[9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: *_K'ANWAR MATATA_*🦜 _Matar Sayyadee_ _Wattpad @Matar_Sayyadee_ _K'anwar Matata ba kirkirarren labari bane! Sai da na samu yarda da aminta sannan na soma rubuta shi. Dan haka idan yayi shige da naki irin labarin, arashi aka samu. Sannan ina gargad'i da babbar murya, ban yarda a juya min labari ta ko wani siga ba, ba tare da izini na ba ko kuma a d'aura min a YouTube!_ _K'anwar matata isn't free wooo! Na fad'i tun wuri saboda kar ki soma karatu kiji free pages sun k'are ki soma k'orafi baki san cewa na kud'i bane tun farko. Naira d'arin ki biyar ya ishe ki samun karanta labarin daga farkonsa har k'arshe. Wannan karon babu please matar Sayyadee dan Allah ki saka ni a paid group I'll pay later yanzu bani da kud'i ne. Matar Sayyadee baza ta tab'a saka ki a group ba sai kin yi payment. Ehe, pay before service!_ Page 1 Kuka take yi sosai a gaban doctor d'in tana fad'in, "Na rantse da girman Allah doctor ban tab'a yin sex ba a rayuwa ta! Ban san ta yanda aka yi wannan ciki ya shiga ba. Sai dai idan ture aka yi min." Shuru doctor Kamal yayi yana kallonta irin kallon ta raina masa hankalin nan. Daga shigar jikinta gaba d'aya ya fahimci ita d'in ba mai kamun kai bace. Wando ne pencil a jikinta sai monkey jacket d'in da ta daura a kai. Kanta kuwa wani uban kitson attachment ne wanda aka yi mata shuku _Ghana weaving_ dashi kalar maroon da bak'i. Gaba d'ayanta bata yi kalar mutunci ba. Hatta k'umbar hannunta artificial ne irin zaro-zaro d'in nan. Gashin idanunta ma artificial d'in ne suma zaro-zaro dasu. Kallon results d'in dake hannunsa yayi wanda ya nuna masa 2weeks pregnancy a jiki sannan ya kuma d'agowa ya kalleta tare da mik'a mata yana fad'in, "Scanning machine ba zai tab'a maki k'arya ba! Sau uku kenan ina tura ki kina yin scanning, na k'arshen nan ma da kai na naje nay maki saboda confirmation. Amma still the results is same. Dan haka, ya rage a gare ki da ki koma kiyi tunani da kyau a inda kika samo cikin jikin ki. Lot's of patient are waiting outside. I'm done with you!" Fad'in doctor Kamal yana nuna mata hanyar waje. Don tuntuni yake ta danne fushinsa. Ya tsani yaga mace mara kamun kai a rayuwarsa. Wani irin kuka ta kuma fashewa dashi tare da fad'in, "Please doct...." Bata kai ga k'arisa maganar ba ya nuna mata k'ofa a fusace tare da fad'i, "Out of my sight right now before I call security to throw you out. Y'an iska yara k'anana daku sai biye-biyen maza saboda abun duniya. Sai bayan sun d'ura maku ciki sai kuzo kuna mana kuka wai baku san ta yanda akai kuka yi cikin ba saboda kun raina mana hankali. Idan kuma aka sakar maku fuska sai ku fara rok'o akan a zubar maku da cikin. Dama Allah ya rik'a d'aukar rayuwar ku lokacin da ake k'ok'arin cire maku cikin. Y'an iska kawai!" Doctor Kamal ya fad'i. Ita kuwa tun lokacin da ya buga tsawa na farko tayi saurin d'aukar handbag d'inta da paper d'in da ya turo mata ta fita da sauri gabanta na fad'uwa don ta tsorata sosai da yanayin doctorn. Fita tayi daga asibitin gaba d'aya. Sai da tayi nisa da asibiti sannan ta nai mi wani waje gindin bishiya ta zauna tana kuka sosai. Wata mota ce tazo ta wuce ta gabatar da gudu, can kuma motar ta dawo da baya da baya har inda take. Sauke glass mai motar yayi tare da fad'in, "Sssss, hi babe! Wani irin d'agowa tayi tare da watsa masa harara sannan ta mai da kanta tsakankani cinyoyinta tana kuka. Mai motar kuwa yaja motarsa ya bar wajen ya bar mata k'ura. Tashi tayi ta soma tafiya a hankali dai-dai lokacin da aka yi wani irin tsawa alamar hadari ya had'u sosai. Da sauri ta kalli sama taga gab ake da a tsuge da ruwan sama. Bata damu ba ta cigaba da tafiya. Ko taku biyar bata yi ba aka tsuge da tuwan kamar da bakin kwarya. Bata fake ba ta cigaba da tafiya a k'afa, don ji take dukan ruwan kamar shi zai yaye mata halin da take ciki. Sai da taga bata iya ganin gabanta da kyau sannan ta samu wani d'an rumfa da few mutane ke tsaye a wajen wanda kusan gaba d'ayan su y'an achab'a ne da passengers. Ruwan nan ya kai tsayin awa guda kamun ya sassauta saboda lokacin gab da magriba ne. Yayyafi ake yi irin wanda zai iya jik'e jikin mutum jagab. A hakan ta kuma shiga ruwan ta dunga tattakawa. Duk da irin nisan da gidansu ke dashi haka ta tako a k'afa tun daga wani k'aramin private hospital dake fire brigade dake tudun nupawa har Jos road by Abeokuta Street. A wannan lokacin har d'iga take yi tun daga tsakiyar kanta har cikin pant d'inta. Ko da ta tura k'ofar gidan su ta shigo, babu kowa a tsakar gidan as she expected, sai tayi saurin shiga d'akinsu. Kwance ta taras da Na'ima a kan gado tayi d'ai-d'ai tana waya sai mulmula take yi from edge to edge d'in gado. Kallo d'aya tayi mata ta d'auke kai tare ajiye handbag d'inta a kan side drawer sannan ta soma cire boyfriend jacket d'in jikinta ta ajiye a gefe ta zame dogon jeans d'in jikinta ta kasance daga ita sai pant sannan ta nufi wajen wardrobe ta d'auki zani ta d'aura a k'ugu sannan ta zame pant d'in jikinta ta cire tare da unbuttoning shirt d'in jikinta ta cire har da bra sai ta ja janin sama. Zare ribbon d'in kanta tayi ta had'a da jik'ak'k'un kayan da ta cire ta saka a wani bokiti yellow mai tambarin Maggi Star da ba ruwa a ciki sannan ta dauki towel wanda ke hannun wardrobe ta rufe kanta tare da d'aukar butanta da babu mai tab'awa a cikin gidan ta fita ta nufi bayin su dake tsakar gida tayi fitsari ta kama ruwa ta fito daga bayin ta d'aura alwala sannan ta koma d'akin. Wardrobe d'in ta bud'e ta d'auki doguwar riga jallabiya ta saka. Towel d'in da ta fita dashi kuma, ta yi amfani dashi ta goge jik'ak'k'an attachment d'in kanta sannan ta dauki hijjab ta saka tare da shimfid'a darduma ta tada sallar magriba. Har ta idar da sallah Na'ima bata gama waya ba, kuma babu abunda take fad'i sai dirty talks ita da wanda take wayar dashi. Juyawa tayi ta kalleta for 3seconds sannan ta cire idanunta ta mayar kan kwan fitilar da ya kawo haske a d'akin alamar an kawo wutan lantarki. Mik'ewa tayi ta nannad'e dardumar ta mayar inda yake sannan ta cire hijjab d'in jikinta ta ninke ta ajiye sannan ta dauki kettle ta cika ruwa a ciki ta jona. Tana jonawa ana d'auke wuta kamun kuma tayi wani yunk'uri suka sake dawo da nepar. Hamdala tayi a cikin zuciyarta sannan ta bar wajen ta dawo kan kujera one sitter dake d'akin guda d'aya tal ta zauna tare da had'a kai da guiwa tana tunanin ta ina ciki ya shiga jikinta ba tare da d'a namiji yayi penetrating a jikinta ba. Wasu hawaye masu zafi suka shiga gudu a kuncinta. "What I'm doing to tell him now? Our marriage is in 4weeks now. Kuma nayi masa rantsuwar ban tab'a sanin wani d'a namiji ba a rayuwata. Sai kuma ga ciki yanzu! Ta ina zan fara yi masa wannan bayanin ya yarda dani. I'm dead! Shikenan wannan ma zai gudu kamar sauran. Nima bazan tab'a aure ba kamar sauran y'an uwa na. Na shiga uku na!!" Ta fad'i a cikin zuciyarta tana hawaye daidai lokacin da ta soma jin wani shuuuuu alamar ruwan da ta saka a kettle ya soma tafasa. Cikin sauri ta isa wajen ta kashe socket d'in sannan ta zare igiyar kettle d'in tare da d'aukar kettle d'in ta juye ruwan zafin a cikin wani bokiti ta fita ta nufi wajen pampo ta kunna ruwa. Kasancewar ruwan na zuba da uban gudu, sai take yi tana saka hannunta domin jin yanayin zafin ruwan. Kashe pampo d'in tayi bayan yanayin zafin ruwan yayi mata ta d'auki bokitin ta kai ruwan bayi sannan ta dawo d'akin ta d'auki soso da sabulun wankanta ta fita, kuma har lokacin yayarta Na'ima bata gama wayar da take yi da saurayinta ba. Bayan kamar 15mins ta fito daga bayin dai-dai lokacin da mahaifiyar su Lami ta fito daga nata d'akin tana fad'in, "Sarah, ashe kin dawo cikin gidan nan shine baza ki iya zuwa d'aki ki fad'a mi kin dawo ba saboda bak'ar mugunta irin naki! Duk saboda kar ki sammun abunda kika samo ko? Dad'in abun ba ke kad'ai na haifa ba" Turo baki Sarah tayi tare da fad'in, "Ni fa Lami asibiti naje ba wani waje ba. Allah ya kiyaye inyi yawon banza." Rik'e baki Lamin tayi tare da fad'in, "Iyeeh! Za kici ubanki ne shegiya asararriyar yarinya. Da kyawun ki zaki je ki lalata kanki. Uban wa kika ga yayi aure a cikin yayyinki su hud'u gasu nan kina gani? Kuma a cikinsu babu wacce bata kawo abun arziki cikin gidan nan. Ku shidda mata Allah ya kashe ya bani domin ya wanke min bak'in cikin da mahaifin ku ya saka min a zuciya shekara da shekaru. Amma babu wulak'antacciya mara mutunci da rashin son cigabar uwarta sai ke Saratu! Kai Allah yayi wadaran naka ya lalace. Kin nane a jikin namiji guda d'aya, d'an iska yaron da ba wani abun arziki gare shi ba. Kin kafa k'ahon zuk'a shi kike so sai kin aure shi, to don ubanki shine ajalinki da y'an k'ananun shekarunki. Yaro d'an iska sai fankama shi ba uban kowa ba. Zan ga yanda za'ayi auren nan wallahi. Zaki ci uban ki! Dani kike zancen." Da kallo Sarah ta bita har ta shige d'akin da shine mallakin mahaifin su a gidan. Ta jima tsaye da bokiti a hannu sanyi na busata kamun ta ja k'afafunta da suka yi mata sanyi ta shige d'akin su. Turus ta tsaya lokacin da ta d'aga labule tana kallon Na'ima wacce ke rik'e da takardar result d'in dake nuna Sarah wanda ke nuni da tana d'auke da juna biyu. Cikin sauri Sarah ta fad'a d'akin tare da warce takardar a hannunta tana mai hararar Na'ima. Na'imar ma hararan take maka mata tare da fad'in, "Munafuka annamimiya! To yau asirin ki ya tonu. Ashe kema shek'e ayar ki kike yi a wajen, amma idan kin shigo gida sai ki rik'a nuna kamar ke ta Allah ce. To yau dai asirin ki ya tonu. Kuma wallahi sai na fad'awa Lami." Tana fad'in haka tayi saurin sauka daga kan gadon ta bangaje Sarah ta fice daga d'akin tana kwala kiran sunan Lamin. Da sauri Lami ta fito daga d'akin mijin nata tare da fad'in, "Lafiya haka Na'ima kike kwala min kira? Ko wani abun alkhairin ne ya same mu" fad'in Lamin dai-dai lokacin da Nuratu, Hassana da Marfu'a suka fito suma suna tamabayar lafiya. Na'ima kuwa wani shewa tayi tare da nuna k'ofar d'akin su inda Sarah ke ciki tana mai fad'in, "Yau dai anyi walk'iya a cikin gidan nan. Mai mana gori da mun aje y'ay'an shegu ita ma tana gab da ajiye maki shegen jika." Ta k'arisa maganar tana mai kallon Lami da ta saki baki tana kallonta. "Ke ban fahimta ba, fitar damu cikin duhu dan Allah Na'ima." Fad'in Nuratu. Sai da Na'imar tayi wani shegen gud'a sannan tayi nuni ta baya izuwa ga d'akin su tace, "Ustaziyar gidan nan dai ciki ne da ita. Dama kwana biyun nan kullum sai inga tana ta kuka, idan ta tambayeta mai ke damunta, sai tace min babu komai. To yau dai bayan ta fita zuwa bayi domin wanka, sai na bud'e jakarta don in d'auki turarenta in fesa saboda Ajeeb ya kira ni yana k'ofar gida, kawai sai ganin takarda nayi a ciki, shine na fiddo na bud'e, nan kuwa nayi arba da ciki har na sati biyu a jikin takardan. "Gaba d'aya wani irin shewa suka d'auka dashi har da tafawa. Nuratu tace, "Zancen gori ya k'are a cikin gidan na. Wallahi Lami yarinyar ta k'ara min rashin kunya ko kuma ta dukan mu y'ay'ana a cikin gidan nan sai naci uwarta yasin. Shegiya y'ar iskan yarinyar mai mugun hali. Dama fa ni Lami tuntuni na gane Sarah tana biye-biyen maza a waje. Abunda ya saka take nuna mana kamar bata yi, duk dan saboda kar ta kawo wani abu cikin gidan nan ne a amfana da ita saboda bak'ar rowarta da mugun hali. To yanzu dai anyi walk'iya. Wallahi duk abunda kike fita kina samowa sai kin fito dashi kowa yaci a gidan na. Tun da muma duk abunda muka samo dake ake cinsa. Ehe! "Sai a lokacin Lami tayi magana, "Lallai yau naga abunda ya girmi kakana! Dama haka halinki yake Sarah? Lallai! Dama ance makashin ka na tare da kai. Wai ni yau y'ar da na haifa da ciki na ce take kyamatar bani abunda take fita tana samowa. To Wallahi fitowa za kiyi fi fad'a min uban da yayi maki ciki, don billahil lazi bazan kyale sa ba, list zan yi masa na abubuwan da zai kawo cikin gidan nan. Don ba zai yuwu in ciyar da ku y'ay'ana ba, kuma sannan in ciyar da y'ay'an ku ba. Ko su y'an uwanki da kika ga ina d'awainiya da y'ay'ansu, biyana suke yi su da samarin nasu. Ki fito don ubanki Nuhu kamun nazo d'akin nan na idda ke!" _Ya kuka ji labarin?_ https://chat.whatsapp.com/J22NLS9qVTz0L9CatOjFr7 [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: _K'ANWAR MATATA_*🦜 _Matar Sayyadee_ _Wattpad @Matar_Sayyadee_ ☀️ *ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*☀️ Page 2 Sarah dake matsar hawaye zaune a bakin gado ta mik'e ta fito ta tsaya nan daga bakin k'ofa ba tare da ta kalli inda su Lamin suke ba. Sama kawai ta zubawa idanu tana kallon hadarin da ke k'ara had'uwa. "Oh ni inzo nan ke nan in same ki ko, shafaffa da mai!" Fad'in Lami a fusace kamar zata yo kanta. A hankali Sarah ta sauko daga kan dandamalin k'ofar d'akin ta nufi inda su Lamin suke tana kallon k'asa. "Munafuka annamimiya, makira! Sai ki rik'a yi sumumi-sumumi kamar ta kirki, ashe a bayan fage Allah kad'ai ya san abubuwan da kike shukawa. Ya kiyi magana ko sai na hamb'are ki a nan wajen?" Lami ta fad'i tana mai kai mata duka Sarah tayi saurin kaucewa. "Lami wannan yarinyar fa ba magana za tayi ba sai ki had'a mata da duka. Kin fi kowa sanin irin taurin kai da kafiyarta tun tana k'ank'anuwarta. Ke kika bamu labari idan tayi zuciya ko nono kika bata bata karb'a, idan kuma kika matsa mata ta kama, to ranar kan nonon ki kamar zai tsinke tsabar cizon da take ganna maki. Ai wannan yarinyar jaraba ce a gidan nan. Ita ta d'ebo halin tsoho kaf!" Fad'in Hassana tana hararar Sarah. Sarah kuwa wani d'agowa tayi ta watsa mata harara tare da fad'in, "Idan ni annoba ce, ke kuma wulak'antacciya tsinanniya mai zagin uban da yayi sanadiyar zuwan ki duniya! Na gwammaci inyi ta d'ebo hali da dabi'un mahaifina har k'arshen rayuwata da in d'auki irin naku halin. Ko kunya bakya ji, babu aure amma kin ajiye y'ay'a uku duk shegu. Kuma a hake kike fita kina yawo kowa ba kallon ki yana nuna ki a unguwa. Ku jawo mana abun fad'a da zai bibiyi tsatson mu har k'arshen mu. Allah ya isa tsakani na daku kun hana ni aure saboda mugayen halayen ku. Duk wanda ya fara zuwa waje na, k'ark'arinsa sati d'aya, shima kamun ya gano asalin su wanene y'an gidan mu. Yana ganowa yake blocking d'ina kuma ba zai sake dawowa ba." Ta k'arisa maganar tana mai fashewa da kuka. "Kutumar bura uba......! Lami kina jin irin maganganun da y'ar iskar yarinyar take min a cikin gidan nan ko!" Fad'in Hassana tana mai nuna Sarah da hannu tare da girgiza jiki. Kau da fuska Sarah tayi tana mai kallon gefe. Lamin kuwa d'aga hannu tayi ta wanke fuskan Sarah da mari sai da tayi taga-taga zata fad'i, sai Allah ya taimaka ta tsaya da k'afafunta tare da dafe fuskan tana kallon Lamin hawaye na zubo mata. "Dan uban ki Nuhu, ita sa'ar ki ce da zaki tsaya kina mata rashin kunya? Ta tara y'ay'an shegun dan ubanki! Ke menene wannan yanzu a cikin ki? Shegiya kema kina tare da abun gorin amma kike yiwa wata. Za kici ubanki dani a cikin gidan nan idan na kafa maki k'ahon zuk'a." Fad'in Lami tana mai nuna ta da yatsa. "Lami ke baki gano ta bane? So take ki mance da maganar da kika soma na sai ta fad'a maki uban cikin dake jikinta." Fad'in Marfu'a. "Kwarai sai yanzu na fahimci zancen Marfu'a. To ban mance ba dan ubanki. Uban wa ya yayi maki tsirara ya kwashi albarkatun roman jikin ki? Nace wani shegen ne yanzu in fita in kwankwasi gidan su?" Fad'in Lami tana mai jawo Sarah gabanta. Sarah kuwa wani kukan ta kuma fashewa dashi tare da duk'awa a wajen tana fad'in, "Ni dai Allah ya san cewa babu namijin da ya tab'a kaiwa ga jikina. Ni ban ta yaya ciki ya shiga jikina ba wallahi." Baki sake Lami da y'an uwan ta suka bita da idanu. Na'ima ce tayi k'arfin halin fad'in, "To a ruwa kika sha dab kutumar uban ki? Kuji min shegiyar yarinya zata mai damu y'an iska wanda basu san inda ke masu ciwo ba." Lami kuwa tsabar takaici bata san lokacin da ta kai k'asa inda Sarah take duk'e ta shak'o wuyarta tare da wanke fuskanta da mari hagu da dama sannan ta tura ta baya ta fad'i dab'as sai da ta dafi k'asa da duka hannayenta biyu. "Ku shiga d'aki ko waccen ku ta d'auko lafiyayyan bulalanta kuyi ta jibgar shegiya har sai ta magantu tukun zaku kyaleta. Ni anya kuwa ba canje aka yi min a asibiti ba kuwa?" Lami ta fad'i tana shurin Sarah da k'afafunta. Gab'a d'ayan su kuwa dama cike suke da ita, ko wacce ta d'auko bulalanta a hannunta tayo kan Sarah suka shiga lafta mata bulala ta ko'ina a jikinta. Tsabar zuciya irin na Sarah ko gezau, kuma gashi tana jin azaba duk sanda bulalar ta sauka a fatar jikinta. Don har rige-rige suke yi wajen aje bulalar a kan fatarta. Ita burinta d'aya, Allah yasa wajen dukan nata su zubar da cikin dake jikinta ta huta da mugun abun kunyar nan da take d'auke dashi. "Wallahi duk wacce ta k'ara kai duka jikinta sai ta bar gidan nan a cikin daren nan tunda ba gidan uwar ku bane." Fad'in mahaifin su da fitowarsa kenan daga cikin d'akinsa. Wani yamutsatstsan tsohe wanda wahalar rayuwa duk ta gama cinyesa ya fad'i hakan hannunsa rik'e da sanda yana dogarawa har ya k'ariso inda Sarah ke duk'e a k'asa. D'aga sandar yayi kamar zai makawa Na'ima da ta kuma d'aga bulalar zata zabgawa Sarah, sai tayi saurin ja baya tare da fad'in, "Kul! Wallahi kar ka kuskura ka tab'a ni da k'azamar sandan nan naka. Don kana sauke min sandar a jiki, kaji na rantse maka sai na rama." Ta fad'i hakane tana mai zaro masa idanu kamar shima zata kai masa bulalar dake hannunta. Mik'ewa Sarah tayi a zafafe tare da fad'in, "Wallahi kika tab'a jikin mahaifina sai na kashe ki a cikin gidan nan, ai nafi shekaru sha takwas a duniya, hakan na nufin na isa d'auri." Matsowa kusa da Sarah yayi yana d'ingishi tare da fad'in, "Kul, Saratu! Kar in kuma jin kin sake furta irin wannan maganar. Ke d'in yarinyar albarka ce. Ki barta, duniya ta ishi kowa riga da wando, wanda bai shigo bama jiransa take yi. Kiyi hak'uri kin ji. Koma d'aki. Idan kowa be yarda da ke va, bi na yarda dake y'ata. Ke kuma, kije Allah ya isa tsakani dake. Allah zai min sakayya Lami." Wani irin gud'a Lami ta saki tare da fad'in, "Wallahi Allah ya isar ka babu inda zata je sai dai ta koma kanka. Ai nice ma ya kamata nayi maka Allah ya isa irin wannan uk'uba da na sha a gidan ka kamun Allah ya wanke y'ay'a mata shidda ya bani. Dan ma dai gud'a d'aya a cikin su azzaluma ce mai irin halin ka wacce bata son share min hawaye. Yanzu wannan akurkin kake tutiya dashi har kake kira gida? Lallai! Bayan da ba dun taimakon su y'ay'an da kullum kake zagi da ikirarin zaka kore su sun taimaka sun d'an yi gyare-gyare a gidan ba, har zai kallu balle ma a kira sa gida. Ka dai ji kunya wallahi Nuhu. Kuma y'ay'ana babu inda zasu je. Zama a cikin gidan nan dole, idan kaji ana daram dam-dam to ni da y'ay'ana kenan a cikin gidan nan. Sai dai idan kai ne zaka fice ka bamu waje don billahil lazi naci gida! Y'ay'a bakwai na haifar maka, d'aya namiji, sai tsala-tsalan mata har shidda. Ni ai wallahi har yau tsinewa soyayya nake yi da har ta rufe min idanu ta jani da kyawuna na fuska da na jiki amma na b'uge da auren fak'iri irin ka wanda aka haifesa da bak'in fentin talauci. Nuhu ka fita harkata da ta y'ay'ana tun kan in kai ka k'ara kotu a raba tsakanin mu." Wani dogon tsaki Nuratu taja tare da fad'in, "Ni wallahi Lami ban san mai kike yi har yanzu da wannan tsohon ba da baki rabu dashi ba. Ke kan ki da zaki d'au wanka ki fara shafa mayuka masu gyare jiki kina hawa leses masu tsada da atampofi, wallahi da wani mayen mai kud'i zai yi wuff dake kema kije kici arziki ki bar arziki inda yake. Don wallahi ba wani tsufa kika yi ba, kawai wahalar wannan tsohon ne ya mai da ki haka." Ta k'arisa maganar tana hararen mahaifin nata. Shi kuwa wani irin kukan bak'in ciki ya fashe dashi tare da dogara sandar shi ya juya ya koma d'akinsa wanda ba k'aramin abu yake fitowa dashi ba, ko alwala da sallah a ciki yake yi. Yana da bahon da yake alwala a ciki, sannan kuma akwai wani bokitin penti k'arami da yake yin fitsari ko ba haya a ciki wanda Sarah ce ke d'awainiyar fitar dasu tana zubar da abunda yake ciki tare da wankewa sannan ta dawo masa dashi ta ajiye. Da sauri Sarah tabi bayansa ita ma tana kukan tana kuma bashi hak'uri. Lami kuma harara ta bisu dashi tare da fad'in, "Munafukan banza da wofi! Kin ga yarinyar nan, wallahi za'a iya had'a baki da ita a kashe mu. Kuma zan yi maganin ta." Tana gama fad'in haka taji an banko gidan da k'arfi an shigo da gudu tare da afkawa d'akin ta. Da idanu duk suka bishi a tsorace, dai-dai lokacin da wani matashi shima ya fad'o gidan ya tsaya tsakar gida hannunsa rik'e da k'atuwar adda yana huci. Gaba d'aya su Na'ima suka koma bayan Lami a tsorace. Shi ko matashin ya k'ariso har inda suke fuska babu rahama tare da karta addan a k'asa yace, "Na rantse da ubangijin Yunusa da Musa, idan ba'a fiddo min da wayar k'anwata da d'an ki ya kwata yanzu ba, duk sai na sassare ku a cikin gidan nan. Ni dashi kar ta san kar billahil lazi. Dalla malama ware ki amso min waya a hannun kafurin d'an ki ko kuma yanzu lahira tayi bak'o." Ya k'arisa maganar yana zarowa Lami idanu. Jikin Lami da y'ay'anta gaba d'aya babu inda bai rawa saboda kaf cikin gari babu wanda bai san *Naliliyo* ba. D'an daba ne sosai wanda kisan mutum a wajensa kamar take kiyashi ne. Da sauri Lami ta juya zata shiga d'akinta domin karb'o wayar, sauran y'ay'an zasu rufa mata baya ya daka masu wata uwar tsawa tare da fad'in, "Duk wata kafurar da ta motsa a cikin ku sai na kashe a nan waje." Gaba d'aya suka k'ame k'am kamar an dasa bishiya. Mintuna kad'an sai ga Lami ta fito hannunta d'auke da iPhone 7plus a hannunta ta mik'awa *Naliliyo* har da d'an duk'awa. Fizge wayar yayi tare da nuna Lami da hannu sannan yace, "Ki hawa kafurin d'an ki kunne, wallahi ko da wasa na k'ara ganinsa ya gitta ta k'ofar gidan mu, to gawarsa ma sai tayi maki wuyar gani." Yana gama fad'in haka ya juya ya fice daga gidan. Na'ima ta saki dogon tsaki tare da fad'in, "Wannan d'an iskan wata rana sai ya jawo mana abunda zai saka a k'ona mu da ran mu a cikin gidan nan. Kullum fa sai kin bashi kud'i amma duk da haka sai ya fita ya jawo mana magana. To gashi nan dai yau ya d'auko mana maganar *Naliliyo* har yana ikirarin zai kashe shi. Wallahi kiyi masa magana Lami ya fita harkan gidan jarababben d'an DABAN nan. Tom!" Kamun Lami tayi magana Lukman (lucky boy) ya fito a fusace yana mai tsira mata hannu tare da fad'in, "Zan ci uwarki a gidan nan idan kika k'ara saka mun baki a cikin al'amura na. Ke uban wanene bai san cewa ke tantiriyar karuwa bace mai y'ay'a har biyu na shegu, dan ma d'ayan ya fad'i ta hannu hagu (Mutuwa) da yanzu y'ay'an ki uku duk shege. Wallahi kika k'ara saka min baki a cikin al'amura na, sai na maki mugun duka a cikin gidan nan. Y'ar iska taxi no garage!" Kallonsa Lami tayi a fusace tare da fad'in, "Kai! Kai Lukman!! Kayi min shuru a wajen nan. Kar in kuma jin bakin ka. Ba yarka bace ita? To ban so ka k'ara fad'in wannan maganar. Ka shiga d'aki ina zuwa akwai wasu kud'i da na ajiye maka." Juyawa Lucky boy yayi yana wani tafiya a b'ankare tare da fad'in, "Karfa ki dad'e kin san ban son jira." Lami kuma mai da dubanta tayi izuwa wajen Na'ima tare da fad'in, "Kin san dai ba hankali bane ya ishe sa, ki rik'a fita harkan sa." Turo baki Na'ima tayi tare da wucewa fuuuu tana fad'in, "Ai ke Lami sam baki son laifinsa, kullum sai dai ki rik'a d'iban kud'i kina bashi yana zuwa yana shaye-shaye dasu." Lami bata ce komai ba ta wuce d'aki domin bawa Lucky boy dubu biyar d'in da tayi masa alk'awari jiya. Sauran y'an matan ma duk suka shige d'aki. Sai da Sarah taji shuru a tsakar gidan sannan ta fito ta nufi pampo ta d'auro alwala saboda kwala kiran sallar isha'i da taji ana yi a masallacin dake gaban gidan su kad'an. Dawowa d'akin tayi ta taras da duka yayyinta a ciki ko wacce sai cab'a kwalliya take yi saboda lokacin fitar su yayi. Dama haka suke yi, wasu idan sun fitan ma, sai suyi kwana biyu, uku har sati basu dawo ba. Wata rana kuma a ranar suke dawo can cikin dare. Darduma Sarah ta shimfid'a ta tada sallar isha'i, don dama ita kad'ai ce a cikin su take yin sallar, to Lamin ma bayi take yi ba balle ta saka su a hanya. Sai bayan ta idar ta sallah ne ta saka doguwar riga irin mai kama jikin nan, sai ta d'aura k'atuwar suwaita a kai sabida sanyin da take ji. Tana cikin zuge zip d'in suwaitar aka kwad'a sallama a cikin gidan nasu tare da fad'in, "Wai ana sallama da Sarah inji Farouq." Ras gaban Sarah ya yanke ya fad'i, don gani take yi kamar tana fita suka hada idanu zai gane akwai ciki a jikinta. Da sauri ta lek'o tsakar gidan tare da fad'in, "Kace tana zuwa yanzu." Tana gama fad'in haka ta dawo d'akin domin d'aukar hijjab d'in da ta cire yanzu bayan ta idar da sallah. "Kanin ubanta yazo, jikinta sai rawa yake yi domin taje ta gaida shi." Fad'in Nuratu tana hararar ta. K'ala Sarah bata ce ba, sai ma hijjab d'inta da ta fara k'ok'arin sakawa. "Shegiya ko irin jan ajin nan baki iya ba. Daga ya turo jikin ki na rawa zaki fita." Fad'in Marfu'a. Sarah kuwa ko kallo basu ishe ta ba, ficewa ma tayi daga d'akin bayan ta gama sanya hijjab d'inta. A k'ofar gidan ta ganshi sanye da wando jeans da blue T-shirt, kansa sanye da facing cap ya jingina da wani k'arfe dake jikin gidan mak'otan su yana kallon d'aid'aikun mutanan da suke fitowa daga masallacin kasancewar ba'a jima sosai da idar da sallah ba. Juyowa yayi tare da zuba mata idanu har ta k'ariso inda yake tare da fad'in, "Sannu da zuwa. Ina wuni?" Kallonta yake yi for almost 2mins kamun ya bud'e baki yace, "Ina kika je d'azu na ganki kin ruwa ya maki duka?" Saurin d'agowa tayi ta zuba masa idanu, sai kuma ta sunkuyar da kanta gabanta na fad'uwa don gani tayi makar zai ga an rubuta _Ina d'auke da ciki_ a kan goshin ta. "Tambayar ki nake yi kin yi min shuru." Farouq ya sake magana a karo ba biyu. Sai a lokacin Sarah ta bud'e baki tare da fad'in, "Asibiti naje." Kallonta yayi tare da maimaita "Asibiti." K'ara d'agowa tayi ta kallesa a karo na biyu, sai kuma tayi saurin kau da kai tana kallon k'asa tare da wasa da zoben dake hannunta. "Are you sick Sarah?" Girgiza kai tayi tare da fad'in, "Dubiya naje yi. Lokacin da na fito kuma ban samu abun hawa ba saboda hadari. Shine ruwan ya duke ni, amma kuma ba fake. Da ruwan yayi sauk'i ne shine na fito shiyasa ka ganni a jik'e." Ajiyar zuciya Farouq ya sauke tare da fad'in, "Amma baki san hakan da kika yi zai iya jawo maki rashin lafiya ba. Mai yasa ma baki kira ni nazo na d'auko ki na dawo dake gida ba? And ina ta kiran wayar ki bakya d'aga wayar." Ya fad'i hakan yana mai folding hannunsa. Ko kamun Sarah tace wani abu an banko k'ofar gidan su, cikin sauri duka su biyun suka juya suka kalli k'ofar gidan. D'an duk'awa Farouq yayi tare da fad'in, "Mama ina wuni?" Harara Lami ta watsa masa tare da fad'in, "Uwar ka ba, ka baro ta can gida. Ni ba mamarka bace. Kaga wacce ta haifa nan." Ta k'arisa maganar tana mai nuna Sarah da hannu sannan ta cigaba da fad'in, "Ba gaisuwa ka na taho nan in amsa ba, zuwa nayi ka fad'a min shin kai ne uban cikin dake jikin Saratu ko kuwa. Don idan kai ne, wallahi na rantse list d'in ka daban ne. Kuma kar kayi tunanin zan yi maka ragi." Hannu Sarah ta d'aura a kai tare da fad'in.................. *_Chart me up 08128755583_* [09/09, 10:03 A [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: _K'ANWAR MATATA_*🦜 _Matar Sayyadee_ _Wattpad @Matar_Sayyadee_ ☀️ *ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*☀️ Page 3 Hannu Sarah ta d'aura a kanta tare da fad'in, "Haba Lami wannan wani irin magana kike yi haka? Mai yasa a kullum burin ki, ki zubar min da mutunci a idanun Farouq? So kike kiyi ta danka mu a cikin gidan babu aure?" Sarah ta fad'i tana kuka sosai. Shi kuwa Farouq da idanu kawai yake bin Sarah da mahaifiyarta kamar wawa. Don sam bai son gasgata abunda kunnuwansa suke ji. "Bak'ar munafuka! To sai nayi magana. Wato baki so nima na samu rabo na ko? To wallahi komai dani za ayi shi. Juyo nan ka bani amsar tambayata, shin kai ne uban cikin dake jikinta?" Wani irin b'acin rai ne yake tasowa tun daga can k'asan zuciyar Farouq, bai iya magana ba sai kallon fuskan Sarah yake yi yana son jin wani k'arin bayani ko kuma ta k'aryata zancen da mahaifiyar nata take yi. Amma maimakon haka, Sarah sai girgiza kanta kawai take yi hawaye na zubowa daga idanunta. "Wai ba da kai nake yi bane Umar da kayi min banza kamar wata sa'ar ka!" Lami ta fad'i a zafafe. Gyara tsayuwa Farouq d'in yayi tare da kallon Lami k'asa-k'asa sannan yace, "Ban san maganar da kike yi akai ba! Kwata-kwata ma ban fahimci mai kike cewa ba Mama." Dak'uwa Lami tayi masa tare da fad'in, "Uwarka nace kaji? Ai nasan ka fahimci wannan ko! To ni menene ma na tsayawa sai naji ko kai ne kayi cikin ko ba kai bane. Bayan na san kai d'in fak'iri ne ba wani abun kirki zan samu daga gare ka ba. Amma sai dai ka sani, daga yau ban k'ara bata ko loma d'aya daga cikin abincin gidana, don sai taci ne abun cikinta zai ci, kuma ni da in ciyar da jinin ka, gwara na ciyar da karuwai goma babu lada." K'asa-k'asa Farouq yace, "Ai yanzu ma karuwan kike ciyarwa a cikin gidan." Kallonsa Lami tayi tare da matso da kunnanta tace, "Kace me?" Kau da kai Farouq yayi tare da fad'in, "No babu abunda nace!" Dogon tsaki taja sannan ta juya ta shige cikin gidan har da bugo masu k'ofa. Kicib'is suka ci da Na'ima taci uban kwalliya ta tsuke cikin k'ananan kaya kamar d'iyar arna, "Y'ar albarka har zaki wuce?" Yamutsa fuska tayi tare da fad'in, "Eh! Idan kun ji shuru ku rufe gidan kawai, don ba lallai na dawo gida na kwana ba." "To Allah ya tsare." Fad'in Lami har da d'aga mata hannu. Duk abunda Na'ima da Lami suke cewa, tsaf a kunnan Sarah da Farouq. Fitowa Na'ima tayi daga cikin gida tare da gallawa Farouq harara ta saki tsaki tare da tsirtar da yawu. Har tayi gaba, sai kuma ta dawo dai-dai inda Farouq d'in yake a tsaye tare da sauke glasses d'in fuskanta k'asa kad'an sannan tace, "Ina fatan masoyiyar taka ta fad'a maka tana d'auke da ciki har na tsawon sati biyu." Ta k'arisa maganar tana daga yatsunta biyu a fuskan Farouq d'in. Wani banzan kallo Farouq ya bita dashi mai cike da tsana. Sarah kuwa ji tayi dama tana da layar b'ata ta danna kawai ta ganta a cikin gida saboda tsananin kunya mai had'e da tsoro da take ji. Farouq yana kallo Na'imar ta bud'e gaban motar wani mutum wanda a haife ta haife ta, yaja motar suka bar layin. Juyowa yayi tare da kallon Sarah wacce kanta ke k'asa, ya jima yana kallonta tare da had'iye wani miyau mai d'aci da ya tokare masa mak'oshinsa sannan yayi k'arfin halin fad'in, "Sarah mai nake ji haka daga bakin mahaifiyarki da y'ar uwarki?" Kuka kawai Sarah ta fashe dashi do ita kanta abun jinsa take yi kamar hauka ko rainin hankali ta bud'e baki tace bata san ta yanda aka yi ciki ya shiga jikinta ba. D'agowa tayi ta kallesa tare da fad'in, "Ni wallahi tallahi....." D'aga mata hannu yayi tare da fad'in, "Na fahimta, basa son alak'ata dake ne shiyasa suke son raba mu da wannan zancen na su. Ni kuma idan har ba canza hali za kiyi ba Sarah, babu mai raba mu idan ba mutuwa ba. Ni dai alfarma d'aya nake rok'o a wajen ki Saratu, dan girman Allah ko sau d'aya kada rayuwar da y'an uwanki suke yi ya burge ki. Idan kika mun haka, ni kuma zan cigaba da tsaya miki duk rintsi, kunnuwata zasu kasance a toshe, haka babu wani suka naki ko kuma laifin y'an uwanki da za ayi amfani dashi wajen nuna min bak'inki har yayi tasiri a waje na." Kuka Sarah take yi har da shasshek'a, ita kad'ai tasan mai take ji a cikin zuciyarta. "To wai kukan na miye ne haka? Idan har ba b'acin rai na kike son gani ba, ki share wad'annan hawayen naki." Bayan hannu Sarah ta saka ta share hawayen fuskanta tare da k'irk'iran murmushin babu babu inda ya tsaya sai iya lab'b'anta. "Yauwa ko ke fa! Sannan abu na gaba, ban ji dad'in yanda ba ganki d'azu ba, na d'auka tuntuni mun riga mun gaba magana akan irin shigar da kike yi. Kin san fa da shigar jikin mutum kad'ai akan iya gane wanene shi. Dan girman Allah ki daina saka wannan zaro-zaron gashin idanu nan da wannan k'umbar dake hannunki. Ni wallahi kyama yake bani. Wanda Allah yayi maki ma ya ishe ki Sarah." Hawaye na zuba a idanunta ta furta, "In sha Allah daga yau ba zan k'ara saka d'aya daga cikin abunda ka lissafo ba." Ajiyar zuciya Farouq yayi tare da fad'in, "Allah ya miki albarka amaryata ta sati hud'u masu zuwa. Ki shiga gida hadari ne sosai a gari. Sai mun yi waya." Bata iya cewa komai ba sai murmushin da tayi tare da yi masa bye-bye ta shige cikin gidan. Tana turo k'ofa ta jingina da k'ofar tare da dafe k'irjinta da hannu d'aya sannan ta toshe bakinta da d'ayan hannun tana kuka sosai. Juyawa tayi ta lek'a ta wani d'an rami a jikin k'ofar, ga mamakinta sai ganin Farouq tayi tsaye a wajen amma ba k'ofar gidan yake kallo ba, wani wajen yake kallo daban. Can kuma ya saki ajiyar zuciya tare da tsallake kwatar dake gaban gidan ya wuce. Sai a sannan Sarah ta zame k'asa ta fashe da wani irin kuka mai tafasa zuciya. Ta jima a wajen tana kuka kamun ta mik'e ta nufi cikin gidan. D'akin su ta shiga ta cire hijjab d'in jikinta ta ninke tare da rataye sa a hannun wardrobe sannan ta cire suwaitan jikinta ta mak'ale a abun rataye jaka sannan ta kashe wutar d'akin don babu kowa a ciki, sauran y'an uwanta suna d'akin Lami kamun masu zuwa fita dasu su k'araso. Hawa kan gadon tayi ta kwanta rigingine tana sak'awa da warwarewa akan cikin dake jikinta. Sosai tayi zurfi a tunanin ta yanda aka yi ta samu ciki, sai dai duk iya zurfin tunaninta, bata gano bakin zaren ba, don zata iya dafa Qur'ani tayi rantsuwa bata tab'a sanin wani d'a namiji ba a duk tsayin rayuwarta. Daren ranar bacci b'arawo ne ya kwasheta. Kiran sallar asubahi kuwa, a kunnanta ladani ya kwad'a shi. Saukowa tayi daga kan gadon tare da kunna wutan d'akin haske ya kawo, babu kowa a d'akin, hakan ne ya tabbatar mata da ita kad'ai ta kwana a d'akin. Don da ace y'an uwanta sun dawo daga yawon banzan su jiya, babu abunda zai saka su kyale ta ta kwanta a kan gado ba tare da sun turo ta k'asa ba. Kai tsaye d'akin mahaifinta ta nufa, kamar yanda tayi tsammani hakan ce ta faru. Zaune ta samu mahaifin nata ya fuskanci gabas yana sallah a zaune. Don ciwon k'afar nasa bai barin sa yayi sallah a tsaye. Tun kusan shekaru biyar baya sallah dare ta zame masa tamkar jinin jikinsa. K'arfe uku kamar a kunnansa take bugawa saboda sabo da tashi. Bai kuma komawa bacci sai gari yayi tarwai tukun. Sarah d'aukar roban pentin da yake yin bowali tayi ta fitar dashi tare da zubar dashi a makewayi sannan ta dawo dashi ta ajiye sannan ta fita ta koma bayin ta kamo ruwa sannan ta fito ta d'auro alwala. Kamar zata wuce, sai kuma wani zuciyar ta jata ta nufi d'akin Lami. Tun daga bakin k'ofar take jin wani wawan munshari mara dad'in sauraro kamar an danne rago. Hannu ta d'an d'aura akan k'ofar ta tura, sai taji k'ofar a bud'e. Tura kai tayi ta shiga d'akin tare da lalubar bango ta kunna globe d'in dake d'akin. Lami ta hango tayi wani irin washarere a kan gadon kamar gawa, babu riga a jikinta daga ita sai d'aurin k'irji, shi kansa zanin yayi gefe, mamukanta kuwa d'aya ya kalli arewa, d'aya ya kalli kudu. Gata Ma sha Allah irin jibga-jibgan matan nan ne. Hatta bakinta a bud'e yake. Kau da kai Sarah tayi ta kalli d'ayan gefen da autarsu y'ar shekaru goma sha bakwai da watanni take. Ita ma dai bacci take yi cike da rashin tsari domin bacci ne irin wanda ba'a son musulmi ya rik'a yi wato ruf da ciki. Hannu Sarah ta kai ta d'aka mata duka cinyarta ta baya da yake a kwaye. Da sauri Aina'u ta kai hannu wajen ta Sosa ba tare da ta yanke baccin da take yi ba. Wani dukan Sarah ta kuma kai mata, wannan karan a furgice ta mik'e tana mitsitsitsike idanu tare da sakin wani irin hamma kamar d'iyar arna. Sai da ta ware rass sannan ta k'arewa Sarah kallo wutar balbalin bala'i na taruwa a kwayar idanunta. Don Aina'u irin fitsararrun yaran nan ne wad'anda duk girman mutum ko da kuwa jikinsa kaf furfurace bata raga masa. Y'an unguwanmu sun ce ita ce tayo sak halin Lami, wasu sun ce tafi Lami d'in ma. Tun tana k'ank'anuwarta makirar yarinya ce ta bugawa a jarida. Ga salo kamar wata uwar mata. "Uwar me zan maki cikin daren nan da zaki zo ki katse min bacci na!" Fad'in Aina'u kamar harcenta zai zazzago, don ta kasance irin matan nan masu harshe. Duk yanda tayi magana a hankali, ji za kayi kamar a kwar gida take magana. Da dare da rana basu da bambamci a wajenta. Yanzu haka da tayi magana kasancewar dare mai d'aukar sauti, har sai da mahaifinsu dake d'akinsa ya jiyo sautin muryanta. Hatta Lami mai bacci kamar gawa sai da ta farka a firgice tana sambatu. "Sallah nazo tashin ki kiyi. Don gashi can shirin tada sallar ake yi a masallaci. Ace duk k'arar speaker d'in masallacin can ba zai iya tada ku kuyi sallah ba!" Fad'in Sarah tana mai k'ok'arin juyawa ta bar d'akin duk da kuwa ta san cewa ba sallar za suyi ba. "Dan ubanki baza muyi sallar ba. Idan mun d'aga k'afa zamu shiga aljanna sai ki dawo damu baya saboda ta ubanki ce! Fita ki bar d'akin nan tsohuwar annamimiya!" Fad'in Lami tana mai nuna mata hanyar k'ofa. Komai Sarah bata ce ba, sai ma ficewa da tayi daga d'akin ta koma nata d'akin ta shimfida darduma ta tada salla. Tana nan zaune ko da ta idar da sallar har sai da gari ya waye tass, lokacin k'arfe bakwai sannan ta soma jin bacci a idanunta, amma kuma bata son yin baccin. Burinta ta shirya ta kuma fita domin yawon bin asibitoci ko za tayi dace da asibitin da scanning machine d'insu zai k'aryata cikin da wasu asibitocin da suke cewa tana dashi. Ta yunk'ura zata tashi daga kan sallayar taji muryoyin mata na tashi a tsakar gidan su. Gabanta ne ya buga da k'arfi sai tayi saurin d'aga labule kad'an ta lek'a waje. Da sauri ta saki labulen tana mai dafe k'irjinta da zuciyarta ke barazanar fasowa ta fito saboda arba da tayi da yayyin Farouq mata uku da kuma aunties d'insa guda biyu, gaba d'aya fuskokinsu a turbud'e.............. _Ko mai zai faru a gaba?🤔_ *AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE* _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_ _*infection*_ _Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_ _07084653262_ [09/09, 10:03 AM] Matar Sayyadee: 🦜 [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: _K'ANWAR MATATA_*🦜 _Matar Sayyadee_ _Wattpad @Matar_Sayyadee_ ☀️ *ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*☀️ Page 4 "Ah'aaa! Yaya haka, menene haka kuma zuwa da sassafen na sai kace karb'an kud'in bashi? Ni fa bani son irin wannan naci tun ba'a je ko'ina ba." Fad'in Lami wacce fitowarta kenan daga d'aki baki duk miyan bacci. Bayanta kuma Aina'u ce ke mik'a tare da hamma babu addu'a sai wani "umm'iyyyyyyy!" Take fad'i kamar k'atuwar rago ko kuma bijimin sa. D'aya daga cikin matan wacce sai jijjiga take yi, ga dukkan alamu tafi kowa a cikin su hassala tace, "To dama uban me zai kawo mu wannan wulak'antaccen gidan wanda babu albarka cikinsa in ba tsautsayi ba. Banda fitina da jawowa kai jidali irinta Umar Farouq, menene abun so a cikin y'ay'an gidan nan wanda gaba d'aya kowa ya gama sanin karuwan gida ne su." D'ayar siririyar cikin sy tayi saurin cafe zancen wajen fad'in, "Aunty Bilkisu ai gansama-gansaman zaurawar gidan nan sun wuce karuwan gida, don ni kam ba zan Kira su da y'an mata tunda tun daga kan babbar har k'aramar babu wacce bata san dad'in d'a namiji ba." Saurin cafe zancen k'aramar cikin su tayi tare da fad'in, "Yo aunty Halima ai ga zahiri tunda kina ganin shegu ta kowani lungu na gidan an ajiye. Kai Allah yai wadaran naka ya lalace. Wallahi ko wucewa ta kwar gidan nan ban k'aunar yi balle har in tako k'afata cikin gidan nan." Lami kuwa dake tsaye suke fad'in duk abunda yazo bakinsu, wani shewa tayi tare da nuna wacce aka kira da aunty Halima tace, "Alhamdulillah, ko yau na fad'i na mutu za'a nuna abunda na bari ace Allah sarki ga y'ay'an wance da ta bari. Ke kuwa fa? Ko b'ari kin tab'a yi ne? Idan fitsari banza ne, kaza tayi ma. Kuma y'ay'ana Kainuwa ne, babu yanda aka iya dasu. Duk wani munafurcin ku da k'ananun maganganunku, kanku zai koma." Aunty Halima wani tsalle ta daka kamar za tayi wasar y'ar gala-gala sannan ta bugi k'irji kare da fad'in, "Haihuwa idan har irin taki ce Lami, kada Allah ya bawa ruwan maniyy d'in mijina isa ga mahaifata. Ai da Haihuwa irin y'ay'anki wallahi gwara b'arinsu. Lami haihuwa irin taki ko, na gwammaci har in koma zuwa ga ubangijina ban ajiye ko kwai d'aya a duniya ba. Kuma ki bud'e kunnuwanki dakyau kiji, idan har ni k'anwar mahaifiyar Umar Farouq ce, to wallahi auren sa da Sarah sai dai bayan raina. Domin Na'ima har gida taje ta samu mahaifiyar Umar ta fad'a mata y'arki da ake son mak'alawa d'ana, tana d'auke da ciki. Dama kuma banda hauka da rashin hankali, mai Farouq zai ci da d'iyar karuwa, tubabbiya wacce sana'ar danginsu kenan karuwanci! Mun bar maku duk wani abu da aka kawo gidan nan da sunan naiman auren y'arku, sai dai amma ki sani, babu aure tsakanin zuri'arki da namu zuri'ar." Wani irin rushewa da kuka Sarah tayi jin abubuwa da Aunty Halima take fad'i A bayyyane ta soma fad'in, "Shikenan, Farouq d'in ma ya sub'uce min. Dama na sani ba zan tab'a aure ba a rayuwata." Ta fad'i hakane tana mai kaiwa cikinta duka da duka hannunta biyu. Lami kuwa kitchen d'in dake tsakar gidan ta nufa tare da d'auko katoton tab'aryarta mai nauyi da tsayi tayo kan su Aunty Halima don har cikin ranta taji zafin maganganun da aunty Haliman tayi mata. "Aunty Halima, aunty Halima!" Siririyar mai suna Najma ta kwad'a kiran sunan aunty Halimar tare da fizgo hannun aunty Bilkisu ta janye ta baya saboda kawo tab'aryar da Lami tayi. "Barta, barta ta jawowa kanta bala'i Najma. Wallahi ba zan gudu ba, karyar hauka take yi, idan ta isa ta buga min taga abunda zai faru da ita yau d'in nan." Fad'in aunty Halima amma deep down tana jin tsoran kar Lami ta buga mata zabgegiyar tab'aryar dake hannunta. Lami kuwa k'ara yowa kansu tayi da tab'aryar ta d'aga sama zata kwad'awa aunty Halima da tayi k'arfin hali tak'i guduwa. Caraf taji an rik'e tab'aryar ta baya, a fusace ta juya suka yi idu hud'u da Sarah wacce idanunta suka kad'a suka yi jazur alamar tayi kuka. "Cika min tab'aryana ko inci ubanki cikin gidan nan!" Lami ta fad'i da k'arfi tana mai zarowa Sarah idanun. "Dan girman Allah Lami kar ki tab'a su, ki kyale su. Yanzu idan kika bugawa d'aya daga cikin su, RAI kuma yazo yayi halinsa, ya za kiyi?" Fizge tab'aryar tayi tare da fad'in, "To idan na kashe sai me? Ko kotu aka je babu wanda za tuhume ne don sune suka biyo ni har cikin gidana. Duba kiga cikin zuri'ar da kike son shiga, su kansu tun daga yanayin shigarsu zaki fahimci babu abun arziki a gidan. Daga ganin kayan jikin wannan shanyayyiyar matan (Tai nuni da aunty Bilkisu) kayan jikinta kwance ne. To a nan wajen mai na sama yaci balle ya baiwa na k'asa. Shashasha! Ni Allah ya yiwa Na'ima albarka da har taje gidan su Farouq d'in ta fad'awa mahaifiyarsa kina d'auke da juna biyu. Dama kuma nayi rantsuwa idan har ni y'ar Samuel da Debora ce ba zan tab'a bari kiyi aure da d'an iskan yaron nan ba. Sai gashi Allah ga kawo hanya mafi sauk'i. Ke bama shi ba, babu ke babu aure da kowani namiji a duniya nan." Salati gaba d'aya su Aunty Halima suka d'auka suna tafi. "Eh lallai! Yau na tabbatar da ke d'in cikakkiyar arniya kuma bakatafiya ce ke. Kin fi k'aunar suyi ta gantali a titi suna yawon hotel-hotel suna kawo maki kud'i kina musu goyon shegu ko? Tirr! Shiyasa aka ce idan za kayi aure ka auri uwa ta gari domin ta haifo maka y'a'yana nagari. To kema kan ki ba tarbiyar gare ki ba balle ki bawa y'ay'anki tarbiyan." Kamun Lami tayi magana, sai ga Na'ima da Nuratu sun shigo gidan a tare ko wacce hannunta rik'e da manya-manyan ledoji. Washe baki Lami tayi tare da fad'in, "Ka ga y'ay'an albarka wanda aka haife su tsiya na barci!" Baki sake su Aunty Halima suke kallon su Na'imar da sai wani yatsine-yatsine suke yi. "Lami akwai ruwan wanka kuwa a gidan nan? Don ni wallahi a mugun gajiye na dawo. Mutun hud'u suka yi ciniki na." Amshe maganar Nuratu tayi tare da fad'in, "Wallahi nima a gajiyan nake tib'is. Ni mutum d'aya ne ma ya d'auke ni muka tafi _Asa pyramid_, wallahi ko runtsawa banyi ba. Ruwan zafi nake buk'ata sosai in galgasa jikina." Washe baki Lami tayi tare da fad'in, "Y'ay'an albarka, y'ay'an gwal kenan. Babu ruwan zafi amma yanzu nan zan had'a wuta na d'aura maku, ku shiga daga ciki naga alama babu k'arfi a jikin ku gaba d'aya duk kun yi laushi." Su aunty Halima kuwa, wannan ta kalli wannan, sai wannan ta kalli wannan, haka su kayi tayi tsakanin su suna mamakin hali irin na Lami. "Way'annan kuma mi suke yi a nan gidan?" Fad'in Nuratu tana kallon su d'ai-d'ai. Sai da Lami ta balla masu harara sannan tace, "Wai zuwa suka yi su fad'a mana sun janye auren da suke nema na Sarah. Baki ganni da tab'arya a hannu ba, ai tahowa nayi in sheme y'an iska." Gaba d'aya daga Nuratun har Na'ima kallon Aina'u suka yi tare da fad'in, "Ke dan ubanki tsayuwar mi kike yi da baku tare ke da Lamin kun kakkarya k'ashin bayansu ba!" Aina'u tayi wani tafi tare da fad'in, "Ai ni jira kawai nake yi Lami ta fara kai hannu kiga suga yanda ake yi a cikin gidan nan, don billahil lazi babu wacce zata fita da kaya a jikinta. Sai na tabbatar mun yi masu tsirara sannan mu hankad'a su waje." Cire siririn gyalenta Na'ima tayi sannan taci d'ammara dashi tare da kallon Nuratu tace, "Maza je rufo mana k'ofar gida saboda kar su samu damar fecewa." Da gudu Nuratun ta nufi k'ofa ta saka lock tare da sakata sannan ta dawo. Wani dogo sanda wanda aka ajiye a barandar d'akin mahaifinsu Nuratu ta d'auko, Na'ima kuma ta d'auko muciya, ita kuma Aina'u ta koma d'aki ta d'auko wata murd'ad'd'iyar bulala. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Nasiba sai da nace maku kar muzo gidan nan. Mu kira kawai a waya ya wadatar. Yanzu kinga d'aya daga cikin jahilci da rashin hankalin nasu ko." Fad'in aunty Lubabatu wacce bata cika fitana ba, asalima ita taso abi komai a hankali amma Mama ta matsa su tafi su fad'a masu sun janye neman auren. "Wai nan tsoro kike ji? Ai wallahi sarkin yawa yafi sarkin k'arfi, mu biyar ne fa!" Fad'in Rahima wacce ita ma tunda aka fara fad'an bata ce komai ba sai yanzu. "Baki da hankali hala? Gidansu fa muka iske su. Wallahi mune a ciki ko kotu aka je!" Ko kamun wani ya fara magana a cikin su, Nuratu ta shak'o wuyar aunty Halima ta baya ta kaita k'asa. Ganin haka ya saka gaba d'ayan su suka hau Nuratu da duka domin ceton aunty Halimar don tana kaita k'asa ta hau dukanta da sandar da ta d'auko. Suma su Lami na ganin haka, sai suka hau kansu da duka. Aina'u sai zabgawa ko waccen su zambad'ed'iyar bulalan hannunta take yi, Na'ima kuma tana maka masu muciyar hannunta. Kan kace kwabo, kasancewa su Nuratun da makami a hannunsu, tuni jini ya fara sharara a goshin aunty Luba, Aunty Halima da Najma. Don sun fi kowa buguwa. Ga shaidan bulala ta ko'ina a jikinsu. Sarah kuwa gefe ta koma tayi ta rusa kuka don ita kanta ta samu nata rabon wajen ceton su aunty Halimar. Baba ne ya samu ya fito da kyar don k'afar na matsa masa da ciwo sosai. Yana fitowa tsakar gidan ya tsaya turus, don tun shigowar su aunty Halimar yake sauraran komai daga ciki yana share hawayen bak'in ciki. Babu wacce yake tausayi banda Saratu don ya san ba k'aramin damuwa zata shiga ba na fasa auren nan nata da ake shirin yi. "Ke! Nuratu, Na'ima, Lami, Aina'u, wallahi kamun na iso wajen nan ku rabu da mutanan nan. Ku wasu irin yara ne kamar dabbobi. Kai ko dabba baza tayi abunda kuke yi ba. Babu wawuya mara hankali a cikin su kamar ke Lami. Wallahi kuka yi kisa a cikin gidan nan, nine nan zan bada shaida duk a tafi a rataye ku." D'agowa Lami tayi tana haki tare da fad'in, "To sai me idan mun kashe sun? Ai dama ni na jima da sanin ba k'aunar mu kake ba ni da y'ay'ana. Kana d'aka kana jin duk maganganun da matan nan suke fad'a min, amma baka iya fitowa ba, sai da kaji muna d'aukar mataki tukun zaka fito kana wani maganar banza da wofi, yara, ku cigaba da d'umamun su!" Ko rufe baki bata yi ba, su Nuratu suka cigaba da dukansu aunty Halima. Tsabar azaba aunty Luba kuka take yi tana basu hak'ura amma basu saurara ba. Baba kuwa dogaro sandar shi yayi tare da isowa inda suke ya d'aga sandar ya makawa Lami, sannan ya kuma d'agawa ya bugawa Nuratu da Aina'u, ya d'aga zai bugawa Na'ima, tayi caraf ta rike sandar tare da tura shi baya sai da ya kai k'asa k'afarsa ta markwad'e, Aina'u kuwa d'aga k'afa tayi dagangan ta take yatsun k'afarsa har da murzawa. Wani irin salati Baba ya saki tare da fashewa da kuka yana mai kai hannu kan k'afarsa da Aina'un ta mitstsike. Nuratu kuwa hannu ta saka ta dungure masa kai tare da fad'in, "Wallahi kar ka kuma ka kai hannunka jikina." Da mugun gudu Sarah ta iso wajen ta d'auke Aina'u da gigitaccen mari, sannan ta kuma d'aga hannu ta zabgawa Nuratu da Na'ima mari, sannan ta kuma d'auke Aina'u da mari don a idanunta ta mitstsike k'afar mahaifinsun. "Dan uwarki ni kika mara?" Fad'in Na'ima tana mai nuna kanta, Nuratu kuwa muciyar dake k'asa ta d'auka ta bari Sarah dashi a fuska, nan da nan fuskan ya tashi, bakinta kuma ya kumbura ya soma fidda jini don har ta wajen bakinta dukan ya samu. "Allah ya isa shegiya y'ar iska! Kuma wallahi nima sai na rama!" Fad'in Aina'u tare da yin hanyar pamfo da gudu ta d'auko bokitin da aka cika ruwa aka ajiye tayo kan Sarah wacce ke tsugunne dafe da kuncinta da Nuratu ta buga mata muciya. Sai ji tayi shaaaaa an antayo mata ruwan sanyi tun daga tsakar kanta har cikin pant d'inta. Saurin kallon gefenta tayi inda Baba yake saboda jin wani ajiyar zuciya da ya sauke, sai tayi arba dashi a jik'e shataf, don ba ita kad'ai Aina'un ta jik'a ba har da baban. Baba kuwa kallon Aina'u da Na'ima yayi yana fad'in, "Ni! Ni ko? Ina mahaifinku zaku saka hannu ku ture ni har sai da ba kai k'asa ko? Aina'u ni kika kwarawa ruwan sanyi a jiki har mitstsike min k'afa ko!" Sai kuma ya kalli Nuratu ya ce, "Nuratu ni kike saka hannu kina dungurewa kai kamar d'anki ko?" Ya fad'i hakan yana nuna kansa wasu zafafan hawaye na biyo kuncinsa. "Kuje! Duniya zata koya maku hankali." Ya fad'i yana mai fashewa da kuka tare da k'ok'arin mik'ewa. Sarah kuka take yi sosai ganin yanda jikin mahaifinsu ke wani irin rawa kuma yana kuka sosai. "Lami dan ubanki kizo ki bani abinci yunwa nake ji!" Fad'in Safwan d'an Na'ima. Saurin kallon Lami Na'imar tayi tare da fad'in, "Yanzu Lami dama yaran nan basu karya ba? Haba Lami! Haba!! Wannan wani irin wulak'anci ne. Nafa bar komai na abincin yaran nan." Marairaicewa Lami tayi tare da fad'in, "Yi hak'ura Na'ima, dama fitowa ta kenan domin in d'aura masu abincin sai ga wad'annan fitinannun mutanan sun shigo." Kallon su Na'imar tayi tare da fad'in, "Zaku fita ku bar gidan nan ne ko kuwa sai kun sake ji a jikinku?" Babu wanda yayi magana cikinsu sai ma kama junansu da suka yi suka nufi k'ofar gida. "Sake ni Saratu kije ki bud'e masu kwar gidan ki basu hak'uri ki dawo." Fad'in Baba yana mai share hawayen da suka kasa tsayuwa a idanunsa. Sarah bata sake shi ba sai da ta kai shi wajen barandarsa sannan ta nufi k'ofar gida da gudu, nan tayi arba dasu suna ta kiciniyar bud'e gidan. Hannu Sarah ta kai bayan sun bata hanya ta bud'e masu gidan tare da saurin kai guiwowinta k'asa ta shiga fad'in, "Aunty dan girman Allah kuyi hak'uri da abunda y'an uwana suka yi maku. Ku......" Katseta aunty Bilkisu tayi tare da fad'in, "Matsa mana a hanya mu wuce tun kamun nayi ball dake a nan wajen." Aunty Luba kuwa saurin cewa tayi, "Mai ya kawo maganar Ball kuma! Ke jeki gida mun ji mun yi hak'uri. Bamu hanya mu wuce tun kamun shan ruwan mu a duniya ya k'are. Wannan da muka sha ma, ya ishe mu ishara!" Ta fad'i hakan tana mai bud'e gidan. Karaf gaba d'ayan su suka yi ido hud'u da Farouq dake k'ofar gidan. Da sauri Sarah ta mik'e tana kallonsa, kallon irin na bankwana. Najma kuwa tana arba dashi ta fashe da kuka tare da soma labarta masa abunda ya faru. Wani irin yunk'uri Farouq yayi zai fad'a cikin gidan ganin yanda jini ya b'ata gaba d'aya gaban rigar aunties d'insa da k'annan nasa. Saurin rik'osa aunty Luba tayi tare da fad'in, "Bada yawuna ba wallahi ka shiga cikin gidan na, yaran da har mahaifinsu duka suke yi, to uban waye baza su daka ba a cikin fad'in duniyar nan. Farouq dama inda kake nai man aure kenan? Wallahi, tallahi ko da ace yarinyar nan ba ciki bane a jikinta, kai da ita sai dai a lahira idan da rabon auren a can. Sam wannan gidan ba gidan had'a zuri'a dasu bane." Sarah kuwa da sauri ta fito daga cikin gidan ta zube a gaban Farouq, ko kamun ta bud'e baki ya d'aga hannu ya wanke fuskanta da gigitaccen mari tare da nuna ta da hannu yace............ _08128755583 WhatsApp only dan Allah. Ban [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: _K'ANWAR MATATA_*🦜 _Matar Sayyadee_ _Wattpad @Matar_Sayyadee_ ☀️ *ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*☀️ Page 5 A gigice Sarah ta d'ago tare da dafe kuncinta tace, "Farouuuuq." sai da ta ja sunan cike da tausayi tana kallon fuskansa hawaye na shatata a idanunta. Bakin Farouq har rawa yake yi wajen fad'in, "Kar ki kuskura ki k'ara kiran sunana anan wajen idan ba haka ba karya ki zan yi billahil lazi. Wawuya shashasha mai fuska biyu. Ashe watsatsatsiya ce ke kamar sauran y'an uwanki. Kin cucuni Saratu da har kika saka ni na d'auki dakon sonki a cikin zuciyata har tsawon shekara. Allah ya isa tsakani na dake. Kuma ki sani, ko da ace daga ni sai ke muka rage a duniya, har sai dai na mutu babu aure. Banza budur-bazar." Kuka Sarah ta fashe dashi jin zafafan kalaman da Farouq ke fad'a mata. So take yi ta bud'e baki tace wani abu, amma rawar da bakinta yake yi ya hana ta iya furta ko kalma d'aya. Ji tayi an watso mata papers a fuska. Bin papers d'in tayi da idanu, sai kuma ta kai hannu ta dake rawa ta dauki paper d'in ta bud'e. Waro idanuwa tayi ganin papers d'in scanning d'inta ne har guda uku wanda tayi jiya. Bata iya cewa komai ba don ta san babu abunda zata fad'i wanda zai saka Farouq ya yarda da ita. Tsirtar da miyau Farouq yayi tare da kama hannu aunty Luba yace, "Aunty mu wuce anan kada amai ya kama ni dan Allah. Don ganin fuskan yarinyar nan kawai yana saka ni tashin zuciya." Rintss idanu Sarah tayi tana jin bugun zuciyarta na k'aruwa tamkar yanda jirgin k'asa ke malala gudu akan titinsa. Bata iya tashi a wajen ba sai da ta kwashi mintuna kamun ta mik'e, shima sabida mutanan da suke wucewa suna zund'enta ne ya saka tayi k'arfin halin tashi ta tura k'ofar gida ta shiga. Kai tsaye d'akin mahaifinsu ta wuce duk da maganar da Lami take mata a tsakar gida tana yiwa yaran Na'ima wanka, amma bata kula ta ba. Tana shiga dakin ta zube a k'asa sai da guiwowinta suka bugu da k'asa, amma bata damu da zafin da taji ba. Wani irin kuka mai tsuma zuciya ta fashe dashi tare da fad'in, "Wallahi, tallahi, billahil azim Baba ban tab'a sanin wani d'a namiji a rayuwata ba. Baba namiji da na tab'a bawa kaina. Ban san ta yanda akayi ciki ya shiga jikina ba. Na shiga uku na lalace Baba. Shikenan nima ba zanyi aure ba?" Sunkuyar da kai Baba yayi yana mai zubar da hawayen tausayin Sarah. Dakyar ya iya d'ago kai ya kalleta tare da fad'in, "Saratu da badin manzon Allah SAW yayi hani da d'auke mace a burni a kaita k'auye ba, da nace ki tattara kayanki ki koma _Wamba_ kiyi auren ki acan. Amma kuma Saratu babu ta yanda za ayi ki samu ciki ba tare da d'a namiji ba. Kin tabbata baki tab'a zuwa wani waje ba an baki abun sha kin sha ba? Watak'ila ta nan aka yaudare ki." Girgiza kai Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ban tab'a zuwa party ba. Ko k'awaye bani da balle su gayyace ni." Shuru Baba yayi na kayan tsawon mintuna biyar sannan ya nisa tare da d'agowa ya kalleta yace, "Jeki d'akin ki Saratu. Allah shi yasan abunda ke b'oye. Duk wanda yake k'ok'arin cutar dake, in Sha Allah, Allah ba zai bashi dama ba. Kina gani da idanunki Saratu, kina ganin irin wulak'ancin da mahaifiyarku da sauran y'an uwan ki suke min a cikin gidan nan. Kina tunanin ko ban bud'e baki nayi masu baki ba, Allah ba zai tsine masu ba. Ni dai Sam ban yi sa'ar mace ba. Haka zan koma ga Allah da bak'in cikin Lami da y'ay'anta. Sai da y'an uwana suka yi min gargad'i, amma kuma nayi kunnar uwar shegu dasu. Gashi yanzu ina girbe abunda na shuka." Baba ya k'arisa yana mai fashewa da kuka. Itama Saratu kukan ta fashe dashi tare da fad'in, "Kayi hak'uri Baba. Dan Allah ka cigaba da hak'uri dasu kamar yanda ka saba." Bai d'ago ba ya ce, "Saratu y'ay'an ciki na suke duka na! Wallahi tallahi har mahaifina ya koma ga ubangiji, bai tab'a fad'i na fad'a ba balle har in d'aga in kallesa inyi masa k'unk'unai. Wannan jarabta ce kawai daga Allah!" Shuru Saratu tayi tana mai jin k'una sosai a cikin ranta. "Na'ima y'ay'anta uku babu aure, dan ma Allah yayi wa d'ayan cikawa da yanzu y'ay'anta hud'u duk babu uba. Nuratu biyu, Marfu'a nada d'aya, Hassana kuma tayi y'an biyu, ko wata uku ba'ayi ba da d'aya daga cikin y'an biyun ya koma. Wannan bak'in cikin kawai ya isa ya kashe ni Saratu. Gashi itama autar taku Aina'u tana so ta fad'a cikin halakar da y'an uwanta suke ciki. Yanda idanunta suke a tsatstsaye, wallahi ni sai nake ganin ma kamar sai tace duk abunda y'an uwanta suke yi basu yi komai ba akan wanda zata yi ita." "A'a baba, addu'a zaka yi mata. In Sha Allah hakan ma ba zai faru ba. In Sha Allah Aina'u baza tayi halin su Na'ima ba." Girgiza kai Baba yayi tare da fad'in, "Uhm! To Allah yasa. Amma da kamar wuya. Hatta shi kansa namijin da Allah ya bani tilo, sakarai ne. Tunda shima shaye-shaye babu wanda bai yi da kuma d'aukar kayan mutane. Jiya da daddare, ina jin lokacin da wannan yaron wa yake da suna?" " *_Naliliyo_*" Fad'in Sarah. "Yauwa eh shi! Ina jinsa yana karta adda a k'asa yana zage-zage. Kuma uwar na d'aure masa gindi. Ya Allah idan wani laifi nayi maka kake min wannan jarabawar, Allah na tuba ka yafe min dan tsarkin mulkinka." Da "Ameen." Sarah ta amsa tana mai jin tausayin kansu ita da mahaifin nata. "Tashi kije Sarah. Kije kiyi ta addu'a. In Sha Allah, Allah zai kawo maki mafita. Ki k'addara dama can Umaru ba mijinki bane. Idan kuma mijinki ne, wallahi duk wannan abun da ya faro, babu makawa sai anyi wannan auren." Share hawaye Saratu tayi tare da fad'in, "Nagode Baba. Amma dan Allah idan ka yi min izini, zan koma asibiti domin ganin likita." Sai da ya gyara k'afarsa sannan yace, "Saratu ki bari gobe kyaje. Yanzu ki koma d'akinki ki huta." Mik'ewa Saratu tayi tare da fad'in, "To Baba, nagode Allah ya baka lafiya." Da Ameen ya amsa, ita kuma ta fice daga d'akin. Sanye yake cikin jeans d'in _Secret Circus_ da shirt na kamfanin _Saint Laurent_, sannan ya sanya takalmin _Stuart Weitzman_. Babu abunda ke tashi a jikinsa sai turaren _Imperial Majesty_, kallon kansa yayi a cikin k'aton madubin dake d'akinsa ya saki lallausar murmushi ganin irin kyawu da yayi. Juyawa yayi ya nufi wani katoton showglass wanda ba komai bane a ciki sai mahaukantan expensive sunglasses, wani waje ya danna sai ga glass d'in ya zuge, rabi yayi sama, rabi yayi k'asa. Sai da ya k'arewa glasses d'in idanu sannan ya kai hannu ya d'auko _Bulgari Flora_ wanda duk cikin sunglasses d'insa yana matuk'ar k'aunar wannan. Madannin ya kuma dannawa glass d'in ya rufe sannan ya juya ya koma wajen madubi ya d'auki Microfiber cloth ya goge glasses d'in sannan ya saka a fuskansa. Yanda yayi matuk'ar yi masa kyau, zaka d'auka dan shi kawai aka yi glasses d'in. Sai da ya k'ara kallon kansa from head to toes yaga he's perfectly dress sannan ya d'auki iPhone d'insa a kan bed ya nufi k'ofa ya murd'a ya fito. "Barka da fitowa ranka ya dad'e" Shi gaba d'aya tsorata yayi don bai tsammaci ganinta a k'ofar d'akinsa ba. "Laure! Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un. Wai ni Ibrahim ya zanyi dake ne wai dan Allah? Sau nawa zan fad'a maki ki daina zuwa kina tsayuwa a k'ofar d'akina kamar wata security. Dan Allah, dan Allah Laure ki daina firgita ni. Ni wallahi babu abunda ke tada min hankali da tsoro kamar wad'annan kacakoren hakwaran na...." Tun kamun ya kai k'arshen zancen ta fashe da dariya wanda ya bayyanar da manya-manyan hakwaranta na sama guda hud'u da suka turo suka yi curko-curko a waje. Sam bata iya rufe bakinta ruf saboda hakwaran. "Precious Lord in heaven! Laure bar nan wajen tun kamun na zubar da wad'annan kacakoren hakwaran wallahi." Ja da baya tayi tare da fad'in, "Ni hwa tsaya kaji Ya Khalif (Khalil), Hajiya ce tace nazo nayi kiranka tana can parlor kai take jira. Kuma ni kayi mani wanin (warning) akan kar ba kuskura na kuma shigar maka d'aki kai tsaye. Kuma nayi k'ok'arin danna wanna madannin amma na kasa. Kasan ni d'in ce kamar a duk'e aka haifo ni sabida rashin tsaho." Harara ya maka mata tare da fad'in, "To naji bar nan wajen." Washa bakin ta kuma yi sai da ya matsa baya don da gaske shi hakoran nata tsoro suke bashi. Gaba tayi kad'an, sai kuma ta juyo tare da fad'in, "Nace dan Allah yaya khalif ko zaka d'an sammun wannan turaren naka mai shegen k'amshi anan, ko baka cika min ba wallahi nagode." Ta k'arisa maganar tana mai ciro wata k'aramar kwalba irinta fiya-fiya a k'ark'ashin zaninta. Yunk'urowa yayi kamar zai kai mata duka ta juya a guje ta nufi dogon corridor d'in da zai fitar da kai katoton parlorn gidan. Tsaki yayi sannan ya jawo k'ofar d'akina nasa ya murza key tare da saka key d'in cikin aljihun wandonsa ya soma tafiya majestically har ya iso parlor. Tsaye yaga Laure da mopa a hannunta, maimakon tayi abunda za tayi, sai ta b'ige da kallon katoton tv na bango dake manne a jikin bango. Wani film d'in India mai suna *_Sultan_* ake haskawa d'ai-d'ai inda yake gudu domin kamo jirgin leda. Babu abunda Laure kayi sai kyalkyalewa da dariya. Khalil na k'arisowa ya d'auki remote dake hannun kujera ta jefi Laure dashi a goshi, don Hajiya tayi kiran sunanta har sau hud'u amma film ya d'auke mata hankali. Kuma ita ta zubar da juice d'in da Hajiya ke sha sabida rawar kanta. Saurin susa goshin Laure tayi tare da fad'in, "Laa! Wallahi kuma naji kamshin turaren ka, wata zuciyar tana ce min kai ne ka k'ariso, amma wanna gayen ya tafi da imani na. Dan Allah Hajiya zaki biya min kud'in jirgin inje indiya mu gaisa tare da d'aukar hoto dashi? Na san wallahi zai ji dad'i idan ya ganni. Na san har fim sai mun yi tare in fito a budurwarsa." Harararta Khalil yayi tare da fad'in, "To dan gidan ku matsayin saka ki a cikin keji ana zuwa ana ganin ki ba zaki samu ba, shashasha kaiwa. Za kiyi abunda ke gabanki ko sai na isko ki nan wajen." Marairaicewa tayi tare da fad'in, "Allah sarki yaya khalif. To na rantse maka fad'in k'asar indiya samu mai kyawuna abune mai matuk'ar wuya. Ko kai d'innan da kad'an ka fini kyawu." Zama yayi kuwa da Hajiya yana mai fad'in, "Tabbas, babu shakka. Dama ai samun irin ki a indiya ai sai an tona. Don ko namun dajinsu sun fiki kyawun gani." Turo baki tayi tare da fad'in, "Kina dai jin sa ko Hajiya!" "Kar ma ku soma saka ni cikin shirmen ku. Ke da Khalil dai kamar kuna ganin hanjin juna." Fad'in Hajiya dai-dai lokacin da Maryam matar wan Khalil tayi sallama ta shigo d'akin hannunta rik'e da wani kyakkwar kula. Dai-dai inda Hajiya take ta ajiye kulan tare da fad'in, "Tom and Jerry! Kun soma fad'an naku ko." Kallon kukan da aunty Maryam ta ajiye a gaban Hajiya yayi sannan ya kalli aunty Maryam d'in tare da fad'in, "Ai kin san Allah, sai na kori yarinyar daga gidan nan. Ni da gidanmu amma bani da sakewa. Babu ranar duniya da wannan yarinyar bata tsora tai da muggan hakwaran nan nata." murgud'a baki Laure tayi tare da fad'in, "Halittar Allah kake zagi. Idan ka isa halicci kiyashi anan wajen mu gani. Sai rowar tsiya, d'an turaren da mutum zai baka kad'an cikin kwalba amma ya kiya sabida rowar tsiya. Wallahi Hajiya dai kowa ya san ita d'in hannunta a bud'e yake kamar kasuwar kwari ta Kanon mu. Ko ina kayo rows oho! Kuma Hajiya kice ya bani makulli in tai in gyara masa d'aki." _Mastika gum_ da yake matuk'ar k'aunar ya fiddo daga aljihunsa ya jefa a baki ya hau tauna a hankali yana lumshe idanu. Allah ya had'a wani strong love tsakaninsa da chewing gum. Da yuwa kaga bakin Khalil babu gum a bakinsa. Kuma gaba d'aya chewing gum d'in da yake ci daga waje ake kawo masa. Yasan expensive gum da yawa. Yana biyan kud'in jirgi ya keta hazo kawai domin sayo chewing gum. Kullum cikin browsing yake domin ganin sabon chewing gum d'in da aka yi. Hajiya tayi-tayi har ta gaji akan yi masa fad'a ya daina ci amma Sam yak'i bari. Har hak'ori an tab'a cire masa tsabar cin chewing gum amma hakan bai saka ya daina ci ba. "Dan gidan ku ina yi maka magana shine ka d'auki d'an iskan abun nan da ba tsana ka jefa a baki kana tauna." Tsayawa da taunar yayi tare da fad'in, "Dan Allah Hajiya ki daina saka damuwar uncle Ridwan a zuciyarki. Ya kamata ki saba da riginarsu yanzu. Wai shi so yake na auri Nina, ni kuma da in auri wacce wani namijin ya riga ni saninta, gwara na mutu babu aure. Na tsani mace mara kamun kai. Hajiya Nina fa bata san iya adadin mazan da ta kwanta dasu ba........... 08128755583 🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜 _Matar Sayyadee_ _Wattpad @Matar_Sayyadee_ [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜 _Matar Sayyadee_ _Wattpad @Matar_Sayyadee_ ☀️ *ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*☀️ Page 6 "Ni kai min shuru da wannan zancen banzan naka. Sam Khalil baka k'aunar gudun b'acin raina ko? Kafi kowa sanin su wanene y'an uwan mahaifinku, sam basu raina abun magana. Mahaifin naku ya kwanta dama, amma duk da hakan baza'a bar ni na sarara ba. Menene a ciki idan ka auri Nina d'in. Kuma da kake zancen y'ar iska ce, kai ka tab'a kamata red-handed ne? Nifa bani son sharri da k'azafi." Mik'ewa Khalil yayi tare da fad'in, "I love you Hajiya. Sai na dawo. Ki cewa Laure taje laundry ta kwaso min kayana ta kai d'akinki. Kada ta sake ko wajen k'ofar d'akina taje." Yana gama fad'in haka ya nufi k'ofa. Aunty Maryam sai k'umshe dariyarta take yi ganin irin uban tagumin da Hajiya ta buga tana k'arewa Khalil kallo har ya gama ficewa daga d'akin. Mai do da dubanta ga aunty Maryam tayi tare da fad'in, "Saki, saki dariyarki Maryam." Dakyar aunty Maryam ta iya gimtse dariyar tare da fad'in, "Hajiya ba dariya zan yi ba." Gyad'a kai Hajiya tayi tare da fad'in "Uhm, Maryam ban san mai Ibrahim ya maida ni ba. Gaba d'aya ya mai dani kakarsa. Kina ji a gabanki ina yiwa yaron nan magana amma don tsabar wulak'ancin sai ce min yayi wai wani I lobiyu sai na dawo. Har da bani sak'o in fad'awa Laure. Dani yake zancen. Allah ko yak'i Allah sai yayi aure nan kusa. Idan har yace bai son Nina, ba zan takura masa ba, amma kuma dole ne ya fiddo wacce yake so. Na gaji da zagin da iyayensa suke min a kansa. Shekaru talatin da biyar, yana da aikin yinsa, to uban mai yake jira kuma. Muhalli dai ga b'angarensa nan kullum cikin kwaskwarima da gyararraki yake yi. Yaron sai shegen k'arya da kashe kud'i kamar bai san zafin nema ba. Kina gani akan dank'on da kullum bashi da aiki sai na taunawa kamar tsohuwar karuwa sai yayi takakka ya biya kud'in jirgi har wata k'asar. Zai ci gidansu dani yake zancen." Fad'in Hajiya tana mai jawo kulan ramar dake gabanta ta bud'e ta soma ci. "Hak'uri za ai Hajiya. Addu'ar tagari za kiyi masa ya zab'o tagari a hankali." Rama cike a bakinta tace, "Rabu dashi Maryam. Idan ya kai ni bango, bazawara shikan wawa zan samo masa kuma sai ya aure ta." Dariyar da aunty Maryam keta rik'ewa ta kufce tare da fad'in, "Lallai Hajiya kin so rigima. Tun Khalil na yaro ke kike bamu labari komai sabo yake so. Duk wani abu da wani ta riga sa amfani dashi bai tab'a amfani da abun balle kuma ace matar da zai aura wani ya riga sa auran ta. Lallai Hajiya kin d'auko da zafi. Har na hangi Khalil gashi can da auran bazawara. Kin san Allah Hajiya barin garin nan zai yi baza ki sake ganinsa ba sai an d'ebi shekaru." Rufe kulan Hajiya tayi tare da fad'in, "To ya tafi mana Maryama. Ni na huta ma da magana. Ni da na san haka zai rika jawo min zagi, da ban takura sai ya bar wannan k'asar ya dawo Nigeria da aikin sa ba. Sai shegen kwalliya da fesa manya-manyan turaruka masu shegen k'amshi da tsada, amma duk uban kwalliyar nan abokansa sunce min ko hakoransa y'an mata basu gani a waje. Ni ko ya yake kula da marasa lafiyan oho! Kin tuna wannan yarinyar Salma da ta mak'ale masa daga ya dubata a asibitinsa? Yarinyar arziki har gida nan take zuwa gaishe ni. Amma yaron nan sai da ya koreta ta daina zuwa. Kai ni lamarin Khalil na ban takaici. Ni ko dai aljana ce ta aure shi?" Aunty Maryam gyara zama tayi tare da fad'in, "Hajiya babu wata aljana lokacine kawai bai yi ba. Amma idan yayi shi da kansa zai kawo maki budurwarsa har gida." "Allah ya amsa Maryamu ko na huta da mita da kiraye-kirayen wayar dangin ubansa." Fad'in Hajiya. B'angaren Sarah kuwa, ko da ta koma d'akinsu, can k'uryan gado ta hau ta nannad'e cikin bargo sabida wani zazzafan zazzab'i daya lullub'eta. Can kamar kusan mintuna talatin, lokacin zazzab'in ya k'aru sosai taji shigowar Hassana wacce dawowarta kenan daga yawon ta zubar d'inta. Zama tayi a bak'in gadon ba tare da ta lura da Sarah dake kwance cikin bargo ba can k'arshen gadon. "Honey wai kana nufin baka gaji dani ba? Mu kwana muna abu d'aya amma ace ka kasa gajiye dani." Wani dariya Hassana ta saki har da kwanciya flat tana kallon ceiling ga dukkan alamu taji dad'in amsar da wanda take waya dashi ya bata. Don har da wani mik'a tayi. "Kamar ka sani kuwa. Wallahi duk ka tada min da sha'awata. Kasan fa muryanka kad'ai ma kawai na sakani haniniya." D'an shuru tayi sai kuma tace "Allah ko! To ban mintuna uku kacal zan kira ka yanzu." Tana gama fad'in haka ta yanke wayar tare da mik'ewa ta cire kayanta gaba d'aya har da P&B. Kasancewar idanun Sarah a kulle suke, bata san abunda Hassanar ke aikatawa ba. Sai bayan kamar mintuna goma ta jiyo nishi sama da kuma maganganun batsa. A hankali ta bud'e idanunta tare da d'an d'ago kanta da take jinsa kamar zai tsage. Gabanta ne yayi wani irin mugun fad'uwa ganin yar tata tsirara da wani abu mai shape d'in al'aurar namiji yana wani irin k'ara ita kuma tana turawa tare da gogawa a gaban nata. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel! La'ilaha illallah Muhammadur Rasulillah!! Allahumma arji'ini fi musibati." A razane Hassana ta d'ago ta kalli Sarah, ita kuma Sarah saurin kawar da kai tayi saboda ganin al'aurar wanda take video call dashi ta cikin wayar don lokacin da Hassanar ta razana wayar ta fad'i kuma ba kifawa tayi ba. Mugun tsaki Hassanar taja ganin Sarah ce, don ta d'auka wani abun tsoro ne. D'aukar wayarta tayi tare da fad'in, "Baby mu cigaba. Wannan banzan K'anwar tawa ce da nake baka labari ce." Fad'in Hassana. Sarah kuwa duk da rashin k'arfin jikinta da kuma sarawar da kanta yake yi, haka nan ta mik'e ta dafa bango ta fice daga d'akin don baza ta iya wannan mummunar ganin ba. Tana fitowa daga d'akin wani irin yunk'uri ya taso mata na amai, cikin sakwanni biyu ta soma kakari tana kelaya wani irin amai mai mugun wuya kasancewar ba wani abun kirki bane a cikinta. Don hatta ruwa idan tasha dawowa yake yi. Ruwan bohol ko kuma fanta mai mugun sanyi ne kawai yake iya d'an zama a cikinta. Shima kuma sai tana sha tana hutawa. Lami, Aina'u da Nuratu na tsakar gidan amma babu wanda ya iya mik'ewa yazo domin taimakonta. Tsabar yanda take amai d'in hatta fitsari zuba yake yi a jikinta. Tun tana amai a duk'e har ta zauna dirshan a k'asa tana bubbuga kanta da hannunta amma babu wanda ya tanka balle ya kawo mata d'auki. Nuratu ma Wak'a ta soma yi na habaici da isgilanci. Azaba ya ishi Sarah, bata san lokacin da ta soma d'aga hannu tana fad'in, "Babu mai taimako nane? Lami ki taimaka min dan girman Allah. Nuratu, Aina'u, ku taimaka min zan mutu, wallahi mutuwa zanyi." Lami ce ta soma magana, "Dan ubanki ki mutun mana. Kowa da kike gani a cikin gidan nan kud'insa yake cirewa ana yi masa hidima. Kema da kin cire mugun hali sa son kin fad'i uban cikin dake jikinki, da yanzu shalele kike a cikin gidan nan. Amma tunda kince mugun hali kika saka a ranki, mugun halin ya cece ki." Tana gama fad'in haka ta sab'a Yabo d'an wajen Na'ima a baya, shi kuma ya tak'ark'are ya ganna mata wani arnan cizo a tsakiyar bayanta sakancewar baya k'aunar goyo, ita kuma Lami burinta tayi ta kima sa a baya don Na'imar tace tana kula dashi sosai. Don duk cikin y'ay'anta, tafi k'aunar Yabo. Zafin cizon ya saka Lami tafiya ta gaba a gigice ta had'a kai da wani dogon k'arfe dake kan barandar d'akinta sai da goshinta ya k'umu kuma yayi k'ulu k'atoton. Dariya Aina'u ta fashe dashi tare da fad'in, "D'an bura uban yaro! Kema ai Allah ya k'ara Lami. Kin fi kowa sanin Yabo bai k'aunar goyo amma sabida naiman suna kika kima shi a baya. To ai ga babbar Yabo nan kin samu a kan goshin ki." Kwance zanin Lami tayi ta sauke sa tare da dungure masa kai, aikuwa take ya b'are baki ya fashe da kuka. Da sauri Lami ta saka tafin hannu ta rufe masa baki tare da fad'in, "Na shiga uku zai jawo min jidali da safen nan. Yi hak'uri d'an lele. Yanzu zan shiga d'aki na d'auko maka sweet mai tsinke." Sarah kuwa dake jibge a k'asa tana ta faman bugun goshi kamar zata fita hayyacinta, kira sunan Aina'u ta shiga yi tana fad'in, "Aina'u dan girman Allah ki taimaka min, Wallahi zan baki dubu d'aya." Mere baki Aina'u tayi tare da fad'in, "Now you're talking. Amma kuma yasin dubu d'aya tai min kad'an, dubu biyu zaki bani." Dai-dai nan Baba ya fito da sandarsa a hannu ya kalli inda Sarah take tausayinta ta kashe sa a tsaye, mai da dubansa yayi izuwa wajen Aina'u tare da fad'in, "Aina'u yanzu taimakon y'ar uwar taki ce sai da kud'i?" Mik'ewa tayi tare da fad'in, "A'a fa Baba! A'a! Walleh gwamnati ta hana aikin banza. Ta biya yanzu taga aiki da cikawa. Don ma ta samu zan karb'i kud'in in taimaka mata. Duk cikin gidan nan waye zata bawa kudi ya amsa don taimakonta idan ba niba. Idan zata bada 2k ta bayar a taimaka mata, idan kuma baza ta bada ba, ta sha zamanta." Girgiza kai Baba yayi tare da fad'in, "Ungo nan gashi ni zan cika mata. Karb'i ki taimaka mata ta gyara jikinta ku tafi asibiti." Wani kallo tabi baban dashi tare da fad'in, "Oh wai har da su zuwa asibiti? To lallai kud'i ya k'aru. Ni na d'auka taimaka mata kawai zanyi ta d'auraye jikinta ta koma d'aki! To kud'in ku dubu uku, idan kuna dashi, a cika aiki, idan babu, in koma in zauna." Shuru Baba yayi yana kallon Aina'u, sai kuma ya mayar da dubansa ga Sarah yaga halin da take ciki. Sai ya koma d'akinsa, bayan kamar mintuna biyu ya fito tare da fad'in, "Zo Aina'u, ga dubu uku kamata ki taimaka mata ta wanko jikin nata sai ku tafi asibitin." Mik'ewa Aina'u tayi don har ta zauna tare k'arisawa ta amshi kud'in sannan tace, "Ko kai fa d'an tsoho. Tsohon nan kud'i fa gare ka naga alama!" K'ala bai cewa Aina'u ba, sai ma kallon Sarah da yayi tare da fad'in, "Allah ya baki lafiya." Sannan ya juya ya shige d'akinsa. Aina'u kuwa, k'arisawa wajen Sarah tayi ta kamata ta mik'e ta kaita har gindin pamfo ta wanke mata jiki. "Aina'u taimaka min da fanta mai sanyi a shago dan Allah. Akwai naira dubu d'ari biyu, ki d'auki d'ari biyun ki sayo min." Matsawa baya kad'an tayi tare da fad'in, "To ki tabbata shima akwai kud'insa daban. Don yasin ban aikin banza." Sarah na nishi tace, "Naji ji ki sayo min. Idan muka fita zan cire kud'i a POS sai in biya ki." Ba tare da Aina'u tace komai ba ta juya ta nufi d'akinsu Saran ta d'auko d'ari biyun ta fito ta nufi waje don sayo Fantan. Sarah kuma da kyar ta iya jan jiki ta koma d'akin. Sai da ta d'an yi jimm kamun ta tura k'ofar ta shiga saboda bata son ganin abunda ta baro a cikin d'akin. Alhamdulillah Hassanar ta gama abunda take yi, kwance ma same ta tana kwasar barci. Kai tsaye wajen wardrobe ta nufa ta canza kayan jikinta ta zauna a k'asa tana nishi. Don wani irin juwa take gani. Aina'u ce ta hankad'o labulen ta shigo d'akin tare da dire mata kwalbar fanta a gabanta mai sanyi. "Nagode Aina'u!" Shine abunda Sarah ta fad'i tare da kai kwalbar bakinta ta cire kwankwalatin ta hau shan fantar. Kad'an tasha taji kamar za tayi amai sai ta mayar da kwankwalatin ta rufe ta ajiye a gefe tare da mik'ewa ta d'auki hijjab ta saka ta cewa Aina'u, "Muje Aina'u. Zamu d'an tsaya a shagon Nura zan cire kud'i, taimaka min ki d'au min jakata." Jakar ta d'aukar mata suka fita daga d'akin. "Lami mun tafi." Fad'in Aina'u. "To sai kun dawo. Ki tabbatar kin karb'i kud'inki." Wani murmushi Aina'u tayi tare da fad'in, "Kin san wannan dole ne Lami, sai dai mun dawo d'in." Ita dai Sarah bata ce komai ba ta nufi hanyar k'ofar gida. Sai da suka biya ta shagon Nura Sarah ta cire 11k ta bawa Aina'u 1k na sayo mata fanta da tayi sannan suka tsari napep suka shiga. "Ina zamu je Hajiyoyi?" Fad'in mai napep. "Ka kai mu wani asibiti mai kyau da kasan sun san aikin su sosai." "An gama Hajiya!" Fad'in mai napep d'in. Sun d'an yi tafiya mai tsayi mai napep d'in ya tsaya a bakin wani katafaren asibiti kamar ba a k'asar Nigeria ba, a saman asibitin an rubuta *_Khalilullah Specialist hospital_* "Kai! Kana hauka ne da zaka kawo mu wannan asibitin? Shin baka san tsadar asibitin bane?" Fad'in Aina'u. Ko kamun mai napep yace wani abu, Sarah ta sauko daga keken tare da zaro dubu d'aya ta mik'a masa ya cire kud'insa ya bata canji. Sai a sannan ya kalli Aina'u tare da fad'in, "Ai gani nayi kunyi kalar asibitin shiyasa na kawo ku nan d'in." Harara ta zabga masa tare da bin bayan Sarah da har ta kusa shiga cikin gate d'in. Sai da ta d'an had'a da gudu tukun ta isketa tare da fad'in, "wannan wani irin iskanci ne haka zaki wuce ki barni? Don kin samu na rakoki ko? Gobe rana ce ai!" Ba tare da Sarah ta kalleta ba tace, "Yau d'in ma kud'i nane dana Baba ya sakaki taimako na, gobe ma idan kika ga kud'in, biyo ni za kiyi." Aina'u bata kuma cewa komai ba har suka shiga reception d'in asibitin. Gaba d'aya numfashinsu ya kusa d'aukewa sabida tsabar had'uwar da asibitin yayi. Aina'u kuwa baki bud'e take bin lungu da sak'on asibitin da kallo. "Baiwar Allah dan Allah Ina zan je na bud'e file?" Fad'in Sarah bayan ta tab'o wata nurse da tazo wuce wa. Da hannu nurse d'in tayi mata nuni da wajen sannan ta wuce. Sarah kuwa k'arisawa tayi tare da yin sallama ta gaishe da saurayin da ta gani a wajen sannan tace, "File nake so a bud'e min. Ina son ganin doctor." Wani file ya d'auko tare da kallonta ya mik'a mata wani k'aramar paper tare da fad'in "Je ki biya wannan a wajen cashier sai ki dawo min da receipt d'in." Karb'a tayi tare da fad'in, "Ina ne wajen dan Allah?" Shima da hannu ya nuna mata wajen. Tana zuwa ta mik'a masu papern, matar dake wajen ta d'ago ta kalleta tare da fad'in, "Kud'in ki dubu bakwai. Don kinyi sa'a babban doctor ne zai duba ki. Bud'e file dubu biyu, sai kud'in ganin likita dubu biyar. Shuru Sarah tayi, domin idan ta bada 7k saura 2k a jikinta. Da mai zata biya kud'in scanning? Don ta san tabbas za ayi mata scanning. Aina'u ce tazo wajen ta tsaya, Sarah tayi saurin cewa, "Dan girman Allah Aina'u aramin dubu hud'un hannunki, idan mun koma gida zan baki." Ciro kud'in Aina'u tayi ta mik'a mata tare da fad'in, "Amma fa ki sani, wallahi sun haifu. Ba dubu hud'u zaki mayar min ba." Komai Sarah bata ce mata ba. Sai mik'awa cashier kud'in tayi tare da mik'a mata receipt ita kuma ta karb'a ta koma wajen wanda ke bud'a file ta mik'a masa. Sunanta ya tambaya tare da age, adresss da kuma phone number sannan ya nuna mata inda zata je tare da shaida mata ya turawa doctor file d'inta ta computer. Consultant room taga an rubuta a sama. Har zata murd'a sai kuma ta d'an tsaya jim ta juyo ta kalli Aina'u dake zaune a kan kujera ta d'aura k'afa d'aya a kan d'aya tana danna waya. Ajiyar zuciya ta sauke tana fatan ace wannan karon idan an dubata ace wani ciwo ne daban a jikinta ba ciki ba. Kwankwasa k'ofar tayi sannan ta tura ta shiga. Wani gaurayayyen sanyi Ac taji ya ratsata mai tafe da wani k'amshi mai shiga zuciya da b'argon d'an Adam. Har sai da Sarah ta lumshe idanu tana mai fatan ace ta cigaba da jin wannan k'amshi har abada saboda yanda yayi mata wani irin dad'i da salama a cikin zuciyarta. Ba tare da ya d'ago kai ba yayi mata nuni da kujerar dake gaban teburinsa. Zama tayi tana mai wasa da hannunta. Shi kuwa doctor wani rubuce-rubuce yake yi a jikin wani file. Ya d'auki mintuna uku kamun ya ajiye file d'in ya zare glasses d'in dake fuskansa sannan ya juyo da computer yayi danne-danne tare da fad'in, "Saratu Nuhu ko?" Ya fad'i hakane tare da juyowa ya kalleta dai-dai lokacin da itama ta d'ago kai idanunsu suka sark'e dana juna. A mugun firgice Sarah ta mik'e tare da tura kujeran da take kai baya gabanta na wani irin mugaba kamar yanda dak'ik'an agogo yake bugawa. Bakinta na rawa tace, "kkkk.... Kai!" Shima da matuk'ar mamaki ganinta ya furta, "Ke ce?" Da sauri ta juya ta fita daga office d'in har tana k'ok'arin kifawa tayi saurin dafe bango. Aina'u dake charting ganinta kawai tayi ta fito kamar wacce aka biyo ta tayi waje da sauri. Ita ma mik'ewar tayi tana fad'in, "Sarah! Sarah!! Lafiya?" Dai-dai lokacin ya fito shima ya bita a baya, Aina'u na ganin haka ta rufa masu baya amma suna isa wajen gate d'in suka ganta har ta hau napep, napep d'in ya wuce. Juyawa Aina'u tayi ta kallesa tare da fad'in, "Lafiya? Mai ka mata? Ko HIV kuka gano tana d'auke dashi?" Wani irin kallo Khalil yayi mata tare da fad'in, "Ni ko dubata ban yi ba. Kin santa ne?" Ya tambaya duk da kuwa yana ganin kamannin jini a fuskar Aina'un. "K'anwarta ce ni. Ni ke binta." Ajiyar zuciya ya sauke tare da fad'in, "Ko zaki shigo mita muje in sauke ki sai in san gidan naku daga nan." Wani kallon up and down tayi masa, ganin babu k'arya sai tace, "To amma kai mai yasa kake son zuwa kaga gidan mu?" Kai tsaye ya bata amsa da, "Saboda ina son had'uwa da yayarki. Auren ta nake son yi. Na jima ina naimanta sai yau Allah ya had'a ni da ita." Wani dariya rainin hankali Aina'u ta kwashe dashi tare da fad'in, "Lallai! To ka ko san abunda ya kawota nan asibitin? To bud'e kunnuwanka da kyau in fad'a maka. Ciki ne da ita har na tsawon watanni uku, kuma zuwa tayi nan domin a zubar mata da cikin. Mu gidan mu bamu aure. Kar ka wahalar da kanka don baza ka tab'a samun Sarah matsayin mata ba. Ko da yake, ban san tsananin son da kake mata zai saka kayi auren ragowar wani ba. Ni na barka lafiya." Tana gama fad'in haka tayi gaba. Shi kuwa Khalil mutuwar tsaye yayi kansa na wani irin juyawa jin wai wacce yake matuk'ar k'auna ce take d'auke da juna biyu. Tirr ya auri mazinaciya a rayuwarsa. Idan kuma hakan ta faru, daran ranar da ya fahimci haka, a ranar zai korata gidansu. Don ya san zama da zargi babu aure, shi kuma ba zai tab'a iya auren yarinyar da zuciyarsa zai rik'a kokwanto a kanta ba. Har ya fara tafiya ya tsaya cak tare da maimaita abunda Aka Aina'u tace masa cikin zuciyarsa "Ciki wata biyu? Kai ba zai tab'a yuwuwa ba." ya fad'i a bayyane tare da bin bayan Aina'u da sauri............. _AKWAI FA SAURAN CHAKWAKIYA A GABA SOSAI. DON HAR YANZU BA'A SOMA LABARIN BA. SHIN TA YAYA SARAH TA SAMU CIKI BAYAN TAYI RANTSUWA DA ALLAH BATA TAB'A SANIN D'A NAMIJI BA, WANENE DOCTOR D'IN DA SARAH TA GANI HAR TA TSORATA DA GANINSA TA GUDU BA TARE DA TAYI ABUNDA YA KAITA ASIBITIN BA? MAI DOCTOR KHALIL YAKE NUFI DA YACE BA ZAI YUWU BA ACE SARAH NA D'AUKE DA CIKIN WATA BIYU? A INA YA SAN SARAH, KUMA MENENE ALAK'ARSU? WACECE LAMI? WANENE BABA NUHU? SHIN MAI MAI K'ANWAR MATATA YAKE NUFI? TUN FA DA AKA SOMA LABARIN BAMU GA MATAR BA, BAMU GA MIJIN BA, BARE KUMA K'ANWAR. HMM WALLAHI Y'AR UWA KAR KI BARI AYI WANNAN LABARIN BABU KE. DOMIN AKWAI CHAKWAKIYA MAI ZAFI A CIKINSA._ *_A NAN NA KAWO K'ARSHE. FREE PAGES, GA MAI BUK'ATAR KARANTA LITTAFIN K'ANWAR MATATA, SAI YA TURO D'ARINSA BIYAR ZUWA WANNAN ASUSUN BANKIN 0592412800, ZULFAU SAID GT BANK, SAI KI TURO DA SHAIDAR BIYANKI DA WANNAN NUMBER 08128755583_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MAZA* 🦜 *7* Da sauri yabi Aina'u yana kwala kiran "Ke! Ke!! Dan Allah tsaya." Aina'u najin muryansa ta k'ara sauri don bata fata ko cikin mafarkinta wannan doctor d'in ya kasance mijin Sarah. Cikin sauri ta tari Napep ta fad'a ciki. Cak Khalil ya tsaya yana mai bin napep d'in da idanu har ya daina ganinsu. Ya jima tsaye a wajen yana jin wani abu na tasowa a k'asan zuciyarsa. Hannu ya kai ya yamutsa gashin kansa kamun yayi wani irin tsayuwa tare da tura hannunsa cikin aljihun wandonsa yana kallon sama. Can kuma ya juya da sauri tare da komawa office d'insa. Yana jin ana gaishesa amma ko juyawa bai yi ba balle ya amsa. Direct wajen computer ya nusa ba tare da ya zauna a kan kujera ya d'an rankwafo yayi danne-danne jikin computer tare da saurin d'aukar wayarsa ya kwashi numbers d'in Sarah dake rubuce a file d'inta sannan ya kashe computer d'in ya zira wayarsa cikin aljihu ya fita daga office d'in bayan ya rufo k'ofar ya saka key. Wayarsa ya fiddo ya danna ya lalubo numbern doctor Kamal tare da shaida masa ya bar asibiti yazo yayi replacing d'insa akwai wani abun gaggawa da zai je ya aiwatar. Yana gama waya da doctor Kamal ya fita ya nufi parking space. Wata arniyar mota *_Pagani Zonda HP Barchetta_* that worth 17 million ya shiga tare da yi mata key ya bar asibiti. Sai da ya hau titi kuma sai ya rasa inda zai je. Juya kan motor yayi ya nufi Sokoto road inda gidan su yake. A wani k'atoton mansion ya danna horn, cikin sauri mai gadi ya wangale gate shi kuma yayi shiga tare da yin parking anan harabar gidan ba tare da ya isa parking space ba. Fitowa yayi daga cikin motar ya shiga cikin gida da sassarfa, babu kowa a parlor do haka kai tsaye ya haura sama ya saka key ya bud'e d'akinsa tare da shiga ya maida key d'in ya rufe k'ofar sannan ya nufi wajen wani wawaken waje da aka rufe sa da tinted glass ya danna wani abu glass d'in ya zuge. Wata jaka ya fiddo y'ar karama mai hannun chain kalar pink. Sai da ya jujjuya jakar a hannunsa sannan ya k'arisa wajen gado ya zauna a bakin gadon tare da zuge zip d'in jakar ya zazzage a kan gado. Abunda ya fara cin karo dashi shine d'an kunne guda d'aya kalar bak'i hook d'insa ya b'alle. Murmushi yayi tare da maida d'an kunnan cikin jaka sannan ya d'auki kud'in dake kan gadon wanda a cikin jakar ya fad'o. Dubu d'aya ne da d'ari bakwai, Sai turaren soft da lipgloss. Sune kawai abunda yake cikin jakar. Mai da komai yayi a cikin jakar tare da kwantawa rigingine yana tuno wasu abubuwa da suka wuce a cikin idanunsa kamar yanzu komai ke faruwa. Cikin sauri kamar an tsikaresa ya tashi zaune tare da zaro wayarsa k'irar Samsung mai matuk'ar kyau da tsada yayi dialing number Sarah da ya d'auka. Sai dai tayi ringing har ta gaji ba'a d'auka ba. Ya kira yafi sau goma amma babu amsa. Tsaki yayi tare da jefar da wayar a kan gado. Yana bala'in bak'in cikin ya kira waya ba'a d'aga ba. Shi a k'a'ida sau d'aya yake kira bai k'ara na biyu. Mirginawa yayi tare da mik'a hannunsa ya jawo drawer ya tura hannu ya d'auko _Mastika Gum_ ya b'are ya watsa a baki ya hau tauna yana mai lumshe idanu. B'angaren Sarah kuwa tun da ta hau keke napep gabanta ke wani irin bugawa sai da ta saka hannunta ta dafe k'irjinta don ji take yi kamar zuciyarta zai faso k'irjin ya fito. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Shine abunda ta dunga maimaita tun tana yi cikin zuciyarta har ya soma fitowa fili. Matar dake kusa da ita ta kalleta tare da fad'in, "Baiwar Allah lafiya?" Sarah bata bata amsa ba sai cewa mai napep d'in tayi, "Tsaya, tsaya zan sauka anan." Parking mai napep yayi ita kuma ta sauko gaba d'aya bata cikin hayyacinta. Mik'a masa d'ari biyar tayi tare da juyawa ta soma tafiya ko karb'an canji bata tsaya yi ba. Shi kuwa mai napep yaja napep d'insa yayi gaba. Sarah kuwa tafiya ta cigaba dayi a k'asa tana kalle-kalle. Tayi tafiya mai nisa kamun Allah ya had'a ta da wani asibiti a gabanta. Hamdala tayi tare da nufa cikin asibitin kai tsaye. Bud'e kati tayi sannan ta zauna domin jiran layi yazo kanta. Kamun layi yazo kanta har wani zabura take yi tana mik'ewa saboda tsabar k'aguwa. Sai da mutane takwas suka ga likita sannan aka kira sunanta. Cikin sauri har tana tuntub'e ta fad'a cikin office d'in a burkice. Doctor yayi saurin d'agowa ya kalleta, ganinta a hargitse sai yayi mata nuni da wajen zama tare da fad'in, "Have a sit." Zama tayi da sauri dama kuma abunda take jira kenan. K'ura mata idanu doctor Alpha yayi kamun yace, "Young lady, how can I help you?" Ai kamar Sarah jira take sai ta fashe da kuka, bai yi yunk'urin hanata ba, sai ma jingina da yayi da jikin kujera yana kallonta, sai da tayi mai isarta sannan ya mik'a mata tissue ta karb'a ta goge hawayen. A karo na biyu doctor da ya kasance bayarabe kuma bai jin hausa sannan kuma a haife ya haifi Sarah, yace, "My daughter what's the problem? Feel free to tell me exactly what's wrong with you. Let's have heart to heart conversation." Ajiyar zuciya Sarah ta sauke tare da fad'in, "Sir can I ask you a question?" Hannunsa biyu ya d'aura akan desk d'in dake gabansa ya bata full attention d'insa tare da fad'in, "You can ask any question. I'm here for you." Sai da ta sunkuyar da kai sannan tace, "Doctor can someone get pregnant without sexual penetration?" Sai da doctor yayi wani murmushi sannan ya kalli Sarah tare da fad'in, "What's your name young lady?" Ba tare da ta d'ago ba tace, "Sarah, Saratu Nuhu." Murmushin ya k'ara yi a karo na biyu tare da fad'in, " *_Pregnancy happens when a sperm fertilises an egg, which can happen even if you've not had sexual intercourse (penetration)._* During vaginal penetrative sex (where the penis enters the vagina) semen can be ejaculated. Semen is the liquid produced during ejaculation and contains millions of sperm. As soon as the penis is erect, (before ejaculation), a liquid called pre-ejaculate or "pre-cum" is produced. This liquid can contain thousands of sperm. The ovaries release 1 or more eggs (ovulation) 12-16 days before a period starts. The sperm enters the body through the vagina, then travels through the cervix and womb to the fallopian tubes, where the egg is usually fertilised (conception). The egg can be fertilised by sperm contained in semen or pre-ejaculate." Kallon doctor Sarah kawai take yi alamar bata fahimce sa ba. Ganin hakan a fuskanta, sai ya sake yin murmushi tare da fad'in, "Here is the explanation, *_It is possible to get pregnant if sperm comes into contact with the vagina, if for example:_* *_your partner ejaculates very close to your vagina your partner's erect penis comes into contact with your genital area (vagina or vulva)_* *_The risk of getting pregnant in this way is very low because sperm can only live for a short time outside the body._*" A tsorace Sarah ta mik'e tsaye, shima doctor mik'ewa tsayen yayi tare da fad'in, "Hey calm down. Have a sit let talk." Da kyar ta iya zama tare kallon doctor babu kyaftawa. Shima doctor zama yayi tare da fad'in, "Sarah are you pregnant?" Ai fad'in haka da yayi Sarah bata san lokacin da ta mik'e da sauri ba ta fice daga office d'in har da had'awa da gudu. Shima doctor da mamaki yabi bayanta yana kiranta amma bata jo juyo ba ta bar asibitin. Tana fitowa ta nufi asibitin _ZAKARIYYA_ dake magajin gari. Cikin sa'a ita ce mutum na biyu da doctor ya gani, tana shiga tayi ta soma rab'e-rab'e har sai da doctor Usman ya d'ago yana kallonta har ta naimi waje ta zauna. Bai ce mata komai na tsawon mintuna biyu, ita kuma sai wasa da jelar hijjab d'in jikinta take yi. "Me ke damun ki?" Taji saukar muryansa a cikin kunnanta har sai da hantar cikinta ta kad'a. A hankali ta d'ago hawaye shab'e-shab'e a fuskanta. Doctor Usman bai yi mamaki ba don idan da sabo sun saba da ganin haka a wajen y'an mata sabon shigan fara iskanci idan sun yi ciki ko kuma masu fama da cutar HIV sabon shiga, ko kuma irin shagwab'ab'b'un yaran nan masu kuka idan basu da lafiya. "Me ke damun ki?" Ya sake tambaya karo na biyu. Bud'e baki Sarah tayi zata fara magana bakinta ya soma rawa sai ta kuma fashewa da kuka. Bai yi yunk'urin hanata kukan ba, ita da kanta tayi mai isarta sannan tace, "Doctor da gaske ne mace na iya d'aukar ciki ba tare da namiji ya kasanceta ba?" Cikin zuciyar doctor Usman yace, "Anzo dai-dai wajen!" Amma a zahiri sai kallonta yayi tare da fad'in, "Ciki gare ki?" Gyad'a masa kai tayi tare da fad'in, "Duk asibitin da naje sai ace ina d'auke da juna biyu, kuma ni wani namiji bai tab'a kusantata ba." Mik'ewa doctor yayi tare da fad'in, "Tashi ki hau wancen gadon zanyi maki scanning." Babu musu Sarah ta hau kan gadon tare da d'age rigar jikinta sama tana mai lumshe idanu hawaye na zirarowa daga k'urmin idanunta. _AquaSonic_ (gel d'in da ake zubawa a ciki kamun scanning) ya zuba mata tare da soma yi mata scanning. Kallon fuskanta dake a rufe yayi tare da mayar dashi kan screen d'in computern dake nuna b'aro-b'aro tana d'auke da ciki. Bai fad'a mata ba sai mik'awa mata tissue yayi tare da fad'in, "Goge jikinki ki koma ki zauna ina zuwa." Gaban Sarah na fad'uwa ta goge cikin nata tare da sauka daga kan gadon sannan ta koma inda ta taso ta zauna tare da had'a kai da guiwa tana addu'a a zuciyarta Allah yasa wannan karon an gano babu ciki a jikinta. Dawowa Doctor yayi hannunsa d'auke da paper d'in da yayi printing ya zauna sannan ya kalleta na kusan second goma sannan yace, "Saratu Nuhu!" A firgice ta d'ago gabanta na bugawa. Kallon paper d'in hannunsa yayi sannan ya kalleta tare da fad'in, "Scanning machine ya nuna kina d'auke da ciki har na tsawon sati a jikinki. Fad'a min gaskiya tsakaninki da Allah ko na iya taimakonki, ta yaya kika yi ciki?" Kuka Sarah ta fashe dashi sosai tare da soma bubbuga k'afarta a k'asa tana jujjuya kanta. "Ba kuka za kiyi ba, fad'a min gaskiya za kiyi ko hakan zai iya sakawa na taimaka maki." Jin haka ya saka Sarah ta tsayar da kukanta cak tare da fad'in, "Wallahi tallahi doctor ni ba y'ar iska bace." Murmushin yayi don idan da sabo ya saba da jin haka a wajen wasu y'an matan. "Naji, fyad'e aka yi maki?" Girgiza kai tayi tare da fad'in, "Bai kai ga jikina ba wallahi. Bai kusanceni ba." Shuru yayi yana kallonta, sai can kuma yace, "Bari na amsa maki tambayar farko da kika min lokacin da kika shigo. Cewa kika yi, Doctor da gaske ne mace na iya d'aukar ciki ba tare da namiji ya kasanceta ba? To amsarki ita ce, dagaske ne mace na iya d'aukar ciki ba tare da d'a namiji ya shiga cikin jikinta ba. Amna idan har mace zata bari namiji yayi wasa da al'aurarsa a jikin nata al'aurar har ya kawo, ma'ana ya fitar da maniyi a kan al'aurarta, to tabbas zata iya samun ciki sai dai kuma sai dai the risk is very low sabida kwayoyin halittar dake cikin maniyi zasu iya rayuwa ne na k'ank'anun lokacin a wajen jikin mace, amma a cikin jikin mace zai iya d'aukar kwanaki biyar zuwa shidda kamun su mutu. Idan har mace ta soma jinin al'ada (Menstruation) to a ranar idan ta fara k'irge, d'aya, biyu har zuwa kwana goma sha hud'u, to a ranar take samar da kwai, kuma a wannan lokacin she's not safe, namiji na kusantarta, zata samu ciki. Kuma sannan kar ki manta na fad'a maki sparm zai iya rayuwa a cikin jikin mace har na tsawon kwana biyar, hakan na nufin idan aka kusanceta 11, 12, 13, ko ba'a kusanceta 14 ko 15 ba zata iya samun ciki. Shiyasa yake da tsananin kyau mace ta rik'e kanta ko da wasan banza kada ta bari wani namiji yayi da ita idan ba mijinta ba. Amma ban san mai yake janku ku y'an mata ba kuke fad'awa tarkon *_Samarin Shaho_*! Su babu abunda suke so sai jikinku, kuma da sunyi amfani daku a k'arshe yar daku zasu yi sune su naimi ta kirki su aura." Kuka sosai Sarah keyi, bata san ta yanda za tayiwa doctor bayani ba, sai cewa kawai tayi, "Nagode doctor da bayanin da kai min." Sosai yaji tausayinta, amma har ga Allah babu wani abunda zai iya yi mata. Kuma ba zai iya bata shawara a kan ta zubar da cikin ba. Sarah kuwa mik'ewa tayi tana jin kanta kamar zai tsage tsabar yanda yake mata azabar ciwo, gashi irin bayanin da wancen doctor d'in yayi mata, shi wannan doctor d'in yayi mata. Sabida haka babu wani buk'atar sake zuwa wani asibiti domin tabbatarwa. Doctor Usman na kallonta har ta fice ta bar cikin office d'in. Ko da ta fito, a wajen asibitin ta samu wani d'an dandamali ta zauna saboda jirin dake d'ibanta sosai. Ga wani uban yunwa dake kwakwular cikinta. Had'a kai da guiwa tayi tana tariyo abunda ya faru kwanaki goma sha takwas da suka wuce................ *_DAN DARAJAR GIRMAN UBANGIJI KAR KI FITAR MIN DA BOOK. WALLAHI TYPING AKWAI MATUK'AR WAHALA DA CIN RAI. KI TAIMAKA MIN Y'AR UWA!_* *_DUK MAI SONA TA HANYAR SAYAN BOOK D'INA KAWAI ZAI GWADA MIN, TURA D'ARIN KI BIYAR KI SHA KARATU CIKIN SALAMA BISA WANGA ACCOUNT 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK SAI KI TURA DA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA 08128755583_* *_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 8* Kuka take yi sosai har da shashshek'a tana jin ina ma bata zo duniyar ba balle wannan abun ya same ta. Taso ta kasance ta daban a cikin y'an uwanta, sai gashi ita ma an rubuto a cikin k'addararta akwai samun ciki ba tare da aure ba. Sosai ta tsani rayuwar da y'an uwanta suke yi wanda mahaifiyarsu ita ce ta d'aura su a kan wannan turba saboda son abun duniya. Da ana canza mahaifiya da tabbas ta jima da canza nata mahaifiyar. Mahaifinta ne ya fad'o mata a rai, ta san tabbas shi zai fahimceta, to amma wanda zata aura fa? Tuno hakan ya saka ta kuma rushewa da kuka. "Shikenan ni ba'a rubutomin aure a nawa littafin ba. Na shiga uku! Ni wallahi da nayi ta zama a cikin gidan mu ina kwasar bak'in ciki, gwara na tafi *_Wamba_* wajen dangin mahaifina nayi zama na a can. Ban damu da ko k'auye bane ko birni! Buri na in ganni a d'akin mijina ina bautar ubangiji!" Sarah ta fad'i a bayyane tare da mik'ewa ta soma tafiya a k'afa kasancewar layuka shidda ne ya rabasu da inda take. Kan titi _Kasuwar gwari_ ta mik'e tayi ta tafiya har ta iso _Jos road_ sannan tayi k'asa kasancewar can k'asan Jos road d'in suke. Ga zafin rana, ga kuma zazzab'in dake damunta da matsanaici ciwon kai wanda ya ninku sakamakon kukan da tasha. Tana isa k'ofar gidansu gabanta ya yanke ya fad'i ganin motar y'an sanda da kuma y'an sandar a kwar gidansu ga kuma uban cincirundon samari da y'an mata har da wasu matan auren layin da suka fito suna baiwa idanunsu abincin. Tana isowa gaba d'aya idanun jama'a ya dawo kanta. "Yauwa, ga d'aya karuwar ta dawo. Da gani ba gida ta kwana ba. Ai mu dai Allah bai had'a mu da makwaftar kirki ba. Ni dama tashin su za ayi daga unguwar nan don muna da y'ay'a mata dake tasowa kada suga abunda suke yi suma su soma jin sha'awar yi." Fad'in wata mata tana hararar Sarah. Sarah kuwa kutsawa tayi cikin mutanan nan ta shige cikin gidan. Turus ta tsaya ganin Baba a tsakar gida dafe da goshi gaban rigarsa duk jini yana kuka, gefe kuma su aunties d'in Farouq ne da k'annansa maza da mata a gefe sai girgiza suke yi suna fad'in wallahi baza su yarda ba. Nuratu, Aina'u, Na'ima, da Hassana kuma a waje d'aya suna fad'in babu inda zasu je kuma babu uban da ya isa fitar dasu zuwa police station. Lami kuwa sai fad'i take, "Ko kotu za'a je, aje ban jin tsoron uban kowa, sune suka biyo mu har gida da fitina, mu kuma muka kare kanmu." Baba dake kuka ya kalli officer d'in da yake magana cikin lalama akan su Lami su biyosa zuwa station yace, "Bawan Allah d'an sanda, ni na baka umarnin ka tafi dasu da tsiya, idan sunk'i kuyi amfani da k'arfin ku na hukuma ku fitar dasu, amma kuma banda wancen da ta shigo yanzu, don babu hannunta a kan duk abunda ya faru." Ya k'arisa maganar yana nuna Sarah. Police d'in kuwa, bai saurari maganar Baba, sai bada baki yake yi, don babu yanda za ayi ya nuna power ya fitar dasu Nuratu zuwa police station domin Hassana budurwarsa ce, Marfu'a kuma yanzu haka ma tana d'akinsa a wajensa ta kwana jiya. Hassanar ya kira gefe, da kyar taje tana wani cin magani. Sun jima suna magana, a yanda yake lallaminta, zaka d'auka uwarsa ce ita. "To naji, amma wallahi baza mu wuce mintuna ashirin ba a can." Da sauri yace "Na maki alk'awarin haka." Sai da taja tsaki sannan ta koma tayiwa y'an uwanta magana sannan suka fita su duka banda Sarah da ta jingina da bango abun duniya duk ta ishe ta. Ta gaji da matsalar mahaifiyarta da y'an uwanta. K'arisawa tayi wajen Baba duk da jirin da take ji domin taimaka masa ya tashi. Rik'e mata hannu yayi tare da fad'in, "Bari zan iya tashi Saratu. Kema naji jikin naki da zafi sosai. Ya aka yi Aina'u ta rigaki dawowa daga asibitin, ko fad'a kuka yi?" Sai da ta taimaka masa ya mik'e tukun sannan tace, "A'a ba fad'a muka yi ba, nice na baro ta a can asibitin." Baba bai k'ara cewa komai ba sai nufa wajen pamfo da yayi ya wanke goshinsa sannan ya nufi kan baranda ya zauna a kan tabarma tare da fad'in, "Saratu, kiyi hak'uri duk laifi nane da na kasa zab'a maku uwa ta gari. Y'an uwana sun nuna basu son na auri Elizabeth (Lami) amma na nace ni ita nake so sabida yanda ta nuna min k'auna a wancen lokacin. Ban tab'a d'auka Elizabeth za tayi min butulci a rayuwata ba." Kallonsa Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ka bani labari, ta yaya ka had'u da Lami har kuka yi aure, kuma mai yasa danginka suke fushi da kai har yanzu? Bamu san kowa naka ba, haka suma basu san mu ba. Dangin Lami ma babu wanda ya san mu, muna bamu san kowa ba sai aunty Rose Merry wanda Lami tace mana y'ar uwarta ce." Sunkuyar da kai Baba yayi tare da fad'in, "Rose Merry ba y'ar uwar mahaifiyarku bace, asali ma itace mai d'aura mahaifiyarku akan turba mara kyau. Taso mahaifiyarku ta koma addininta da ta baro, amma kuma sai mahaifiyarku ta nuna ita tana son addinin musuluncin da ta karb'a." Sarah tace, "To amma Baba Lami bata sallah, bata azumi, duk wani abu na musulunci Lami bata yi. Kuma a hakan ne take cewa tana son musuluncin?" Ajiyar zuciya Baba yayi tare da fad'in, "Nima na jima ina wannan zargin Saratu. Anya kuwa mahaifiyarku bata koma addinin kiristancinta ba kuwa? Domin duk ranar lahadi da sassafe take barin gidan nan, kuma bata dawowa Sia wajajen d'aya ko biyu." Shuru Sarah tayi tana tuno wata rana da mahaifiyar tasu ta dawo daga inda take zuwa duk ranar lahadi, sai ta ganta d'aure da wani zani mai hoton k'atoton cross a jiki, zanin biyu ne, da ta d'aura d'aya a k'ugu, sai ta d'aura wani a sama kasancewar dama farar rigar less ce a jikinta. Ga wani k'aramin Bible a kan gado. "Lami! Wannan wani irin kaya ne haka a jikinki irin na y'an coci?" Saurin kallon jikinta Lami tayi tare da fad'in, "Kai, kin ganni nan d'azu da na fita, shine wata mota tayo kaina, garin na kauce mata sai na fad'a cikin kwata, kuma dama kusa nake da gidan auntynku Rose Merry, shine ta bani wad'annan kayan na saka. Yanzu ma Allah-Allah nake in cire su." Sarah ta kalli Bible d'in tare da fad'in, "Wannan kuma fa Lami!" A harzuk'e tace, "Ke dan ubanki uwata ce ke? Kin cika ni da tsinannun tambayarki. To Rose Merry d'in ce ta bani na ajiye mata a nan anjima idan zata wuce gida zata biyo tanan ta karb'a." Kallonta Baba yayi tare da fad'in, "Lafiya Saratu kike dogon tunani haka?" Sauke ajiyar zuciya Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ina tuna wani abu ne. Ina ji a jikina Lami ta koma addinin kiristanci." Daga nan ta kwashe duk labarin abunda ya faru wancen ranar ta fad'a masa. Da mugun mamaki Baba ke kallon Sarah, sai kuma ya girgiza kai tare da fad'in, "Babu abunda Lami ba zata iya aikatawa ba. Lami ta daina bani mamaki sai dai tsoro. "Baba mai ya same ka a goshin ka?" Fad'in Sarah ganin har goshin ya tasa. Sai da ya shafa wajen sannan yace, "Lami ce taje jifan y'an uwan saurayinki da suka yi cincirundo domin d'aukar fansar abunda suka yi shine ta same ni a goshi, kuma kin san budar ba ta roba bace. Don ma Allah ya tsare." Cike da tausayi Sarah yace, "Allah ya k'ara tsareka Baba." Da ameen ya amsa tare da kallonta yace, "To Sarah ya ake ciki? Mai likitocin suka ce wannan karon?" Fad'in Baba yana kallon Sarah data sunkuyar da kai tana hawaye. "Baba akwai cikin?" Sai da gaban Baba ya fad'i da jin haka, amma ya d'aure tare da fad'in, "Kuma Saratu har yanzu baki gano bakin zaren ba?" Shuru Sarah tayi don bata san ta inda zata fara yiwa Baba bayani ba. Hawaye ne kawai ke zubowa daga idanunta yana d'iga a kan tabarmar da suke kai. "Saratu ni mahaifinki ne. Kuma kin san duk fad'in gidan nan babu wanda na shak'u kuma nake jinsa har cikin raina cikin y'ay'ana idan ba ke ba. Kar ki damu, zan fahimceki. Zan kuma yi maki nasiha matsayina na mahaifinki kuma in karb'i k'addararki da hannu bibbiyu. Sai dai ba zan tab'a jin dad'i ba idan har ke da kanki kika kai kanki wajen wani namijin bayan kin yi mi alk'awarin baza ki tab'a yin irin rayuwar da y'an uwanki suke yi ba." Kuka Sarah ta fashe dashi tare da fad'in, "Na rantse da girman ubangijin halittu ban tab'a kaiwa wani namijin jikina ba domin yayi amfani dani. Wallahi, tallahi duk abunda ya faru tsausayi ne Baba. Ban san ta yanda zanyi maka bayani ba Baba. Amma wallahi ban tab'a karya maka alk'awarin da ba d'auka ba." Ko kamun Baba yayi wata maganar wani yaro ya kwad'o sallama tare da fad'in, "Wai ana sallama da Sarah a waje. Wai dan girman Allah ta fito mintuna biyar kawai!" *_Kuyi hak'uri da wannan, anticipate a long page tomorrow _* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* *_ZULFA'U SA'EED IBRAHIM AKA 👉MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 9* Kallon yaron Sarah tayi, sannan ta maida kallonta izuwa wajen Baba tare da fad'in, "To kuma wanene? Na san dai Farouq ba zai sake dawowa k'ofar gidan nan domin ni ba." Baba yace, "Kije kiga ko wanene ke kiran naki. Allah yasa dai lafiya." B'ata rai Sarah tayi tare da fad'in, "Da kuma so nake na kora yaron yaje yace bazan zo ba." Girgiza kai Baba yayi tare da fad'in, "Ba'a haka Saratu. Ba'a wulak'anta d'an Adam. Kije kiga ko wanene." "Je kace tana zuwa!" Sarah ta fad'i tare da mik'ewa don har yanzu tana ganin jiri-jiri ga kuma yunwar dake kwakwular cikinta. D'aki ta koma ta canzo hijjab d'in jikinta ta saka wani brown wanda ya kai mata har guiwa sannan ta fito tana dafa bango ta nufi waje. Baba na kallonta har ta fice kamun ta ya sunkuyar da kai yana tsiyayar da hawayen tausayinta. Sarah kuwa tana fita taci karo da wata arniyar motar da bata tab'a ganin irinta ba k'irar *_Aston Martin Vulcan_* kalar ash mai duhu. Ba ita kad'ai ba, hatta jama'ar layin fitowa suka yi suna kallon motar. Shi kuwa _Khalilullah_ sai da ya gama k'are mata kallo ta cikin tinted glass d'in motar sannan ya bud'e tare da ziro k'afarsa d'aya. Farar kyakkwar k'afar ta soma bi da kallo kamun taga ya fiddo da gangan jikinsa, tun daga d'an yatsan k'afarsa take kallo har ta sauke a kan fararan manya-manyan idanunsa masu matukar d'aukar ido. Wani irin lumshe idanu tayi jin daddad'an k'amshin turaren *_Imperial Majesty_* da ya bugi hancinta. Sosai take matuk'ar son k'amshi musamman a yanayin da take ciki. Folding hannunsa yayi tare da jingina a jikin motar yana kallonta. Bud'e idanu tayi a hankali ta kuma sauke idanunta a kansa karo na biyu tayi saurin b'ata fuska tare da k'ok'arin juyawa zata koma cikin gida. Cak ta tsaya sakamakon jin abunda yace, "Kul! Kar ki sake ki bar wajen nan idan ba haka ba zan baki mamaki." Juyowa tayi ta watsa masa harara tare da bud'e baki za tayi magana shi kuma ya d'aura d'an yatsansa a kan bakinsa tare da fad'in, "Ssshh! Ko kalma d'aya." Yana fad'in haka ya tako cike da isa ya iso inda take a tsaye tare da fad'in, "Kin yi missing d'ina ko?" Karo na biyu ta kuma watsa masa harara tare da d'an matsawa baya kad'an jin kamar zasu had'e da juna ga kuma wannan mayataccen k'amshin nasa dake naiman sumar da ita a tsaye. "Zan kwakwule idanun nan naki idan suka kuma hararata." Kallon gefe Sarah tayi tare da fad'in, "Menene matsalar ka dani ne? Mai yasa ka addabi rayuwata? Dan girman Allah ka kifa daga rayuwata in samu salama. Ka barni da bala'in daka jaza min dan girman Allah!" Sarah ta k'arisa maganar tare da fashewa da kuka. Kallonta ya dunga yi ba tare da ya ce mata tayi hak'uri ta daina kuka ba. Sai da tayi mai isanta sannan ya saka hannu cikin aljihu ya fiddo da wani d'an ma daidaicin handkerchief ya mik'a tare da da fad'in, "Come on, wife those tiers of yours!" Karb'an handkerchief d'in tayi tana mai watsa masa harara sannan ta kai kan fuskanta, kamun ta share hawayen sai da ta zuk'i k'amshin turaren tukun. "To bani abuna." Ya fad'i yana mai mik'a mata hannunsa. Mik'a masa tayi tare da fad'in, "Ai dama bani na rok'a ba." Amsa yayi tare da yin murmushi ya maida cikin aljihunsa sannan yace, "Kin matuk'ar bani wahala Sarah! Kin san kuwa irin naiman ki da nayi?" Kamar ta shak'e masa wuya haka take ji, wani tsaki tayi tare da fad'in, "Idan abunda ya kawo ka wajena kenan, juya ka bar k'ofar gidan nan yanzu. You're not welcome here. Out of my sight. Kuma yanda ka tarwatsa min farin ciki, kai ma baza ka tab'a samun farin ciki ba." Maimakon maganganunta su bashi haushi, sai yayi wani irin murmushi mai sauti tare da fad'in, "Idan har bazan tab'a samun farin ciki ba, to kema baza ki tab'a samu ba Sarah. Domin an halicceki ne domin ni kawai. Farin cikina yana tare dake, haka kema farin cikinki yana tare dani ne. Sannan kuma ina so ki saka wannan maganar da zan maki yanzu cikin kwakwalwarki, ba ai min tsaki! Kar ki sake." D'ago jajayen idanunta tayi zata saki masifa sai ga keke napep ya tsaya a bayan motar _Khalil_. Aina'u, Nuratu, Na'ima da Hassana a baya, sai Lami dake zaune a gaba ta rik'e k'arfe. Fitowa suka yi gaba d'ayansu suna k'arewa motar _Khalil_ kallo. Lami ce ta riga kowa magana tare da fad'in, "Kun ga wata arniyar mota! Wallahi tunda uwata ta haife ni ban tab'a ganin mota mai kyawu ba irin wannan." Na'ima ta kalli Nuratu tare da fad'in "Kamar fa *_Aston Martin Vulcan_* nake gani." Nuratu tace "Ya kike fad'i da kaya a jikinki! Ai kuwa tabbas ita ce wallahi." Zagayawa suka yi domin su k'arewa motar kallo dakyau. Idanunsu ya sauka akan Sarah dake kallonsu tana addu'ar Allah yasa kar su nuna halinsu _Khalil_ ya raina ta. Sai dai Addu'arta bata karb'u ba domin da sauri Lami ta k'arisa wajen tana k'arewa _Khalil_ da Sarah kallo. "Eh lallai! To yau dai Allah ya tona asirinki kin kawo sa har k'ofar gidanku. Wato saboda kin ga bama gidan ko?" Sai ta maida dubanta ga _Khalil_ tare da fad'in, "Samari kalle ni nan, nice mahaifiyar Sarah." D'an sunkuyar da kai _Khalil_ yayi tare da risinawa yace, "Sannu da zuwa Mama, ina wuni, mun sameku lafiya?" Shan mur Ki tayi tare da waigawa ta k'ara k'arewa motar _Khalil_ kallo sanna ta maido dubanta ga _Khalil_ d'in tare da fad'in, "Bafa lafiya ba. Domin dai yanzu haka daga police station muke ni da sauran y'ay'ana gasu nan kana kallonsu." Tayi nuni da su Nuratu da suka k'ariso suma. Kallo d'aya yayiwa Aina'u ya shaidata, kuma itama ta gane sa. Kau da kai tayi tana tsaki cikin zuciyarta. Shuru _Khalil_ yayi yana sauraran Lami. Ita kuma ta cigaba, "To ni bama duk wannan ba, ashe kai ne uban cikin dake jikin Saratu, amma don tsabar iskanci da mugunta irin nata, sai tak'i fitowa ta fad'a min gaskiya don kar a dangwali arzikin dani, to yau dai Allah yayi sai mun yi foureyes da kai. Don haka akwai list d'in da nake rubutawa in ajiye sabida irin haka. Don fisabilillahi bazan iya ciyar da y'ay'ana kuma in ciyar da nasu y'ay'an ba. A k'a'ida ta zama cikin gidana, a cikin su kaf...." Tayi nuni da su Nuratu tare da cigaba da fad'in, "Duk wacce tayi ciki to kawo saurayin take gidan nan muyi tsada dashi domin d'awainiya da cikin, bayan ta haihu kuma, ni can cigaba da kula da babyn, cinsu, wankansu da duk wani abun da suke buk'ata. Don haka kai ma zan baka wannan list d'in, na ganka da maik'o a jikinka, don haka list d'inka daban ne." Kuka Sarah ta fashe dashi tare da durk'ushewa a wajen. Lami kuwa da baki ta nuna ta tare da fad'in, "Munafuka! Kiyi kukan jini ma. Wallahi sai na kawo masa list d'in nan kuma sai anci arzikin dani." Turo baki Aina'u tayi tare da watsawa Lami harara tace, "Sai kuma aka ce maki shi yayi mata cikin? To bashi bane!" Ta k'arisa maganar a tsawace. _Khalil_ kuwa mutuwar tsaye yayi yana kallon Lami da sauran y'ay'anta. So yake yaji ana tashinsa ana fad'a masa cewar mafarki yake yi, amma sai tsungulin cinyarsa yake yi ta baya, da yaji zafi sai ya tabbatar fa lallai ba mafarki bane. "Wannan wani irin gida ne na kawo kaina?" Fad'in _Khalil_ cikin zuciyarsa, amma a zahiri bakinsa ko motsi ya kasa yi sai bin Lami da idanu yake yi. Zuciyarsa na tabbatar masa da cewar Lami ba ita bace mahaifiyarsu Sarah. Ga dai y'ay'a nan kyawawa Allah ya bata, amma kuma babu tarbiya. "Jira ni, bari na shige na kawo maka list d'in." Fad'in Lami tare da shigewa cikin gidan. Na'ima kuwa, kallon Sarah tayi tare da fad'in, "Lallai Sarah kinyi babban kamu babu k'arya! Ina jiran nawa kason a cikin jira. K'anina a bata nawa kason ta kawo min." Fad'in Na'ima tare da shigewa. Nuratu kuwa sai kallon motar take yi ita da Hassana suna Santi. Don har hotuna suka yi a jikin motar kamun suka shige cikin gidan. Aina'u kuwa wani kallo tabi Sarah dake duk'e a k'asa tana kuka tayi tare da jan dogon tsaki ta kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Baka dai ji warning d'in da nayi maka ba kenan? Kana wahalar da kanka ne. Don tabbas gidan mu ba'a aure." Tana gama fad'in haka ta fad'a cikin gidan. _Khalil_ ya jima a tsaye mamaki kamar ya kashe sa kamun ya duka ya kalli Sarah cike da dakewa yace, "Mik'e.!" Yanda yayi maganar cike da command ya saka bata san lokacin da ta mik'e tsaye ba. Jiri ne ya kwashe ta tayi baya zata fad'i yayi saurin tarota ta fad'o jikinsa dai-dai lokacin da Lami ta fito hannunta rik'e da wata doguwar paper. Wani dariya tayi tare da fad'in, "Kaiii jama'aa! To ai da shigowa kuka yi daga ciki sabida idanun jama'a. Ka san fa unguwar nan an saka mata idanu." Wani irin kallo ya jefi Lamin dashi, don wani irin tsanarta yaji ya darsu cikin zuciyarsa. "Ungo amshi nan!" Fad'in Lami tana mai mik'a masa paper d'in. Da kamar ba zai amsa ba, sai kuma ya mik'a hannu ya amshi paper d'in yana kallon cikin idanunta. "Sai na ji sak'on ka, kuma da kanka nake son kazo." Tana gama fad'in haka ta juya ta koma ciki. Da idanunsa da suka rikid'e suka koma jazur yake kallon Sarah tare da daga mata wani gigitaccen tsawa yace, "Mai kike nema? Nace mai kike so da baza ki iya fad'a min ba? Mai yasa kika min haka? Mai yasa kika bawa wani kanki Saratuuu??" Bakinsa har rawa yake yi don har hasaso yanda abun ya kasance yake yi a idanunsa. Kuka Sarah ta fashe dashi don sosai ta tsorata dashi. "Ke! Ba kuka nace kiyi min ba, bayani zaki yi min. Uban wa yayi maki ciki?" Yanda yake maganar da k'arfi da kuma tsananin b'acin rai sai ya sanya jikin Sarah soma wani irin rawa tana kallonsa. "Ki bar kallo na ki bani amsa. Waye kika bawa budurcinki?" Bata san lokacin da ta bud'e baki tace, "Na rantse da girman Allah babu namijin da ya tab'a sanina matsayin mace." Wani kallo ya watsa mata tare da fad'in, "Ke nan karya ko kuma ince k'azafi aka miki." Da k'arfi kuma cike da tsoro tace, "Eh ina da ciki kuma uban cikin......." Bai bari ta k'arisa ba ya fizgi hannunta da k'arfi tare da nufar inda motarsa yake yayi. Da dannu d'aya ya bud'e gaban motar tare da jefa ta ciki ya kunne sannan ya zagaya ya koma mazaunin driver tare da shiga yayiwa motar key, "Ina zaka kai ni? Ka bud'e min mota in fita. Na shiga uku mai zaka min?" Wani irin kallo keep quiet yayi mata tare da jan motar ya figeta a guje ya bar layin. Kuka sosai Sarah keyi tana fad'in, "Stop the car I'm begging you. Dan girman Allah ka tsayar da motar nan inyi maka bayani. Kar ka cutar dani a karo na biyu bawan Allah! Ka dubi girman Ubangiji! Idan har baka da y'ay'a, kana da k'annai ko kuma y'ay'an y'an uwa. Dan Allah ka mai dani gidan mu." "Quite!" Ya fad'i da mugun k'arfi tare da taka wani irin burgi dai-dai gate d'in asibitinsa. Sai da Sarah tayi gaba ta dawo ta buge guiwarta. Kallon asibitin tayi a firgice, sabida tsananin rud'ewa bata gane asibitin ba, ta d'auka hotel ne. "Na shiga uku ni ka mai dani gida dan Allah!" Ko kallonta bai yi ba sai ya danna wani mahaukacin horn mai kashe kunnuwan mai sauraro. Da mugun sauri mai gadi ya bud'e gate d'in shi kuma ya danna hancin motar ciki tare da naiman waje yayi parking tare da fitowa daga cikin motar ya zagaya ya bud'e side d'in da Sarah take ya bud'e ya fizgo hannunta. Hankali tashe take kallonsa tare da, "Na rok'e ka da girman ubangijin ka barni na koma gida." Bai saurareta ba sai jan hannunta da yayi zuwa cikin asibitin. Nurses da idanu suka bisu ganin yana janta tana ita kuma tana kuka. Dai-dai nan doctor Kamal ya fito daga wani office daban. Da idanu shima ya bisu don kallo d'aya yayiwa Sarah ya gane itace wacce tazo tana kuka tana fad'a masa is bata san ta yanda aka yi tayi ciki ba, bayan kuma sau uku yana tura ta yin scanning kuma yana ganin cikin. Mamaki yake yi sosai ta ina _Ibrahim_ ya santa. Kai tsaye office d'in da yake mallakinsa ya bud'e tare da tura Sarah ciki sannan ya shiga ya kallo k'ofar tare da murza key. Yanda gaban Sarah ke bugawa da k'arfi har ana iya ganin hakan ta gaban hijjab d'inta sabida yanda yake d'agowa. Nuni yayi mata da gadon da yake duba marasa lafiya tare da fad'in, "Kwanta a can!" Ja da baya Sarah tayi tare da fashewa da kuka tace, "Bazan Kwanta ba, wallahi bazan kwanta ba ko zaka kashe ni." A fusace yace "Ni kike fad'awa haka?" Ya fad'i hakane yana mai matsowa, sai kawai ji tayi ya d'agata cak tare da d'aura ta a kan gadon. Yunk'urawa tayi zata sauko ya danneta da hannunsa guda d'aya tare da zuba mata tsinannun idanunsa yace, "Na rantse da ubangijin da ya busa min numfashin kika k'ara yunk'urawa da niyyar saukowa sai na maki abunda har ki mutu baza ki manta ba." Sarah na jin haka ta sadak'ar tare da komawa ta kwantar da kanta ta rintse idanunta hawaye na silalowa daga k'urmin idanunta. Gani take yi kamar tarihine zai maimaita kansa. Bata k'ara tabbatar da haka ba sai da taji hannunsa yana yaye doguwar rigar dake jikinta zuwa cikinta. Da sauri ta rik'e hannunsa da k'arfi ba tare da ta yunk'uro ba tana mai fashewa da kuka. "Sake min hannu!" Ya kuma fad'i da k'arfi. "Kayi hak'uri! Kayi hak'uri!! Kayi hak'uri d'an girman Allah!!!" Shine abunda Sarah tayi ta maimaita. Shi kuwa _Khalil_ ko sauraronta bai yi ba sai ma zame pant d'inta da yayi k'asa tare da ware mata k'afafunta. Wannan karan ta yunk'uro ya maida ta da k'arfi sai da bayanta ya bugu tare da tura yatsarsa d'aya ciki, hakan yayi dai-dai da wani irin ihu da Sarah ta