukatana, shine haske a garemu baki daya . Don shigowan zainab a cikin rayuwana a sannu a hankali ta fara kawo min sauyi na canza min lissafina da nakeyi da farko a kanta. Kasancewan zainab din yarinya mai wayau da ilimin addini yasa abubuwa suka fara cabe min a rayuwa . A lokacin haka nake gani don yawan nasihanta a gareni da saka min ido kawai da tayi kan duk wani abinda nakeyi ba tare da takura min ba . Sai hakan yasa na fara kunyar kaina na da jin nauyin ta har ya kai na rage wasu abubuwan da nakeyi a fili saboda kaucewa idonta din. Tunda nasan tasani amma bata nuna min tauye mata hakkinta da nakeyi yana damunta ko abin yana bata mata rai sai har idan ta kamani da idon tane mukan kwashi fitina sosai da ita. Nasan kuma hakan da take min yana a cikin rashi gatan da take ganin bata dashi ko kuma fin karfi iyayyene dake aiki a kanta. Don ga nawa tunane sai nakan yawaita yiwa iyayyenta da yan uwanta alheri don na kawar da zargi ko kaskanci a idanu su. Nasha shawaran da zuciyana akan in rabu da ita kamar yadda mahaifiyan mu keso hakan, amma sai in kasa hakan don hankalin yarinyar da nake gani kuma gashi duk da tasan dabi,u na marasa kyau baisa ta wullakantani ba. Ban kara tabbatar da hakan ba saida na sakasu karatu ita kanwarta da suke tare idon ta ya kare budewa a can chaina din sosai amma hakan baisa zainab ta raini ba ko naji watarana ta fadawa wani ga halaiyana marasa kyau. Mun sha fama da zainab akan rayuwan maza da maza da nakeyi wanda take iya kokarin ta a kai taga na daina wanan akidar . Amma sai hakan ya gagareta da farko na dauka tanayine don na kasa, kasancewa da ita a matsayun muna ma,aurata . Sai daga baya na gane abin ba haka yake ba har kasan zuciyar ta tanayine kawai don ta fitar dani cikin wanan rayuwan na fasadi danake aikatawa. Yan kungiyan mu sun sha ban shawara in kasheta in huta idan zata kawo min matsala a rayuwana, ko su kansu suyi yunkurin hakan in hana su. Naji mami tace ikon Allah wai a kashe mutum kamar dan kiyashi kai haba jafar wanan wani irin rayuwa ka jefa kanka a ciki hakane ? Lokacin na dago kai na kalle shi da idona da yake tab da hawaye bakin ciki tare da tausayin kaina da nakeji akan abubuwan da yake fadi din da bakin sa. Malam ne ya katse shi da fadin gaskiya malam jafar ka aikata sabo mai girma a rayuwa. Ya aikata kan sai dai addua a yanzu tunda Allah ya taimakeshi ya daina a yanzu ga baki daya. Yanzun malam saika fada muna matsayin da auren su yake ciki a yanzu don kowa yasan zaman shi a yanzu din mami ce duk take wanan maganan tana kallon malam din. Taci gaba da fadin don a nawa fahintar ya tsaya yana gyaran wani zance haka mai tsawo da bashi ya taramu a nan ba tun dazun. Why mami why zakice kada na fada ya zama dole in fada a gaban kowa don in kara samun addua da taimakon da Allah zai gafarta min zunubai na jafar yace. Kafada din ba,a hana ba kana kawo muna wani zancen zainab can tun dazun mami ta fada a hasale. Malam dake kallon su yace Na,am watau ainihi danki yana da gaskiya haka ake son mai tuba da gaske ya kasance kada yaji kunyar fadan girman zunubin sa komai girman sa don tuba. Haka zalika ita wanan yarinyar ya nuna inda nake yace tayi matukar kokarin azo a yabe ta kuma a sota ko dan halinta. Don a wanan zamanin ba ko wace mace bace zaki samu da aikata hakan ta iya boye sirin mijinta a cikin ta daga ita sai shi sai Allah kadai su san da sabon da yake aikatawa haka. Jafar ya tare malam da fadin wallahi malam abinda zai baka mamaki shine ita din zainab ta shiga ta fita a kasan chaina ta samo min maganin da a yau zan iya komawa kamar kowa. Na,am malam yace tare da kara masha Allah yarinya kinyi kokari da kika samu wanan yabon a bakin mijin ki haka. Wallahi malam ba gyarata nakeyi ba ko don wani ya sota a yau ina fadin gaskiyan abinda tayimin ne a rayuwa nan dai ya kora masu labarin komai har da na kakana malam da yake bashi. Humm,umm ita zainab din duk ta iya hakan ashe ba karya ake fada ba da ake fadin yan kauye komai karantan su ka barsu inda ka gansu. Shige shige da biye biyen malam ya kare a gidin su yau na kara gaskanta wanan maganan . Kwarai mami in dai wanan din shine shige shige zainab ta shiga inda yafi nan din data shiga ya mamud ya fada. Don kuwa mu zainab ta gama muna komai na rayuwa tunda ta kwato muna dan uwan mu cikin bala,i. Rufa min baki kada in saba maka a wurin nan yanzu mami ta fada dama nasan shirin ku akan hakan yasa na biyo bayan ku inji me kuke kullawa. To bari kuji koda malam yace akwai zama a tsakanin su aure sai na karawa jafar shi tunda nayi niyar hakan kuma zan nuna masa ni na haifeshi ba wani ba. Enough mami enough don Allah in anyi magana kice aure zaki kara min aure zaki kara min ga abinda ya dace kimin bakiyi ba lokacin da nike bukatan taimako. Yanzu da zainab din tayi shine kuma abin laifi ai Allah yace tashin in taimakeka baki tashi din tsaye ba a kaina ita ta tashi har yanzu tana a mai laifi a wurin ki mami ? Me wanan yarinyar tayi maki haka mami kika tsaneta ne lokaci daya haka halarcin zainab a gareki ba kadan bane har idan ke kika haifenin da kike fadi. Yarinyar da zan yi amai ta kwashe in fitar da kazanta da namiji dan uwana ta zauna tana gani iyaka taci kuka ta gaji ta share hawayen ta bata taba fadawa wani wanan maganan ba har yau itace kike kokarin ganin kin bakantawa mami ? Wallahi dani kadaine danki mami da sai ince bake kika haifeni ba kila don son baki kawai na kina nuna min don yadda zainab zata zaunar dani tana min wa,azi mami kin taba min hakan ? A matsayina na mai,aikata babban laifi irin wanan don haka mami ki gafarceni akan zainab a yanzu zan iya batawa da kowa a duniyan nan. Zainab tayi min komai a rayuwa ta yadda ba zan iya kimanta darajan ta a zuciyana bayan naki daga ke sai zainab ne mata mafi daraja a idona har abada. Yau zainab ta tunar dani nauyi da kunyar ubangijina da ke kaina wanda na manta dasu saboda rudin duniya da nake bi a baya. Aiko mami zainab tayi min komai a rayuwana, kukan da nasake ne ina kaiwa kasa ya dakatar da dan rigiman daya kaure a tsakanin su lokaci daya a wurin. Malam ka taimakeni kai mun rai ka ceci rayuwana ka rabani da ahalin mami ga baki daya a yanzu nima na gane mami ba zata taba kauna ta ba a duniyan nan. Duk abinda yaya ya fada anyi shi har ga Allah dama wanda bai sani bai fada din ba duk anyi su a baya. Kuma bayi don kowa ba sai don Allah da halarcin mami a gareni da kuma shi kanshi ya jafar din ya taimakeni da abinda ba zai taba barina a rayuwa na bashine illimi. Mami ta sanadiyar ta nabar kauye rayuwa na ya inganta a sanadiyar ta haka tayi min riko na tsakani da Allah da ba zan taba mantawa da hakan ba don ita uwace hakkun har gobe a gareni. Aurena da ya jafar shine kadai kiyayar mu da mami a fahintana don haka malam ka yake duk wani alaka na aure dake tsakanina da ya jafar a yau don Allah. Na karasa cikin wani irin kuka ma idaga hankalin mai saurarena a lokacin duk sukai shiru suna saurarena tare da zuba min ido gaba dayan su. For god sake mami dame wanan abin yai kama haka yarinyar nan dai kema kin sani ta dalili ki ta san bros ta kuma fadi don ki take masa komai. Koma bata fada ba kowa ya sani don zainab yarinyace mai hankali da natsuwa ke kanki kinsha fadin haka ko a bayan ta yan aiki nawa kika canza zuwa yanzu jamal ne mai wanan maganan rai bace. A ranan nasan tarbiyan yahudawa mami tayiwa diyan ta ashe tunda kowa na iya fadin magana kai tsaye a gareta ba tare da ta damu da hakan ba. Don da ace hakan yai mata zafi da wata uwarce a take zata yankewa kowan su kauna a wurin yau naga amsan abinda ya dade yana min yawo a zuciyana . Kan yadda mami bata damu tabi umurnin hjy ba idan ta tsawta mata kan wani abu da takeyi wanda bai dace ba din. Salamu Alaikum malam ya fada cikin muryan uztazai wanan ya saka masu natsuwa a wurin malam din yaci gaba da fadin . Wa,izu billah wanan abin bai kawo kallo ba a tsakanin ku watau anihin dai wanan zancen naku yasani nazarin abubuwa da dama a cikin yanayin zancen nan a yanzu. Da farko na fahinci akwai wani abu da ke a kasa tsakanin ku a gidan nan tun farko sai abu na biyu shine. Watau ainihi kan zancen wanan boyar Allah watau hjy zainab gata a zaune watau anihi hajiya iyami ina son ki san wani abu. Shi lamarin ubangiji mai sauki ne idan bawa ya daukeshi da sauki watau wanan boyar Allah ita din haskene a gareku baki daya a gidan nan. Haske irin wanda ake kira da Nurul dar sai ya kasance a cikin wanan zancen gaba daya kunyi amfani da baiwan yarinyar nan kun kuma amfana da ita ko. Yanzu duk ba wanan ba don lokacin sallah ya gabato sai mu gagauta yin bayani kan abinda ya kawo mu nan a yanzu. Na farko dai bayan nasiha da zan ma kai malam jafar akan tsoron Allah a yanzu dai Alhamdullahi sai ka ya waita istgifar wanan yafiya yana tsakanin Allah da bawan shi. Ba wani dan Adam da ya isa ya furta wani kalami akan hakan face mu godewa Allah ga baki daya muka yawaita istigir akan mu da dukkan musulmi baki daya . Ke kuma hjy zainab ki godewa Allah da har kika samu yabo haka gun abokan zaman ki ga baki daya ko wanan ya ishe ki alfahari a duniya. Zancen akwai aure ko babu aure a tsakanin auren nan yanzu zabi ya rage gareka kai mai auren a hannun ka. Idan kaga zaka bar matan ka auren ku na nan daram har abada sai dai idan kaika janye igiyan auren ta a kanka yanzu. Aure dai an riga da an daura a tsakanin a bisa tsarin musulunci ba tare da wani manufa ba ga madaura auren ku din a lokacin kaga ke nan aure ya dauro a tsakanin ku ke nan. Wanan zancen da ake hasashe ba addini ya fadi hakan ba tsarine na wasu mutane da suke fadab hakan. Amma dai da ace har yanzu baka tuba ka koma ga Allah, ka daina wanan abubuwan bane to sharia ta yarda da a raba auren naku don taje gaba itama ta samu daidai da ita kada ka cuta mata a nan Sai dai ina kira a gareku gaba dayan ku kiyayye kyautatawa iyayyen ko da a wajen tausasa harshe ga mahaifa musanman uwa . Duk wanda yaji hakan yasan dalilin fadan hakan da malam din yayi garesu ya kara da fadin sai na karshe mu kyautatawa wanda ya kyautata muna koda na rana daya ne shima zai bukaci kyautatawan ka watarana a kan shi. Don haka kada mu zamo masu manta alheri komai kankantanshi don kada Allah ya jarbce mu ta hanyar da bamuyi tsammani ba a rayuwa. Da wanan nake son inyi sallama dakuba taikace Allah ya gafarta muna kurakuran mu da wanda muka sani da wanda bamu sani ba Allahuma amin. Yayi muna sallama bayan anyi addua an shafa ya mike zai tafi ya jafar ya saka hannu a cikin aljihun shi ya ciro kudi masu yawa yace a bashi. Da sauri malam din yace sam ba don kudi ko wani abin sadakan ku nazo ba son kunfi karfin hakan a gareni. Zanso na gana daku ku ukun nan kafin ka bar kasan nan idan kun samu lokacin haka yayi masu sallama ya tafi. To ai shike nan bukatan kowan ku yanzu ya biya shiyasa kuka dauko min malam khalid don shi din ya inma bakin sa yazo yai muna wa,azi. Wa,azi kuma mami akan me zaizo yayi maki wa,azi mu mun kirashi ne yazo ya warware wanan zancen kowa yasan matsayin shi. Please is enough a bar zancen komai a yanzu ke zainab tashi muje gida daga nan ya fada yana mikewa. Kamar banji me yake fada ba a lokacin kaina na kasa sade ban dago daga yadda nake ba tun dazun din. ZAINAB IDRIS MAKAWA. ASSALAMU ALAIKUM YA YAN UWA MUSULMAI BARKAN DA GANIN WANAN RANAN NA ALHAMIS UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN. KADA KI MANTA TASHIN DARE A WANAN RANAN MAI ALBARKA KI YAWAITA ISTIGIFAR GA ALLAH KI NEMAWA KANKI GAFARA ALLAH YA BAMU IKON TASHI YA KUMA KARBA MUNA IBADUN MU AMIN. TUNI LITTAFIN DAI NA KUDINE BA A YARDA WATA TA KANTASHI BA IDAN BATA BIYA BA. Yana tsaye a kaina yana kallona ba tare daya sake magana ba duk sun zuba min ido suna kallo na don ganin ban motsa daga yadda nake ba sai hawayen da nakeyi. Sai ya mamud ne ya mike ya tako har inda nake tsugune ina sake hawayen bakin cikin dake cina abu goma da goma sun taru min a kaina lokaci guda. Zainab kiyi hakkuri ki tashi ku tafi ya fada a gefena cikin nuna damuwa a gareni jin haka na dago kai da idona daya yayi ja don kukan da nasha ina fadi da kyar. Tare da girgiza kaina gareshi yaya ba zan koma gidan ya jafar ba kai masa magana yayiwa mahaifiyar shi biyayya kan abinda take so dashi. Allah ya gani da zuciya daya nake zaune dashi tankar yar uwa ta jini don duk abinda mami take nuna min banta jin kinta a raina ba haka diyan data haifa ina jinku tankar yayyuna ne na jini don yadda kuka rikeni tun farko. Bada case din ya jafar daya hadani da mami ba wani sabani daya taba shiga tsakanina da mami duk zamana da ita. Ban yarda na auri ya jafar dan son raina ba sai bisa tursasawan hjy gwaggo dashi kanshi ya jafar din da sukai min barazana a lokacin. A daidai nan na dago kaina na dan kalleshi ido da ido tare da fadin yaya a wanan maganan meye laifina a cikin hakan ina duk saboda darajan mami na aikata hakan. Yanzun kuma kaji a gaban kowa shima ya fadi bai aureni don yana sona ko wani abu nawa ba sai dan bukatan kanshi da yake ganin zai fiddashi ga idon jama, a. Alhamdullahi kuma dukkan su bukatan su ya biya a kaina don Allah kusa ya sake don wanan abin ya kare daga yau din nan yaya ? Na fada ina kara sake wani itin kuka mai tsuma zuciya lokaci guda daga inda mami take zaune ta zuba min ido take fadin kenan da sanin hjy dama duk hakan ya faru ashe ? Shiko ya jamal sai cewa yakeyi ai gashi idan za ai magana a fadi gaskiya mami ki hana duk wanan abin da yarinyar nan takeyi ni nasan taimakon ki takeyi wallahi. Kune dai da baku yarda ba da farko kuke ganin don bukatan kanta take hakan yanzu sai ku sama mata maslaha itama taje ta huta. Jafar daya juya ya bamu baya yana cika yana batsewa ya juyo a hasale yana fadin wallahi baku isa ba babu mai rabani da matana wallahi . Sai ko idan bana raye wanan kan na yarda da hakan naji mun yaudare ki din da farko daga ke har hjy data shawo min kanki a lokacin baku san komai ba . Yanzu da nayi comfessing ina neman gafaran Allah da naku duk wanan din bai maki ba zai ba ya fada yana tsureni da idanun shi da sukai wani ja dasu. Fine naji ya fada cikin wani irin zabura yana fadin sai ki fadi yanzu me kike son nayi maki don ki hakkura mu tafi ? Na duka na baki hakkuri ko kudi kike sin na zuba maki fadi iya yawan kudin da kike koda duka dukiyanane zan iya ko mami kike son ta baki hakkuri gata zaune. Ki fada duk a yanzu ko wanine daga ciki za ai maki a yanzun nan ba sai an jima ba. Kai kai kai Allah ya rabamu da rashin tarbiya wallahi da tashi a cikin daulan da ba kwabo wadattace ga mutum. Duk wanan abinda ya fada a yanzu shi a nasa zaton sune abinda zai kwantar min da hankali ko wani abu can. A hankali na girgiza kai tare da fadin ko daya yaya jafar bana rayun ko daya daga cikin abinda ka lissafo min din a yanzu. Na farko kana ganin dukawan ka a gareni ka ban hakkuri zai iya dawo min da farin cikin bakin cikin da nasha a wurin ka da mami da yan uwanka dake kina. Ko kuma kana ganin kana da kudin da zai iya sayen mutucin na da imani na a hakan. Sai mami gata a zaune mami uwace mafi soyuwa a gareni mafi girma da daukaka a idona ita da innata data kawoni duniya don bayan inna sai mami tayi imin komai a rayuwana ba zan taba manta harcin su ba a gareni. You see mami kinji, kinji yarinya karama tasan halarci irin wanan, ta yaya ku manya zaku kasa gane hakan ? Har ma wani dadi zainab ta samu a lokacin da take ta fadan kin mata halarci bayan tauyen ta da akeyi ana mai da ita kamar wata boya a ciki gidan nan kowa ya tashi ko ruwane zainab dai zainab dai ku din nan yau kunji inda akewa mutum alheri ya rama ta wani hanya. Don ku din nan ba irin wullakancin da bakuyiwa zainab a gidan nan ba yau gashi tafi ku da komai a duniya. Don ko kafanta ba wanda ya taka a cikin ku kaf din ku ba wanda yayi lilmin zainab a yanzu ya fada yana nuna su da yatsan hannun shi. Ku rage wullakanta dan Adam don Allah don watarana baku san me Allah zai mai dashi ba jamal ya fada a hasale yana mikewa tsaye. Ya girgiza kai ya saka hanayen shi cikin aljihun shi yana kokarin barin wurin. Sautin muryan mami ne dake kuka yaji ya hanashi tafiya a lokacin ya juyo da mamaki yana kallon mami din da kuka takeyi wiwi a lokacin. Ya mamud da sauri ya karasa wurinta yana fadin haba mami me yai zafi haka wanan ai saiki tada hankalin mutanen gida da wanan kukan naki. Zuwa lokacin ko har sun karaso don Rufaida datake labe saman bene tana sauraron abinda ke wakana duk da bata ji sosai a lokacin daga inda take labe. Tadai labe din tana kallo don tasan wani abu ke faruwa a lokacin a yadda taganmu zazaune yasa data hango mami na kuka kuma kaman ana fada ta fito da sauri tana fadin kuzo akwai abindake faruwa a waje da su mami don Allah. Hakan yasa suka fito a cikin tashin hankali zuwa waje sai dai suna tunkaro wurin suka tsaya duk abinda ake fada a kunnuwan su ne lokaci. Sai suka fara dan kalon juna a tsakanin su kafin hjy ta karaso tana fadin wai meke faruwa a wurin nan ne haka tun dazun ? Sai kuma dan yanayin mami ya dauke mata hankali ta kurawa yar nata ido tana binta da kallon a cikin mamaki. Iyami kin bata wayau ki yau har abin naki yakai ki zaunar da yarinyar nan haka a waje kina ci mata mutunci haka. Ki duba nan duk yayan kine a nan aure kuma zasuyi suje gidan wasu shin kinsan irin *abifaru sakamakon hakan zai zo masu ? Shifa komai ka aikata a duniyan nan kai da kanka zaka girbi abinka da hannun ka shin iyami baki gudun yaran nan su tarar da uwar mijin data dara irin gasawa yar nan da kikeyi ? Kowa yai shiru a wurin ana sauraron abinda hjy din take fadi sai rufaida ce ta bude baki tace wa tsohuwar kinyi kuskure hjy don mu kan ba zamuyi aure irin wanan na cusa kai haka ba gaskiya. Ki min shiru Rufaida mami ta fada wa yar nata cikin tsawa a hasale taci gaba da fadin ana nuna maku hanya har kina ci gaba da magana haka. Fada min yanzu meye laifin yarinyar nan zainab a nan don kawai ta auri yayan ku ko dan ta zauna a cikin mu har abada. Yanzu na gaji da wanan halin da kukewa yarinyar nan zainab ku barta ta zauna lafiya da mijin ta don ko ta muna komai a rayuwa don ta zauna da dan uwan ku tsakani da Allah ba don wani abuba. Yau na gaskanta hakan abinda kuke yawan fada min tayi ko kun gani sam abin ba haka yake ba ashe . Don yanzu a wirin nan na gaskanta hakan na gane gaskiya abin ba hakana bane bawai ta asirce shi bane ko wani abu. Tayi ne don ta farauta min rai wanda nasan da wuya a nan a samu wace zata iya yin abinda zainab din tayi min. Kowa wurin sai kallon mami yakeyi don jin furcin ta a kaina taci gaba da fadin ina son ku sani daga yau ba raini ko wullakanci ga yar uwanku kuma matar yayan ku gata a zaune gaban ku zainab. Ikon Allah hjy da takai zaune ta fada har lokacin tanawa mami din kallon mamaki kafin mami din tace hjy don Allah ki tafi gida dasu in an jima zanzo gidan da mamud da jamal mu sameku a can. Mamakine ko al,ajabi ya cika min zuciya a lokacin don saukowan mami haka da sauri sai abin ya fara daure min kai na. Wanda nasan ba ni kadai nashi yin wanan tunanen ba a wanan lokacin kusan duk wanda ke wurin yana mamakin hakan. Hjy ta kalli jafar tana fadin mu tafi tashi zainab mu koma gida tun lokacin sallah bai shige muna a hanya ba. Ba yadda na iya haka na dago kafata da kyat na fara ja don barin wurin ba tare dana iya yiwa kowa magana ba na fara tafiya. Sai Anty Na,imace kewa dani zainab Allah bamu alheri sai munzo maku yawon weekend tunda naji ance kun kusa tafiya. Dan murmushin yake na gefen fuska na sake ba tare dana bata amsa ba na wuce wirin motan mu kai tsaye. Driver na ganin hakan ya mike ya taso da sauri ya nufo inda nake ina kokarin bude motar ya bude min na shiga na zauna ina jiran isowan su dan shi ya tsaya yana magana da su ya mamud. Ita kuma hjy da mami suke tafe a hankali zuwa wurin motan da alaman dai duk maga sukeyi daya shafemu. Yayin da yan matan suke tsaye suna kallon mamaki na sauyawan mami lokaci guda haka bayan zuwan mu gidan ne koma meye ya faru. Bayan sun karaso bakin motan mami ta dan leko tana fadin zainab kada ki nuna masa komai don Allah sai nazo anjima din insha Allah. Da kyat na iya budan bakina ina fadin to mami nagode cikin yanayin damuwa don shi kawai zan iya fada a lokacin. Yana shigowa ya buga kofan motan da karfi saida na kadu mami take fadin kabi sannu fa kada ka tayarwa kan ka da wani ciwo kuma. Ok ok don't mind ya fada tare da girgiza kanshi yana amsawa ba tare daya kallo inda take tsaye ba. Hjy na fadin yama ja din aishi zai wahala shi daya sai kuma matar shi da zai wahalal a banza daga dan maganan fatan baki zai bata rai haka kamar soja a filin daga. Mami ta daga, daga bakin motan tana fadin Allah ya tsare hjy ta amsa da amin sai kinzo. Shiru cikin motar ba wanda ke magana sai driver ke faman sharara gudu don umurnin da ya bashi na yai sauri. Allah ya gyara mun isa lafiya ba wanda yai magana haka muka fita wanan karon bai tsaya jiran hjy ba su jera kamar yadda mukafita a gidan. Sai nice ba tsaya muka jera tana fadin tana tafiya ikon Allah yar nan nace ko wanan uztazun daya zo ya sauko da uwar taku da sauki haka a kan ku ? Ai bai isa ya canza ta ba hjy sai Allah din dai da kika fada yanzu tace ai kuwa yar nan . Tana dafa step din da zai hau da ita shiga cikin gidan take fadin a, to ai tace zata shigo anjima ai Allah ya kaimu, muji dame kuma zata zo din. Har muka shiga gidan tana magana akan mami din muka shiga ciki ana muna sannu da dawowa sai ita ke amsawa a lokacin.. Har dakin ta na kaita kafi na juya na nufi nawa part din a gajiya ga kasala ga tunane dake cina da yunwa a lokacin. Wanka ba shiga a gurguje don na makara da ga sallah a lokacin na fito na tayar da sallah din bayan na idar ne na zauna na dan gyara jikina na saka wani simple riga a jikina da zan dan sha isaka a lokacin. Na koma na haye gado don ina bukatan hutu da kadaicewa ni kadai a dakin lokacin don yin nazarin abun da nake son ganowa kan nadaman da mami ta nuna tayi din a yanzu. Kofa aka turo a lokacin ban dade da kwanciya ba na dan juyo a hankali ina kallon mai shigowa dakin anty Fadila ce ta shigo tana fadin . Kun dawo a gajiye abinci na dinning tun dazun an gama sai dai nakaiwa hjy nata yanzun kafin in zo nan. Nakine dana oga a dinning din yanzu sannuku da aiki nace a hankali sai dai anjima zan fito in danci tace shi oga fa ko za a kai masa nasa ne part din shi ? No ki barshi idan yana so zaiyi maga ai na fada ina gyara mike kafana tare da bayana dana jingina da gado. Tace da a debo maki ko ferfesun ki sha zaifi zama ciki ba komai na girgiza kai kafin ta karasa fadan abinda zata fadi din. Sai kuma ta kara fadin ina ganin fa zuwa friday aikina zai kare daku zan bar gidan nan ke nan a ranan ta fada a cikkn murmushi tana kallona. Da sauri na juyo gareta ina fadin wanan satin ke nan tace eh insha Allah ranan ne zan kamala komai in tafi a yadda aka tsara min. Haba dai gaskiya da son samu ne zaifi kyau ki hakkuri har mu tafi idan mun tafi ai kinga shike nan saiki tafi a binki ko ? Gaskiya hakan da wuya don iya month din da aka ban ke nan kuma na gama hada duk wani bayani da suke so a yanzu . Gashi ban taba zywa aiki wani gida har wani yasan abinda ya kawoni a gidab sai wanab gidan naku abin kamar sihiri wallahi yadda har kuka gane me ya kawoni gidanku da sauri haka ? Dan murmushi na sake ina kawar da kai tare da tunanen maganan data fada sai na dauka tana sk jin wani abune daga bakina duk da tasan ba zata taba samun amsanta a wurina ba amma ta gwada sa,an ta ta gani ko zataji din. Kwanciya na gyara ina fadin tare da hamma kin san shi din mutum ne mai natsuwa da lura da komai. Tace wanan kan na sani ai shiya ja min wanan dadewan tare daku don na kasa fahintar komai a kanshi duk zama tare daku din . Ganin da tayi alaman ina son hutawa ta mike tana fadin barin baki wuri ki huta naga kamar a gajiye dai kike yanzu baki jin hira nacs wallahi na gaji gaskiya ta mike ta fita daga dakin tare da rufo min kofana. Fitan ta daga dakin tun ina tunane har barci ya daukeni ban sani ba ban falka ba sai kusan karfe biyar na tashi ina salati. Ban samu fitowa falon ba sai dana kamala komai a lokacin na samu fito har shidda ya wuce koda na fito. Jin hayaniyan tunda na fito dakin hakan ya sanar dani muna da baki a gidan ga yadda naji ana dararaku na dauka wasu bakina sai ina karasowa naga ba wasu baki bane su mami ne da hjy a falon ake wanan dariyan haka. Kunyan kaina naji a yadda na fito falon tun kan ya watso min irin kallon da yake min na warning na riga na tsargu da hakan. Hakana na daure na karaso ina gaida su da zuwa ba kunya ko wani dar a idon mami take fadin diyata mun zo mun samu kina barci ai nace kada su tasheki a barki ki huta. Lah mami ai da an tasheni din nayi sallah na fada ina dan dariyan da bakai ciki ba na kai kasa ina gaida ita kamar yadda na saba take fadi cikkn dakewa ke zo nan bana son in kara ganin kina jin kunya na haka kikaga yan uwan ki suna min. Na gaisa dasu yaya duk ina zaune suke