kwala da uban k'arfi. K'ara k'ok'arin tura yatsar yayi cike da mamaki a karo na biyu. Wannan karan gaba d'aya Sarah ta d'ago tana fad'in, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Zare hannunsa yayi tare da jawo Vaginal Examination lamb ya haska wajen sosai. Cikin da tsananin mamaki yake kallon fuskanta bayan ya d'agota. Tausayinta sai ya rufe shi tare da dana sanin abunda yayi mata yanzu. Ja mata pant d'in yayi sama tare da kwantar da ita flat ya zuba mata _AquaSonic_ gel sannan ya soma scanning cikin. Wani mugun ajiyar zuciya ya saki ganin ga ciki nan b'aro-b'aro ya nuna a jikin screen d'in computern. "Tashi ki zauna." Ya fad'i politely. Mamaki ne ya cika Sarah jin yanda yayi mata magana a sanyaye. Babu musu ta tashi ta zauna tana kallon tiles d'in dake shimfid'e a office d'in still her heart is beating soo fast. Sauko da ita yayi tare da kai ta kan kujera ta zauna. A gabata ya duk'a yana kallon fuskanta tare da fad'in, "Sarah hakan na nufin cikin nan dake jikinki, nine ubansa?" *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: *KANWAR MATATA*🦜 *PAGE 10* Kuka Sarah ta fashe dashi tare da fad'in, "Tun da na taso nake tsan-tsan da jikina. Bana k'aunar irin rayuwar da y'an uwana suke yi. Abun yana mun ciwo sosai a zuciyata, hakan ya saka na d'auki alwashi in Sha Allah babu wani d'a namijin da zai sanni matsayin y'a mace, sai mijin da ya biya sadaki ya aure ni. Amma ka rusa min tsari, ka cuce ni kayi min ciki. Ka jefeni da bak'in fentin da ba zai tab'a goguwa ba a rayuwata. Aure na saura sati hud'u, na dad'e ina burin zama matar aure, amma ka rushe min wannan burin, ka jefa ni a sahun sauran y'an uwana masu tab'o a goshi. Yanzu mai zan ce da wannan d'an idan ya fito duniya. Ta yaya zan yi masa bayani idan ya tambayeni ina mahaifinsa. Tabbas ka aikata abunda kace zaka aikatan, dama wancen ranar kace min sai ka min abunda har abada ba zan tab'a mancewa ba, kuma tabbas har abada bazan mance ba, kuma wannan abu zai ta bibiyata har mutuwata. Mai nayi maka bawan Allah? Mai yasa zaka min wannan cutar? Shin baka da k'anwa ne? Idan wani yayi mata abunda kayi min, ya zaka ji a zuciyarka? Baka tunanin Allah zai iya rama min abunda kayi min a kan y'ay'anka! Duk abunda kayi sai an......" Bai bari ta k'arisa ba ya saka tafin hannu ya toshe mata baki tare da k'ureta da idanu kamar zai fashe da kuka. "Nayi maki rantsuwa da girman ubangijin daya halicceki, ya halicceni da duk abunda yake cikin duniya, wallahi, tallahi ban tab'a zina ba, ba d'abi'ata bace. Na bar abunda ya faru tsakanina dake matsayin K'addara ko kuma ince maki jarabawa. Sarah tun lokacin da wannan abun ya faru, ina dai rayuwa ne kamar ina cikin farin ciki amma kuma a bad'ini abun ba haka bane. Shaidan ne da kuma zafin zuciya ya rinjayeni. Amma ni banda niyyar cutar dake. Ke shaida ce a wancan ranar da niyyata shine cutar dake, duk da na fahimci ke d'in cikakkiyar budurwace, da ba zan kyaleki ba sai na ratsa jikinki. Allah yayi sai nayi ajiya a cikin shiyasa har na samu natsuwa a wajen jikinki. Ki yafe min Saratu! Ki yafe min tabbas na b'ata maki record. Amma ina so ki saka cikin ranki, wallahi tallahi tun bayan da abun nan ya faru Allah ya jarabceni da zazzafar soyayyarki, kuma nayi maki alk'awarin sai na share maki hawaye na cika maki burinki na zama matar aure. Ni nan _Ibrahim Khalil Nasuruddeen_ zan aureki in killaceki a cikin gidana. Zan taya ki rainon d'anmu ko y'armu har ya fito duniya, bayan nan kuma ko sati baza ki k'ara a gidanku ba zan aureki." Mik'ewa Sarah tayi tare da fad'in, "Bana fatan ka kasance matsayin mijina. Domin ban san a matsayin mai zan rik'a kallonka ba. Cuta dai ka riga ka gama cutata. Ka b'ata min record. Idan har na aureka zan rik'a kallo kamar ba don Allah ka aureni ba. Kaje kayi rayuwarka nima nayi tawa. Kaje ka samu y'ar masu kud'i da asali dai-dai kai, nima kuma idan ina da rabon auren a duniya, Allah zai had'a ni da dai-dai ni." Da sauri _Khalil_ yasha gabanta tare da fad'in, "Kar ki min haka Sarah, dan Allah kar ki hukuntani ta haka. Wallahi tallahi, Allah shine shaida na akan irin k'aunar da nake maki. Dan Allah don't reject me Saratuuu." Gitta shi tayi tare da fad'in, "Y'ay'an masu kud'i zasu iya yin komai saboda suna da wanda ya tsaya masu, ko da kud'in su zasu iya taka kowa kuma ya taku. Na san idan kaso yau ba zan k'ara kwana a duniya ba, sai dai ina rok'onka da girman ubangijin ka fita daga harkata, kar ka k'ara kusanto inda nake ko kuma ka nuna ka sanni. Idan kayi min haka, wata k'ila in iya ji a zuciyata zan iya yafe maka." Kallonta ya dunga yi yana jin k'una cikin zuciyarsa, "Sarah rayuwarki a hannuna take da zaki ce idan naso ba zaki kwana a duniya ba yau? Dan Allah kar ki k'ara wannan maganar. Da mai kud'i da talaka duk d'aya ne a wajen ubangiji. Ke baki san talaka yafi mai kud'i kwanciyar hankali ba. Bama wannan ba, kin san da cewar idan Allah yaga dama sai ya kwace dukiyar da ya bawa mai kud'in ya bawa talaka har sai wannan mai kud'in ya dawo yana naima k'ark'ashin talaka. Dani dake bamu da wani bambamci Sarah. Dan girman ubangijin ki gafarceni kar ki min azaba da rashin amincewarki." Kau da kai Sarah tayi tare da fad'in, "Bud'e min k'ofa in wuce gida, don idan zamu wuni mu kwana mu kuma k'ara kwana amsa ta d'aya ce a gare ka. Kaje ka naimi dai-dai da kai." Wani abune yazo ya tokare wuyarsa, tun da yake a duniya bai tab'a furtawa wata mace Kalmar so ba a rayuwarsa, sai dai shi ba zai iya k'irga adadin matan da suka furta masa kalmar ba. Y'ay'an masu kud'i, turawa har da indiyawa, amma bai tab'a bawa d'aya daga cikinsu full attention d'insa ba balle har soyayya ta k'ullu. Amma wai yau gashi gaban k'aramar yarinya yana rok'onta akan ta soshi tana wasa da zuciyarsa. Ajiyar zuciya ya sauke, miskilancinsa suka hau kai tare da jik'imarsa, wani irin kallon gefen idanu ya bita dashi tare da fad'in, "Haka kika ce? So be it! Amma kuma ni zan tabbar maki babu wannan macen da _Khalil_ zai bud'e baki yace yana sonta ta k'i. Kamar yanda d'ana yake kwance a cikin mahaifarki, to haka _Khalil_ zai kasance cikin zuciyarki, sannan kuma wallahi babu wannan namijin da ya isa ya shiga gonar _Khalil_. Idan har ba _Khalil_ zaki aura ba, to zo rubuta ki ajiye babu ke babu aure!" Yana gama fad'in haka ya koma ya zauna ya soma danne-danne cikin computer yayi kamar ya manta tana cikin office d'in. Sarah kuwa da ta gaji da tsayuwa sai ta sulale k'asa ta zauna tana mai da numfashi. Da gefen idanu ya kalleta, sai kuma ya d'ago gaba d'aya tare da fad'in, "Wallahi wallahi idan baki tashi a k'asan nan ba kika bari nazo wajen nan zan baki mamaki!" A fusace Sarah tace, "Wani mamaki? Nace wani mamaki ne kuma ya rage baka bani ba." Ba tare da yace komai ya mik'e a fusace. Ko kamun yayi taku d'aya ta mik'e da sauri ta zauna a kan kujeran dake fuskantarsa. Wani dariya ne ya taho masa amma yayi saurin mayar dashi tare da kau da kai yana murmushi don dama ba zuwa wajenta zai yi ba, kawai barazana ce domin ta bar tiles d'in saboda sanyi. Zama yayi tare da cigaba da abunda yake yi. Ita kuma Sarah sai harare-harare take yi. Sun kwashi kusan awa guda sannan ya mik'e tare da fita ya kullo k'ofar. Sarah na ganin ya fice kuma ya kullo k'ofar ta kifa kanta akan desk d'in ta fashe da kukan bak'in ciki. Shi kuwa _Khalil_ yana fita suka ci karo da doctor Kamal dama kuma wajen _Khalil_ d'in zai zo. "Wajenka dama zan zo." Gyara tsayuwa yayi tare da yin bake-bake a k'ofar office d'in ya wani ci d'aci tare da fad'in, "To gani!" Sai da doctor Kamal ya kalli k'ofar office d'in sannan yace, "Ka kira ni emergency akan inzo nan kai zaka je yin wani abu, sai kuma gaka na ganka tare da wannan yarinyar. _Khalil_ ba halinka bane. Dan Allah kar kace zaka zubar mata da cikin dake jikinta. Y'an iskar yara sai sun gama yawon banzan su a tit....." A mugun tsawace _Khalil_ yace, "Enough! Enough doctor Kamal Isah Bashir! Kar ka k'ara jifan Sarah da wad'annan kalmomin. Sarah ba irin matan da kake tunani bane." Baki bud'e doctor Kamal ke kallon _Khalil_ don bai tab'a ganinsa a irin wannan yanayin sabida mace ba. Macen ma mai d'auke da cikin shege. A iya sanin da yayi wa _Khalil_ ya tsani y'an iskan mata. " _Khalil_ this lady that you're protecting haka, she's prostitude! Duk abunda zata fad'a mak......" Bai kai k'arshen zancen ba yaji wani gigitaccen mari ya sauka akan kuncinsa sai da yayi saurin saka hannu ya dafe kuncin yana mai kallon gefe-gefe. Ganin babu kowa kuma babu wanda yaga komai sai ya kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Ibrahim ni ka mara? Ni ka mara saboda ina fad'a maka gaskiya." Wani kallon banza yayi masa tare da fad'in, "To hell with the fucking stupid gaskiya gaskiyarka. Idan bakinka ya kuma kuskuran kiran matar da zan aura da karuwa, na rantse maka da ubangijin rana da wata sai na d'aureka kuma babu uban da ya isa ya fito da kai. Kuma cikin jikinta it's mine. Na fad'a da babban murya, cikin dake jikin Sarah, nawa ne! Kuma duk uban da ya isa ya kira ta da karuwa yaga abunda *_Ibrahim Khalilullah Nurudden_* zai aikata." Yana gama fad'in haka ya wuce fuuuuuu ya nufi pharmacy domin d'auko mata magunguna don tun d'azu yake lura da ita jiri take gani kuma babu k'arfi a jikinta. Shi kuwa doctor Kamal da mugun tsananin mad'aukakin mamaki yabi _Khalil_ d'in da idanu. Don ya mugun sanin hakinsa. In fact tare suka yi karatu a _London_ har kammalawan su. Yasan yanda ya tsani Zina da kuma mazinatan. Sannan yaga mata kyawawa iri-iri, turawa, indiyawa, larabawa duk bai fad'a halaka ba sai akan wannan tatsitsiyar yarinyar duk da ita ma kyakykyawar ce. Shafa kumatunsa da suka ji mari yayi tare wucewa ya bar wajen. _Khalil_ kuwa sai da ya d'auko duk magungunar da yasan Sarah zata buk'acesu sannan ya dawo office d'in hannunsa d'auke da leda mai tambari da sunan asibitin still kuma fuskansa a mugun d'aure. "Ki tashi in mayar dake gida." Ya fad'i sounding command. Cikin sauri ta mik'e shi kuma ya fita tabi bayansa. Kulle k'ofar yayi tare da fad'i, "Kiyi tafiya a hankali kar ki fad'i. Ko in rik'e ki?" Da jin haka tayi saurin yin gaba don taga alama sam bai da kunya. Har wajen motarsa suka isa, shi ya bud'e mata gidan gaba ta shiga sannan ya zaga ya shiga driver sit sannan ya tada motar yayi reverse ya bar cikin asibitin. A hankali ya dunga tafiya ba tare da ya k'ara ce mata ko uffan ba har suka isa k'ofar gidansu Sarah. Parking yayi tare da kashe motar ya juyo ya tsura mata idanu. Tana jin idanunsa na yawo a jikinta amma tak'i kallon wajen. Ledan maganin ya d'auko tare da fiddo da magungunan ciki sannan yace, "Hey, kalle ni nan." Kamar baza ta juyo ba, sai kuma ta juyo ta kallesa tana mai turo baki gaba. Tsurawa kyakkwar bakinta kallo yayi yana tuno ranar da tsautsayin ya afka. "Kin san wani abu? Tsiwarki ita ke ja mutun yayi maki abunda bai yi niyya ba. Ko wancen ranar ke kika ingiza ni har mai afkuwa ta afku. Idan kika b'ata rai ko kuma kika turo baki, wani irin kyawu kike k'ara yi sosai. Sai ki rik'a looking very sexy!" Wani irin kuka Sarah ta fashe dashi jin abunda yace. Bak'in ciki take ji idan yana maganar cikin dake jikinta. "Kin san Allah idan kina kukan nan, wancen ranar ba'ayi na gaske ba, amma ina ganin soon an kuwa zuwa wajen." Hannu ta kai zata bud'e k'ofar taji sa a gark'ame. Kallonsa tayi tare da shagwab'e fuska tace, "Dan girman Allah ka bud'e min, kaji ma kiran sallah ake yi!" Kallon maganin da ta fito dashi yayi tare da fad'in, "Kalli nan, wad'annan guda ukun kullum sau d'aya zaki rik'a sha, wannan kuma safe da dare. Allah ya k'ara maki lafiya Matata. Kiyi min magana da Mama idan kin shiga ciki. And lastly, wallahi kar in k'ara kiranki a waya kik'i d'agawa. Don wallahi komai dare sai nazo, kuma ni kai na ban san mai zai faru ba idan nazo d'in." Yana gama fad'in haka ya cire lock d'in yana kallon fuskanta. Bud'e motar tayi ta fita a hankali ba tare da ta d'auki ledar ba, sai da ta rufe k'ofar sannan ta lek'o ta window kasancewar ya zuge glass d'in tare da fad'in, "Ba zan d'auka ba, dan girman Allah kar ka fasa abunda kace za kayi. Kuma bazan sha maganin ba. Ka tafi da tsiyarka. Kuma cikinka dake jikina, a leda zan juye na watso maka shi a fuska na huta da jaraba." Da wani irin hanzari ya cafki hijjab d'inta ya cukuikuyota da hannu d'aya tare da fad'in, "Maimaita mai kika ce?" A gigice tace, "Na rantse cewa nay na manta ga ledan maganin nan baka mik'o min ba. Kuma wancen farin ma ya ma kace ayi amfani dashi." Dariya ce ta taho masa sosai amma bai yi sai murmushi ya saki tare sa d'aukar maganin da d'aya hannunsa ya mik'a mata. Da sauri ta amsa har da fad'in, "Nagode" shi kuma ya saki hijjab d'in nata tayi saurin barin wajen ta nufi k'ofar gidansu ba tare da ta waiga ba. Tana bud'e k'ofar suka ci karo da Baba ya fito karo na bakwai ko Allah zai sa ya ganta. Don lokacin dasu Na'ima suka baje a tsakar gida babu labarin da suke yi sai na _Khalil_ da irin motar da yazo da ita. Jin hakan sai ya tada hankalin Baba ya soma tunanin ko Sarah ta soma hawa layin y'an uwanta ne. Ya jira kusan mintuna ashirin ko Sarah zata dawo amma yaji shuru, ya daure ya k'ara goma akai, ganin har lokacin shuru sai ya mik'e ya d'auki sandarsa ya fito waje amma wayam. Yana jin sanda su Na'ima suke dariyar ya fita nemo y'ar gwal. "Baba dama dawowa kayi kar ka wahalar da kanka. Don saurayinta yazo sun fita tare." Fad'in Hassana. Bini-bini Baba ke fitowa ya duba ko Sarah ta dawo amma wayam. Sai a karo na bakwai sannan ta turo k'ofar suka yi ido hud'u. Wani ajiyar zuciya Baba ya sauke tare da fad'in, "Saratuuu!" Sai kuma ya fashe da kuka. Da sauri Sarah ta waiga taga motar _Khalil_ na nan, sai taji hankalinta ya tashi don bata son yardar da Baba yayi mata ya rushe. A gigice ta soma magana, "Wallahi Baba ba abunda kake tunani bane. Dan Allah ka daina kuka." Ta fad'i tana mai fashewa da kukan. Da sauri _Khalil_ ya bud'e mota ya fito tare da k'arisowa wajen ya duk'a tare da fad'in, "Ina wuni Baba?" Baba dake matsar hawaye ya d'ago ido ya kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Bawan Allah na rok'e ka da girman ubangijin idan ba alkhairi bane ya kawo ka wajen Saratu kayi tafiyarka Allah ya had'a ka da dai-dai da kai. Ka dubi Allah da annabi kar ka lalata min tarbiyan y'ata guda d'aya da ta fita zakka!" Shuru _Khalil_ yayi na y'an dak'ik'u tare da fad'in, "Baba wallahi alkhairi ne ya kawo ni wajen 'yarka ba sharri ba. Ni da niyyar aure nazo k'ofar gidan nan ba da niyyar yaudara ba." Da sauri Sarah ta kalli Baba tare da fad'in, "Baba kar ka yarda da maganarsa, fatar bakinsa ne fad'i amma cikin zuciyarsa ba haka bane. Shine sanadiyar duk abunda ke faruwa dani yanzu. Shine dalilin rugujewar farin cikina. Shine dalilin fasuwar aure na. Baba wannan dake durk'ushe a gabanka shine uban cikin dake jikina." Ta k'arisa maganar tare da fashewa da kuka. Baba kuwa ji yayi kamar an d'iga masa dalma a kunne. Rintse idanu yayi cike da k'una a zuciya yace, "Bawan Allah mai muka maka? Mai d'iyata tayi maka ka tarwatsa mata rayuwa? Kana ganin kayi min adalci kenan? Ban tab'a b'ata d'iyar wani ba, wannan jarabawace kawai daga mahalicci!" Idanun _Khalil_ gaba d'aya sun kad'a kun yi jazur ya d'ago tare da kallon Baba yace, "Baba, dan alfarmar ubangiji halittu ka saurare ni ko da na mintuna biyar kacal. Wallahi, tallahi rantsuwar musulmi ban zo nan da niyyar cutar kowa ba, zuwa na nan k'ofar gidan nazo ne domin in auri 'yarka." Hakanan baba ya d'an ji _Khalil_ ya kwanta masa. Kallon Khalil d'in yayi tare da fad'in, "Shiga masallaci kayi sallah, idan an idar kayi sallama zan aiko Saratu ta shigo da kai har ciki. Bari na shiga nima nayi sallar." Wani sanyi ne ya ziyarci zuciyar _Khalil_, cike da ladabi yace, "Nagode Baba!" Ya fad'i hakane tare da mik'ewa ya nufi masallacin gaban gidansu Sarah wanda yake daga hannun hagu, yayin da nasu gidan yake daga dama. Baba ma shigewa yayi Sarah na biye dashi kanta a k'asa hannunta rik'e da ledar magungunan da _Khalil_ ya bata. Gaba d'aya suna tsakar gida har da y'ay'ansu. Rabo d'an wajen Na'ima ya kalli Sarah tare da fad'in, "Lami ga Saratun ta dawo daga wajen saurayin nata." A fusace Sarah tace, "Daga wajen ubanka na dawo." Na'ima mahaifiyarsa ta taso a fusace tare da fad'in, "Zan ci ubanki a cikin gidan nan wallahi idan kika ce zaki rik'a takurawa d'ana. Babu ruwana da cikine a jikinki duka zan maki." Harararta Sarah tayi tare da fad'in, "To ai sai ki kashe ni kawai. Banza kawai." Yunk'urawa Na'ima tayi zata taho wajen Sarah karaf Lami ta rik'e ta tare da fad'in, "Barta! Yanzu haka duk salon kar ta bamu abunda ta samo ne daga hannun saurayin nata." Juyowa Baba yayi tare da kallon Sarah yace, "Saratu wuce ciki kinj." Babu musu Sarah ta shige ciki. "Ban gane abunda kake nufi ba Nuhu anyi yamma da kare!" Ko kallonta Baba bai yi ba ya shige d'aki. "Ahafff! Ba na fad'a maki ba Lami. Baba fa ya san duk tsiyar da Sarah take shukawa. Raba kud'in suke yi a tsakanin su shiyasa kike ganin yafi sonta akan mu gaba d'aya." Fad'in Aina'u. "Na ko tabbatar da maganarki yanzu Aina'u. Aikuwa dani suke zancen." Fad'in Lami tana kwafa. Dai-dai nan Sarah ta kuma fitowa ta nufi fanfo Lami na harararta. Alwala da d'auro sannan ta kuma komawa d'aki. Tana idar da sallah ta jiyo muryan Baba yana kwad'a kiran sunanta. Da sauri ta fito ta nufi baranda inda ta ganshi tsaye a bakin k'ofar d'akinsa, "Yi maza gashi can yana kwad'a sallama, je shigo dashi." Da "To Baba" Sarah ta masa tare da juyawa. Na'ima kuwa kallon Hassana tayi wacce itama kallon nata take yi sannan gaba d'aya suka mai da dubansu ga Lami wacce tayi suman tsaye tana kallon Baba cike da mamaki. Mintuna biyu sai ga Sarah tafe, _Khalil_ biye da ita a baya. Bai kalli kowa a cikinsu ba, don har yanzu bai gama tabbatar da cewar Lami ita ce cikakkiyar mahaifiyarsu Sarah ba. Dama kuma tuni baba ya shige cikin d'aki. Sallama _Khalil_ yayi tare da shiga don tuni baba ya amsa tare da bashi damar shiga. Yana shiga Sarah ta bar wajen zata wuce d'aki Lami ta shak'o ta tare da fad'in, "Dan ubanki shine zaki kai sa wajen mahaifinku! Wato kin fi k'aunarsa dani ko? To wallahi baku isa ba komai dani za'a ci." Tana gama fad'in haka ta fad'a d'akin babu sallama lokacin _Khalil_ suna k'ara gaisawa da Baba. "Na rantse da, girman Allah Nuhu baka isa Kaci kud'in nan kai d'aya ba. Ai nice na d'auki cikin Sarah wata har tara na kuma sha wuya nayi nak'uda na haife ta. Fito da duk wani abu da yaron nan ya baka ayi kaso." Sai kuma ta mayar da dubanta ga _Khalil_ wanda kansa ke a k'asa tare da fad'in, "Kai kuma Munafuki................ *_Na rok'e ke ki da girman ubangiji kar ki fitar min da littafi. Kud'in karatu kawai kika biya ba kud'in mallakar littafi ba. Kiji tausayin marainiyar Allah don wallahi Sana'a na d'aukesa ba nishad'i ba. 🙏_* *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*[9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 11* "Kai kuma Munafuki! Ya muka yi da kai d'azu?" _Khalil_ ko d'agowa bai yi ba, balle ya kalleta har ya amsa maganar ta. "Lami wannan wani irin rashin hankaline haka? Yaya zaki shigo min d'aki babu sallama kuma kin san ina da bak'o! Wannan ai rashin hankaline. Malama fitar min daga d'aki." Harara ta makawa Baba tare da fad'in, "Ba zan fita ba wallahi. Sai anyi komai a idanuna. Wato daga kai sai y'arka ne zaku rik'a cin kud'in ko? To wallahi baza ta sab'u ba bindiga a ruwa!" Karkacewa _Khalil_ yayi ya fiddo da rafar kud'i y'an dubu-dubu ya mik'a mata tare da fad'in, "Gashi. Ni magana nazo muyi da Baba ba wani abu ba." Fizge kud'in Lami tayi da sauri don a zatonta Baba zai kawo hannu ya warci kud'in tana mai sakin murmushin ganin tashin farko an bata dubu d'ari. "Yauwa to ko kaifa. Ai wallahi da baka ban kud'in nan ba, Sarah baza ta k'ara cin ko loma d'aya a cikin gidan nan ba. Kuma duk aikin wahalar gidan nan ita zata rik'a yinsa. Babu ruwana da tana d'auke da k'aramin ciki." Taga gama fad'in haka ta harari Baba tare da ficewa daga d'akin. Da idanu _Khalil_ yabi Lami yana mai tabbatar wa kansa ba ita bace mahaifiyarsu Sarah. Baba kuwa kunya ce ta kama shi kamar k'asa ta tsage ya shige ciki. Da kyar ya iya bud'e baki tare da fad'in, "Dan Allah kayi hak'uri. Haka halin Lami yake. Sam bata da girma sai na jikinta." Kallon Baba _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Baba wacece ita?" Sai da Baba ya sunkuyar da kai don kunya yake ji ainun ya nuna Lami matsayin matarsa uwar Y'ay'ansa. A hankali cike da rauni Baba yace, "Matata ce. Uwar y'ay'ana!" Fad'in Baba hawaye na wanke fuskansa kasancewar mai sauri kuka. "Amma Baba ba ita bace mahaifiyarsu Sarah ko?" Hannu Baba ya kai ya sharce hawayen idanunsa tare da fad'in, "Ita ce. Wallahi samari ita ce ta haifi duk Y'ay'an dake cikin gidan nan." Wani irin ajiyar zuciya mai k'arfi _Khalil_ ya saki yana mai jin matsanaicin mamaki. "Kana mamaki ko? Na san za kayi mamaki Samari. Ba kai kad'ai ba, da yawan mutane basu yarda Lami itace ta haifi su Sarah sabida irin tarbiyan da tayi masu sakamakon son abun duniya. Ita gaba d'aya kallon wad'annan yaran take yi matsayin babban jarinta. Sam ta mance su d'in amane Allah ya bata. Na'ima ita ce y'arta ta fari, sai Nuratu, Lukman, Hassana, Marfu'a, sai auta Aina'u. Duk Y'ay'an Lami ne. Ita ta haife su da cikinta." Hassana ma y'an biyu ne, d'ayan tun a ciki ya mutu. Da yanzu su takwas ne, shidda mata maza biyu." Da tausayi _Khalil_ ke kallon Baba tare da fad'in, "To Baba ya aka yi irin haka yake faruwa a cikin gidanka, amma baka da ta cewa?" Sunkuyar da kai Baba yayi yana mai jin d'aci da k'una sosai cikin zuciyarsa tare da fad'in, "Lami tafi k'arfi ba Samari! Duk yanda zanyi maka bayani, baza ka gane ba. Amma Lami ta raina ni, bata ganin mutunci da darajana tun da na samu karayar arziki. Shiyasa y'ay'ana suma suka taso da d'abi'un da suka ga tana yi min. Guda d'aya ce ta fita zakka. Saratu na tausayina sosai, tana bani girma, tana kula dani kuma tana gudun b'acin raina. Tana sona sosai kuma duk abunda nace tayi, shi take yi, idan na hane ta kuma har abada ta bar abun nan kuma baza ta kusance shi ba." Gyara zama _Khalil_ yayi tare da soma fad'in, "Baba da farko dai hak'uri zan soma baka, dan Allah ka yafe min domin na cutar da kai. Tabbas 'yarka Sarah mutuniyar kirki ce. Kuma duk wani abu da ya faru tsakani da ita, wallahi ba da son ranta bane. Ban san ta yanda zanyi maka bayani ba Baba. Amma wallahi nima ba mazinaci bane. Tsautsayine ya afka mana daga ni har ita Saratun. Kuma wallahi ban d'auka sanadiyar abunda ya faru tsakani da ita ta samu ciki ba. Na jima ina naiman ta, amma ban ganta ba sai yau da Allah ya kawo ta asibitina. Baba dama ni ina son Sarah, kayi hak'uri ya yafe min kar kace zaka hanani ita saboda wannan abu da ya faru, ni nayi alk'awarin Sarah na haihuwa sati baza ta zagayo ba sai da aure na a kanta. Tun daga yau da na san Sarah na d'auke da cikina, d'awainiyarta gaba d'aya ya dawo kai, cinta, shanta da komai nata. Dan Allah Baba kar ka hana ni Saratu." Shuru Baba yayi yana wani tunani a cikin zuciyarsa. Ya jima bai yi magana ba, kuma bai d'ago ba. _Khalil_ kuma addu'a kawai yake yi Allah yasa Baba ya amince. Ajiyar zuciya Baba ya sauke tare da fad'in, "To! Ni bazan ce ban amince ba, matsalar guda d'aya ce. Shin idan kai ka amince zaka auri Saratu, iyayenka fa? Kai da kanka kaga irin gidan da kake neman aure. Kasan su wanene y'an uwan Sarah da kuma mahaifiyarsu. Gaba d'aya unguwarnan anyi masu tambari. Karo na biyar kenan ana fasa auren Saratu saboda bak'in fentin da y'an uwanta suka goga mata. Kud'in goro ake yi masu. Gani ake yi ita ma Saratun yawon banza take yi. Idan kai ka amince, iyayenka zasu amince ka auri Saratu ne?" Sai da _Khalil_ ya d'ago suka had'a idanu da Baba sannan ya sunkuyar da kai yace, "Baba mahaifiyata sam bata da matsala. Mace ce mai fahimta sosai. In Sha Allah baza'a samu matsala da family na ba. Amincewar ka shine kawai nake buk'ata Baba." Fad'in _Khalil_ amma deep down ga san k'arya yake yi, ya san tabbas za'a sha daga da Hajiya, duk da yana da yak'inin zata amince musamman idan ta samu labarin yayiwa Sarah ciki, amma y'an uwan mahaifinsa ne yasan za'a mugu-mugun kai ruwa rana dasu. "To shikenan, Ubangiji Allah ya shige mana gaba yasa muna da tsawancin kwana." Da "Ameen" _Khalil_ ya amsa yana mai jin farin ciki a zuciyarsa. "Baka shaida min sunanka ba." Fad'in Baba. "Sunana Ibrahim Baba." Jinjina kai Baba yayi tare da fad'in, "Ma sha Allah!" _Khalil_ kallon k'afar Baba yayi tare da fad'in, "Baba ka dad'e kana ciwon k'afar nan ne?" Kallon k'afar Baba yayi tare da fad'in, "Shekaru talatin da biyu kenan ina fama da ciwon nan, tun Na'ima na da shakara d'aya a duniya" da mamaki _Khalil_ ya kalli Baba tare da fad'in, "Kuma baka je asibiti ba?" Murmushin Baba yayi tare da fad'in, "A kan ciwon k'afar nan sai da na rasa komai nawa. Da wannan gidan kawai na tsira. Ai da abun yafi muni ma. A hankali Allah ke ta kawo sauk'in." K'urawa k'afar idanu yayi kamun yace, "Allah ya baka lafiya Baba. Zan rik'a zuwa lokacin bayan lokacin. Sannan in Sha Allah zan zo na d'auke zuwa asibitina a duba k'afar sosai." Ya fad'i hakane tare da saka hannu a aljihu ya fiddo rafar kud'i y'an dubu-dubu guda biyu ya ajiye a kan yaloluwar katifar Baba. "Zo-zo-zo, d'auke kud'inka dan girman Allah. Wanda ka bawa Lami ma ya isa haka." D'ukawa _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Baba dan girman ubangijin kada ka k'i karb'an kud'in nan. Ka d'auke ni matsayin dank'a na cikinka. Nasan baza ka k'i karb'an kud'in hannun dank'a ba. Kayi min wannan alfarmar Baba." Ajiyar zuciya Baba yayi tare da fad'in, "To d'auke daya ka bar d'aya dan Allah Ibrahim." Hannu _Khalil_ ya kai ya d'auka tare da fad'in, "Nagode da karamcin ka Baba. Allah ya saka da alkhairi. Sai na sake zuwa." D'aga masa hannu Baba yayi tare da fad'in, "To d'ana nagode nima. Allah yayi albarka." Da ameen ya amsa tare da fitowa daga d'akin. Gaba d'ayansu suna tsatstsaye a tsakar gidan suna kallon k'ofar d'akin Baban, sun k'osa ya fito ya basu nasu rabon don Lami tace kwandala baza ta basu ba. Yana fitowa suka saki murmushi tare da fad'in, "K'aninmu har an fito." Babu yabo babu fallasa yace "Eh" tare da mik'a masu kud'i da Baba ya sashi ya d'auki d'aya tare da fad'in, "Ku raba!" Yana fad'in haka ya fita. Da sauri Lami ta bishi a baya, sai da ya kai k'ofa sannan ya tsaya tare da juyowa, sam baya ganin girmanta matsayinta na surukarsa. Fuska ya tsuke sosai tare da fad'in, "Lafiya?" Murmushin tayi tare da kwance zanintata sake d'aurawa sannan tace, "Dama maganar abincin Sarah ne. Dama na fad'a maka tun farko, ni ban ciyar da y'ay'ana kuma in ciyar da nasu Y'ay'an. Kaga ai yanzu Saratu tana d'auke ne da cikinka, dole ne duk wani abincin da zata ci da duk wani abu da zata nema kai zaka kawo kud'i a sayo. Ko baka duba list d'in da na baka bane?" Fuskan nan a tsuke _Khalil_ yace, "Ban duba ba, amma zuwa anjima za'a kawo komai. Sannan a kula da ita sosai. Duk abunda take buk'ata a kira ni a waya a sanar min. Kar a bari ta sha wani magani idan ba wanda na kawo ba. Idan wani waje nayi mata ciwo, immediately a kira ni a sanar min. Sannan abu na gaba, idan wani abu ya samu ciki na, ba zan kyale kowa ba. Ki turo min ita idan kin koma." Fad'in _Khalil_ tare da bud'e gidan ya fita. Don wani irin haushi da tsanar Lamin yake ji. Sam bata cancanci zama surukarsa ba. Lami kuwa tab'e baki tayi tare bud'e gidan ta kallesa tsaye jikin k'arfen gidan mak'otansu, mik'a masa wayarta tayi kirar Itel tace, "Saka min number d'inka don ban da shi." Karb'an wayar yayi tare da danna digits d'insa ya mik'a mata. Ita kuma ta amsa tare da juyawa ta koma cikin gidan. D'akin su Sarah ta shiga, zaune ta same ta a k'asa hannunta rik'e da kwalbar fantan da Aina'u ta sayo mata d'azu kamun su tafi asibiti. Da fantan ta iya shan maganin da _Khalil_ d'in ya bata. Don ruwa bai wuce mak'ogoronta. "Sai ki tashi ki fita yana jiranki a waje." Fad'in Lami tana kallon Sarah dake maida numfashi. "Waye?" Fad'in Sarah tana kallon Lami. "Ubanki ne. Idan kin fita zaki gansa." Lami ta fad'i tare da juyawa ta bar d'akin. Sarah kuwa turo baki tayi tare da mik'ewa ta saka hijab d'inta da ta cire ta fita. Yana nan inda Lami ta barsa. Tana bud'e k'ofar suka yi ido biyu dashi. Kwafa yayi tare da fad'in, "Na d'auka ai baza ki fito ba." A shagwab'e tace, "To wai ni mai zanyi maka ne? Dan Allah ka fita daga harkata." Gyara tsayuwa yayi tare da fad'in, "Zaki fara shagwab'an naki ko? Ki dai kiyayi kan ki, tom! Dama zan fad'a miki Baba ya riga ya damk'a min ke. Don haka ke tawa ce. Kuma sannan ki kular min da kanki da kuma babyn mu. Mai kike so in kawo miki a idan zan zo gobe?" Kuka ta saki tare da fad'in, "Wallahi kar ka k'ara zuwa mana gida. Ni bana son ganinka. Kuma babu abunda zai saka na aure ka. Ina haihuwa zan baka abunda na haifa maka, shikenan mun rabu!" D'age gira yayi tare da fad'in, "Za dai ki haifa min ko? In dai zaki haifa min baby d'in ai shikenan. Sai muyi deal ni dake. Idan kin amince, kamar yanda kika ce d'in, kina haihuwa zan karb'i d'an nawa shikenan kowa sai ya kama gabansa." Da sauri Sarah tace, "Eh na amince!" Waro idanu _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Tun kamun ma kiji deal d'in har kin amince. Ok, to shikenan. Na farko, duk lokacin da nazo, zaki fito, kar fa kiyi tunanin don in ganki zan zo, sam baby na nazo gani. Sannan idan na kira ki a waya, dole ki d'auka, shima ba don inji muryanki bane, lafiya babyna zan ji. Sannan duk abunda kike son ci zaki fad'a min, shima fa kar kiyi tunanin ke zan sayo mawa, a'a sam baby na na sayo mawa don nasan shi ke saka ki kwad'ayin. And dole ki rik'a shan magani tare da kiyaye duk wani abun da zai damu cikin jikin ki, sannan idan lokacin zuwa asibiti yayi, zaki je dole domin a duba min baby na. Idan kin amince da wannan sharad'in, bayan kin haihu ni da kaina zan shaidawa Baba na janye maganar auren ki, amma kuma idan baki harda ba, duk wad'annan abunda na lissafo dole ayi su, kuma a k'arshe sai na aure ki dole." Zaro idanu Sarah tayi tare da fad'in, "Kuma duka wad'annan sharad'in sai na cika?" D'aga k'afada tare da tab'e baki _Khalil_ yayi tare da fad'in, "If you wish, ki karya d'aya daga ciki. Amma ki sani, karya d'aya daga ciki yana nufin rushe deal d'in gaba d'aya. Kuma kin san dai abunda zai faru." Marairaicewa tayi tare da fad'in, "To ta yaya zaka gane idan ina son wani abu, kuma nak'i in kira in fad'a maka? Kuma misali idan ka kira wayar bana kusa fa?" Dariya ne ya kama _Khalil_, amma sai yayi murmushi kawai tare da fad'in, "Zan yi connecting CCTV camera ta inda zai r'ika hasko min duk wani motsin ki, idan ma bakya kusa na kira waya, zan sani, idan kuma da gangan ne, shima zan sani." Turo baki tayi tare da fad'in, "To amma baza a rik'a dad'ewa ba ko idan ka kira wayar?" D'aga kai sama yayi tare da fad'in, "Eh to, sai yanda babyn cikin ko yayi suggesting." Shuru tayi tana tunani, can kuma tace, "To amma kayi alk'awari idan na haihun zaka amshi babynka ka tafi baza ka sake dawowa ba?" B'ata rai yayi tare da fad'in, "Ohh wato baki ma yarda dani ba ko? Wato ga k'atoton mak'aryaci ko? To na ma fasa deal d'in. Zan yi duk abunda nace da k'arfi da yaji." Da sauri har da d'aga hannu Sarah tace, "A'a dan Allah kayi hak'uri ba haka nake nufi ba. Na amince da deal d'in." Wani mugun dariya ne ya kama shi cikin zuciyarsa. K'are mata kallo yayi ya tabbatar da yarinya ce ita. "Shekarunki nawa?" Ya tambayeta. Kanta a k'asa tace, "I'm 21years old." Sai da ya kuma kallonta daga sama har k'asa sannan yace, "I see. Yanzu to ki shiga gida. Deal d'in mu zai fara daga yau. Bye ki kular min da kanki." Sarah bata san lokacin da tace, "Bye" ba har da d'aga masa hannu. Sai bayan ta shiga cikin gida sai haushin kanta ya kamata. _Khalil_ kai tsaye gida ya nufa, cikin mota sai sak'e-sak'e yake yi na yanda zai tari Hajiya da maganar Sarah. Ya san dai akwai k'ura. Shi yafi jin nata ma akan nasu Uncles d'insa. Don idan har ta amince, to shafawa idanunsa toka zai yi. Ai ba wani zai zauna masa da matar ba. Beside shi ya lalata masu yarinya don haka shi zai d'auki abunsa. Horn yayi mai gadi ya wangale masa gate ya shigo. Sai da tayi parking mai kyau sannan ya fito daga motar. Gani Honda anyi parking d'insa daga gefen motarsa, ya saki siririn tsaki don ya shaida ko su wanene suka zo gidan. Kamar ba zai shiga ba, sai kuma ya doshi hanyar cikin gida amma ta baya ta yanda babu wanda zai fahimci ya dawo gidan. Sai dai abunda bai sani ba, tun shigowarsa Uncle Ameeru ya gansa, don shi ya fito harabar gidan domin amsa waya. Kuma yana kallonsa lokacin da yabi ta baya ya shige cikin gidan zuwa d'akinsa. A fusace Uncle Ameeru ya shiga ciki tare da Fad'in, "Bilkisu! Bilkisu!! Wallahi babu abunda za muce maki sai Allah ya isa! Yanzu tsabar yanda baki nunawa _Ibrahim_ mahimmancin mu ba matsayinmu na k'annai da yayyin mahaifinsa, shine zai dawo cikin gidan na don bai son ya ganmu sai ya zagaya ta baya ya shige ciki. Na san ma kece zaki kira sa a waya ki fad'a masa mun zo don ya doje mana. Wallahi Bilkisu ki kiyayi kanki damu. Kuma yanzu-yanzu ki tashi ki wuce ki kira mana shi dan ubansa." Hajiya da ranta yayi mugun b'aci da abunda _Khalil_ yayi, mik'ewa tayi tare da fad'in, "Kuyi hak'uri dan Allah. Bari na kira sa." Tana gama fad'in haka ta nufi wani corridor da zai sadata da matattakar da zai kai ta d'akin _Khalil_ d'in. _Khalil_ na shiga d'aki ya zauna bakin gado tare da kai hannu ya jawo side drawer ya d'auko *_MASTIKA GUM_* ya jefa a baki ya hau tauna yana mai kwanciya rigingine tare da saka hannayensa biyu ya tallabo kansa yana tunanin hanyar da zai bi yayiwa Hajiya bayanin Sarah da kuma cikin dake jikinta. Ya san Hajiya sai ta kusa kashesa da masifa. Don da ana aro baki, sai ta aro tabbas. Da ace mahaifinsa nada rai ne, to da worse kenan, don ko da ace zai amince ayi auren, to sai ya kullesa a prison ko da na sati biyu ne tukun. He's father *_Nurudden Muhammad Ibrahim_* was the chief justice of Nigeria (CJN) before he died. Yana da mahaukatan kud'i wanda kwakwalwa ba zai d'auka ba. Sam baya d'aukar raini da rashin adalci. He raised all his children very well. "I really miss you papa. I miss everything about you daddy. Allah ya jik'anka da rahama ya gafarta maka." Yana fad'in haka ya lumshe idanu siraran hawaye na zubowa daga idanunsa. Dai-dai nan jai ana danna doorbell da k'arfi. Da sauri ya tashi zaune yana kallon k'ofar. Wani abu ya danna daga gefen gadonsa, sai ga hoton Hajiya b'aro-b'aro ajikin wani screen dake saman k'ofarsa. Kai baza ka tab'a ganin screen d'in ba sai idan shi ya danna wannan madannin. Da sauri ya sauka daga kan gadon tare da isa wajen k'ofar ya bud'e. Ido hud'u suka yi da Hajiya ranta a mugun b'ace. "Ai sai ka fito tun da kai a rayuwarwa kafi so kaga raina yana ta b'aci." Tana gama fad'in haka ta juya tabi corridor d'in da ta biyo. Shima bayanta yabi don yasan dama tatsuniyar gizo bata wuce ta k'ok'i. Fuska babu yabo babu fallasa ya isa parlor. A zazzaune ya taras da gaba dayansu su biyar k'annai da yayyin mahaifinsa. Zama yayi a kan carpet tare da fad'in, "Barkan ku da zuwa Uncles." Uncle Ameeru ya kallesa tare da fad'in, "Kalle ni, ungo nan!" Ya fad'i haka tare da yi masa dak'uwa............ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 12* Sai da ya isa k'ofar gidan sannan ya d'auko wayarsa dake gefensa ya lalubo number Sarah da yayi saving da *_My endless bliss_* yayi dialing, ringing uku ya amsa kiran tare da fad'in, "Hello, Assalamu alaikum." Tab'e baki yayi kamar tana kallonsa tare da amsawa da, "Hi, wa'alaikissalam." Da sauri Sarah ta cire wayar daga kunne tana k'arewa special number d'insa kallo wanda ya k'are da 3 guda shidda a k'arshe. Turo baki tayi don sarai ta gane muryansa, gashi kuma tana tsoran yanke kiran don bata manta da deal d'in su na d'azu ba. "Wake magana!" "Bugun zuciyarki!" Kai tsaye ya bata amsa yana mai sakin murmushi. Sarah kuwa yana fad'in hakan zuciyar nata ta soma bugawa. Shuru tayi bata k'ara cewa komai ba. Sun d'au lokaci har na tsawon mintuna biyar babu wanda ya sake yin magana. _Khalil_ ya ciro wayar daga kunne, kamar yanda itama Sarah ta fiddo nata domin ganin is he still their. Sai taga yana reading kamar yanda shima ya gani daga can, mayar da wayar yayi kan kunnansa tare da fad'in, "Tun ba'a je ko ina ba, har kin fara karya dokar ko?" K'ara turo baki Sarah tayi daga can tare da fad'in, "To ni ai kai ne baka yi magana ba, kuma ni ban san mai zan ce ba." Gyara zama yayi cikin motar tare da fad'in, "Ki fito ina waje." Waro idanu Sarah tayi tare da fad'in, "Waje kuma? Ni dai......." Sai kuma tayi shuru bata k'arisa ba. "K'arisa maganarki mana, ke dai baza ki fito ba ko?" Kwanciya tayi rigingine tare da fad'in, "Ni dai Allahna yana sama yana kallo ba haka nayi niyyar cewa ba." D'age gira yayi kamar tana kallonsa tare da fad'in, "Au Allah d'in naki ne ke d'aya mai son kai. To idan ba tsoro ba ki fad'i abunda kika yi niyyar fad'i daga farko mana." Sai da ta juya idanuta sannan tace, "Ni dai so nake in ce maka, ni dai gaskiya.... Gaskiya, ummm-ummm...." Dariya ya saki tare da fad'in, "Kin ga k'aryar ma ta kasa fitowa. To bari na juya kawai kin ga kenan deal d'in mu ya rushe." Waro idanu Sarah tayi tare da mik'ewa da sauri tana fad'in, "Wallahi a'a, wallahi ni dai a'a ba haka nake nufi ba. Gani nan zuwa yanzu." Sosai ya saki dariyarsa tare da fad'in, "Matsoraciya, ana so ana kaiwa kasuwa." "To mai ake so d'in." Ta tambaya tana hararar wayar. " _Khalilullah_ mana." "Khalilo." Ta fad'i cikin zuciya har da Allah ya kiyaye. Bata san cewar a zahiri tayi maganar ba sai da taji yace, "Ni ne _Khalilo_ d'in?" "Na shiga uku na!" Ta fad'i jin ashe a bayyane tayi maganar. "Ki fito maman twins kar ki b'ata min lokacina." "Mene? Ni wallahi ba maman Twins bane. D'aya kawai zan haifa maka. Shima don babu yarda zanyi ne. Ai don dai zubar da ciki haramun ne, kuma tamkar kisan kai mutun yayi, da zubarwa zanyi wallahi." Fad'in Sarah. "Don Allah ki gwada! Da na baki tsan-tsan mamaki don kin san Allah sai na kuma yi maki real ciki kin haihu." Kuka Sarah ta saka tare da fad'in, "Kuma ba zan fito d'in ba. Mugu kawai!" "Dan Allah ban rok'eki ba, kar ki fito d'in cikin mintuna biyu rak." Yana gama fad'in haka ya katse wayar. "Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wannan wani irin jaraba ce haka? Ga duka ga tsinke jaka." Fad'in Sarah tare da share guntun hawayen da suka zubo mata ta nufi wardrobe ta d'auki Vail madaidaici ta yafa a kan riga da skirt d'in jikinta wanda ya amshi k'irar jikinta cif-cif. Babu ko hoda a fuska sai wani d'aure fuska take yi tare da fita waje ba tare da ta kalli y'an uwanta dake tsakar gidan ba. Babu mai shigar arziki a cikinsu. Marfu'a ma shayar da y'arta Fadwa take yi y'ar shekara d'aya da wata biyu. Ko kasheta za ayi baza ta iya nuna uban y'ar ba saboda yawan samarinta. Ga y'ar fara tas kyakkyawa kamar mahaifiyarta. Don duka Y'ay'an Lami kyawawa ne, duk da Lamin ita ma ba laifi tana da kyau, Sai dai ita bak'a ce, hasken Baba suka yo da kamannin fuskansa shiyasa gaba d'aya suke kama da juna sai dai wancen tafi wancen dogon hanci, ko kuma k'irar jiki. Wata kuma dimple gareta, wata kuma wushirya. Masu dimple d'in sune, Sarah, Na'ima da Hassana, masu wushirya kuma, Aina'u, Nuratu da Marfu'a, Lukman ne kawai ya d'auko Lami kaf, kamanni da hasken fata. Sai Aina'u da itama ba fara bace sosai kamar sauran y'an uwanta. Kuma ita tana da d'an jiki irin na mahaifiyarsu. Da kallo suka bi Sarah dukkan su, kuma babu wanda ya tambayeta ina zata je. Tura k'ofar gida tayi tare da fita ta coge a k'ofar gidan tana k'arewa motar da yake ciki kallo ta gefen ido tana mamaki shi motoci har nawa gare shi haka. Shima kuwa ta cikin tinted glass window d'in yake k'are ma halittar jikinta kallo yana mai jin wani irin matsanaicin kishi na taso mata. Domin gyalen dai bai da maraba da babu don babu abunda ya b'oye a jikinta. Ga shape d'inta da ya fito kamar zanata aka yi. Hannu ya kai ya d'auki glasses d'insa ya mak'ala a idanunsa tare da bud'e motar ya fito, luckily sai ga wasu almajirai su biyar zasu wuce, da hannu ya yafito tare da bud'e boat ya nuna masu abunda zasu kwashe su kai gidansu Sarah. Sarah na ganin uban kayan da ake fitowa dasu a cikin boat, back seat da kuma front seat ta bud'e ido tana mamaki don kamar za'a bud'e shago. Sai da aka gama kwashe kayan tsaf ya sallamesu sannan ya nufi wajenta don tuni ta bawa almajiran nan waje ta koma gefe. Fuskan nan b'utu-b'utu ya kalleta tare da zare glasses d'in fuskansa. Lokacin da Sarah ta d'ago ta saka idanunta cikin nasa, sai da gabanta ya fad'i ganin yanda launin idanunsa suka canza, duk lokacin da ta kalli idanunsa a wannan yanayin, tuno mata da ranar da aka samu cikin jikinta yake yi. "Ke har yanzu baki yi hankali ba ko Sarah!" Duk lokacin da ya furta sunanta, sai taji duk duniya babu wanda ya iya kira kamarsa. "To ni kuma mai nayi yanzu?" Ta fad'i tana mai turo baki. Ko kamun yayi wata magana, Lami ta turo k'ofar gidan tare da fad'in, "Sannu-sannu! Sannu da k'ok'ari yaron arziki! Wannan irin uban kaya haka? Kai an gode sosai. Ai irin ku ake so masu hannu a bud'e. Allah yayi maka albarka." Fad'in Lami tana washe baki. Sarah kuwa ji tayi kamar ta kwalla ihu tsabar takaici. Don Lami ta riga ta gama zubar mata da mutunci. Shi kuwa _Khalilullah_ ko kallonta bai yi, sai cewa kawai yayi, "Ameen." Yana kallon fuskan Sarah da ta gama b'ata masa rai. Juyawa Lami tayi ta koma ciki. Sarah kuwa sunkuyar da kai tayi tana jin hawaye na taruwa a idanunta. "Kar ki yarda wannan hawayen su zubo _Mine_, kar ki yarda su zubo don idan suka zubo nayi maki alk'awari sai na lashe su tsaf kuma a titin nan." Da kyar Sarah ta iya maida hawayenta suka koma, don ta san tabbas duk abunda _Khalil_ ya fad'a zai iya yin fiye da haka tun da dai yanzu haka cikinsa ne a jikinta. "Dan Allah kayi hak'uri da halin mahaifiyata." Mai makon yayi sharhi akan maganar da tayi, sai cewa yayi, "Sarah idan kina son zaman lafiya dani, kuma kina gudun abunda zai je ya dawo, to kar in kuma ganinki da irin d'an iskan gyalen nan. Wai ke baki san ba irinku bane suke saka gyale ba? Wallahi yawancin mata ku kuke ja ana yi maku fyad'e. Kin san cewa Allah yayi ku ma Sha Allah ta yanda ba kowani namiji zai iya had'iye miyansa akan ku ba, amma sai ku rik'a fitar da surar jikinku. Wasun ku ma har k'ari suke yi don kawai su burge samarin. To ni wallahi ban so, kuma ban so na sake ganin irin haka. Ki kiyaye ni _Mine_. "Wai wani _Mine_ sabida kinibibi. Ko ta ina na zama na shi oho!" Fad'in Sarah amma a zahiri sai cewa tayi, "Zan kiyaye daga yau in Sha Allah!" Politely ta fad'i maganar. Shi kuma _Khalil_ yace, "That's very good. Allah ya baki iko. Yanzu menene kike buk'ata?" "Turaren jikinka." Ta fad'i a cikin zuciya saboda yanda k'amshin yake fizgarta, don na yau ma yafi mata dad'i akan wanda ya saba sakawa. Amma a zahiri sai cewa tayi, "Babu komai. Ni babu abunda nake buk'ata. Abunda ka kawo yau ma yayi yawa." Harararta yayi tare da fad'in, "To ke na kawo mawa? Ni su Baba da mama da y'an uwanki da kuma babyna dake cikinki na kawo mawa. Akwai chocolate, wannan duka naki ne, au na baby na. D'an kai hannu cikinki ki fad'awa babyna daddynsa na gaishe sa." Ko kallonsa bata yi ba, balle tayi abunda yace, kuma dama shima ya san ba yi za tayi ba. Yana kallonta sosai, bini-bini zata shak'i iska ta lumshe idanu, ya karanci psychology, hakan ya fahimtar dashi abunda Sarah take shak'a. Murmushi yayi tare da fad'in, " _Mine_ akwai abunda kike so amma jik'imarki ta hana ki bud'e baki ki fad'a min ko?" Bud'e idanunta tayi a kansa tare da fad'in, "Ni babu abunda nake so. Kawai zuciyarka ce ta fad'a maka gaibu." Kallonta yayi na second hud'u sannan yace, "Ki rantse da girman Allah turaren jikina baya fizgar hankalinki har yake saka ki lumshe idanu." Mamaki ne ya kashe Sarah ganin ya d'ago jirginta. Sai ta diririce ta rasa mai zata ce sai kawai tayi shuru tana kallon k'asa. Komawa mota yayi, mintuna biyu sai gashi ya dawo da kwalin turaren *_Imperial Majesty_*, bakinsa kuma yana taunar masoyin nasa _Mastika gum_. "Wai kai baka gajiya da cin chewing gum ne?" Fad'in Sarah wacce bata ma san lokacin da tayi masa wannan tambayar ba. "Kin tuna wancen ranar haka kika ce min mai d'abi'u _KARUWAAA_?" Sai da ya,ja waa d'in yana dariya. Rufe fuska da hannunta Sarah tayi tare da fad'in, "To ai kai d'in ne ka cika cin chewing gum." "Shikenan kuma duk mai cin chewing gum ya zama karuwa ko? To ai gashi kin tunzurani kin saka nayi maki halin karuwan har gaki da tsaraba." Da gudu Sarah ta juya zata gudu ya rik'e hannunta tare da saka mata kwalin turaren a hannunta sannan yace "A sauka lafiya, a kuma gaishe min da Baba." Yana gama fad'in haka ya sakar mata hannu ita kuma ta shige cikin gida da sauri. Da gudu Lami ta rungumeta tare da zabga gud'ar da ya karad'e gidan, hatta Baba dake d'aki sai da ya toshe kunne yana fad'in, "A'uzu billahi minash shaid'anir rajim!" Lami kuwa sai ta hau yiwa Sarah kirari, "Yarinyar mai goshin arziki, yarinya mai k'irar matan manya! Gabanki fari bayanki fari k'al, d'awisu duk inda kika gitta sai an kalleki. Wuhuhuuuu ina gwanin wani ga nawa gwanar. Ni na san banyi asarar haihuwa ba wallahi. Kai jama'aa." Tana fad'in haka sai ta hau rawa da wak'a irin na matan zumunta, sai dai bata kiran sunan yesu almasihu sabida kar Y'ay'an su b'aro jirginta don duk da basu sallah, sai sun ga dama, baza suji dad'i ba idan suka fahimci ta koma addinin kiristanci wanda take ganin shine addinin gaskiya a gareta. Sarah kuwa sarai ta faminceta, a zuciyarta sai addu'ar shiriya take nemawa mahaifiyar tasu akan ta gane gaskiya ta natsu. Aina'u kuwa wani dogon tsaki tayi tare da fad'in, "A dai yi mu gani idan tusa zata hura wuta." A cikin zuciyarta. Sarah kuwa kaucewa tayi ta shige d'akinsu ta kwanta a kan gado tana tuno ranar data fara ganin _Ibarahim Khalilullah_ a rayuwarta. Tun da ta taso k'awa d'aya tal tilo take dashi a rayuwa, Muniba. Muniba na d'aya daga cikin mutanan da suka d'aura ta a kan hanyar madaidaiciya domin if not because of her she would have joined her siblings. Amma kasancewar Muniba ta taso gidan mutunci da tarbiya, don babanta shine limamin masallacin _Mai duguri road_, kuma an d'aura su akan ingantacciyar tarbiya. Makarantar bokonsu d'aya tun daga primary five har suka kammala secondary school, Muniba tayi k'ok'ari sosai wajen saita Sarah a kan hanya madaidaiciya, don farko itama ta soma d'auko rawan kai da y'an gidan. Irin su shigar banza, zagin d'an Adam duk tsufansa, rashin kunya da saurarsu. Muniba ita tayiwa Sarah registration na islamiyar da take zuwa *_MADARASATUL TATBIQUT TA'ALLIMUL ISLAMIYA_*, kuma makaranta ce da ba'a wasa ko kad'an. Kuma da ikon ubangiji sai da Sarah tayi sauka sai dai bata samu damar cigaba ba kamar yanda Muniba ta cigaba. Baba Nuhu sosai yaji dad'in haka, don ko a wancen lokacin, Sarah ita mai k'aunar mahaifinta, kuma tana jin maganarsa sab'anin Lami. Don ita b'ata tab'a sha'awar karuwanci ba kamar yanda sauran y'an uwanta suke yi. Burinta shine tayi aure ta zauna a d'akinta k'ark'ashin kulawar miji. Sai dai Baba Nuhu bai da k'arfi sosai wanda zai iya biyawa Sarah kud'i both islamiya da boko don lokacin ta kammala secondary school har ta yi jamb kuma ta samu admission a polytechnic na tudun wada, kuma Evening. Kuma registration kawai 63thousand ne. An buga an buga babu ta inda kud'in nan zasu fito, kuma Lami tayi rantsuwa da Allah kwandala baza ta biya mata ba, tunda ita bata taimaki kanta ba, babu yanda za'ayi ita ta taimaka mata. Haka Sarah tayi ta fad'i tashi har ta samu aiki wa wani babban restaurant wanda zasu rik'a biynata 20k duk wata. A kuma wannan lokacin wani babban yayan Muniba ya gansu tare da Sarah a bakin titi lokacin zata tafi restaurant inda take aiki, ita kuma Muniba zata tafi poly don ita ba evening lectures take yi ba. Ai kuwa yana dawo gida ya fad'awa mahaifinsu yaga Muniba da yarinyar gidan karuwai. Bayan ta dawo daga school aka mata dukan tsiya kuma ana zama mata jan layi akan idan ta ketara ta kuma had'uwa da Sarah kashinta ya bushe kuma baza ta k'ara zuwa makaranta ba sannan aure za ayi mata kamun ta jawo masu abun kunya kuma da ko wanene aka samu za ayi mata auren. Wannan shine dalilin rabuwarsu da Muniba. Ko a hanya basu k'ara had'uwa ba tun bayan da Muniban ta fad'a mata abunda mahaifanta suka yanke. Don ko a wannan lokacin Sarah bata daina saka k'ananun kaya ba shiyasa kowa yake mata kallon y'ar iska. A restaurant d'in nan ta soma ganin _Khalil_ yaje cin abinci. Shi kuma idan bai ci abinci a gida ba, babu inda yake zuwa yaci abinci hankalinsa a kwance kamar wannan restaurant d'in. Don abincin gargajiya suke yi kala-kala mai dad'i da tsafta. Sau uku ana aikenta kai masa menu, kuma duk taje sai sunyi fad'a don kallon y'ar iska yake mata, ita ma kuma kallon da take masa kenan don kullum da chewing gum a bakinsa, duk da kuwa ba k'as-k'as-k'as yake yi ba. Amma ganin duk lokacin da tazo kawo masa Menu wani harara take jifansa dashi tana magana k'asa-k'asa, shi kuma sarai yana jin ta sarai, don ce masa take yi karuwa. Shi duk wajen babu wacce ya tsana irinta, haka itama. Dad'inta ma sai ya kwashi watanni bai zo ba. Ta kwashi tsawon shekara biyu tana aiki a wajen har ta kammala diploma d'inta. Ranar da suka yi sign out, bak'ar skirt ta sanya iri straight d'in nan mai tsagu ta baya, sai fara k'al d'in shirt da mutane suka yi signing da maka ta ko'ina a jikin rigar gaba da baya. Kanta kuma tayi parking d'in gashinta a tsakiyar kai da yaci uban acuci maza na attachment, babu d'an kwali a kanta, sai wani siririn Chantilly Vail da ta yafa. K'arfe shidda ta tashi a aiki, bayan ta gyara jikinta ta kuma fesa turare sannan ta nufi wajen madam za tayi mata sallama don ita take bata kud'in motar komawa gida. "Aunty na gama zan wuce." "Yauwa Saratu, karb'i wannan hanyar wucewa gidanku ne, zaki kai wannan sak'on *Golden diamond hotel*, wani customer d'in mu ne ke son tuwon shinkafa miyar egushi. Kuma shi abinci idan ba na nan wajen ba, bai son na wani waje. Please ki tsaya ki kiyi delivery d'in wannan sai ki wuce gida. Ga kud'in transport." Ta k'arisa maganar tare da mik'a mata 1k da kuma ledan take away a ciki. Karb'a tayi tare da juyawa ta fita daga restaurant d'in. Zuciyarta d'aya ta nufi hotel d'in kasancewar har numbern d'akin aunty ta fad'a mata. Tana zuwa reception ta samu wani inyamuri tayi masa magana, duk a tunaninta shi zai karb'a ya kai masa abincin. Amma sai taga inyamurin ya daga waya ya kira can d'akin yayi magana da wanda zata kaiwa abincin. "Ok Sir!" Shine kawai abunda taji ya fad'a tare da yanke wayar sannan ya kalleta tare da fad'in, "Madam you can go in!" Da kamar za tayi musu, sai kuma ta nufi hanyar da zai sadata da matattakar da zai kaita room number d'in da yake ciki. Knocking tayi, daga ciki aka ce "Yes come in!" Tura k'ofar tayi tare da shiga kanta a k'asa. Shi kuwa juyowa yayi hannunsa rik'e da waya yana amsa kira yana fad'in, "Hajiya Allah idan basu bar gidan nan ba bazan dawo ba. Haka kawai sun bi sun takura mana mu da gidan uban mu!" Dai-dai nan ya d'ago idanu ya sauke a kan Sara dake tsaye. "Hajiya zan kira ki ina zuwa." Yana fad'in haka ya katse wayar tare da jifan Sarah da mummunar kallo sannan yace, "Ko ina sai kin nuna rashin kamun kanki ko? Idan banda zubda da kai da rashin aji, duk mazan dake restaurant d'in naku a rasa wanda za'a aiko ya kawo min abinci sai ke." "Ni dai ba y'ar iska bace tunda de bana zaman hotel, kuma ba'a tab'a gani na ina taunar chewing gum kamar karuwa ba. Kallo d'aya za ayi maka a fahimci kai wani irin mutum ne. Kai ne mara kamun kai ba ni ba. Kuma ni ga abunda ya kawo ni hotel nan na ajiye maka." Ta fad'i haka tare da ajiye masa ledan a kan center table zata juya. Fizgota yayi tare da fad'in, "Ke wanene d'an iskan?" Fizge jikinta tayi tare da fad'in, "Kada hannunka ya k'ara tab'a jikina. Jikina yafi k'arfin ka wallahi. Ni ba gantalallun y'an matan daka saba kwanciya dasu bane anan hotel d'in. A fita a samu dai-dai da kai. Ni ba sa'ar ka bace!" A tsawace yace, "Wallahi idan kika k'ara magana sai na baki mugun mamaki anan d'akin." A tsawace Sarah tace, "Iya kaci kace zaka kashe ni ka b'oye gawata. Ni dalla malam matsa min a hanya in wuce don wari da k'arni zina ya ishe ni." Tana maganar ne gabanta na fad'uwa amma tsaurin idanunta ya hanata yin shuru. Wani gigitaccen mari ya dauketa dashi tare da fad'in, "Zan nuna maki halin karuwan da kike ambata na dashi kullum." Yana gama fad'in haka ya danna switch d'in d'akin wuta ya d'auke tare da d'agata cak ya jefa kan gado. Wani irin ihu ta saki tare da mik'ewa zata duro daga kan gado amma ya riga ta hawowa kan gadon tare da yi mata rumfa kuma ya sakar mata nauyinsa gaba d'aya a jiki sannan yayi amfani da hannunsa ya zame shirt d'in jikinta. Jin ta damesa da ihu ya kai hannu ya bige bakinta tare da fad'in, "Dama ai kin saba bin mazan, ihun uban mai kike min." Duk da tana cikin mugun tsoro da tashin hankali hakan bai hanata magana ba tace, "Mugu azzalumi, mai halin karuwai. Wallahi sai na kashe ka idan kayi min wani abu." Bai saurareta ba ya kai hannun ya d'aga rigar jikinta ya cire, jikinta sai rawa yake yi, da taga fa tabbas dagaske yake yi zai rabata da mutuncita da take tak'ama dashi, kuma ga alk'awarin da tayiwa Farouq wanda da kyar iyayensa suka amince ya turo gidansu har aka tsaida maganar aure. Sai ta fashe da kuka ta soma rok'ansa tana bashi hak'uri. Shi kuwa tuni ya cire hook d'in bra d'inta ya shiga wasa da ilahirin lallausar jikinta. Abunda bai tab'a tun da uwarsa ta haifesa, sai gaba d'aya ya rasa nutsuwarsa, don bai tab'a body contact da mace ba a tsawon rayuwarsa. Don ko side hug bai yarda dashi ba. Tunaninsa ya bar jikinsa har bai san lokacin da ya zame wandon jikinsa ba ya ware k'afafunta tare da yunk'urin shiga jikinta. Wani mahaukacin ihun da ta saki ne ya dawo dashi hankalinsa, da mad'aukakin mamaki ya kuma tura jikinsa a karo na biyu, amma still gan ya jita. Tun da yayi yunk'uri na biyu bai kuma yi ba, sai ya canza salon wasan kasancewar ya riga ya d'ad'd'ago sha'awarsa gaba d'aya. Jikinsa ya dunga gogawa a nata jikin kusan tsawon mintuna sha biyar har ya samu nutsuwa sannan ya mirgina ya bar jikinta yana maida numfashi. Ita kuwa Sarah kuka take yi sosai duk da kuwa ta san bai isa ga jikinta ba. "Mugu azzalumi kawai." Ta fad'i tana kuka. Shi kuwa idanunsa a rufe yake fad'in, "Naji, duk nine. Kiyi hak'uri ki yafe min. Kin ga ai ban raba ki da budurcinki ba." A fusace tace, "Wallahi ba zan tab'a yafe maka ba. Karuwi kawai. Mijina ma ba zai tab'a yafe maka ba don ka cutar dashi ka shiga gonarsa." "Haka be naji duk ba amince. Kiyi hak'uri amma ki min afuwa. Tsautsayine wallahi ba hali ba bane." "Halinka ne Allah kuwa. Mugu mai lalata yaran mutane a hotel." Mik'ewa yayi ya tashi zaune. Da saurin ta mirgina sai ji kake tim a k'asa ta d'auka wani abun zai kuma yi mata. "Wayyooooo Allah na shiga uku k'afata." Ta fad'i da k'arfi dai-dai lokacin da ta d'auki boxer d'insa ya saka tare da saukowa ya kunna switch d'in d'akin. Da sauri Sarah ta jawo zanin gadon ta rufe jikinta tana kuka sosai da bak'in cikin abunda yayi mata. Matsowa yayi domin yaga halin da k'afar take ciki, wani irin ihu ta saki tare da k'ank'ame jikinta. Matsawa yayi yana kallonta. Ita kuwa sai k'ara kakkare jikinta take yi tana kuka. "I'm sorry kin ji. Ina zuwa yanzu bari na dawo." Ya fad'i hakan tare da d'aukar dogon wandonsa ya saka da riga ya fita da sauri. Sarah na ganin ta fita ta mik'e da sauri ta d'auki kayanta ta saka. Ko tsayawa d'aukar jakarta bata yi ba domin kada ya dawo ya idda ita. Da sauri ta bud'e d'akin ta fice daga hotel d'in tana b'oye-b'oyen fuska. Lokacin da _Khalil_ ya dawo bai d'auka bata d'akin ba ganin ga jakarta a kan gadon. Zama yayi a gefen gado hannunsa rik'e da wani magani yana jiran fitowarta daga bayi, mintuna biyar suka shud'e yaji shuru, wani biyar d'in ya k'ara shud'ewa nan ma shuru. Mik'ewa yayi tare da isa k'ofar bayin ya soma kwankwasawa, jin shuru sai ya tura k'ofar. Wayam ya gani. Da mugun sauri ya tashi ya fita ya dunga dube-dube ko zai ganta, amma babu ita babu dalilinta. Gashi babu wani makama da zai gane inda take, ko sunanta bai sani ba. Komawa cikin hotel d'in yayi tare da bud'e d'aukar jakarta da wani abu kamar d'an kwali da ta bari ya fita ya bar hotel d'in. Tun daga wannan ranar _Khalil_ bai sake farin ciki ba, kullum cikin neman Sarah yake yi. Kuma Allah bai k'ara had'a su. Sai bayan kwanaki ashirin da uku a asibitinsa. Aina'u ba k'aramin tashin hankali ta shiga ba ganin irin uban kaya da _Khalil_ ya jido. Ji take kamar zuciyarta zata hudo k'irjinta ta fito tsabar bak'in ciki. "Hajiya tun d'azu ake kiran wayarki." Fad'in Laure tana mai mik'awa Hajiyar waya. Amsa Hajiya tayi bayan ta shafa addu'a don sallar magriba ta idar kuma dai-dai nan aka kuma kiran wayar. "Assalamu alaikum" Fad'in Hajiya bayan ta amsa kiran ta kara a kunne. "Wa'alaikissalam, dan Allah Ina magana da Hajiyar doctor _Ibrahim Khalil_ ne mai asibitin *_Khalilullah specialist hospital_*?" Kallon Laure Hajiya tayi tare da mata nuni da hannu alamar ta fita bayan ta amsa da "Eh ita ce. Allah yasa lafiya?" Daga can aka d'an yi jim kamun wacce ta kira wayar ta soma fad'in, "Hajiya akwai wani abu da d'anki yake b'oye maki mai matuk'ar muni wanda ke baki sani ba. Kuma a irin tarbiyan da kuka bashi idan na fad'a maki abunda yake aikatawa, sai kin girgiza." Hankalin Hajiya tuni yayi wani irin mugun tashi ta soma fad'in, "Baiwar Allah ya zaki kira ni kina fad'a min irin wannan maganganun masu d'aga hankali? Mai _Khalilullah_ yake aikatawa wanda ban sani ba?" "Uhm! Hajiya idan d'an ki ya dawo, ki tambayesa wacece Saratu?" Mik'ewa Hajiya tayi tana fad'in, "Dan Allah yarinya kiyi maganarki kai tsaye, mai _Ibrahim_ yake aikatawa wanda ban sani ba?" "Hajiya d'an ki dai yana da budurwa, ko kuma ince maki dadironsa! Don kuwa yanzu haka da nake fad'a maki, ki fara tanajin jiran isowar jika nan da wata takwas masu zuwa, don kuwa d'an ki yana neman wata yarinya wacce gaba d'aya gidansu karuwai ne kowa ya sani. Sunanta Saratu ana ce mata Sarah. Tana da yayyi mata hud'u, kuma gaba d'ayansu babu wacce bata ajiye shege ba a cikin gidan. Sannan kowa ya san su karuwai ne. Kuma abunda zai baki mamaki, a gaban uwarsu da ubansu suke. Idan kuma baki yarda da maganata ba, idan _Khalil_ ya dawo tambayar da zaki fara yi masa shine wacece Saratu. Yanayin da zai nuna kawai ta isa ya tabbatar maki da zance na. Na barki lafiya Hajiya." Tsabar tashin hankali da rikicewa Hajiya fitsari ta soma saki ba tare da sani ba, da rarrafe ta shiga bayi ta soma sakin zawon tashin hankali............ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* *_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 13* *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* Abu kad'an ke saurin d'aga mata hankali. Babu mamaki yanzu idan aka duba BP d'inta aga ya hau. Ta jima duk'e a bayin kamun ta iya cire kayan jikinta tayi wanka sannan ta sake d'auro alwala ta fito ta sauya kaya. Tuni wani zazzafan zazzab'i ya rufeta sai kakkarwa take yi a bakin gado. Dai-dai nan Laure ta shigo bakinta d'auke da sallama tana fad'in, "Hajiya a kawo maki zogalen yanzu?" Da sauri ta k'arisa shigowa d'akin tana fad'in, "Hajiya lafiya? Mai ke damun ki? Yanzu fa na barki lafiya kina amsa waya." Dakyar Hajiya tace, "Tafi ki kira min Maryamu yanzu a b'angarensu." da sauri Lauren ta juya ta bar d'akin har da had'awa da gudu ta nufi side d'in aunty Maryam tare da danna doorbell. Mijinta Yaya Abdul-Hakeem ne yazo ya bud'e k'ofar tare da fad'in, "Lafiya Laure na ganki a rud'e?" Ya fad'i don shima dawowarsa kenan daga wajen aiki. Yanzu nan kuma yake son shiga wajen Hajiyar. "Yaya Abdul Hajiya ce ba lafiya shine tace in kira mata aunty Mar....." Ko kamun ta k'arisa maganar har ya tureta ya fito da sauri ya nufi side d'in Hajiyar kamar zai tashi sama. Aunty Maryam ma da sauri ta fito don fitowarta kenan daga kitchen taji abunda Laure ke fad'awa mijin nata. Bin bayansa suka yi ita da Lauren hankali tashe. Ko da yaya Abdul ya isa d'akin Hajiya, gaba d'aya ta gama firgicewa. Jikinta yayi mugun zafi musamman ta wajen kanta. Zama yaya Abdul yayi tare da tallabo Hajiyar yana fad'in, "Inna lillahi! Hajiya mai ya same ki. Ai bamu ga ta zama ba. Mu tafi asibiti kawai." Dai-dai nan aunty Maryam d'in ta shigo ita da Laure. "Abdul-Hakeem d'au wayarka yanzu ka kira min _Khalilullah_." Hajiya ta fad'i hakan da kyar. Yaya Abdul bai kawo komai a ransa ba sanin k'anin nasa ai doctor ne. Maybe don yazo ya duba tane don Hajiya ta tsani zuwa asibiti. Wayarsa ya fiddo tare da kirar _Khalil_ d'in. Ringing yayi har ya katse ba'a d'aga ba, zai sake kira kenan sai ga shigowar kiran _Khalil_ d'in. D'agawa Abdul-Hakeem yayi tare da fad'in, "Kana ina?" Daga can _Khalil_ yace, "I'm sorry yaya, na fito da wayar kenan zan d'auka sai katse. Gani kusa da gida." "To kayi maza ka shigo yanzu. Hajiya ba lafiya." Yana gama fad'in haka ya katse wayar. _Khalil_ kuwa ji yayi gaba d'aya hankalinsa ya tashi. K'ara gudun motar yayi duk da yana gab da layin. Mintuna biyar suka k'ariso dashi gidan. Ko parking mai kyau bai yi ba ya shigo gidan ya nufi d'akin Hajiya kai tsaye. Nan ya tarar dasu sun yi curko-curko. "Hajiya mai ya same ki, taso mu tafi asibitina dan Allah." Da kyar Hajiya ta d'ago kanta ta zubawa _Khalilullah_ idanu tare da fad'in, "Abdul-Hakeem ku d'an bamu waje." Tana fad'in haka gaban _Khalil_ ya yanke ya fad'i. Don har ji yayi wani k'aramin zufa ya gangaro daga goshinsa. Abdul-Hakeem babu musu ya mik'e ya fita, aunty Maryam da Laure suka bi bayansa tare da rufo masu k'ofa. _Khalil_ shuru yayi kamar ruwa ya cinyesa, don hakanan jikinsa Hajiya ta gano abunda yake b'oyewa. " _Ibrahim_" Hajiya ta kira sunansa da muryanta da yayi rauni. Hankalin _Khalil_ ta tashe yace "Na'am Hajiya." "Wacece Saratu?" A mugun furgice duk da kuwa zuciyarsa na bashi ta gano ko kuma wani ya fad'a mata ya d'ago bakinsa na rawa yace, "Haj..... Hajiya ban gane abunda kike fad'i ba." Hannu Hajiya ta d'aga ta wanke masa fuska dashi tare da fashewa da kuka tace, " _Khalilullah_ ka b'ata wayanka. Baka kyautawa kanka ba. Dadiro _Ibrahim_? Yanzu har kayi rik'an da zaka ajiye dadiro a waje _Khalil_. Kana da kud'i, kana da wajen zama, duk wani abu da namiji zai mallaka kamun yayi aure, ka mallaka _Mu'azzam_, amma shine sabida shaid'an ya buga maka gangi, giyar kud'i na janka, shine zaka butulcewa Allah ta hanyar yin abunda ya haramceka dashi. Ka bani mamaki _Khalil_. Ashe irin tarbiyan da muka gina ku a kai ni da mahaifinku, watsar dashi kayi? _Khalil_ baka yi wa kanka da mu adalci ba. Ka b'atawa zuri'ar suna. Ashe dai da gaskiya su Ameeru da suke cewa ka ajiye dadiro. Shiyasa a kullum burinsu shine suyi maka aure sabida sun san lalatar da kake yi a waje. Baka min adalci ba _Mu'azzam_!" Ta k'arisa maganar tana mai fashewa da kuka takaici. Shima _Khalil_ d'in kukan ya soma yana fad'in, "Hajiya dan girman Allah kar kiyi mani kuka. Kukanki bala'i ne a gare ni. Ki tsaya inyi maki bayani. Duk wanda ya fad'a maki na ajiye dadiro wallahi sharri yake min kawai yana son shiga tsakanina dake ne. Wallahi tallahi ban tab'a ajiye dadiro ba a rayuwata. Kuma Hajiya ban tab'a ratsa jikin wata y'a mace ba. Ban san ta yanda zan yi maki bayani ba ki fahimceni ni." Hajiya tsagaita kukanta tayi tare da fad'in, "Kenan sharri ake maka baka san wata Saratu ba." Girgiza kai yayi tare da fad'in, "Na santa Hajiya, amma ba ta yanda kike tsammani ba. Ita ce wacce nake fad'a maki ba tsayar matsayin wacce zata zama uwar y'ay'ana." Wani ajiyar zuciya Hajiya ta saki, sai kuma tace, "To maganar ciki fa? An ce kayi mata ciki in tsammaci zuwan jika nan da wata takwas. Ya matsayin wannan maganar take?" Shuru _Khalil_ yayi yana kallon k'asa. Sai kuma ya d'ago tare da kama hannayen Hajiya duka biyun yace, "Hajiya dan girman Allah kiyi hak'uri da abunda zan fad'a maki yanzu. Amma ki saurare daga baya sai ki yanke hukuncin da kika ga ya dace. Dagaske Sarah tana d'auke da ciki, kuma nawa ne." Tass Hajiya ta sauke masa mari tare da nuna masa k'ofa tace, "Fita! Fita nace ka bar min d'aki yanzun nan!!" Ta kuma fad'i a tsawace. Da sauri ya mik'e tsaye tare da fad'in, "Haj......" "Fita _Khalil_ kar ka sa nayi abunda zan dawo ina dana sani. Fita nace kar in fad'i mummunar kalma a gare ka." Fad'in Hajiya tana matsar hawaye. Da sauri _Khalil_ ya fita tare da rufo mata k'ofar. Shi babban tashin hankalinsa, kar jininta ya hau. Yana fitowa daga d'akin ya nufi waje ya zauna tare da kama kansa har akai kiran sallar Isha sannan ya mik'e ya nufi masallaci. Hajiya kuwa kuka tayi sosai har da majina. Bayan ta idar da sallar isha'i wanda tayi sa da kyar, sannan ta lalubi wayarta ta dannawa babban wansu soja mai muk'amin *_LTG (Lieutenant general)_* dake zaune a abuja, a can yake da iyalansa gaba d'aya kasancewar aikinsa a can yake. Bugu d'aya yayi rejecting tare da karanta, "Assalamu alaikum Hajiya." "Amin wa'alaikassalam." Tun daga yanayin yanda ta amsa kiran ya tabbatar babu lafiya, mik'ewa yayi d'aga kwancen da yake ya zauna tare da fad'in, "Hajiya lafiya? Mai ke faruwa?" Kuka Hajiya ta fashe dashi tare da fad'in, "Marmari daga nesa (Bata kiran sunansa kasancewarsa d'an Faari) duk abunda kake yi ka d'auki sakuis (excuse) kazo gida gobe, kuma ka kira wancen yaron na Kano shima ina son ganinsa har da k'anwarku Aisha. Duk kuzo ina neman ku gobe." Gaba d'aya tunanin _LTG Abdallah_ akan maganar gadonsu ne, don wani lokacin haka uncles suke sako mahaifiyar nasu a gaba duk akan dukiyar da mahaifin nasu ya bari. "Dan Allah Hajiya ki kwantar da hankalinki, in Sha Allah gobe zan biyo jirgi ni da Aysha. Zan kira mijinta yanzu ina gama waya dake." Fad'in LTG Abdullah don Aysha d'in a nan Abuja tayi aure, kusan a hannunsa take, don shi ya aurar da ita. Ita ma soja take aure ana Abujan. Katse wayar Hajiya tayi tare kifa kanta a kan pillow tana zuciyarta na mata zafi, gaba d'aya Y'ay'anta daga maza har matan lafiya k'alau ta aurar dasu, Nafeesa ta je gidan mijinta lafiya, haka Aysha. Mazan ma gaba d'aya babu wanda ya d'auko mata abun kunya sai _Khalilullah_. Kuma duk cikin y'ay'anta shi, yana da wani special guri a zuciyarta. Don shi d'in favourite d'inta ne. Duk da kuwa ba shine auta ba. Nafeesa ce autarta. B'angaren _Khalil_ kuwa yanda yaga rana, haka yaga dare. Abun duniya duk yabi ya ishesa. Sam ba ta haka yaso hajiya taji wannan maganar ba. Yaso ya shaida mata da kansa ta hanyar da ko zata jijjiga ba kamar haka ba. Tunani ya dunga yi wanene ya san abunda ke faruwa har ya d'aga waya ya kira Hajiya, "Doctor Kamal!" Fad'in _Khalil_ a bayyane. Da sauri ya mik'e zaune yana jin wani irin matsanaicin b'acin rai da tsanar doctor d'in. "Wallahi sai na baka mamaki Kamal. Ni zaka had'a da mahaifiyata. Zaka san koni wanene. Daga kai na baza ka k'ara irin wannan munafurcin ba." Saukowa yayi ya nufi bayi yayi alwala tare da fitowa ya shimfid'a darduma ya dunga yin sallah yana rok'an Allah sauk'i da sassauci akan lamarin. Bai tashi daga kan darduma ba sai da yaji kiran sallar asubahi na shiga masallaci sannan ya mik'e ya fito. Sai da ya fara bi ta d'akin Hajiya tukun, da sand'a ya murd'a k'ofar a hankali tare da bud'ewa. Karaf suka had'a idanu da Hajiyar dake zaune a kan darduma, don kamar yanda ya kwana sallah haka ita ma. Da sauri ya jawo k'ofar ya rufe tare da barin wajen ya nufi masallaci. Sai bayan da aka idar da sallah har fito zai koma cikin gida yayansa Abdul-Hakeem ya tare sa, bayan sun gaisa yake ce masa, " _Khalil_ mai ke faruwa Hajiya tayi kiran kowa na gidan nan cikin gaggawa? Yaya Abdullah ma yana hanya zuwa anjima zai biyo jirgi shi da Aysha. Kuma nima Hajiya ta saka na kira mijin Nafeesa akan ha kawo ta gobe. Wani irin meeting kuma za ayi yau a gidan nan? Allah yasa ba dai akan rigimar gado bane. Nifa wallahi abunda Papa ya tafi ya bari bai tab'a d'ad'ani da k'asa ba, abun na tara da gumina ma ya ishe ni zaman duniya." Tun da ya fara maganar _Khalil_ jinsa kawai yake yi amma kwakwalwarsa da tunaninsa sun yi nisa tun lokacin da yace masa yaya Abdullah na hanya. Wannan masifaffan mai bak'ar zuciya kamar da taurin kai. Don shine ya d'auko Papa sak. Shi kaifi d'aya ne, idan yace yes, to ko duniya zata tashi yes d'in ne, idan kuma yace no, tofa ko ana ha maza ha mata babu mai canza shi. Kuma duk gidan tsoransa ake ji. Shine babba kuma zai iya kaiwa shekaru hamsin da biyar a duniya. Daga shi sai yaya Barrister (Muhammad Kabir) kenan, shi yana da sanyi hali. Ba k'aramin abu ke b'ata masa rai ba. Idan kaga yana zafi da magana sosai, to fa a kotu ne musamman idan Shari'a ake yi akan fyad'e. Shi yaci gajiyar Papa don tun yana k'aramin yake fad'in "Papa idan na girma irin aikinka zan yi in rik'a Yankewa mugaye hukunci. Daga Barrister sai Abdul-Hakeem wanda shi kuma SSS ne, (D'an sandar farin kaya). Daga shi sai _Doctor Khalilullah_, sai Aysha, sai auta Nafeesa. "_Khalil_ kana jina kuwa." Fad'in ya Abdul yana tab'a hannunsa ganin yayi zurfi a tunani. "No, babu komai ina zuwa." Fad'in _Khalil_ tare da nufa part d'in Hajiya. Kai tsaye d'akinsa ya shige yana safa da marwa. Kwankwasa k'ofar d'akinsa aka yi, da sauri ya juya yana kallon k'ofar. Hannu ya kai ya danna wani switch sai ga Laure ta bayyana akan screen d'in dake saman k'ofarsa. Ajiyar zuciya yayi tare da nufa k'ofar d'akin ya bud'e, "Yaya _Khalif_ ina kwana?" Saude ta fad'i a sanyaye don tun jiya take jinta wani iri ganin uwar d'akinta babu lafiya. "Lafiya k'alau ya aka yi?" Ya amsa tare da jefa mata tambaya. "Hajiya ce tace in fad'a maka yau kar ka bar gidan nan akwai bak'in da zasu zo anjima." Shuru yayi yana kallon Laure kamar ita ce Hajiyar, can kuma ya nisa tare da fad'in, "Ok, to jeki." Yana gama fad'in haka ya rufo k'ofar tare da zama a bakin gado ya rik'e kai. Gaba d'aya natsuwa ta bar jikinsa. Gabansa sai dukan tara-tara take yi. Bai isa sakawa cikinsa ko ruwan Lipton ba har k'arshe sha d'aya yana nan zaune a d'aki yana sak'awa da warwarewa. Su aunty Maryam da Laure kuwa, sai kaiwa da komowa suke yi a kitchen suna had'awa bak'i abinci. Nafeesa ta riga kowa zuwa kasancewar ita mazauniyar Kaduna ce. Ana tayi aure a kabala shooting range. Hankalinta sosai ya tashi ganin halin da mahaifiyarsu take ciki. Don har a wannan lokacin jiri hajiye take gani, kuma idanunta sunyi luhu-luhu alamar taci kuka. "Hajiya dan girman Allah mai ke faruwa? Idan dai akan su uncle ne, dan Allah ki fitar da damuwarsu a zuciyarki. Har kuka gama zaman ku da Papa bai saka maki ciwo ba, sai y'an uwansa ne zasu buwayeki. Dan Allah Hajiya ki bari." Girgiza kai Hajiya tayi tare da fad'in, "Uhm, baza ki gane ba Nafeesa, bari dai sauran y'an uwanki su iso. Ni ba akan y'an uwan mahaifinku bane. Da sune ne abun da sauk'i." Shuru Nafeesa tayi tana tunani a zuciyarta to mai ya faru idan har ba su uncle bane. K'arfe sha d'aya da mintuna arba'in, yaya Barrister ya iso gidan shi da matarsa aunty Khairat da yayansu uku, Sam'an, Sahla da Nu'aima. Nan aka dunga oyoyo-oyoyo. Ko mintuna goma basu yi da zuwa ba, soja marmari daga nesa, LTG Abdullah ya iso shi da Aysha da kuma tawagar sojojin da suka yiwa unguwar k'awanya. Don gaba d'aya unguwar sai da suka shaida *_Lieutenant General Abdullah Nurudden Muhammad_* ya shigo unguwar. Tun da _Khalilullah_ ya lek'o ta window ta can saman d'akinsa yaga uban sojojin sun gewaye gate d'in gidan, wasu ma har ta cikin gidan yaji kamar an cire lakar dake jikinsa. Laure gaba d'aya ta rud'e don har wani zawo-zawo take ji sabida ba k'aramin tsoro da shakkar _LTG Abdullah_ take yi ba. Don shi fuskansa ma bata cika fara'a ba. Kai tsaye gaba d'aya suka wuce d'akin Hajiyar ban da _Khalil_ da ko lek'owa parlor bai yi ba. Har k'asa k'asa ya _LTG_ ya duk'a gaban gadon da take tare da fad'in, "Hajiya ina wuni, mun same ku lafiya? Ashe baki ji dad'i ba. To menene amfanin _Ibrahim_ a cikin gidan nan da ba zai iya kai ki asibiti ya duba ki ba. Wallahi wani irin iskanci ne. Ina yaje?" Hawaye Hajiya ta soma yi tare da fad'in, "Ni na hana a kai ni asibitin, don ciwon dake damuna, _Khalil_ d'in ne sanadiyarsa. Marmari, _Khalil_ ya b'ata mana sunan famili. Ya rusa duk wani tarbiyar da muka ginasa akai. So mu had'u mu duka a parlor, bayan anci abinci, sa muyi maganar." Kai a k'asa zuciyarsa na tafasa ganin mahaifiyarsa na hawaye yace, "Hajiya abinci ba zai ciwu ba, har sai naji abunda yake damunki nayi maki maganinsa tukun." Gaba d'aya su Barrister, Aysha da Nafeesa har da yaya Abdul suka ce, "Hajiya abinci tabbas ba zai ciwu ba har sai munji matsalarki." "Ku aika Laure ta kira _Mu'azzam_ a d'akinsa ya fito mu tafi can parlor ayi maganar a can." Mik'ewa Nafeesa tayi tare da nufa corridor d'in da zai sadata da d'akin yayan nata tana mamakin wani irin laifi ya aikata da har Hajiya take cewa ta b'ata masu sunan family. "To ko zubar da ciki yake yi a asibitinsa?" Fad'in Nafeesa cikin zuciyarta dai-dai lokacin da take knocking d'in k'ofar d'akina. Bud'ewa yayi, kallon fuskansa kawai za kayi ka tabbatar yana cikin tashin hankali. Kuma ba komai ke d'aga masa hankalin ba irin fushin Hajiya. "Nafeesa!" Ya fad'i a hankali yana kallonta. "Na'am yaya _Khalil_. Tun d'azu gaba d'aya muka zo amma babu kai a wajen. Hajiya tace kaje parlour duk muna can." Fitowa yayi gaba d'aya tare da kullo k'ofar yace, "Muje Nafeesa. Hankalina ne gaba d'aya a tashe. Har da ya Abdullah ko?" Gyad'a masa kai tayi suna tafiya a jere tare da fad'in, "Yaya _Khalil_ wai don Allah mai ke faruwa ne Hajiya ta kira mu gaba d'aya? Wani abun kayi ne?" Bai ce mata komai ba har suka k'ariso parlourn. Bai iya d'aga kai ya kalli kowa a cikinsu ba. Neman waje tayi daga gefe ya zauna kansa a k'asa tare da fad'in, "Ina wuni ya Abdullah? Sannu da zuwa ya Barrister. Kun zo lafiya?" Babu wanda ya amsa gaisuwarsa. Bai damu ba don dama ya san dole hakan zata kasance. Ya Abdullah kuwa duk ba sai ainahin abunda _Khalil_ d'in ya aikata ba, sai jifansa yake yi da wani irin mugun kallo. Su kad'ai ne a parlor, don ko Barrister da yazo da matarsa, tana can ita da Y'ay'anta a part d'in ya Abdul-Hakeem. Sune kawai isu-isu a parlourn. Don maganar tasu tana buk'atar privacy. "Abdul-Hakeem bud'e mana taro da addu'a." Fad'in Hajiya wacce ke hakimce a kan kujera tana girgiza k'afa. Sai bayan yaya Abdul-Hakeem d'in ya gama addu'ar sannan Hajiya tace, "Na kira ku ne anan wajen ba don komai ba, sai don saboda _Ibrahim_. Na san dukkan ku kun san bak'ak'en maganganu da kuma zagi da nake jurewa daga wajen dangin ubanku. Tun yana da rai suka kafa min k'ahon zuk'a har ila yau da ya kasance babu shi a raye. Kuma kun san cewa iyayenku suna son had'a _Khalil_ aure da Nina wanda shi kuma yak'i bada fad'in kai a cewarsa bata da kamun kai ita mazinaciya ce." Da sauri yaya Barrister yace, "Hajiya idan dai a kan wannan maganar ce ta Nina, to ba wai bane. Don ni da kaina na tab'a ganinta a wani babban hotel a Kano ita da wani sa'an mahaifinta." Da k'arfi Hajiya tace, "Kayi min shuru! Ai ita da _Khalil_ d'in zani ce ta tadda muje." Da sauri _Ya LTG_ yace, "Hajiya ban fahimta ba." Gyara zama tayi tare da fad'in, "Yanzu kuwa zaka fahimta. Kai _Khalil_ yi masu bayani abunda ka aikata." Kansa a k'asa gabansa na fad'uwa ya d'ago ya kalli Ya Abdullah, wata uwar hararar da ya watsa masa ya saka yayi saurin sunkuyar da kai k'asa." Wani mahaukacin tsawar da yayi, ba _Ibrahim_ kad'ai ba, hatta ita kanta hajiyar sai da ta tsorata. "Za kayi magana anan wajen ko sai na taso na taka cinyarka tayi dagwa-dagwa!" A razane _Khalil_ yace, "Hajiya wallahi, tallahi wa billahil azim ba halina bane. Tsautsayine ya saka nayi mata fyad'e har ta samu ciki." A mugun mamakance da bak'in ciki ya Barrister da ya Abdullah suka ce "Fyad'e!" Wani mik'ewa _Lieutenant Abdullah Nurudden Muhammad_ yayi tare da isa inda _Khalilullah_ yake tare da............ *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* *_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 14* Here are the list of my books: 👇 1. Anya uba nane? 2. Auren cikin gida (paid) 3. Ni da shi abu d'aya ne 4. Zina babbar bala'i ce 5. Bani da gata (paid) 6. Garwashi 7. Sai a lahira (paid) 8. D'an Faari (First born) (paid) Wani irin murmushi mugunta ta saki bayan ta kalli goron fantar. Bud'ewa tayi tare da jefa duka kwayoyin sannan rufe da k'arfi ta girgiza tare da saka shi cikin aljihun doguwar rigar dake jikinta ta nufi hanyar gida cike da jin dad'i. Ko da ta shiga d'akin, bata samu Sarah a ciki ba lokacin Baba yayi kiranta tana d'akinsa domin tattauna da ita game da batun aurenta da iyayen _Khalil_ suka yi. Sai ta ajiye fantar a dai-dai inda ta san Sarah na shigowa zata gani sannan ta bar d'akin ta koma d'akin Lami inda ta same su duka a d'akin suna tattauna game da zancen aure da iyayen _Khalil_ suka yi. "Kuma ke Lami sai ki yarda? Tabd'ijam! Bayan kin hana d'aya daga cikin yin soyayya mai zurfi balle har hakan ya saka mu bujire maki wata ran muce aure muke so. Ai kamar yanda muke zaune a gida har wannan lokacin, haka ita ma zata zauna babu wani zancen aure." Fad'in Aina'u wacce ta tsinci maganar daga sama kawai ta tsumbula baki. "Kuji min shegiyar yarinya! Ke da Naima wanene babba da har zaki bud'e baki kiyi wannan maganar. Ke da ko b'ari baki tab'a yi ba cikin gidan nan har kyayi wannan maganar. Wai ma Lami tana da samari ne masu fita da ita?" Fad'in Nuratu. "Ina fa!" Lami ta bada amsa a gajarce. "Har wani fad'i take kamar yanzu har yanzu bamu yi aure. Dudu-dudu fa bata wuce sha bakwai sha takwas ba amma har take wannan maganar. To Na'ima tace me ita da take da shekaru talatin da d'aya a duniya?" Dogon tsaki Na'ima taja tare da fad'in, "Bar y'ar iska. Lami dube ni nan in baki shawara idan zaki amsa. Kin ga, kar ki sake kice zaki ja game da batun auren Sarah da _Khalil_. Kin ga dai uban sojojin da suka zo gidan na d'azu, kuma da bakinki kike bamu labari Y'ay'anta gaba d'aya hukumomine, daga soja, sai d'an sandar farin kaya da kuma lauya. Kuma kin san akwai dukiya babu k'arya a wajen su. Wallahi Lami sai kin fi jin dad'i idan Sarah ta shiga gidan matsayin mata ba dadiro ba. Kuma kince mana dagaske fyad'e yayiwa Sarah ba kanta ta kai ba. Yanzu idan kika k'i amincewa, da zarar ta haihu karb'e y'ar ko d'an kawai za suyi, shikenan ku da k'ara ganinsu sai Allah. Amma idan auranta yayi, arziki har mu sai mun ture don Sarah ba marowaciya bace kowa ya sani. Maganar gaskiya idan ta fito a fad'eta ko yaya take." Shuru Lami tayi tana auna maganganun Na'ima. Aina'u kuwa wani dogon tsaki taja tare da fad'in, "Wallahi idan har tsautsayi yasa aka yi wannan auren, sai na zame wa Sarah bala'i daga ita har su dangin mijin nata." A zuciya tayi maganar. "Ke Na'ima, Saratu fa tana da mugun hali. Ina tsoron kar ta shiga gidan arziki ta manta cewar nice wacce tayi sanadiyar zuwanta duniya. Da ace zata iya shawo kanta kawai yayi ta d'ura mata ciki a waje yana kashe mata kud'i ni kuma ina kula da yaran ina kame y'an currencyn zai fi min. Amma zuwan gidan matsayin matarsa sai inga kamar akwai matsala. Don a irin kallon rainin da yaron yake min, sai inga kamar zai iya hana ni zuwa gidan ko kuma ita ya hana ta zuwa nan d'in. Kuma tsaf ubanku zai goya masa baya." Marfu'a tayi karaf tace, "Kuma wallahi Lami zai iya hakan. Don ko mu baki ga irin kallon da yake mana ba matsayin yayyin budurwarsa." Gyara zama Lami tayi tare da fad'in, "To ya kuke ganin za ayi kenan?" Karaf Aina'u tace, "Lami, zubar da cikin kawai za ayi!" Da sauri gaba d'aya suka kalleta tare da fad'in, "Baki da hankali ne Aina'u? Ai idan aka zubar da cikin kamar rabasu aka yi. Halan baki san abunda baban wansu yace ba ko?" Fad'in Hassana. Yamutsa fuska Aina'u tayi irin ban san komai d'in nan ba tare da fad'in, "Mai yace shi babban wan nasu?" "To cewa yayi idan har aka zubar da cikin to babu aure tsakaninsu." Fad'in Lami. Tsaki Aina'u tayi tare da fad'in, "To dama ba auren ake so a samu hanyar fasuwarsa ba?" "Ke dak'ik'iya ce wai? Idan har haka ta faru ai fita za suyi daga harkan mu gaba d'aya kuma su hana shi _Khalil_ d'in zuwa gidan nan. Kin ga kenan anyi two-zero babu ciki, babu auren." Murmushi Aina'u tayi tare da fad'in, "To ku saurare ni da kyau. Shin ke Lami baki lura da irin son da shi _Khalil_ d'in yake wa Sarah ba? Idan da ace ba sonta yake yi ba, babu abunda zai saka ya nemi gidansu har yazo ya samu mahaifinta suyi magana, kuma sannan ba zai tab'a d'auko iyayensa ya kawo su gidan nan ba. Sannan da baya sonta ba zai tab'a yarda shine uban cikin jikinta ba. Kar ki manta shi likitane. Da zai iya duk dabaru ya cire cikin ya kuma koreta. Idan ta nemi tona mata asiri yayi amfani da dukiyarsa ya kulle ba ita kad'ai ba har damu y'an uwanta ko kuma ya kai mu kotu yace zamu b'ata masa suna da sharri. Duk k'auna ce mai zafi ya kawo haka. Kuma wallahi kinji na rantse maki Lami, da ace _Khalil_ bai son Sarah, babu abunda zai kawo shi, shi da iyayensa gidan nan a yau. Kuma a gaban idanunsu ya dunga kwarara godiya bayan Baba da y'an uwansa sun amince ya auri Saratu." Hannu Marfu'a ta bata suka tada tare da fad'in, "Shegiya k'anwata! Ina maki kallon k'aramar yarinya ashe kwakwalwarki na ja. Na yarda da maganar Aina'u yasin Lami. Ko ya kuke gani y'an uwana?" Ta k'arisa maganar tana kallon su Nuratu. Na'ima tace, "Ni dai maganar zubar da cikin nan har yanzu bai gama kwanta min ba. Duk da kuwa zuciyata tana rawa akan wata rana Sarah zata iya juya mana baya sabida mijinta. Babu wata shawara ce sai wannan Lami?" "Gaskiya ni dai babu a waje na." Fuska kumbure Aina'u tace, "Shikenan Lami tunda ni kun d'auke k'aramar yarinya wacce shawararta bai da wani amfani. Idan komai ya kwab'e maku nan gaba, zaku tuna wannan ranar wallahi." Tana gama fad'in haka ta tashi ta fice tana mai dana sanin yin maganar zubar da cikin kasancewar basu amince da shawararta ba. Sarah zaune gaban Baba tana hawaye, "Saratu, ba zan tilasta maki ki auri _Ibrahim_ ba, sai dai a matsayina na mahaifinki, ina mai baki shawara da ki bawa zuciyarki hak'uri ki amince da wannan yaro don Shi kad'ai ne rufin asirinki. Na yaba da hankalisa da kuma karamci irin na iyayensa. Kuma ina da kyakkyawar zato akan zasu rik'e ki bisa amana tamkar y'ar cikinsu ba suruka ba." Jan majina Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ba kukan nake yi ba sabida ban son zab'in da kayi min, kukan farin ciki nake yi sabida zab'a min kai da Allah yayi matsayin mahaifi. Wallahi ko mahaukaci ka zab'a min matsayin mijin da zan zauna dashi, zan amshe shi hannu bibbiyu in kuma yi biyayya a gare shi. Nagode sosai Baba, Allah ya k'ara maka lafiya. Sannan nayi maka alk'awarin yiwa _Khalilullah_ biyayya har k'arshen numfashina idan har Allah ya rubuta ni matarsa ce. Bazan tab'a baka kunya ba Baba." Tausayi da k'aunar Sarah ya lullub'e Baba, "Allah ya maki albarka Saratu, Allah ya saka maki da alkhairi ya kuma zab'a maki abunda yafi zama alkhairi a rayuwarki ya shirya sauran y'an uwanki. Ubangiji ya jib'anci lamuranki. Je ki kwanta ki huta. Allah ya tashe mu lafiya." Da "Ameen" Sarah ta amsa bayan ta matso masa da duk wani abunda za zai buk'ata cikin dare sannan ta fice. Sai da tayi alwala a fanfo tukun ta nufi d'aki domin yin sallar shafa'i da wuturi. Tana shiga babu abunda idanunta suka fara gani sai wannan robar fanta mai sanyi da Aina'u ta ajiye sai naso yake yi. Hakanan Sarah taji bai wani burgeta ba. Sallaya ta shimfid'a tare da tada sallah. Tun bayan shigowarta d'akin Aina'u ta shigo ya kai sau biyar amma tana ganin robar fantar a inda ta ajiye. Ji take kamar ta shak'o wuyar Sarah da bacci ya kwashe bisa darduma ta d'ura mata wannan fantar. Da k'afa ta dunga shurin Sarah har sai da ta farka, "Ga Fanta nan mai sanyi idan zaki sha. Na sayo ne d'azu domin in sha, sai kuma ya fitar min a rai. Ki shanye ba sai kin biya. Tun d'azu dama ke na ajiyewa ganin duk gidan nan kece mai son Fanta." Bacci a idanun Sarah ta mik'e zaune tare da fad'in, "Bar mi shi a wajen. Sai zuwa anjima nasha yanzu cikina a cike nake jinsa." Ba tare da Aina'u tace komai ba ta fice haushi kamar ya kashe ta na rashin shan fantar da Sarah bata yi ba yanzu. Tana fita daga d'akin wayar Sarah ta soma ringing. Kai hannu Sarah tayi tare da d'auko wayar dake kan one sitter dake d'akin. Kallo d'aya yayiwa numbern ta gane _Khalil_ ne duk da kuwa bata yi saving number d'in ba sabida 3 d'in guda shidda da ya k'are da numbers d'in. Sai da ta turo baki sannan tayi picking tare da mik'ewa ta hau kan gadon sannan tace, "Assalamu alaikum!" Ajiyar zuciya _Khalil_ ya sauke tare da fad'in, "Amin wa'alaikissalam amaryata. Har kin fara bacci ne baki jira naji yanda kuke ba?" Bata ce masa komai ba sai ma mirginawa da tayi zuwa k'arshen gadon. "Baza kiyi magana ba?" Ya fad'i yana mai gyara kwanciyarsa. "To ni mai zan ce? Bacci fa nake ji sosai." Ta fad'i tana mai lumshe idanu." "To kiyi baccin ki mana. Na hana ki ne?" _Khalil_ ya fad'i yana murmushi. "To ta yaya zan yi bacci bayan ka hana ni? Ka kashe wayar to sai in kwanta." "Wato kin manta da deal d'in mu kenan ko?" Ya fad'i har da yiwa wayar hannunsa gwalo kamar tana ganinsa. Itama hararar wayar tayi tare da fad'in, "Tab! Ai yanzu babu wani zancen deal kuma." Waro idanu yayi tare da fad'in, "Inji wa ya fad'a maki haka? To ni dai har yanzu deal d'in mu na nan." Bata san lokacin da tace, "Duk da manya sun shigo cikin zancen?" Dariya ne ta kama shi, amma sai ya gimtse tare da fad'in, "Da kin haihu zan yi abunda nace maki zanyi. Zan karb'i baby na sai in fad'awa Baba na janye. Kin ga ai shikenan na zama mai cika alk'awari." Nan da nan Sarah taji bacccinta ya washe har da tashi daga kwance ta zauna tare da fad'in, "To ni ya zanyi da Baba kenan bayan nayi masa alk'awarin zan yi maka biyayya? Ni dai gaskiya a rushe....." Sai kuma tayi saurin yin shuru tana mai toshe bakinta da hannunta. Dariyar da yake ta rik'ewa ta kufce tare da fad'in, "Ashe dai ana son _Khalil_ d'in ake masa yanga." K'ok'arin yanke kiran take yi yayi saurin fad'in, "Kar ki fara ki yanke min waya tunda ba ke kika kira ba, ni na kira ki." "To wai ni kai aljani ne? Ta yaya kasan yanke wayar zanyi?" Sarah ta fad'i tana sauraran jin abunda zai ce. "Da motsin hannunki na gane. Kar kiji tsoro _Khalil_ d'inki ba aljani bane. Yanzu dai yaya kike?" "Lafiya." Ta bashi amsa kai tsaye. "Menene wani Lafiya! Sai kace yak'i. A haka ne zaki min biyayyar da kika ce kin yiwa Baba alk'awari." "Ni dai to ai babu abunda nayi maka. Tambayata kayi ni kuma na baka amsa." Ta fad'i tana mai lumshe idanu do hirar tana mata dad'i, hatta d'an bacci da take ji sai da ya gudu. "Hirar na maki dad'i ko?" "inji wa?" Sarah ta fad'i da sauri don mamaki _Khalil_ yake bata kamar wani aljani. Shi kuwa ya dai fad'a ne kawai don yaji mai zata ce. "Saurara in yi maki wata wak'a kiji." Yana fad'in haka ya soma fad'in, " _Ina kewaaa ina kewar masoyiya! Ina kewaaa ina kewar aminiyaa!! Abokiyar shawara, kece kin d'ara, kin sab In ba dake ba sai in hak'ura. Ki bani y'ar dama, a san dani nima, ki mini alfarma ki sanya ni a zuciya. Ki kau da y'an gulma, irinki ke nema, suna ta shan famaaa sun zaga ko ina. Mace ba ai ba kece, kuma kin san mun dace, a kanki na zauce! Magana d'aya ba shakka, hannu d'aya kan jinka, ta yaya zai d'auka, samunki baiwaa ce. Bakya fushi, ki murmushi, don sanki na shiga raina, ko babu ni in kin tunani wannan shine muradina. Nasan kina da buri kuma sannan kina da tsaarinki, da zaki sa cikin ranki, nine zan zama angonki. Farar tumfafiyata, daban cikin mata, a sonki nai rata a kanki na gane kaina. Kece nai wa alk'awari, mace d'aya kuma kin zarce d'ari, kin zam min bangon sukari, ko a ina kece. Sirrin ciki yazo fili, kin iya ado da d'an kwali, mai kyan ido da sa kwalli, an iya miki zanen lalli. Tun da na same ki na huta, saura sunka nazarta, bana iya kallon mata kiji kalmar dana furta. Akwai dad'i abunda kake so in ya soka, shi fatan da kakewa wasu sai ya bika. So sa'a ce, samun nasarace, ke sa ai daceee, ni kam na samu. So akwai tsada, sanyi sai randa, shanu ke hud'a furar mu nai damu. Nai nasara samunki, barni na zam jigonki, zan b'oye sirrinki ba ran da zan tona. kewa, keee, kewa! Ina kewaa, ina kewar masoyiyaaaaaa!_" Gaba d'aya ya gama kashe mata jiki da zazzak'ar muryansa, sai taji wak'ar ma a bakinsa yafi dad'i kamar shi ya rera ba auta wazirin ba. "Ka tab'a shiga studio ne?" Ta jefe shi da tambaya. "A kanki dai zan fara _mine_" "Kuma ka iya wak'ar sosai wallahi." Sosai yaji dad'in yabawa da tayi har sai da ya saki siririyar murmushi tare da fad'in, "Kullum zan rik'a rera maki wak'ok'i kala-kala a kunnanki idan kika dawo kusa dani. Kina so?" "Ni dai babu ruwa na Allah!" Dariya ta bashi kuma sai da ya daran kamun yace, "Da aka yi me?" "Ai dai babu kyau irin maganganu da kake yi" d'aga idanu sama yayi tare da fad'in, "Wanne kenan a ciki?" Ya fad'i yana k'umshe dariyarsa. "Oho!" Ta fad'i don ta gane so yake ta maimaita mai yace. "To yanzu dai abunda nake so dake, ki d'aura hannunki a kan cikinki kiyi addu'a sosai, sannan kiyi addu'ar bacci ki kwanta. Will call you in the morning kamun na tafi asibiti. Bye I love you." Yana gama fad'in haka ya katse kiran tare da rungume wayar yana jin kamar Sarah ya rungume ita da cikin dake jikinta. Allah ya d'aura masa k'aunar wannan ciki. B'angaren Sarah itama wani murmushi ta saki bayan ya katse wayar. Sai muryansa yake tayi mata echoing a cikin kanta lokacin da yake rera mata wak'ar kewa na auta waziri. Cike da farin ciki bacci mai dad'i ya kwashe ta bayan tayi addu'a kamar yanda ya umarceta. Aina'u kuwa ko da ta sake shigowa d'akin taga Sarah nata sharar bacci kuma bata sha fanta ba, sai taji kamar ta danna mata pillow ta mutu kowa ya huta. Fita tayi bata sake dawowa ba sabida yanda ta shak'a. Da asubahi Sarah ta tashi domin yin salla, babu kowa a d'akin don duka yayyin nata ba gida suka kwana ba. Tana jiyo kukan Fadwa daga d'akin Lami sabida ba'a yayeta ba haka Marfu'a take tsallaketa ta barta wajen Lami ta tafi gantalin da ta saba. Fitowa Sarah tayi ta kama ruwa sannan ta d'auro alwala. Sai da ta dubo Baba taga shima ya d'auro alwalar sannan ta koma d'aki dan yau bata yi gigin zuwa d'akin Lami domin tada su ba. Bayan ta idar da sallah, wani baccin ne ya kuma fizgarta. Kiran da _Khalil_ yayi mata ne ya farkar da ita. Amsa wayar tayi cike da muryan bacci tana fad'in, "Ina kwana, an tashi lafiya?" Daga can _Khalil_ yace, "Lafiya k'alau. Halan baki tashi ba?" Gyara kwanciyarta tayi tare da fad'in, "Kiran wayarka ne ta farkar dani." "I'm sorry ki koma baccinki. Amma kuwa ki sanar da Baba zuwa anjima wasu zasu kawo kaya. A fitar da duka abubuwa dake cikin dak'unan gidan please. D'akuna uku ne ko?" Da "Eh" Sarah ta amsa tana mamakin mai kuma za'a kuma kawo masu a gidan. "Yauwa to ki koma barcinki. In Sha Allah by 11:00am zasu zo." "Allah ya kawo su Lafiya." Sarah ta fad'a shi kuma ya yanke wayar tare da saka safa sannan ya saka takalmi dama kuma abunda ya rage ya saka kenan ya fito daga d'akinsa ya kulle ya nufi d'akin Hajiya. Sai da ya kwankwasa sannan ya turo ya shiga. A zaune a gefen gado ya samu hajiyar sai ninke kayan sawanta take yi. "Ina kwana hajiya?" Lafiya kawai tace masa tare da cigaba da abunda take yi don har yanzu haushinsa take ji. "Hajiya ina Laure da kike wannan aikin da kanki." "Tuni ta koma gidan ubanka da zama. Tashi ka fice ka bani waje. Sha-sha-sha kawai." Da sauri ya mik'e yana mai fad'in, "Allah ya huci zuciyarki Hajiya. Sai na dawo." Ko kallonsa bata kuma yi ba har ya fice sai a sannan ta d'ago ta watsawa bayansa harara. Bai had'u da kowa ba kasancewar ko k'arfe takwas na safe bai yi ba. Kai tsaye wajen motarsa ya nufa tare da shiga yayi reverse ya fice daga gidan zuwa asibiti. Sarah kuwa bata iya komawa bacci ba ta sauko daga kan gadon ta nufi d'akin Lami. Sai da tayi sallama sannan ta shiga, a zaune ta samu Aina'u tana shan tea da, bread da kwai. Gefe kuma Lami ne sai gyangyad'i take yi don bata samu bacci ba jiya sabida damunta da kuka da Fadwa tayi tayi jiyan. "Ina kwana Lami." Lami bata amsa ba sabida wani gyangyad'i mai dad'i da ya kwashe ta. "Lami." Karo na biyu Sarah ta kuma kiran sunanta, firgigit ta farka har miyau na zubo mata daga baki. "Wannan wani irin iskanci ne haka Saratu? Ya zaki tashe ni kuma na san kin san ban samu ishashshen bacci ba jiya." "Kiyi hak'uri, dama _Khalil_ ne yace in fad'a maku a fitar da duka kayan d'akunan gidan b'aki za suzo anjima." Tuni Lami ta watstsake tare da fad'in, "Da gaske kike yi Sarah. Wayyo Allah arziki yazo mana har cikin gidan mu. Maza tashi Aina'u a fara aiki tun yanzu kamun sauran y'an uwanki su dawo." Tsabar bak'in ciki Aina'u ko magana bata yi ba sai ma mik'ewa tayi ta bar d'akin don ji tayi bread d'in da ta saka a baki d'aci yayi mata kamar tana taunar magani. Lami kuwa tashi tayi ta soma fitar da wasu kayan. Ganin Aina'u ba taya ta za tayi ba, sai ta fita ta kira almajirai suka shiga fitar da kaya. Sai da suka fitar da kayan d'akinta kaf sannan suka soma fitar da na Baba kasancewar Sarah taje tayi masa bayani. Zuwa k'arfe goma sun gaba fitar da duka kayan gidan har da nasu d'akin Sarah. Lami tsabar zari har ta kira dillaliya ta saye gado da katifar d'akinta da na Sarah. Taso had'awa har da katifar Baba amma ya hanata. Sai da hakan ya kai su ga rigima har Lami na zaginsa tana kiransa matsiyaci. Lokacin da sauran y'ay'an nata suka dawo suka ga gaba d'aya babu komai a d'akunan gidan suka shiga tambayar ba'asi. Nan Lami ta shiga fad'a masu cewar ai _Khalil_ ne zai kawo masu sabbin kayan d'aki yau shiyasa aka fitar da komai ta sayar. Sarah kuwa mamaki ne ya cika ta ko yaushe suka yi hakan da Lami d'in. Ita dai ta san _Khalil_ ce mata kawai yayi a fitar da kayan d'akunan gidan. Gaba d'aya su Na'ima suka hau murna banda Aina'u da ta bar gidan sabida mugun hali. K'arfe sha d'aya dai-dai kamar yanda _Khalil_ ya fada sai ga tsayuwar motar company a k'ofar gidansu Sarah. Kwalaye suka dunga shigowa dasu suna ajiyewa a tsakar gidan. Sai da suka gama kwaso kayan tsaf sannan suka tambaya inane d'akin Baba. Da hannu Sarah dake tsakar gidan ta nuna masu, caraf Lami tace, "Wallahi tallahi babu uban da ya isa, da d'aki na za'a fara. Ai ni ce na sha wuyar mak'uda ba shi ba." Ma'aikatan ba tare da musu ba suka d'auki kwalayen tare da shiga d'akin Lamin da aka share tsaf aka goge, don ita d'akinta akwai tiles. Cikin mintuna talatin saboda kwarewarsu har sun kammala had'a gado da komai. D'akin ba k'aramin kyau yayi ba. Gadon kalar b'aki da purple. Wardrobe d'in kuma irin mai cin bangon nan ne mai k'ofa shidda. Hatta labule sabo suka saka mata sannan suka mak'ala mata TVplasma sannan suka fita suka koma d'akin Baba. Shima haka suka jera masa nasa kayan irin na Lami sak sai dai akwai bambamcin launi. Shi nayi farare ne k'al. Kuma kamun su saka sai da suka shimfid'a masa lallausar carpet da ya mamaye d'akin mai tsada kalar blue-black. Sannan suka saka masa TVplasma irin flatscreen d'in nan wanda kud'insa zai kai 250k zuwa 300k, dama kuwa akwai masu had'a dish a waje kuma har sun kammala, sai kawai suka shigo suka yi settings kasancewar ko wani d'aki yana da decoder d'insa. D'akin Baba har da tvstand mai kyau. D'akin su Sarah suma ab had'a masu nasu furniture d'in wanda ga kasance white and baby pink. Kuma gadonsu six by seven ne yayin da su d'akin Baba ya kasance six by six. Gaba d'aya gidan sai ya koma kamar gidan amare. Komai sabo. Don har da dank'areran deepfreeze da kuma fridge _Khalil_ ya siya masu. Wajejen k'arfe biyu suka kammala komai suka wuce. Lami kuwa sai uban gud'a take yi. Lokacin da ta shiga d'akin Baba domin taga irin nasa gyaran, sai bak'in ciki ga rufe ta ta shiga surfa bala'i mai yasa ita ma ba'a saka mata Tvstand stand ba. Baba kasancewar baya son tashin hankali yace ta d'auka ta kai d'akinta. Babu kunya kuwa ta kama ita da Nuratu suka mayar d'akin nata. Aina'u kuwa ba ita ta dawo gidan ba, sai bayan magriba. Tana sauka daga napep ta taras da zambad'ed'iyar motar _Khalil_. Wani mugun tsaki ta saki tare da isa k'ofar gidan ta tura ta shiga kuma a dai-dai lokacin ta hangi bayan _Khalil_ d'in zai shiga d'akin Baba. Tsayawa tayi tana k'arewa d'akunan kallo ganin ko Wanne da sabbin labulaye. Dai-dai nan Sarah ta fito daga bayi hannunta rik'e da buta, tazo dai-dai inda Aina'u take, sai ta saka mata k'afa tayi wani irin mugun fad'uwa, ji kake tim. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sarah ta fad'i da k'arfi tana mai kai hannu k'asan mararta. Aina'u kuwa sai tayi saurin sunkuyawa tana fad'in, "Sannu Sarah, garin yaya kika fad'i haka." Gaba d'aya gidan suka fito, _Khalil_ ya riga kowa fitowa da gudu jin muryan Sarah tana salati. Ita kuwa Sarah sai cewa take "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, cikina, wayyo Allah cikina." Rintse idanu _Khalil_ yayi da k'arfi ganin zini na gangarowa daga k'afafunta............... *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* *_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 15* _Jinjina a gare ku my fans, kuna nishad'antar dani musamman y'an K'ANWAR MATATA comments section, irin su my besty (Queen Zarah), Rahamanatou, Oum Muslim, Mrs dimples, Halimatouu, Maman auwal k'awata, Jik'amshi collection, Mrs Z A musawa, Hadiza Mbello, Tatiesha Rufa'i, My Rabi'a, Yayata maman Islam, Babyshamas, da abokiyar fad'ata Ummu Muhammad da sauran da basu ji sunasu ba duka. Ina maku sonso. Allah ya bar k'auna mutanan Lami da Aina'u😜_ Ba tare da jin wani kunya ba _Khalil_ ya ciccib'i Sarah yayi waje da ita Lami biye dashi ita da Nuratu da Na'ima. Aina'u kuwa wani irin murmushi jin dad'in hak'arta ta cimma ruwa duk da bata tab'a kawo cewar abunda ya faru da Sarah zai iya faruwa da ita ba sanadiyar fad'uwar da tayi. Ita tayi ne kawai sabida mugunta. A baya ya shimfid'ar da ita, da sauri Lami da su Na'ima suka shiga cikin motar, _Khalil_ kuma ya zagaya ya shiga mazaunin gaba tare da tada motar ya bar unguwar da gudu ganin ba k'aramin jini ke zuba daga jikin Sarah ba. Baba kuwa kamar ya fashe da kuka, gashi babu k'afar bin bayansu. Sai dai abunda yayi matuk'ar bashi mamaki ganin Aina'u tana bin jinin Sarah da ya zuba a k'asa tana wani dariyar k'ata. Kwata-kwata bata lura da Baba dake bakin k'ofa yana kallonta ba. "Aina'u kar dai kece sanadiyar abunda ya samu y'ar uwarki yanzu?" Da sauri ta kalli inda baban yake a tsaye tare da fad'in, "Da aka yi yaya kenan Baba? Shikenan babu damar nayi dariya. To ni dariyata wani abu take nufi can daban." Juyawa Baba yayi tare da komawa d'akinsa don ya dad'e da sanin Aina'u ba k'aramar muguwar yarinya za ayi ba. Sai tace Lami bata yi komai ba a duniya. Amma abunda har yanzu ke bawa Baba mamaki shine, don me za tayi hakan? "Ya ubangijin sammai da k'assai, ga Baiwar ka nan ka jib'anci lamuranta. Allah ka bata lafiya." A bayyane yayi maganar yana mai d'aga hannu sama. A can asibiti kuwa, gudun laifi, tun kafun ya k'arisa ya fiddo baya tare da danna kiran number Hajiya domin shaida mata abunda ke faruwa. Don babu abunda gabansa ke yi sai fad'uwa ganin jiya-jiya suka gama kankara masa warning akan kar ya kuskura yace zai cire cikin dake jikin Saran. Ringing uku Hajiya ta d'aga tare da fad'in, "Assalamu alaikum." "Amin wa'alaikissalam, Hajiya dan Allah ki saka driver ya kawo ki asibitina yanzu. Saratu ce ba lafiya gamu tare da y'an uwanta zuwa asibiti. Fad'uwa tayi kuma jini ya b'alle mata." Da sauri Hajiya ta soma fad'in, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Ai babu wani driver da zai kawo ni, tunda ga Muhammad Kabir a gida, bari na kira na fad'a masa abunda ke faruwa sai ya kawo ni." "To Hajiya nagode." Yana fad'in haka ya katse wayar tare da cigaba da driving da gudu yana yi yana juyowa yana kallon Sarah da ta jima da fita cikin hayyacinta sabida irin jinin da take zubarwa. Suna isa asibitin ya fito da sauri tare da bud'e gidan ya kuma ciccib'ota gaba d'aya jinin jikinta ya gama b'ata jikinsa amma ko a jikinsa. Cikin asibitin ya nufa da ita don ko tsayawa nurses su gunguro gadon marasa lafiya bai yi ba. Doctor Hayat, Doctor Nurain da doctor Kamal sune suka amshi Sarah tare da shiga da ita emergency kuma suka hana _Khalil_ shiga sabida ganin yanda ya rud'e, koma ya shigan ba wani abu zai iya yi ba. Mintuna goma tsakani sai ga Hajiya ita da aunty Maryam, aunty Khairat matar ya Barrister da shi kansa Barrister d'in. "Ina uwata take?" Fad'in Hajiya lokacin da ta k'ariso. Waro idanu tayi ganin gaba d'aya jikin _Khalilullah_ ya b'aci da jini. "Subhanallah!" Hajiya suka fad'i a tare ita da au aunty Maryam. Yaya Barrister kuwa cewa yayi, "Garin yaya haka ta faru?" _Khalil_ kuwa sai danne hawayen dake taho masa yake yi tare da fad'in, "Baban ne yace tayo masa kira na yana son magana dani, to naje ko zama ban kai ga yi ba, sai kawai jin talatin ta muka yi. Gaba d'aya muka fito muka taras da ita kwance a k'asa jini na zubar mata." Fuska cike da damuwa hajiya tace, "Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Fad'uwa tayi kenan? Allah ya bata lafiya alfarmar ubangiji. Kai jama'a ni Mai gado!" Fad'in Hajiya tana da zabga tagumi. Can kuma ta kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Ka d'auke kaje gida ka canzo kaya sai ka dawo. Gaba d'aya jikinka ya b'aci da jini." " _Hajiya_ dan Allah kiyi hak'uri wallahi bazan iya yin ko taku d'aya ba har sai naga halin da baiwar Allah nan take ciki." Kallon Hajiya Barrister yayi tare da fad'in, "No, Hajiya kyale shi bari naje gidan na d'auko masa wasu kayan sai ya canza a cikin office d'insa." "Yauwa Allah yayi maka albarka. Maza je ka d'auko masa." Fad'in Hajiya. Aunty Maryam da aunty Khairat so suke su tambayi wacece babu lafiya, amma babu fuska wajen kowa don kowa cike yake da tashin hankali kar ma ace _Khalil_. Har yaya Barrister ya dawo daga gida ya kawo wa _Khalil_ kaya babu labarin Sarah. Sai da Hajiya tayi jan idanu sannan ya karb'i kayan ya nufi office domin canzawa. Sauri-sauri ya wanke jikinsa sannan ya saka kaya tare da fitowa. Duk k'aunarsa da turare yau ya manta anan saka wani abu wai shi turare a jiki. Nufa k'ofar emergency d'in _Khalil_ yayi gadan-gadan don ya gaji da tsayuwar gawon shanu. "kai! Maza dawo nan ka barsu suyi aikinsu. Idan ma ka shiga, mai za kayi." Fad'in Hajiya. Dawowa _Khalil_ yayi dai-dai lokacin da doctor Kamal shi da doctor Hayat. Da sauri ya nufeso tare da fad'in, "Ina Matata? How is she?" Da mamaki gaba d'aya suke kallonsa sabida Kalmar wife da ya kira don sun san bai da wata mata. Amma sai suka shanye mamakin. Doctor Kamal bai yi magana ba, doctor Hayat ne yace, "She's conscious now, amma tana buk'atar jini sabida ta zubar da jini da yawa. Sannan kuma I'm sorry to say, "She loose the baby. Babu cikin!" Zamewa _Khalil_ yayi ya duk'a a wajen tare da rik'e kansa yana nanata Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! "Kai, dakta mai ke faruwa?" Fad'in Hajiya ganin yanda _Khalil_ ya duk'e tare da kama kai yana salati. Barrister ya soma yi mata bayani don yaji komai, "Hajiya ita uwar ta farfad'o, sai dai tana buk'atar jini sabida ta zubar da jini da yawa, sannan kuma an rasa cikin jikinta." "La haula wala quwata illah billahi. To Allah yasa hakan shine alkhairi. Sai ayi gaggawa bata jinin ko. Amma kai dakta, ka tabbatar ba wani abu tasha ba cikin ya zube?" Fad'in hajiya tana kallon doctor Hayat. Girgiza kai doctor yayi tare da fad'in, "Gaskiya Hajiya babu wani abun da tasha wanda yayi sanadin fitar ciki. Mahaifar dama bata yi wani kwari ba. So sanadin mummunar fad'uwar da tayi ne ya jawo hakan." Dogon ajiye zuciya Hajiya ta sauke, don ta riga ta raya a zuciyarta in dai har zubar da cikin nan aka yi, to fa har abada d'anta ba zai auri Sarah ba ko da kuwa _Khalil_ d'in ne ya zubar da cikin. Mik'ewa _Khalil_ yayi tare da shiga cikin emergency d'in don har a lokacin ba'a fitar da ita zuwa ward ba. Kallonta ya dunga yi ganin lokaci k'ank'ani har tayi wani irin mugun rama tayi haske. Da sauri ya juya ya fita tare da nufa lab domin a d'ibi jininsa don jininsa irin wanda zai iya bawa kowa ne idan aka cire O-negetive. Leda biyu aka d'iba a jikinsa. Tuni har an maida Sarah d'akin hutu an kuma d'aura mata jinin _Khalil_. Lami kuwa da y'ay'anta sai tararrabi akan hukunci da za su yanke ganin cikin jikin Sarah ya zube. Lami kwata-kwata damuwarta ba rashin lafiyar Sarah bane. Damuwarta d'aya kada jin dad'in nan da suka soma samu a jikin _Khalil_ ya yanke sakamakon zubewar cikin jikin Sarah d'in. Sam basu gane yanayin Hajiyar ba, don fuskanta babu yabo kuma babu fallasa. Hajiya bata bar asibitin nan ba, sai da Sarah ta farfad'o sosai har tana ina gane kowa da kowa lokacin har anyi sallar magriba. Amma su Aunty Maryam tuni ya Barrister ya maida su gida sabida girkin da za'a kawo nan asibitin. Ya Abdul-Hakeem ne ya kawo abincin a cikin manya-manyan kula masu matuk'ar tsada sannan ya d'auki Hajiya ya mayar da ta gida. _Khalil_ kuwa sallar magriba ce ta fitar dashi, don tun tuni yana gefen Sarah tana yin motsi yake soma tambayarta ko wani wajen nayi mata ciwo. Sarah kuwa tun da ta samu labarin cikin dake jikinta ya zube, wani irin numfashin rahama da natsuwa ta sauke tana mai godewa ubangiji don ita kad'ai ta san halin da take ciki. Sam bata son shiga cikin sahun y'an uwanta na ajiye d'a ko y'ar shege. "Allah na gode maka da ka cire cikin ta hanyar mafi sauk'i. Allah na gode maka." Duk a cikin zuciya tayi maganar. Baba kuwa na can hankalinsa a tashe jin babu wani feedback game da Sarah. Sai da yayi kamar zai yiwa Aina'u kuka sannan ta kira masa Lami kasancewar shi bai da waya. Shi d'in ma sai da ya bata dubu d'aya sannan ta kira. Bayan sun gama waya da Lami ta fad'a masa halin da ake ciki, sai ya mik'awa Aina'u wayar dake tsaye tana jin matsanaicin farin ciki jin ciki ya zube. "Shegiya! Ai nayi wa kaina alk'awarin sai na raba ki da _Ibrahim_. Wallahi ba zan bari ki shiga gidan na ba. Mayya kawai!" Tana gama fad'in haka ta juya ta fice daga d'akin tare da komawa nasu d'akin ta kwanta a kan gado tare da jawo ledar tsire mai kulin da ta siya ta hau jefawa a baki tana tauna tana lumshe idanu. A can asibiti kuwa, wajajen k'arfe tara da rabi, bayan su Lami sun gana hani'an da abincin da Hajiya ta saka su aunty Maryam suka yi, sai _Khalil_ yace masu ya kamata su tashi ya kai su gida, don mutum d'aya aka amince ya kwana da majinyaci. "Lami tunda ga yara a gida, ku tafi kawai ke da Nuratu, ni zan kwana anan da ita." Lami ji tayi kamar ta shak'o Na'ima, amma jin abunda _Khalil_ yace sai tayi shuru. "Eh hakane. Mama ke ki koma gida, ita sai ta kwana da itan. Idan yaso gobe sai ku dawo da safe. Dare nayi. Muje na sauke ku a gida." Fita Lami tayi ba tare da ta k'ara cewa komai ba. Don gani take kamar wani abun dad'in Na'ima zata ci idan ta tafi. Ko kuma _Khalil_ d'in yayi mata wani kyauta. Har gida ya sauke su tare da shiga wajen Baba ya kwantar masa da hankali tare da shaida masa in Sha Allah nan da wasu y'an kwanaki Sarah zata warware. Hajiya tana isa gida ta d'aga waya ta kiran number d'in ya Abdullah. Kamar kullum ya yanke kiran tare da kiranta. "Assalamu alaikum, marmari sai kaji abunda ya faru ko?" Fad'in Hajiya. "Wa'alaikissalam, Muhammad Kabir ya kira ni ya fad'a min komai, amma Hajiya an tabbatar da a asibitin ba wani abu tasha ba? Don jiya kamun na bar Kaduna sai da na wakilta wad'anda zasu min bincike yarinyar. Kuma binciken ya iske ni tun a jiyan. Hajiya maganar dai babu dad'in ji, don sai da nayi dana sanin amincewa da wannan maganar auren. Don fisabilillahi gaba gidan tun daga kan uwarsu babu tarbiya. Dama-dama ita yarinyar ma, an samu mutane hud'u zuwa biyar da suka yabi halinta." Shuru hajiya tayi tana sauraran ya Abdullah kamun tace, "To marmari ya za muyi, _Khali_ dai ya riga ya jawo mana magana. Tunda har yaji ya gani, kuma ita yarinyar ta samu shaida ko yaya ne, hakanan za muyi hak'uri ayi auren kawai don nan gaba bamu san wani irin magana zai je ya d'auko mana ba. Kuma maganar ciki, dagaske b'ari tayi amma ba ta hanyar shan magani ba. Allah ne ya kawo hakan ta sanadin fad'uwa da tayi." Ajiyar zuciya ya Abdullah yayi tare da fad'in, "To shikenan Hajiya. Tun da har hakan ya kasance, ba sai an d'au wani dogon lokaci ba, da zarar Yarinyar taji sauk'i, zan zo Kaduna sai muyi magana dasu uncle Ridwan sai aje a kai kud'in auren." "Kaga inda matsalar take kenan. Allah yasa dai kar su tada k'ananun maganganu dai!" Fad'in Hajiya, "Ki kwantar da hankalinki, in Sha Allah baza a samu matsala ba." "To Allah yasa!" Fad'in Hajiya. A can asibiti kuwa, sai da gaba d'aya nurses suka fahimci Sarah budurwar _Khalil_ ce sabida yanda yake nan-nan da ita. Kwanan Sarah uku a asibiti, amma ko sau d'aya Aina'u bata tab'a zuwa dubata ba. A asibitin nan kuwa, wani irin soyayya ce da shak'uwa mai zafi ta shiga tsakanin Sarah da _Khalil_ ta yanda har idan bata ganshi ba, ta dunga kallo agogo tana kuma duban hanya. Da taji motsin bud'e k'ofa take saurin kai idanunta wajen. Satinta biyu aka sallameta, baza ka tab'a cewa daga ciwo ta tashi ba sabida wani irin haske da kyau har da d'an k'iba da ta k'ara. Cike da murya da farin ciki ta isa d'akin Baba tana mai jin kewarsa. Abunda ya bata mamaki ganin Baba a tsaye babu sandar da yake dogarawa. Da mamaki take kallon Baba har da zagaya shi. Dariya yayi tare da fad'in, "Bar mamaki Sarah, mahaifinkin ne dai a tsaye gabanki. Kin ga ikon ubangiji ko? Allah dai ya yiwa _Ibrahim_ albarka domin shi ya zo ya d'auke ni ya kai nj asibitinsa na k'ashi aka duba k'afata. Kuma har gida kullum ake zuwa ana min gashi. Kuma Alhamdulillah k'afar ta soma warkewa don yanzu haka zan iya zagaye tsakar gidan nan babu sanda." Da matsanaicin farin ciki Sarah ta soma fad'in, "Alhamdulillah! Alhamdulillah!!, Allah mun gode maka. Baba Ashe zaka samu lafiya? Kai Alhamdulillah." Baba yace, "Ki godewa ubangiji sannan ki godewa _Ibrahim_ Saratu. Domin sanadinsa ne kika ganni a haka yau a gabanki. Saratu don girman Allah, kiyiwa yaron nan biyayya, babu abunda za kiyi ki b'ata min rai Sarah kamar ki k'i yin zaman lafiya dashi. Hakan zai b'ata min rai kuma zan rik'e ki a zuciya domin yaron nan ya gama yi mana dukkan alkhairi shi da iyayensa." Sarah wani irin matsanaicin soyayyar _Khalil_ ne taji yana hud'a ko wani sak'o da lungu na zuciyarta. D'ukawa tayi tare da fad'in, "Baba nayi maka wannan alk'awarin na zama da _Khalil_ da zuciya d'aya, kuma ko da sab'ani ya shiga tsakanin mu wata rana, ba zan tab'a juya masa baya ba. Kuma ba zan tab'a rabuwa dashi ba har sai idan shine ga gaji da zama dani." "Allah yayi maki albarka Saratu. Allah yasa auren da za kuyi mutuwa ce zata raba shi." Sai da Sarah ta saka gyale ta rufe fuskanta sannan tace, "Ameen" tare da mik'ewa ta fita daga d'akin ta koma nasu d'akinsu ta d'auko wannan turaren da _Khalil_ ya bata tare da fesawa sosai sannan ta canza hijjab ta saka wani don a waje suka bar _Khalil_ d'in. Sarah tayi alk'awarin yau zata bayyanawa _Khalil_ baki da baki cewar tana sonsa. A tsaye a k'ofar gidan ta same sa yayi folding hannunsa yana kallon k'ofar gidan. Tana fitowa ya saki ajiyar zuciya tare da fad'in, "Har na k'agu ki fito." Murmushi tayi tare da fad'in, "To ba yanzu muka rabu ba." "To ba kece kika ce kar na wuce na jira ki ba. Na k'agu inji mai zaki fad'a min." Murmushi ta k'ara yi karo na biyu tare da fad'in, "Wai sanyi kake ji?" Harararta yayi tare da fad'in, "K'arshen sanyi, a Atlanta nake." Dariya ta saki wanda ya k'ara bayyanar da bayyannar kyawunta, gaba d'aya kumatunta sai da suka lob'a. "Ban da Allahn musuru, amma ina ji a jikina da d'a ko y'ata ya fito duniya, da dake zai yi kama sak. Ke kyakkwa ce." Rufe fuska tayi da hijjab d'inta tare da fad'in, "Har na kai ka kyau? Kai fa kama kake min da wannan matashin kudancin indian _Ram Charan_" waro idanu _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Haba dai! Ke kuma kin san dawa kike kama, _Aishwarya Rai_, wallahi kin ma fita kyau." Rufe baki Sarah tayi tare da fad'in, "Kar ka yarda Na'ima taji, don ita ce aka cewa suna kama da Aishwarya." "Wa, to ai kin fita kyau wallahi." Dariya tayi tare da fad'in, "Beauty is in the eyes of the beholder." "Eh d'in naji, ko ma dai menene, ke d'in kyakkyawa ce kuma ta musamman. Wani albishir za'a fad'a min ne aka hana ni tafiya gida." Sai da Sarah tayi farr da idanu sannan tace, "Abunda kake muradin ji kullum daga baki na kuma fuska da fuska." Gyara tsayuwa yayi tare da fiddo wayarshi ya danna recording ba tare da ta san me yayi ba. "Gwara in gyara tsayuwa da kyau kar inzo in fad'i in suma don dad'i." Dariya tayi tare da fad'in, "Ba zan bari ka kai k'asa ba zan taro ka. Idan har ina waje, baza ka tab'a fad'uwa ba in Sha Allah!" Da mamaki yake kallonta don bai tab'a tsammani zata iya magana haka ba. "Yanzu kina da k'arfi taro ni?" Ya tambaya yana mata gwalo. "Ba da k'arfin cin tuwo zan rik'o ka ba, zuciyata ce zata rik'o ka. Ka manta kai da kanka ka fad'a an halicceni ne domin kai, kuma kai ma an halicceka ne domin ni? To ai zuciyoyinsu a had'e suke kuma tare suke bugawa kuma gangan jikinmu a tare suke sarrafuwa, sabida haka d'aya ba zai tab'a barin d'aya ya fad'i ba. Ka saka hakan a ranka." Mutuwar tsaye _Khalil_ yayi yana jin maganganunta na shiga ko wani sak'o da lungu na jikinsa har sai da tsikar jikinsa ya tashi. Wani irin kallon k'auna ya dunga binta dashi kamar zai had'iyeta. "Ina sonka _Khalilullah_, Ina k'aunarka har cikin zuciyata." Dum yaji wani abu kamar guduma ya bugi dodon kunnensa, wani irin shauk'i na mamaye ilahirin jikinsa. Ji yake dama yana da dama da jawota zai yi jikinsa ya rungume sosai. Aina'u dake lab'e jikin k'ofa tana sauraransu, don tun lokacin da Sarah ta fita ta biyota a baya. Wasu irin ruwan hawaye ne ke gudu a fuskanta. Ji take kamar ta koma cikin gida da gudu ta d'auko kaifaffiyar wuk'a ta soki zuciyar Sarah dashi ta tafi ta bar duniyar. "Sarah, nagode ba wannan alfarma da kika min na sanya ni cikin zuciyarki da kuma bani damar kasancewa dake har mutuwa. Ina so ki sani, zan killaceki a nan, (yayi nuni da zuciyarsa), ba zan tab'a bari kiyi hawayen bak'in ciki ba, idan har za kiyi hawaye, to na farin cikine, nayi maki wannan alk'awarin. Zamu dunk'ule mu zama d'aya Sarah. Zan tarairayeki ta yanda ko bugun zuciya mai k'arfi bazan bari kiyi ba. Zan kula dake fiye da yanda ake ririta kwai. Zan mayar dake sarauniya, sannan in kasance bawanki. Sarah baki ba zai iya musulta yanda zanji dake ba. Allah ya nuna min ranar da zan mallakeki matsayin mata. Wannan ranar kawai nake jira. Zan gwada maki practically abunda ake nufi da k'auna. In Sha ni da ke, _couples for eternity_ ne. Rayuwar aurena dake, babu condition Sarah, unconditional love nake maki Sarah. Ko da zaki zama mara k'afa da hannu, soyayyarki baza ta tab'a canzawa ba a gare ni. Allah yayi mana jagora." Hawayen farin ciki kawai Sarah take yi, bata tab'a tunani ko cikin mafarki akwai wanda zai iya fad'a mata wad'annan kalaman ba. Ashe dai ita ma za tayi farin ciki a rayuwa. "Wallahi idan har ina da rai, ni Aina'u ba zan tab'a bari alk'awarin daka d'auka ya zama cikakke ba, ba zan tab'a bari kuyi farin ciki ba nayi maku wannan alk'awarin." Aina'u ta fad'i cikin zuciya tare da saurin barin wajen tana kuka don kalaman da _Khalil_ ke fad'awa Sarah ba k'aramin k'ona zuciyarta yake yi ba. Sarah da _Khalil_ kuwa basu san da ita ba, sai cigaba da kwararo kalaman love wa junansu suke yi har kusan goma na dare sannan suka yi sallama kamar kar su rabu. Bayan da ta dawo d'aki kuma, _Khalil_ na isa gida suka dasa soyayyar ta waya. Bayan sati biyu da sallamo Sarah, Ya Abdullah ya diro Kaduna, ko sauka gidan Hajiya bai yi ba, kai tsaye ya tafi family house d'in mahaifinsu domin ganawa dasu Uncles d'in nasa akan batun auren _Khalil_ d'in kuma dama tuni sun d'an fara maganar a waya. Kasancewar suna d'an shakkarsa, basu wani tattada jijiyoyin wuya ba, sun tsayar da magana akan zuwa gobe sai suje can gidansu iyayen Sarah a tsayar da magana. Bayan Ya Abdullah ya dawo gidan Hajiya, sai ya sanar mata yanda suka yi da Uncles d'in nasa. Sosai Hajiya taji dad'i jin babu wani tashin hankali da aka yi, duk da ta san dama basu cika yin haukar da suka saba yi ba a gaban Abdullah sabida suna shakkarsa. _Khalil_ kuwa da ya samu labari, sai da ya shiga d'aki ga kulle k'ofa sa hau tik'ar rawa kamun nan ya kira Sarah ya shaida mata abunda ake ciki. Itama dad'i ne ya kasheta. Bayan sun gama wayar ta fita tayi alwala ta dawo d'aki tayi raka'a biyu ta dunga rok'on Allah akan Allah yasa ayi wannan auren kada shima ya rushe kamar na baya. Don sosai ta saka _Khalil_ a cikin ranta. Bayan magriba _Khalil_ yazo har gida ya fad'awa Baba in Sha Allah gobe iyayensa zasu zo domin neman auren Sarah. Baba ya shaida masa babu komai sai sun zo. Bayan fitar _Khalil_ sai da Baba yayi hawaye tuno y'an uwansa na _Wamba_ don da yana tare dasu, da su zasu karb'i wannan aure. Haka nan ya aiki Sarah ta kira masa abokansa guda uku wanda suka had'a Sana'a tun suna matasa. Da sukan zo gidan su dubasa, amma ganin irin tijara da zagi da Lami take masu, sai suka d'auke k'afarsu a gidan, sai dai idan suka had'u da Sarah sai su aiketa da gaisuwa, idan kuma suna da d'an wani abu, sai su bata ta kai masa. Har gidan suka zo, da suka ji dalilin kiran kuwa, ba k'aramin farin ciki suka ji ba, kuma suka tabbatar masa da goben in Sha Allah dasu za ayi komai. Washa gari misalin bayan la'asar, sai ga jiniyar motocin sojoji, su kawu suna cikin nasu motar, shi kuma ya Abdullah yana cikin nashi a tsakiyar convoy, sai kuma wata sabuwar mota dal da wani soldier ke driving. A k'ofar gidan suka yi parking. Soldier ya bud'ewa ya Abdullah mota tare da sara masa ya k'ame. Bai fito ba, nuni kawai yayi masu da wata mota. Cikin k'ank'anin lokaci sojoji suka kwashe gaba d'aya abunda ke cikin motar suka yi ciki da su. Buhunhunan shinkafa kamar za'a bud'e shago, manya-manyan galolin manja da mangyad'a, huhunan goro, katon-katon na sweet da chewing gum, wani k'atoton centre carpet wanda kud'insa ya kai 500k, sai wasu had'ad'd'un takalma k'afa ashirin da wani k'atoton akwati wanda babu komai a cikinsa sai lesses da atamfofi masu tsadar gaske da kuma Key d'in mota. Gaba d'aya uban kayan, kayan saka ranar auren Sarah da _Khalil_ ne. Har dasu gas da manya-manyan stainless steel irinsu bokiti da. Irin dai al'adar da ake yi. Ga manya-manyan juices na kwali da na goro har da ruwan gora kala-kala. Lami kuwa mad'aukakin mamaki ne ya kamata don bata san da zuwansu ba. Baba bai fad'a mata ba, haka ita ma Sarah bata ce komai ba. Sai da aka gama shigar da kayan tsaf sannan ya Abdullah ya ziro k'afarsa ya fito dai-dai lokacin da su uncle suma suka fito. Abokan Baba su suka yi masu jagora har cikin d'akin Baba, sosai ya Abdullah yaji dad'in ganin gyaran da _Khalil_ d'in yayi wa baban da kuma ganin ya soma samun sauk'i. Bayan gaishe-gaishe sai suka fara magana akan abunda ya kawo su. "Aure dai bama so a saka ki da tsayi. Idan ma baku shirya ba, mu ashirye muke don bama buk'atar komai naku." Fad'in uncle Ridwan. Sam maganar bata yiwa ya Abdullah dad'i ba. Kuma sai da hakan ya nuna a fuskansa. A natse ya Abdullah ya soma magana, "Baba, uncle yana nufin idan babu takura, muna so kar bikin ya wuce sati biyu. Kar ka takura kanka, Saratu kawai muke buk'ata a gidanmu, amma idan kana ganin kana da naka uzurin, za muyi na'am da duk lokacin da ka saka." "Kaji d'an iskan yaron nan yana k'ask'antar damu a gaban wannan wulak'antaccen fak'irin mutumin. Shi har ya isa yana talaka ya ja da maganar mu" fad'in Uncle Ameeru amma cikin zuciya. Ba Baba bane yayi magama, abokinsa Baba Isma'ila ne yace, "A'a babu komai. Lokacin da kuka saka d'in ma yayi. Allah ya sa hakan shi yafi alkhairi." Cike da girmamawa ya Abdullah yace, "To mun gode Allah ya saka da alkhairi. Ga wannan makullin motar, Hajiya ce ta bada kyauta a bawa mai sunan mahaifiyarta Sarah, kaya kuma gasu nan duk Hajiya ce ta lissafa mana muka sayo, tace na al'ada ne da ake yi idan za'a saka rana. Ga kuma sadaki nan." Ya fad'i hakan yana mai mik'a bunch d'in dubu-dubu guda biyar, jimilla ya kama dubu d'ari biyar cif. "Wannan kud'in ai sunyi yawa. Ba sayar da Saratu za muyi ba ai. Makullin mota kuma, ina naiman alfarma ku rik'e a wajenku duk lokacin da Sarah ta shigo gidan, sai ku damk'a mata." Sosai ya Abdullah yaji dad'in rashin ganin kwad'ayi a fuskan baba, sai yayi murmushi tare da fad'in, "Baba ai sadaki bai yawa duk da albarkan ake nema. Amma duba ga yanayin da muke ciki yanzu, ko billion aka bada kud'in sadaki, ai bai yi yawa ba. Zan dai mayar da makullin motar sai tazo tukun kamar yanda ka buk'ata, amma maganar rage sadaki kam ayi hak'uri." "To Allah ya sanya alkhairi ya sa ayi damu." Gaba d'aya d'akin aka amsa da amin. Bayan tafiyarsu, Baba ya ce su Baba sama'ila ko wannen su ya d'auki buhun shinkafa d'aya ya tafi dashi. Nan Lami ta daka tsalle tace ba zai yuwu ba tunda ba ubansu ya kawo ba. Ai kuwa Baba ya haukace mata kuma basu bar gidan nan ba sai da buhun shinkafa kowa d'aya. Don buhunar shinkafar guda ashirin ne ciff. Nan Lami ta dunga surfa bala'i ba'a fad'a mata za'a zo kawo kud'in auren Sarah ba, sannan kuma tace dole a fito da sadakin a raba. Ko kallonta Baba bai kuma yi na ya koma d'akinsa tare da yiwa sadakin Sarah mummunar b'oye don yayi rantsuwa kwandala ba zai bata ba tunda ba hakkinta bane shima kuma ba nashi bane. Gaba d'aya yaran gidan basa nan lokacin da aka kawo kayan auren Sarah. Sarah d'in ce kawai ke gida don ita bata zuwa ko ina. Lokacin da suka dawo kuwa, ba k'aramin rud'ewa suka yi ba ganin uban kayan saka ranar Sarah da aka kawo. Da Lami ta fad'a masu har da mota, yanke jiki Aina'u tayi ta suma, babu wanda yayi tunanin bak'in ciki ya saka ta ta suman. Data farfad'o kuwa kuka ta fashe dashi. Tambayarta suka soma yi, sai tace masu ciwon kai da basir ne ke damunta. Mintuna biyar bata k'ara yi a gidan ba. Ameeru, duba nan kaga abunda aka turo min da b'oyayyiyar number, karanto muji don Allah. Ni na kasa fahimta. _ASSALAMU ALAIKUM. NA SAN ZA KAYI MAMAKIN WANNAN SAK'ON DA NA TURO MAKA. ABUNDA YA SAKA NA TURO KUWA, GANIN GIDANKU GIDAN MUTUNCI NE, KUMA MAHAIFIN KHALIL YA RASU KOWA NA GANIN GIRMA DA K'IMARSA HAR KUWA YAZU DA BAYA CIKIN DUNIYAR. NA SAN BAKU YI BINCIKE BA GAME DA GIDAN DA KUKA JE KUKAI KAYAN AURE BA. TO INA MAI BAKU SHAWARA KU KOMA DA KYAU KUYI BINCIKE, DOMIN DAI YARINYAR NAN BA TA KWARAI BACE. BATA JIMA DA ZUBAR DA CIKI BA. RUFA-RUFA AKAI MAKU. GIDAN NAN BA GIDAN MUTUNCI BANE DOMIN TAKEN GIDAN SHINE *GIDAN KARUWAI* IDAN KUMA BAKU YARDA DA MAGANATA BA, ZA KU IYA YIN BINCIKE DOMIN TABBATARWA. DON YAYYIN YARINYAR BABU WACCE BATA AJIYE SHEGE BA. IDAN KUMA HAR KUKA AMINCE WANNAN YARINYA TA SHIGO CIKIN ZURI'ARKU, TO KAMAR FA RUWAN KWATA KUKA D'IBA DA HANNUNKU KUKA ZUBA A CIKIN RUWA MAI KYAU!