dan hira kafin mami din ta juyo gareni tana fadin tun dazun fada mukewa mijin ki . Kina daki don Allah zainab ina son ku kawar da komai daya faru a baya a zukatan ku a zauna lafiya . Wani zance a yanzu duk a bar tuno da abinda ya riga ya wuce duk da nasan hakan yana da wuya amma dai a daure. Hjy da bata san zancen ba ta dora da fadin sabani dai suka samu har ya kaisu gareki yau din ai amma kuma zuwan nasu gaban ki kuma yayi rana sosai. Tunda hakan yasa har tsakanin ke dasu a yanzu kun fahinci juna don ni abunda yafi damuna shine irin yadda kika sake wa yan nan kattan yan matan naki sukewa yarinyar nan iya shege ko a gaban kowa. Don kawai suna takaman ta taba zama a karkashi su a baya wanan abin yana cimun rai sosao wallahi Amma yau yadda kikai masu din nan yasa na fara fita kwakwanton da nakeyi na uwayen yaran nan . Don sai nake zargin idan kuna wani abu dasu kamar ba kai sake suka barki ba Allah. Budan bakin mami sai cewa tayi nima hjy watarana nakan yi zargin hakan a kan su wallahi don kinga Rufaida halin uwarta sak ta dauko ga hali. Bata kaunan taga wani yazo ya rabeni a gidanan ko kadan sai naci mata mutunci wani lokaci takan shiga hankalin ta. Laifi kine iyami yaushe za a zauna da uwayen mata nan dasu wai kuma budurwai duk ki sa su fito da miji ki aurar da yan banza. Mami tace ai mazan sunki fitowane har yanzu ba mashinshini suna nan min zube cikin gida sai karyan banza wallahi. Basu rasa mazajen aure ba kawai dai basa son masu son su dinne suna ganin sun fi karfi su auri kalan mazan ne ya mamud din ya fada. Su koma gida mana idan hakane karatune dai sun samu yanzu ba sai ko wacen su ta koma gidan su ba inji jamal. Kai a bar cen nan please ayi wanda ya kawo ku don Allah 3ni wa yan nan yan iskan yara ina ga nine zan koresu ranan da wata ta karawa zainab iskanci a gidan nan.. Bama zasu ba a yazu indai ba yaran banza suke ba yadda uwar nan nasu tayi masu dazun da haka har mami ta gaiyaceni zuwa dakina da sunan zatayi sallah . A can ne muka samu kebewa da ita bayan mun sallame ta kira sunana na dago kai a hankali na kalleta ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI ALHERIN DAKE CIKIN RANAN NAN ALLAH YA SADAMU DASHI. INAWA YAN UWA TUNI GA YAWAITA ADDU,A A WANAN RANAN ALLAH UBANGIJI YASA MU DACE AMIN, , , , , Mun idar da sallah kowa na saman sallaya a zaune yana addu,a kafin mami ta shafa ta juyo tana bin dakin da kallo ta ko ina kafin muryan ta ya biyo baya tana fadin. Zainab nasan zakiyi mamakin ganin saukowa na haka da sauri cikin dan lokacin da bakiyi tsamanin hakan ba ko ? Kallon ta kawai nayi duk da gabana yana faduwa daga yanayin da take kallona din hakan baisa na katse addu,an da nakeyi ba a lokacin . Saidai kawai kan dana kadawa mami din a lokacin alaman naji taci gaba da fadin kada ki dauki hakan wani dama a gareki yanzu da zaki ga kin kai wani ko kinfi wani ne a yanzu a gida na zainab. Kada wanan dama ya saki dauka na manta me kukai min a baya duk ina fada maki wanan zancen ne ki san matsayin ki a cikin mu. Don ban shirya dana ya ma zauna zaman aure dake ba balle a kaiga haifan jikokin da basu da usulin da nake so. A raina nace ashe shiyasa kika aurowa ya mamud Nuriya take garaku yadda take so itin hakan kike so ke ko ? Ganin na fara shiga dogon nazarin kan zancen dake fita a bakinta din ko ina mamakin abinda take fada min din yasa taci gaba da fadin kwarai zainab. Na sani kin yi kokari kan jafar din fine dama ai duk mace da take hasashen wani abu dolene ta dage ga abinda take so har ta cinma burin ta. Bance bakiyi kokari ba kamar yadda ya fada kinyi kokari kowa ya sani amma wanan bashine dama a gareki ba. Allah ya gani ba irin ki nake so da dana ba zainab nafida son diyana su auro min wa yanda ke da asali don hakane ma bani kaunan ki hada shimfida da jafar a yanzu. Wani kallon mamaki nayiwa mami din har lokacin ban samu bakin magana a gare ta ba don mamaki tace kwarai kuwa zainab don. Kin fi kowa sanin son da nakewa jafar cikin diyan dana haifa kuma nake dasu a yanzu a duniya. So da kaunan da nakewa danane yasa na nuna a gaban kowa komai ya wuce a wurina har na gane kurena don gudun halin da zai sake fadawa nan gaba kan hakan, shiyasa na daure nayi hakan don fitar shi cikin halaka. Wanda nasan bani kadaine wanan abin zai shafa ba a yanzu har ke da kike kirarin matarsa ce ke, don Allah kadai yasan abinda kikawa jafar a yanzu yake mutuwar a gareki haka. Murmushi na sake a nan, don na kasa hade maganan da take fada min a lokacin nace mami ke nan nasan da wanan nasan kuma hakan kafin ki furta a yanzu din don tun a gidan ki na hango hakan a idon ki. Sai dai saukin abin ni Allah bai dora min son daki ba tun farko a zuciyana don har yanzu kallon kyama nake masa ga irin abubuwan sabon daya aikata a baya. Ba wata mace ko uwa da zata so a danganta da mai itin wanan bakin fasadin a duniyan nan yanzu. Kuma kada ki manta cewa ko lalacewan tashi ta farko banice sanadin shi ba a haka na sameshi da abinshi kuna tare dashi hakan na zauna a kyamace dashi ? Don me kuma a yanzu zan jefashi cikin wani rayuwa bayan nina san irin wahalan da nasha a baya don naga ya dawo mutum kamar kowa abin alfahari a yanzu ga wasu. Sai dai kuma mami a yanzun wanan maganan naki ya haska min idona sosai kan daki din yanzu na gano manufarki ga hakan a kan danki don haka. Ni a yanzu har na fiki son jafar don ga alama nina fiki sanin zafin shi a yanzu don jafar mijina ne ke kuma danki. Kinga ma,ana nan ina nufin koda yaushe ina tare da jafar ke kuma uwace sai lokacin daya tuna dake yaje gareni kinga na fiki damuwa da damuwan danki. Ido tas ba kunya nake fada mata wanan maganan da umma ta tsara min in fada mata idan bukatan hakan ya taso don mami tasan yanzu ba da bane a wurina. Ko zan samu saukin irin hattarana da suke nuna min ita da diyan ta mata da bansan abinda nayi masu ba har yanzu. Zainab ni zaki kalli idona ki fada min magana irin wanan haka a gabana ashe dama karyan yi min biyayya kike a gaban mutane kike nuna hakan ? Lah mami bana karya ko a kan gaskiyana sai dai maganan ya dangaci hakane a yanzu a da ina tunanen barin danki din don kwanciyan hakanlin ki gareni. Amma yanzu na gane kurena a kan hakan ko aure nawa nafita nayi dole a saka sunan jafar a na farko a cikin mazajen dana aura a duniyan nan. Don haka barin shi ma bai taso a gareni ba kamar yadda kike son in barshi din ki auro masa wata wace kike ganin itace ta dace dashi a yanzu din bani da banda asali ba kamar yadda kika fada yanzj. Don haka zama da jafar yanzu na fara tunda mijina naso na bai damu da koni wacece ba ya gani yasoni a hakan da wani manufa da a yanzu ya zama muna alheri ga baki daya mu. Idan asiri nayiwa jafar har yake sona sai nake ganin ai banice farau wurin yin hakan ba aga yar kauye a aureta ta zama wani abu a duniyan nan. Ta joyo a hasale zata kai min duka aka budo kofan shine a tsaye a yadda ya gamu ya tsaye rike da kofan a hannun shi yana raba idanu a tsakanin mu Kafin na wayance da fadin mami kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zan sake ba kuma nayi maki alkawarin komai zai kara daidaita a tsakanin mu insha Allahu. Na fada a dan maraice kamar ina ladabi kan wani zance data fada ya bata min rai a lokacin ya karaso cikin dakin yana fadin . Mami is ok ai ku tafi gida kawai zamu zauna mu sasanta kan mu zainab me hakkuri ce da yafiya wanan zance ya wuce a yanzu ai. Nace don Allah ya jafar ka tayani bawa mami hakkuri bisa abinda nayi a dazun ya bata mata rai ba zan sake kuskure irin wanan ba insha Allahu. Don't mind with that mami ba zatai fushi dake ba zainab tunda kina son mu da zuciya daya kina kuma zaune damu a cikin amana. Da ba don ke bace a gidan da yanzu yar leken asirin gidan nan ta gama kai rahotona zuwaga magabatan ta ko, akan abinda tazo nema game dani a gidan nan. Sai Allah ya taimakeni zainab din ba mai yawan surutu bane haka don haka bana tsamanin ta samu abinda take son samu a wurina a yanzu. Sabon zance ke nan kuma a yanzu mami takeji daga bakin shi akan fadila, a cikin rawan jiki mami din ke tambayan shi wai wata yar aiki dai yace wanan dai da take zaune damu a gidan nan. Yar sandan ciki ce ita an turota ne gidan nan ta zauna damu duk tsawon shekarun tana bincike ne a kan mu haka. Labarin da sirin mutum wani lokaci akan sameshi ga matar ga matar mutumce mami sai ya kasance zainab din bata fadawa kowa sirin takeyi ba har nawa din bata hiran hakan da bakuwar fuska. Innalillahi ya akayi kuke zaune da yar leken asiri a cikin gidan nan me take nema a wurin ka har tazo ta zauna maka a gida hakan nan tana maka zagon kasa. Aiki tazoyi a kaina bata san mun gane hakan ba zaune kawai muke da ita me zata fada mami tunda bataga abinda tazo bincike ba a kaina din. An turotane tayi bincike a kaina, don su gano irin abinda nakeyi nake samun kudin da suke gani nake dashi don su a zaton su ina wani smogling din wani abu da gwaunati bata son a shigo dashine a kasan nan. Ko ina kaiwa wani kasan abinda suke tuhuma ke nan suka turo min ita a maysayin yar aiki a gidan nan take zaune tare damu. Mami me zata fada tunda bata gani ba ni wanan abin baya damuna ko kadan kawai dai ta gama zaman ta ta kara gaba. Mami ta amsa da fadin dama na sani wanan matar munufukace tun farko sam batayi min ba rayuwan ta yana nuna ta faye wayewa da yawa. Tun da naga kansu hade da matar ka nake tsoron wanan matar wallahi ashe hasashena ya zama gaskiya a kanta. Kai mami don kawai tana gidan nan ne kike ganin su da zainab din amma ai zainab ba halinta magana haka ba. Zainab din ma idan mun koma karatu zata fara kuma zata fara aiki da mun koma din zakiyi alfari da wanan sarakuwan naki nan gaba kadan insha Allahu. Karatu ni ba karatune a gabana ba in daiga kun fara haihuwa a tsakanin ku in samu jikoki irin su ihisan daga tsatson ka. Kai ya fara sosawa yana dan murmushi tare da fadin with time mami zasuzo har sai kin gaji da dauka. Ya juya zancen mami din ya juyo dashi dashi da tace wanan matar taka ai ba haihuwan take so ba ita sai dai idan da wata matar zaka haihu jin hakan yasa ya juyo da sauri yana kallon ta a cikin mamaki. Mami wanan maganan fa inma zolayan zainab kikeyi ki daina don Allah kada kisa hankalinta ya tashi a yanzu A kan wanan zancen hankalina zai tashi sam wallahi na fada ina dan murmushi naci gaba da fadin ai bazan so in kasance cikin irin mata dake tauyewa mazajen su hakkin ba. Su hanasu aure alhalin suna son karawa auren a zuciyan su ni alfahari zanyi da hakan ba nuna bakin ciki ba . Kaida Allah ya bawa ikon yin hudu a lokaci daya don me zanyi bakin ciki don za a kara maka aure a yanzu . Abin alfahari ne a gareni yanzu idan zaka kara din aini ban son zama kamar laya a wuya. Na mike na bar inda nake tun idar da sallah mu din zuwa bakin gado ina daukan wayana dake aje a kunne ina recording din zancen mu da mami a ciki. Mami muje ko ya fada haka ya dawo da ita cikin tunanen jin zafin maganan dana saka mata din don itama ai hana mijin ta kara aure tayi a lokacin. Rai bace mami tafito a dakin duk da kokarin da takeyi na wayace hakan a fuskan ta sai haka bai yuyu ba a lokacin. Gaki mana ranki a bace kika fito hjy dake kallonta ta fada tace ba komai hjy gajiyene kawai . Har kofa muka kaisu na dawo tare da hjy mun dan zauna kafin in mike zuwa dakina na shiga na sake alwala nayi sallah. A wirin na zauna na dauko wayana na kira layin umman su Nafisa na kwshe duk yadda mukayi na fada mata. Umma tace dama na fada maki ban yarda da nadamar wanan matar ba a lokaci daya haka tace wai ta sauko. Tayi hakan ne kawai don ta batarwa mutane da hankali ke kuma ta jefaki a cikin damuwa yanzu sai ki zage sosai ki bi mijin ki ki kara kwantar da hankalin ki a kan auren ki. Bayan mun gama waya da umma Nafisa ta karba ta bar wurin tana fadin yau kin min daidai kan matar nan wallahi wai me take nufi dake ne zainab ? Nace koma me take nufi ai yanzu ya saura gareta tace tunda ta nuna hakan wallahi yanzu ki shirya ma zamakin sosai kada ki tafi baki shiryawa zaman ki ba don zata iya yi maki komai a duniyan nan tunda bata kaunar ki dai a ranta yanzu. Dama tasone ta more maki kawai suci moriyan ki karshe ta hadaki da yan aikin gidan ta aure taci gaba da more maki ko yaushe. Sai Allah ya fitar dake ya dora ki saman ta da bata taba zaton hakan ba a rayuwan ta ai dole ta yi bakin ciki dake yanzu . Don alama ya nuna duk cikin diyan ta mijin ki tafi so a rayuwan ta fiye da yan uwan shi . Allah zainab ki tari mijin ki a yanzu kuma kija hankalin shi sosai tunda kinsan ba sabawa yayi dayin hakan ba kila sai kin koya mai a yanzu. Nace cikin harara kamar tana ganina a lokacin nake fadin akace maki ni din na iya ko ? Ko baki iya ba dai kedin mace ce ai don haka sai ki koya kawai daga yanzu zan turo maki wani wa,azi na abubuwa ki saurara sai ki fara daga yau zanyi magana naji ta kashe wayan tana dariya. Ba a dade ba naji massage suna shigo min na duba itace ke fadin ki bude ki saurara na turo maki sakon Allah bada sa,a sauraren in samu lada ga hakan nima. Tsuki nayi na jefar da wayan na shiga wanka bayan na fito ne wayan yana ringin na dauka sa,adatu ce a layin take fadin inna ce tace yau baki kira ba tun safe ko lafiya in kira mata ke taba inna muka gaisa tare da tambayan lafiyan su. Muka dan taba hira kafin taba kannena wayan muka gaisa dasu kowa na fada min abinda yake so in sayo mai idan zanzo sallaman su . Na kashe wayan ne har zan aje saina tuna da zancen sakon Nafisa hakan yasa na kunna data na na shiga sakon na fara saurare ina shafa mai ajikina lokacin dare ya somayi har goma da rabi yayi gashi ban ko ci abinci ba a lokacin. Ashe shima rashin fitana ya hanashi cin abincin sai gashi dakin ya shigo a daidai lokacin ina kashe wayan dana saurari wa,azin a ciki. Zama yayi a bakin gado ina saka rigan dana dako saida na gama yake fadin me kika fadawa mami dazun daga maganan wasa kika sake mata magana haka ? Amma kinsan mami ita kadaice gun mahaifin mu ai zata dauka da ita kike wanan maganan ai jin hakan sai nayi murmushi ina fadin. Ba zan taba fadawa mami maganan da zai bata mata raiba don mahaifiya take a gareni saida wani dalilin yasa kaji na fadi hakan a yanzu ma. Oudio wayana ne ya soma magana ya dago kanshi da sauri tare da juyowa a inda nake tsaye yana sauraren zancen mu da mami na dazun din. What ya fada har ya mike ya koma ya zauna tare da dafe kanshi na dan wani lokaci ina tsaye na hade hannaye a wuri daya ina kallon shi. Tare da fadin tsamanin hakan yasa na danna wayana ya dauki komai don sheda a gareni duk da hakan ba wai haka na nufin raini ko wani abu zai shiga tsakani mu bane da mami. Har kayi tunanen na fada mata maganan da zai bata mata rai dani bayan an shirya mu a yanzu di nida ita. Kawai na fadi hakan ne don abinda nima take tunanen yi a gareni don haka a yanzu ka barni don Allah in koma gidan mu don ka shirya da mahaifiyar ka a zauna lafiya. Koyin hakan zai kawo maku kwanciyan hankali a tsakanin ku daga fadin hakan naja bakina nayi shiru tare da zuba mashi ido. Sai kawai naga ya mike zubur ya fita daga dakin ya barni nan a tsaye ina binshi da kallo kafin in fada saman gado don takaici. Nakai minti talatin a hakan ina sakawa ina warware a zuciyana kafin in mike zubur na shirya duk wani shiri da zanyi najawo kofan dakina na saka masa key na fita zuwa part din shi kai tsaye. Yana kwance saman gadon kamar yadda ya saba idan yana cikin yanayin damuwa har na rufo kofan na karaso bakin gadon bai motsa ba. A hankali na kai zaune ba tare da nayi mai magana ba ina karatun addu,oin kwaciya na gama na kai kwance a gefe shi da dan nisa a tsakanin mu . Ranan tuesday in Allaj ya kaimu zamu koma don haka ku fara shirin tafiyan mu ya fada ba tare daya motsa din ba. Na fada ma ba zan zauna ba yaya gidan mu zan koma don mami ta tsaneni har cikin ranta ba zan taba yin haske a zuciyar ta ba. Idan zaman kanki kikeyi ki koma gida din a yanzu ya fada tare da gyara kwanciyan shi duk a zatona dana shigo zancen mami din zai min kan musayan maganan da muka fadawa junan mu. A hankali yakai hannun shi ya kashe hasken dake dakin kawai ji nayi ya mirgino ta gefe na ya rungumeni a cikin jikin shi gaba dayan shi ya sakar min nauyin shi yana wani irin ajiyan zuciya. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI BARKAN MU DA WANAN SAFIYAN ALLAH YA SADAMU DA RAHAMOMIN SA ALLAHUMA AMIN. LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALLAMA KADA MU RIKE JUNA GA HAKAN, , , , Yar uwa ko zaki tuna da wata boyar Allah mai suna mama Ai ko mama Aisha a cikin groups din mu da Allah ya karbi ranta a sanadiyan ulcer rana daya duk munyi hira da ita a ranan zuwa yamma Allah ya kirata zuwa gareshi. Yar uwa ko kin gane ta ko baki gane ta ba ina mata baran addu,a a wurin ki ubangiji Allah ya kai haske a kabarin ta ita da sauran yan uwa musulmai da suka kwanta dama tun zamanin Annabi Adamu har zuwa wanan ranan ta yau ubangiji Allah ka haskaka kabarin su idan tamu tazo mu cika da kyau da imani Allahuma Amin, , , , , Wani iri naji har kasan zuciyana a lokacin duk da ya saba rike ni sometime sai dai wanan rikon yayi daban da na kullun daya ke min a baya. Don rikone dake nuna yana a cikin zafin rai a lokacin da farko nayi yunkurin hana hakan a gareshi don yadda nake jin zafin shi dashi da mahaifiyar su a lokacin. Tunanen kalamin umman su Nafisa ne cikin huduban da tayi min da cewa ki rugumi kaddara ki karbi mijin ki da hannu biyu don shi Allah ba ruwan shi a shanin aure idan kin saba mai zai tuhume ki ga hakan. Ruguman mijin shine zai kara kawo mai natsuwa a zuciyan shi don akwai wani sirin boye dake tsakanin miji da mata da sai Allah ne yasan wanan. Zakiga komai sabanin daya shiga tsakanin ki da mijin ki da zaran sun kwanta a wuri daya komai sai ya wuce a zukatan su a koma daidai. Koda ko abin bai tafi duka a zuciyan su ba a sannu zaizo ya gushe ba tare da sun san dalilin hakan ba a gare su wanan sirine da Allah yabarwa kanshi sani. Idanuna na runtse danayi wanan tunanen ina jin yadda yake ajiyan ziciya hannun shi nabun sassan jikina a hankali hakan ya zame min bakon abu din babu na mijin daya taba taba min jiki da suna jin dadi a zuciyar shi sai wanan ranan. Inda hannun shi yakai ne yasa ni dan yi kamar na zabura lokaci guda shi din ma wani irin haniniyar da dawakai keyi yayi a lokacin wanda har hakan ya bani dan tsoro da sauri na bude idona na sauke a kanshi. Yanayin da naga fuskan shi duk rashin wadattacen haske dake dakin lokacin hakan bai hana na yadda fuskan shi ya sauya ba zuwa wani yanayin da ban taba ganin shi ba a cikin sa. Ganin na bude idona yake fadin kamar mai rada a lokacin bayason wani yaji abinda yake son fadi. Be cool bby i don't wana hurt you, be cool dis my first time to be with a girl like dis, , , , , Dan abin da zan iya tunawa ke nan yana fada a lokacin dan cafkan da yakai min a saman kirjina tun wanan lokacin na fice a cikin hayacina ga baki daya ban san duniyan da aka kaini ba . Sai hawayen dake dan gangarowa ta gefen fuskana da ban san kona meye ba don kanshi ya gaji da jagulana ya barni a lokacin. Saida na dan dauki lokaci ban iya motsawa a yadda nake ba kafin can na dan fara daga hannu na a hankali ina neman rigana daya cire a cikin dabara saman godon. Daga gefena nake jin yadda yake ta faman sauke numfashi tare da ajiyan zuciya duk a lokaci daya yake wanan kamar wani wanda yai tseren gudu tsira daga abin cutarwa ya tsere mar. Ko ya fahinci abinda nake nema ne a lokacin sai naga ya dan miko min kamar cikin fushifushi daga hakan ya koma ya mirgina yana gyara kwanciyan shi da kyau. Hakan ya ban daman samun in mike da sauri na nufi banda ina tsugunawa sai fitsari shaaaa don tsoro ko bakon yanayine oho ? Har wanka saida nayi ina hawaye ga nawa wautan har da wankan tsarki saida nayi kafin in fito ban dakin don naji ana fadin daka kasance da namiji wanka ya hau kan ka kenan. Hakan yasa na hada da tsarkake kaina a bandakin a zato na yayi barci a lokacin ina hawa gadon naga shima ya mike ya nufi bayin a hankali na rufe ido na mayar dasu lumshe sai dai tunanen da nakeyi kawai a lokacin har barci ya dan saceni ban sani ba . Jin ruguman da yayi min yasani dan bude idona a firgice ina kallon yadda ya matseni a cikin jikin jin da yayi na dan falka a tsorace yayi saurin fadin shiiii baiyi amfani da baki ba wurin fadin wani magana. Gabana yana faduwa don haka kawai dan tsoron daya fara yi dani yasa na tsorace da al,amarin shi ga baki daya ganin yadda yai min din. Can murya kasa kasa kamar maganan ya zama mai dole a lokacin ya fara fadin Fadila ta fada min asabar zata bar gidan nan kwata kwata . Wani irin ajiyan zuciya na sauke tukun kafin ince haka ta fada min amma na roke ta da tabari har mu bar kasan ta tafi. Ta yarda da hakan ya tambaye har lokacin ina rike a cikkn jikin shi bai sakeni ba nace batayi min wani bayani ba bayan hakan. Ba zata yarda ba na sani don aikin tane ya kare a gidan nan zata koma masu da bayanin abinda ta samu a nan din jin hakan yasa na danyi yun kurin barin jikin shi. Saidai bai sakeni din ba yana matse dani yake fadin kiyi tunanen abinda ya dace muyi mata kafin ta tafin jibi. A haka mukai barci yana rugume dani a cikin jikin shi sai gashi gaba dayan mu, ranan mun makara ga sallah asuba, a gagauce muka samu yin sallah lokacin shidda da rabi na safe tayi a lokacin. Ina idar da sallah na gaida shi a cikin kunya ban tsaya a dakin ba na koma dakina ina shirin kwanciya karan wayana dana bari ne ya tayar dani. Na dauka kada ya katse Nafisace sai mamakin kiran da take min da safe haka ya kamani na daga da rawan jiki gaba yana dan faduwa don kiran safe ba dadi ke gareshi ba wani lokaci. Ina dauka abinda naji tana fadi yasa hankalina ya fara kwanci tana fadin amarya amayra a cikin dariya naja wani tsuki ina fadin. Ke yar iskace wallahi, ni har kinsa gabana faduwa wallahi wanan kira haka da sasafen nan haka ai saiki tsorata mutum dashi. Ai dole gaban ki ya fadi tunda yau kinji maza a jikin ki da sauri na tareta da fadin ke dan Allah magulmaciya to abinda kike son ji bashi din ya faru ba. Naga alama tunda naji muryan garau ai amma jafar bai kyauta min ba da bai samu banza ya lalatsa muna ke ba wanan bakin ya mutu a yau din nan da anyi magana kice kema daidai kike da kowa har yanzu. Allah yafiki Nafisa don adduan ki bai karbu ba wallahi yayan naki da yake mace kamana shima matsoracine irina . Har me zai iyayiwa mace a yanzun duk da kirarin da yakeyi wai ya warke a yanzu ta kwashe da dariya tana gadin. Yarinya kidai bi sannu wallahi kada muji ana kara maki ruwa asibiti wata rana sai abin ya ban dariya na kashe wayan ina fadi a raina hakan ai ya kusa faruwa dani a jiyan Allah daine ya taimakeni. Ban iya fitowa dakin ba sai wajajen sha biyo da rabi koshi don lokacin sallah ne da yayi a lokacin nasan na tashi a wanan lokacin. Wanka nayi na fito yi sallah kafin na gyara jikina na fito waje na lura da baya gidan don motocin shi da bangani ba a lokacin. Babu kowa a falin na nufi part din hjy in gaida ita na samu bata gidan wai sun fita tare dashi zuwa gidan mami . Banyi mamakin jin hakan ba don nasa zancen bai wuce maganan jiya daya farune tsakanina da mami zai kaisu gidan a yau. Dan tun barin hjy asibiti sai jiyan da muka fita tare da itane taje gidan saidai su mami din su zo gaida ita a nan gidan nasa. Abu bai dameni ba tunda nasan ina da gaskiya akan zancen don haka na share maganan a raina don yanzu an kai bana jin shakkar mami din kuma ko kadan a zuciyana kamar baya can da nake jin tsoron ta. Don ada can ko muryan ta naji sai gabana ya fadi don tsoron ta da gudun saba mata da nakeyi amma a yanzu sam na daina jin hakan. Ko dan na kara shekarune ko kuma dan budewan da idona yayi a yanzu ne ban sani ba wanda nasan ita ma a yanzu dai tasan da hakan. Abinci na zauna naci don har sun gama abincin rana a lokacin ina kanci sadiya ta fito ta ganni zaune take fadin. Anty kin tashi dazun nayi ta lekawa kina barci har yaya yasa na dauko mashi wayan ki a daki ban san me yayi dashi ba kuma ya bani na mayar maki dashi. Ina anty take na tambaye ta ba tare dana bata amsa ba na kawar da maganan tana dakin ta ta shiga tayi sallah ta bani amsa. Mikewa nayi bayan na gama zuwa dakin sai da nayi sallama ta amsa na shiga tana zaune tana waya ganina baisa ta daina wayan ba. Abinda naji tana fadi yasa na gane da yan gidan su take wayan a lokacin har ta kare a gurguje ta juyo tana fadin na barki zaune ko madam. Mun tashi lafiya na fada tace lafiya kalau, zuwa na biyu gaida ke na samu kina barci wallahi sai yanzu na tashi nabata amsa. Abinci yana falo ta sake fadi ai har naci yanzun dana tashi din ashe hjy ta fita ita da yaya na tambaye ta. Eh naga sun fita duk ransu a bace bayan sun dade a daki suna magana dashi da ita kafin su fita din hjyn ma ke fadin gidan mami zasu tafi yasa na san inda zasu din. Nasan kin san komai anty tun farko abindake akwai tsakanina da mami shine jiya din muka tafi akai muna sulhu ta nuna komai ya wuce a wurin ta ai. Jiya kin gansu a gidan nan da yamma ai tace eh nace bayan sun zo nan din kuma ta sake nuna hakan a gaban kowa komai ya wuce a tsakanin mu din. Bayan munje sallah da tace a dakina zatayi nan dai na kwashe komai na fadawa fadila din yadda mukayi da mami din ranan. Na karasa da fadin to yanzu nasan a kan wanan zancen ne suka tafi gidan don wanan maganan yasa yaje mata harda evidence din shi da yake dashi kan hakan don na dauki komai a lokacin. Tace kai subbahanallahi wanan matar kamar bata da imani wai bata tunanen ita din uwace haka na iya faruwa ga wani nata koda bata da diya macw ne ? Irin uwanyen mijin nan suna da yawa saidai wasu basu taba yarda a gane hakan a garesu har duniya ta gane zasuyi tayin abin a boye ne sai sunga bayan mutum idan ba Allah ya hau da kai kansu ba. Wasu kuma baro baro suke fitowa fili su nuna bakin cikin kan matan diyan su din tunda kinji cikin maganan ta ai ta fadi tafi son shi fiye duk diyan ta. Kinga ke nan koba keba zata iya yin hakan da kowa a kanshi don haka zainab don darajan Allah ki zauna da mijin ki lafiya. Nayi nazarin mijin ki na gane shi mutum ne mai kyautatawa iyali da son kulawa na tare dashi don haka yadda take sone bata samu ba a gareshi din ba kuma zata taba samun hakan ba tunda a yanzu ya gane ko waye mami din kan iyalin shi. Ba zai taba yarda da hakan ba idan ba wani kaddara ya kaddaro hakan ba a gareku nayi saurin fadin idan ma zata yi din tayi ai wanan bai damuna a yanzu. Umm,umm zainab kada kice hakan don yanzu ba zakice ga kan aure ba tukun don baku fara zama zamana aure ba dashi a tsakanin ku. A lokacin zaki gane waye miji a wurin ki da barnan da mami din ke son tayi maki a lokacin. Jin hakan yasa na danyi murmushi sai nake fadin motar ki tana ina yanzu na daina jin kina zancen ta fa ? Kai wanan motar ai wahala ta fara bani daga baya kawai na sayar da ita nasa a cikin ginan da mukeyi don ina son mu samu gida na kan mu nida mahaifana. Allah sarki na fada kawai muka dauki wani hiran rayuwa mun dan dade a dakin muna hira kafin mu fito dukkan mu waje. Su hjy sai bayan la,asar suka dawo gidan kowan su ya nufi part di shi bayan na fitone nasan sun dawo gidan na shiga wurin hjy don mu gaisa. A zaune take tana duban wani abu a cikin leda na zauna muka gaisa nayi masu an dawo lafiya. Kafin ta amsa min saida ta tabe bakin ta tana fadin ke dai mun dawo da wanan abin kunyan da uwar ku tazo jiya tayi a gidan nan. Nikan da ba don ba sai ince an sauya iyamine ta koma haka ko ince an min hurhuren ta a can turai data zauna a can. Yarinya da kafiyan tsiya kamar mutanen farko yau ai dai taji dan nata dama haka duniya take ai ka yi aimaka. Idan tace ba zataji magana ta ba ko shawarana ta daukeni da mutunci itama yau taji a jikin ta kamar yadda nake ji a kanta din. Don yau danta ya fada mata data rabaki da shi ta rasashi har abada a duniyan nan don haka ta rabu masa da mata haka. Shigowan shi hjy tace kinga sa nan yau a kanki yayi fadan da bai taba yi ba a gabana sai dana tsawata mashi ya daina haka. Common kin faye surutu ya fada yana fadawa saman gadon dake dakin a rigingine ya kwanta yana kallon daking din dakin. Shiru yayi muna ta hiran mu da hjy kafin yace zainab kinyi shawara kan magana fadilan din nace eh nayi . A cikin turanci yake maganan na fada mai abinda na hango a kanta din yace is ok kawai zuwa can ya mike ya fita daga dakin. Mikewa nayi nabi bayan shi abinci na hada na sameshi ya fito ya zauna bai wani ci ba ya mike ya koma saman kujeran dake falon ya zauna. Na gama hada kayan na biyo bayan shi muka zauna a wurin sadiya na fitowa take gaidashi yace sadiya kin fara shiri ko. Zamu koma ne yaya ta tambaye shi yace next week insha Allahu nake son mu koma . Zamu je Anchau ke nan kwanan nan ta sake tambayan shi da hakan zaku koma kuma again ya tambayeta shima. Zamuje mana mu yi masu sallama na fada don ba zamu wuce bamu sallamesy ba gaskiya ke nan ba next week zamu tafi ba ke nan idan hakane. Kowan mu yai shiru shi yace ok sai kusa ranan da zaku din kafin mu tafi yana fadin haka ya mike ya shige part din shi. Bai kara fitowa ba sai da dare na sameshi zaune ya maida hankalin shi gun laptop din shi yana aiki a ciki. Jin motsina yasa shi dan dago kai yana fadin hado min ruwan zafi na aje wayata da zanin sallah na juya nabar dakin zuwa yi abinda yace nayo din. Saida ya sha tea din shi ya gama ya hau gadon ya dan dade ko me yakeyi ban sani ba sai can najishi yana dan kiran sunana ban bude ido ba. Ba kunya ba tsoro abinka da tashin turai ba kunya ko sanin ya kamata kegaresu wai nice yau ya jafar ke fadin yana son ya kasance dani . Ki taimaka a yau nake son na kasance dake if posible ya fada min kai tsaye kai wa,iyazu billahi wani irin naji wanan maganan a kunnuwana. Jin bai samu amsa a wurina ba yasa naji yakai hannu a jikina ya fara tabani na dan zabura don ban gama fargaban zancen shi sai jin hannun shi saman jikina nayi. Sannu a hankali yake bin ko ina da sallo yana dan kara matse ni ina runtse ido tare da kiran sunan Allah a zuciyana. A lokacin nake tunanen maganan shi ta farko dani zuwan mu chaina da yake fadin shi da mace sai friendship ko zumunci kawai ke tsakanin shi da mace babu wani sha,awan da yake jin gun diya mace a rayuwan shi. Sai gashi yau shine kuma din yake yin abinda mai sha,awan wani abu a jikin mace yakeyi yana sake wani irin sauti dake fitowa daga ko ina din jikin shi. Ban kara yarda shi din bane saida yake kara sautin gurnanin da yake sauka min a kunnuwa ina jin kamar a mafalki hakan ke gudana a tsakanin mu . Sautin ya zo min a baza da kuma tsoro a lokaci guda dan wani irin ihun daya yanka lokaci guda tare kokarin shigana da yake kokarin yi a lokacin . Duk ilahirin jiki shi na wani karkarwa nima hakan nawa ya shiga yi a lokacin gaba dayan mu muna a cikin wani irin yanayine mai ban tsoro s garemu . Ina jin yadda jikin shi ke wani irin bada sauti mai kama da ana kara wani bangare na mutum a lokacin kas kas kas amma kuma hakan baisa ya dana yin abinda yakw da niyar yi din ba a lokacin. Wa,izubillahi a cikin lokaci gudane komai ma da zai faru din ya faru damu don dai ya samu din yakai garemu yayin daya koma kamar mara hankali lokaci guda. Zai shiga cikin wani yanayin da bai taba shiga ba ke kuma baki taba gani ko jin hakan ba ki daure ga duk wanan abinda zaki gani hakan shine karshen wani fitina ko shirin shi ke nan a duniya. Hakan shine rushewan duk wani abinda bai sani ba dake boye a ruyuwan shi zancen kakar maya ne ya fado min a rai . Tace zaki jirki kamar yadda zai jirkitan idan kinga hakan ki jika wanan kusha a tare ta daga hannayen ta ta ware su a lokaci guda alama komai ya wuce ke nan. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA DA FATAN MUN TASHI LAFIYA ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA DA ALBARKA DAKE A RANAN NAN AMIN, , , , , Dare mahutun bawa ne a lokacin kowa ya kwanta yana hutun gajiyan rana da samun sauki a cikin rayuwan yini. A wani gida dake unguwar sarki a cikin garin kaduna kamar yadda kowa yake kwance yana barci haka kuma ahalin gidan nan suke kwance suna hutu suma kamar kowa. Ihun da aka sakene a lokaci daya ya tayar da duk ilahirin wanda ke barci a gidan lokacin sai dai wanda ke wani abin baiyi barci ba. Wani ihun ta sake sakawa wanda yasa kowa na gidan fitowa waje da sauri don ganewa idon su abinda ke faruwa. Ihune yanzu ba kakautawa sai kiran sunan iyami da mijinta marigayi matar keyi a cikin tashin hankali. Wanda hakan yaba duk wanda ke gidan a lokacin tsoro sai faman fadi takeyi Allah ya isa Rakiyan hayi. Ko kuma tace kai ina karya dai sam wanan ba zai taba yuyuwa ba ace ka karye bayan nice kadai mai iya karya wanan kwalban haba dai sai kuma ta fashe da dariya da tabe tana son fita waje da gudu. Ke ke ke haulatu wai meye wanan haka kikeyi kika tayarwa mutane da hankali ki duba har kananan yara sun fito don wanan ihun da kike sakewa mutane haka s cikin dare. Wani irin mikewa tayi tsaye da karfi tana fadin ni ni ni sai kuma ta gitgiza kanta tana fadin karyane iyami karyane wallahi. Ba zaki shigo ki fini ba a gidan nan na fada maki iyami sai naga bayan ki har diyan ki wanan dan naki jafar da ake fadin yafi kowa taurari masu haske a cikin zirian nan sai na mayar maki dashi abin kyama a gun jama,a. Wani tsaya Alhaji Adamu ya dakawa matar tashi uwar gidan shi kuma uwar yayan shi manya ke nan a gidan. Yana fadin wai haulatu kina da hankali kuwa kikw fadin wanan maganan haka Rakiyan hayi dake mukaje dauko kwalba wai yanzu kwalba ya fashe ya tarwatse a sanadiya wata. Zance ta fara sakewa kamar mai bada labari sai salati duk wanda ke wurin suke sakewa diya ta naja baya daya bayan daya suna kuka. Hankalin kowa a tashe don sun gama fahintar abinda ke gudana a lokacin yayiwa iyami da jafar danta asirine yanzu asirin ya kare ya koma mata.. Dole aka sakata daki aka kulle don tonon asirin yayi yawa a lokacin suka dawo sukai zugun zugun a waje suna jinta tana ci gaba da fadin irun abinda tayi a gidan. Kowa hankali tashe gabani asuban farko sukaji dukan kofa a zabure samarin gidan dake waje cirko cirko suke tambayan waye da daren nan haka. Alhaji hayi yace nine Alh hayi na layin ku mijin aminiyar hajiya haulatu matar kanin mahaifin su jafar uwa kuma ga Rufaida a yanzu. Da sauri Alh Adamu ya karaso kofan yana fadin lafiya Alh a cikin daren nan haka yace daga waje inda yake tsaye ina fa lafiya Alh wanan matar Rakiya mai dakina tun cikin dare muke fama da ita da hauka tuburan . Sun je sun aikata sheri tare da maidakin hjy ta nan gidan yanzu kuma abu ya koma mata tana can tana faman tonawa kanta asiri gaban diya da kishiyoyin ta tun dazun. Kai innalillahi Alh Adamu ya fada yana bude kofa kafin yace muma nan tun misalin sha biyun dare muke fama da Haulatu cikin irin wanan halin. Wa,iyazu billahi ai zance ya baci ke nan kuma da na dauka tana a hayacin tane muji abinda ya kawo haka a bakin ya don sai sunan hjy iyami da danta take ambata cikin sambatun nata. Abinda itama take fada ke nan shiyasa na gane cewa sunyi wani aiki akan iyamin da yanzu ya karye ya koma kan su kuma. Yanzu dai dole mu nemi malamai su warware muna abinda ke faruwa ko kuma a kira ita hjy iyamin aji ko tana da masaniyan hakan. Ba sai an kirata ba a yanzu don hakan kamar sirin mu ne Alh gara a fara neman malamai din don kada hakan ya kawo wani fitina kuma. Fitina Alh Adamu ai ita da ta dauko fitan sai dai ya kare a kanta wallahi banji ban gani ban kuma aiketa aikata hakan ga wani ba balle abun ya dameni. Wanan zancen ma yasa ka fargar dani hanya yanzu gidan su zan bugawa waya suzo su dauke ta su tafi can su karasa wanan abin kunyan badani ba wallahi. Da sauri Alh Adamu yace kada ai haka Alh ai lafiya suka baka ita shi zaka duba ba sai yanzu da haka ya cika da ita ba zaka tura masu ita gida yanzu. Nasani amma hakan zanyi kai in zaka tsaya gidan ka ya koma gidan kallo zuwa safe daga haka ya juya Alh na kiran shi bai tsaya sauraron shi ba ya tafi. Sai dai abinka da babban gida sai gashi tunda asubahin nan a samu wanda ya kira mami ya fada mata duk abinda ya wakana a gidan. Hankalin mami din ya tashi sosai haka yasa bata iya kara komawa barci ba da sasafen nan ta tayar da yaran ta take fada masu abinda ke faruwa a kaduna din. Itama Rufaidan yan uwanta sun kirata tun a cikin dare suka labarta mata abinda ke faruwa kuka ta rushe dashi har hankalin yan uwanta ya tashi sun dauka ko mutuwa aka aiko mata anyi. Sunyi tambayan duniyan nan tana cewa dasu ba komai har suka gaji suka kyaleta saidai basu koma barci ba suna hira a dakin su. Har akai sallah kowa ya watse don zuwa office da zasuyi don ranan aikine ranan sai dai kuma jin tun safe an bude get dib gida mami ta fita yasa hankalin su kuma tashi. A falo suka hadu da Aisha data fito tana mamakin fitan mami din a wanan lokacin suka hade dssu falon nan suke fada mata zancen Rufaida din ta shiga dakin wurin ta. Tayi tambayanta tana ce masu ba komai ita gida zata tafi ranan ganin haka yasa Aisha daga waya ta kira hjy dake hanyar gidan mu tana fada mata abinda ke faruwa da Rufaida din. A cikin hasala hjy ke fadin kada ku barta taje ko ina munafukan banza da wofi kawai ta kashe wayan. Mamakine ya kama Aishan jin abinda mahaifiyan nata ta fada kan rufaida din da take ji da ita kamar yar cikin ta. Ganin irun mikan da yake faman yi yana hamma da wani irn nishi yasa naja jikina da kyat har na sauka saman gadon ni kaina ina cikin wahala don yadda ga baki daya nake jin jikina kamar ba nawa ba a lokacin. Ga zafin wahala dake cina ga hankalina da yake tashe a lokacin don tabbasa nasan da a cikin hayacin shi yake da ba abinda zai hana shi taimaka min a lokacin. Bandaki nayi karfin halin shiga na sakewa kaina ruwan zafi kafin na dan fara jin sa,ida a karkashina da nake jin bakon yanayi a gareni. Da kyat na fito bandakin da bin bango har na kai kofa na bude na fita zuwa dakina Allah ya taimakeni ba kowa daya ganni a lokacin har na bincika kayana nafito na koma dakin da sauri. Na shiga na samu ya fado saman gadon da gani akwai alaman ciwon ciki mai karfi ko wani abu dai yana damun shi sosai a lokacin. Da kyat na iya kai gwiwana kasa na dago kansa da kyat ya dan bude idanun shi kadan ya mayar dasu ya rufe nayi dubaran bude bakin sa a hankali na fara dura mai maganin ya hade. Yana shiga makoshin shi ina jin wani kara da yakeyi har ya sauka mai lokaci daya naga yayi wani irin zabura da karfi badan Allah ya gyara ba daya barar da kofin maganin dake hannuna a lokacin. Idanuwan shi ya ware yana kallona nayi mai sannu tare da kara daga kofin ruwan maganin da niyar kai masa a bakishi. Yayi saurin rike min hannu yana kallona kasha zaka samu lafiyan abindake damun ka a yanzu na fada a cikin damuwa. A take ya bata fuska nace yi hakkuri ka hade ya bude bakin na kara dura mai ya karba yasha yana bata fuska ya hade da sauri. Ya maida idon shi ya lumshe wanan karon kan zaune ya mike da sauri jikin shi yana wani irin karkarwa tsoro ya kara kamani lokaci guda can naji ya sake wani irin gyatsa mai karfi saidana zabura. Bai jima a zaunen ba ya koma ya kwanta a kasa inda yake da farko din sai ga wani irin zufa yana karyowa a goshin shi lokaci daya kuma sai gaba daya jikin shi zufa ya karyo mai. Nidai ina gefe daya ina kallon ikon Allah kafin ya bude idon again ya sauke a kaina yana nuna min AC dakin da hannu don har yanzu ya kasa bude baki yayi magana har lokacin. Tambayan shi nayi a kara ko a rage ya gyada min kai haka yasa na mike da kyat na kara karfin AC har karshe a hankali ya fara sauke ajiyan zuciya. Ganin da nayi kamar zaiyi barci a lokacin yasa nace dashi ko zaka daure ka koma saman gado ka dan kwanta a can . Kamar bai jini ba sai can ya mike da karfi a lokacin ma na farga da jikin shi babu komai dan abin rufane kawai daya kwaso ya dan rufa a gaban shi. Saida naga ya kwanta ya dan fara samun natsuwa na dauki sauran maganin da yake aje nashanye gaba daya maganin idan ya sauka ciki yana da zafi nikan da cikina baida komai banji irin abinda shi yaji ba. Na sake gyatsan kamar yadda shima ya sake din daya sha ina jin wani zafi a jikina na koma saman gadon na dan kwanta sai barci. Lokacin dana farka shidda ta gwauta na samu nakai ban daki da kyat ina sake ruwa a jikina ina gasa ko ina . Wai sai lokacin kuka yazo min na dade a ban dakin ina kuka kafin in fito in tayar da sallah sai da na idar na tayar dashi ya zabura yana salati kafin kuma ya koma ya dafe kai da sauri na dan wani lokaci. Sai can ya mike ya shiga ban dakin ya dan dade kafin ya fito wurin wardrobe din shi ya nufa ya dauko riga ya saka saida naga ya tayar da sallah . Na nufi gadon da nake gyara na canza zanin gadon zuwa sabo ban tsaya har ya idar ba na fice dakin zuwa dakina. Don a matse nake komai wuri kawai nake nema da zan kai kwance a lokacinb kaya na saka a jikina na kwanta tunanen abinda ya faru a daren jiyan ne yake dawo min a raina. A hankali na mayar da idona na runtse a cikin takaici da bakin ciki ina nadaman kasancewa a cikin wanan halin. Yau mace idan ka ganta tare da mijin ta ka barta kawai a inda ka ganta ba sai ka tono abinda ke boye ba. Don matsalan gidan wani daban yake dana gidan wani sai dai abin na wata yafi na wata abin ban mamakine . SHI ABU A CIKIN DUHU DAI SIRINE kawai a barshi a boye a yadda yake zaifi sauki. Barci ya dauke ni har na tsawon wani lokaci a cikin barcin nake jin ana tashe ni sadiya ce tsaye a kaina take fadin ki tashi anty ina ga kamar ba lafiya a gidan nan. Don ga mami nan tazo tun dazun a cikin kuka har ya jafar ta shiga dakin takirashi suna dakin hjy ana hayaniya tun dazun din kowa sai kuka yakeyi. A zatona abinda ya fado min a rai shine zancena da mami daya faro a jiyan da sukaje mata dashi. Shine har yanzu basu bar zancen ba a tsakanin su saidana danyi wanan tunanen na dago ina cewa sadiya ki zauna nan kada ki kara fita falin ga baki daya. Ta kalleni a cikin mamaki kamar zatayi magana sai tayi shiru kafin ta kai zaune gefen gado ta kurawa kofa ido. Mikewa nayi a hankali cikin dabara na daure ina tafiya zuwa ban daki na samu na kai da kyar nayi fitsari na dade ina gasa kaina kafin na fito a lokacin naji dan dadin tafiya a yanzu. A daidai lokacin da nake zama take fadin wai anty mami din tana da kishiyane jin haka yasa na dago ina kallon ta nace sadiya meye damuwan ki da zancen mami ne ? Anty ji nayi mana yanzu suna fadin wai kishiyan mami din ta haukace jiya da dare wai tayi masu asiri ya karye. Wani irin faduwan gaba ne ya ziyarce lokaci daya dana ji hakan a take zancen malam kakan mu ya fado min a rai. Da yake fadin akwai asiri a jikin mijin ki karyewan shi zai samu ne kawai a jiki ki duk ranan da mijin ki yakai jikin ki komai zaizo karshe da yardab Allah. Kedai kawai kuci gaba da amfani da maganin nan da wanda tsohuwar nan ta baku a can akwai waraka a cikin sa sosai insha Allahu. A sannan ne za ku gane waye yake bibiyan mijin ki tun yana karamin shi har zuwa yanzu din don dai akwai hannu sosai ga al,amarin shi. Kallon sadiya din nayi kamar zan yi magana sai naga wanan maganan bata kai ta gane abinda ake nufi ba. Na dan jima a zaune kafin na mike ina fadin barin zo sadiya ki jirani a nan na fada na fita daga dakin. Ina kokarin shiga dakin nake jin muryan ya mamud yana fadin ko an kaisu kotu dawa zaki sharia mami ? Kawai dai ki barsu da Allah tunda har Allah ya fara tona masu asiri tun nan duniya kowa ya gama jin abinda ya faru a gari dama duniya. Kawai ko haka aka barsu ai ya wadatar sai mu kara godewa Allah da har aka gane su a yanzu. Na shiga dakin da sallama sai hjy dasu yayane suka iya amsanin sallama su mami kan basu iya amsa min ba a lokacin. Na gaida hjy tare da mami na juya wurin yaya ina gaidasu ya jafar ke fadin ni abinda yake ban mamaki me nayi mata da har take kiran sunana a zancen ta na hauka. Dama an fada muna haka zai faru ai amma sai ta wani dalilin asirin zai karye daga wata mace kuma don komai da mata ake karya asirin shi ai dama. Sai nayi tunanen wani sabon sheri mami kuma zata dora min don ban karkare sanin maganan da sukeyi din ba a dakin na san dai kan zancen da sadiya ta fada min ne . Yanzu dai kunji abinda daddy sulaiman ya fada ai tana fadi wai itace sanadin hana jafar haihuwa kohin aure ys mamud ya fada. Haba innalillahi wa,inna alaihim raji,un ga magani a jikin mu muna ta faman wahala da abu a jikin mu shekara da shekaru haka. Dolene ma mu tafi kadunan a yau din nan don ayi komai a gaban mu su san muji komai tunda shi Alh Adamun wai baya son mu ji zancen. Dama dazun muna hanya Aisha ta kirani wai Rufaida sai rusan kuka takeyi taki kuma fada masu abinda ya same ta. Ina fa zata fadi wanan abin kunyan garesu hjy ta fada taci gaba da fadin ni ko zamar yar nata a gidan ku ban yarda dashi ba tun farko wallahi. Yanzu ku tashi mu koma gidan kai jafar ka shirya sai mu hadu a airport dakai idan lokaci yayi. Kai ya kada masu yana fadin ba inda zanje mami ku tafi kawai na barta da Allah don yau ni jikina haka na tashi bana jin dadin shi hutu kawai nake son samu a yanzu. Ka zauna din amma mu dole ne mu tafi do ba a san iya sherin da sukai ta bin mutane dashi ba haka tunda ba imani ke gareta ba. Ta yaya mutum zai yi wanan sherin hakan tsawon wanan shekarun kuma hankalin shi kwance ya mamud ya fada. Ka bar mace shu,uma inda ka ganta komai akace wanan matar tayi zata iya don irin yadda akasha fama da ita a baya har saida lokacin iyayye suka shiga tsakanin su hjy ta fada. Mami ta sauke wani ajiyan zuciya tace ni ai jikina ya mutu wallahi sai nake ganin abin kamar a mafalki. Har suka tafi basu daina maganan ba a ranan kuma suka isa kaduna duk da sun so ganin matar amma sai suka samu wai an tafi da ita wurin mai magani. Kafin wani lokaci magana ya zagaye unguwa da gari duka kowa yana fadin albarjacin bakin shi akai. Ya jafar din ne yayi min bayanin abunda ke faruwa a tsanake kafin hjy kuma ta kara ban labarin zaman su da abinda akace din tayiwa mami da jafar din. Nikan abin mamaki ya bani don nasan matan sosai zamana a gidan mami takan shigo lokaci lokaci zance ita din bata damu da zuwa gidan mami din ba sai idan haka ya kama na tazo. Sai dai idan tazo din akwai yin iko gare ta don ban da shakat sai idan ta tafi nake samun sauki. Ranan kan yasha waya daga mutane daban daban da suka shafi yan uwan su na bangaren mahaifin su da tunda nazo gidan ba gane mami bata yadasu ba. Da dare ma zancen daine sukayi da hjy da take fadin ai ka bar mamaki don ba mijin su daya ba take wanan kishin da uwarku. Shi mutum mai hassada haka Allah kan yo shi da halin sa a jini kawai kyashi da hassada ke kamasu har su aikatawa dan uwan su keta. Dama irin wanan kishin yafi zafi a tsakani don daya bata kaunan taga daya ta fita da komai alhalin kuma ba miji daya suke aure ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI BARKAN MU DA YAU BARKAN MU DA GIDA FATAN ALHERI GAREKU A KULLUN, , , Haka abubuwa a kwana nan biyun suka taru sukai muna yawa ga abin daure kai mutum na gani a filin Allah don abinda zai baka mamaki bini bini mami zata kirani wai tana ban labari yadda abin yake faruwa a can kaduna. Yanzu ma din hakane ina zaune misalin sha biyun rana wani kiranta ya shigo min sai naji gabana ya kara faduwa don nasan wani maganan daya dangaci wancan din na uwar Rufaida da ake fama a yanzu. Ina dauka da sallama tana fadin wai zainab kin san matan nan har akanki wai taje gidan boka ai muna asiri in tsane ki da duk wanda ke tare dani. Sai yau dai da mukaje gidan tana ganina ta shiga tono tonon asiri tana hintar kanta tana fadin kinfi karfina iyami kin fi karfina . Sai abin ma yaso ban dariya amma na daure a fili ina fadin wa,iyazu billahi mami me wanan matar take nufine dake ? Mami naga dai duk yadda akeyi kin masu a rayuwa ga yarta kuma a hannun ki kina rikewa tsakanina da Allah. Mami din tace to ai zainab baki sani ba wai ashe ko zaman Rufaida din wurina wai ashe da dalili sun shirya hakane don ita Rufaida din ta auri daya daga cikin diyan dakina. Wai ashe kuma jafar dinki take so shine suke faman neman asiri da zasu samu kan jafar dani da kuma karya wanan asirin da yanzu ya kare take wanan fallasan haka. Na nisa tare da fadin O ikon Allah ita kuma kalan nata rayuwan ke nan mami, ba zata iya dogara ga Allah yayi mata mafita ba na rayuwa sai ta danganta rayuwan ta da gidan boka da malamai ? Su saba ne da hakan tun farko ni kingani na ban taba yarda da irin wanan halin bin malamai da bokaye ba a rayuwana. Komai yazo nakan saka hannu bibiyu in rungume shi in fadawa Allah damuwa akan lamari injira sauki daga gare shi. Allah yasa mufi karfin zuciyan mu na fada tace to amin kedai zainab aisu masu wanan irin halin zakiga kullun a cikin talauci suke. Saboda hassada da bakin ciki suka sakawa zuciyan su da haka mukai sallama da ita wanda nasa ko zuwa dare zata kara kirana a kan zancen. Ina kashe wayan nake fadin a fili Allah mai iko yau nice da mami haka muke hiran arziki a tsakanin mu. Dama hakkurine da wuya duk abinda kaji ana fadin kayi hakkuri a kansa har ka iyayidin insha Allahu hakkurin ka baya zama banza. Yau da banbi maganan magabata na da shawaran manyan dake tare dani da ban kaiga cin ma hakan ba a rayuwana. Shine ya shigo dakin yayi tsaye tare da tsura min ido kafin yace dawa kikw magana hakane tun dazun nake jin ki. Dan dago kai nayi tare da saurin mayar da kaina kasa don yanzu tun faruwan wanan abin a tsakanin mu bana iya hada ido dashi sosai a yanzu din. Mami ce ta kirani take ban labarin mamab su Rufaida na bashi amsa kai tsaye kafin inji yace kai mami tasaka zancen matan a ranta sosai. Ni na riga na barta ga Allah ga duk abinda tayi min nasan dai ban taba cuta mata ba a rayuwa tunda nake ta iya min wanan mugun sihirin haka. Ni yaushe ne matar nan zata bar gidan nan wai ya tambaya na gane fadila yake nufi don haka nace dashi ina ga rokon ta danayine yasa ta janye tafiyan har lokacin tafiyan mu. Kina ganin hakan bata sabawa dokan aikin su ba ya tambayeni yana kallona nace bana jin hakan don da zai saba din ba zata yarda ta tsaya ba ai. Kafada ya daga tare da fadin ok a fili idan dai ta tashi ga wanan ki bata ya miko min key da envelope sabo na karba tare da masa godiya kamar nice akaba kyautan . Ko ban san komai ba nasan wanan makulin motane ya bata ya juya yana fadin ida ta tashi sai ta tambayi Hadi driver zai nuna mata motar ta dauka. Na kara mashi godiya ya fita daga dakin sai abin ya ban mamaki kwarai da gaske don ban taba tsamanin zaiwa fadila irin wanan kyautan ba haka. Dakin ta na nufa kai tsaye bata cikin dakin yasa na fito na shiga surun sadiya a can na samesu zaune suna kallo nace ashe kina nan yanzun daga wurin ki nake tafe ai baki dakin. Tace ina nan tare da mutumiyar muna kallo sakon ta dake hannu na na mika mata ta kalla a cikin maki kafin ta karba daga hannuna. Yayan mu yace a baki idan zaki tafi naga ya dace in baki tun yanzu don ki sani ta bude baki cikin mamaki sai kuma tace wanan duk nawa ni kadai a take yanayin ta ya sauya. Sauka tayi daga saman gadon sai kawai naga ta zube a kasa tana godiya kai haba anty bani ya kamata kiwa hakan ba ai na fada ina zama. A sanadiyan ki ai na samu duk wanan alherin da ace banyi zaman lafiya da kuma tsakani da Allah daku ba duk wanan alherin ba zan sameshi ba ai. Sadiyace ta katsemu da fadin yaushe zamu tafi gurin su inna anty ta jefo min tambayan nace ina gadai a cikin satin nan ne don baiyi magana akan tafiyan ba har yanzu. Ke nan zakuyi tafiyane kuma nace eh zamu mayar da hjy daga nan mu wuce gida muyi masu sallama. Lalai hakan na da kyau ku koma kafin ku bar kasan nan zaifi amma kuma kune zaku mayar da ita gida ke nan na dauka mamice zata kaita gida ? Mami yanzu haka tana kaduna a can zamu samesu don gaba dayan su suna can kadunan kwana biyu ke nan da tafiyan su. Naji hjy na fada jiya a waya wai mami tayi hakkuri ta bar zancen ga Allah sadiya ta fada ba zata iya kyale zancen ba don ko waye dole hankakin shi ya tashi . Amma tunda Allah ya mata fada a yanzun gaskiyane ta barta da Allah zaifi laifi akai mata ke nan ko fadila ta fada ? Eh to laifin ne nan dai na dan fada masu komai sama sama tayi saurin fadin ummhum nasan da hakan wallahi don inda ta taba zuwa a kanki wani lokaci an fada min hakan . Sai dai abinda bai shafeka ba tunda bashi ya kaini ba a lokacin yasa ban dauki zancen da karfi ba mun dan dade muna hira kafin mu watse a dakin. Duk kwana kin nan yaya bai kara cewa zai nemini ba nima kuma naji dadin hakan da darene mun kwanta yake fadin ya gama shirin tafiyan hjy mu shirya gobe da yamma zamu kaduna daga nan muje anchau muyi sallama dasu. Allah ya kai mu na fada ina gyara kwanciya naji saukan hannun shi yana fadin ban son zuwa kaduna a yanzu don gaba daya garin ya fice min rai. Dan juyowa nayi ina fadin laifin mutum daya zai shafi sauran yan garin itama din da tayi ai Allah ya fitar ma da hakkinku tun a nan duniya ta fara ganin mugun halin ta. Kome mutun zai aikata idan ba alheri bane a rayuwan shi banzane don komai dadewa sai ya tambayi mutum ? Abinda nake tunane ke nan a yanzu na rasa me nayiwa wanan matar har bata sona haka ? Bakai tawa ba da farko ta dauka ta cuci mami ne don da ita take hamaiya bada kai ba. Ajiyan zuciya ya sauke tare da dora hannun shi saman jikina naji gaba na ya fadi lokaci guda duk da tsorin shi da nake yanzu har ya san da hakan. Shine dalilin da ya dan sarara min ya kyale ni a yanzu din amma ni kuma sai nake ganin ai rashin sabawa da zama da mace da bai iya bane yasa bai wani damu da kulani din ba. Ko wanan ranan gaskiya nasha bakar wahala gun yaya don bai tausaya min ba haka ya koma kamar wani zaucace a gareni. Washe gari mun isa kaduna bayan sallah magariba gidan na mami shiru da a yanzu duk sai na ganshi wani iri can kamar bashi ba. Kodan yanzu idona ya bude da ganin ginan zamanine oho abinci mukaci kawai yace wai mu fito mu tafi . Nayi mamakin jin ba a gidan zamu kwana ba ashe abinda ban sani ba shine yana da wani irin keraren gida cikin kaduna ashe haka ma ya mamud shima a yanzu ya bar gidan mami din. Gidane na gani na fada na shiga tsara nayi mamakin hakan sosai danaga gidan lafiya lau komai ba laifi gida ya hadu. Nan ma dai din bai kyakeni ba don mun zuba soyayya a wanan gidan sai dai kawai a kawo muna abinci daga restaurant muci safe da yamma . Ko gidan mami bamu lekawa sai dai su ya jamal dake dan leko mu a ranan mu na ukku a gidan ne da dare muna falo bayan mun gama cin abinci wayan shi yai ringing ya dauka. Naji yana fadin ina gida mana lafiya jin hakan yasa na dan dago ina kallon shi daga inda nake kwance na dan kishin gida saman jikin shi. Banji me akace ba yace ku shigo mana ina kokatin jaye jikina a nasa don jin abinda ya fada din amma kuma sai naji ya rikeni ya hana in tashi din . Ga mamakina Aisha ce suka shigo tare da wani saurayi da ganin shi irin samarin nan ne yan karya diyan masu kudin garin. Mun gaisa dasu idon saurayin yana kaina hakan yasa ya jafar din kara daure fuskan shi sosai yake fadin umm, humm . Kince kina son ganina ne akwai magana fadi abinda zaki fadi ina sauraren ki sai ta dago ido ta kalleni kafin tace dama magana nazo muyi yaya a kan magana na da Hashim gashi nazo maka dashi ku gaisa. Yace waye shi tace kai tsaye shine wanda nake so kuma mami bata yarda ba har yanzu ya kalli yarin yace mami din ta fada maki haka da bakin ta sai tayi shiru. Nan ya fara yiwa guy din tambayoyi yana bashi amsa kafin yace da ita alright zanga mami din muyi magana da ita kafin in tafi. Daga haka ya fita batun su ni kan ba wani maganan kirki ne a tsakanin mu ba tunda na fahinci wani irin daukan kai da take min tun dawowan mu din kasan na kama kaina ga al,amarin ta ga baki daya. Sallama sukai mai suka tafi ya tashi ya rufe gidan ya dawo ya zauna yana fadin ban san meke damun yarinyar nan ba zata kwaso min wanan ta kawo mi shi har gida. Haba dai gidan dan uwanta tazo fa ba wani wuri ba kuma da gani tana son yaro nan sosai yasa tazo wurin ka ka taimaka masu . In ba haka ba ai ya mamud ma yana garin da gurinshi zasu tafi ba wuri ka ba amma kuma ta zabi nan din tazo. Wayan shi ce ke ringing ya dauka saurare ya tsaya yi har na wani lokaci kafin naji yace yanzun nan suka fita nan ita dashi. No ban samu mata fada ba don tana tare da yaro a lokacin ni dai mikewa nayi ya bini da kallo don ranan sadiya tabi ya jalal da yazo zuwa gidan mami wurin hjy saboda idan muna daki da yaya ita kadai ke zama ba abokan hira. Ya gama wayan ya shigo daki ya samu na shiga wanka koda na fito yana tsaye a wurin window kamar mai tunane. Zama nayi bakin mirrow ina shafa mai yazo ya tsaya a bayana yana fadin ana magana kan Aisha kin bata rai. Ba tare dana juyo ba muna facing din juna a cikin mirrow din nace dashi shi sha,anin aure ne yaya ba ai masa haka tunda shi take so har ta kawo shi gareku ai idan ba laifin sai ku bari tayi abinta. Wa zai bari ta auri wana guy din kece yarinya da baki san komai ba wanan da ganin shi tashin waje ne bai koyo komai ba a can sai iskanci . Wani kallo nayi mai da sauri don jin abinda ya fada din yace yes nasan abinda zakice ai ko nayi nawa a lokacin ina kokarin danne hakan a kasata ai. Amma baka zaton auren shi din a dalilin ta zai iya gyaruwa ya bar wanan a kidar ya dawo dai dai ba dai wanan din ba na fada maki ke yarinyce ya wuce ya shige ban daki ya barni zaune ina tunane. Ban san yadda sukayi da mahaifiyar su ba ni dai ranan sai ga Aisha din da gani tasha kuka tun a gida don idonta da yayi ja ga duk wanda ya ganta. Sun dade da dan uwan nata a dakin shi suna magana don ta shigo ni fita nayi muna waya da Nafisa da tace zasu shigo dasu umma. Ta fito ko sallama ban samu ba ta fita tana sharan hawaye su umma suka zo gidan sai hankalina ya dauku garesu na manta da zancen nasu. Ranan a gidan su umma suka wuni tare dani da zasu tafine yayi masu alheri mukai sallama suka tafi. Mun je gida mun samu Asabe na cikin wani hali na rashin lafiya kai tsaye yace a kawota asibiti kaduna wanan kuma ya kara dauke hankalin mu sai dai Asabe din duk da gatan data samu lokaci yayi ba magani a wanan jinyar ta rasu tana saka muna albarka ni dashi har innan mu. Mun kuma koma can gida muka kwana daya na dawo kaduna daga nan muka dawo Abuja . Sai muka fara shirin tafiya sai kuma ga zazzabi har saida na kwanta asibiti don jirgitan danayi ga zazzabin. Hankalin jafar din ya tashi sosai da ciwon nawa sai da mami take ce masa kowa fa haka yakeyi idan an samu juna biyu duk da hakan bai gane me mami din take nufi ba. A karshe dai tana murmushi take fadin nifa naga kamar matar ka na da cikine amma a bari saka makon ya fito a gani. Ciki mami ciki ke ga zainab din sai kuma ya shafo kanshi zuwa fuska yana dan murmushi ya rungumi mami din lokaci guda. Itama mami din dadi taji a lokacin tana dan bubuga bayan shi tare da fadin Alhamdullahi jafar tunda baka halaka ba ga baki daya gashi yanzu har zaka iya haihuwa ashe. Koda na falka suna zaune su uku sun tasani gaba suna kallona dan binsu da kallo nayi na dan lokaci kafin in dan motsa baki ina gaidasun Suka amsa tare da yi min ya jikin nace da sauki ina yun kurin tashi don aman daya tayar dani daga barci a lokacin. Shine yake tambayan ina zan tafi da yaga ina sauka daga gadon da sauri na kaaa magana sai dana ns bude baki wani amai yazo min da sauri na nufi wirin da nake zaton ban dakine a wurin daga gefen dakin. Tin ina amai a duke har na koma yi tsugunne haka yssa shi shiga bayin yana min sannu na fito a galabaice bayan na kurkure bakina da ruwan daya ban. Wasa wasa wanan ciwon saida yasa muka kara kwanaki a kasan don jikina yaki dadi sam ga mutane sai faman zolayata sukeyi da sunan mai ciki da har lokacin ban yarda da hakan bani. A haka muka tatara muka koma Chaina sai dai saboda yanayin jikin nawa yasa yace in nemo wace zamu zauna ko a gidane mu tafi tare. Akwai wata babban yar malam dake gida auren ta ya kare kuma bata taba haihuwa ba gorin kishiya ya fitar da ita gidan miji tana gida zaune da itace zamuyi tafiyan don kanwa take ga innan mu ke nan don haka muke kiranta da mama Ladi. Duk da mami bata so hakan ba a cikin ranta ba wai bata son zuwa da ita din bane don tana bangarena a,a. Saidai a ganin ta matar ba zata iya bani kulawan da ya dace ta bani ba don tana yar kauye har ta kula mata da abinda ke cikin cikina a yanzu. Ba wata dole din da ita muka tafi hakana don na nuna ita nake son muje don yadda nayi zama da mahaifiyar mama ladi din maizube. Ban samu wani wahala ba ga tafiyan don mun isa lafiya sai dai barcin da nayi tayi bayan saukan mu din. Zaman mu da mama ladi ba wani matsala a cikin shi don ina jin dadin zama da ita sosai kuma ina bata girman ta na uwa a gareni haka shima a bangaren shi kamar yadda yaji muna kiranta da mama Ladi hakan yake kiran ta dashi. Yayin da sadiya kan tuni ta koma school din su don tana da permition na barin wurin dan lokaci daya daukan mata. Ban yarda na zauna ba tun da muka dawo duk da laluran dake gareni na ciki din bai hana mai da hankali wurin tsare ibada na ba don samun kariya a wurin Allah. Haka itama mama ladi mace ce mai yawan ibada sosai bata da wasa wurin aiwatar da ibadun ta . Tsorona kada yan wanan kungiyan su kawo muna hari ko su kara jan ra,ayin shi ya koma cikin su tunda yanzu sunga ya barsu kwata kwata bai tare dasu. Don tunda zamu dawo mami tayi min magana akan na taimaka na mayar da hankali akan shi sosai don Allah don ita da son samune ma ba zamu koma wani kasa ba a nan gida zamu zauna tare dasu. Wanan na rike a zuciyana ina kallon duk wani shige da ficen shi a yanzu din bana yarda in yi nisa dashi ko a dauki lokaci banji inda yake ba. Sai hakan kuma ya kara jawo muna shakuwa sosai dashi don ko ban kirashi ba shi zai daga waya ya kirani yaji lafiyan mu. Har mama Ladi na fadin don lura da tayi dashi idan ya dawo aiki sai yazo inda nake ya rungumeni a jikin shi ya dan zauna tare dani na dan lokaci. Take fadin wai irin wanan zaman namu ba na malam bahaushe bane da iyakarshi da mace sai idan dare yayi yana da bukatan ta. Nayi dariya ina fadin mama aiko a hauwan na da can baya ke irun wanan dabi,an na yanzu kan sun waye suna abinda ya kamata suyi na kulawa da iyalin su. A kwana a tashi har cikina ya isa haihuwa a lokacin mami wayan ta ko yaushe kiran mu takeyi taji halin da nake ciki. Har dai Allah ubangiji ya saukeni lafiya na haifi da na miji mai kama da ubanin shi sak don bai raga su da komai ba har tsayin su da irin yanayin yayan mami duk ya kwaso su sak. Basu wani tsayar dani ba a asibitin don ina da lafiyana na dawo gida duk abinda kakan maya ta bani da an haihu na fadawa mama ladi komai tunda na karbo maganin. Don haka batayi wasa wirun bashi maganin ba tun a asibiti tayi dubaran dura mashi ya fara sha yana bata fuska. Sai dai abinda ya dan sa jikina sanyi shine yanayin yaya jafar din game da haihuwan nawa dana zata zai nuna farun cikin shi sosai ga hakan. Sai banga hakan ba ga fuskan shi sam kamar yanayin shi yana a cikin damuwa a ranan ya dan dade tsaye a kan yaron yana kallon shi kafin ya juya ya fita ya bar dakin. Na bishi da kallo haka har muka dawo gida sai ya zauna yayi shiru shi kadai kamar mai tunane ganin hakan da nayi ne yasa na fahinci akwai wani abu a kasa wanda ni din ban sani ba. Wanka na fito mama da Sadiya suna zaune dashi ta gama shirya shi na dan kalleta nace mama zaki iyayiwa yaron nan hayakin nan da malam ya bamu da sauran maganin shi duk a dura mai koda kadan ne ki kuma shafa mai su. Tace mai zai hana yanzu kuwa hakan tabi ko ina da hayakin bayan ta gama masa komai yadda ya dace naga kuma ta daga shi tana addua har muna iya jin abinda take karanto mashi a lokacin. Mun kwanta lafiya Allah kuma ya tashemu lafiya tunda asuba naji ana buga muna kofa na fito daga wanka ke nan kamar yadda mama ta umurceni da yi. Muka kalli juna da mama Ladi din kafin ta nufi kofan ta bude kai mama Ladi ta san kanta sosai a wurin addini gaskiya don zuwan ta ba karamin rana yayi min ba. Shine tsaye a kofan idon shi a kan mu yake fadin lafiya dai kuka kwana ko yake tambaya ba tare da ya amsa mata gaisuwan da take mashi ba. Lafiya kalau gashi har tayi wanka shi kuma dan yanzu nake batun in masa yana da rai ko ya fada . Ban san lokacin dana dan sake man dana dauko zan shafawa jikina ba a lokacin na nufi wurin gadon da yaron ke barci shida sadiya hankalin su kwance a lokacin. Hannuna nakai a daidai saitin kirjin yaron kafin na mayar zuwa hancin shi naji numfashin shi yana sauka lafiya. Na dago ina kallon shi daga inda yake tsaye ya tsura min ido nace dashi me hakan ke nufi ban gane wanan tambayan da kai min ba yanzu ? Nima ban sani ba ya fada yana barin dakin zaune nakai dabas na kalli mama Ladi da itama mamaki ya kashe ta a wurin ta kasa magana a lokacin. Kada ki dauki wanan wani abu wata kila dai mafalki yayi daku ya razana ai kinga kamar a firgice yake koda ya shigo dakin . Na bude baki da kyat ina fadin mama kashe yaron nan zasuyi don tun jiya a asibiti naga hankalin shi a tashe sosai daya tambaya akace namijine na haifa. Wanan sai Allah ya isa ya kashe bawan sa zainab kada ki sa hakan a ranki har kikai ga yin sabo tunda zargi kike masa yanzu. Har in ma akwai wani kulli tattare da yaron nan Allah yafi mai shi da sherin shi duka don mu da ayan Allah muka dogara bama tsafi bama tsubo. Duk wanan zancen na mama hankali bai kwanta ba mikewa daga inda nake zaune a gurguje na shirya na fita daga dakin zuwa wuri shi. Na sameshi yana sintiri a dakin yana rike da casbaha a hannun shi daga shi dogon jallabiya a jikin shi lokacin. Jin motsina yasa ya dan juyo yana kallo na har na karaso inda yake tsaye din har yanzu yana numfashin normal ya kara tambayana. Nace eh sai dai ban gane dalilun wanan tambayan dakake tayi kan yaron nan ba tun dazun na tambaye shi. Bai ban amsa ba illa juyawan da yayi zuwa bakin gadon shi ya zauna na bishi da kallo kafin in iya daga kafa zuwa wirun shi din naja na tsaya. Don gaba daya na fita hayacina tunda na fahinci akwai matsala kan yaron nan dan mala,ikin Allah dako nonon uwa bai fara iya jaba sai ma da darene kafin mu kwanta mama ta matsa a fara koya mashi jan nonon da taimakon ta ya dan fara kamawa bawai ya iya jan ba. Ko ka bada jinin shi ne dama ka barmu a cikin duhu na tambaye shi a cikin wani irin kakausan murya dake nuna ba tsoro a zuciyana lokacin. Sai lokaci ya dago kai ya kalleni idanuwan shine suka kada sukai wani irin ja dasu lokaci guda yace nasan ba zasu barshi ba zainab . What na fada a razane kagin in koma fadin innalillahi wa,inna alaihi raju,un nakai zaune kafin in fashe da wani irin kuka lokaci guda . Hannun shi naji a jikina yana kokarin rikeni zuwa jikin shi nayi maza na jaye ina fadin kada ka tabani mugu azzalumi kawai. Nayi nadaman sanin ka a yau din nan yaya da wanan rayuwan bakin cikin zan dinga riska a tare dakai na kwamace Allah ya kasheni kafin in girma har in sanka. Wani kallo yai min da jajayen idanun nasa yace cikin karfin hali zainab ni kike kira yau da azzalumi haka a gabana. Nace idan ba azazlumi kake ba me kake jafar jin na kira sunan shi kai tsaye haka a karo na farko yasa ya danyi min wani irin kallo kafin yace dani. Ban zata a yanzu zaki min wanan judgen din ba ke da kanki bayan kin fi kowa sanin tubana da nadamana na gaskiya shi har ga Allah. Akan me zan shede ka bayan ga abinda ka fada a yanzu kuma tun jiya din naga alaman damuwa a tare dakai don bakayi farin ciki da haihuwan yaron nan ba. Fine naji kin gani din kuma kin gane amma ya kamata ki saurareni tunda har kinga damuwa a gareni. Ni nasan ka,idan sune har idan mutum ya kubuta daga garesu zukaga da gaskiya ya barsu din sai sun dauki fansan akan abinda ya haifa idan namiji ya fara haihuwa a duniya. Cikinane yabada wani irin sauti kulululu, , , lokaci guda numfashina naji kamar zai tsaya a lokacin kafin naji yana fadin saidai nayi mamakin ganin basu taba yaron nan ba har ya kwana yana numfashi. Akwai abu dayan biyu zuwa uku walau addu,an mune dana yan uwa Allah ya karba . Walau kuma addau,an ya hade da tsarin da kikai muna amfani dashi don gaba daya basa son zuwa wurina don sun daina bibiyata sam a yanzu. Kokuma yaron nan ya soma cin abinci ko kafin suzo gareshi yaci wani abu ko yasha nonon ki shine dalili zainab ba wani abuba don haka ki daina zargina da hakan. Allah yafisu jini dana dana yafi karfin tsafi ko wani abu don ina tare da Allah da ayar Allah a tare dani. Dana ya sha zamzam da dabino haka kuma yasha nonona tun daren jiya din ba zasu iya min komai da yarda ubangijin mu Allah. Ba zasu iya ba har abada na sani don da zasu iya din da sunyi suma sun fada kuma sun barmu din sai dai tsoron wanan nakeyi dama akan su. Nasan da diya mace ce basu ko kallon ta yarinyar ta tsira ke nan shi yasa ake son bawa idan zai tuba ga sabon da yaiwa Allah yayita har kasan zuciyar shi. Kuma tsakani da Allah ya tsarkake zuciyar da mu,amulan shi ga kowa sai Allah ya tsaya mashi ga duk al,amuran shi . Na gane hakan a yanzu da kuma wani samir da hakan ya faru dashi don a yanzu yaran shi biyar komai sun kasa yi dashi da iyalin shi. Haka nima na tsira ke nan zainab tunda har yaron nan a yanzu shima ya gagaresu tabawa ke nan har abada dashi da duk wani dan da zan haifa a bayan wanan din. Jin hakan yasa na dan tsagaita kukana ina fadin dama Allah ya fada duk wanda ya barshi yabar imanin shi da kariyan shi daga abin ki. Sabon Allah baida wani fa,ida sai tarin nadama a karshe da wahala da mutun zai dinga gani a rayuwan shi. Yace wanan haka yake zainab tashi muje na kara ganin yaron nan in masa addua don ya tsira ya kuma tseratar damu daga wanan bala,in nasu har abada insha Allahu. Jikinane yayi sanyi lokaci guda na kasa motsawa daga inda nake zaune din hannu ya kai ya mikar dani daga aurin muka fice daga dakin. Tun kan mu karasa dakin muke jiyo kukan yaron muka isa da sauri yana hannun mama Ladi tayi masa wanka tana masa gashi nayi mamakin hakan ashe da abin gashinta tazo irin namu na gargajiya na gida . Ya dade tsaye yana kallon yadda mamadin kewa yaron kafin ya fice cikin walwala da annuri a fuskan shi. Gado nabi na lafe ina sauke ajiyan zuciya a hankali tare dayiwa Allah godiya bisa kariyan da yake bamu a kullun nayi ta tasbihi har barci ya daukeni ban sani ba. Sai can na tashi a dan firgice ina kallon inda yaron yake goye a bayan mama ganin na motsane mamake fadin ki tashi kici abinci ba a son cikin mai haihuwa da yunwa ko kadan . Hamdala nayi namike na tashi na shiga ban daki sai da darene nake fadawa mama komai daya faru sai bayan ta gama mamakin hakane tace insha Allahu Allah ya fisu yafi karfin tsafin su kuma. Yan gida sun kiramu gwargwado sun muna barka mami ta nace akan sai yan suna sunzo anyi suna a nan chaina. Dole ya yarda din suzo ciki masu zuwa aka bawa bangarena mutum biyu mami kuma ta kafe dole da inna a cikin masu zuwa din . Don tazo taga inda nake zaune da badon hakan ba inna ba zata taba sanin inda mu biyu diyan ta muke rayuwa ba. Sai ta wanan dalilim suka zo tare da Nafisa kawata daga kaduna suka zo da ita sai bangaren su ya jafar din suma mutum uku sun zama su biyar sukazo muna sunan. Satin su biyu a wurun mu suka juyo suka dawo yaro yaci sunan mahaifin su jafar din Isma,il suna kiran shi da Anur. Farin cikin inna nan baya musaltuwa don bata iya boye hakan ba saida muka kebe ne nake fada mata komai daya faru dani a rayuwan aure tunga farko har karshe kodana kai karshe inna na hawaye . Tace Lalai zainab ABU CIKIN DUHU SIRINE yanzu kabar mutum a yadda ka ganshi kada ka tona cikin sa zakaga abinda baka zata ba idan ka tona din. Musanman wa yan nan masu kudin na zamani da zakaga mutum yayi arziki a cikin dan kankanin lokaci ba a san inda ya samu arzikin shi ba. A haka kuma zaka ga mutane na shige masa don kawai su samu abin duniya a hannun shi Allah ne sheda ban yarda kin zauna da bawan Allahn nan don nasan yana da abin duniya haka ba. A,a Allah ne shedan zuciyana ya kuma ga manufata a hakan na baki hakkuri don halarcin mahaifiyan shi a garemu. Nafisa ta amsa da fadin haba mama ta yaya zaka san irin haka har ka dauki danka ka kai wanan wurin koda kana da yaya da yawa ai akwai tausayin rai ko ? Don ma shi jafar yana da imani da tausayi da halin halarci a zuciyan shi yasa abubuwan suka zo mai da sauki haka. Sun tafi sun barmu da kewan su ina shayar da dana da yayi wayau ya girma har lokacin ban daina bunshi da addua ba da neman taimako munayin shi gaba dayan mu gidan. Ban mantawa mun fita da ANNUR da baban shi lokacin ina da karamin ciki a jikina ciki na biyu muka hadu da philis a wani mahada. Yana ganin nin mu saida ya kadu na shedashi bayi saurin fadin A,uzubillahi mina shetanin rajin . La,ilaha illa anta subuhanaka inni kuntu minal zalumin sai ji mukayi daram yayi hatsari nayi mamakin yadda ya jafar bai nuna yasan shi ba a wurin . Muka tafi muka barshi a cikin wani hali mutane sun taru a kanshi har muka dawo ina mamakin hakan a zuciyana daga baya nake jin wai ashe daga hadarun nan bai kara tashi ba har ya mutu a hakana karfin ayan Allah ya hau kanshi na fada a zuciyana. I zuwa yanzun da nake baki labarin nan haihuwana ukku duka maza muna kuma lafiya na kara karatu yaya yai min hanya an daukeni aiki a wani babban company a nan chaina ina aiki. Bukin kanwata sa,adatu yazo lokaci daya dana Aisha da Na,ima shine zuwan mu Nigeria da yara na uku lokacin don koda hjy ta rasu kakar su jafar bamu samu zuwa ba a lokacin ina da cikin dana na biyu. Tunda Nuriya ta kyala udo ta gammu ta kasa biye kishin ta ga hakan don duk yaran data haifa matane bayan dan ta na farko. Har yakai ta kasa boye hakan a zuciyan ta sai da ya kai har mamu tayi mata kashedi kan hakan kada tarihi yazo ya maimaita kan shi . Ayin buki lafiya nasu Aisha aka farayi kafin na kanwata sa,adatu mun shiga mun fita nida kawata Nafisa da baka gane kawance ne kawai a tsakanin mu don mun zama yan uwa itama tayi auren ta a jos har da yara biyu. Nan nazama abin kallo ga mutane wanda baisan irin rayuwan dana sha a baya ba yana min kallon na more miji. Ni kuma ina masu kallon basu san ABU A CIKIN DUHU SIRI BANE. Alhamdullahi godiya ga Allah ma daukakakin sarki daya bamu rai da lafiyan kai karshen labarin mrs jafar lafiya nima mai rubutawan ina rokon duk wanda na sabawa a dalilin wanan labarin ya yafe min don Allah . Tsokaci gareku iyayye don Allah a dunga kula da irin mutanen da ku kanku iyayye kuke zama dasu don wani ba da zuciya daya yake zaune dakai ba a wanan zamanin. Haka a dage wurin yiwa zuria addua ko wani lokaci muna cikin wani zamani mai kama da rashin imani yanzu ya kaura a zukatan bayin Allah. Haka yan mata a daina ruwan ido aga mai kudi ba bincike a fada mai sai anje gida aga abinda bashi bane a gidan . Ubangiji Allah ya tsare ya kare dukkan musulmi daga fadawa ko wace irin fitin nan wanan zamanin Amin taku ZAINAB IDRIS MAKAWA SAI MUN HADU A SABON NOVEL MAI SUNAN( ANA DARA)