_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* Paid book 08128755583 *_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *PAGE 16* A zafafe Uncle Ameeru ya mik'e tare da fad'in, "Na rantse da Allah ba zan tab'a bari ayi auren nan ba. Dole ne muje gidan can yanzu mu saka su a gaba muje mu kwaso duk abunda muka kai gidan. Mun janye maganar auren." Wani murmushi uncle Ridwan yayi tare da fad'in, "Gaskiya baka da hankali Ameeru!" "Rabu dashi mana, ni ai kallon wawa nake masa daga nan zaune. Ko ka manta cewa yayi ba zai auri y'armu ba saboda ta lalace? A gaban idanunmu gaba d'aya babu kunya ya fad'a mana wannan maganar. Har yanzu maganar tana sukar zuciyata. Ai ni wannan abu ba dad'i yayi min wallahi. Naji dad'i sosai da ya zam yarinyar gantalalliya ce. Kun ga kenan mun samu hanya mafi sauk'i da zamu cimma burinmu. Kawai had'a kai za muyi da yarinyar mu kashe d'an iska da ransa, musamman ma Bilkisu da ta hana mu rawar gaban hantsi. Shegiya duk hukumomi ta haifo, daga soja, sai d'an sandar farin kaya da kuma d'an iskan nan Barrister da ya gaji ubansa." Fad'in uncle Zayyanu. Uncle Shamsu kuwa cewa tayi, "Ni wallahi duk cikin y'ay'an Bilkisu nafi tsanar d'an iskan yaron nan _Khalil_ da wansa Abdullah. Kun ga da ace yaron nan soja a Kadunan nan yake, wallahi watarana sojoji zai saka su b'alla k'afafuwanmu. Bakwa ganin yanda yake nuna isa yana wani fankama kawai don ya kasance soja. Ni dama a kashe d'an iska acan wallahi." "Shegu taurin rai garesu kamar ubansu. Wani irin farmaki ne bamu kaiwa Nura ba, amma yana nan kamar kainuwa har sai da lokacinsa yayi. Mun sha wuya wallahi." Fad'in uncle Ameeru. Uncle Shamsu yace, "To yanzu dai mu tsayar da mafita. Mai kuke ganin za muyi? Ta yaya zamu b'ullowa ita yarinyar da zai aura?." Uncle Ridwan ya fad'i. "Ku bar min duk wannan a hannuna." Fad'in uncle Ameeru. "Yauwa Ameeru. Na sanka indai ta wannan fannin ne. Da ace yarinyar nan da ta turo sak'o ta bar wani makama da za mu bibiyeta, da ta cab'a don ta hanyarta zamu samu bayanai masu dama. Don ga dukkan alamu bak'in ciki take yi shiyasa ta tona asirin wancen, watak'ila kuma k'awa ce. Duk da hakan dai kuma za mu bincike gaskiyan labarin da ta bamu a kan gidan sabida mu san ta yanda zamu b'ullowa abun." "Yauwa nima abunda nake so in fad'a kenan." Uncle Zayyanu ya fad'i. Hajiya babu abunda take yi sai shirye-shirye. Gaba d'aya ta gama kiran dangi na kusa da na nesa na shaida masu auren _Khalil_ da za ayi nan da sati biyu. Aunty Maryam kuwa har ta gaji da zuwa kasuwa ita da aunty Khairat, don tun da aka saka bikin Aunty Khairat tazo don tuni har sun koma Kano, sai dai can ta baro Barrister shi sai ana saura 2days biki zai zo sabida aikinsa. Duk da kayan lefen kusan gaba ki d'aya a Dubai suka sayo har da akwatin, don private jet suka bi suka yo sayayyar kasancewar duka bangarori hud'un sun saki kud'i, Yaya Abdullah 5million ya bada, ya Barrister kuma ya bada 3million, ya Abdul-Hakeem ya bada 2.5million, shi kuma mai gayya 10.million ya bada. Hajiya kuma ita ta saya akwati set d'aya mai guda goma sha biyu. Gaba d'aya jimillar kud'in suka kama 20.5million. Dasu gaba d'aya su aunty Maryam, aunty Khairat da wata autar su Hajiya suka tafi Dubai. Sai da suka sayo akwatina set uku, na hajiya dozen, sauran biyun kuma mai guda six-six sai dai masu d'an karan tsada kuma gaba d'aya sai da aka cika su da mahaukan kaya masu tsada, don lesses d'in da aka saka babu na k'asa da 200k, kaya dai kamar za'a bud'e shago. Bayan sun dawo gida Nigeria kuwa, haka suka dunga yawon kasuwa suna k'aro wasu abubuwa don sai da suka dawo Hajiya tayi ta fad'a ganin babu kayan uwa da uba. Ana Nigeria suka k'ara had'o set d'in akwatuna guda uku irin mai biyu d'innan da kit. D'aya shaddojine da takalmar maza da turare da huluna masu tsada wanda ya kasance na Baba, sai d'ayan set d'in kuma aka zuba atamfofi da lesses da manya-manyan mayafai da takalma da turare. Shi kuma na Lami, sai d'ayan set d'in akai wa y'an uwan Sarah komai kala biyar-biyar, lesses kowa ta samu biyu, haka shadda da atamfa, sai takalma uku-uku da jakunkunarsu har da sark'a da y'an kunne. Gaba d'aya a parlourn Hajiya aka zube kayan. Sosai Hajiya taji dad'i don gaba d'aya babu k'arya. Yawan kayan ya saka ba komai Hajiya ta iya gani ba daga cikin kayan Sarah don akwatuna har set uku, wanda gaba d'aya jimillar akwatunanta kawai sun kama 24. _Khalil_ kuwa sai dad'a gyara b'angarensa yake yi wanda ya kasance four bedroom a k'asa da wawakeken parlour guda biyu mai d'auke da, dinning sai kitchen da store wanda girmansa da tsaruwarsa ma kawai abun kallo ne. Sama kuma two bedroom da parlour d'aya. Can gidansu Sarah kuwa, Lami da Aina'u ne kawai basa farin ciki da wannan aure da za ayi, gwara ma Lami ita gani kawai take yi idan akai auren shikenan za'a daina kawo mata abun arziki, yayin da Aina'u ita tsabar hassada ce da mugun hali. Babu kuwa kullum bakinsa bai rufuwa sabida farin ciki, sai shirye-shirye yake yi. Don yanzu Alhamdulillah har waje yana iya fita ba tare da sandar ba. Yana zuwa wajen abokansa suna ta shirye-shirye don Baba yace har walima sai yayi. Sarah kuwa babu wacce ke fad'o mata a rai irin K'awarta Muniba, duk duniya ita kad'ai ce k'awarta, gashi kuma tuni iyaye sun raba tsakaninsu. Kamar Baba ya san halin da take ciki, har gida yaje ya samu liman (Mahaifin Muniba) ya bashi katin gayyata sannan kuma ya rok'eshi alfarmar ya bar Muniba tazo wajen Sarah suyi shirye-shiryen biki don duniya bata da wata k'awa sai Muniba. Mahaifin Muniba yaji dad'i sosai jin Sarah za tayi aure kuma yace wa Baba in Sha Allah Muniba zata zo. Sarah na zaune tana sak'awa da warwarewa, don basu jima da waya da _Khalil_ ba yake shaida mata zuwa anjima zai zo suyi maganar shirye-shiryen da za tayi na auren tunda gaba d'aya bikin yanzu ya rage saura kwana bakwai don har anci sati d'aya daga cikin ranakun auren da aka saka. "Assalamu alaikum!" Da mugun gudu Sarah ta fito jin kamar muryan Muniba. "Munibaaaaaaaaaa!" Ta fad'i sunanta da k'arfi cike da farin ciki ta rungumeta tana fad'in, "Wayyooooo Allah na, Muniba kece? Zo mu shiga daga ciki." Ta kama hannunta suka shiga cikin d'aki. Sakin labule Aina'u tayi, don tun jin sallamar Muniban ta d'aga labulen d'akin Lami tana kallon su. Dogon tsaki taja tare da fad'in, "Duk ku gama zumud'inku, wallahi wannan aure ba mai yuwuwa bane. Bamu y'an iska marasa sanin darajar kai irin y'an uwan mahaifin _Khalil_ d'in ma, ace a tura maku irin wannan sak'o amma baza ku tashi kuyi bincike tare da d'aukar mataki ba. Y'an iska kawai!" Duk a zuciya tayi maganar tare da shigewa tana mai yin kwafa tare da fad'in, "Ina da shiri a k'asa mai zafi, duk sai kunci ubanku." "Ke kuma dawa kike kwafa?" Fad'in Lami. A zafafe tace, "Babu ruwanki dani. Tom!" Tana gama fad'in haka ta zari gyale tare da ficewa daga gidan. "K'awata nayi kewarki. Ya aka yi su Baba suka bari kika zo gidan nan?" Sarah ta fad'i bayan ta bud'e d'an k'aramin fridge d'in dake d'akin ta d'auko mata ruwan sanyi da exotic. "Masha Allah! Haka kuka yi gyara a gidan? Wuri yayi kyau. Wannan irin makeken gado haka!" Ta fad'i hakan tare da hawa kan gadon tana shafawa. "It's a long story Munee, naji dad'i da Baba yaje yayiwa babanku magana don wallahi ke kad'ai ce k'awata a duniya gashi kuma d'azu muka gama waya dashi akan zai zo ya sallami k'awayen amarya." Saukowa Munee tayi tare da fad'in, "K'awata wa kika kamo haka? Kwanaki nake ta jin rumours wai kin yi cikin Shege Farouq ya fasa auranki. Ni ina jin maganar ta shiga kunnan hagu ta fita ta dama. Kuma kin san wake fad'awa mutane? Aina'u fa!" Tab'e baki Sarah tayi tare da fad'in, "Uhm, kyaleta. Kin san su suna goyon bayan Lami ne, basu son inyi aure. Ni kuwa zaman mai zan yi a gidan. Ai gwara na tafi nawa gidan nayi bautar ubangiji." Hannu Munee ta bawa Sarah suka kashe sannan tace, "K'awata kenan! To shi angon naki a ina yake." Gyara zama Sarah tayi ta d'an bata labarin in brief saboda ciki ba don abinci kawai aka yisa ba, duk da kuwa ta yarda da Muneeban. "K'awata na taya ki murna wallahi. Allah ubangiji ya sa mijinki ne ya kuma baku zaman lafiya mai d'orewa." "Ameen k'awar arziki." Daga nan suka fad'a hirar yaushe gamo har har lokacin da _Khalil_ yayi kiran Sarah a waya ya shaida mata yana waje. Tare suka fita da Muneeba zuwa wajen _Khalil_ d'in. Lokacin da Muneeba tayi arba da _Khalil_ rud'ewa tayi don b'ata tab'a hasaso haka yake ba. "Wannan itace k'awar tamu?" Fad'in _Khalil_ yana murmushi don tsabar rud'ewa Muneeba ta kasa gaishe shi har sai da Sarah ta d'an tsunguleta a cinya sannan ta dawo hayyacinta. "Kamar mai asibitin _Khalilullah specialist hospital_ ko? Ka tab'a duba ni sau d'aya a asibitin ka." Dariya yayi tare da fad'in, "K'aninsa ne, ba shi bane." Ya k'arisa maganar yana mai kashewa Sarah idanu. Dariya Sarah tayi tana kallon Muneeba dake masa anya kuwa. "Gaskiya kamannin sun b'aci. Kai ne mijin k'awar tawa kenan?" "In Sha Allah!" _Khalil_ yayi saurin fad'in. "Ma sha Allah! To bud'e kunnuwanka da kyau zan baka amana." Hannu biyu _Khalil_ ya saka ya rik'e kunnuwan nasa tare da fad'in, "Ina jinki k'anwarmu." Dariya Sarah ta kwashe dashi ganin yanda yayi tare da bada full attention d'insa wa Muneeba. "Wannan k'awata ce kuma aminiyata. A yau karo ba farko ina mai damk'a amanarta a hannunka, kar inji ko a cikin mafarkina tana kuka, idan ma za tayi, to ya kasance na farin ciki. Sannan a rik'a lallab'ata kamar kwai. Baka da matsala in dai aka zo fannin biyayya, don k'awata akwai biyayya kuma na tabbata za tayi maka biyayya. Yi, nayi, bari, na bari. Duk zata kiyaye su. Kai ne babba, key na controlling gidanka yana hannunka, Sarah kamar motarka ce, duk inda ka nufa da ita, nan zata bi. Saboda haka, dan girman Allah, kar inji Sarah tayi kuka da kai." Sosai _Khalil_ yaji Munee ta kwanta masa a rai. Murmushi yayi tare da fad'in, "An gama aunty Muneeba. Hud'ubarki ta shiga sosai." Juyawa tayi ta kalli Sarah tare da fad'in, "K'awata na dawo kanki, kin ga, wallahi kiyi masa biyayya domin aljannarki na k'ark'ashin k'afarsa. Idan ya take, sunanki sorry, don haka kema kar inji yayi kuka dake. Irin tarairayan duk ki rik'a masa. Kamar irinsu, Gwandi, zaka sha gwanda, honey zaka sha Honey, Sweety zaka sha swee....." Kamun ta k'arisa cewa sweet d'in daga _Khalil_ har Sarah suka fashe da dariya. Ita kanta Muneebar dariyar take yi. "Gaskiya k'awar mu naji dad'in wannan hud'uba naki. Mun gode Allah ya saka da alkhairi kuma mun d'auka." Murmushi a fuskanta tana mai taya k'awarta farin cikin samun miji kamar _Khalil_ tace, "To ma Sha Allah. Haka nake so ai." Gyara tsayuwa _Khalil_ yayi tare da fad'in, "To yanzu wani shirye-shirye kuka tsara ta wajenku?" Kallon Sarah Munee tayi sai kuma ta kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Gaskiya ta wajen mu, walima kawai za muyi da k'awayen mu na makaranta da kuma mutanan anguwa. Ko ya kika ce k'awata?" Ta k'arisa maganar tana kallon Sarah. Gyad'a mata kai Sarah tayi tare da fad'in, "Eh hakane." "To ustazai. Ni dai abokaina sun had'a min dinner. Don haka bayan an d'aura aure akwai dinner sai ku kasance cikin shiri. Allah yasa k'awar tamu tana da account?" Ya k'arisa maganar yana kallon Munee. "Eh ina da shi." Fad'in Munee. Fiddo wayarsa yayi tare da fad'in, "Fad'a min account number d'in." Bayan ta fad'a masa da sunan bank d'in, a take yayi mata transfer d'in 500k. Waro idanu Munee tayi lokacin da tayi arba da kud'in da ya turo don har sai da ta murza idanu. Tun da take kud'i dubu ashirin ma basu tab'a zama cikin account d'inta ba ko da mistake, sai ga dubu d'ari biyar sun shigo yau. "Wad'annan kud'in fa? Wallahi sun yi yawa. Duk na minene haka." "Duk na walimar ce." Ya fad'a kai tsaye. "Dan Allah sunyi yawa wallahi." With serious face yace, "Basu yi ba. Kuma kar ki sake magana. Kuje kuyi duk wani hidimar da za kuyi dasu. And in Sha Allah two days before the wedding za'a kawo maku raguna guda uku da drinks. Yanzu haka ma idan kun koma gida kuyi list d'in duk wani abubuwan da zaku buk'ata sai ku turo min." Gaba d'aya Muneeba is speechless. Sai gyad'a kai kawai take yi. B'ata tab'a yin y'an matan amare ba, amma ta sha gani da ji, wani lokacin ma da fad'a ake k'arewa da abokan angon domin wasu dakyar suke fitar goma zuwa sha biyar. "Bari na baku waje, sai kin shigo k'awata." Fad'in Muneeba. "To k'awarmu, mun gode sai ta shigo tunda ni baza amin sallamar ba." Dariya Muneeba tayi tare da fad'in, "Sai da safe asha soyayya lafiya." Tana gama fad'in haka ta shige gida tana dariya. Sun jima a waje suna hirar su ta soyayya, sai da zai wuce yake fad'a mata ta fad'a a gida gobe za'a kawo akwati. Tana shigowa gida ta nufi d'akin Baba kai tsaye ta fad'a masa sak'on _Khalil_ shi kuma ya cire dubu hamsin a cikin kud'in da _Khalil_ ke basa idan yazo gaishe sa yace taje gidan su Muneeba ta kaiwa mahaifiyarta ayi y'an soye-soyen fulawa da kuma kaji. Sannan ya ware wasu kud'i ya ajiye wanda idan y'an kawo kaya sunzo a basu tukwuici. Da Muneeba zata wuce gida tare suka tafi wajen mahaifiyarta tayi mata bayanin sak'on da Baba ya turo ta ta fad'i. Hannu biyu Mama ta karb'a har ta bada sautu saboda a sayo komai da wuri kasancewar gobe bak'in za suzo. Anan ne kuma Sarah da Muneeba suka fad'a mata yanda suka yi da _Khalil_ game da walimar da za suyi da kuma kud'in da ya turo. Ita kanta mama tayi mamakin kud'in, amma da taji anan mahaifin _Khalil_, sai mamakin ya sake ta don ta san irin kud'in da suke dashi. Mama tambayar Sarah tayi shin akwai wani gyara ne da ake mata na jiki a gida, sai Sarah ta fad'a mata babu abunda ake mata. A take mama ta kira waya aka turo mata number d'in wata kwararriyar mai gyaran jiki da yake tana home service. Cikin awa d'aya ta iso da duka kayan gyaran jiki. A cikin kud'in _Khalil_ da ya turo aka tura mata 200k domin soma fara yiwa Sarah gyaran jiki daga yau da daddare. Ai kuwa na dare d'aya tal sai da Sarah ta tabbatar an soma gyara jikinta. Baba da kansa yaje har d'akin Lami ya shaida mata y'an kawo akwati za su zo, sai da tayi masa kallon sama da k'asa tukun sannan tace, "To wata uwar zan yi masu da kazo ka tsaya min a kai?" Murmushi kawai baba yayi tare da juyawa ya koma d'aki don dama yaji a jikinsa babu wani abu da Lami za tayi shi yasa ma ya tura Sarah can gidan su Muneeba. Na'ima ce ta kalli Lami tare da fad'in, "Gaskiya Lami ba haka ake yi ba. Idan fa za'a kawo akwati, dangin amaryar sha tara na arziki suke yiwa dangin ango kamar irin su soye-soyen kaji, su meatpie, samosa, spring rolls da sauraransu har da tukwuicin kud'i. Kuma ni ina ji a jikina ba k'aramin kaya za'a kawo wa Sarah ba." Harara Aina'u ta makawa Na'ima tare da fad'in, "Munafuki annamimiya!" A cikin zuciyarta. Amma a zahiri sai cewa tayi, "Wallahi Lami kar kiyi komai. Kin san halin masu kud'in nan da shegen raini da d'aga kai kamar dan su Allah yayi duniyar." Da sauri Na'ima tace "Ke dai Aina'u annamimiya ce. Idan baza ki kashe wuta ba, to kar ma ki soma hurawa. Shegiya gwara dai ki fito da naki nashinshinin bar yiwa wata hassada. Ko sau d'aya bam tab'a jin wani yazo yana sallama dake ba." A fusace Lami tace, "Wannan wani irin maganar banza ce haka Na'ima? Ban so! Kar ki kuma yi mata irin wannan maganar. Ni kaf y'ay'ana babu wanda bai da farin jini. Farin jini a nono na kuka tsotsa." A fusace Aina'u tace, "Ni ko mai zan yiwa Hassana a jikin wannan banzan da zata aure! Allah ya kiyaye in auri wanda zan zama baiwarsa. Ai duk wata shegiyar da tayi aure ta san inda ta kai kanta. Daga wanke min kayana, dafa min abinci sai goge min takalmi. Sannan idan dare yayi ya kwashi romon albarkan jikin banza a banza ya tashi ya kakkab'e jikinsa kuma ba shi zai hana gobe yayi maki muzurai ba. Watak'ila ma naira d'ari biyu sai kinyi kamar za kiyi kuka ka mun ya cire ya baki. Allah ya sawake nayi aure! Ita ma da kuka ga ina nuna kamar ina jin haushi, sabida y'ar uwata ce ina hango mata wahala musamman da zata shiga gidan masu arziki. Kun ga sun samu y'ar aiki a sama wacce bata da salary." "Nace ba, da kike wannan hak'ik'icewar, ina naki tsayayyan kwarton?" Fad'in Na'ima tana harararta. Aina'u za tayi magana kenan Luckyboy ya fad'o d'akin tare da fad'in, "Ke Aina'u, gasu can a waje suna jiranki." Kwafa Aina'u tayi tare da mik'ewa babu ko gyale ta fice daga d'akin. "Kina ji ko Lami, dan Allah kar kibi shawarar Aina'u, kiyi amfani da kud'inki kiyi masu sha tara ta arziki, sannan gayya fa ake yi. Dole sai kin kira k'awayenki domin su zasu karb'i kayan ba ke ba." Fad'in Na'ima. "Wai maganar me kuke yi haka? Ni sallame ni kawai Lami in ware. Kuma eh, naga anyi eh ya ne a cikin gidan nan, amma ba'a bani rabona ba. Ke nan ni ba d'an gidan bane?" "Ungo wannan, tafi ni ka ishe ni." Fad'in Lami tare da mik'a masa dubu talatin. Da idanu Na'ima tabi kud'in sannan ta juyo ta kalli Lami bayan fitar Luckyboy tare da fad'in, "Lallai ma Lami! Dama duk uban kud'in da muke baki, da wanda _Khalil_ yake baki Lucky kike tattarawa kike ba yana tafiya shi da abokai suna shaye-shaye." Lami ko taro bata yi ba sai zurawa plasma TV tayi tana kallon arewa kamar bata san mai Na'imar ke cewa ba. Washa gari wajajen k'arfe biyu sai ga dirar motoci masu kawo lefe sun zo. Dama kuma Munee na gidan, da sauri ta fiddo waya ta kira mahaifiyarta ta shaida mata sun zo don ita ce tace su fad'a mata a waya idan sun k'ariso. Cikin k'ank'anin lokaci sai ga mama da tawagarta su k'ariso gidan hannunsu nik'i-nik'i da manyan kuloli. A nan tsakar gidan aka shimfid'a masu k'atoton tabarma. Su suka yi insisting sabida d'akin ba d'aukar su zai yi musamman da irin kayan da suka zo dashi. Aunty Maryam, aunty Khairat, kanwar Hajiya, matan uncles da matar ya Abdullah ne suka kawo kayan. Su suka fara shigowa, sai da suka gama gaisawa da mahaifiyar Munee da mutananta da ta gayyato. Na'ima kuwa hana Lami fitowa tayi don cewa tayi sai tayiwa Baba da mahaifiyar Munee tujara akan abunda suka yi mata. Sai zage-zage take tana fad'in akwai wani banzan alak'a tsakanin Baba da mahaifiyar Munee. Allah yaso babu wanda yaji abunda take fad'i sai Na'ima da take ta faman bata baki a d'aki. Kuma ta kulle d'akin ta ciki duk da kuwa tana so ita ma taje taga kayan da ta hanga ta window driver na wucewa dasu yana ajiyewa a nan tsakar gidan. Sai da ya kawo duka sannan aka soma bubbud'ewa. Babu abunda ke tashi sai kabbara da gud'an mata. Tun mata na irge har suka hak'ura don b'ata lissafi suke yi. Mata sai uban santi suke yi da gud'a. Gaba d'aya gidan ya cika da mutanen dake ganin kayan Sarah. Aina'u kuwa zawonta uku a cikin wando ganin mahaukatan kayan da aka zubawa Saran. Bayan an gama gani, mama ta ware na Baba, Lami da kuma wanda aka ce na k'annai da yayyin amarya ne ta ajiye a gefe, sauran kuma aka bar su nan tsakar gida. Dubu d'ari uku Baba ya bada matsayin tukwuicin duk da kuwa bai san adadin kayan da zasu kawo ba. Y'an kawo akwati sun mik'e zasu wuce kenan sai ga tawagar matan zumunta sun shigo gidan da wani irin mahaukacin gud'a suna tafi tare da yin wak'ok'in coci. Gaba d'aya sai kallo ya koma sama. "Elizabeth kina ina? Ashe aurar da yarinyarki za kiyi amma shine baza ki gayyaci mutanan coch ba. Baki kyauta ba sam. Pasto William yayi fushi dake kuma yace idan baki kai Sera (Sarah) ya saka mata albarka ba, auren ba zai yi albarka ba. Yace ya baki kwana biyu ki kaita ayi mata wankan zunubi kamun ta shiga gidan miji. Da k'arfi aunty Rose Merry take maganar duk da kuwa bata ga Lami a tsakar gidan ba. Aunty Maryam da aunty Khairat da kanwar Hajiya, sai wannan ta kalli wancen, sai wancen ta kalli wannan. Da suka ga abun ba na k'arewa bane, sai suka yi salama suka tafi domin sosai dai aunty Rose Merry da tawagarta suka baje suna wak'ok'in suna kiran sunan yesu almasihu. Idan suka buga wani ihu har hanjin mutum sai ya kad'a. Baba dake d'aki kuka kawai ya fashe dashi. Don bai tab'a kawowa Lami zata iya yin wannan iskancin ba. Lami dake d'aki ita ma mamaki ne ya kamata don ko da wasa bata tab'a fad'awa mutanen coch d'insu zata aurar da y'a ba. Ko aunty Rose Merry da take k'awarta bata fad'a mata ba. "Na'ima wallahi bani na gayyace su ba, kuma ban san wanda ya kira su ba." Na'ima kuwa kallon mahaifiyarta take yi cike da tuhuma tare da fad'in, "Lami dama kina zuwa coch? Wa za ayiwa wankan zunubin?" Lami bata ba ta amsa ba, sai wucewa da tayi ta bud'e k'ofar ta fita ta samu ce aunty Rose Merry dake ta kwasar ihu da kiran yesu suna d'ad'd'aga kayan akwatin Sarah. "Hajiya kina bacci ne aka kwaso maki dangin arna matsayin surukarki?" *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* *_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜*KANWAR MATATA*🦜 *PAGE 17* "Hajiya kina barci ne zaka kwaso maki dangin arna matsayin surukarki? D'iyar Elizabeth ce kuma Wallahi matan zumunta cike da gidan har da zancen zuwa wajen Pasto domin ayiwa ita matar _Khalil_ d'in wankan zunubi." "Wankan Zunubi?" Hajiya ta fad'i cike da mamaki tana kallon K'anwar tata Marwanatu. "Wallahi tallahi Hajiya kar ki yarda da wannan aure idan ba haka ba akwai mummunar matsala. Wannan wani irin bahagon gida ne haka." Fad'in Inna Marwanatu. Amma abunda ya matuk'ar d'aure mata kai da bata mamaki shine ganin hajiya tayi murmushi tare da cigaba da ware anko da take yi wanda ta sayawa y'an uwa da abokan arziki. "Hajiya dariya fa kika ki. Na fad'a maki irin wannan magana mai d'aga hankali shine kike murmushi mai makon ki fusata ki kira waya a fasa wannan aure." Ajiye kayan da ta d'auko tayi tare da kallon Marwa sannan tace, "To ai ni ban fahimceki bane Marwa. Shin laifin uwar ne zai shafi y'ar ko kuwa? Ba ita bace arniyar idan rrtkq a kina magana akan a fasa auren. Ko da kuwa itace, ai addininmu bai haramtana mana kawo su cikin mu, mu dai matsayin mata addini bai amince mana da mu zauna dasu ba. Kuma wannan yarinyar da _Khalil_ zai aura, bayan binciken da marmari yayi, na saka anyi min nawa da kai na a kanta. Don haka ita kad'ai zamu kawo cikin gidan nan ba ba mahaifiyarta ko kuma matan zumunta ba. Idan aka kawo ta cikin gidan kowa ga watse ai shikenan ko? Don Allah Marwa bana son in k'ara jin wannan maganar, ya tsaya tsakanin mu kawai." Da sauri Marwa tace, "Amma Hajiy....." "Dan girman Allah ki bar wannan maganar haka Marwanatu." Tsit Marwa tayi bata kuma cewa komai ba sai ma juyawa da tayi ta bar d'akin. Tana fita Hajiya ta jingina da gado tare da fad'awa duniyar tunani don fisabilillahi ta daure ne kawai a gaban Marwa ta kare surukar tata da gobe amma ba wai don bata firgita da labarin da taji ba. "To ko dai in d'auko yarinyar nan ne har sai anyi biki? To kuma ai ba'a tab'a haka ba a al'adar hausawa. Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Allah kana gani, kafi kowa sanin dalilin wannan had'i. Allah kasa alkhairi ne albarkacin soyayyar da kakewa fiyayyan halitta." A bayyane tayi magana tare da jan dogon ajiyar zuciya. "Baba, shawara zan baka, ka saka a kwaso duka kayan can na waje, idan ba haka ba wallahi duk yawon kayan can Sarah baza ta tafi da abun arziki ba." Na'ima ta fad'i ba tare da ta damu da kukan da ta iske baban nayi ba. D'agowa Baba yayi ya kalli Na'ima, bai tab'a d'auka za'a samu wacce zata iya wannan maganar hankalin a cikinsu Na'imar ba. "Na'ima kuje ku kwaso kayan tsaf ku kai gidan liman Muhammadu mahaifin k'awar Saratu. Ku kira yara su kwashe kayan zan biya kud'in." Da to Na'ima ta amsa tare da fita dama kamun tazo d'akin Baba ta saka su Nuratu sun saka idanunsu sosai a kai gudun y'an sibaren na ayye. Cikin abunda bai wuce mintuna ashirin ba, Na'ima ta had'a kan yaran anguwa da almajirai sun kwashe kayan tsaf an tafi dasu gidan mahaifin Muneeba. Lokacin Lami na d'aki ita da k'awayenta matan zumunta. Sai da ta fito domin d'ibar masu nasu kayan kamar yanda suka yi mata fanfo, sai taga wayam duk da kuwa tana jin hayaniyar yara lokacin da suka zo tafiya da kayan, amma sai tayi tunanin ko y'an ganin kaya ne. Da masifa ta hau tambaya ina kayan. "Suna gidan k'awar Saratu. Can Baba yace a kai sabida yawan mutanen da suke shigowa gudun sata." Fad'in Na'ima. "Kutumar kaza-kazan can......... To wallahi ku fita ku dawo da kayan nan yanzu. Uwar wani ce ta haifar min y'ar da har za'a ce an kai kayan y'ata wani gidan. Wallahi ba liman ba ko sarkin makka ne sai naci kaza-kazansa (Ta wulwulo zagi) idan bai saka an maido mi da kaya y'ata ba." Fad'in Lami. Baba dake d'aki ya kai wuya, bai san lokacin da ya fito daga d'aki ba tare da fad'in, "Lami, na gaji da halinki. Wallahi tallahi idan kika k'ara magana akan wannan kayan sai na sake ki. Haba! Kin takura min kin hana ni shan iskan duniya cikin salama. Kuma wallahi idan y'an iskan k'awayenki basu fito sun bar gidan nan ba, sai na masu itace. Idan kuma sun ce k'arya ne, su k'ara mintuna biyar suga abunda zai faru." Matan zumunta na jin haka suka fara fitowa d'aya bayan d'aya. "Ku koma, babu inda za kuje. Wallahi dai-dai nake da kai Nuhu a cikin gidan nan. Idan ka fasa saki na, Allah ya tsine maka albarka. Kuma kaya sai an dawo dasu gidan nan." A zuciye Baba yace, "Kije na sake ki saki d'aya, bi........" Da wani irin mahaukacin gudu Sarah ta fito tare da jan burki ta kifa guiwarta a k'asa tare da fashewa da kuka tana fad'in, "Kar ka k'arisa, kar ka k'arisa Baba dan girman Ubangiji. Wallahi in har ka saki mama akan kayan akwati na, ba zan tab'a yin auren ba na fasa. Dan girman Allah ba dan halin Lami ba Baba ka mayar da ita. Baba ina wannan hak'uri da ka dad'e kana yi ya tafi? Haba babanmu." Ta k'arisa maganar tana mai fashewa da kuka. "Na gaji ne, na gaji Saratu. Saratu nayi iya hak'urin da zan iya yi da mahaifiyarku. Ta tafi kawai ai tana da dangi." D'aya daga cikin matan zumunta ta soma fad'in, "Yesu almasihu kayi mana tsari da irin wannan mutanan da ka tsine masu." Zabura Baba yayi tare da rarumo wani narkekiyar langen ya rafka mata a tsakiyar baya, sauran kuma yayi kansu. Da gudu har da k'undunbala suka fice daga gidan. D'aya har tana sakin tusa. K'afafunta Baba Sarah ta rik'e tana fad'in, "Baba dan Allah kayi hak'uri ka mayar da Lami." Baba yace, "Kiyi hak'uri Sarah, zamana da Lami akwai cutarwa. Gwara kawai ta tafi." Wani irin kuka Lami ta fashe dashi tare da fad'in, "Azzalumi ka rabo ni da y'an uwana ka kawo ni nan kana cutar dani. Yesu ba zai tab'a yi maka albarka ba. Shiyasa sabida mugun halinka ya maka mummunar tsinuwa ka zama talaka. Kuma ko ka sake ni, ina nan gidan sai dai kai ka fita ka bar gidan." "Haba Lami, kukan me kike yi. Muje na kama maki d'aki ki zauna ki bar masa gidansa." Fad'in Aina'u tana hararar Baba. "Ban yi mamaki ba Aina'u. Banyi ba! Ai kina da abunda kike rabawa maza suna baki kud'i dole kice zaki kamawa mahaifiyar taki d'aki." Su Nuratu kuwa ko uffan basu ce ba. Na'ima kuwa kumbarta take yankewa yayin da Marfu'a ke wankewa yarinyar ta kashi bayan ta cire mata pampas. "Eh d'in. Da ace ka sauke duk wani hak'k'inmu dake kanka, ai baza mu kasance a yanda muke haka ba. Kai ne mugun daka cutar dam......" Ba tare da ta k'arisa ba Sarah ta sauke mata tagwayen maruka a fuska hagu da dama sai da tayi zaman y'an bori. Dama kuma kamar jira Ainau take ta rarumo wani sanda tayi kan Sarah dashi. Da sauri baba ya shiga tsakaninsu, Aina'u bata yi wata-wata ba ta saukewa Baba sandar a k'agu kasancewar ya d'aga hannu wajen k'ok'orin kare Sarah. "Wasssh Inna lillahi!" Baba ya furta hawayen azaba na sauko masa har kan kuncinsa. Wani irin fuzgewa Sarah tayi ta kai Aina'u k'asa ta hau kai mata wani irin duka ko ta ina a jikinta. Da kyar Lami da Na'ima suka d'aga Sarah a kan Aina'u wacce bakinta bai mutu ba sai auno ashar take yi marasa dad'in fad'e. "Ki kashe ta shegiya y'ar iska. Allah ya tsine maki albarka Sarah. Yesu ina rok'onka a yau ka hana Sarah kwanciyar hankali ita da Nuhu mahaifinta. Ba dai ubanki kika zab'a a kaina ba, to kije yesu ya tsine maki ke da ubanki. Ba dai ya sake ni ba." Ta k'arisa maganar tana mai jan kwafa. Wani irin kuka Sarah ta fashe dashi don ta san illar bakin uwa a wajen y'ay'anta. Da gudu ta k'ara kama k'afafun Baba tare da, fad'in, "Baba kayi min rai ka rufa min asiri kar bakin uwa ya kama ni ka mayar da Lami d'akinta. Dan Allah Baba. Wallahi idan baka mayar da Lami ba, ba zan tab'a zaman aure ba. Ko an d'aura auren sai na gudu na bar gari." D'agota Baba yayi tare da fad'in, "Share hawayenki Saratu. Bakin Lami ba zai tab'a kama ki ba don babu abunda kika yi mata. La'anarta kanta zai koma. Ki bar kuka, na mayar da ita d'akinta sabida ke. Domin ke nayi hakan ke d'aya." Fad'in Baba. "Aikin banza kawai!" Fad'in Aina'u. "Banza yi maki baki ba Aina'u, Allah ya shirye ki." Baba ya fad'i yana girgiza kai. Sarah kuwa wani d'an sauk'i taji a zuciyarta jin Baba ya mayar da Lami d'akinta. Da daddare har d'aki Sarah ta sami Lami tana kuka tana bata hak'uri akan ta janye tsinuwar da tayi mata, amma ko kallonta bata yi sabida ba k'aramin fanfo Aina'u tayi mata ba akan Sarah d'in. Sarah d'aki ta koma ta zari mayafi ta nufi pos ta ciro kud'i har dubu d'ari ta dawo gida ba bawa Lami akan ta karb'i kud'in amma ta yafe mata ta janye batun tsinuwa. Ganin Aina'u bata nan, sai ta amshe kud'in tace mata taje ta yafe mata. Ajiyar zuciya Sarah ta saki, sai a sanan taji hankalinta ya kwanta har ta iya tafiya gidansu Muneeba domin a cigaba da yi mata gyaran jikin da ake mata kullum da safe da kuma daddare. Don yanzu basa had'uwa da _Khalil_ sai dai a waya kawai. Don Mama (mahaifiyar Muneeba) da kanta tayi magana dashi a waya a kan yayi hak'uri ba zai k'ara ganin Sarah ba sai ranar aure. Ya amsa ne kawai don yana jin nauyinta. Amma kullum mak'ale take da waya. Wani lokacin sai mai gyaran jikin ta kwace wayar ta kashe sannan ake yin gyaran a nitse. Aina'u kuwa, kwana d'aya, biyu, uku, bata ji wani motsi daga gidansu _Khalil_ ba duk da gayyato matan zumunta da tayi sabida komai ya rushe. Karo ba uku kenan plan d'inta bai yin aiki. "Dole in tafi matakin k'arshe na hana auran nan." Tana fad'in haka ta fiddo wayarta tare da danna wata number tayi magana tsayin mintuna goma sannan ta yanke wayar tana murmushi. Tun daga wannan ranar Aina'u bata k'ara nuna komai ba. Daga k'arshe ma shiga cikinsu Sarah tayi ana ta hidima da ita. Sarah ba k'aramin wani irin tsananin kyau ta k'ara ba. Sosai dilkan da ake mata ya amshi jikinta. Sai wani glowing take yi kamar wata kulb'a. Ana gobe d'aurin aure, mai gyaran jiki tayi mata lalli ja da b'aki wanda ya kuma fito da kyawunta kasancewarta farar mace. Ba k'aramin kyau lallin nan yayi ba. A ranar kuma _Khalil_ ya kasa jurewa ya dunga rok'on Muneeba akan ta taimaka masa ta fito masa da Sarah da dabara ya ganta ko na mintuna biyar ne. Muneeba tace masa kar ya damu bayan Isha zata fito masa da ita. Don tun saura kwana biyar biki Sarah ta koma gidansu Muneeba da zama gaba d'aya. Kamar yanda suka yi alk'awari kuwa, ana idar da isha'i _Khalil_ yayi parking ta bayan gidansu ga kira Munee a waya. Sarah bata san shirinsu ba, kama hannunta kawai Munee tayi tare da ce mata tazo ta nuna mata wani abu. Har gaban motar _Khalil_ ta kaita ta, a jingine ta same sa jikin motar yaci kwalliya cikin wasu k'ananan kayan da suka yi masa matuk'ar kyau. Da kallo kawai yake ta bin Sarah da idanu ganin wani mahaukacin kyau da ta k'ara yi masa. Sai yaga kamar canzo masa ita aka yi. "To gata nan, dan Allah kar ku dad'e kaga mama ta fahimci bama cikin gidan." Sai a sannan _Khalil_ ya kalli Muneeba tare da fad'in, "Godiya nake k'awarmu. In Sha Allah baza mu jima ba." Wucewa tayi ta bar su tsaye suna kallon juna. "Nayi kewarki" a tare suka fad'i. "Ba wani nan kin ba kiyi kewa ta ba tun da baki tab'a cewa mu had'u ko a sace ba." Fad'in _Khalil_. "To ai ni tsoro nake ji kar mama ta gane." Sarah ta fad'i a shagwab'e. Shima shagwab'ewar yayi kamar yanda tayi tare da maimaita tace. Rufe fuska tayi da hijjab d'inta tare da fad'in, "Ni dai bana so." Nan ma ya kuma kwaikwayonta. K'afa ta bubbuga a k'afa tare da fad'in, "Ni dai ka bari." dariya yayi tare da fad'in, "To naji, mu shiga mota naga kamar tsayuwar yana damunki." Da sauri tace, "A'a ni dai na sai na shiga ba. Ai ka ganni, zan wuce kada mama ta gane bana nan." Waro idanu yayi tare da fad'in, "To ai ko mintuna biyar d'in basu cika ba. A hakan d'in ne kike cewa kin yi kewata?" Ko kamun Sarah tayi magana wayarta ta soma k'ara, ganin Muneeba ce duk sai ta rud'e ta shiga fad'in, "Munee ce ke kira na, shikenan na shiga uku watak'ila Mama ta gane bana gidan. Dan Allah zan wuce gida." ta k'arisa maganar tare da marairaicewa. Bud'e mota yayi tare da fiddo leda ya ya kama hannunta tare da fad'in, "Ungo wannan inji Hajiya. Amma dan Allah ki tsaya in miki hoto guda d'aya kawai." ya fad'i tare da fiddo wayarsa yayi mata hoto a jikin motar. Kallonta yayi tare da fad'in, "Haba mana, smile." Yanda ya fad'i smile d'in ne ya bada dariya. Sai hoton yayi kyau sosai don hatta dimples d'inta sai da suka lob'a duka. "Kayi wa Hajiya godiya, bye sai da safe." Ta fad'i hakan tare da saurin juyawa ta soma tafiya. _Khalil_ bai bud'e motarsa ya shiga ba sai da yaga tasha kwana. Taku uku tayi taji an jawota da k'arfi an toshe bakinta tare da shak'a mata wani abu a cikin tsumma. Take ta sune jikinta gaba d'aya ya saki. Cikin sauri maza ukun suka tura ta cikin wani k'atoton buhu suka d'aura akan wheelbarrow tare da turawa har zuwa wajen wata mota golf sannan suka bud'e booth suka jefa ta ciki Sannan suka rufe tare da shiga suka bar wajen.......... *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* *_MATAR SAYYADEE_* [9/30, 10:43 AM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *18* "Ke, bana son hauka! Kaza ce ita da zata b'ata? Ba ke kika kira wayarta ba? Kamun na juyo yanzu ki nemo min matata a duk inda take idan ba haka ba a kaf zuri'arku bana tunanin akwai wanda zan iya kyalewa ko jaririne." Yana gama fad'in haka ya katse wayar tare da yin reverse ya fizgi motar da gudu don har yayi nisa da layin. Muneeba kuwa jikinta ne ya soma wani kakkarwar tsoro zufa na yanko mata. Wayarta ta haska ta soma bin hanya tana kwala kiran "Sarah" ko Allah zai saka ta amsa. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Fad'in Munee tare da saurin d'ukawa ta d'auki takalmi da kuma ledar da _Khalil_ ya ba Saran. Kuka Munee ta fashe dashi tare da fad'in, "Inna lillahi wa'inna ilaihir, Allahumma arji'ini fi musibati. Saratu kina ina? Mun shiga uku, wayyo Allah, Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un." Haka ta dunga yin gaba tana dawo baya tare da ambatan sunan Allah. _Khalil_ nayin parking ya nufi hanyar da Sarah tabi a gaban idanunsa, kicib'is suka yi da Muneeba dake kuka tana kiran sunan Allah. "Ke!" Ya daka mata wani irin tsawa tare da fad'in, "Ki bar wannan haukan kukan ki fad'a min ina matata take." Gaba d'aya sai Muneeba ta sake rikicewa saboda yanda yake daka mata tsawar. Takalmin Sarah da ledan hannunta kawai ta mik'a masa jikinta na rawa. Hannu ya kai ya amsa yana kallon ledar da kuma takalmin. Tabbas ledar da ya bata ne kuma takalmin ma nata ne. Ransa ne ya k'ara b'aci, bai iya yi mata wani magana ba sai wayarsa da ya fiddo ya danna number d'in ya Abdullah-Hakeem. Ringing uku ya d'auka yana fad'in, "Ango kasha k'amshi." Shi kuwa _Khalil_ cewa yayi, "Yaya motocin mutanan ku uku nake so yanzu. An sace Sarah. So nake gaba d'aya daga farkon Jos road har zuwa k'arshe a zuba mutanan ku, duk wanda aka yayi kala da rashin gaskiya a kama shi." Tashi zaune ya Abdul-Hakeem yayi tare da fad'in, "An sace Saratu? Wannan ma k'arya ne. Ka kwantar da hankalinka yarinyar nan in Sha Allah baza ta kwana ba. Yanzu zan kira yaya Abdullah domin ya turo mana da sojoji, kuma zan kira abokina ACP Lawal Yakubu domin a bamu police guda talatin. Gamu nan zuwa yanzu. Koma wanene yayi wannan aikin zai san ya tab'o jinin Chief Justice Nurudden Muhammad Ibrahim." Yana gama fad'in haka ya katse wayar tare da soma kiran yaya Abdullah. Yaya Abdullah ya fisa ma d'aukar zafi don kamar zai fito ta wayar. Kuma take yayi waya bariki aka turo motar sojoji har biyar. Tun daga Katsina round about mutanan dake Jos road suke jin jiniyar y'an sanda da sojoji. Matasa gaba d'aya hankalinsu ya tashi. Mutane sai firfitowa suke daga gidajansu suna kallo, wasu kuma suna dannawa nasu gidan sakata. Y'an daba da y'an shaye-shaye kuma sai nemar mab'oya suka soma yi. Tun daga farkon Jos road y'an sanda da sojoji suka samu position suka tsaya fuska babu rahama ko kad'an har k'arshe layin. Su Hajiya Lami kuwa cewa tayi, "Yanzu haka saboda d'aurin auren da za ayi gobe ne aka turo so domin su bamu tsaro." Na'ima tace, "Babu shakka kam!" Baba dake d'aki kuwa hakanan yaji hankalinsa bai kwanta ba. Aina'u kuwa gaba d'aya ta kasa sukuni sai lek'e take yi tana kiraye-kirayen waya. Muneeba kuwa sai kuka take yi a gaban _Khalil_ tana mashi rantsuwar ba da ita aka had'a baki ba kuma wallahi bata san inda Sarah take ba, bata san ko wa ya sace ta ba. Shikuwa _Khalil_ kwakkwarar motsi ya hanata don cewa yayi bai yarda da ita ba. K'aran jiniyar motocin sojoji da y'an sandan da suka iso inda suke ne ya k'ara hargitsa mata tunani ta saki wani marayan kuka tana k'an'k'ame jikinta. "Ke!" Wani soja ya buga mata uban tsawa sai gata a zube a k'asa ta sume dai-dai lokacin da ya Abdul-Hakeem ya iso wajen. Shi da kansa ya zira hannu ta cikin motar _Khalil_ ya d'auko ruwa tare da yayyafawa Muneeba. A firgice ta farfad'o tana fad'in, "Wallahi bani bace, ban sa wanda ya sace ta ba, kuma wallahi bani na kirata a waya ba." Hannu ya Abdul-Hakeem ya saka a baki tare da fad'in, "Shssh! Kwantar da hankalinki babu abunda za ayi maki a nan wajen. Yi min bayani mai ya faru." Ajiyar zuciya Muneeba ta sauke tare da fad'in, "Sarah tu a gidan mu take kwana tun saura kwana biyar bakinta. Kuma mama ta hana mu fita kuma ta cewa _Khalil_ ya hak'ura da zuwa tad'i har sai an kawo masa ita gida sabida ana mata gyaran jiki. To kullum sai suyi ta damuna su biyu suna cewa suna kewar juna. Shine jiya muka yi waya da shi _Khalil_ akan in taimaka masa in fito masa da Sarah suga juna ko mintuna biyar ne, shine na fito da ita ba tare da sanin mama ba na kawo ta wajensa sai na koma gida domin basu waje suyi magana. To K'anwar Sarah tazo gidan mu tana neman ita Sarah har mama taji shine ta tambaye ni ina Sarah, sai nayi mata karyar tana ban d'aki shine nayi sauri na fito domin in kira ta mu koma gida. To da nazo nan d'in sai naga babu motar _Khalil_ sai nayi ta kiran number d'in Sarah amma ba'a d'agawa, daga k'arshe ma aka kashe. Shine na kira shi _Khalil_ d'in ina tambayarsa Saratu, sai ya fara min ihu wai ai nice na kira ta har ta tsora tace wata k'ila an gane bata gidan ne sai suka yi sallama ta tafi. Kuma ni wallahi, tallahi ban kira ta ba." Haushi ne ya kama _Khalil_ jin rantsuwar da tayi akan bata kira Sarah ba, bai san lokacin da ya d'aga hannu zai wanke fuskanta da mari ba, da sauri Abdul-Hakeem ya tare hannunsa tare da fad'in, "Baka da hankali ne? Ko in barka kayi binciken ne da kanka? Ashe babu amfanin kiran mu da kayi kenan?" Matsawa baya _Khalil_ yayi tare da fad'in "I'm sorry." Kallon Muneeba yaya Abdul-Hakeem d'in yayi tare da fad'in, "Ina wayarki?" Da sauri ta mik'a masa wayar hannunta na rawa shi kuma ya mik'a wani dake gefensa. Cike da ladabi ya amshi wayar sannan ya sara masa tare da koma cikin mota ya kunna computer ya soma danne-danne cikin sauri da kwarewa. Muneeba kuwa da mararta ke cike da fitsari, ihu d'aya za'a kuma buga mata ta saki fitsari. Mintuna biyar sai ga wannan da aka ba waya ya dawo tare da fad'in, "An kira number d'in sau bakwai mintuna goma sha bakwai baya amma ba'a d'aga ba kuma daga baya aka kashe wayar. Lokacin da ake kiran wayar ba'a d'aga ba, nabi diddigin layin, makwamusan suna dai-dai round about d'in stadium, kuma an kashe wayar ne a dai-dai wajen tare da jefar da waya. Don har yanzu diddigin layin na wajen. Sannan kuma an kira wayar k'arfe bakwai da mintuna arba'in da uku, sai dai har ya gama ringing ba'a d'auka ba." Da sauri _Khalil_ yace "Lokacin muna tare, kuma a wannan ne Sarah hankalinta ya tashi ta wuce gida." Abdul-Hakeem ya kalli Muneeba tare da fad'in, "Kin ce baki kira Sarah ba, kuma gashi bincike ya nuna kin kira da misalin 7:43." Kuka Munee ta saka tare da soma rantsuwa tana fad'in, "Na rantse da ubangijin da ya halicceni ban kira taba, bani na kira ta ba." "To idan baki kira taba, waye ya kira ta? Kin ba wata wayar ne a wannan lokacin?" Shuru Muneeba tayi tana tunanin wa ta ba wayar a wannan lokacin? Kallon Abdul-Hakeem tayi tare da girgiza kai tace, "Ban ba kowa wayata ba a wannan lokacin. Kuma wallahi ban kira ba." "Oga wannan yarinyar fa baza tayi magana ba har sai mun tafi da ita." Fad'in wani police. Tuni Muneeba ta soma sakin fitsarin da ya dad'e da cika mata mara tare da durk'usawa a k'asa tace, "Na rantse da girman Ubangiji da ya halicceni ban sace Saratu ba. Wallahi bani bace. Dan Allah kar ku tafi dani." Yaya Abdul-Hakeem tun kallon farko da yayi wa Muneeba ya san cewar bata da hannu a cikin sace Sarah da aka yi, sai dai tabbas duk wanda yayi hakan yana tare da ita amma ita bata san hakan ba. "Wa kika ce tazo neman Sarah har mamanki taso ta fahimci bata gidan?" Da sauri Muneeba tace, "Aina'u!" Wani harara _Khalil_ ya watsawa Muneeba tare da fad'in, "Aina'un ce za ta sace Sarah?" Girgiza kai Muneeba tayi tare da fad'in, "Ba haka nake nufi ba." yaya Abdul-Hakeem kuwa cewa yayi "Aina'u tayi amfani da wayarki ne lokacin da tazo?" Da sauri Muneeba ta girgiza kai tare da fad'in, "Bata yi ba. Cewa kawai tayi ina Sarah. Ni kuma nayi saurin janta gefe nace tayi shuru kar mama taji don ta hana mu fita ni kuma na saci hanya na kai Sarah wajen _Khalil_. Ita kuma sai ta mik'o min kayan Sarah tace in bata baza ta iya jiran Sara ta dawo ba, don itama jiranta ake yi saurayinta yazo." "Wani irin kaya ta kawo mata, kuma dama Sarah ce tace ta kawo mata kayan?" Fad'in ya Abdul-Hakeem. "Eh ita ce tace ta kawo mata doguwar rigar baccinta da kuma hula." Jinjina kai Ya Abdul-Hakeem tare da fad'in "Jeki gida, zan neme ki idan buk'atar hakan ta taso." Da sauri Muneeba ta juya har da had'awa da gudu ta bar wajen. Shi kuma _Khalil_ a fusace ya kalli ya Abdul-Hakeem tare da fad'in, "Ya ka barta ta tafi? Ita ce suspect d'in fa." Ko kallonsa ya Abdul-Hakeem bai yi ba, sai daga ma d'aga kiran da aka yi masa yayi tare da sakawa a kunne. "Ok kar ku tab'a komai gamu nan zuwa." Yana gama fad'in haka ya yanke wayar tare da kallon _Khalil_ yace, "Shiga mota ka biyo bayan mu." Shi kuma ya nufi motar da ya shigo bayan ya bawa sauran y'an sandan umarni akan kar ku yarda su bar wajen har zuwa gobe shi kuma ya shiga motar da ta kawo sa suka nufi Barnawa inda wanda ya kira yanzu ya fad'a masa. Kasancewar gudu suke yi kuma ga shi dare ne babu mototi akan titi sosai, cikin k'ank'anin lokaci suka isa. Wasu cincirundo y'an sanda ne a zagaye da wata mota k'irar golf, sai wasu matasa su shidda an fito dasu sun yi kneeling a k'asa fuskokinsu a kumbure. Abdul-Hakeem na isowa wajen ya fiddo pistol tare da kicking ya d'aura akan goshin d'aya daga cikin su, zawo ne ya soma zubowa daga jikinsa na tsoro tare da fad'in, "Kar ka kashe ni dan Allah. Wallahi ba muyi mata komai ba. Tana cikin buhu a bayan mota." Da jin haka haka ya Abdul-Hakeem nufi bayan motar bayan ya saka hand gloves sannan ya bud'e tare da warware saman buhun. Da mugun gudu _Khalil_ ya iso wajen zai kai hannu ya d'auko Sarah da bata da maraba da gawa amma ya Abdul-Hakeem ya tare sa tare da fad'in, "Wait a minute!" _Khalil_ bai saurari ya Abdul-Hakeem ba ya ciccib'o buhun ya fito dashi tare da fiddo Sarah da gaba d'aya jikinta a sake yake ya nufi motarsa da ita ya bud'e back seat da d'ayan hannunsa ya shimfid'ar da ita tare da soma ceto ranta don ya duba pulse d'inta yaga akwai rai a jikinta. Tsabar wahala kawai tasha da kuma abunda suka shak'a mata. Numfashi ya soma bata ta bakinsa yana hura mata. Sai da ta d'au tsayin lokaci kamun ta ja wani irin dogon numfashi tare da rirrik'e damatsen _Khalil_ d'in da k'arfi. Wani irin ajiyar zuciya ya saki tare da d'agota ya had'a da jikinsa ya rungume k'am-k'am. Yana jin yanda bugun zuciyarta ke tafiya da k'arfi. A can waje kuwa, wani irin mahaukacin duka sojoji hud'u suka rufe su dashi. Sai da suka karya k'afafun su da hannaye sannan suka jefa su cikin mota. Yaya Abdul-Hakeem kuma k'arisowa yayi ya kwankwasa motar _Khalil_ sai a sannan ya saki Sarah dake kuka a hankali ya fito daga motar. "Ka mayar da yarinyar gidan iyayenta. Sojoji da y'an sanda zasu cigaba da bata tsaro har sai an d'aura aure gobe an kawo ta gida tukun zasu bar layin." _Khalil_ yace, "To yaya. Amma ya akai aka gano su?" Murmushi ya Abdul-Hakeem yayi tare da fad'in, "Tun da muka gama waya da kai na kira wani daga wajen aikinmu, kwararren masanin na'ura na tura masa number d'inka. Na number d'inka yabi diddigin layin Sarah. Ko da nake wa yarinyar nan tambayoyi, wasu na can tuntuni sun bi bayansu har Allah yasa suka damk'o su. Sai dai kuma koma wanene wanda ya saka aka sace Sarah, ba k'aramin wayau gare shi ba, don bai yarda ya bar wani makama ba, ko su wanda muka kwamushe yanzu, basu san ko wanene ya basu aikin ba. Kuma da boyayyiyar number ake basu umarni. Kuma sun ce muryan namiji ne ke basu umarnin." Da mamaki _Khalil_ yace, "To wanene wannan yake son ganin baya na ta hanyar raba ni da Sarah?" Kai tsaye ya Abdul-Hakeem yace "Makiyi!" "Allah ya shiga tsakanin mu da koma wanene. Kuma in Sha Allah aure babu fashi. Gobe za'a d'aura aure." Fad'in _Khalil_. "In Sha Allah. Ma mai masu yarinya gida dare nayi." "To yaya sai na dawo gidan. Don Allah kar ka fad'awa Hajiya ka santa nan da nan hankalinta ke tashi" Sai da ya hararesa sannan yace, "To yaya _Khalil_, ai ka san dama bani da hankali." Dariya _Khalil_ yayi tare da bud'e gidan baya inda Sarah take ciki ya shiga. "Stop crying my baby. Gani a kusa dake. Bazan k'ara bari haka ya faru dake ba. I'll always protect you my wife. Kiyi hak'uri laifina ne. Da ban zo ba, hakan ba zai faru ba." Share hawaye Saratu tayi tare da fad'in, "Ko kazo, ko baka zo ba, haka sai ya faru tunda rubutaccen al'amari ne." Hannu ya kai ya share mata hawayen da suka gangaro tare da fad'in, "Gobe, by this hours, kina kwance a k'irjina, ba zan bari ko sauro ya hau kan jikinki ba bare kuma d'an Adam." Hannu sara ta saka ta rufe fuskanta tare da fad'in, "Ni dai ka bari. Mu tafi gida dare nayi." Dariya yayi tare da fita daga motar ya koma mazaunin drive ya kunna tare da barin wajen ya hau hanya. Sarah ganin basu yi hanyar gidansu Muneeba ba, sai tace, "Gidan su Muneeba zaka kai ni fa." Sai da ya juyo sannan yace, "Babu gidan wata Muneeba da zaki k'ara kwana. Gida zan kai ki. Ni ban yarda da Muneeba d'in nan ba. Ina zargin har da saka hannunta a sace kin da aka yi. Don tana ta rantsuwa wai ita bata kira ki ba lokacin da muna tare dake." Waro idanu Sarah tayi tare da fad'in, "Dan Allah kar kace haka. Wallahi Muneeba baza ta tab'a cutar dani ba. Babu hannunta wallahi." Kallon titi yayi tare da fad'in, "love, mugu bashi da kama. Ki bar wannan maganar. Gida zaki kwana." Kuka Sarah ta saka tana fad'in, "Wallahi Muneeba ba muguwa bace." Banza yayi da ita har yayi parking a k'ofar gidansu. Uban dandazon sojojin da ya ta gani a k'ofar gidansu sai da ta tsorata. Ganin da sauri sojoji kusan hud'u sun nufo su tare da bud'e gidan baya ina take, baya san lokacin da ta kwala ihu ba sai da _Khalil_ ya tsorata tare da fitowa da sauri ya ture wani soja yana fad'in, "Baby lafiya?" Da hannu tayi masa nuni da, sojan dake tsaye k'ik'am kamar an dasa shi. "Malam matsa mana. Baka ganin tsoranka take ji." Da sauri sojan ya matsa, shi kuma ga kamo hannunta ya fito da ita. Har tsakar gidansu ya raka ta dai-dai lokacin da Baba ya fito daga d'aki yana fad'in, "Wanene nan wajen?" Amma ganin _Khalil_ da Sarah tsaye sai hakan ya bashi mamaki don ga san Sarah a gidan Liman Muhammadu take kwana. "Ibrahim lafiya? Wani abun ya faru ne? Shiyasa naji jiniyan sojoji ko ta ina kenan d'azu?" Baba ya jero tambayoyi gabansa na fad'uwa. Jin muryan baba sai gaba d'aya mutanan gidan suka fito. Aina'u kuwa har da cin tuntub'e tana waro idanu ganin Sarah a tsaye. "Baba wani tsautsayine ya d'an afku, amma Alhamdulillah yanzu." Daga nan ya kwashe komai ya sanar da baban. Salati Baba da su Na'ima suka d'auka. Lami kuwa wani uwar yare mai tsawo ta dire tare da fad'in, "Yesu almasihu kana ganin komai. Mak'iya sun fara bina don sun ga y'ata zata auri babban mutun d'an gidan manyan mutane." _Khalil_ kuwa kunnansa ne suka yi masa wani duum jin Lami tace _Yesu almasihu_. Bai gama dawowa daga duniyar mamaki ba, Lami ta kuma cewa, "Ya Uba mai-iko duka, mai-yawan jinkai, mun rantse, mun bache daga tafarkokinka kaman batattun tumaki. Mun cika bin dabarun zukatanmu da muradinsu. Mun sab'a dokokinka masu-tsarki. Abin da ya wajabba garemu, mun bari: Abin da ya wajaba mu bari, shi muke yi; Babu lafiya garemu. Amma, Ya Ubangiji, ka yi mana jinkai, mu masu-sab'o abin tausai. Ya Allah ka yafi masu fad'in laifinsu, Masu tuba kwa ka amshe su: bissa alkawalin da ka furta ma yan Adam. Almasihu Isa Ubangijinmu, Uba kuma mai-yawan jinkai, ka sa duk mai neman mu da sharri ya koma masa, kada kayi duba da laifinmu a gare ka. Ya Almasihu mai-tsarki ka amsa addu'armu Amin." Ba _Khalil_ kad'ai hatta su Nuratu sun firgita da jin maganganun mahaifiyarsu. Marfu'a kuwa kallon Lami tayi tare da fad'in, "Lami dama ki koma addinin kiristancinki? Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Gaskiya Lami baki kyauta ba. Shikenan baki da rabo a lahira." Aina'u tayi caraf tace, "Tunda kece da aljannar sai ki hanata ai. Ai gwara ita an san cewa kirista ce, ke kuma fa? Kina amsa sunan musulma amma ban tab'a ganin kin aje goshinki a k'asa ba. To Menene marabarku kenan? Kowa dai yasan bambamcin musulmi da kirista shine Sallah." A fusace Marfu'a tace, "Dan uwarki dake nake magana? Alhamdulillah tunda da na furta kalma La'ilaha illallah Muhammadur Rasulillah. Kuma dai ai ance duk wanda ya furta Kalmar bai dauwama a wuta." _Khalil_ gaba d'aya ji yayi kamar ana zare nasa wani abu a jiki, yayi dana sanin shigowa cikin gidan. Sai yaji dama a k'ofar gida ya tsaya har Sarah ta shige ciki. "Ke, ba kowa bane yake da rabon shiga addinin kiristancin. Addini na shine addinin gaskiya. Kuma ni tun farko ban tab'a yin wani addini bayan addinina ba. Addinin ku ya cika tsauri da yawa, mutum yayi da dungure sau biyar a rana, wata d'aya ana azumi, ba'a sata, ba'a k'arya ba'a saduwa, ba'a shan burkutu. Abubuwa da yawa addininku sun hana. Addininku addinin takura ne." Sai a lokacin Baba ya bud'e baki tare da fad'in, "Ke Lami! Ki kiyaye harshenki. Addinin Musulmi addinine na gaskiya kuma addini ne mai bawa kowa y'anci. Duk abunda kika lissafo addinin da kike ik'irararin shi kike yi, shima yayi hani akai. Babu wani Bible d'in da ya halasta duk abunda kika lissafo. Idan kinga dama ki zama mara addini gaba d'aya, wannan ruwanki ne. A gaban sirikinki kike wad'annan maganganun sabida baki da hankali da tunani." Da sauri _Khalil_ yace "Baba sai da safe, sai da safe Sarah." Yana fad'in haka ya juya. Aina'u kuwa wani farin ciki taji ya ziyarci zuciyarta ganin reaction d'in _Khalil_. Tana ji a jikinta auren Sarah dashi ba zai yuwu ba gobe. Baba juyawa yayi tare da shiga d'aki Sarah ta bishi a baya. Su Nuratu ma suka shige d'aki. Aina'u kuwa, hanyar toilet ta nufa. Tana shiga ta rufo k'ofar tare da kiran wata number bayan ta shiga magic voice ta mayar dashi na tsofaffi sannan ta b'oye number. Ringing uku aka d'aga wayar tare da fad'in, "Zance ya b'aci, su Arowa suna state CID yanzu haka. Sai dai sunana bai fito ba, don kamar yanda ake b'oye number ana canza muryoyi ana kirana, nima haka nake musu. Ni dai koma wanene nake magana dashi yanzu haka, bamu da matsala domin babu wanda ya san mu." Aina'u wani murmushin jin dad'i tayi duk da tasan ko ta fashe babu wanda zai kamata don bata bada k'ofar da za'a ganeta ba. "Yayi kyau! Zan kira ka idan wani aikin ya kuma b'ullowa." Tana gama fad'in haka ta yanke kiran ta fito daga bayin ta koma d'aki." "Baba wallahi ban san ko su wanene suka min haka ba. Amma ga dukkan alamu anso ayi garkuwa dani domin kud'i. Tunda kaga da zan ba'a yi hakan ba sai da aure na ya kusa kuma da d'an Chief Justice Nurudden Muhammad." Ajiyar zuciya Baba yayi tare da fad'in, "Ubangiji Allah ya kare ki daga sharrin mutum da aljan. Wannan aure kuma, idan ma anyi hakan ne domin a fasa,in sha Allah an riga an d'aura a sama, shaidar duniya kawai ake jira. Tashi kije ki kwanta, in Sha Allah da safe zan je can gidan liman Muhammadu inyi masa bayani komai. Ni kai na ban ji a jikina Muneeba zata had'a baki da wasu domin a sace ki. Amma zan je gidan gobe da safe." "To Baba Allah ya kai mu." Sarah ta fad'i tare da ficewa daga d'akin ta koma nasu. "Sarah kin tab'a karanta littafin hausa mai suna _Ayi dai mu gani_?" Fad'in Aina'u tana mai danna wayarta. Kallon Sarah tayi tare da fad'in, "Kin fara karatun novels ne na hausa?" Sarah ta fad'i tana mai kallonta. Ba tare da Aina'u ta kalleta ba tace, "Eh, yau kwana uku da na fara da wani littafi mai suna _Iska na wahalar da mai kayan kara_, yanzu kuma _Ayi dai mu gani_ nake karantawa." Girgiza kai Sarah tayi tare da fad'in, "Gaskiya ban karanta ba. Ban ga kinyi lalle ba, kuma har nan na turo mai lalli d'azu da safe. Su Na'ima duk anyi masu ja da b'aki." Tab'e baki Aina'u tayi tare da fad'in, "Ni kinsan lalli bai dame ni ba. Kuma da safe bani nan naje kitso. Za kuyi wani program ne?" Zama Sarah tayi a bak'in gadon tare da nannad'o gashin ganta ta tura cikin hula ta k'eya tare da jawo hulan har zuwa goshinta saboda kar gyaran kan da akai mata ya lalace. Tace, "Eh, naga duk su Na'ima ma sunyi kitson ai. Ni ko da da nake saka attachment, ba zan iya yin wannan uban k'ananan kitson ba. Na'ima muga naki, kamar yafi na Aina'u k'anana ko?" Sarah ta fad'i maganar tana kallon kan Na'ima wacce taja hulan kanta baya. "Wai! Gaskiya kitson yayi k'ana. Sauk'in ta ma a can inda kukai kitson ake tsefe maku." Nuratu tace, "Ni ko kinga nawa bai kai nasu k'anana ba. Ghana weaving akai min manya." Ta fad'i maganar tana mai jan hular kanta. "Ni da Hassana fixing kawai akai mata. Don wallahi naji bazan iya zaman kitson ba. Basir!" Fad'in Marfu'a tana mai zame Fadwa da ta gama shayar da ita daga jikinta ta kwantar. "Amma dai ba anan zata kwana ba ko? Don na tsani kukan daren nan da take yi. Duk ta hana mutum bacci." fad'in Aina'u. "To nan zata kwana. Ni ban san wani uban gulmar ce ta dawo dake kwana anan d'akin ba, ai da a d'akin Lami kike kwana." Cike da rashin kunya Aina'u tace, "To nan d'in naga damar dawowa da kwana. Ai gidan ubana ne." Ficewa daga d'akin Sarah tayi ganin zasu fara raba halin nasu da suka saba. D'akin Baba tayi sallama ta shiga. Zaune ta same shi a kan gado yana kallon Sunna Tv. "Baba dan Allah wayarka zaka ara min." Ba tare da yace komai ba ya d'auko wayar a gefensa ya mik'a mata ita kuma ta amsa tare da ficewa. Number d'in _Khalil_ tayi dialing, ringing biyu yayi sai yayi rejecting tare da biyo kiran. Sarah na d'agawa yace, "Assalamu alaikum Baba." Sarah sai ta canza murya tare da fad'in, "Wa'alaikassalam d'ana." A tare suka saki dariya, _Khalil_ yace, "Ke nine d'an naki? Za kiyi bayani gobe a irin wannan lokacin." Hararar wayar Sarah tayi tare da fad'in, "Bayanin mai zan yi? Ni babu wani bayani da zan yi." Dariya _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Kuma kin san na mance y'an iskan da suka d'auke min ke sun yar da wayarki, wallahi na kira yafi sau shurin masak'i, dole ma gobe da sassafe in kawo maki waya. Ba zan juri rashin jin muryanki ba." "To bayan gobe zamu kasance tare har abada." Sarah ta fad'i a kunyace. "Na'am, maimaita dan Allah love." K'it ta kashe wayar tare da mayarwa Baba wayarsa. Daga can kuwa _Khalil_ kamar ya fasa ihu, yana tsoron kira yaji wayar a hannun Baba. Washa gari da sassafe kamar yanda _Khalil_ ya fad'i, sai gashi da sabuwar waya k'irar LG mai tsananin kyau da tsada, wani tsohon MTN sim d'insa ya saka mata a ciki ya kawo mata. Na'ima ta fito zata shago ta gansu a tsaye suna magana. Wani irin kyau suka mata, sai taga kamar anyi su don juna ne don ba k'aramin dacewa suka yi ba. "K'anina ayi hak'uri haka, anjima kad'an zamu kawo maka ita." Murmushi kawai _Khalil_ yayi ita kuma ta wuce. Dai-dai nan Muneeba ta iso wajen, tana ganin _Khalil_ ta juya da sauri. Shima _Khalil_ da sauri yabi bayanta yana kiran sunanta don jiyan sunyi magana sosai da ya Abdul-Hakeem ya fahimtar dashi Muneeba bata da hannu a ciki. "K'awarmu dan Allah kiyi hak'uri da abunda ya faru jiya. Tashin hankali ne ta saka nayi abunda nayi. Koma wanene a matsayina abunda nayi shi zai yi. Kiyi hak'uri kinga ma na kama kunnena. Kar ki manta ke kika ce min in kula da k'awarki sosai kada tayi kuka. To hud'ubarne ya shiga kunnena." Kuka Munee ta fashe dashi tare da fad'in, "Naji tsoro jiya, banyi bacci ba. Mama kwana tayi tana mun fad'a. Sai da baban Sarah yazo gidan mu yayi mana bayanin anga Sarah sannan hankalinmu ya kwanta. Wallahi ko a cikin mafarkina bai tab'a zuwarmin in cutar da Saratu ba." "Naji na yarda dake Muniba. Dan Allah kiyi hak'uri." Fad'in _Khalil_. Sai da ta murgud'a baki sannan tace, "Na hak'ura dan ba halinka ba." Sai ta juya ta kalli Sarah data k'ariso ta rungumeta tare da fad'in, "Alhamdulillah k'awata. Duk wanda yayi maki wannan abun Allah ya tona asirinsa." Da Ameen Sarah ta amsa tare da jan hannunta bayan ta d'agawa _Khalil_ hannu. Baki _Khalil_ ya bud'e tare da fad'in, "Har munyi sallama." Muneeba tace, "Anjima zamu kawo maka ita sai kaga dama ka barta tazo wajen mu." _Khalil_ kuwa cikin zuciyarsa cewa yayi, "Kamar kuwa kin sani. Don ina raba Sarah da wannan gidan, ko zata zo to tabbas ina jiranta a waje, tana gama gaishe da Baba zata fito mu wuce." Kan kace me, gaba d'aya gidan su Sarah ya cika da mutane har da y'an unguwa da basu tab'a shigowa ba. Don Na'ima gida-gida tabi ta kai masu chewing gum. Bamu abunda ke tashi sai k'amshin soye-soyen nama sa, rago da kaji. Don shanu k'osassu biyu aka yanka, raguna hud'u kaji d'ari da hamsin. Y'an matan zumunta kuwa sun fi hamsin sunyi ankon wani koriyar atamfa sai hada-hada suke yi baki na motsi. Sarah kuwa komawa gidansu Munee tayi don acan suke sitting. Mai make-up tazo ta tsan-tsara mata kamar ka sace ka gudu. K'arfe d'aya da mintuna sha biyu wasu uban jiniya mai tafe da convoy na ya Abdullah suka shigo layin kasancewar k'arfe d'aya da rabi za'a d'aura auren anan masallacin layinsu. Sai ga tawagar manya-manyan mutane da abokan mahaifinsu. Jos road kamar zata tsage sabida mutane. Muneeba hannun Sarah ta kama suka koma can d'akin Baba mahaifin Muneeban sabida kiran wayarta da _Khalil_ d'in yake ta yi don wayar Sarah na hannunta. Kuma nan gidan ma a cike yake da k'awayensu na islamiya da poly. Don duk sai da Na'ima ta gayyace su. Bayan ta bata wayar ta fita. Sarah na picking ta jiyo zazzak'ar muryan _Khalil_ na mata wak'a, If you make me clean I will be clean. If you make me whole I will be whole. If you make me yours I will be yours And I won't run anymore. If I seek you, will I find you there. If I call your name will you still hear Is it too late or can I start again Can I begin again Oh. Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Don't ever let me go Can you drown it in the deepest sea. Can you cast it far as west from east Can you raise me up to live again So I can live again Oh... Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Don't ever let me go I'm surrendering my will You are crumbling all the walls I've built My defence is coming down Down I can't deny you I am broken open wide Now you can come inside My defences have come down Down I can't deny you I'm surrendering my will You are crumbling all the walls I've built My defence is coming down Down I can't deny you I am broken open wide Now you can come inside My defences have come down Down I can't deny you Oh... Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Oh... Don't ever let me go Don't ever let me go Don't ever let me go Don't ever let me go. "I will never let you go. Never, ever!" Fad'in Sarah. "And I'll always be there for you my love. Sai mun had'u anjima." Yana gama fad'in haka ya katse wayar. Aina'u na tsaye a tsakar gida abun duniya duk ya isheta ta jiyo shalar da ya tsayar da bugun numfashin ta zube a k'asa sume. "An d'aura auren _Ibrahim Khalil Muhammad Nurudden_ da amaryarsa _Saratu Nuhu_ akan sadaki naira na gugan nera har dubu d'ari biyar, lakadan ba ajalan ba." _KANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 THROUGH THIS ACCOUNT NUMBER, 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH 08128755583_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *MATAR SAYYADEE*🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *19* Da gudu mutane suka yo kanta suna mata firfita. Lami kuwa kuka ta fashe dashi tare da, "Mun dawo gareka Yesu, munyi tuba mun nemi yafiyarka. Masu bin mu da sharri ka jefesu da mutu. Almasihu kayi tsinuwa mai tsayi a garesu." Aunty Rose Merry tace, "Elizabeth me ke faruwa? Mai ya sami Lili (Aina'u)." Ita haka take kiran Aina'u. Lami ta fyace majina tare da fad'in, "Rose, don anga yarana suna da farin jini kamar ni dai, shine ake binsu da sharri, jiya ma haka aka sace Sarah sai can dare aka ganta, yau kuma Aina'u. Kwana biyun nan haka take suma. Idan na tambayeta ko wani waje na mata ciwo ne, sai tace min basir da zazzab'i ke damunta." Wata mak'ociyar Lami tayi wufff tace, "Aikuwa Lami ki tashi tsaye, don basir mummunar ciwo ne don har hauka yana sakawa." Hannu biyu Lami ta d'aga ta kyasta yatsunta tare da fad'in, "Yesu almasihu mai tsarki ba zai tab'a bari y'ata tayi hauka ba. Over my dead body!" Dai-dai nan Aina'u ta farfad'o tana mai fashewa da kuka tare da tambayar, "An d'aura da gaske?" Y'an biki sai aka koma kallon juna. Aunty Rose Merry tace, "Lili mai aka d'aura?" Jin katob'arar da tayi sai tayi tsit ba tare da ta cewa aunty Rose d'in komai ba. D'aga ta Lami tayi tare da fad'in, "Basir d'in ne Aina'u?" Kai kawai Aina'u ta d'aga mata tare da nufa d'akinsu domin canza kaya don ruwar da aka zubar a wajen na girki ya b'ata mata jiki. Can gidan su Muneeba kuwa, a kunna Sarah aka d'aura auren don ana shirye-shiryen fara siga ya kirata a waya tana sauraran komai tana hawayen farin ciki. Ana fad'in salati goma ga annabi ta zube a k'asa tayi sujjada. Ta jima bata d'ago tana tsiyayar da hawayen farin ciki kasancewa mata aure da wanda take so. Sai da Munee dake kusa da ita ta d'ago ta tukun. Sai ta fashe da kuma tare da rungume Muneeba tana fad'in, "Alhamdulillah!" Gaba d'aya d'akin sai su hau fad'in *_بارَكَ اللَّهُ لَكَ، وَبَارَكَ عَلَيْكَ، وَجَمَعَ بَيْنَكُمَا فِي خَيْرٍ._* *_Barakal-lahu lak, wabaraka ‘alayk, wajama’a baynakuma fee khayr._* Ma'ana, _Allah Ya sanya albarka a gareki, yayi maki albarka kuma ya hada tsakaninku da alheri._ A tare gaba d'aya suka amsa da ameen. Ya Abdullah ba k'aramin b'arin kud'i yayi, don duk wanda ya samu halartar d'aurin auren nan ya samu kyautar k'atuwar jaka mai d'auke da kwalbar turare mai tsada wanda kud'insa ya kai 75k da agogo da kuma take away mai d'auke da lafiyayyar friedrice with chicken da kwalin exotic da ruwan gora da kuma kyautar kud'i har dubu biyar. Ko ina labarin d'aurin auren ake yi. Layin kuwa damk'an kamar ana d'aurin auren shugaban k'asa ko kuma y'ar sarki. Don ma akwai uban sojoji da y'an sanda da aka zuba sabida tsaro. Can cikin gidan su Muneeba kuwa, nan naga y'an gayyar sod'i, su Hajiya akarammiya Queen Zarah sai zazzare idanu ake yi ana yagar tsokar kaza, bayanta kuwa gaba d'aya y'an comments section ko wacce da plates d'inta mai d'auke da uban abinci da kaji ga kuma k'atuwar jaka rataye a hammata wanda za ayi guzuri.😜 K'arfe bakwai dai-dai sai ga wasu had'ad'd'un mota sun shigo layin na d'aukar amarya. Wata arniyar mota *_Czinger 21clC_* wacce kyauta ce ga ango zuwa ga amarya ita ce a tsakiyar convoy d'in motocin, kuma a itan ne za'a saka amarya. Y'an comments section sai tureniyar shiga mota ake yi. Can na hango Oum Muslim dake fama da laulayi suna y'ar matsatsi ita da Mrs dimples. Su takwas suka gwamutsu a bayan motar, Rahamanatou kerere na hangota a saman cinyar Hadiza Mbello. Mama mahaifiyar Muneeba ta kama hannun Sarah wacce ke rizgar kuka har gaban Baba ta durk'usar da ita sannan ta fita daga d'akin. Baba ma hawayen yake yi, don duk kaf Y'ay'ansa babu kamar Sarah. "Saratu! Ni dai alfarmar da nake nema a wajenki shine, ki tausaya min ki tausayawa kanki ki natsu a gidan mijinki. Yi, nayi, bari na bari. Dan girman Allah ko da wasa kada ki yarda ki b'ata masa rai, kar ki cutar dashi kuma kar a had'a baki a cutar dashi, ki rik'e sirrinki, duk rintsi kar ki yarda ki rik'a yad'a tsakaninki da mijinki. Ki koyi tauna magana kamun ki firtawa mijinki, ko kiyaye cikinsa, sannan ki kar ki yarda ki nuna farin ciki yayin da yake cikin bak'in ciki, haka kar kiyi b'akin ciki yayin da yake cikin farin ciki. Kar ki yarda ki soma kai k'ararsa wajen mahaifiyarsa idan ba abun bane da ya zama dole iyaye suji, yawan kai k'ara na sa duk yanda mutum yake jinki a ransa lokaci guda ko gunduresa tare da fita ransa. Saratu ina baki shawarar nan ne cike da umarni a matsayina na mahaifinki. Idan har kika rik'e wannan abubuwan da ba fad'a maki, zaki ci ribar zaman aure in Sha Allah. Allah yayi maki albarka ya baku zaman lafiya da zuri'a d'ayyiba." Yana kawowa nan Sarah ta fashe da wani irin kuka tare da rungume Baba k'ank'am tana fad'in, "Ka yafe min duk wani laifin da na tab'a yi maka wanda na sani da wanda ban sani ba. In Sha Allah nasiharka babu wacce zata bar kunne, ruhina har zuwa gangan jikina. Baba ka yafe min." Hawaye Baba yake yi yana fad'in, "Baki min komai ba sai biyayya Saratu, na yafe maki duniya da lahira. Allah ya maki albarka. Kuzo ku tafi da ita gidan mijinta." Baba ya k'arisa tare da d'aga murya don su Maman Muneeba suji. Dakyar maman Muneeba suka janyeta zuwa d'akin Lami, "To, Lami ga y'arki nan zata wuce gida miji. Kiyi mata nasihar zaman aure." Gaba d'aya k'awayen Lami y'an Zumunta suka had'a baki wajen fad'in, "Yesu almasihu ya tsareki a gidan mijinki, ya kare ki daga idanun mak'iya da munafukai. Yesu ya kawo zuri'a mai yawa da albarka." Lami kuwa cewa tayi, "To Sarah, ni dai abunda zan fad'a maki shine kar ki dai manta duk rintsi nice na kawo ki duniya, idan kika samu hutu da abun arziki kika kyale ni, daga nan zanyi rok'o Yesu ya tsinewa zaman aurenki. To, ni dai babu ruwana." Da sauri maman Muneeba tace, "Haba Lami ke kuwa, ke da zaki saka albarka sai ko b'ige da wannan irin maganganu haka. Bai dace ba." Mik'ewa Lami tayi tare da fad'in, "Naji k'arar bus d'in da nayi maku haya ta iso. Ku firfito kuje kada motoci d'aukar amarya su tafi, ni bazan samu zuwa ba sabida har yanzu Aina'u na kwance babu lafiya." A cikin zuciya maman Muneeba tace, "To ai mu Alhamdulillah za muce da wannan rashin lafiya, don da kije ki bar abun kunya gwara kinyi zamanki. Dama kuma mai zai kai uwar amarya kai amarya." Amma a zahiri sai d'ago Sarah tayi tare da fad'in, "Tashi muje Allah zai albarkaci aurenki in Sha Allah." Sai da ta saka ta cikin motar sannan ta shiga, mutane biyu daga cikin mak'ota suma suka shiga tare da rufe motar sai da motocin suka yi gaba kamun sauran tawagar y'an sanda da sojoji suka bisu a baya har gidansu _Khalil_. Matan zumunta sun buga uban layi biyu a k'ofar gate, sanye suke da koriyar atamfa da farar less kan nan yasha d'aurin gwargwaro orange mai ratsin green hannunsu sanye da farin safar hannu. Sai wak'a suke yi suna layi kamar zasu fad'i sai kuma su zabura su saki wani irin ihu suna fad'in, "praise the Lord!" Sai sauran suce, "Halleluyah!" Mai gadi kuwa k'in bud'e masa gate yayi sai da K'anwar Hajiya wacce aka je d'auko amarya tare da ita tayi masa magana sannan ya bud'e suka shiga da ihu suna fad'in, "Yesu almasihu mai girma mun gode maka da ka kawo yarinyarmu cikin wannan gida mai girma da kyau." Gaba d'aya y'an biki dangin hajiya da na mahaifin _Khalil_ suka fito suna kallon abun mamaki. Motar amarya kuwa har k'ofar d'akinta ya ajiye ta. Maman Muneeba ta kama hannunta har k'ofar d'akin sannan tace, "Saratu yi Bismillah ki shiga da k'afar dama." Sarah tayi kamar yanda mama ta umarceta. Gaba d'aya kusan zuciyoyinsu tsayawa yayi da bugawa lokacin da suka yi arba da had'ad'd'en parlourn Sarah wanda yaji Turkish furniture masu kyau da tsada. Curtains da lallausar center carpet d'in d'akin kawai abun kallo ne. Tv d'inta irin curve d'in nan rafgege dashi. Tsaruwar d'akin baki ba zai iya misaltawa ba. Y'an matan zumunta da suka shigo, wani irin gud'a suka saki tare da soma wak'a. Sune har d'ayan parlourn da yake k'asa kasanslcewar parlour biyu ne a k'asa. Basu ga tsan-tsan kyau da tsaruwa ba sai da suka haura sama. Daga parlour har zuwa bedrooms abun kallo ne. Su Na'ima kuwa ko wacce sai da ta d'au video a waya. Bayan an gama kallon d'aki har kitchen da aka loda uban kayan abinci a store, don babu abunda _Khalil_ bai zuba ba har da kaji da naman rago a deep freezer. Daga nan suka d'auki Sarah suka nufi cikin gida wajen Hajiyan _Khalil_ don mik'a ta amana, sai dai nan suka bar matan zumunta a parlourn Sarah gudun kar kuje suyi abun kunya. Hannu bibbiyu hajiya da y'an uwanta suka amshe su. Don lokaci da suka iso gidan tare da tawagar y'an matan zumunta, dangin hajiya suka yi gangami domin isar da gulma, tuni Hajiya tayiwa tufkar hanci kuma tace bata son tsegumi da tashin hankali. Sai kowa ya gumtse guntun gulmarsa yayi shuru. *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262*[10/1, 12:16 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *20* Sai da suka je gaban Hajiya sannan suka durƙusar da Sarah. Da sauri Hajiya ta taro ta tare da faɗin, 'Ɗiyata dawo nan kusa dani ki zauna, kar ki zauna a ƙasa." Faɗin Hajiya bayan ta zaunar da Sarah kusa da ita wacce fuskarta ke lulluɓe da gyale. "To Hajiya ga ƴarki nan Sarah, don Allah a saka mata idanu, idan tayi ba dai-dai ba a kwaɓa mata. A riƙa nuna mata abunda ya kamata, sannan dan Allah a riƙa hakuri da ita yarinya ce. Ki ɗauke ta tamkar _Khalil_, yanda zaki hukuntasa idan yayi laifi, haka itama zaki hukuntata. Basu da bambamci a wajenki." Faɗin maman Muneeba. Murmushi Hajiya tayi tare da kamo kafaɗun Sarah tare da faɗin, "Sarah ɗiyata ce ba suruka ba. Ba kuda damuwa domin gida kuka kawota. Allah ubangiji ya basu zaman lafiya mai ɗorewa da zuri'a ɗayyiba." Da ameen duka ƴan ɗakin suka amsa. "Laure, fito min da akwatin nan." Hajiya ta faɗi da ƙarfi saboda Lauren ba a kusa da ita take ba. Laure ta fito tare da akwatin da hajiyan ta umurceta da ta fito dashi tana ja da kyar don danƙam yake da kaya a ciki. "Ga kyauta nan zuwa ga ɗiyata. Allah ya bada zaman lafiya mai amfani." Godiya su maman Muneeba suke tayi sannan suka ɗauki akwatin, har ƙofa Hajiya ta rako Sarah tana ta saka mata albarka. Bayan sun dawo ɗakin Sarah sai suka buɗe akwatin tare da fiddo kayan ciki. Turaruka ne irin na gida su humra masu ƙamshi da su turaren wuta na rushi na jiki, kaya, ɗaki da kuma tsuguno. Sai abayoyi da lafayas masu yawa da kuma tsana. Bayan kowa ya gama gani sai suka mayar da komai suka rufe suka ɗaura mata a saman wardrobe. A parlour kuwa, matan zumunta kowacce ta fiddo da hoda da jan baki tana ƙara gyara fuskarta saboda samun labarin za'a tafi dinner yanzu. Su maman Muneeba kuwa, faɗa suka ƙara yiwa Sarah sosai kamun suka yi mata sallama. Kuka Sarah ta fashe dashi ganin zasu tafi su barta har da Muneeba don mahaifinta yace ƙafarta ƙafar mahaifiyarta. Munee rungume Sarah tayi suna kukan tare. Dakyar mama ta raba su ganin zasu ɓata masu lokaci kuma ana jiransu a waje domin a maida su gida. Bayan sun tafi sai yarage daga ita sai matan zumunta da kuma ƴan uwanta dake ta shirye-shiryen zuwa party. Kowacce sai ƙure a daka take yi. Wata budurwa ce ta shigo hannunta riƙe da wani ƙatoton kit na makeup. "Dan Allah ina amaryar da za'a shirya? Lokaci na ƙurewa." Da hannu Na'ima tayi mata nuni da hanyar ɗakin da Sarah take ciki tare da cigaba da shafa powder ɗinta. Budurwar ta haura sama tare da shiga ɗakin da Sarah take ciki, waya ta sameta tana yi. Sai da ta gama wayar da take yi da _Khalil_ sannan ta juyo ta kalli budurwar. Murmushi budurwar tayi tare da faɗin, "Angonki ne ya turo ni inyi maki kwalliyar zuwa dinner." Murmushi Sarah ta mayar mata tare da faɗin, "Ok, amma dan Allah kiyi min haƙuri inyi sallar isha'i." Zama makeup artist ɗin tayi tare da faɗin, "Babu matsala. Yi sallar ki." Ko da Sarah ta idar da Sallah, gaba ɗaya an gama kwashe su Na'ima da ƴan matan zumunta zuwa wajen dinner. Sai da mekeup artist ɗinnan ta fiddo mata da wata lafiyayyiyar gown a cikin wani dogon kwali kalar milk ta saka sannan ta soma yi mata kwalliya. Ba ƙaramin kyau tayi ba. Rigar kamar don ita aka yi sa saboda yanda ya amshi jikinta. Ita kanta makeup artist ɗin bata taɓa yiwa amarya kwalliyar da ya ruɗa ta ba irin Sarah. Ba ƙaramin kyau tayi ba. Tuni tayi mata mahaukatan pictures ta watsa a whatsapp status, Facebook da instagram sannan ta rubuta _The beautiful bride of Ibrahim Khalilullah Nurudden Muhammad son of late ChiefJustice Nurudden Muhammad)_ a ƙasan hoton. Sai ga uban likes. Comment kuwa babu adadi, na masu addu'a da kuma masu mamakin auren don ba'a yaɗa a social media ba. Ƙarfe takwas da arba'in wata auntyn _Khalil_ ta shigo tare da kamo hannun Sarah suka fita daga dakin tare da rufowa. Har gaban lafiyayyiyar sabuwar motar _Khalil_ ta kaita tare da buɗe gidan baya ta saka ta a ciki sannan ta rufo ƙofar. Lumshe idanu tayi tare da shaƙo kamshin turaren _Imperial Majesty_. A hankali ta buɗe idanunta jin hannun _Khalil_ a cikin nata hannun. Kai hannun saitin bakinsa yayi tare da kissing sannan yace, "You look very beautiful wifey." Ɗagowa tayi suka haɗa idanun, kasa ƙifta idanun tayi saboda wani irin kyau da yayi, shi sanye yake cikin ɗanyan shadda golden colour wanda ɗinkin ya amshi kayan da kuma jikinsa. Hura mata iskar bakinsa yayi a fuska tare da ɗage gira yace, "Wannan kallo haka, cinyeni za kiyi?" Kau da kai tayi tare da faɗin, "Kayi kyau da yawa ne ai." Juyowa yayi yana facing ɗinta sosai tare da faɗin, "Juyo ki kalli mijinki da kyau, naki ne ke ɗaya. Ni wallahi duk kishi ya kama ni kamar mu juya kawai mu koma gida abun mu. Kyawun da kika yi is over love." Ya faɗi hakan yana mai jawota jikinsa gaba ɗaya. Da sauri ta tashi a kan jikin nasa tana mai nuna masa driver da idanunta. Ɗage gira yayi tare da faɗin, "Kar ki damu makaho ne baya ganin mutanen dake cikin motarsa musamman da daddare. Bar ni naji ɗumin matata." Ya faɗi yana mai ƙara jawota jikinsa. "Ni dai kwalliyata wallahi!" Ta faɗi cike da shagwaɓa. "Ai ni akai wa. Barni na more abuna." Ya faɗi hakan ba tare da ya sake ta ba har suka cikin wajen da ake taron. Sai da aka shiga aka sanar da zuwansu sannan su Na'ima suka fito tare da abokan _Khalil_ ɗin waɗanda za suyi masu jagora zuwa ciki. Su Na'ima sune a gaba sai ango da amarya a tsakiya, abokan ango kuma a baya. Sai da suka zo kofar shiga hall ɗin sai suka tsaya, MC kuma ya saki wakar _Laye_ ta kiss Daniel. Gaba ɗaya hall ɗin ya kaure da tafi saboda shigowar ango da amarya. Sai da suka ɗan taka kamun suka isa wajen da aka tanada domin su suka zauna. Mc ya kira sunan Hajiya umaima k'anwar mahaifin _Khalil_ tazo ta buɗe taro da addu'a tare da yiwa ango da amarya fatan alkhairi. Tun tana yi aunty Rose Merry taje ta yiwa Mc raɗa a kunne. Aunty Umaima na komawa wajen zamanta Mc ya kira aunty Rose Merry daga da dangin amarya domin itama tayi jawabi tare da sakawa ango da amarya albarka. Da taku ɗai-ɗai aunty Rose Merry ta fito tare da karɓan mic ɗin tace, "Da farko dai ina godiya ga Yesu Almasihu da ya nuna mana wannan rana na auren ƴata Sera (Sarah). Praise the Lord!" Ta faɗi da ƙarfi yayin da matan zumunta suka haɗa baki da ƙarfi suka bata amsa da "Hallelujah!" Gaba ɗaya hall ɗin ya ɗau wani irin shuru kowa da abunda yake faɗi a zuciya. Aunty Rose Merry ta cigaba da faɗin, "Na dawo gareka ɗana. Wannan yarinya dake kusa da kai, ka riƙe ta gaskiya bisa amana. Idan kayi haka, Allah zai yi maka albarka. Praise the Lord!" Ta ƙarisa maganar da ƙarfi ƴan matan zumunta suka amsa mata da "Hallelujah!" Ta cigaba, "Ka bata duk hakkinta da yake kanka. Kar ka barta da yunwan ciki. Sannan kar ka riƙa yin nisa da ita, ka kasance kullum a tare da ita kusa-kusa sosai. Kar ka barta da yunwarka, ka bata kanka da lokacin ka duk lokacin da ta buƙata. Kar ka bari ta kalli waninka da sha'awa, ka kasance jarumi sosai." Tana kawowa nan gaba ɗaya hall ɗin aka fashe da dariya don kowa ya fahimci mai take nufi. Ita kuwa sai cigaba da magana tayi ko a jikinta, "Ke kuma amarya na dawo kanki, kar ki kuskura ki bari mijinki yaji sha'awar wata mace, ki bashi hakkinsa gaba ɗaya, kiyi masa girki mai daɗi, ki bashi a baki, idan yazo saduwa dake kar kiyi masa yanga. Duk position da ya saki, ki tsaya cak, idan kuma kince za kiyi yanga, kina kallo karuwai za su tafi da kurwar mijinki. A toh!" Nan ma Wani dariyar aka kuma fashewa dashi, Sarah kuwa kunya kamar zata kashe ta. _Khalil_ kuwa murmushi kawai yayi tare da girgiza kai. Aunty Rose Merry kai mic dai-dai bakinta tayi kamar zata cinye tare da soma waƙa, " _Ango idan kayi da kyau, akwai sakamo, kar kayi mugunta zaka girbe watarana!" Ƴan matan zumunta an kunnosu, gaba ɗaya suka fito suka hau amshi da, " _Amarya idan kinyi da kyau akwai sakamakon, kar kiyi mugunta zaki girbe watarana_" Mc yace, "Mun gode, mun gode, mun gode. Dan Allah jama'a a tafa masu" Gaba ɗaya wajen ya kaure da tafi shi kuma ya karɓi Mic ɗin hannun aunty Rose Merry suka koma mazauninsu. Daga nan aka shiga shagulgulan biki. Mc ya kira ango da amarya domin su ɗan taka tare da nishaɗantar da mutane. Hannun Sarah cikin na _Khalil_ suka taso daga wajen zaman su tare da tsayuwa a filin. A kunna _Khalil_ yayiwa Mc magana, shi kuma MC yace, "To jama'a, magana ake yi na ango da amarya. Ango yace a saka masa wak'ar soyayya mai daɗi don tare zasu waƙe kansu shi da amaryarsa. Dj idan ka shirya." Ya faɗi hakan tare da miƙawa Sarah mic kasancewar ya riga ya bawa _Khalil_ nashi. Ɗagewa Sarah gira _Khalil_ yayi tare da faɗin, "Wannan gasa ce tsakanina dake. Kuma ni zan ci" Itama ɗage masa girar tayi tare da faɗin, "Da gaske kai zaka ci?" Gaba ɗaya a idanun mutane suka yi komai, sai hall ɗin ya kaure da tafi har da masu fito da cike da wani irin salo mai tafe da ƙauna sukai maganar. Dai-dai nan DJ ya saki waƙar auta MGboy ina ji dake. *_Ina ji da ke ni ba zan barki ba, ni kullum a fatana mu kai har ga ran aure* *_Ina ji da kai nima bazan barka ba, kullum tunanina yaushe ne za muyo aure_* *_Idan lokaci yayi ni naki ne, idan lokaci yayi ni mijin ki ne. Idan lokaci yayiiiii! Idan rabbi yaso na aureki ƴan mata_* *_Ba mai kai ni jin daɗi idan munyi aure, cikin zuciyata kai kaɗai ne ka tare. Taho sahibinaaaa! Idan so ya kai so dole ne ai batun aure_* *_Kin game ko ina dukka jiki kin mamaye, ke kika ban ƙauna wanda kuɗi basa saye. Naji ana cewa kyan tafiya ai waiwaye nawa da na fara kanki na dosa kai tsaye. Ni kuma soyayya gadonta nayo ba wai haye, ki zo muyi batu, amma batun zuciya ya fiiii* *_Zan iya rantsuwa ba wanda yaffika, ba wai kyauba ko wanka azo gunka, ko mai ka haɗa ni dai ina yinka. Ba laifi bane inna yi kishinka. Kai zan sa a zuciya can na ɓoyeka. Ba wata ƴa da zata gane ka sai de a ran aure_* *_Da sanki a ƙirjina na baki wajen kwana_* *_Nayi mafarki ma har ka zama angona_* *_To ki sani sahun farko kar aji kukana_* *_Baza kayi kuka ba zauna daga dama na_* *_Kin zama komi na kin haɓɓaka ƙarkona_* *_Na soka iya sone da yadda da ƙarfina_* *_Shine sanadi nima bazan miki ƙarya ba_* *_Kai zaka zamo Sarki a fadata nima_* Gaba ɗaya wajen babu wanda basu burge ba don gaba ɗaya waƙar na tafiya ne daidai da motsin jikinsu, don har jawota zuwa jikinsa yake yi. Kuɗi kuwa kamar za suyi kuka saboda yanda aketa liƙa su. Ƙarfe sha ɗaya aka tashi. Kuma taro ya tashi tafiya. Mota har gida ta kwashi kowa ta mayar. Su Na'ima ma daga wajen dinner suka yi gida a mota guda. _Khalil_ ma daga shi sai matarsa. Karfe sha ɗaya da rabi suka iso gida. Kasancewar babu kowa a farfajiyan gidan, kowa ya shige ɗaki yana huta gajiya, sai _Khalil_ ya cicciɓi matarsa kamar baby yayi side ɗinsu da ita. A ƙofar ɗaki ya direta tare da buɗe ɗakin ya kuma cicciɓanta bayan ya kullo ɗakin da key yayi sama. Kai tsaye ɗakin da ya kasance nashi ya direta a kan gado tare da cire takalmin ƙafarta ya ajiye sannan ya hawo gadon ya kai hannu ya warware igiyoyin bayan rigar tare da soma zuge zip tayi saurin kai hannu ta baya ta riƙo hannunsa. Matsowa yayi dai-dai kunnanta tare da janye gashin da yake wajen ya kama kunnanta kaɗan ya ɗan ciza sannan ya hura. Tsikar jikinta yayi wani irin yarrr har bata san lokacin da ta lumshe idanu ba. A kunna ya soma yi mata raɗa, "Please kar ki kasance cikin matan dake yiwa mijinsu ƙudundune. Ni mijinki ne, ki saki jikin dani. Ko kin manta abunda ƙasar mama ta faɗi ɗazu a wajen dinner ne." Rimtse idanu tayi saboda hucin numfshinsa dake sauka a cikin kunnanta yana saukar mata da wani irin kasala. Cikin dabara ya saka hannu ya zuge zip ɗin duka tare da ɓalle hook ɗin bra ɗinta. Da sauri ta kuma rimtse idanun jin lallausar hannunsa akan fatar jikinta. Bata ankara ba ya Juyo da ita gaba ɗaya ta faɗo jikinsa, wani irin runguma yayi mata tare da saɓule hannun rigar jikinta ya zaro bra ɗin ta ya wurgo shi ƙasa ya shiga wasa da jikinta. Gam ta rintse idanunta saboda wani matsanaicin kunya da ya rufeta. Ɗago da fuskanta yayi tare da faɗin, "Buɗe idanunki kiga wani abu." Ƙin buɗewa tayi saboda kunya, cakulkuli yayi mata da hannu biyu tayi wani irin zillo tare da faɗawa jikinsa ta saki kukan shagwaɓa." Kwantar da ita yayi tare da yi mata rumfa yana kallon idanunta da yake a kulle gam. Babu abunda yake tunowa sai ranar da ya suka taɓa kasancewa a haka a _Golden diamond_ she was screaming kamar zata tsaga masa kunne duk da bai kai ga jikinta ba. "I love you Soo much Sarah!" Ya faɗi hakan tare da haɗe bakinsu ya shiga bata deep kiss na kusan 5minutes sannan ya ɗagata don ya fara sauka daga kan layi. Hannunta kare da ƙirjinta ya ɗagota tare sauke gown ɗin ƙasa gaba ɗaya sannan ya ɗagata cak ya zareta ya ajiye a gefe. Saurin juya baya tayi shi kuma ya tattaro gown ɗin ya kai cikin wardrobe ya ajiye sannan ya ɗauke ta cak zuwa bayi tana noƙewa. "In yi maki wankan ne ko zak....." Tun kamun ya ƙarisa tace, "Zan yi da kaina." Murmushi yayi tare da fita daga bayin ya kullo mata ƙofa ya koma ƙasa. Ko da Sarah ta gama wanka, towel ta ɗaura kuma gaba ɗaya da kaɗan ya wuce mazaunanta don idan ta duƙa mazaunan zasu kasance a wajen. Kaɗan ta buɗe Ƙofar ta fito, ganin babu kowa sai ta fito da sauri domin ta shirya kamun ya dawo ɗakin. Wata red nightgown ta gani a kan gadon. Ɗagawa tayi ta jujjuya tare da faɗin, "h'umm! Waye zai saka wannan ɗin? Ba dai Saratu ba." Tana gama faɗin haka ta nannaɗe tare da ajiyewa dai-dai lokacin da _Khalil_ ya turo ƙofar ya shigo hannunsa riƙe da tire. Wani irin sufa tayi tare da faɗawa kan gadon ta cukuikuye kanta da zanin gadon. Ajiye turen yayi tare hawowa kan gadon. Riƙe zanin tayi ƙam tana faɗin, "Don Allah ka fita in saka kaya." Bai saurareta sai da ya janye zanin gadon sannan ya haɗata da jikinsa yana raɗa mata, "Allah idan baki natsu ba, shi kansa towel ɗin, ciresa zanyi." Tsit tayi jin abunda yace. Tiren ɗin ya ɗauko ya ɗaura a kan gadon tare da faɗin, "Oya come let me feed you." Girgiza kai tayi tare da faɗin, "Ni dai na ƙoshi." Ta faɗi. Janyo ta yayi jikinsa tare da yago kazar ya saka mata a baki, sau uku kawai ta ƙarba tare da narke masa tana kukan shagwaɓa akan ta ƙoshi. Lafiyayyan madaran shanu ya zuba a cup ya kafa mata a baki, bai zame ba sai da yaga ta shanye tsaf sannan ya zuba shima ya sha tare da ɗaukar tire ɗin da sauran kazar ya fita dashi zuwa kitchen. ko kamun ya dawo tayi saura ta saka wata rigarsa da ta kawo mata har guiwa sannan tayi saurin gyara gadon. Hannunsa ɗauke da hijjab da wata doguwar rigar abaya ya shigo. Dariya ya kwashe dashi ganinta sanye da rigarsa da yayi mata yawa. Juya masa baya tayi tana turo baki. "Mrs _Khalil_ tashi ki ɗauro alwala kizo mu godewa Ubangiji." Ba tare da musu ba ta sauko ta nufi toilet. Bayanta ya dunga bi da kallo har ta shige bayin. Mintuna biyu ta fito ɗaure da alwala lokacin tuni shi har ya shimfiɗa darduma. Da hannu yayi mata nuni da abaya da hijjab. A kan rigarsa dake jikinta ta saka abayan sannan ta saka hijjab yaja su sallah. Raka'a biyu suka yi. Bayan sun sallame ya kwararo masu addu'o'i sannan ya dafa goshinta tare da faɗin, " _Allahumma innee as'aluka min khairiha wa khairi maa jabaltaha 'alaihi wa'a uzhubika min sharriha wa sharri maa jabaltaha 'alaihi_" yana kaiwa nan ya jawota ya rungume k'amk'am tare da raɗa mata, "Finally, you're mine Sarah!" Ya faɗi hakane yana mai kaiwa ko ina na jikinta kiss. Tuni ya gama kashe mata jiki gaba ɗaya domin saƙonninsa suna amsar ko wani saƙo da lungu na jikinta har bata san lokacin da ta saki jiki gaba ɗaya ba. Cak ya ɗauke ta zuwa gado ya shimfiɗe tare da yi mata rumfa ya cigaba da kashe mata jiki da zafafan romance. Sai da ya bari ta kunnu iya kunnuwa don gaba ɗaya ba tare da ta ankara ba ya gama fatali da duk wani suturar jikinta sannan ya soma karanto addu'ar saduwa. Sarah bata dawo hayyacinta ba sai da taji baƙon lamari da gigitata har bata san lokacin da tayi wani irin yunƙuri ba tare da buɗe baki za tayi ihu yayi saurin tare ihun da bakinsa ya shiga shafa kanta yana hura mata iska. Hawaye kawai suke gangarowa daga idanunta suna sauka a kan gadon. Sosai _Khalil_ yana ƙoƙari tare da dauriyanta. Don tun yunƙurin farko bata kuma yi ba sai hawayen da take yi sai kuma wnit lokacin da take faɗin, "Wayyo Allah na zaka ji min ciwo!" *Wallahi ba ƙaramin wahala nasha ba tun jiya nake typing ɗin nan. Keyboard ɗin ne bai min typing da sauri. Nafi sabawa da ɗayar wayata. Duk daɗewar nan kuga abunda nayi😭😭😭* *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* [10/1, 12:17 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *21* Sosai yaji tausayinta kasancewar babu ƙarya ta jigata da yawa. Bayan komai ta lafa. Da kansa ya cicciɓeta har bayi ya galgasa mata jiki. Ko a wajen sanyata cikin ruwan zafi tayi dauriyan ba kaɗan ba. Babu abunda take yi sai ciccije baki da faɗin "Wassh!" Har ya kammala gasatan sannan ya nannaɗota cikin towel ya dawo da ita kan gadon sannan ya buɗe ƙaramin fridge ɗin dake ɗakin ya ɗauko ruwan gora tare da ɓallo paracetamol da pain killer ya miƙa mata, hannunta na rawa ta karɓa ta watsa a baki tare da korawa da ruwa sannan ta kwanta tare da dunƙulewa waje ɗaya tana rawar tsari. Kashe wutan ɗakin yayi tare da hawa kan gadon ya lulluɓesu da bargo sannan ya jawo ta jikinsa ya rungume. Nan da nan baccin wahala yayi gaba da ita, shi kuma sai ya tashi zaune ya jawota a hankali ya ɗaura kanta a saman cinyarsa. Hannu ya kai ya kunna bedside lamp mara haske wanda ya bashi daman kallon fuskanta sosai, sai sauke ajiyar zuciya take yi. Baccin ma a shagwaɓe take yinsa. Don sai wani kwaɓe fuska take yi tana ƙara shigewa jikinsa dama kuma Sarah akwai son jiki kamar mage. "You're my early paradise, my one and only, my four in one, infact my everything. You're _Khalilullah's_ happiness! Without you Sarah, I can't survive. Sarah a yau mun haɗe mun zama ɗaya, ke _Ibrahim_ ce, _Ibrahim_ kuma kece. Saratu baki na ba zai iya misalta maki yanda nake jinki a raina ba, yanda kika bani farin ciki a yau, Allah yayi maki sakayya da gidan Aljanna." Kamar a mafarki haka Saratu take ta jin maganganunsa. Gam ta kamo hannunsa ta riƙe, cike da magagi irin na bacci ta soma faɗin, "Kai jinin dake yawo a jikina ne, duk wani bugun zuciyata da tunaninka take tafiya, _Khalil_ tun lokacin Sarah ta soma tozali da kai ka sace zuciyarta, kuma a kullum bata taɓa fasa addu'ar Allah ya mallaka mata kai ba. Rayuwar Sarah Nuhu, da taka take tafiya. Tsayawar taka dai-dai take da tsayawar bugun zuciyar Sarah. Sarah ta mallaka maka komai nata, a yau da kuka zama ɗaya kuma, ta ƙara damƙa maka akalar rayuwarta. Ka taimaka ka rungumi Sarah a ko wani irin hali, don Sarah tayi wani oath akan cewar, no matter what, kuna tare for rever and ever." Wani irin murginata yayi tare da yi mata rumfa ya shiga kissing ɗinta yana faɗin, "Nagode wife, nagode. And I promise babu wanda ya isa ya shiga tsakanin mu. Mun riga mun zama hanta da jini." Wasu mahaukatan French kiss ya soma bata. Ganin gaba ɗaya ya soma fita hayyacinsa don har ya soma ƙoƙarin komawa gidan jiya ta soma turesa tana faɗin, "Ka tausaya min, wallahi akwai zafi. Ciwo yake min kuma bacci nake ji." A kunne ya raɗa mata, "Kiyi haƙuri ki bani sau ɗaya kawai, zan biki a hankali ta yanda baza kiji zafi irin na ɗazu ba, don Allah wifey." Shuru tayi hawaye na gangaro mata. "Inyi?" Ya faɗi a tausaye. Ɗaga masa kai tayi tana mai danne kukan da yake taho mata. "Allah ya miki albarka!" Ya faɗi tare da yi mata kiss a goshi sannan ya kai hannu ya kashe bedside lamp ɗin. Wannan karan tafi karon farko shan wahala, don sai ya zame mata kamar fami. Sai dai ba ƙaramin dauriya tayi ba. Babu kwarorowa sai "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un" da yayi ta shan kira da kuma su Lami, Baba da kuma sauran ƴan uwanta. Bayan komai ya natsa ya kuma yi mata gashi karo na biyu tare da wankan tsarki, shima yayi sannan suka kwanta yaja masu bargo nan da nan bacci yayi awon gaba da dukansu don dare yayi sosai biyu ma ta wuce. Sun so makara sallar asuba saboda jimawar da suka yi basu yi bacci ba. Da sauri _Khalil_ ya diro daga kan gadon jin alamar za'a tada sallah a masallaci. Sauri-sauri ya ɗaura alwala tare da sanya doguwar rigar jallabiya sannan ya fita zuwa masallaci. Bayan an idar da Sallah ya fito, a ƙofar masallacin suka haɗu da ya Abdul-Hakeem. Hannu ya bawa _Khalil_ suka tafa tare da faɗin, "Ango-ango, ango ka sha ƙamshi. Ai na ɗauka yau an ɗauke maka sallar asuba yau. Don tuntuni nake ta kallon hanya ko zan hangi fitowar ka." Ya ƙarisa maganar yana dariya. Dariyar shima _Khalil_ yayi tare da faɗin, "Babu wani jin daɗin da zai zo min a cikin duniyar nan da zai hanani gaida Ubangijina. Ai ta hakan ne zan nuna masa jin daɗin abunda yayi min domin ya dauwamar dani a cikin farin ciki." Hannu ya Abdul-Hakeem ya kai ya mari ƙeyarsa kaɗan tare da faɗin, "Ƙanina har wani girma da natsuwa naga ka ƙara daga jiya zuwa yau. Allah dai ya ƙaro zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba." Da "Ameen" _Khalilullah_ ya amsa daga nan gaba ɗaya suka nufi side ɗin Hajiya kasancewar haka suke tun farko, ana saukowa sallar asuba sai sunje sun gaidata sannan kowa ke komawa ɗakinsa. Sai da suka yi knocking sannan ya Abdul-Hakeem ya murɗa handle ɗin sannan suka shiga. Zaune suka sameta a kan darduma tana lazumi. Sai da ta kammala sannan suka haɗa baki wajen faɗin, "Hajiya barka da asubha. Kin tashi lafiya?" Da murmushi ta amsa da, "Lafiya ƙalau Alhamdulillah! Ya kwanan iyalan naku?" Duka suka amsa da, "Lafiya ƙalau." "To ma sha Allah! Abdul-Hakeem ya ake ciki da masu tafiya yau? Kasan Maiduguri ba nan kusa bane. Jirgin za su bi koko yaya?" Hajiya ta faɗi tana kallon ya Abdul-Hakeem. "Eh jirgi zasu bi Hajiya, don ya Abdullah kamun ya juya zuwa Abuja jiya, sai da ya bani kuɗi naje nayi masu booking flight. Jirginsu zai tashi ƙarfe sha ɗaya na safe. Sai a faɗa masu su kasance cikin shiri." Hajiya tace, "To shikenan. Allah ya saka da alkhairi ya ƙara buɗi da kuma kare ku daga sharrin maƙiya na kusa da na nesa." Da "Ameen." Suka amsa sannan suka tashi suka fita. A parlour suka taras da Laure tana kakkaɓar kujeru, cikin sauri ta gaida ya Abdul-Hakeem kasancewar basa ƴar wasan da suke yi ita da _Khalil_, a taƙaice ya amsa tare da fita daga parlour ɗin. Sai ta juyo ta kalli _Khalil_ tare da faɗin, "Yanzu dai ko darajan amarya naci ai, don Allah a ɗan sammin turaren." Ta ƙarisa maganar a marairaice. "Za'a sammiki albarkacin amarya kamar yanda kika ce. Anjima kizo ki karɓa." Washa baki tayi gaba ɗaya haƙoran sai suka yo waje. Da sauri yaja baya tare da faɗin, "Wallahi idan kina so mu shirya kar ki kuskura ki firgita min mata da wannan haƙoran naki kamar yanda kika firgita ni." Da sauri tace, "Halit......" Sai kuma ta fasa ƙarisawa ta canza maganar, "Ba zan ma ƙara buɗe bakin ba." "A'a ƙarisa abunda kika yi niyyar faɗi kawai. Da kuwa kinyiwa turarenki." Ya faɗi yana hararenta. "To ai shiyasa ma nayi gum da bakin nawa. Ho na Saratu, bada kanka a sare!" "An ƙara miki turare ɗaya." Faɗin _Khalil_. Wani tsalle ta buga na jin daɗi shi kuma yayi dariya tare da fita daga ɗakin. Ko da ya koma ɗaki sai ya taras har Sarah tayi sallah ta koma ta kwanta. Ya gane hakanne ganin hijjab ɗinta a kan sallaya. Jallabiyar jikinsa ya cire ya ninke sannan ya ɗauki hijjab da sallayar ya ninke ya ajiye sannan ya hau kan gadon ya jawo Sarah jikinsa ya ja masu bargo suka. Hamdala yayi jin jikinta ya rage zafin da ya ɗauka jiya. Don kwana tayi da zazzaɓi. Basu suka farka ba sai ƙarfe sha ɗaya. Ta riga shi farkawa don motsinta yaji ya tashi tare da shafa fuska yace, "Good morning my angel!" Lumshe idanu tayi tare da faɗin, "Good morning, happiness." Kiss yayi mata a goshi tare da faɗin, "Ya jikin naki?" Gyaɗa masa kai kawai tayi tana ɗan cije baki saboda jikinta da yayi mata tsami. Naga kamar baza ki iya tashi ba, let me carry you." Ba tare da ya jira abunda za tace ba yayi wuff da ita. "Ni bayi zan shiga, ni dai bayi zani ka sauke ni dan Allah!" Ta faɗi tana harhaba ƙafafunta. Shi kuma ƙin ajiyeta yayi har sai da ya direta a cikin jacuzzi tub sannan ya fita domin bata damar taimakon kanta. Wanka tayi sosai ta gargasa jikinta sannan ta saka rigar wanka fara ƙal ta ƙulle igiyar sannan ta leƙo, sai da ta tabbatar baya nan sannan ta fito daga bayin ta saka silipas dinsa ta fita daga dakin da sauri ta koma nata ɗakin don babu kayanta a cikin ɗakinsa. Sai da ta fara ƙarewa ɗakin kallo tukun tana yaba kyawunsa sannan ta isa wajen mirror ta shafawa jikinta mai me ƙamshi da saka laushin fata. Simple make-up ta tsantsarawa fuskanta sannan ta feshe jikinta da turare sannan ta miƙe ta isa wardrobe ɗinta ta ɗauko wani haɗaɗɗan less wanda aka masa ɗinkin riga da skirt. Ya amshi jikinta sosai. Gaban madubi ta dawo ta tsantara ɗaurinta kuma dama ita gwana ce wajen iya ɗaurin ɗankwali. Turarensa ta ɗan fesa kaɗan a jikinta sannan ta ɗauko gyale ta yafa. _Khalil_ na kitchen yana ƙoƙarin soya kwai yaji door bell, sai da ya juye kwan a plate ya kashe gas sannan ya fita ya buɗe ƙofa. Washe baki Laure tayi tare da miƙa masa kwalaban fiya-fiya guda biyu. "Ke daɗi na dake rashin hankali, wannan kwalaban kuma na minene?" Turo baki tayi tare da faɗin, "Yo ba kai kai min alƙawarin turare har biyu ba." Riƙe ƙugu yayi tare da faɗin, "Sai kuma aka ce don nayi maki alƙawari sai kizo min ɗaki da sassafe kina damuna da buga ƙofa." Kallon basket hannunta tayi tare da faɗin, "Aunty Maryamu ce fa ta aiko ni na kawo maku abun kari shine na taho da kwalaban don ka saka min turaren. Ina amaryar taka? Ni ƙamshin kwai ma nake ji yasin?" Ta ƙarisa maganar tana shinshine-shinshine. "To baƙar mayya, ban abunda aka aiko ki ki wuce ki bani waje. Kuma ki takuran in hana ki turaren, yasin." Ya ƙarisa maganar kamar yanda take yin magana, daidai suka ji ƙarar takalmin Sarah tana saukowa daga steps. Juyawa yayi da saurin jin daddaɗan ƙamshin turarenta da ya daki hancinsa, don humran da Hajiya ta bata jiya da kuma _Imperial Majesty_ da oud ta shafa, sai suka haɗu suka bada haɗaɗɗan ƙamshi mai sanya natsuwa a zuciyar wanda ya shaƙi ƙamshin. " _Naaji na gani zan baki lokacina, tunda kinka nuna ƙauna dare da rana, baki nuna so, domin arziki na, kikan tsare mutunci ko bakya gaba na. Ke nake gani, ke nake gani. Ke nake gani, to bani kula kowa_." Yana tafiya ne yana waƙar har ya isa inda take ya kamo hannunta ya bata kiss a goshi. Laure kuwa sake baki tayi tana kallon su. Ganin _Khalil_ ya manta da ita a wajen sai ta soma waƙa ita ma tana faɗin, " _Ga abinci ku, ga abincinku, kuzo ku karɓa, a baani turare in wuce_." Da sauri _Khalil_ ya tare gaban Sarah yana faɗin ku kuke ganinmu ba mu muke ganin ku ba. Anya Laure babu aljanu jikinki kuwa. Wannan irin murya haka kamar na samudawan farko. To tuf-tuf-tuf. Kurwar matata kur. Maye ko aljani yaci kanshi. Ga ƙatuwar murya ga uban kacakoran haƙora." Shigowa sosai Laure tayi tare da dire basket ɗin sannan tace, "Wallahi tallahi halittar ubangiji. Kuma dai nafi matar kyau." Juyowa yayi gaba ɗaya ya kalleta daga sama har ƙasa tare da faɗin, "Eh Lallai babu shakka." Sai kuma ya bushe da dariya tare da faɗin, "Ga shawara idan zaki ɗauka, kije kuyi shawara ke da mai gadi ya samo ƙatuwar keji ya ajiye a ƙofar gate, bayan kin gama aikinki na cikin gida sai ki fita waje ki shiga kejin nan, wallahi ba ƙaramin kuɗi zaki samu ba, don duk wanda ya zo wucewa sai ya ajiye maku kuɗi." Kuka ta fashe dashi tare da faɗin, "Sai kace wata biranya zan shiga keji. Kuma turaren ma ba'a so." Tana gama faɗin haka ta juya Sarah tayi saurin kai hannu zata riƙota _Khalil_ ya riƙe hannun tare da faɗin, "Tsaya ki sha kallo." Sai da ta kai bakin ƙofa sannan ta juyo tare da faɗin, "Baza ka bani haƙuri ba? Ke kuma amarya ko ɗan irin cin-cin ɗin nan ma baza ki bani ba. To wallahi ban fita ko ina sai an bani turarena da cin-cin." Kallon juna _Khalil_ da Sarah suka yi suka fashe da dariya. _Khalil_ yace, "Ahaf, ba na faɗa maki ba. Ai mayya ce! Idan ban bata turaren ba sai ta lashe kurwata!" Murguɗa baki tayi tare da faɗin, "Eh naji ɗin komai zaka ce kace idan har za'a ban turaren." Kiss yayi ma Sarah a kumatu tare da faɗin, "Ina zuwa love, bari na ɗauko mata ta wuce ta bamu waje." Gyaɗa kai kawai Sarah tayi. Yana wucewa Laure ta matso kusa da Sarah tare da faɗin, "Wallahi ke kyakkyawa ce. Kin ganki kuwa? Wane kajuli (Kajol) ta ƙasar hindiya. Gaskiya ya _Khalil_ ya iya zaɓe yasin. Ku wani yare ne?" Murmushi Sarah tayi tare da faɗin, "Babana ɗan Nasarawa ne a wani ƙauye da ake kira _Wamba_" Riƙe haɓa Laure tayi da faɗin, " _Wamba_? Ni ban ma taɓa jin sunan garin ba. To mamanki fa?" Ko kamun ta bata amsa suka ji saukowar _Khalil_ hannunsa riƙe da kwalin turare guda biyu. Washe baki Laure tayi tare da faɗin, Alhamdulillahi ni Laure! Nagode ya Ibrahim" ta faɗi tun kan ya miƙa mata turaren. Taɓe baki _Khalil_ yayi tare da miƙa mata yace, "Sai a sakar min mara inyi fitsari." Amsa tayi bakin yaƙi rufo, haƙoran sunyi cirko-cirko a waje. "To, to a wuce a bani waje." Sai da ta kai ƙofa sannan tace, "Aunty Saro, sai nazo dan ya _Khalif_ ya fita." Da ƙarfi Khalil yace, "Kika ƙara kiran matata da wannan sunan sai na cire shegun haƙoran nan. Kuma kar in sake inga ƙafafunki a ɗakina." Dariya Sarah tayi tare da faɗin, "Amma ya kuke da ita?" Sai da ya kulle ƙofar ya saka key sannan ya dawo inda take ya rungume ta sannan ya ce, "ƴar uwa ce, lokacin da Hajiya taje Maiduguri aka haɗo ta da ita domin ta riƙa taimaka mata da wasu ayyukan. Ance dai abokiyar wasan mu ce, ban dai san asalin yanda muke da ita ba." Sarah tace, "Hajiya ƴar Maiduguri ce ko?" Zama yayi a kan kujera ya ɗaurata a kan cinyarsa tare da faɗin, "Mahaifinta Shuwa ne, mahaifiyarta kuma Kanuri, kuma duka tana jin yaren." Kallonsa tayi tare da faɗin, "Kai fa, kana jin yaren?" "Gwada yara min naji ko zan iya mayar maki?" Faɗin _Khalil_. "To ai ni ban iya ba." Sarah ta faɗi. Kwanto da kanta yayi a kan ƙirjinsa tare da faɗin, "Kar ki damu, wata rana zaki san ko inaji ko ban ji." "To baba fa, wani yare ne?" Sai da ya nuna kansa Sannan yace, "Babana?" "Eh babanmu." Ta bashi amsa tana nuna ita dashi. "Sorry babanmu har dake. Shi kuma Mahaifiyarsa bafulatana, mahaifinsa Kanuri." "Kai Kanuri ne kenan?" Faɗin Sarah. "Kwarai da gaske!" Ya bata amsa tare da miƙar da ita zuwa dinning sannan ya ɗauko basket ɗin da Laure ta kawo abinci ya ajiye a kan dinning ɗin sannan ya koma kitchen ya ɗauko kwan da ya soya. "Ni na soya wannan da kaina. Ci kiji?" Faɗin Khalil cike da farin ciki don ya soya kwai. Sarah kuwa tun kallon farko da tayi wa kwan taga tsakiya ya babbake. Hannu ta kai ta ɗan yago gefe inda bai ƙone ba ta saka a baki. Da sauri ta furzo shi jin magi har kwakwalwar kanta. "Ya dai?" Faɗin Khalil bayan yayi saurin zuwa inda take. Bata ce komai ba ta yanko ta saka masa a baki. Dakyar ya iya juriya ya haɗiye yana yamutsa fuska. "Wai wai wai! Daɗi!" Faɗin Khalil yana yin haka👌da hannu. "To maza cinye shi!" Ta faɗi tana masa tuni da plate ɗin da idanunta. "Kiyi haƙuri na kaiwa Madhu itama taci. Don duk abunda na saka a baki itama sai ta ci." "Wacece kuma haka?" Tayi saurin faɗa. Shi kuma yace, "Madhubala wutar kyau, masoyiyata kenan?" Tuni annurin fuskanta ya canza ta tsaya kawai tana kallonsa. Kumatunta yaja tare da faɗin, "Kishi, to mage na ce wacce na ɗauko all the way from Paris. Zaki sota sosai idan kin ganta. Very beautiful." Sai a lokacin ta saki fuska tare da faɗin, "Laa! Kaman ka san ina son mage sosai. Tana ina?" "Tana side ɗin Hajiya. Idan mun gama karyawa zan kai ki, ki gaida Hajiya sai mu ɗauko abun mu daga nan." Ya faɗi hakane tare da soma serving ɗinsu a plate ɗaya. Yana bata a baki tana bashi har suka kammala sannan suka kwashe kayan tare suka kai kitchen yana wanke-wanke tana ɗauraya har suka kammala. Towel ya ɗauko ya goge mata hannu dashi sannan suka fito parlour. "Bari na ɗauka maki babban mayafi sai muje wajen Hajiya." Ya faɗi hakan tare da nufar sama. Mintuna kaɗan ya dawo ɗauke da gyale. Da kanshi ya soma nannaɗa mata gyalen a kai dai-dai lokacin da suka ji door bell. A tare suka kalli ƙofar, sai da ya gama saka mata sannan ya nufi ƙofar ya buɗe. Ido huɗu suka yi da Aina'u tana sakar masa murmushi. *KIRA ZUWA GA MARUBUTA* _A matsayinka na ɗan Nigeria bai kamata kayi murnar Independence ba, bai kuma kamata kabar wani yayi ba!_ _dalilina kamarhaka_ _a satin daya_ _gabata an sace ɗalubai a jahar Zamfara, an kashe wasu a sakkoto, An harbe wasu a cikin Jos, a kaduna kuwa an tare jirgin ƙasa an kwashe mutanen cikinsa wanda har yau ba'a san inda sukeba!_ _kai yanzu ko tafiye tafiyen da akeyi da an daina saboda irin wannan matsalolin!_ _Kuma duk haka yana Faruwa ne saboda sakacinmu na mutanan AREWA, ko har kun manta da ƴan matan da aka sace a cikin jahar Barno state a shekarar 2014 su ɗari biyu da sabai'n da shida?!, ƴan matan ƴan matan chibok, toh haryanzu ba'a san inda saura suke ba..._ _Idan mukace AREWA muna magana ne da ƴaƴan cikinta waɗanda suka sami ɗaukaka koya take kama daga Ƴan social media, ƴan film, mawak'a, masu shirin barkwanci, tare da_ _*Marubutan mu*, mu taso mu buɗe baki muke_ _magantuwa, muyi amfani da wannan damar ta social media, kuna ganin celebrity ɗin nan na kudu daya mutu zargi suke akan kashe shi akayi ba tabbatarwa ba, amma ji yadda abun ke yawo a ƙasa baki ɗaya!_ _mu kuma ƴaƴa mata ake kwasa ake shiga jeji dasu, banda tsadar rayuwa, da azaba da ƙuncin da muke ciki, kidnapping, kwace, Haure, ana kashe mana ƴan uwan mu ɗaruruwa batare da munce komaiba!_ _shin da mukayi shirun gajiya_ _sukayi suka daina ko kuwa abin ta'azzara yayi?_ _a matsayinki/ka na *Marubuciya, Marubuci* ƴan AREWA ga dama tasamu, masu novel na kuɗi dama free, masu ɗaukakar cikin mu dama sabbin tasowa, magana ake aji murya iri ɗaya gabaɗaya a social media a yau first October dan already no more Independence, Dan girman Allah kar mu raina abin da zamuyi, koda baƙya update na novel kiyi koda shot writing akan matsalar dake faruwa!_ _kar mutsaya sai abi yazo kan ƙanwarka ƙanina babana ko mamana, Kaduna Zamfara Barno Kano da dukkan arewa muɗin duka abu ɗayane, dan Allah marubata mufito ƙwanmu da ƙwarƙwata mutaya ƴan uwanmu ƴan_ _social media isar da saƙo, tunda mu baiwar rubutu_ _ubangiji ya bamu muyi amfani da ita wajan yin gƴara._ _ubangiji yayi mana Jagora ya Allah ka sakawa duk wacce tayi ƙoƙarin tallafawa da gidan Aljannatul-Firdausi_. *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* [10/2, 8:21 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MAZA* 🦜 *22* Da sauri Sarah ta ƙariso wajen tana faɗin, "Lah, Ai'n kece? Shigo mana kin tsaya a waje kamar baƙuwa. Ke ɗaya ce?" Hanya Khalil ya bata ta shigo tare da faɗin, "Bamu san da zuwanki ba, ashe kina tafe" kai tsaye yayi maganar don har ga Allah bai so zuwanta ba don zata shiga haƙƙinsa na rashin bashi damar kasancewa da matarsa. Da kallo ta bishi tana ji kamar rungumesa saboda ƙaunarsa dake fuzgarta. Shi kuwa Khalil komawa yayi ya zauna tare da ɗaukar remote ya kunna tv ya ɗaura ƙafa ɗaya akan ɗaya. "Ai'n mai zaki ci? Ki zauna mana." Wani kallo Khalil ya watsawa Ai'n ɗin tare da maida kallonsa izuwa ga Sarah yace, "Babe, ba girkin da za kiyi, saboda ban so kiyi stressing kanki shiyasa na fita da kaina na haɗa maki breakfast. Ohh nama manta, akwai sauran abincin da Aunty Maryam ta aiko mana dashi gashi can a dining. She should go and serve herself kamun mu dawo daga cikin gida wajen hajiya. Let go wife!" Ya faɗi hakan tare da kama hannun Sarah ya saka cikin nashi. Kallonta Sarah tayi tare da faɗin, "Aina'u bari muje mu dawo. Hajiya zanje na gaisar in dawo yanzu." Yaƙe tayi tare da faɗin, "Ok sai kun dawo." Suna fita Khalil ya saki tsaki tare da faɗin, "Killjoy?" "Wa?" Sarah ta tambaya tana kallonsa. "Ƙanwarki mana. Bata iya zuwa gidan amare ba. Ita da ake bari sai irin bayan sati biyun nan, duba fa ki gani ko 12:00 bai yi ba. Ni dai wallahi an shiga haƙƙina. Ɗaukar hutun wata guda nayi domin in huta tare da matata, amma naga alama ana son hanani more amarcina." Tsungulinsa tayi a hannu har sai da ya furta, "Auch! Mai nayi maki?" "Duk fa wanda zai zo ba kwana zai yi ba, dole zai tafi ya bar mu tare, to menene abun damuwar bayan we will always sleep together babu mai raba mu?" Cak ya tsaya yana kallonta tare da faɗin, "Haba, dagaske? Za ki biyani duk bashin soyayyar da aka hanani nunawa da ranar?" Dukan kafaɗunsa tayi tare da faɗin, "Wallahi happiness kana da negative mind. Ni ba abunda nake nufi kenan ba." "To ni kuma kinga abunda nake nufi kenan." Faɗin Khalil. Da sauri tayi gaba saboda kunyar da ya bata. Haɗawa yayi da gudu ya isketa tare da faɗin, "Yarinya kina da aiki, wai kunyata kike ji? Taɓ, kina ruwa can gaban breaker." Cak ta tsaya kasancewar sun iso daidai ƙofar part ɗin Hajiya. Shi ya ƙarisa tare da murɗa handle ɗin ƙofar ya shiga bakinsa ɗauke da sallama. Gaba ɗayansu suna parlour ana hira, Hajiya, yaya Abdul-Hakeem, yaya Muhammad Kabir, Aunty Maryam, aunty Khairat, aunty Zakiyyah matar yaya Abdullahi, Nafeesa, Aysha, Laure, Aunty Jamila autarsu uncle Ameeru, sai ƴaƴansu da kuma kaɗan daga cikin sauran mutanen Maiduguri da basu koma ba. Juyawa Khalil yayi tare da faɗin, "Babe, shigo mana." Da sauri Aunty Khairat ta tsunguli aunty Maryam jin sunan da Khalil ya kira Sarah dashi suka bushe da dariya. Ita kuwa Sarah a kunyace ta shigo ɗakin kanta na kallon ƙasa ƙafafuwanta na harɗewa. Har ƙasa ta duƙa tare da faɗin, "Hajiya ina kwana?" Da murmushi a fuskar hajiya ta amsa tare da faɗin, "Zo taho nan kinji ƴata." Zama tayi kusa da ƙafafun Hajiya a kan capet sannan tabi kowa ɗaya bayan ɗaya ta gaida su, kowa ya amsa fuska cike da fara'a babu nuna wani kyara ko wulaƙanci. Khalil ɗin ma gaida waɗanda suka girme shi yayi, wanda ya girma kuma suka gaida shi. "Yayanmu ka iya zaɓe fa wallahi." Faɗin Nafeesa tana ƙara leƙo fuskan Sarah. "Kun san ni komai nawa mai kyau ne shiyasa matata sai da na hanga na waiga na zaɓota zuƙeƙiya gata nan." Aunty Zakiyyah matar ya Abdullahi tace, "Gaskiya Ibrahim baka da kunya, a gaban yayyin naka nake irin wannan magana haka." "To Aunty kuma ni mai nace? Yabon matata fa kawai nayi." Faɗin Khalil yana dariya. "Wai, Hajiya sai kinyi haƙuri don zaki ga rawar kai!" Gaba ɗaya aka kwashe da dariya. Saukowa ƙasa Khalil yayi tare da zama daidai inda Sarah take sannan yace, "Wife, na san baki san kowa a nan wajen ba idan aka cire Laure da tazo ɗakinmu ɗazu. Bari na fara ta kan wannan babbar aunty, (yayi nuni zuwa ga Aunty Zakiyyah), ita ce matar babban wanmu, sojane a Abuja yake aiki. Lokacin da papa yake dai rai, we all are living there duk dani zaman na hutune don a abroad nayi rayuwata kaf, Hajiya ce ta matsa na dawo saboda Allah ya rubuta sai na haɗu dake mun ƙunla alaƙa mai girma. Last year suka aurar da second daughter ɗinsu mai sunan Hajiya ana kiranta little hajjaju, very smart girl don ni ta biyo a kwakwalwa." "Ai ka san mu duka kwakwalan tunkiyoyi gare mu sai kai ɗan gwal" Faɗin yaya barrister. Waro idanu Khalil yayi tare da faɗin, "Ni ba haka nake nufi ba. Mine saurareni kiji." Ya ƙarisa maganar yana kallon Sarah, "Wannan sunansa ya Abdul-Hakeem, wannan itace matarsa Aunty Maryam wacce ta aiko mana da breakfast ɗazu, ƴarsu ɗaya Maimoon... Wannan kuma shine ya barrister, shi kuma kin ga matarsa nan, sunanta Aunty Khairat, ƴaƴansu biyu...." Haka ya dunga nuna mutanan parlour ɗin yana mata bayani. Ita dai kai kawai take ɗaga masa. Yanda aka amsheta kowa na nan-nan da ita ya saka ta mance da wata Aina'u. Shikuwa Khalil yana sane, addu'a kawai yake yi cikin zuciyarsa Allah yasa ta gaji da jira ta wuce gida. Ɓangaren Aina'u kuwa, bayan fitarsu babu inda bata buɗe ta duba ba, sai faɗin, "Kan bala'iiii!" Kawai take yi tana kwafa. Sai da ta gama tsaf sannan ta dawo parlour ta zauna a kan kujera tana girgije-girgije ƙafa, "Wallahi in har sunana Aina'u ɗiyar Lami da Nuhu, wallahi tallahi ba zan taɓa bari kiyi farin ciki ba, ba dai anyi auren ba, enjoy the first week of your marriage before the war begins!" Ta ƙarisa maganar tana mai rausayar da kai. Tun tana ƙirga mintuna har ta dawo awa. A can cikin gida kuwa, kirar sallar azahar ne ya fitar da mazan zuwa masallaci yayin da matan suka ɗauro alwala. Bayan kowa ya idar da Sallah, sai suka haɗu gaba ɗaya a dinning don har an kammala lunch. Kujerun dinning ɗin irin mai sha huɗu ne, kuma sun ɗauke gaba ɗaya don ma yaran an haɗa masu a parlour don suna da yawa. Khalil ƙafa ya tura ya shafo ƙafar Sarah, ɗagowa tayi suka haɗa idanu ya kashe mata idanu, gaba ɗaya a idanun Hajiya komai ya faru amma sai ta nuna kamar bata ga komai ba ta cigaba da cin abincinta. Zumbur Sarah ta miƙe tana faɗin, "Inna lillahi!" Gaba ɗaya aka haɗa baki wajen faɗin, "Mai ya faru?" Khalil kuwa har ya zagaya ta bayanta tare da jan kujeran da take kai baya. "Na manta ina da baƙuwa a ɗaki. Kuma tun ɗazu tana can tana jirana." Hajiya tace, "Laure maza haɗo mata abinci a basket ki tafin mata dashi." Khalil kuwa tsaki yayi a zuciyarsa don bai so ta tuna ba. Shima abincin da bai ƙarisa ci kenan ba yabi bayan matarsa. Kowa Sarah ta murɗa handle ta shiga, a zuciye Aina'u ta juyo zata fara ruwan bala'i sai ga Khalil ya shigo rai ɓutu-ɓutu. Washe baki Ai'n tayi tare da faɗin, "Kun jima, har nayi bacci na farka. Amma dai mancewa kuka yi nazo ko?" Ko kamun Sarah tayi magana caraf Khalil yace, "Ni na ɗauka ma kin wuce ai. Ashe kina nan kina jira." Sarah tace, "Kiyi haƙuri Aina'u wallahi mancewa nayi kina nan. Kinci abincin?" "Ban sani ba shegiya munafuka. Wato kin shigo cikin arziki har kin soma wulaƙanci. Kiyi, lokacinki ne. Nawa na nan zuwa." A Cikin zuciya tayi maganar, amma a zahiri sai cewa tayi, "Naci!" Sama Khalil ya hau yana faɗin, "Love, ɗauko min energy drink a fridge ki kawo min sama." Da "To" ta amsa tare da nufar kitchen ɗin. Da wani irin kallo mai tattare da shauƙi Ai'n tabi bayan Khalil. Sarah kuwa kitchen ta shige ta ɗauko drink ɗin ta dawo parlour tare da faɗin, "Aina'u ina zuwa dan Allah. Bari na kai masa na dawo." Ko tari Aina'u bata yi ba. Sarah kuwa dama bata jira cewarta ba ta nufi sama, kwance ta same shi daga shi sai boxer yana danna waya. Yana jin shigowar ta ya ajiye wayar tare da miƙa mata hannu alamar ta taho garesa. Sai da ta ɗan yi jim sannan tayi taku ta isa gareshi. Janyota yayi gaba ɗaya ta faɗo jikinsa ya saka hannu biyu ya rungume tare da faɗin, "Taho inji ɗumin jikinki matata." Ya ƙarisa maganar yana sunsunar wuyarta. "Dan Allah ka sake ni, Aina'u fa tana parlour." Hannu ya kai ya cire ɗan kwalin kanta ya cusa hannunsa cikin gashinta tare da faɗin, "Duk wacce tazo gidan amare ai ta san hakan zai iya faruwa da ita, ni kuma saboda wata Aina'u ba zan ƙi hutawa da matata ba." Ya ƙarisa maganar tare da murginata yayi mata rumfa yana kallon kyakkyawar fuskanta. "Waiyy! Nauyi gareka, ɗaga ni." Ta faɗi duk da kuwa be sakar mata nauyi ba. Jin abunda tace sai ya ɗan sakar mata kashi talatin a cikin nauyin nasa. Da sauri ta shiga bugun bayansa tana faɗin, "Nauyi, nauyi, nauyi! Wallahi ka sakar min nauyi." "Au haba, dagaske?" Kukan shagwaɓa ta sakar masa tana tsungulin damtsensa. Juyawa yayi ta koma samansa tare da zagaye ƙugunta da hannunsa ya matso da kansa ya haɗe bakinsu ya shiga bata deep kiss, Sarah kuwa sai mutsu-mutsu take zata kwace kanta yayi saurin juyata ta koma ƙasa yayi mata runfa ya shiga bata zazzafan romance, tun tana noƙewa har ta saki jikinta ba tare da ta shirya ba ta shiga mayar da martani. Sai da komai ya kammala ta shiga kukan shagwaɓa tana faɗin zafi. Shi kuwa ya biye mata yana ta lallashi. Tare suka yi wanka wanda a can bayin ma sai da suka ɓata lokaci, suna fitowa daga bayi ana kwaɗa kiran sallar la'asar. Sauri-sauri ya shirya ya fita gudun kar yayi missing ɗin sallah. Turus ya tsaya ganin Aina'u a zaune ta cika tayi faam, shi har ga Allah ya manta da ita a cikin gidan. "Ashe kina nan" shine abunda ya faɗi kawai tare da fita daga parlour. Wani irin kukan baƙin ciki Aina'u ta saki tare da miƙewa a zuciye tayi sama, kamun ta tura ƙofar ɗakin sai da ta tsaya ta goge hawayenta tukun sannan ta tura ƙofar. Juyowa Sarah dake gaban mirror tayi, sai da gabanta ya faɗi ganin Aina'u. "Sarah don nazo gidanki shine zaki min wulaƙanci ke da mijinki? Nagode kuma da izinin Allah ba zan sake zuwa gidanki ba." Tana gama faɗin haka ta juya zata fita. Da sauri Sarah ta miƙe tare da kamo hannunta tace, "Dan girman Allah ƙanwata kiyi haƙuri, wallahi ba wulaƙanci nayi maki ba. Kiyi haƙuri ki yafe min na san ban kyauta miki ba. Dan Allah Aina'u" ta faɗi tana mai haɗe hannunta biyu. "Amma Sarah....." Sarah tayi saurin cewa, "Dan Allah kiyi haƙuri ki bar maimaita magana. Zo ki zauna ina zuwa." Ta riƙo hannunta tare da zaunar da ita a kan gado ita kuma ta isa gaban mirror ta busar da gashin kanta sharp-sharp sannan ta saka riga da skirt English wear sannan ta saka dogon hijjab ta tada sallah. Bayan ta idar da sallar ta cire hijjab tare da nannaɗe dardumar ta ajiye sannan ta zauna kusa da Aina'u tare da faɗin, "Kiyi haƙuri Aina'u, tashi mu sauka ƙasa musha hira." Ta faɗi hakan tare da kama hannun Aina'u wacce ta gama ƙarewa gadon kallo ganinsa a hargitse kuma dama sai ƙarewa gashin Sarah kallo take yi ganinsa jiƙe kamun ta soma busar da kanta. Suna isowa parlour Khalil na shigowa. A gaban Aina'u ya kama kan Sarah tare da sakar mata kiss a goshi tare da faɗin, "Allah ya yi maki albarka!" Sannan ya nufi sama. Baki sake Aina'u ta bishi da kallo har ya ƙule kamun ta zauna tana sakin ajiyar zuciya. Aina'u ba ita ta bar gidan nan ba sai bayan magrib. Washa gari ma ta kuma dawowa, Khalil kamar ya fasa ihu don itace ta soma danna doorbell ko taran safiya bata yi ba kuma sai bayan magrib ta wuce duk ta hana su sakewa. A rana ta uku ce Khalil ya kai bango, don yana buɗe ƙofa yaga ita ce ko amsa gaisuwarta bai yi ba ya juya ya koma sama kuma yaƙi faɗawa Sarah tazo, kuma be bar Sarah ta fito daga bedroom ba ma balle ta sauko parlour taga Aina'un. Ranar har lokacin tafiyarta yayi bata ga ko ƙeyar Sarah ba, shima Khalil ɗin sau biyu ta gansa, lokacin da ya buɗe mata ƙofa da kuma lokacin da ya sauko zuwa kitchen ya dafa indomie da kwai ya koma saman, kuma ko kallon inda take bai yi ba. Sallah ma azahar da la'asar a ɗaki suka yi tare. Tsabar haushin da Aina'u taji, bata san lokacin da tayi wani irin kwallo da magen Khalil ba sai da ta karye a ƙafa sannan ta fizgi jakarta ta fita daga gidan. Tun daga ranar bata kuma dawowa gidan ba. Khalil kuwa kamar zuciyarsa za tayi bindiga ganin Madhu ɗinsa a karye sai kuka take yi. Haka ya kwashe ta zuwa asibitin dabbobi aka gyara mata ƙafar. Satin Sarah biyu a gidan Khalilullah, sun yi sabo da ƴan gidan sosai, kuma kullum da rana idan Khalil ya tafi sallar azahar a side ɗin hajiya take zama ita da Aunty Maryam har lokacin la'asar sannan kowacce ke komawa nata ɓangaren domin ɗaura girki. Sarah ta saba da nacin Khalil yanzu, kullum suna manne da juna babu daren banza. Ba ƙaramin soyayya suke zubawa ba a gidan. Ɓangaren kuwa, ranar da ta bar gidan Sarah keke napep ɗinsu yayi hatsari ta samu gocewar ƙashi a cinya, kuma babu wanda ya sanar da Saran. Wata ɗaya yazo ya wuce, biyu, har uku, Sarah tayi wani irin kyau da ƙiba da haske. Duk wanda ya ganta ya san tana cikin kwanciyar hankali. Yau da take cikin wata uku da kwana goma a gidan miji, Khalil yayi surprising ɗinta bayan gama nacinta akan tana son zuwa gida taga baba dasu Lami. Kamar an sakata a aljanna saboda farin cikin Khalil yace ta shirya zasu je gaida su baba. Wata lafiyayyiyar shadda ta saka kalar ruwan toka wanda yaji stone work iri ɗaya da na jikin Khalil. Sai da ɗauko farin gyale da farin takalmin vinci ta saka. Kaɗan ta fesa turare saboda Khalil bai so idan zasu fita ta riƙa fesa turare sosai. "Wow! Wife kin ganki kuwa?" Hularsa ƙube wanda Hajiya ta ɗinka masa da kanta ta saka masa tare da jawosa ta koma ta gabansa ta kwanto a jikinsa shi kuma ya ɗaura kansa a kan wuyanta, ita kuma tayi masu hoto. Ba ƙaramin kyau hoton yayi ba. "Wai nace ba, wani yare ne ku? Don nasan ku dai ba Hausawa bane." Yan maganar ne a cikin kunnanta. Sai da ta lumshe idanu sannan tace, "Na faɗa maka mu ƴan Nasarawa ne can _Wamba_. Baba yace sunan unguwarmu layin abakwa. Duk cikin mu babu wanda ya taɓa zuwa. Sunan yaren baba _Nindire_. Kuma yana ji sosai. Don akwai abokansa ƴan can, muna ji suna yi idan sun haɗu." "To ke kina ji?" Girgiza kai tayi tare da faɗin, "Ko zo in kashe ka." Dariya yayi shafa cikinta tare da faɗin, "Ɗana dake nan ko ƴata, za suji Kanuri in Sha Allah, zan riƙa yi musu, kuma Hajiya ma nasan za tayi masu." Kallon cikinta tayi sannan ta kallesa tare da faɗin, "To ai ni bani da ciki." "Ni da nayi cikin ai na sani." Ya bata amsa yana dariya. Kallon cikinta dake a shafe tayi, bata san lokacin da murmushi ya suɓuce mata ba tana fatan Allah ya amshi bakinsa. "Muje ko Queen" ya faɗi yana mai nuna mata hanya. Fita tayi ya biyota a baya, ji kawai tayi an ɗauke ta cak, bai sauketa ba sai da ya kawota har ƙofar ɗaki. Ɗakin Hajiya taje domin shaida mata zata gida, ba ƙaramin sha tara na arziki ta haɗa mata ba danginsu sabulai, turaruka, shadda da atamfofi har da manya-manyan zannuwar gado guda biyu. Khalil ta parking ta fito da gudu tayi cikin gida, babu kowa a gidan daga Lami sai Aina'u da ƴaƴansu Na'ima. Rungume Lami tayi tana mai farin cikin ganinta, da idanu tabi Sarah dashi, can kuma ta murza idanunta tare da faɗin, "Sarah! Kece haka?" Ta faɗi hakane tare da kaiwa ƙasa ta shiga faɗin, "Yesu Nagode, Nagode Yesu da kaba yarinyana kwanciyar hankali. Almasihu na koma gareka, ka saka albarka a rayuwar ƴata. In to my heart, in to my heart, come into my heart, Lord Jesus, come in to stay, come into my heart Lord Jesus, ameen!" Ta ƙarisa addu'ar tare da rungume Saran. Baba Nuhu kasa haƙuri yayi Sarah ta shigo, sai gashi ya fito yana farin, da gudu ta ƙarisa tare da faɗin, "Babaaa! Kai ne haka? Kaga yanda ka ƙara lafiya da kyau." Dariya baba yayi tare da faɗin, "Albarkacin haihuwarki ne Sarah, ban san mi zan cewa mijinki ba sai dai kawai ince Allah ya bashi Aljanna. Kullum cikin hidima yake mana. Ba'a haɗa cikakken sati bai zo gidannan gaishe ni ba." Zaro idanu Sarah tayi tare da kwaɓe fuska tace, "Amma shine bai taɓa zuwa dani ba sai yau, kuma baya faɗa min yazo." Murmushi baba yayi tare da faɗin, "Nine nan nace masa kar ya yarda ki soma fita sai kinyi wata uku da aure, shiyasa ko kwanciyar Aina'u a asibiti nace kar a faɗa maki." Zaro idanu Sarah tayi tare da faɗin, "Yanzu Aina'u ta kwanta asibiti baba shine ba'a faɗa min ba? Ni wallahi ba'a kyauta min ba." Dai-dai nan Khalil ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. Bayan baba ya amsa yace, "Ke dama tare kuke da Ibrahim ɗin shine baki faɗa ba tuntuni saboda sakarci." Turo baki kawai Sarah tayi tana jin haushin rashin faɗa mata kwanciyar asibitin da Aina'u tayi. Har ƙasa Khalil ya duƙa ya gaida baba sannan ya gaida Lami, baba ne kaɗai ya amsa banda Lami don haushinsa take ji tunda Aina'u ta faɗa mata abunda yayi mata ranar ƙarshe da ta ziyarci Sarah. Ɗakin baba ya shige sukayi ta hira, yayin da Sarah ta shiga ɗakin Lami, tayi tayi Aina'u ta kulata amma ko kallonta bata yi ba. Da Lami kawai suka yi hira. Duba hamsin ta bawa Lami da kuma tsarabar da Hajiya ta bata, Lami kamar ta goyata tsabar murna. Baba ma dubu hamsin ɗin ta bashi da shadda ɗaya da zanin gado, albarka ya dunga saka mata. Anan idar da la'asar suka taho gida. Tun daga wannan rana Sarah ta soma wani irin rashin lafiya, gwajin farko da Khalil yayi mata ya nuna ciki, ɗaukarta yayi zuwa asibitin yayi mata scaning, sai ga cikin wata biyu har da sati biyu. Sosai take laulayi mai zafi wanda yaci uban na farko. Sau uku tana kwanciya a asibiti, abinci kuwa ko ƙamshinsa bata so, daga ruwan bohol sai fanta mai sanyi. Komai Khalil ke yi mata, wanka, wanki da gyaran ɗaki. Idan kuma yana asibiti, Laure ko Aunty Maryam ke yi mata. Wata ranar labara, tana kwance a akan kujera tana maida numfashi taji alamun ana murɗa handle ɗin ƙofa, tana ɗago kai tayi arba da ƙatuwar akwati Aina'u naja. Duk da bata jin ƙarfin jikinta bata san lokacin da ta tashi zaune ba tana bin akwatin da kallo............ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* [10/5, 11:21 AM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *23* "Aina'u, lafiya?" Faɗin Sarah cike da mamaki. Aina'u wani haɗe rai tayi tare da faɗin, "Ban gane Lafiya ba. Ko bakya son gani nane in koma inda na fito?" Sauke ajiyar zuciya Sarah tayi tana ƙara kallon akwatin ta gefen idanu tare da faɗin, "Ya zaki ce haka Ai'n, kawai nayi mamakin ganinki ne." Aje akwatin tayi a nan tsakar ɗaki tare da zama akan one sitter tace, "Wash, akwatin nan ba dai nauyi ba, daga gate zuwa nan kamar zan mutu haka naji. Nazo taimaki ne ganin baki da lafiya, ina nan har ki haihu." Wani miyau Sarah ta haɗiye jin abunda Aina'un tace, ita damuwarta ɗaya, rashin kamun kan Aina'un na yawan surutun faɗi ba'a tambayeka ba. Bata so kyakkyawar alakar dake tsakaninta da Hajiya da kuma Aunty Maryam ya samu matsala sanadin Aina'u. "Ya ubangiji Allah maji roƙon bayi, kasa zuwan yarinyar nan gidan nan alkhairi ne." Sarah ta faɗi cikin zuciya. Taɓe baki Aina'u tayi ganin Sarah ta faɗa dogon tunani, cikin zuciyarta ta furta, "Kuma wallahi zama cikin gidan nan dole." Jiki babu kwari Sarah ta miƙe tare da faɗin, ɗauko akwatin naki na nuna maki ɗakin da zaki sauka." Miƙewa tayi tana wani taɓe fuska tare da jan akwatin, ta cikin second parlour suka bi zuwa bedrooms ɗin dake ƙasa, "Zaɓa ɗakin da kike so a cikin ukun nan sai ki zuba kayanki a cikin wardrobe." A yatsine Aina'u tace, babu ɗaki a sama ne sai nan ƙasa? Nafi son saman." Sai da Sarah ta kalleta sannan tace, "Eh babu, don can ɗin daga ɗakina sai nashi." A gadarance Aina'u tace, "To kuma bazan iya zama a naki ɗakin ba ko? Tunda ai naga a ɗaki ɗaya kuke kwana ke da Khalil ɗin." "Aina'u bafa zai yuwu ki zauna a sama ba, don zaki shiga haƙƙin mijina da ni karan kaina. Kiyi zamanki anan zaki fi walawa." Ba tare da Aina'u tace komai ba ta buɗe ɗaya daga cikin ɗakunan dake a jere ta leƙa, girgiza kai tayi irin bai matan nan ba ta buɗe ɗayan, shima dai bata shiga sai da ta duba na ƙarshen sannan ta fito ta dawo na tsakiyar ta soma jera kayanta cikin, duk da halin da Sarah ke ciki sai da ta taimaka mata wajen jera mata kayan. Bayan sun gama suka dawo parlour. Ko zaman mintuna biyar bata yi ba ta tashi tare da faɗin, "Tunda ba'a man tayin abinci ba, bari nayi wa kaina." Tana gama faɗin haka ta shige cikin kitchen tana waƙa. Da idanu kawai Sarah ta bita sannan ta girgiza kai. Indomie ta dafa da kifin gwangwani sannan ta ɗauko avocado Juice ɗin da Aunty Maryam ta haɗawa Sarah ko zata ta fito ta zauna a ƙasa. Wani irin kakarin amai ta soma yi tare da toshe bakinta tayi hanyar toilet ɗin dake parlour ɗin da sauri ta soma sheƙa aman a ƙasa. Aina'u kuwa wani taɓe baki tayi tare da faɗin, "Gama shan baƙar wahalar tukun, amma baza ki taɓa ganin kwanki ba a duniya in dai ina raye! Shegiya mayya mai ɗuwawun saurin ɗaukar ciki. To kin ɗauki ciki ma ba tare da saduwaba, inaga kuma an sadun.. Shegiya mahaifar zan yi sanadin lalacewarsa inga ƙarshen saurin ɗaukar cikin naki" duk a zuciya tayi maganar yayin da tayi kwafa a fili ta cigaba da cin indomie ɗin ta." Sarah kuwa tun tana saka ran ganin Aina'un tazo kawo mata ɗauki har ta fidda rai. Aina'u kuwa bayan gama cin indomie ɗin ko plate ɗin bata ɗauke ba ta hau kan kujera ta ɗauki remote ta kunna kallo. Sarah kuwa ƙaramar azaba tasha ba don babu komai a cikinta sai tsabar wuya da take sha. Da kyar bayan ta wanke jikinta ta dawo parlour ɗin ta dunga birgima a ƙasa tana riƙe ciki. Duk abunnan da take yi ko sau ɗaya Aina'u bata ce mata sannu ba. A hankali ciwon cikin dake damunta ya kafa, jirin da take gani shima kamar anyi ruwa an ɗauke, lokacin bacci har ya ɗauke Aina'u a kan kujeran da take kai. Kallon Aina'un tayi tana mamakin taurin zuciya irin nata ganin duk malelekuwar da take yi ko sannu bai haɗata da ita ba. Infact tama ɗan ɗago taga halin da take ciki bata yi ba, amma a hakan take cewa tazo zama da ita domin taimakonta har ta haihu. Tashi Sarah tayi ta haura sama ta shiga jacuzzii tayi wanka da ruwa mai zafi sannan ta fito ta tada sallar la'asar kasancewar ta ɗauro alwala kamun ta fito. Riga kawai ta zura da dogon hijjab ta tada sallah, bayan ta idar ta isa gaban madubi ta tantsara kwalliya kasancewar Khalil ya kusa dawowa don sau da dama a gida yake sallar magrib. Wando ta sanya pallazo kalar emerald green da shirt mai button kalar grey sai ta kama jekar shirt ɗin biyu ta ɗaure ta gaba. Gashin kanta kuma tayi parking ɗinsa in a low ponytail jelar gashin ya zuba har gadon bayanta. Turensa _Imperial Majesty kaɗai ta fesa tare da saukowa ƙasa, tun daga kan steirs Aina'u ke ƙare mata kallo ganin wari irin kyau da tayi, tayi haske sosai hips ɗinta kuma sun ƙara cika. Tana saukowa kai tsaye kitchen ta nufa tare da buɗe fridge ta ɗauko can fanta wanda yayi mugun sanyi ta dawo ta zauna kan kujera tare da ɗauka ƙafa ɗaya a kan ɗaya ta buɗe fanta ɗin ta shiga sipping a hankali tana lumshe idanun. Aina'u kuwa babu abunda take yi sai aika mata da harara ta gefen idanu. "Zuwa anjima kamun Happiness ya dawo za muje can cikin gida ki gaido Hajiya da sauran mutanen gida." Faɗin Sarah ba tare da ta kalli inda Aina'un take ba." "Ok" shine abunda Aina'u tace tana mai faɗin, "Nine ajalin farin cikinki, kiji daɗinki iya jin daɗi kamun turn ɗina ya zagayo. An kusa fara yaƙin wallahi, yaƙi ne da yafi na biafra!" Sai da tasha rabin fantan nan sannan ta mayar dashi cikin fridge tare da komawa sama ta ɗauko ƙatoton hijjab har ƙasa ta saka ta dawo parlour tare da faɗin, "Ki taso muje cikin gidan." Miƙewa tayi tabi bayan Sarah da tayi gaba tana yi mata daƙuwa a baya. Sallama suka yi, babu kowa a parlour sai TV dake ƙara, "Zauna anan ina zuwa." Sarah ta nuna mata kujera tare da wucewa tabi corridor ɗin da zai sadata da ɗakin Hajiya. Ai'n kuwa sai bin parlourn ɗakin take yi tana jinjina kai tare da mamakin dukiyar da aka kashe wajen tsara gidan gaba ɗaya, don ko ina ka kalla babu ƙarya. Tare Hajiya da Sarah suka fito daga ɗakin kamar ƙawaye, don ita Hajiya ƴaƴa ta ɗauki matan ƴaƴanta ba surukai ba. "Sannu da zuwa Aina'u, ai kin kyauta da kika zo taya ƴar uwarki jinya, Saratu na shan wuyar laulayi, don ma dai yarinya ce mai dauriya." Faɗin hajiya tana zama a kan kujera. Har ƙasa Ai'n ta zamo tare da faɗin, "Ina wuni Hajiya, mun same ku lafiya?" Cike da jin daɗi Hajiya ta amsa da "Lafiya ƙalau, ya wajensu mahaifiyarku?" Aina'u ta amsa da, "lafiya ƙalau" sosai Sarah taji daɗin yanda Aina'u ta gaida Hajiya. Sun ɗan jima a nan ɗakin Hajiya kamun suka tafi ɗakin Aunty Maryam, Kallo ɗaya Aunty Maryam tayi wa Aina'u taji sam bata kwanta mata a rai ba, sai dai ta amsheta faram-faram. Basu jima a nan ba suka komai side ɗin Sarah ganin har shida tayi. Ko mintuna biyar basu yi da dawowa ba Khalil ya dawo, yana danna doorbell Sarah ta saki wani murmushi don ta san shine ta tashi ta nufi ƙofa ta buɗe tana yi masa wani irin kallon love mai sumar da wanda ake yiwa. Hannun biyu ya saka ya kama ƙugunta tare da jawota kusa dashi yana kallon cikin idanunta tare da faɗin, "Mine, kin San fa baki da lafiya amma shine kike neman tsokalata da irin wannan kwalliyar da dressing ɗin ko?" Aina'u dake zaune kan kujera sai leƙo kai take yi tare da dogon wuya tana jin takaici na neman kasheta. Wani lunshe idanu Sarah tayi tare da kwantar da kanta a kan ƙirjinsa tace cike da shagwaɓa, "Tun ɗazu ni da babynka muke son jin ɗumin jikinka, gaskiya an kusa fara tafiya dani asibitin nan." Rungume yayi sosai tare da faɗin, "Lallai kuwa duk lokacin da na ajiye ki a office babu abunda zan iya aikatawa, don wallahi bazan iya duba ko petient ɗaya ba. Muje Wife ki kula dani kamun a kira sallah." "Uhm!" Aina'u tayi gyaran murya don ta lura har Sarah ta mance da zamanta a parlourn balle kuma Khalil da bai san tana wajen ba. A tare Khalil da Sarah suka kalli inda Aina'un take, lokaci guda fara'ar fuskansa ya ɗauke don shi tun asali bai ƙaunar Aina'u tun da ta dunga maimaita masa ya rabu da Sarah su gidansu ba'a aure yaji ya tsane ta. Kuma haka nan duk lokacin da zai yi arba da ita sai gabansa ya faɗi. Bai taɓa jin ya tsani Na'ima ko Hassana, Marfu'a da Nuratu ba, su da ya sha ganinsu a hotels daban-daban da maza kala-kala, amma Aina'un da bai taɓa kamata da kowa ba, sai yake jin muguwar tsanarta. "Ina wuni?" Faɗin Aina'u tana wani kwarkwasa. "Lafiya" kawai yace tare da ɗaukar matarsa cak suka yi sama. Da idanu Ai'n ta bisu hawaye na zubo mata, duk suka haɗa idanu da Khalil, babu abunda take hangowa sai wutar ƙiyayyarta. Yanzu hakan ma abunda ta gani kenan, yana ganinta mood ɗinsa ya canza. "Wife naga Aina'u har wannan Lokacin, bata jima da zuwa bane?" Faɗin Khalil bayan ya ajiyeta a kan gado. "Ta jima da zuwa, nan zata kwana!" Shuru Khalil yayi bai son ya fito ƙiri-ƙiri ya nuna mata bai son zaman Aina'u da su a gidan don ko yaya Sarah zata ji zafi tunda ƴar uwarta ce ciki ɗaya. "Kayi shuru Happiness!" Faɗin Sarah. Murmushi yaƙe yayi tare da faɗin, "She's welcome! Ai akwai ɗakuna da yawa a gidan, idan ma nan bai yi mata ba, ga side ɗin Hajiya." Murmushin jin daɗi Sarah tayi tare da faɗin, "Thank you love, nan ɗin ma ya ishe ta, har na saka kayanta a bedroom ɗin dake ƙasa." Miƙewa yayi tare da faɗin, "Let me take a shower, yanzun nan zaki fara jin kiran sallar magrib." Ya faɗi hakane tare da soma cire kayan jikinsa ya rage daga shi sai boxer sannan ya shiga bayi. In a few minutes ya fito yana tsane jikinsa, ya samu har Sarah ta fito masa da kayan da zai saka. "Allah ya yi maki albarka Wife, jiki dai yana ta ƙara improving, ma sha Allah! Kin yi amai yau?" Gyaɗa masa kai tayi tare da faɗin, "Sau ɗaya kawai. Amma babu zazzaɓi sai ciwon mara, amma yanzu ban jin komai." "Ina sha Allah zaki zo ki daina gaba ɗaya." Ita ta taimaka masa wajen shiryawa. Yana gama saka kaya yayi mata kiss a goshi tare da fita daga ɗakin don an soma kiraye-kirayen sallah. Da ya sauko bai ga Aina'u a parlour ba, tsaki yayi tare da faɗin, "Da ƙafafuwan da kika zo zaki gudu. Na san maganin ki." Ya faɗi tare da ficewa daga ɗakin. Bai dawo ba sai da aka idar da isha'i. Yana shigowa ya sami Aina'u da Sarah a parlour suna hira, bai ce komai ba ya haura sama, ko gaba shigewa bai yi ba Sarah ta miƙe tabi bayansa. "Shegiya fitinanniya mayyar miji, za kici ubanki ne." Faɗin Sarah ƙasa-ƙasa. Tun daga nan bata ƙara jin motsi Sarah ba sai washe gari ƙarfe sha ɗayan safe, shima Khalil ta rako wande ke sanye da ash ɗin suit na kamfanin _Tom Ford_, gashin kansa yayi luwai-luwai yasha gyara. Sai ƙamshin _Imperial Majesty_ yake yi. Dama kuma Aina'u ta jima tana zaune tana duban hanya ta inda zasu fito. "Ina kwana? Har zaka fita kenan? Ka tsaya kayi breakfast mana na girka maka." Ba tare da ya kalleta ba yace matata ta riga ta bani abinci na kuma ƙoshi, Wife bye-bye ki kular min da kanki." Ya ƙarisa maganar yana mata kiss a goshi. Hannu ta ɗaga masa tana faɗin, "Allah ya tsare, kar dai ka bar min kanka da yunwa, ka tabbatar kaci abinci." "Ina sha Allah" ya faɗi tare da fita. Aina'u kuwa kamar zata fashe don baƙin ciki. "Sarah mai nayi wa mijinki ne? Naga kamar bai son zamana a cikin gidan nan." Kamo hanunta Sarah tayi tare da faɗin, "Kar kice haka Ai'n, Khalil nada kirki sosai, don dai baku saba bane kawai. Amma da kun saba zaki ce na faɗa miki." "To ni naga sai wani shashsha min ƙashi yake yi. Idan baku son zamana ai sai in tattara in wuce gida." Faɗin Aina'u. "kin cika ƙorafi wallahi, menene abun ɗaga jijiyoyin wuya haka? Sai dai idan kin gaji ne sai in tashi in ɗauko maki kuɗin mota a ɗaki." Faɗin Sarah. "To babu inda zanje ina nan a nan sai naga abunda ya turewa buzu naɗi." Aina'u ta faɗin cikin zuciya, amma a zahiri sai tayi gum. "Tashi muje side ɗin Hajiya." Faɗin Sarah tana miƙewa. Aina'un ma miƙewa tayi tabi bayan Saran. "Tooo, wannan mai suffar karuwai ɗin kuma daga ina, gashi dai tana ɗan kama da Aunty Saratu." Faɗin Laure cikin zuciya don jiya basu haɗu ba. Suna haɗa idanu, Aina'u ta sakar mata wani hararar da ya kaɗa ƴaƴan hanjinta tayi saurin kau da kanta. "Su Aina'u ne, sannunku ku ƙariso mana." Faɗin Hajiya tana nunawa Aina'un kujeran kusa da ita. Kamar mutuniyar kirki ta duƙa kamar jiya ta gaida Hajiya da kuma Aunty Maryam ɗin da tayi mata kallo ɗaya ta kau da kai. Laure kuma saurin juyawa tayi ta bar parlourn don kar ta gaida Aina'un don za su iya zuwa sa'anni ko Laure ta bata shekara guda. Anan suka yi yininsu, Sarah bazata taɓa iya tuna when last taga Aina'u na sallah ba sai yau da suka kai har la'asar a side ɗin Hajiya, amma kana ƙarewa sallar kallo zaka fahimci akwai naƙasu a cikinta, don dungure-dungure kawai take yi. Satin Aina'u guda, amma kullum bayan sun gama hira a side ɗin Hajiya sun dawo bata ƙara saka Sarah a idanu sai kuma gobe ƙarfe sha ɗaya ko sha biyu idan za tayiwa Khalil rakiya don tunda yayi aure bai cika fitar sassafen nan ba sai an kira shi emergency kasancewar akwai doctors a asibitin. Yau Aina'u ta shirya tsiyar da za tayi masu wanda zai hana su bacci, sai da ta bari dare yayi sosai sannan cire ribbon ɗin kanta ta hargitsa gashin kanta sannan ta kalli kanta sosai a madubi, daga ita sai wata transparent doguwar rigar bacci ko bra babu sai wani ɗan iskan pant mai igiya, murmushi tayi sannan ta isa wajen ƙofa ta fita ta nufi sama. Sai da ta isa ɗakin da ta tabbatar da nan ne suke ciki sannan ta riƙe handle ɗin ta soma jijjiga ƙofar da ƙarfi tana ihu tare da knocking. A wannan lokaci kuma Khalil na duniyar nishaɗi shi da matarsa suna raya sunna........... *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *24* Wani irin yunƙurowa Sarah tayi zata fizge jikinta tana faɗin, "Happiness ana buga ƙofa." Da hannunsa ya maida ita tare da yin kamar bai ji abunda take cewa ba ya cigaba da birkita tunaninta da salonsa, tuni ta manta da wani bugun ƙofa da ake yi. Aina'u kuwa jin babu alamun za'a buɗe Ƙofar kuma ta tabbatar ana ji, sai wani baƙin ciki ya tokare mata wuya ta cigaba bugun ƙofar da dukkan ƙarfinta. Khalil kuwa bai sararawa Sarah ba sai da ya samu nutsuwa tukun, lokacin har Aina'u ta gaji ta zauna a bakin ƙofar tare da haɗe kai da guiwa. Khalil kuwa sunkutar matarsa yayi tare da shiga bayi suka yi wanka sannan suka dawo suka kwanta ya ƙara masu gudun ac tare ja masu barko ya rungume abarsa suka yi bacci. Aina'u taci kuka kamar ranta zai fita, ba ita ta bar ƙofar ɗakin nan ba sai da taji kiran sallar farko sannan ta koma ɗakinta ta faɗa kan gado tare da rushewa da kuka. Da asubah Khalil ya tashi ya shiga bayi ya ɗaura alwala sannan ya fito ya tada Sarah sannan ya wuce masallaci. Kasancewar ranar asabar ce babu aiki, tun da ya haura sama suka koma bacci shi da matarsa, basu suka sauko ƙasa ba sai sha biyu. Aina'u kuwa ta leƙo yafi sau ba adadin domin ganin ko sun sauko ƙasan amma wayam sai ta gaji har bacci ya ɗauke ta kasancewar bata samu bacci ba. Kitchen ya shiga ya ɗauko mata can fanta ɗinta mai sanyi tare cupcake ya bata kasancewar ta ɗan fara iya cin cake ɗin. Bayan ta gama cin cake da fanta ɗin sai tayi matashi da cinyarsa tare da cire hular kanta shi kuma ya soma warware all back ɗin da Aunty Maryam tayi mata guda goma saboda ya fara tsufa, "Mine, idan mace kika haifa ko, sunanki zan mayar, idan kuma namiji ne...." Tun kamun ya kai ƙarshe tayi saurin faɗin, "Sunanka zaka mayar." Murmushi yayi tare da faɗin, "Mai yasa kika ce haka?" Juyo da kanta tayi tana facing ɗinsa tare da faɗin, "Saboda soyayyar da nake maka ne." Hancinta yaja tare da faɗin, "Nima haka love." Dai-dai nan Aina'u ta leƙo, hango Sarah kwance a kan cinyar Khalil yana yi mata tsifa suna hira cike da nishaɗi, sai taji kamar ta zazzagawa kanta petur ta cinnawa kanta ashana ta babbake. Komawa tayi cikin ɗakinta tana saƙe-saƙen abunda zata ɓullo dashi nan gaba. Tun daga wannan rana Aina'u bata ƙara gigin zuwa buga masu ƙofa ba, sai ta tsiri zama a side ɗin Hajiya da zaran ta tashi daga bacci, bata kuma dawowa side ɗin Sarah sai isha'i. Cikin ƙanƙanin lokaci Aina'u tayi wani irin mugun shiga jikin Hajiya. Sosai Hajiya ta sakar mata ganin yanda take yi mata biyayya don har wanki yi mata take yi duk da kuwa akwai mai wanki a gidan. Tun Sarah na mamakin shaƙuwar Hajiya da Aina'un har ta daina. Babu yanda za ayi Hajiya tayi magana ɗaya biyu bata sako sunan Aina'u ba. Laure baiwar Allah kuwa, tun da Aina'u ta dawo part ɗin hajiyan ta saka ta gaba da harara da baƙaƙen maganganu. A gaban Hajiya kuwa sai ta riƙa janta a jiki, ko aiki Hajiya ta saka lauren, sai tayi saurin tashi tayi tana mai faɗin, "Laure huta, ai wuni kike kina aiki." Laure dai sakin baki kawai take yi tana kallonta. "Ummin Moon, wallahi yarinyar nan ƙanwar matar Khalil da take shishshigewa Hajiya, sam bata yi min ba, kama take min da criminal. Akwai alamun rashin gaskiya a ɗabi'un ta. Baki lura da wani abu ba? Tsoro na take ji, duk lokacin na shiga side ɗin Hajiya da sauri take fita bata kuma dawowa har sai na bar ɗakin. Don Allah ki saka mata idanu kina kallon moves ɗinta kar taje ta cutar da Hajiya." Ajiyar zuciya Aunty Maryam ta sauke tare da faɗin, "Wallahi ka riga ni a fili ni kuma na riga ka a zuciya. Laure ta kawo min ƙorafi ba sai ɗaya ba tasha zaginta tana faɗa mata baƙaƙen maganganu, tabi ta kanannaɗe Hajiya ta shiga zuciyata sosai ta yanda baza ta yarda da duk abubuwan da zata aikata idan dai ba hujja ta gani mai ƙarfi ba." Girgiza kai yayi tare da yin kwafa. Bayan kwana uku, gaba ɗaya su Aunty Maryam suna zaune har da Sarah a parlourn hajiya, babu wanda ya lura da Aina'u lokacin da ta zare jikinta ta shiga ɗakin Hajiya. Bayan kwana biyu Hajiya ta tara su tana cigiyar gwala-gwalanta na kusan kimanin 175milions, kowa hankalinsa ya tashi har da Aina'u data zaro idanu tare da dafe ƙirji. Anan dai kowa yayi ta jimami yana tunanin wa zai sace, Aunty Maryam ta kalli Hajiya tare da faɗin, "Hajiya ko dai kin canza masu wajen ɓoyone kika mance?" "Maryamu ban taɓa canza masu wajen ɓoyo ba, duk wanda da ɗauki wannan abu yana sane dashi." Faɗin Hajiya. Karaf Aina'u tace, "Kuma Hajiya kin binciki Laure da kyau? Don naga kaf gudan nan ita kaɗai ke shiga ɗakinki kai tsaye." Da sauri Laure, Aunty Maryam har da Sarah suka kalli Aina'un jin furucinta, "Hajiya shekaru bakwai muna tare, idan ina da wannan hali na ɗauke-ɗauke da kin daɗe da sani tun tuni. Wallahi tun da uwata ta haife ni ban taɓa ɗaukar abun wani ba" faɗin Laure tana mai fashewa da kuka. "A ko wani irin lokaci ɗan adam ka iya canzawa Laure." Faɗin Aina'u tana hararen Lauren. "Ke Aina'u!" Faɗin Sarah a tsawace da sauri Hajiya ta ɗagawa Sarah hannu tare da faɗin, "Bana son in ƙara jin komai daga bakin kowa, ku tashi ku tafi ɗakunan ku. Sarƙa kuma zasu fito domin duk wanda ya ɗauka ba dai ya sayar ba, don duk inda yake sai an kama shi ko kama ta." Gaba ɗaya kowa ya tashi guiwa sage ya bar ɗakin. Suna shiga ɗaki Sarah ta ɗaga hannu ta wanke fuskan Aina'u da mari tare da faɗin, "Wallahi baki isa ki kashe min aure ba, kina hauka ne? Ko baki san Laure ƴar uwarsu bace da har zaki jefeta da wannan mummunar ƙazafin? To bari kiji, ba zan iya da iskancinki ba, ki shiga ɗaki ki tattaro duk wani abu naki kizo ki wuce gida, ina zaune cikin rufin asirina kizo ki tada min hankali, to ba zai yiwu ba. Dama ba wani uban abun kike tsinana min ba, maza tattaro kayanki ga kuɗin mota ki bar min gidana." Hannu akan fuska Aina'u tace, "Ni kika mara Saratu har kina faɗin in bar maki gidanki? To zan tafi, amma sai kinyi nadama mafi muni a rayuwarki! Baki san true colour ɗina ba, amma zan fito maki dashi. Ba dai miji kike taƙama dashi ba, mu zuba mu gani, gaki ga mijin nan." Tana gama faɗin haka ta shige cikin ɗayan parlour ɗin da zai sadata da ɗakinta. Jakarta ta kinkimo ta fito bayan ta canza kaya ta shafa aboniki a idanunta, nan da nan idanunwan suka kaɗa su kai jazur kamar taci kuka ta ƙoshi. Bata taras da Sarah a parlourn ba, sai kawai ta saka kai ta fita daga ɗakin. Sai da ta ajiye akwatinta sannan ta buɗe ta ɗauki wani abu cikin wani ƙatoton box tare da nufa side ɗin Hajiya, Laure ta taras a parlour sai da ta dungure mata kai sannan ta wuce bedroom ɗin Hajiya tare yin knocking haɗe da sallama. Daga ciki Hajiya ta bada izinin shiga, tura ƙofar tayi tare da zama a ƙasa tana kallon tiles ɗin dake shimfiɗe, Hajiya dake tsakiyar gado tana duba wasu kaya ta kalleta tare da faɗin, "Aina'u lafiya?" Kuka Aina'u ta fashe dashi tare da faɗin, "Hajiya kiyi haƙuri, amma yanda kika ɗauke kika riƙe ni tamkar ƴarki ya saka ba zan iya bari a haɗa baki dani a cuceki ba, ga sarƙan ki, Saratu ce ta sace tare da haɗin bakin ƴar aikinki Laure.........." _Dan Allah kuyi haƙuri bana jin daɗi ne shiyasa kuka jini shuru. Yanzu ma cewa nayi bari nayi naku ko kaɗan ne yafi babu_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *25* "Yanzu haka Hajiya ta koreni daga gidan nan saboda na faɗa mata gaskiya abunda take yi bata kyautawa. Yanzu hakan sarƙan nan bata nan na ɗauko shi na kawo maki ba. Nasan za kiyi mamaki mai yasa na tona mata asiri tana matsayin ƴar uwata, to nayi hakan ne saboda na tseratar da ita ganin tayi aure gidan mutunci, bana so aurenta ya mutu sanadin abubuwan da take aikatawa. Shi kansa Khalil ɗin ba jin daɗin zama da ita yake yi ba, a wannan ɗan zaman da nayi na fuskanci haka, kullum cikin ƙorafi take yi masa akan dole sai ya saya mata gida a wani waje ita bata san zama waje ɗaya da uwar miji da matar ƙani ko wa, tafi son zama ita kaɗai ta wala. Hajiya baki ga irin ɓarnar kuɗin da Sarah take yi ba da dukiyar ɗanki, duk abunda tace kamar ta shanye shi, jiki na rawa yake yi mata. Hajiya sai fa kun tashi tsaye sosai akan Khalil!" Hajiya baki sake take bin Aina'u da kallo tana mamakin ƙaramar yarinya irin wannan da hassada da kuma iya tsaro zantukan ƙanzon kurege, don tun daga furucinta na farko ta fuskanci inda ta dosa, babu abunda ke damunta illa tsantsan hassada da mugun hali. "Ina so tambayarki." Hajiya ta faɗi still tana kallon Aina'un. Gyara zama Aina'u tayi har da matsar hawaye tare da faɗin, "Ina jinki Hajiya." "Ke da Saratu uwa ɗaya uba ɗaya kuke?" Jinjina kai Aina'u tayi tare da faɗin, "Uwarmu ɗaya ubanmu ɗaya da ita Hajiya, halin ne kawai ba ɗaya ba." Hajiya tsuke fuska tayi tare da faɗin, "Tabbas kuwa hali ba ɗaya ba. Amma Allah yayi wadaran naka ya lalace! Yanzu saboda lalacewa da rashin hankali da tunani, ƴar uwarki ciki ɗaya kike yiwa baƙin ciki da hassada? Duk wani mai hankali idan yaji wannan magana da kika yi ya san cewa ke munafuka ce kuma baki ƙaunar ƴar uwarki. Ina matsayin uwar mijinta, shine zaki zo kina faɗamin maganganun ɓatanci akan ƴar uwarki saboda naji haushinta! To ki sani, na san wacece Saratu, tun lokacin da aka kawota cikin gidan nan nake lura tare da karantarta, yarinya ce mai natsuwa da hankali. Laure kuma shekaru bakwai kenan muna tare da ita, bata taɓa ɗaukar min ko mayafi ba balle kuma sarƙa. Bata ma san darajarsa, kuma yanda nasan tarbiyyarta da halinta baza ta taɓa amincewa a haɗa baki da ita ba domin a cutar dani. Kuma ni tun ɗazu na fahimci ke kika ɗau sarƙoƙin nan saboda yanda kika riƙa tada jijiyoyin wuya, na rabu dake ne domin inga iya gudun ruwanki don na riga na san baza su taɓa saiduwar maki ba duk inda za kije don sai kin bata risiti (receipt). Kalle ni da kyau, mahaifiyarki ma na haifeta, baki isa kiyi min makirci da wayau ba, kuma auren Khalil da uwata Saratu, mutuwace zata raba shi in Sha Allah. Ba Saratu da take ƴar uwarki ba, Ni kai na mahaifiyar Khalil ban amince ki ƙara tako ƙafarki cikin gidan nan ba. Kuma kin san dai ina da ƴaƴa hukumomi ko? Tashi ki ɓace min da gani tun kamun na wanke fuskanki da mari!" Aina'u da baƙin ciki tarkon da ta ɗana bai kama ba ta miƙe tana yiwa Hajiya wani irin kallo sannan ta juya fuuu ta fita tare da rufo ƙofar da ƙarfi. Laure na zaune ta zubawa talabijin idanu taji saukar mahaukacin rankwashi a tsakiyar ka sai da ta kwanta flat a ƙasa tsabar gigicewa. Dawowa tayi daidai kanta tare da faɗin, "Sai na zama ajalinki, shegiya mummuna!" Tana baro part ɗin ta tsaya tana mamaki domin bata taɓa kawowa a ranta wannan makircin da ta haɗa ba zai yi aiki ba. "Hajiya kin jawowa kanki bala'i da masifa da tashin hankali! Kin yi kuskure tura hannunki a ramin maciji kuma wallahi sai ya ɗanɗana maki zafin dafinsa...." Tana gama faɗin haka ta ja akwatinta ta wuce ta bar gidan. Bayan fitar Aina'u a ɗakin Hajiya, Hajiya ta zabga tagumi tare da faɗin, "Duniya ina zaki damu ne? Ɗan uwanka ciki ɗaya amma shine ke yi maka hassada da baƙin ciki, kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Allah kasa mu cika da imani, Saratu ce dai zama daram dam a gidan nan in Sha Allah!" Wani ajiyar zuciya Sarah ta saki lokacin da ta tabbatar Aina'u ta bar gidan. Kitchen ta shiga domin haɗawa Khalil abinci don ya kusa dawowa. Bayan ta kammala girkin ta haura sama ta cancaɗa wanka ta saka wata doguwar rigar shadda pink colour wanda yasha aiki da baƙin zare, ɗaurin ɗan kwali tayi mai kyau sannan ta fesa turare ta ƙara kallon fuskanta a madubi ta saki murmushi tare da fita ta sauko ƙasa ta zauna a kan kujera ta ɗaura ƙafa ɗaya akan ɗaya tana kallon tanƙameman plasma tv ɗinta dake haska film ɗin _Mohabbatain_ a tashar Bollywood. Da sauri ta miƙe jin ƙarar door bell, buɗe Ƙofar tayi tana kallonsa. Shima kallon nata yake yi daga sama har ƙasa yana faɗin "Ma sha Allah!" Cikin zuciyarsa. Hannu ta kai ta karɓi jacket ɗin hannunsa da ya ratayo tare da kai bakinta saitin kumatunsa ta sakar masa kiss tare hura masa fuska tace, "Kar fa a cinye ni." Hannu ya kai zai cafkota tayi saurin ja baya tana dariya, "Ki tsaya ki gani idan ba'a cinyekin ba." Gwalo tayi masa tare da faɗin, "Ka kama ni idan zaka iy....." Ko kamun ta rufe baki har ya iso inda take ya cafki hannunta biyu tare da haɗata da ƙirjinsa yana mai faɗin, "Ni da zan iya haɗiye kin ma da na huta da kewarki, kullum na fita aiki sai kin hanani sukuni, domin da zarar na bar gida, kece kike min gizo a ko ina." Hannun ta saka ta rungumosa tare da faɗin, "To ni dai matsalata kar dai garin yi maka gizo kaje kaga wata macen ka ɗauka nice kawai kace mata, Ina son ki! Tabbas zuciyata zata buga daga nan." Janyeta yayi daga jikinsa tare da kama hannunta suka nufi sama yana mai faɗin, "Wannan kalmar mai tsada ga macen biyu kawai nake furtawa, Hajiya da kuma ke, bayan ku, babu macen nan gaskiya." Ƙanƙame hannunsa tayi tare da faɗin, "Ina son ka, ina sonka sosai." Bakinsa ya kai dai-dai kunnanta tare da faɗin, "Muje ciki a nuna min!" Tsungulinsa tayi a damtsensa tare da yin dariya. Bayan kwana biyu, Khalil ya fahimci Aina'u bata gidan, hakan ba ƙaramin daɗi yayi masa ba, amma ko a fuska bai nunawa Sarah ba, kuma bai taɓa yi mata maganar ya akai baya ganin Aina'un ba, ita ma kuma bata yi masa maganar ba. "Aunty Rose Merry, ina son don Allah ki kai ni wajen _Hell Ofulafula_ da kike bani labarinsa, amma kar ki bari ko Lami ta sani, ya zama sirri tsakanin mu kamar yanda muka saba." Aina'u ta faɗi bayan ta kamo hannun Aunty Rose Merry ɗin bibbiyu. Aunty Rose Merry da kallon mamaki ta bita tare da faɗin, "Lili mai za kije kiyi a wajen _Hell Ofulafula_? Kin san wanene Hell kuwa? Ko daga jin sunansa kawai ya isa ya firgita ki, ganinsa kuwa, kamar bala'i ne a wajenki." Aunty Rose Merry ta girgiza kai tare da cigaba da faɗin, "Baza ki iya da Hell ba, dokokinsa nada tsauri, bazan baki wannan shawarar ba, domin zai saka ki aikata wani mummunar abu mai girma wanda Yesu Almasihu ba zai yafe maki ba, gwara dai kije wajen _Iya fulowa_, itama ta iya aiki sosai. Wai ma menene za kiyi? Wa kike so ayi wa wani abun!" Faɗin Aunty Rose Merry. Sake hannunta Aina'u tayi tare da ɓata rai ta juya baya tana faɗin, "To shikenan! Amma ni duk abunda kika saka ni, ina yi maki kai tsaye, har babana na cutar saboda ke, amma ni baza ki iya mun ɗan ƙaramin alfarmar nan ba, ashe soyayyar da kike min na ƙarya ne, saboda ke na koma addinin Christian, na kwana arba'in da biyar a cikin ɗakin duhu daga Ni sai pastor William yana min wankan zunubi tare da amfani dani, ya aske min gashin kaina, ya saka na kwanta kamar dabba ina shan nonon kare duk saboda ke, amma shine baza ki iya min wannan ƙaramin abun ba. Shikenan!" Ta ƙarisa maganar tana mai fashewa da kuka. Jawota Aunty Rose Merry tayi tare da faɗin, "Kiyi haƙuri Lili, ba dai _Hell Ofulafu_ kike son zuwa ba?" Gyaɗa kai Aina'u tayi tana share hawayen fuskanta, "To ki kwantar da hankalinki, zan kai ki wajensa, sai dai tafiya ne mai nisa, don a Abia yake can wani ƙauye mai nisan gaske, kuma shi bai jin yaren Hausa, bai jin English, sai Igbo, yoruba da ifem." Wani murmushi Aina'u tayi tare da faɗin, "Wannan ba matsala bane Aunty, ba sai kin raka ni ba, kiyi kwatanci kawai." Shuru Aunty Rose Merry tayi mai tsayi kamun ta saki ajiyar zuciya ta soma zayyano mata kwatanci tsaf har da yanda zata samu tafintan da zai riƙa faɗa mata abunda Hell yace da kuma ita abunda zata ce masa. Bayan kwana biyu Aina'u ta shirya kuɗi tsaf tare da ɗaukar hanyar Abia ba tare da sanin kowa ba idan aka cire aunty Rose Merry, awanni goma sha ɗaya da rabi suka yi a mota kamun suka isa kuma cikin dare. Aina'u ta zauna, ta mike ta rasa inda zata saka kanta saboda gajiyar zaman mota. Taji waƙa a wayarta har na Allah ya isa Kasancewar ta tafi da power bank har taji ya fita a cikin ranta. Hotel ta kama ta kwana, washa gari da sassafe ta nemi wanda Aunty Rose Merry ta Bata number ɗinsa, sai da suka yi ciniki ta bashi 50k kuma ita za tayi masa kuɗin motar zuwa can sannan suka ɗauki shatar mota zuwa *_Asaokpuaja_*. Tafiyar awa Shidda ce ta kai su can, nan ma ɗin mai motar jiransu yayi a bakin wani hanya sabida mota baza ta iya shiga ba, nan ma suka soma cin uban tafiya, sai da suka yi tafiyar awa ɗaya da rabi sannan suka isa wani ƙatoton baƙin gunki wanda aka yi masa penti da jar kala, da mugun gudu Aina'u ta koma bayan Ugo ta ɓoye saboda yanda gunkin ya tsoratata da girmansa, "Una no hear wetin I say before we come here? I tell u say make u no fear if you see anything, because _Hell Ofulafo_ dey look you through here." Yayi mata nuni da ramin hancin gunkin. Ai sai Aina'u ta ƙara kiɗimewa! Wani sautin mara daɗi ciki wani harcen yare ya soma magana a kausashe, take Ugo ya kai ƙasa tare da yin sujada sau uku sannan ya miƙe ya harɗe hannayensa kamar mai neman gafar ya shiga magana cikin yare na kusan sakan sittin sannan ya yuyo ya kalli Aina'u tare da soma yi mata magana da gurɓataccen turanci, "Hell yace ace maki idan baki shirya ba, ki koma gida, idan kuma kika ƙara tsorata anan wajen sai ya maida fuskanki tana kallon ƙeyarki, idan kuma kin shirya kiyi sujada a gaban gunkin nan sau uku." A take Aina'u taji duk wani tsoron da take ji ya fece musamman da ta tuno korar karen da Sarah tayi mata daga gidanta. Zubewa tayi tare da yiwa gunkin sujada sau uku, ana ukun ba tare da ta ɗago ba taji wani irin guguwa mai ƙarfi ya taho ya lulluɓesu, bata kuma buɗe idanunta ba sai a gaban wani garjejen tsohon inyamure jikinsa gaba ɗaya guraye ne, ya kasance irin zabiyan nan ne, domin idanunsa ma basa tsayuwa waje ɗaya. Gaba ɗaya jikinsa yayi ƙuda-ƙuda. Kallo ɗaya yayi wa Aina'u ta soma jin wani irin zawo. Wani mummunar dariya ya ɓarke da ita tare da soma surkulle cikin yaruka daban-daban. Wani ƙatoton tulu ne ya bayyana a gabansa, kallon Aina'u yayi sannan ya kalli tukun sai ga Aina'u cikin tulun, gaba ɗaya komai ya faru ne cikin daƙiƙu biyu. Jan zare ya ɗauko tare da jan mayafi ya kulle tulun tare da ɗauresa. Da sauri Ugo ya miƙe tare da yiwa _Hell Ofulafu_ sujada sannan ya soma tafiya da baya da baya har ya fuce. Sai da Aina'u ta kwana bakwai cikin tulun nan sannan tulun ya face sai gata a watse a ƙasa daga ita sai ɗaurin ƙirji da baƙin zani da jan ɗan kwalin da bai rufe tsakiyar kanta ba. Sai da ta kwashi mintuna talatin tana kwance ko motsi bata yi sannan _Hell Ofulafu_ ya miƙa tare da ɗaga hannu sama sai ga ƙaramin tulu a hannunsa, hannunsa mai tsini ya caka a jikin tulun, take ya soma tsiyayar da jini mai kauri da wari shi kuma ya shiga zagaye Aina'u da tulun sau bakwai. A firgice ta farka tana mai buɗe baki tana shan jinin nan dake tsiyayowa daga cikin tulun. Bayan ya gama wannan ya jawo wata tulun mai ɗauke da wani irin ruwa mai ya ajiye a inda take tare da saka hannu ya fizge zanin jikinta da ƙarfi. Wani abu ya ɗauko mai kama da kofi sannan ya ɗaga hannunsa sama sai ga wata murtukekiyar bulala, idan ya tsiyaya mata ruwan sai ya shauɗa mata bulalan sau biyar a ko ina na jikinta. Sai ruwan nan ya ƙare tas a jikinta, gaba ɗaya jikin nata yayi wani irin ruɗu-ruɗu. Aina'u tayi suma ya kai goma saboda azaba. Ugo na gefe yana kallon komai, kuma dama ya san sai _Hell Ofulafu_ yayi mata hakan, ta hakane yake cire sauran imanin dake jikin duk wanda ya kawo kansa wajensa. Shi da kansa ya barbaɗa mata wani magani a jiki tare da kallon Ugo yace masa ya kaita masaukinta idan ta gama warwarewa sai su dawo ta faɗi buƙatunta. Ugo mai mayar da ita ainahin cikin garin Abia ba saboda nisa, wani bukka ya kaita suna kwana tare, kuma bai barta haka ba kullum sai ya kwanta da ita. Tana ji kuma tana gani amma bata da ƙarfin da zata iya dakatar dashi. Sai da ta kwana goma sha biyu kamun ta samu lafiya. Babu abunda ke huruwa cikin zuciyarta sai wutar ƙiyayyar Sarah da kuma ƙudurin ɗaukar fansa, don duk abunda ya faru da ita a garin Abia kacokan ta ɗaurawa Sarah laifi. Shikuwa Ugo sai sunne-sunne yake yi ya ɗauka Aina'u za tayi bala'i akan kwanciya da ya riƙa yi da ita duk da kuwa ba budurwa ya sameta ba, amma sai ya ga ko kallonsa bata yi ba idan banda ma takura masa da tayi akan su koma wajen _Hell Ofulafu_. Suna shiga ta taras dashi yayi zaman yoga idanunsa a rufe, zama suka yi suna jiran ya gama abunda yake yi, sai da ya kwashi awa guda shi ba a ƙasa ba kuma ba'a sama ba. A tsawace yayi magana da wani yare yana kallon Aina'u da idanunta ke a ƙasa. A kunnanta Ugo ya raɗa mata, "He say make u look his eyes." Ɗagowa tayi suka haɗa idanu dashi, take taji wani zafi mai tafe da raɗaɗi na shiga idanunta. Cikin yare _Hell Ugo_ yace cikin yare, "Naga muradinki a cikin idanunki, surukar yayarki, ƴar aikin gidan, da kuma ita kanta yayar taki, kina so a shiga tsakanin su sannan kuma kina son koma gidan, kuma mahaifiyar mijin yayarki da kika mutu akansa kike so ta buƙaci dawowarki gidan da kanta." A kunne Ugo ya fassara mata. Cikin sauri ta shiga jinjina kanta. "Ajiye rabin miliyan ki tafi." _Hell Ofulafu_ ya faɗi yayin da Ugo ya faɗa mata abunda yace, take ta ajiye masa kuɗin kasancewar tazo dasu. Da hannu ya nuna masu su fita. Bayan sun fita can bukkar suka koma, a ranar ma sai da Ugo ya kuma amfani da ita, washa gari ɗan taxi yazo suka koma can cikin garin Abia, kasancewar ta gaji sosai, bai bata bi motar dare ba, a daren ta yanki tiket ɗin jirgin da zai tashi ƙarfe goma. Yau ya kasance ranar asabar Khalil baya zuwa aiki, zaune suke akan dinning suna cin lunch wanda Khalil ne ya dafa masu wata taliya mai uban romo wai ita Paraguay fried superghetti. "Ni dai tunda nake a rayuwata ban taɓa ganin fried superghetti da ruwa a jikinta ba." Faɗin Sarah bayan ta kalli plate ɗin dake gabanta. "Daɗina dake baki da fahimta wani lokacin. Ance maki sunansa Paraguay fried superghetti!" Jinjina kai Sarah tayi tare da faɗin, "Eh tabbas nagane!" Yanda tayi maganar da shaƙiyanci ya saka Khalil ya zaburo ita kuma ta miƙe da sauri suka shiga zagaye dining ɗin. Daga ƙarshe dai ya kamata tare da cicciɓanta suka yi sama yana faɗin, "Kin ce taliyar babu daɗi amma har da su kashe kwano." "Nifa bance babu daɗi ba, kawai romon ne yayi yawa." Faɗin Sarah dai-dai lokacin da ya sauke ta tsakiyar gado tare da faɗin, "A taimakawa likita yaji ɗumin matarsa, kwana biyu ana ta yi min rowa." Miƙewa tayi tare da faɗin, "Nima ina son jin ɗumin nawa mijin, bari nayi fitsari na dawo." Shafa cikinta da ya ɗan turo tare da faɗin, "A siyar min da fitsarin" Da sauri ta sauko daga kan gadon tare da faɗin, "Ka san dai fitsarin mai ciki bai riƙuwa ko?" Ta faɗi hakane tare da saurin shiga bayi, yanda fitsarin ya matseta ya saka tana shiga ta ɗuka a ƙasa ta soma fitsarin. Wani irin bugawa zuciyarta yayi tare da zaro idanu tana kallon jajayan mitsi-mitsin ƙananan tsutsotsin dake fitowa daga cikin gabanta, miƙewa tayi tare da kwala wani uban ƙara ganin tsutsotsin kamar tuttuɗosu ake yi............. _Alhamdulillah! Na samu lafiya. Nagode sosai da addu'o'ini, my besty (Queen Zarah) thank you Soo much for the concern. Allah ya barmu tare." 🥰😍😍 *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *26* Khalil har sai da yayi wani muguwar faɗuwa saboda yanda ya duro daga kan gadon tsabar rikicewa don duk a tunaninsa faɗuwa Sarah tayi a toilet ɗin. Burum ya faɗa bayin yana ware idanunsa, ganinta yayi ita bata duƙa gaba ɗaya ba kuma ita bata miƙe ba, ƙafafunta sai rawa suke yi, "Laf......." Bai ƙarisa cewa lafiyan ba ya waro idanu yana faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Sarah menene wannan haka? Daga ina suke fitowa?" Ya faɗi yana mai ɗage skirt ɗinta sama sosai. Da sauri ya mayar ya sauke gabansa na bugawa saboda yanda yaga tsutsar na fitowa da gudu kamar fitar jini, wasu ma a dunƙule suke fitowan. "Na shiga uku na, Wayyo Allah shikenan mutuwata ce tazo ta haka!" Faɗin Sarah tana mai ɗaura hannu a kai. Janyota jikinsa yayi tare da faɗin, "Haba mine, sai kace ba musulma ba! Menene na ihun da faɗin irin wannan maganar? Idan kika mutu ni kuma inyi yaya? Bafa wani abu bane na tashin hankali, da yawan mata suna samun irin wannan matsalar. Ki kwantar da hankalinki Allah zai warkar dake cikin ƙanƙanin lokaci zaki ce na faɗa maki. Kuma ma kin manta mijinki likita ne?" Ya faɗi hakan yana sakar mata murmushin tare da ɗaukar ƙatuwar butarsu ya taro ruwan zafi sannan ya dawo inda take tana kuka ya duƙar da ita tare da saka hannunsa ba tare da ko ɗigon kyama ba ya dunga wanko tsutsotsin nan suna zuba a ƙasa. Sarah kuwa ganin yanda jajayan mitsi-mitsin tsutsotsin ke zubowa yayin da Khalil ke wanko su dai ta daɗa rikicewa tana kuka sosai tare da damƙe kafaɗunsa. Sai da yaga tsutsotsin sun daina fitowa sannan yayi mata wanka tare da ɗaukota ya dawo da ita kan gadon don har wani mummunar zazzaɓi ya saukar mata. Ya juya zai sauka daga kan gadon domin wanke bayin don tsutsotsin na nan a ƙasa da uban yawa, caraf ta riƙe hannunsa tare da faɗin, "Doctor meke damuna? Zan warke kuwa? Meke kawo tsutsotsi a gaban mace?" Dariya da wani irin mugun tausayinta ne ya rufe shi jin sunan data kirasa dashi da kuma irin tambayoyin data jero masa, zama yayi bakin gadon tare da janyota jikinsa gaba ɗaya ya rungume tare da faɗin, "Ki kwantar da hankalinki Sarah, nace maki wannan ba wani abu bane, ko wata biyu baya da suka wuce naga irin wannan same problem ɗinnan ga wata tsohuwa. Hakan na iya faruwa when Scratching the anus or vagina, or wiping them after going to the toilet. This can cause the eggs to stick to your fingertips or under your fingernails. If you don't wash your hands, the eggs can be transferred to your mouth or on to food or objects, such as toys and kitchen utensils. Amma akwai maganinsa kuma zaki warke in Sha Allah." Sarah dai jinsa kawai take yi amma bata cikin duniyar da yake ciki, ta jima da tsundumawa kogin tunani da tashin hankali. Addu'a ya shiga tofa mata ganin yanda take zabura har bacci ya ɗauketa sannan ya shimfiɗar da ita ya koma cikin bayin, sai da ya saka handglove ya ɗibi tsutsotsin ya saka a wani container sannan ya wanke bayin tass yayi wanka. Yana ƙoƙarin saka riga ya soma jin ƙarar door bell babu ƙaƙƙautawa, da sauri ya ƙarisa saka t-shirt ɗin ya fito daga ɗakin ba tare da ya lura da zaburar da Sarah tayi ba. Da uku-uku yake tsallake steps ɗin har ya isa ƙofar ɗaki ya buɗe Ƙofar, da Aunty Maryam yaci karo hankalinta a tashe tana kuka, "Lafiya Aunty Maryam, meke faruwa ne?" Da hannu Aunty Maryam tayi masa nuni da side ɗin Hajiya tana faɗin, "Khalil, Laure! Laure ce ke ta aman jini guda-guda, kuma maganarta ya ɗauke." Wani waro idanu yayi tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Ya faɗi hakane tare da nufar side Hajiya da saurinsa, yana zuwa ya kuma taras da gigitacen tashin hankali, "Hajiya tayi wani irin mugun kumbura kamar fulawar da aka kwaɓa da fulawa, wuyarta yayi wani abu kamar mai maƙoƙo ya kuma zazzago, haka ma idanunta, naman ƙasan ya zazzago, babu abunda take yi sai jujjuya kai tana hawaye don ita kaɗai ta san azabar da take ciki. "Maryam ina wayarki, kira mijinki yanzun nan yazo, kira shi nace maki" Khalil ya ƙarisa maganar a tsawace. Aunty Maryam da gudu ta fita zuwa ɓangarenta don a can ta bar wayan jikin caji. Khalil sai ya rasa inda zai saka kansa, ga Laure a gefensa na aman jini tana ƙoƙarin yi masa magana amma babu murya, ga kuma Hajiya na malelekuwa a jikinsa kasancewar ya rungumeta sai kiran sunansa take yi tana faɗin ya taimaka ya cire mata ciwon dake jikinta. A can ɗaki kuwa bayan fitar Khalil Sarah ta fara kwararo uban aman jajayan mitsi-mitsin tsutsotsin nan ta baki ta hanci, ga wani uban tusosi da take saki kamar an buɗe masai tsabar wari, gaba ɗaya ta ɗume ɗakin da wari ga kuma tsutsotsi ko ta ina, gadon gaba ɗaya ya zama abun kyama. Sarah ta suma fiye da sau biyar tana farfaɗowa. Cikin abinda bai wuce mintuna sha biyar ba sai ga Ya Abdul-Hakeem a kan bike don gani yayi idan yace zai yi driving lokaci zai ɓata da yawa, ko kamun ya iso Laure ta fita daga hayyacinta ko motsi bata yi, Hajiya kuma cikin hukuncin ubangiji kumburin jikin da kansa ya saɓe amma kuma sai ta dawo kamar ƴar yarinya sannan zazzagowar da idanunta yayi yana nan da wannan abun da ya fito mata a wuya kamar maƙoƙo. Cak Khalil ya ɗauki Hajiya kamar yarinya ya sakata a bayan mota, ya Abdul-Hakeem kuma ya cicciɓo Laure wacce bata da maraba da gawa.. Khalil wajen Aunty Maryam ya nufa tare da faɗin, "Maman Moon dan Allah ki duba min Sarah a ɗaki itama bata da lafiya sosai." Jinjina kai tayi tare da faɗin, "Babu matsala Khalil, Allah ya basu lafiya dukansu." Da "Ameen" ya amsa tare da saurin shiga cikin motar ya Abdul-Hakeem yaja motar suka bar gidan. Suna fita Aunty Maryam ta nufi ɗakin Sarah domin dubata, tunda Sarah tazo gidan bata taɓa shigar mata ko ɗayan parlourn ƙasa ba bare kuma bedroom, yanzu haka ma sai da tayi tsaam kamun ta haura sama, tun daga last step take jin wani irin unbearable wari mai tada zuciya, nan da nan wani irin miyau ya soma taruwa a bakinta dama kuma ita sam bata shiri da wari, bama ita ba, gani take gaba ɗaya zuri'arsu basa ƙaunar wari, haka ma zuri'ar mijinta (Kun san dai mutanan mai duguri wajen ƙamshi 🤪) musamman ma Khalil mai wanka da turare. Haka dai Aunty Maryam ta dunga ɗauke numfashi, don tana ƙara kusanta kanta da ɗakin Sarah, mahaukacin wari na ƙaruwa. Hannu ta saka ta murɗa handle ɗin ƙofar ta shiga ɗakin, da mugun sauri ta dawo baya ta dafe ƙirji tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Allahumma arji'ini fi musibati!! La ila ha'illallahu Muhammadur Rasulullah, Allahumma la sahala illa maja'altahu sahala!!" Yanda ƙirjinta ke bugawa da sauri-sauri ka ce ƙararrawar mutuwa aka buga mata, sai kawai ta fashe da kuka tare da komawa ɗakin bayan ta saka hannu ta toshe hancinta. Babu abunda Sarah keyi sai miƙa mata hannu alamar ta ceceta, Aunty Maryam kuwa ta kasa ƙarisawa gareta saboda wasu uban tsutsotsin dake mamaye a kan gadon zuwa ƙasa da wuyanta saboda amansu da ta gama yi yanzu. "Sarah meke damunki? Inna lillahi! Wannan wani irin abu ne kuma?" Faɗin Aunty Maryam cikin kuka. "Aunty Maryam mutuwa zan yi!" Sarah ta faɗi tana mai sakin wani irin mahaukacin tusa mai mummunar warin fitar hayyaci tare da wani irin kakarin amai, sai ga aman tsutsotsin nan na fitowa da uban yawa daga bakin Sarah kamar zata mutu, "Wayyoo, wayyoooo Aunty Maryam, Wayyo Allah cikina." Da mugun gudu Aunty Maryam ta fita daga ɗakin don tabbas idan ta kuma minti ɗaya ita ce zata mutun ba Sarah ba, don irin warin da Sarah keyi ba mai misaltuwa bane, tsutsotsin nan banda ta gabanta har ta duburanta fita suke yi, ba suyi mata ƙaiƙayi kuma basu cizonta, amma kuma ganinsu kawai abun tsoro da tashin hankali ne mai girma. Aunty Maryam na fita wuce ɗakinta tana wani irin kukan tausayin halin da Sarah take yi, tunda uwarta ta haifeta bata taɓa ganin kalar wannan cutar ba. Wayarta ta cire daga caji sannan lalubo number ɗin Khalil ta danna masa kira, lokacin shi kuma suna can kan Laure suna ƙoƙarin ceto rayuwarta, sun samu sun tsayar da aman jinin, amma kuma maganarta ya ɗauke gaba ɗaya. Duk irin ihun da za'a yi, ƙarshe ma ko magana aka yi mata a kunne, bata jin komai. Kuma abunda yafi bawa likitoci mamaki, basu ga musabbabin faruwar haka ba. Hajiya kuma suger kawai suka gani sai kuma da kidney wanda Khalil ya san dasu, sai suka bar kumburin jikin Hajiya akan ciwon suger ɗin sanadi, ita kuma Laure babu taƙamaimai musabbabin ciwonta. Haka wayar Khalil dake silent yayi ta ringing yana yankewa. Cikin lokaci ƙanƙani Nafeesa autarsu Khalil, gata da tsohon ciki sai kuka take yi, lokacin da taga Hajiya da kuma yanda halittarta ya dawo, yanke jiki tayi ta suma tana farfaɗowa labour yace gani nazo, dama kuma ashe jiyan kwana tayi da ciwon mara, Kasancewar irin naƙudar Hajiyan suke yi, cikin mintuna talatin ta haifo ƴarta mace. Hankalin Nafeesa bai ɗan kwanta ba, sai da taga hajiyan ta ɗauki jaririyar da kanta tana yi mata addu'a, don Hajiyar bata jin komai a jikinta na ciwo sai damuwar halin da Laure take ciki, yarinya marainiya babu uwa babu uba, dangi sun watsar da ita bata nan bata can kamar wata mota. Da wannan ya karɓa ya gama mora, sai ya turawa wancen, an mayar da ita uwa jaka, dalilin hakane yasa da hajiya ta je Maiduguri bayan rasuwar mahaifinsu Khalil da shekara ɗaya sai ta ɗaukota. Da kakan Khalil da kakan Laure uwarsu ɗaya uba kowa da nashi. "Mu'azzam ka sallame ni na koma gida tunda ni jikina Alhamdulillah, ga kuma Nafeesa da ta samu ƙaruwa, tana buƙatar kulawa sosai kasan haihuwa ce ta fari, kuma daga nan idan mijinta ya amince gida muka yi, sannan kuma ina gargaɗinku da babban murya kar ku sake ku tadawa marmari daga nesa hankali, tunda dai Allah ya ban lafiya ba sai yaji ba, ku bar shi yayi aikinsa hankali kwance, Ko Musaddiq (Barrister Muhammad Kabir) bance a faɗa masa ba." Da sauri Khalil yace, "To amma Hajiya....." "Nace bana son su sani idan har na isa! Sannan kuma maza ka amsar min takardar Sallama mu tafi gida, kuma ina so mu biya ta gidan surukanka zan roƙi alfarmar a bani wannan ƙanwar tata ta zauna damu na wasu lokaci?" Faɗin Hajiya. Da mamaki Khalil yace, "Hajiya, ba dai Aina'u ba ko?" A gadarance Hajiya tace, "Ita fa! Ko baza ka kai ni bane?" "Zan kai ki." Faɗin Khalil tare da ficewa daga ɗakin ya koma office ɗinsa, wayarsa ya fara ɗauka tare da sakawa aljihu ba tare da ya duba ba, gaba ɗaya hankalinsa ya koma gida, so kawai yake yi ya gansa kusa da Sarah don itama dole ya kawota asibiti ya duba abunsa. "Ni da kaina zan duba matata babu wani ɗan iskan da zai gane min jikin mata." Ya faɗi a bayyane tare da fitowa daga office ɗin. Kiciɓis suka yi da ya Abdul-Hakeem, "Yanzu dama wajenka zani, mummyn Moon ta kira ni tana kuka sosai wai Sarah babu lafiya tana ta aman tsuts........." Ba tare da Khalil ya gama sauraron ya Abdul-Hakeem ɗin ba ya nufi hanyar waje da bugun sauri, parking lot ya nufa tare da shiga motar yayi reverse ya bar asibitin a guje. "Ina Khalilullah ɗin? Yazo mu wuce mana!" Faɗin Hajiya wacce ke kallon yaya Abdul-Hakeem. "Hajiya akwai matsala ya wuce gida, matarsa ce babu lafiya, Maryam tace aman wasu jajayan mitsi-mitsin tsutsotsin take yi, abun dai babu daɗin ji." "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wannan wani annobace ya shigo cikin zuri'a ta? Allah gamu gare ka! Laure babu baki, ni da maƙoƙo da zazzagowar idanu, surukata kuma da aman tsutsotsi. Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Allah mun tuba." Faɗin hajiya tana mai fashewa da kuka. "Hajiya kiyi haƙuri ki bar kuka, in Sha Allah, zasu samu sauƙi, ku taso mu tafi gida, to amma wa zai kwana da Laure tunda ba'a bata sallama ba?" Share hawaye Hajiya tayi tare da faɗin, "Tare da ita zamu tafi tunda itama bayan rashin maganar babu abunda ke damunta, kuma ba gida muka yi ba kai tsaye, zamu fara biyawa ta gidansu Uwata domin taho da ƙanwarta ta ɗan zauna damu kaga ni ba ishashshen lafiya ba, Laure kuma babu baki, dole ina neman mai taimako." "Kuma Hajiya sai a rasa wacce za'a ɗauko domin taimakon ki sai ƙanwar matar Khalil, a'a gaskiya Hajiya, don ni haka nan yarinyar bata kwanta min a rai ba." Faɗin yaya Abdul-Hakeem. "To ni ta kwanta min, kuma dole ka kaini gidan na taho da ita." Faɗin Hajiya tana hararensa. Bai kuma cewa komai ba ya juya ya ɗauki akwatin kayan haihuwar Nafeesa ya fita dashi, ita kuma Nafeesa ta rungumo babynta Hajiya a bayanta suka fito. Can gidan su Sarah kuwa, Aina'u ta gama shirinta tsaf don tana ganin komai ta tsakiyar tafin hannunta. Suna parking a ƙofar gidansu ta saki wani murmushi tare da faɗin, "This is the end of you Saratouh Nuhu!" Fitowa kawai Aina'u tayi da akwati a hannu ta fito waje, kallonta Abdul-Hakeem yayi ta yi yana mamakin dama ta san da zuwansu ne ganin ba tare da an shiga da sun shiga ciki ba, kuma basu tura kowa ba har ta fito. Da kanta ta buɗe boat ta saka kayanta a ciki tare da rufewa ta zagayo ta buɗe gidan baya ta shiga tare da rufe motar tana faɗin, "Hajiya ina wuni, ya kuma ƙarfin jikin?" Ita kanta Hajiyar ba ƙaramin mamaki tayi ba jin furucin Aina'u, "Ya akai tasan bani da lafiya?" Faɗin Hajiya cikin zuciya. Amma a fili sai cewa tayi, "Jiki Alhamdulillah Aina'u." Kallon jaririyar hannun Nafeesa tayi tare da faɗin, "An samu ƙaruwa? To Allah ya raya." Ba tare da tunanin komai ba Nafeesa ta miƙa mata jariyar, hannu biyu Aina'u ta amshi jinjirar tana mai faɗin, "kyakkyawa da ita!" Daidai nan yarinyar ta tsandara wani mahaukacin ihuu sai da ya Abdul-Hakeem dake driving ya juyo da sauri yana faɗin, "Lafiya?" Babu wanda ya bashi amsa sai miƙa hannu da Nafeesa tayi tare da amsar jinjirar, sai kuma tsit kamar an ɗauke ruwan sama. Aina'u kuwa wani murmushi tayi ganin kurwar ƴar na yawo a saman motar, can kuma sai ga fuskan *_Hell Ofulafula_* ya wani irin zaro harshe tare da lashe kurwar jinjiran yana mai jinjiwa Aina'un sannan fuskar tasa wanda Aina'u kaɗai ke gani ya ɓace. Khalil kuwa yana parking da gudu ya nufi side ɗinsu yana tsatstsallake step uku-uku har ya isa ƙofar ɗakin Sarah, cikinsa ne ya bada wani irin saurin kuuuuuuuuu tsabar wani dunƙulallan wari da ya shaƙa, amma stil haka ya tura ƙofar ya faɗa ɗakin. Tsalle ɗaya yayi ya isa inda take tare da rungumota gaba ɗaya a jikinsa............. *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *27* "Mutuwa zan yi, mutuwa zan yi Khalil! Wannan ciwon nawa na tafiya ne. Ni kuma haka nawa ƙaddarar yake! Na shiga uku! Baka jin wani irin wari da ƙarnin da nake yi? Aunty Maryam ma ta kasa zama dani a ɗakin nan saboda wari da nake yi, na zama abun kyama!" Wasu irin hawaye ne suka wanke fuskan Khalil amma yayi saurin sharewa saboda baya don zuciyarta ya cigaba da karaya. "Sarah duk duniya idan sun kyamace ki, ni zan kyamace ki ne? Wallahi babu wannan ciwon aduniya da za kiyi na kyamace ki! Ba gani nan ba, kina buƙatar kulawar wani ne bayan nawa? Shin na gaza ne?? Sarah nayi alƙawarin muna tare for better for worse, babu abunda zai iya shiga tsakanina dake don wata lalura ta same ki. Yanzu zan ɗauke ki muje asibiti a duba min jikinki, bari na gyara miki jiki da ɗakin." Ya faɗi hakane tare da janyeta daga jikinsa ya sauka daga kan gadon, kallon wandon jikinsa yayi sai yaga gaba ɗaya tsutsotsin ne manne a jikin wandon, sunkuyar da kai Sarah tayi tana mai jin nauyinsa, ta san tabbas yana ƙaunarta sosai, amma bata taɓa tunanin zai iya yin abunda yake yi mata a yanzu ba, ba tare da kyama ba. Wandon ya cire ya rage daga shi sai boxer sannan ya cicciɓeta ya kaita bathroom yayi mata wanka, abunda ya matukar bashi tsoro shine, ganin yanda tsutsotsin suke ɓulɓulowa, ɗazu da ya wanke mata, su daina fitowa amma kuma yanzu idan yana wankowa kamar ƙara turosu ake yi. "Ya Ilahi!" Shine abunda Khalil ya furta tare da kinkimarta ya fito da ita ya zaunar akan resting chair sannan ya gyara gadon, yanzu kam Sarah ba kuka take yi ba, ido kawai take bin Khalil dashi tana jin wani irin ƙaunarsa na ƙara huda tsokar dake ƙirjinta da ilahirin jikinta har ji take tsigar jikinta na tashi ganin yanda yake nannaɗo zanin gado da hannunsa duk da kuwa tsutsar na taɓa jikinsa, tana kallon yanda tsokar jikinsa shima yake tashi amma a fuska baza ka taɓa ganin wani yanayi na kyama a tattare dashi ba. Wayarsa taga ya ɗauko yayi danne-danne kamun ya kwashi zanin yayin gadon yayi bayi dasu. Ya jima a bayin yana wanke zanin da hannunsa da ya saka handglove sannan ya sake ɗauraye jikinsa yayi wanka tare da ɗauro alwala don lokacin tuni har an idar da Sallar la'asar. Hajiya kuwa suna dawowa gida ta buɗe motar tare da kamo hannun Laure tana jin wani irin mugun tausayinta, da ace tunda ta taso ne bata jin magana da sauƙi da ace lokaci guda kwatsam ta samu lalurar, "Sannu kinji Laure, Allah ya baki lafiya." Ga mamakin Hajiya sai taga Lauren ta ɗaga kanta alamar ta amsa sannun hajiyan, "Laure! Laure, kin ji abunda nace kenan? Alhamdulillah jin Laure ya dawo." Da saurin Nafeesa da ya Abdul-Hakeem suka iso wajen suna faɗin, "Laure kina jin komai yanzu?" Ƙara gyaɗa kai Lauren tayi hawaye na zubo mata daga idanunta, Aina'u kuwa wani taɓe baki tayi don ita ce nan tayi magana da _Hell Ofulafu_ ta cikin tafin hannunta, akan ya dawo da jin Lauren ta yanda idan tayi mata magana za taji, kasancewar ya bata wani abu ta haɗiya idan har tana son wani abu ba sai ta kuma komawa Abia ba, tana matse hannun ta buɗe zai bayyana ta tsakiyar tafin hannunta. "Laure kiyi magana mana, ko baza ki iya ba?" Hajiya ta tambayeta tana mai riƙo hannunta biyu. "Girgiza kai Laure tayi alamar baza ta iya ba." Kuka Hajiya ta fashe dashi tare da faɗin, "Kiyi haƙuri Laure, yanda Allah ya buɗi kunnuwanki, haka zai buɗe bakinki nan kusa in Sha Allah! Muje ciki." Ta faɗi tare da janta gaba, Aina'u kuwa boat ta buɗe tare da ɗauko akwatin ta tabi bayan Nafeesa dake gabanta tana kalonta da gawar babynta dake hannunta tana dariya cikin zuciya. Ya Abdul-Hakeem kuma ɗakin matarsa ya nufa wacce itama tana can tashin hankali ya saukar mata da zazzafan zazzaɓi. Khalil yana idar da sallar la'asar ya koma bayan gidan tare da ɗauko buta da baho ya kawo gaban Sarah ya dunga tsiyaya mata ruwan har ta kammala alwala sannan ya mayar da komai bayin ya fito ya buɗe wardrobe ɗinta ya ɗauko mata hijjab tare da saka mata yace, "Mine kiyi sallah ki kai wa Allah kukanki, in Sha Allah zai yaye maki wannan cutar. Bari na sauka ƙasa na karɓo saƙo." Gyaɗa masa kai kawai tayi tare da kabbara sallar bayan ta kalli gabas a zaunen da take, shi kuma ya fice. Kallon motar ya Abdul-Hakeem yayi tare da faɗin, "Sun dawo kenan!" Cikin zuciya tare da nufar gate, leda ya karɓa a hannun wani matashin yaro irin masu delivery ɗin nan ya dawo cikin gidan ya nufi side ɗin Hajiya, gaba ɗaya a parlour ya same su, Hajiya ta zabga tagumi tare da zubawa Laure idanu. Kallon Laure yayi wacce lokaci guda ta zabge, duk wannan fara'ar da barkwancin sun tafi, sai kallon kowa take yi a firgice. "Ina wuni ya Khalil." Aina'u ta faɗi tana zuba murmushi don babu abunda bata gani ta cikin tafin hannunta, har wanka da alwalar da yayiwa Sarah yanzu da kuma fitar da yayi ya amshi saƙo, bama wannan ba, hatta yanda zuciyarsa ke bugawa da jinin dake zagaye ilahirin jikinsa tana kallon a yanzu haka. Kallon ɗaya yayiwa inda take ya kau da kai ba tare da ya amsa gaisuwarta ba. "Mu'azzam ba gaishe ka Ƙanwar matarka take yi ba!" Hajiya ta faɗi tare da ɗan ɓata rai. "Ita ɗin *_ƘANWAR MATATA_* ce kawai, bayan nan babu abunda muka haɗa Hajiya." Faɗin Khalil cikin zuciya, amma a zahiri sai cewa yayi, "Lafiya!" A tilastance tare da zama akan kujera yana mai fuskantar Laure yace, "Ƙawata ya jikin naki? Allah ya baki lafiya kinji! Ina sha Allah komai zai wuce." Ya faɗi hakane duk da yasan ba zata ji ba, amma ga mamakinsa sai taga ta gyaɗa masa kai tana hawaye. Da sauri ya kalli Hajiya, tun kan yayi magana hajiyan tace, "Cikin hukuncin ubangiji sai ga jin ya dawo, maganar ma nan kusa in Sha Allah." Da murmushi ya juya tare da kallonta yace, "Ki kwantar da hankalinki, in Sha Allah komai zai wuce, ji cigaba da addu'a. Wannan jarabawace daga Ubangijin halitta." Jinjina kai Laure tayi tana mai kallon Aina'u a sace, karaf sai suka haɗa idanu, wani mugun harara Aina'un ta sakar mata tayi saurin kawar da kai, don wani irin mugun tsoron Aina'un take yi, duk suka haɗa idanu sai gabanta ya yanke ya faɗi. "Sai kuma naji wani maganar tashin hankali Mu'azzam, dagaske ne matarka ba lafiya tana aman tsutsotsi?" Hajiya ta faɗi kamar ta fashe da kuka. Cike da damuwa Khalil yace, "Hakane Hajiya, yanzu ma asibiti zamu tafi da ita." Ko kamun Hajiya tayi magana Aina'u ta buga wani irin ihu miƙewa ta dafe ƙirji tare da fashewa da kuka tace, "Wayyoo Allah mun shiga uku, Sarah ce ke aman tsutsotsin?" Wani hararan gefen idanu Khalil yayi mata tare da faɗin, "As if she care!" A cikin zuciyarsa. Hajiya kuma ƙoƙarin kamo hannun Aina'un tayi amma ta goce tare da fita da gudu daga ɗakin, taɓe baki Khalil yayi tare da ajiye ledan da ya shigo dashi a gefe ya kai hannu ya ɗauki babyn Nafeesa akan kujera, tun shigowarsa yake satan kallon babyn, sai yake gani kamar babu rai a jikinta. Cikin dabara ya kai hannunsa saitin hancin babyn, amma bai ji alamun numfashi ba, taɓa pulse ɗin yarinyar ya kuma yi nan ma yaji baya harbawa, wani wawan ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon Nafeesa ta gefen idanu, don ba ƙaramin tausayi ta bashi ba. Ba'a mamakin mutuwa, amma yayi mamakin mutuwar babyn Nafeesa, don ko da Nafeesa ta haifeta, lafiyarta ƙalau kuma akwai kuzari sosai a jikinta da ƙosashshen lafiya! Rufe babyn yayi har kai tare da shimfiɗar da ita a kan kujeran ba tare da ya kalli Nafeesa ba. Nafeesa kuwa kallo ɗaya tayiwa babyn da khalil ya ajiye taji zuciyarta ya buga da ƙarfi bata ma san lokacin da ta buga tsalle ta isa gaban kujeran da ya ajiye babyn ba. "Lafiya Khalilullah ka lulluɓe jaririyar har ka kamar wata gawa?" Faɗin Hajiya wacce gabanta ke faɗuwa kamar zai faso ƙirjinta ya faɗo don ta san idan har aka rufe ɗan adam har ka hakan na nufin babu shi. Girgiza kai Khalil yayi yana kallon tiles ɗin dake shimfiɗe, Hajiya bata san lokacin da ta furta, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Nafeesa kuwa kuka ta fashe dashi tana mai jijjiga hannun Khalil tana faɗin, "Don Allah kar kace min ta mutu, ka sake dubata da kyau, lafiya ƙalau muka baro asibiti, Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Na shiga uku!!" Faɗin Nafeesa tana kallon babyn nata, hannunta kuma yana kan na Khalil dake kallon ƙasa idanunsa sun cika da hawaye. Hajiya kai hannu tayi ta ɗauki jaririyar tana ƙara dubata, kuka ta fashe dashi bayan tabbatar da yarinyar ta koma, "Hajiya ƙarfafa mata guiwa za kiyi ba ki karya mata zuciya da kukanki ba, ita nata tayi kyau tunda bata ɗibi zunubin komai ba, mune abun jin ba ita ba. Allah yasa mai ceto ce. Nafeesa nasan abun da zafi, amma kiyi haƙuri, Allah da ya karɓe abunsa ya fiki sonta, ki gode masa ta hanyar yin tawakkali, kuma dama shi da kansa yace ba wai don munce munyi imani ba shikenan ba zai jarabce mu ba. Allah zai baki wata in Sha Allah, ai ba cewa akai baza ki ƙara haihuwa ba. Ki kwantar da hankalinki kinji, Allah ya baki haƙurin rashi!" Gyaɗa kai Nafeesa tayi zafafan hawaye suna kwaranyo mata, miƙewa yayi ya ɗauki kasar da ya shigo da ita ya fita daga ɗakin don zai iya zubar da hawaye idan yana kallonsu, "Allah mun gode maka, Allah kasa muci wannan jarabawar!" Ya faɗi tare da nufa side ɗin yaya Abdul-Hakeem. Knocking yayi, ba jimawa yaya Abdul-Hakeem ɗin ya buɗe masa ƙofa, "Lafiya Ibrahim?" Faɗin ya Abdul-Hakeem ɗin ganin yanayin Khalil ɗin. "Allah ya yiwa ƴar wajen Nafeesa rasuwa yanzu." Da sauri ya Abdul-Hakeem ɗin yace, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Ba dai jinjirar ba?" Ko kamun Khalil yace wani abu har Aunty Maryam ta iso wajen gabanta na wani irin bugawar tsoro da tashin hankali, don duk a tunaninta Sarah ce ta mutu. "Wallahi kuwa ita, yanzu na shiga ɗakin, su basu ma sani ba sai da na ɗauki yarinyar na duba pulse ɗinta don tun da na kalleta sau ɗaya na fahimci babu rai a jikinta." "Wacece ta mutu?" Aunty Maryam ta faɗi a firgice. "Ƴar wajen Nafeesa ce." Ya Abdul-Hakeem ya bata amsa. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Ba yanzu kake faɗa min ta haihu ba? Mun shiga uku daga wannan sai wannan!" Khalil yace, "Haba Aunty Maryam, Kar kiyi saɓo mana!" Kuka Aunty Maryam ta fashe dashi daidai lokacin da wayar ya Abdul-Hakeem ɗin yayi ƙara. "Gama mijinta nan yana kirana." Ya faɗi tare da picking kiran shi kuma Khalil ya juya tare da nufa side ɗinsa. Aina'u na shiga parlourn Sarah ta fashe da dariya har da kyakyatawa tare da faɗin, "Su Mine da Happiness kenan, ai yanzu aka soma wasan wallahi, ina nan zuwa gare ka Khalil, wallahi sai na mayar da kai masarrafin talabijin!" Sama ta hau tare da tura ɗakin Sarah, da gudu ta fito tana mai danne ƙirjinta saboda wani uban wari daya busota, "Bala'iiiii, gaskiya _Hell Ofulafu_ ka iya aiki, wannan bala'in wari haka, ai ko Lami da babanmu masoyinta baza su iya jurewa ba balle kuma miji! Taɓ, sunanki sorry Saratu. Aini ko buɗe Ƙofar ban iya ƙara yi bare in shiga ciki. Allah dai ya ƙara azabar da yafi haka." Aina'u ta faɗi tare da saukowa ƙasa tana mayar da numfashi. Turo ƙofar Khalil yayi ya shigo, ganin Aina'u zaune akan kujera ya saka shi sakin wani malalacin murmushi tare da faɗin, "Hmm! Har kin gama ihun tashin hankali akan ƴar uwarki na aman tsutsotsi? Kin kasa isa wajenta ko? Dama na san baza ki iya ba, wacce ke ciwon da bai kai wannan ba kin kasa taimakonta sai wannan ne zaki taimaka mata! Nasan wallahi duk ƙaunarki da kuɗi, ko nawa zan baki, baza ki iya kula da ƴar uwarki ba, ban dai sani ba ko idan kinga tana shashshekar mutuwa za ki iya, to ina so ki sani, Ni ba zan taɓa gazawa ba da matata, zan mutune matsayin bawa mai hidimta mata! Ki fice min a ɗaki yanzun nan!! Ke _ƘANWAR MATATA_ ce amma ban san mai yasa ba, baki taɓa burgeni ba, ban sani ba ko hakan nada nasaba da nuna rashin son ƙulluwar auren mu da Sarah tun farko!" Yana gama faɗin hakan ya haura sama. Sai da gabansa ya faɗi jin warin ninkuwa yayi a kan nada, ga tsutsotsi ne nan faca-faca tun daga kan kujeran da take kai har ƙasa, ita kuma kifa kanta kawai tayi akan hannun kujeran tana shashshekar kuka don kukan yaƙi fitowa. Ajiye ledar yayi a kan gado tare da isa wajenta duk da uban warin da take yi ya cicciɓeta ya kaita bayi ya ajiye a cikin bathroom tub sannan ya fita cikin sauri ya gyara inda ta ɓata sannan ya dawo da ita kan gado bayan ya shimfiɗa wani zani gudun kada tsutsotsin su sake ɓata wajen. Wannan ledan ya ɗauko tare da buɗewa ya zaro pampas ɗin manya guda ɗaya ya saka mata........ _Kuyi haƙuri da wannan Please, in sha gobe zan yi mai yawa_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* 🦜 *KANWAR MATATA*🦜 *28* "Mine, Nafeesa ta samu ƙaruwa ɗazu." Ya faɗi maganar yana mai jan skirt ɗinta sama ya zage zip ɗin. Out of excitement tace, "Dan Allah! Alhamdulillah Allah ya raya, don Allah ka ɗauko min picture ɗin babyn in ganta." Kallon fuskanta Khalil yayi, babu abunda yafi kyau da fuskanta irin fara'arta, sai yaji kamar kar ya faɗa mata babyn ta koma. "Ya naga kayi shuru Happiness?" Faɗin Sarah. Ajiyar zuciya Khalil ya sauke tare da kau da kansa daga kallonta yace, "Allah ya amshi abunsa, babyn ta koma." Zaro idanu Sarah tayi tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Ina Nafeesan yanzu? Wani hali take ciki?" Sarah ta faɗi hawaye na zubar mata. Hannunta biyu ya kama tare da faɗin, "Ta ɗauki dangana, ta san cewar Allah da ya amshi rayuwarta ya fita son yarinyar, ta amshi ƙaddararta ta hanyar dangana da fauwalawa Allah komai." A hankali Sarah tace, "Allah ya ƙara mata haƙuri da dangana." Miƙewa yayi tare da faɗin, "Haka ake son duk musulmi da ɗaukar ƙaddara mai kyau da mara kyau idan har ya yarda shi ɗin cikakken musulmi ne, shiyasa nake so kema ki fauwalawa Allah komai ki daina koke-koken nan, in Sha Allah zaki samu lafiya. Bari naje zana'idar in dawo sai mu tafi asibitin, kina buƙatar wani abu?" Girgiza kai Sarah tayi tare da faɗin, "Babu abunda nake buƙata, kayi tafiyarka, Allah yasa mai ceto ce. Nima zan gwada miƙewa inje can wajen Hajiya yanzu tunda ka saka min pampers tsutsotsin baza su zubo ma." Kallonta yayi tare da faɗin, "Idan har kin ga baza ki iya ba, kiyi zamanki gaba ɗaya sun san baki da lafiya. Ki kular min da kanki, sai na dawo." Yana gama faɗin haka ya fita ya bar ɗakin. Hannu Sarah ta ɗaga tare da faɗin, "Ya Ubangiji ga mijina nan, ka kare min shi daga dukkanin cutuwa, ka ƙara masa so da ƙaunata a cikin zuciyarsa, ni kuma bani lafiya mai amfani ta yanda zan bauta masa wajen yi masa biyayya har in dawo gareka. Allah ka bani lafiya alfarmar annabi sallallahu alaihi Wasallam." Ta ƙarisa maganar tare da fashewa da kuka. Can cikin gida kuwa, har mijin Nafeesa da danginsa sun ƙariso, mahaifiyarsa ita tayiwa babyn wanka tare da yi mata sutura, shi kuma Qasim mijin Nafeesa sai lallashinta yake yi yana bata haƙuri akan in Sha Allah zasu samu wani nan kusa. Kamun magrib har sun kai gawan makwancinta sun rufe sun dawo, sai gidan yayi wani irin tsit kowa da irin jimamin da yake yi, yayin da Laure ke wani irin zabura da firgita idan ta kasance ita kaɗai a waje, don babu fuskan da take gani sai na Aina'u da _Hell Ofulafu_ suna tsoratata gashi kuma babu bakin magana. Sarah ta iya fita har side ɗin Hajiya, kallon ɗaya Hajiya tayi mata gabanta ya faɗi ganin wani mahaukacin rama da tayi, don ko ɗazu da safe sun haɗu kamun faruwar komai, "Wannan wani irin cuta ce kamar ta iska?" Hajiya ta faɗi a zuciyarta. Sarah kuwa da bata san halin da Hajiyar ta shiga ba, waro idanu tayi ganin halittarta gaba ɗaya ya canza, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Hajiya haka kika koma?" Aunty Maryam ce tayi saurin tarota ganin zata zube a ƙasa, ta zaunar da ita. Rarrafawa tayi ta ƙarisa wajen Hajiya tare da ɗaura kanta akan ƙafafun Hajiya ta hau rera kuka, hajiya bata iya cewa komai ba sai shafa bayanta da ta shiga yi tana danne nata hawayen. "Oh Allah! Abu kamar jifa, daga wanda halittarsa ta canza, sai kuma wacce maganarta ya ɗauke gaba ɗaya, da kuma mai aman tsutsotsi! Gaskiya wannan abun dubawa ne. Duk mai bin mu da sharri in Sha Allah sai ya koma masa." Faɗin Nafeesa wacce taci kuka ta ƙoshi, idanun nan sun yi jazur." Wani wawan kallon gefen idanu Aina'u tayiwa Nafeesan a zuciyarta tana faɗin, "Ashe kema zaki bi ƴarki kenan!" Sarah kuwa ɗagowa tayi ta kalli Nafeesa tare da faɗin, "Nafeesa wacece kuma maganarta ya ɗauke?" "Laure!" Nafeesa ta bata amsa hawaye na zubowa. Hajiya ta kalli ɗaya daga cikin yaran dake ɗakin tace, "Namrah kunna rediyon can ki kunna mana karatu zuciyar kowa tayi sanyi." Da jin haka wuff Aina'u ta miƙe ta fita daga ɗakin ta baya gudun a ganta, don yi nayi kamar zata shiga toilet ɗin dake parlourn, Aunty Maryam kuwa tunda ta miƙe take lure da ita, don haka nan taji tana mugun zargin Aina'un, sam tun ranar farko data fara ganinta bata kwanta mata a rai ba. Da sauri ta zaga ta baya ta tsaya bayan flowers, sai da ta kalli gefe da gefe sannan ta fiddo hannunta tare danna tsakiyar tafin hannun, cikin second biyar sai ga _Hell Ofulafu_ ya bayyana cikin suffarsa ta tsoro, gefensa kuma wani gajeren halitta abun tsoro ne mummunan gaske, shi ya daka mata tsawa tare da faɗin, "Menene buƙatarki ta gaba?" "Nafeesa! Ita nake so tabi jaririyar, ba bada jininta matsayin ruwan da Hell zai ɗanɗana, sannan ina so a saka mummunar warin da yafi wanda Sarah keyi a jikin mijinta ta yanda zata riƙa kyamatarsa har hakan ya fusata shi yayi mata wulaƙanci, don na san tabbas idan aka yi haka Khalil zai ji haushinta tunda shi ya jure bai kyamaceta ba duk da tsutsotsin dake fita a jikinta da kuma warin da take yi. Sannan na uku, ina so a ɓatar da kokwanto da shakkun da ke zuciyoyin mata da mijin gidan nan a kai na, ina nufin SS Abdul-Hakeem da matarsa Maryam, sannan Barrister Muhammad Kabir da LTG Abdullah ka mantar dasu suna da family ka Kaduna, ina so su manta da kowa nasu dake Kaduna, ko da wasa kar su waiwayi gida! Abdul-Hakeem ma ayi masa abunda zai jawo a koresa daga aiki, don na tsani ƴan sanda musamman na farin kaya!" Wannan mummunar halittar ya fashe da dariya tare da faɗin, "Aikin ya kammala, sai dai jinin ƙanwar Mijin yayarki yayi kaɗan, dole sai kin ƙara da jinin yaro ƙaramin kuma namiji." Shuru Aina'u tayi tana tunanin ta inda zat dea samu jinin yaro ƙaramin, "Rabo ɗan wajen Na'ima!" Faɗin Aina'u a bayyane tana mai sakin murmushi tare da ƙara faɗin, "Na rage maki wahala Na'ima, a sauka lafiya Rabo!" Ɓat _Hell Ofulafu_ da wannan halittar suka ɓace daga tafin hannunta don sun gama sauraran abunda zasu saurara, tun ambaton sunan Rabo da tayi na farko, har _Hell Ofulafu_ ya janyo kurwarsa tare da haɗiyewa. Aina'u na juyawa suka yi idanu huɗu da Aunty Maryam da ta biyo ta a baya, har fitsarin tsoro ya gama wanke jikinta, gaba ɗaya jikinta sai kakkarwa yake yi. Aina'u kuwa wani murmushi ta saki ba tare da ko ɗar ba don Aunty Maryam ɗin taji komai da take tattaunawa da _Hell Ofulafu_. Zagaye Aina'u ta shiga yi tare da faɗin, "Makanta, kurmanta, rashin yin magana, mutuwa ɓarin jiki, mutuwar gangar jiki gaba ɗaya, ƙona ki da ranki, wanne kika zaɓa?" Kuka Aunty Maryam ta soma yi tare da faɗin, "Dan girman Allah Aina'u kiyi haƙuri kar kiyi min ko ɗaya daga cikin abunda kika lissafo, na zaɓi da nayi shuru da baki na, babu wanda zai ji wannan maganar nan daga ni sai ke!" Wani dariya Aina'u ta kwashe dashi tare da faɗin, "Kin ga nayi maki kama da wawuya? Ko da yake, ni nayi maki zaɓi, shine barin gidan nan, kuma kin san wani abu, duk lokacin da bakinki yayi kuskuren buɗewa ya faɗawa wani wannan abun da kika ji, baza ki iya faɗin komai ba, kuma daga ranar baza ki kuma magana ko kiji ba har ki mutu! Wuce kije ki fara haɗa kayanki kamun takardar sakinki ya biyo ki!!" Ta ƙarisa maganar a tsawace tana mai nuna mata hanya. Da sauri Aunty Maryam ta riƙo ƙafafuwanta tare da faɗin, "Na roƙeƙi da girman Allah kar ki raba ni da aurena, wallahi nayi maki alƙawarin babu mai jin wannan maganar har sai idan Allah ne yayi ikonsa, ina son mijina da aurena don Allah kar ki raba ni dasu." Wani mugun tsaki ta ja tare da faɗin, "Sai ki zaɓa, rayuwarki, lafiyar jikinki, ko kuma aurenki?" Shuru Aunty Maryam tayi tana wani irin kukan baƙin ciki. Aina'u ta taɓe baki tare da faɗin, "Gidan na kowa sai yaji a jikinsa, na rantse da Yesu Almasihu mai ceto!" Da saurin Aunty Maryam ta kalleta jin abunda ta furta tare da faɗin, "Babu shakka, ashe shiyasa babu ɗigon imani a zuciyarki, in Sha Allah sai kin girbe abunda kika shuka azzaluma kafurar banza!" A cikin zuciyarta. "Ki wuce kije ki soma haɗa kaya, don yau gidan mai dattin hula da ɗan kwali za'a kwana!" Tana gama faɗin haka ta wuce ta bar wajen tana waƙar zumunta. Aunty Maryam kuwa kuka ta dunga rusawa tana tunanin makomarta, ita da babu uwa, babu uba, rayuwa take yi a wahale a wajen dangin ubanta kamun Allah ya kawo mata Abdul-Hakeem har suka yi aure, idan ka ganta gidansu gaisuwa taje ko kai masu abun arziki don suna ba wasu masu arzikin bane, talla tayi su kala-kala irin su kunun gyaɗa da alale, da daddare kuma burabusko da miyan taushe, kuka da kuɓewa! Har zunɗenta ake yi wai don ta auri ɗan masu kuɗi sai fankama take yi tana ƙoƙarin manta asalinta. "Shinekan wahalata ta dawo sabuwa fil, masu fatan irin haka ta faru dani sun samu dama. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Allahumma arji'ini fi musibati wa aklifni khairan minha!!" Haka aunty Maryam tayi ta nanatawa har ta isa ɓangarenta. Cak ta tsaya a parlour tana kallon tanƙameman hotunsu su uku, ita da Abdul-Hakeem da kuma ƴarsu Maimoon. Can gidansu Lami kuwa, Rabo na zaune kusa da ita da roban abinci a hannunsa yana ci, gaba ɗaya suna tsakar gida suna shan iska kasancewar garin akwai zafi, kawai sai suka ga Rabo ya fara wani irin jijjiga idanunsa na sama, hatta robar abincin dake hannunsa jijjiga yake yi, kumfa baƙiƙƙirin ya soma kwaranyowa daga bakinsa, gaba ɗaya da gudu sukai kansa suna kiran sunansa, Lami kuwa wani tsalle ta buga tare da fasa ƙara ta shiga faɗin, "Yesu! Yesu!! Yesu gamu gareka mun bar zunubi, duk wani dodo ko maye ko mugun dake son tafiya da granson ɗina ka tsine masa, a cikin mu'ujizozinka ka cire shaitan ɗin dake kusa da jikana yaaaa Yesu Almasihu mai ceto!" Tana faɗin maganar ne tana wani irin tuma a ƙasa tare da fasa ihu. Da sauri baba dake ɗaki ya fito, tuni Na'ima dake riƙe da Rabo tana kuka ta nufi wajen baba tare da miƙa masa shi tana mai ɗaura hannu a kai tana kuka. Baba kuwa yana amsar Rabo ya fahimci rai yayi halinsa saboda yanda jikinsa ya sake. Shimfiɗar da shi yayi akan tabarma tare da miƙar masa da hannu sannan ya miƙa hannu ya janyo zanin dake kan igiya ya lulluɓesa har kai. Wani irin baya Na'ima tayi ta tafi luuuuuu ta faɗi ƙasa sumamma! Da gudu su Marfu'a suka yi kanta tare da cicciɓanta suka kai ta ɗaki suka shinfiɗe. Lami kuwa sai kururuwa take yi, hakan ya jawo hankalin maƙota suka cika gidan tam. Baba kuma waya ya ɗaga ya kira abokansa su baba Sama'ila, har aka gamawa Rabo wanka Na'ima bata farfaɗo ba, sai can har ana tunanin kaisa kawai sai ta farfaɗo, har ɗaki baba ya shigo yayi mata nasiha tare da ce masa taje tayi masa addu'a, da kyar ta isa zuwa ta zube guiwowinta a ƙasa kusa da gawar, "Ka yafe min, ka yafe min!" Shine abunda Na'ima tayi ta maimaitawa tana kuka. "Ba'a kuka gaban gawa Na'ima, haramun ne!" Faɗin baba Sama'ila. Hassana ce ta kama hannunta suka fita daga ɗakin don har an kawo makara za ayi masa sallah, Gaba ɗayan su babu mai hijab ko ɗaya, a wajan maƙota suka ara sannan suka iya fita aka yi sallar dasu. Na'ima bata kusa haukacewa ba, sai da aka saka Rabo cikin mota za'a wuce, sai da aka turata cikin gida aka kullo ƙofar saboda yanda take wani irin mahaukacin kukan tashin hankali. Baba kuwa babu abunda dake zuwa bakinsa sai Allah yasa mutuwar nan ta zama sanadin shiryuwar ƴaƴan nasa. Bayan an dawo daga maƙabarta baba yayi ta kiran layin Khalil domin ya shaida masa mutuwar amma bai samunsa, layin Sarah kuma har ta gama ringin ba'a ɗauka ba. Can gidansu Khalil kuwa, Aunty Maryam zaune a ƙasa wayarta a hannunta tayi masa ƙuri tana jiran message daga Abdul-Hakeem akan ya saketa, ɗiririn saƙo ya shigo wayar, gabanta ne ya buga da ƙarfi don har sai da ta rintse idanu tana addu'a, dakyar ta iya duba saƙon, sai taga ashe daga bank ɗinta ne suna tayata murnar zagayowar ranar haihuwarta. Wani wawan ajiyar zuciya ta sauke tare da hamdala a bayyane, daidai nan ya Abdul-Hakeem ɗin ya murɗa handle ɗin ƙofar ya shigo, da wani irin sauri ta miƙe tana kallonsa gabanta na wani bugawa kamar zai faso ƙirjinta ya faɗo. A hankali ya riƙa takowa ita kuma tana matsawa har suka dangana ga jikin bago. Goshinsa ya haɗe da nata tare da faɗin, "Maryama, tun da na aureki tsayin shekaru biyar kenan, baki taɓa yi min wani abun da naji kamar in rabu dake ba, ko wani aiki nake yi na wahala a wajen aiki, idan na tuna da ke, sai inji farin ciki ya mamaye zuciyata tare da fuskantar abunda nake yi domin inyi in gama in dawo gida na ganki, ki sani shi aure rai gare shi, idan lokacinsa yayi, da daɗi da babu daɗi sai an rabu! Kiyi haƙuri Maryam, zan ƙara maimaita maki, baki yi min komai ba sai alkhairi, kiyi haƙuri da abunda zai fito daga bakina yanzu," sai dai ya ɗan yi jim yana kallonta sannan ya haɗe hannunta biyu tare da faɗin, "Ki yafe min, na sake ki saki ɗaya Mary......" Bata bari ya kai ƙarshe ba ta fashe da wani irin kuka tare da gittashi da sauri ta haura sama tare da banko ƙofa, shi kansa Abdul-Hakeem ɗin wasu zafafan hawaye ne suka kwaranyo masa daga idanunsa, ya rasa wani irin wutane yake ta ruruwa a zuciyarsa, haka nan ya dunga jin zafi da raɗaɗi, can kuma ya soma jin shi kawai aure ne ya haƙura dashi, kamar ana ingizashi yaji domin yazo ya saki matarsa da a kullum burinta ta kyautata masa. Aina'u bata koma ɗakin Hajiya ba saboda ƙira'ar dake tashi, sai ta koma can baya ta inda baza taji sautin karatun ba ta zauna tana mai jin zafin furucin Nafeesa, "Sai na ɗanɗana maki azababbiyar mutuwa in dai ni ƴar Elizabeth da Nuhu ce!" Ta faɗi maganar tana sakin kwafa. A ɗakin Hajiya kuwa, Sarah tayi kuka kamar zata mutu, bata soma jin salama a ranta ba sai da aka kunna ƙira'ar nan. Zuwa anjima can sai ga Khalil ya shigo ɗakin, shi bai ma ɗauka ta iya zuwa ba nan ɗin ba, sai da ya shiga ɗakinta ya taras bata nan sannan ya dawo nan, "Ya ƙarin haƙuri Nafeesa?" Luhu-luhun idanunta ta ɗago tare da faɗin, "Alhamdulillah!" Kallon Sarah Khalil yayi tare da faɗin, "Mine taso mu tafi yamma nayi." "Ina zaku?" Hajiya ta tambaya, "Asibiti nake so muje na dubata." Gyaɗa kai Hajiya tayi tare da faɗin, "Allah ya ƙara sauƙi, sai kun dawo." Da ameen Khalil ya amsa, ita kuma Sarah ta miƙe ta fito ya biyo bayanta, abunda ya matuƙar bashi mamaki shine, lokacin da take cikin ɗakin Hajiya, babu wannan warin da take yi ko kaɗan, amma tana fitowa warin ya dawo. Bai ce komai ba har suka isa ɗaki, kalonta yayi tare da faɗin, "Za'a canza pampers ɗin ne?" Girgiza kai tayi. Sai ya nufi wardrobe ya ɗauko hijjab ɗin ta ya saka mata sannan suka fito, a cikin mota ma karatun ya kunna, yana kallon Sarah yanda ta kwantar da kanta jikin kujera tare da lumshe idanu. Suna isa ya shiga da ita lab ya ɗibi jininta ya bada ayi gwaje-gwaje sannan suka fito suka nufi X-ray room, nan ma sai da yayi examining Virgina ɗinta sosai. Kusan test kala goma aka yi mata, basu suka dawo gida ba sai past 10, wasu tests ɗin sun fito a ranar, wasu kuma sai bayan 8days zasu fito, wanda suka fito a ranar guda huɗu ne, kuma gama ɗayansu komai normal, guda ɗaya ne ma a ɗan ga yest infection kaɗan shima kuma na ciki ne, babyn cikinta lafiya ƙalau. Suna dawowa gida ya sake yi mata wanka ya canza mata pampers tayi sallar isha'i sannan suka ci abincin da ya tsaya ya saya masu a restaurant. Yana son faɗa mata ɗan wajen Na'ima ya rasu amma bai son hankalinta ya tashi, don sun yi waya da baba daga baya, kuma ya faɗawa baban bata da lafiya sai dai bai faɗa masa asalin ciwon ba, baban yace masa ba sai tazo ba, tayi zamanta kawai zai faɗa masu bata da lafiya. Haka suka kwanta ba tare da ya faɗa mata ba. Bai ji kyamarta ba, yanda suka saba kwana haka suka kwanta kwance a kan ƙirjinsa, can cikin dare ya jisa sharkaf, cikin sauri ya tashi ya kunna bedside lamp, cike da mamaki yake kallon uban fitsarin da Sarah ta lafta duk da pampers ɗin jikinta ga kuma tsutsotsin nan sun fara fitowa. Tagumi ya zuba yana kallonta tana bacci peacefully bata ma san mai ke faruwa ba, hawaye ne suka gangaro masa na tausayinta, ya jima yana kallonta kamun ya sauka daga kan gadon ya cire boxer ɗin jikinsa don ya jiƙe sharkaf, bayi ya shiga ya wanke jikinsa sannan ya dawo ya soma tashin ta a hankali, miƙa ta soma yi, sai ji tayi hannunta ya sauka a kan lema, da sauri ta ware idanunta tare da tashi zaune tana mai faɗin, "Happiness, fitsari kwance nayi? Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Na shiga uku!!" Tausayi ta bashi sosai, sai kawai ya sunkuceta ya kaita bayin ya ajiye a tub sannan ya fito ya kwashe zanin gadon ya kai bayin tare da ɗauko wani ƙaramin towel da ruwa da liquid soap ya goge katifar sosai sannan ya saki fanka tare da kwasar janin gadon ya shigo dashi bayin ya zuba a bucket sannan ya isa gareta, babu abunda take yi tunda ya ajiyeta sai kuka, "Wallahi tallahi zaki ɓata min rai Sarah! Kanki farau ko ƙarau? Haba! Baki san kukanki na tada min da hankali ba?" Yana gama faɗin haka ya shiga cire kayan dake jikinta, sosai yaji tsoro lokacin da ya cire pampers ɗin jikinta gaba wannan jajayan mitsi-mitsin tsutsotsin sun koma canza colour, wasu sunyi green, wasu yellow-yellow, wasu kuma farare. Bai bari ta gani ba ya ajiye pampers ɗin sannan ya wasa ruwa ya shiga cuɗa jikinta. Sai da ya gama mata wankan sannan ya dawo da ita ɗakin ya ajiyeta a kan gado inda babu lema ya saka mata wani pampers ɗin tare da kayan bacci sannan ya mayar da ita ɗakinsa ya rufeta da bargo ya dawo nata ɗakin ya wanke kayan nan tsaf sannan ya koma ɗakinsa ya kwanta tare da jawota jikinsa. Aina'u dake ɗakin can side ɗin Hajiya tana kallon komai ta tsakiyar tafin hannunta, bata san lokacin da ta jefi mirror da wayarta dake gefensa ba, sai ji kake tatsatsatsatsa! Tafin hannunta ta matsa da ƙarfi, wannan karon _Hell Ofulafu_ bai bayyana ba, wannan mummunar halittar ne ya bayyana tare da faɗin, "Kina da wutar ciki Aina'u, duk abunda muka ce zamu yi, za muyi shi, shin bamu cika maki biyu daga ciki bane? Rabo ya mutu, Abdul-Hakeem ya saki Maryam, yanzu saura warin da za'a turawa Khalil, korar Abdul-Hakeem daga aiki, mutuwar Nafeesa da kuma mantar da LTD Abdullah da Muhammad Kabiru cewar suna da uwa da ƴan uwa a Kaduna. Kar ki ƙara neman mu akan wannan buƙatar, sai dai idan wata buƙatar ke gare ki." Yana gama faɗin haka ya ɓace. Ajiyar zuciya Aina'u ta sauke tare da kwanciya rub da ciki, can kuma ta miƙe ta buɗe zip ɗin jakarta ta ɗauko murɗin wiwi ta saka a baki tare da kunna lighter ta hau zuƙa, sai da tasha murɗi uku sannan ta kora codine kwalba ɗaya sannan ta faɗi yarab a kan gadon ta hau bacci. Bayan kwana uku, sam Hajiya bata lura aunty Maryam bata gidan ba, don tare suka tafi da Moon, ya Abdul-Hakeem kuwa yayi wani irin zugewa, don washa garin ranar da ya saki aunty Maryam aka dakatar dashi daga aiki, Hajiya kuma ta kasa tambayar ina Aunty Maryam ɗin duk da kuwa bata ganinta, wani irin mahaukacin tsoron Aina'u take yi, idan ta ganta gabanta faɗuwa yake yi, Nafeesa ma haka, wannan dalilin ne ya saka ta tattara tabi mijinta duk da dama shima abunda yake so kenan, don dangi sun taso shi gaba akan ta dawo gidan auranta. Zaune Hajiya tare a kan kujera ta rasa abunda ke damunta, ga Laure dake gefenta wacce lokaci bayan lokaci take saka bayan hannu ta share hawayeta, tayi wani irin mugun rama, hatta a fuska sai ƙasusuwa suka fito mata, babu komai a fuskan dai idanu da haƙora yaƙaƙau! Fitowa Aina'u tayi daga ɗakin da Hajiya ta ware mata tana fito, babu wanda ya iya ɗago idanu ya kalleta a cikinsu, "Hajiya ko kin san wannan abun dake hannuna?" Faɗin Aina'u tana mai kai mazaunanta akan kujera, ɗagowa Hajiya tayi ta kalli hannun nata tare da girgiza kai. Sakawa a baki Aina'u tayi tare da kunna lighter ta kai kan wiwi ɗin tayi masa wani irin zuƙa tare da faɗin, "Wiwi ce!" Zaro idanu Hajiya tayi tare da yin gum, Laure kuwa babu inda jikinta baya rawa ga warin hayaƙin mara daɗi mai tada zuciya kuma babu wanda ya isa ya tashi a cikinsu. Sai da tasha murɗi biyu sannan ta kwanta akan three sitter tare ɗaura ƙafa akan saman kujeran tana kallon Tv, can kuma ta juyo ta kalli Laure tare da faɗin, "Ke, tashi ki canza min channel zuwa MBC action." Da sauri Laure ta tashi ta nufi wajen TV ɗin daidai lokacin da Khalil yayi sallama ya shigo ɗakin domin shaidawa Hajiya yana son shi da Sarah su tafi India domin a duba masa jikinta, don gaba ɗaya result ɗin tasa-tasan da aka yi mata a asibitin bai nuna tana ɗauke da matsalar komai ba. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Hajiya! Warin wiwi fa nake ji a ɗakin nan." Da sauri Laure da hajiyan suka kalli juna sannan suka kalli Aina'u da ta wani irin ɗaure fuska. "Hajiya......." Tun kamun ya ƙarisa Hajiya tayi saurin faɗin, "Ni dalla ka isheni da magana, to ni nasha wiwin!" Zaro idanu Khalil yayi, sai kuma ya mayar da dubansa izuwa wajen Aina'u tare da faɗin, "Dan ubanki kece kika sha wiwin ko?" A watse ta kallesa tare da faɗin, "Hajiya ce tasha, ko baka ji ta baka amsa ba." Wani wawan mari Khalil ya ɗauke fuskan Aina'un dashi tare da faɗin, "Dan ubanki zo ki bar gidan nan tun da ba gidan ubanki bane......" *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *29* "To sannu ɗan masu gida! Wai kai Khalilullah mai yasa baka da kawaici ne a rayuwarka? Ƙanwar matarka ce fa! Ai ko don uwata ka raga mata. Gaskiya ka ɗauki hakki, kuma ka bata haƙuri." Faɗin Hajiya rai a ɓace. Nuna Aina'u dake riƙe da kunci yayi da hannu tare da faɗin, "Wannan ɗin zan bawa haƙuri? Kiyi haƙuri Hajiya, ban taɓa tsallake umarninki ba, amma yau kam bazan iya abunda kika umarceni da nayi ba. Hajiya hayaƙi ma ba sonsa kike yi na sani, Laure ko ina da tabbacin bata ma taɓa ganin wiwi ba bare ta kai bakinta, yarinyar dake fama da kanta ma ina taga lokacin shan wiwi! Nayi imani da Allah Aina'u ce tasha wiwin nan, kuma a yau ɗin nan kuma ba yanzu ba, sai ta bar gidan nan wallahi!" Da ƙarfi Hajiya tace, "To kuwa za kayi kaffara don Aina'u babu inda za taje wallahi! Wiwi dai ni nasha gama sauranta nan." Faɗin Hajiya ta hau waige-waigen inda zata hango saurin da Aina'u ta har a parlourn, da sauri tace, "Yauwa gashi nan!" A tare suka kai jiki, ita ta kai hannu, shi kuma ya kai ƙafa ya take sauran guntun wiwin don kada Hajiya ta kai hannu ta ɗauka. "Ai Hajiya da sauri kika yi kika rigasa ɗauka, kin ga idan kika kunna kika yi zuƙa ɗaya a gabansa wata ƙila yafi gasgata maganarki." Wani irin shaƙa Khalil ya kai mata tare da faɗin, "Hajiya zan kashe yarinyar nan sai dai nima a kashe ni." Da sauri Hajiya ta taso ta hau kiciniyar kwace hannun Khalil a wuyan Aina'un da har idanunta sun soma firfitowa, "Wallahi idan baka saki wuyar yarinyar nan ba zan tsine maka Ibrahim." Wani irin wurgi da ita yayi sai da kanta ya bugu da Centre table ɗin dake ɗakin ji kake tatsatsatsatsa ya fashe, take jini ya hau tsartuwa a kan Aina'u wacce tuni ta sulale ta sume, hannu Hajiya ta ɗaura a kai tare da faɗin, "La'ilaha illalah, Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam, Khalilullah!" Da sauri Khalil ya bar ɗakin a zuciye, don shi ko a jikinsa duk da uban jinin da yaga Aina'un na zubarwa. Daga nan fita yayi daga gidan gaba ɗaya domin cuku-cukun passport ɗin Sarah. Hajiya kuwa gaba ɗaya ta ruɗe sai kiran sunan Khalil da ya jima da barin gidan take yi, Laure dake zaune itama ko motsi bata yi ba, addu'a kawai take yi a zuciya Allah yasa daga suman da tayi ta wuce barzahu kowa ya huta. Ruwa fridge Hajiya ta ɗauko ta fasa a fuskan Aina'un, a gigice ta farfaɗo tana zazzaro idanu, can kuma ta tashi da sauri jini na ɗiga ta wuce ɗakin dake mallakinta ta rufo ƙofa, bata damu da ciwon jikinta ba ta matsa tafin hannunta da ƙarfi sai ga Khalil ya bayyana a immigration office suna magana da wani, wani irin zaro idanu tayi tare da faɗin, "Barin ƙasar? To ai sai kuyi tafiyar in gani duk da kuwa na san idan asibitocin duniyar zaku zaga, Sarah baza ta taɓa samun lafiya ba." Tafin hannun ta kuma matsawa, sai ga wannan mummunar halittar ya bayyana fuska a ɗaure tare da faɗin, "To uwar ƴan ƙorafi, menene kuma yanzu?" Kallon gefe tayi tare da kai hannu ta ɗauki kwalbar turaren dake kan mirror ta fasa sannan yanki hannunta na dama tare da tsiyaya jinin a fuskan wannan mummunar halittar sannan ta ɗuka akan guiwowinta tare da faɗin, "Dan tsarkin tsafin _Hell Ofulafu_ ka taimakeni kamar yanda Khalil ya zubar min da jini, ina so shima ya ɗanɗana ɗacin da naji wajen yin kuka da idanunsa, ina son a yau ayi kukan mutuwa a cikin gidan nan, sannan a hana Khalil fita daga ƙasar nan da matarsa, bama ƙasar nan ba, a kasar masa da tunanin nemawa matarsa magani ko da a wajen Kaduna ne!" Ta ƙarisa maganar ne tare da tara kanta dake tsiyayar jini a tafin hannunta, yayin da mummunar halittar nan ya saka harshe yana lashe duk wani jini dake ɗiga a jikinta. Sai da ya gama lashewa sannan ya shiga ɓaɓɓaka mahaukacin dariya tare da turo hannu ya dafa kanta sannan ya ɓace. Lumshe idanu tayi tare da faɗawa bayi don ta san ɓacewar yana nufin buƙatarta zai biya. Khalil yana tsaye yaji kamar an kwaɗa masa guduma akai yayi saurin dafe kan tare da tsugunawa. "Lafiya Khalilullah?" Abokinsa yayi saurin ɗukawa tare da faɗin haka. Bai ce komai ba, amma ya daɗe yana jin wani irin wuuuu a cikin kansa kamun ya miƙe ba tare da yace komai ba ya nufi wajen motarsa, "Ibrahim! Ibrahim!!" Abokinsa yayi kiransa yana bin bayansa, amma ko sauraran bai yi ba ya buɗe motarsa tare da shiga yaja ya bar wajen, sai da yayi nisa da immigration office ɗin sannan ya soma jin wasai a cikin kansa. Aina'u kuwa canza kaya tayi tare da yiwa kanta dressing sannan ta kunna wiwi tasha tare codine saboda zuciyarta da yayi zafi, sai da ta zuƙi wiwi ta fesar sannan tace, "Na rantse da girman Yesu Almasihu, ba don tsananin son da nake maka ba, da wannan marin da fasa kan da kamin ba zai tafi a banza. Da sai na kashe ka a yau ɗin nan, amma duk da haka, You'll pay for it!" Nafeesa na kitchen tana dafa pasta, Qasim na parlour yana kallon Tv kwance akan resting chair dake parlourn yana jiranta ta kawo abuncin, don tun da suka tashi basu ci komai ba, "Honey kin kusa?" Ya faɗi da ƙarfi ta yanda Nafeesan zata ji daga kitchen ɗin, "Soon in Sha Allah!" Faɗin Nafeesa tana mai saka carot da ta gama wankewa, a gigice ta saki ludayin dake hannuta tare da buɗe baki za tayi ihu, cak bakin ya tsaya a buɗe ba tare da ihun ya fito ba, jininta babu inda baya rawa ga fitsarin tsoro dake zirarowo daga jikinta ganin halitta mafi muni a gabanta, harce ya fiddo kamar na maciji ya caki wuyanta ya shiga tsotse jinin jikinta, sai da ya tsotse kaf sannan ta faɗi ƙasa yaraf, shi kuma ya kai hannu ya cire pipe ɗin gas ɗin tare da haɗa gobara a kitchen ɗin sannan ya ɓace ɓat. Da mugun gudu Qasim ya fito daga parlourn jin wani irin warin gas na bala'i, yana tura ƙofar kitchen gas yayi wani irin uban tsalle ya bugi fuskansa, kan kace kwabo gaba ɗaya gidan ya kama da wuta, gas ɗin nan kuwa haka ya dunga tsalle yana faɗawa gidan maƙota. Kasancewar layine na masu kuɗi, tuni har a kira ƴan kwana-kwana na Private, kuma cikin ƙanƙanin lokaci suka iso suka fara aikinsu. Sai da aka fara cire wutan unguwar gaba ɗaya sannan aka shiga kashe wutan, mutane goma sha shida ne suka yi mummunar ƙonewa, daga ciki har da Qasim mijin Nafeesa, gaba ɗaya tun daga kai har tafin ƙafa ya ƙone, ana taɓa jikinsa fata ke biyowa, Nafeesa kuwa tattare dagwargwajajen namanta aka yi, don wasu ma dun manne a jikin tiles da wuƙa aka kankaro, babu abunda ke tashi unguwar sai koke-koken mutane. Ƴan uwan Qasim kamar zasu haukace, wasu suka nufi asibitin da aka kai shi, wasu kuma suna tare da dagwargwajajen naman Nafeesa, ya LTG Abdullah suka kira, sai dai number ɗinsa bai shiga don jiya ya bar ƙasan zuwa China. Mayar da aƙalan kiran suka yi zuwa ya Abdul-Hakeem, shikuma ya kashe wayarsa gaba ɗaya saboda tashin hankalin da yake ciki, Khalilullah da driving zai dawo gida wayarsa ta hau ringing, sai da yayi parking saboda bai ɗaga kira idan yana driving sannan yayi picking, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Shine abunda ya dunga maimaitawa har ya sauke wayar a kunnansa, haɗa kai da steri yayi wasu zafafan hawaye na zubo masa daga idanunsa, ya jima yana hawaye kamun yayiwa motar key ya nufi can gidan Qasim ɗin. Tun daga nesa da layin yake hango hayaƙi da ƙauri duk da an samu nasarar kashe wutan, parking yayi ya nufi inda ƴan uwan Qasim suke, maza huɗu ne da mata biyu, matan sai rusa kuka suke yi, mazan kuma sunyi jigum-jigum suna kallon naman Nafeesa. Kai tsaye wajen dagwargwajajen naman yayi tare da duƙawa yana kallo wasu maƙudan hawaye na zirarowa daga idanunsa, jikinsa har rawa yake yi tsabar tashin hankali, "Allah ya jiƙanki Nafeesa, Allah yasa kina cikin rahamarsa, Annabi yasan da zuwanki." Yana kawowa nan ya fashe da kuka tare da saka tafin hannunsa ya rufe fuskansa. Sai da Mukhtar wan Qasim ya ɗagosa tare da janyesa gefe yana bubbuga kafaɗunsa alamar rarrashi. Haɗa kai da bango Khalil yayi, hawaye sun kasa tsayuwa daga idanunsa, dakyar ya iya controlling kansa ya fiddo wayarsa daga aljihu tare da dialing number ya Abdullah, wayar bai shiga, sai ya kira layin ya Abdul-Hakeem, shi kuma switchoff, sai ya mayar da akalar kiran zuwa layin uncle Ameeru, bigu biyu ya ɗaga tare da faɗin, "Tunda naga kiranka nasan ba alkhairi zaka faɗa min ba, don haka nan baka kira ka gaishe mu, balle kuma yanzu da kayi aure kana ganin kanmu ɗaya!" "Allah yayiwa Nafeesa rasuwa ta hanyar gobara, yanzu haka ina can gidanta!" Shine abunda Khalil ya faɗi tare da yanke kiran ba tare da ya bari uncle Ameeru ya dire salatin da ya ɗauko ba. Uncle Ameeru a gigice ya kira sauran ƴan uwansa a waya ya shaida masu, nan da nan suka haɗu suka yo gida wajen Hajiya maimakon su wuce can gidan Nafeesan kai tsaye, Hajiya najin sautikan muryansu yayin tahowarsu taji gabanta ya faɗi don ta san zuwansu ba alkhairi bane, ɗayan biyu ne, ko sun zo neman kuɗi ko kuma tijarar da suka saba yi mata. Babu sallama suka faɗa ɗakin kasancewar ƙofar buɗe take don Hajiya bata kulle ƙofa idan dai ba dare bane. "Bilkisu ashe abunda ya faru kenan? Allah ya jiƙan Nafeesa, oh! Yaushe-yaushe ƴarta ta koma, ashe itama tana tafe." Da sauri Hajiya ta miƙe tana faɗin, "Ban gane ba mai kuke faɗi ba. Nafeesar ce ta mutu? Nafeesa tawa?" Kallon-kallo aka shiga yi tsakanin su uncle Ameeru, don sun ɗauka ta san da mutuwar, Uncle Shamsu yace, "Kenan baki sani ba, ɗazun nan Khalil ya kira Ameeru yake faɗa masa gobara ta kama a gidan duk sun mutu har da mijin." Hannu Hajiya ta ɗaura akai tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sau uku sannan ta faɗi ƙasa sumamma. Laure a sittin ta fita ta nufi side ɗin aunty Maryam ta shiga bugawa da ƙarfi, ya Abdul-Hakeem na fitowa ta kamo hannunsa ta dunga jansa har ɗakin Hajiya, da sauri ya nufi Hajiya yana jijjigata tare da tambayar mai ya faru da ita, uncle Ameeru ne ya shaida masa abunda ke faruwa, a gigice ya soma karanto Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, can kuma ya cicciɓi Hajiyar zuwa mota ya fita daga gidan zuwa asibiti shi da Laure, su uncle Ameeru kuma suka wuce gidan Nafeesan. A can Asibiti kuwa, jinin Hajiya yayi mugun hawa, ya Abdul-Hakeem bai bar asibitin ba sai da Hajiya ta farfaɗo aka saka mata drip da kuma alluran bacci, bai samu sallar gawa ba, domin yayyafawa naman ruwa kawai aka yi saboda yanda tayi dagwargwaje, Khalil ne yace ba sai Hajiya ta ganta ba, don ganin naman Nafeesa zai iya jefata cikin mummunar hali, ko shi da yake namiji kuma doctor ba ƙaramin tashin hankali yake ciki ba. Suna dawowa daga maƙabarta da ya halartu mutane da yawa, don maza da matan unguwan kowa sai bada shaidar alkhairin Nafeesa yake yi. Sosai ta samu shaida mai kyau daga ƴan unguwa da dangin mijinta, don surukarta har yanzu bata cikin hayyacinta, wani mugun tashin hankalin suka kuma taraswa, gawar Qasim mijin Nafeesa aka dawo da ita shima ya amsa kiran Ubangiji domin ba ƙaramin ƙuna yayi ba, ya riga ya dahu sosai. Khalil dai ba ƙaramin tashin hankali suka gani ba a ranar, yayi wani irin zuru-zuru kamar wanda ya shekara yana ciwo. Haka suka kuma yiwa Qasim sallah bayan an yayyafa masa ruwa, don shima namar jikinsa sai zagwanyewa yake yi, bayan sun kai shi makwancinsa sun dawo, sai suka shiga gidansu Qasim ɗin aka yiwa juna gaisuwar mutuwa sannan shi da Laure da ya Abdul-Hakeem suka wuce asibiti wajen Hajiya duk da ƙanwarta Aunty ya Gana da Aunty Yaana suna tare da ita. Gaba ɗaya duk wanda ka kalla tsakanin ya Abdul-Hakeem da Khalil ba wanda bai zama abun tausayi ba. Hajiya kuwa ta farfaɗo amma ko iya ɗago idanu bata yi, harshenta ma har so yayi ya soma karyewa! Khalil kallo ɗaya yayiwa Hajiyar yaji hawaye sun taru a idanunsa, da sauri yaju ya bar ɗakin. Aunty Yaana da yare tayi wa Laure magana akan ta zauna ta tsaya a tsaye kamar sanda. Zama tayi tana kallon Hajiya hawaye na zuba a idanunta. Hannuta Hajiya ta kamo tare da faɗin, "Laure da gaske Nafeesa ta mutu? Da gaske babu auta Laure?" Sunkuyar da kai Laure tayi tana hawaye, Aunty Yagana tace, "Haba ya Bilki, kullu nafsin za'ikatul maut! Ki daina saka damuwa aranki, Allah ya fiki son Nafeesa, na san abun da zafi, amma daurewa za kiyi, addu'ar ki kawai Nafeesa take bukata matsayin ki na uwa. Bp ɗinki ya hau sosai, idan kina wannan kukan da damuwa ba zai taɓa sauka ba. Dan Allah ya Bilki, kiyi haƙuri ki sakawa zuciyarki haƙurin rashi." Duk cikin yaren Kanuri tayi mata maganar. Sai kuma ta kalli Laure tare da faɗin, "Je kira Khalil yazo yayi mata allurar bacci!" Da sauri Hajiya ta ɗaga hannu alamar bata so tare da danƙe hannun Laure da ɗayan hannunta. Sarah ba ƙaramin wahala taci ba, ga yunwar dake nuƙurƙusan cikinta amma ko motsi ta kasa, ji take kamar ana hura wuta a jikinta saboda wani irin azabar zafi da take ji, ta kai gudun ac ɗin ɗakin gaba ɗaya amma bata daina jin zafin ba, ta haɗa da warware fanka zuwa number ɗin ƙarshe nan ma kamar ƙara hura wutar jikinta ake yi. Ta cire kayan jikinta gaba ɗaya ya rage daga ita sai bra da pampers ɗin da Khalil ya saka mata nan ma dai bata ji wani salama ba, daga ƙarshe sai da ta cire komai na jikinta ta kwanta flat a ƙasan tiles amma still babu wani salama sai ma ƙaruwa da zafin yake yi ga kuma fitsarin da ya zama mara control yana zubo mata, don bata sanin lokacin da take jinsa, zubowarsa kawai take ji, tsutsotsin nan kuwa sun yi faca-faca a tsakar ɗakin. Da kyar ta rarrafa ta faɗa bayi ta dunga kwarawa kanta ruwa a jiki, amma da ruwan ya sauka a jikinta sai taji kamar tafasasshen ruwan zafi ta kwarawa jikinta. Fitowa tayi daga bayin ta zauna daɓar a ƙasa tare da fashewa da kuka tana sosa jikinta saboda wani mahaukacin ƙaiƙayi da ta soma ji kamar an watsa mata karara. Khalil bashi ya shigo gidan ba sai gab magrib gabansa na faɗuwa saboda bai ƙaunar yaga Sarah cikin wani hali gashi ya barta ita kaɗai kuma ya san mahaukaciyar ƙanwarta ba zuwa dubata za tayi ba. Ɗauke numfashi yayi jin wani uban ƙarni, zarni, hamami, ɗoyi da warin da saman gaba ɗaya ya ɗauka. Haka ya daure ya ƙarisa don yasan shi ɗinne dai, idan bashi ba babu mai iya jurewa, yana tura ƙofar ɗakin Sarah na sakin wani mahaukacin gyatsa mai tafe da lafiyayyar tusa mai warin fitar hayyaci, tuni ɗakin yayi wani irin duum akan wanda yake yi. Cikin sauri ya nufeta ganinta tsirara kuma kwance a ƙasa tana susan jiki, "Mine Lafiya, mai ya faru dake!" Da hannu bibbiyu ta soma turesa tana faɗin, "Ka bar nan wajen, wari kake yi, warin jikinka zai kashe ni, ka tashi ka fita nace!" Da mamaki Khalil ya hau shinshina jikinsa yana kallon Sarah, sai kuma yace, "Ɗakin ne ke wari, bari na gyara miki jikinki na gyara ɗakin zaki daina ji." Faɗin Khalil, Aina'u daka ɗakin Hajiya tana kallon komai cikin tafin hannunta ta ɗaura ƙafa ɗaya akan ɗaya tana ɓaɓɓaka mahaukacin dariya. Sarah kuwa duka ta shiga kai masa ta ko ina a jikinsa tana faɗin, "Ka fita nace, wari kake yi, kai abun kyama ne. Ka fita kabar ɗakin nan." Hannunta ya riƙo biyu tare da faɗin, "Naji zan fita, amma bari na gyara maki ɗakin tukun da jikinki." Ta jin haka sai tayi wuf ta miƙe ta shiga jifansa da duk abunda taci karo dashi a ɗakin har tayi sanadin fashe masa goshi. Fita yayi daga ɗakin yana mai matsanaicin jin tausayinta, ya bar gaba ɗaya abunda tayi masa yanzu matsayin depression ne ya kamata saboda halin da take ciki shi yasa take acting haka. Ɗakinsa ya koma yayiwa kansa dressing a goshi lokacin ana kwaɗa kiran sallah sai yayi alwala tare da wucewa masallaci. Sarah kuwa tun sanda aka soma kwaɗa kiran sallah sai taji gaba ɗaya zafin da take ji a jikinta ya kau, sai wani nannauyen bacci yayi gaba da ita. Lokacin da Khalil ya dawo daga masallaci, haka kawai ya yaji yana buƙatar jin karatun Alkur'ani, sai ya kunna ƙira'ar minshawi ya saka wayar a gaban aljihusa, kai tsaye ɗakin Sarah ya nufa, kwance ya sameta a ƙasa, a hankali ya tura ƙofar ya shiga, bai taɓa ta ba sai da ya gyara ɗakin tsaf sannan ya ajiye wayarsa da har a lokacin tana karatun ya cicciɓi Sarah yayi bayi da ita, daga can ɗakin hajiya kuwa, tun da Khalil ya kunna karatun nan ta daina ganinsa a tafin hannunta. Sarah na jinta a hannun Khalil ta buɗe idanunta da sauri tare da zabura, sai kuma ta mayar da idanu ta rufe, wanka yayi mata sannan ya saka ta ɗaura alwala sannan suka fito ya taimaka mata wajen saka pampers ya fiddo mata da kaya marasa nauyi ta saka ya bata hijjab ta tada sallah. Bata ƙara jin warin da Khalil ke yi mata ba saboda karatun da ya kunna, shima kuma bai ji mahaukacin warin ba, sai ya ɗauka saboda ya gyara ɗakin ne. Shi ya dafa masu indomie da kwai, sai da yaga ta ƙoshi tukun ya daina bata, sai taga ya jingina da gado yayi shuru, rai babu daɗi ta kallesa tare da faɗin, "Happiness, mai ke damunka?" Murmushin yaƙe yayi mata don bai ji zai iya faɗa mata Nafeesa ta rasu kuma Hajiya na kwance a asibiti ba, "Ina tunanin ki ne, Mine. Allah ya baki lafiya kinji!" Ya ƙarisa maganar yana kallonsa. Kallon indomie ɗin da tashi ta rage tayi tare da ƙarisowa wajensa ta saka hannu cikin plate ɗin ta dunga ɗebowa tana saka mashi a baki, ba daɗin indomie ɗin yake ji ba ko kaɗan, amma saboda bai son sosa mata rai sai yayi ta amsa har ya cinye. Kwanciya tayi a jikinsa tare da faɗin, "In Sha Allah zan warke" Ga mamakinta sai taji saukar hawayensa akan kafaɗanta, da sauri ta kallesa daidai lokacin da wayarsa ya hau ringing ɗin wakar _I miss You like crazy_, wani irin mahaukacin ihuu Sarah ta saki tare da toshe hancinta tana nuna masa waje alamar ya fita, da ɗumbin mamaki yake kallonta ita kuwa sai turashi take yi tana faɗin, "Fita nace! Fita daga ɗakin nan wari kake yi Ibrahim!!" Miƙewa yayi itama ta miƙe ta dunga turashi har waje sannan ta jawo ƙofar ɗakin ta rufe tare da zamewa jikin ƙofar ta soma wani irin kukan fitar hayyaci, har cikin zuciyarta bata jin daɗin abunda take masa, amma bata san mai yasa take jin wannan warin da ko ta ƙudurtawa zuciyarta zata jure sai ta kasa. Khalil ya jima a ƙofar yana mamaki, can kuma ya juya ya koma ɗakinsa. Wani irin tsallen murna Aina'u tayi daga ɗaki don tana ganin komai tun lokacin da karatun nan ya tsaya. Haka suka kwashi kwana goma suna yi, da ya shiga ɗakin domin gyarata zata hau ihu tana faɗin ya fita wari yake yi, tana kuma turashi da ƙarfi. Wani lokacin ƙarfi yake saka mata ya gyara mata jikinta da ɗakin sai ya ajiye mata abinci ya fita. Wani lokacin kuma sai ya bari sai tayi bacci sai ya shigo ya gyara ko ina don tana iya gyara jikinta ta canza pampers, zarnin fitsari da ƙarni da warin tsutsotsin naso ya kashe ɗakin don bata bari Khalil ɗin yayi abunda ya kamata. Kwanan Hajiya ashirin da uku aka sallamota, tunda suke asibitin ko sau ɗaya Laure bata taɓa sha'awar dawowa gidan ba, haka Aina'u bata taɓa taka ƙafarta taje asibitin ba. Ɓangaren Sarah sai abunda yayi gaba wajen kyaran Khalil, shi kuwa ko afuska bai taɓa nuna ɓarin rai ko ƙosawa da ita ba, sai ma wani irin nunkular kulawa da ya ƙara bata don duk tunaninsa depression ke damunta. Kamar daga sama sai ga Muneeba a gidan Sarah, sosai Khalil yayi murnar ganinta, har bedroom ɗin Sarah ya kaita, kuma a gaban idanun Muneeban ta yiwa Khalil ɗin koran kare, bayan fitarsa Muneeba ta hau Sarah da faɗa kamar ta ari baki, sai kawai Sarah ta fashe da kuka tare da faɗin, "To ni ya zanyi Muneeba, ina zan saka kaina! Ciwo duk yabi ya dame ni, tsutsotsi a gabana, wari da ƙarni gami da hamami a ɗakina. Mijina kuma duk lokacin da ya kusanto ni, wani irin ƙarni da hamami yake min!" Da idanu kawai Muneeba take bin Sarah, can kuma sai tace, "Sarah! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Wani irin abu nake ji haka? Shin baba da Lami sun san wannan zancen kuwa? Ai wannan ba cutar da za ayi shuru da baki bane, dole iyaye suji don cutarki bai yi kala da cutar asibiti ba. Bari ki gani ina zuwa.." Tana gama faɗin haka ta mike tare da ɗaukar jakarta domin zuwa gida ta faɗawa mahaifiyarta abunda ake ciki domin tayiwa babanta magana ayi mata treatment na Islamic. Sai dai miƙewarta yayi dai-dai da miƙewar Aina'u da sauri tare da fitowa ta tsaya bakin gate, Muneeba na fito ta soma tafiya da sauri, sai kawai ji tayi an juyo da ita da auri tare da taɓa goshinta, "Ki kalli gabas kiyi ta tafiya kar ki ƙara waiwayar nan gidan!" Gyaɗa kai Muneeba tayi tare da kallon gabas ta hau tafiya ba tare da sanin inda ta nufa ba. Wani irin dariya Aina'u ta sheƙe dashi tare da faɗin, "Babu mai ja dani ya zauna lafiya, Khalil nawa ne ni ɗaya, don ni aka halicce shi, duk wacce tayi ƙoƙarin rabani dashi sai na ɗanɗana mata azaba, haka duk wacce tayi ƙoƙarin ceton Sarah sai na wulaƙanta rayuwarta!" Tana gama faɗin haka ta juyo ta dawo cikin gida. Cikin Sarah ya shiga na wata bakwai, still babu abunda ya canza, haka kuma Khalil shima bai taɓa canza mata ba. Aina'u ta kai maƙurar ɓacin rai ganin babu wani canji daga Khalil, sai kawai ta hau shirin tafiya Abia domin samun _Hell Ofulafu_ gaba da gaba domin tayi mai kankat.. Ranar wata asabar ta tafi, wannan karan ma Ugo ne yayi mata jagora bayan sun gama watsewarsu. Ba ƙaramin tsafi Hell yayi mata ba wannan karan, sannan sai da tayi masa alƙawarin jinin mutane goma, biyar jarirai, biyar kuma waɗanda suka soma tadawa ƴan shekaru uku zuwa goma. Sannan ya bata wani kwaɗo ƙarami yace ta haɗiye, idan har ta haɗiye duk wanda ta kalla tace yayi wani abu babu musu sai yayi, sannan kuma idan har tana son asirin da za ayiwa Khalil ya kama shi, sai ta kwanta da mahaifinta. "Idan har buƙatata zata biya ko Sarkin maka kace na kwanta dashi zan kwanta dashi." Shine abunda Aina'u tace. Kwananta uku a Abia ta juyo ta dawo Kaduna, bata sauka a ko ina ba sai gida lokacin ƙarfe biyu na dare. Banƙare ƙofar gidan tayi sannan ta shiga, ɗakin baba ta nufa kai tsaye tare da tura ƙofar ta shiga don shi bai saka sakata a ɗaki. A Zaune ta samu baban don tun lokacin da ta tura ƙofar gida ya farka, hannu ta kai ta kunna switch ɗin ɗakin tare da yin wani irin tsayuwan karuwai tana mitsi-mitsin da idanu, shi kuwa baba sai yaga gama ɗaya suffarta ta koma ta Lami sak lokacin da take amarya. Wani irin mugun sha'awa ce ta shiga fuzgar baba har bai san lokacin da ya miƙa mata hannu tare da faɗin, " _Elizabeth_" ba. Aina'u kuwa wani murmushi ta saki tare da kashe wutan ta nufe shi gadan-gadan. Cike da rashin imani Aina'u ta bari mahaifin da yayi sanadin kawota duniya ya kusanceta. Sai bayan komai ya nutsa baba ya sauko daga kan gadon a gigice ya kunna wuta, arba yayi da fuskar ƴarsa kuma autarsu tana saka brezia, hannu ya kai ya dafe saitin ƙirjinsa tare da soma nunata da hannu yana son yin magana amma bakinsa ya karkace. Take ya yanke jiki ya faɗi ƙasa rabin jikinsa gaba ɗaya ya mutu. Aina'u kuwa tana gama saka kaya ta tsallakesa ta bar ɗakin ta koma ɗakinsu. Da sassafe kamun kowa ya tashi ta bar gidan ta nufi gidansu Khalil. Sarah kuwa tun asuba ta soma jin wani irin mahaukacin ciwon mara wanda bai misaltuwa don naƙuda ta soma yi gadan-gadan duk da kuwa lokacin haihuwarta bai yi ba don cikin watansa bakwai, itace har safiya tana abu ɗaya, idan ta kai hannu gabanta tana jin gashi, amma haihuwa taƙi zuwa sai nuƙurƙusan azaba take yi. Aina'u na fitowa daga gida ta shafa tafin hannunta sai ga Sarah ta bayyana cikin halin naƙuda. Wani irin nishine ya taho mata, cikin sauri Aina'u ta haɗe yatsanta biyu ta kame gam, sai Sarah taji kamar an saka igiya an shaƙe wuyarta ga kuma kan ɗa daya soma turowa............ ( _Anya Aina'u ƴar Adam ce kuwa_? 😭) *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *30* Numfashinta ne ya soma ɗauke, idanuwanta kuma suka soma rufewa ga wani irin azababbiyar azabar da take ji a ƙasanta. Hannu ta kai ƙasanta ta kuma taɓo gashin kan babynta daya soma turowa, wani irin ƙarfine ya kuma zuwa mata, da ƙarfi ta furta, "La'ilaha illalah Muhammadur Rasulullah, Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Take taji kamar hannun da ya shaƙi wuyarta an janye shi da ƙarfi, a wani irin nishi tayi mai ƙarfi daidai lokacin da Khalil ya turo ƙofar, da gudu ya ƙarisa tare da taro babyn da yayi fut ya fito, idanunta ne ya soma rufewa kuma ga wani kan babyn na ƙoƙarin fitowa amma kuma ƙarfinta ya soma ƙarewa saboda wahalar da tasha, cinyarta ya soma bugu bayan ya ajiye jaririn dake tsandara kuka akan gado, cicibarta yayi ya kwantar akan resting chair ɗin dake ɗakin ya soma ƙoƙarin cetonta, da taimakonsa Sarah ta kuma sunkuto ɗayan jaririn, yana fitowa ita kuwa ta sume. Rasa inda zai saka kansa yayi, sai ya mance gaba ɗaya taimakon da zai yi mata, da sauri ya fita daga ɗakin ya koma nashi ɗakin ya dawo hannunsa ɗauke da sabuwar reza ya yanke cibin yaran, basu da muguwar ƙanƙanta kamar ba bakwainiba, kuma dukansu maza kamar Khalil ɗin yayi kaki. Ruwa ya shafawa Sarah a fuskanta yana goga tafin ƙafarta har ta farfaɗo, rungumeta yayi tare da faɗin, "Kin gama min komai Sarah, thank you, thank you Soo much mine, mai kike so a duniyar nan inyi maki shi yanzu nan?" Murmushi tayi tare da faɗin, "Ka cigaba da sona har bayan raina, kar ka juya min baya a kowani irin hali!" Ta ƙarisa maganar tana mai shafa fuskansa. Hannu ya kama yayi kissing sannan yace, "Kin riga kin daɗe da samun wannan Sarah, Khalil naki ne ke ɗaya har abada. Tashi mu tafi asibiti a duba min ke." Aina'u gudu take yi akan titi kamar mahaukaciya domin Sarah na fara salati hotonta ya ɓace a tafin hannunta na _Hell Ofulafu_ da wannan mummunar halittar ya bayyana gaba ɗaya fuskansu ɓutu-ɓutu, mummunar halittar nan ya soma magana da ƙarfi, "Kar ki kuskura ki bari a fita da jariran nan daga gidan nan, idan ba haka ba zaki fuskanci hukunci har na tsawon shekara ɗaya, Hell ba zai ƙara amsa buƙatunki ba, don idan har suka bar gidan, jinin jariran bazai shawu ma Hell ba, kasancewar sun shaƙi iskar waje." Yana gama faɗin haka suka ɓace ita kuma ta hau buga uban sauri, cikin ikon ubangiji duk keken da ta tsayar sai yace mata ba zai je unguwar ba. Kawai sai ta hau gudu kamar mahaukaciya a kan titi. Khalil fita yayi ya nufi ɗakin Hajiya jikinsa har rawa yake yi tsabar murna, murɗa handle ɗin yayi don ƙofar a rufe take, tun da Aina'u ta nufi Abi, Hajiya ta tsiri rufe shashinta, shiga yayi amma babu kowa a parlour, kai tsaye ɗakin hajiyan ya nufa, zaune ya same su ita da Laure sun yi jigum-jigum. "Hajiya Sarah ta sauka! Kin samu mazaje har biyu!" Out of excitement ya faɗi. Hajiya ta mance rabon da tayi murna a rayuwarta irin yau, Laure kuwa kuka ta fashe dashi tare da fita da gudu ta nufi part ɗin Khalil ɗin, so take tayi magana ta nunawa Khalil irin farin cikin da take ciki, amma kuma babu bakin maganar, Hajiya Kuma ƙasa ta nufa tare da yin sujada sannan ta ɗago tare da fashewa da kuka tana faɗin, "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Allah ubangiji ya raya bisa sunnar ma'aiki ya kuma karesu daga dukkan sharrin mutum da aljan. Muje Mu'azzam inga jikokin nawa!" Ta ƙarisa maganar tana mai share hawaye. "Hajiya ai ɗauki hijjab ɗinki kawai don daga nan asibiti muka yi. Yaran da uwar suna buƙatar kulawar likitoci." Juyawa Hajiya tayi ta ɗauki hijjab har da na Laure sannan tabi bayan Khalil, a can ɗaki kuwa, Laure har ta soma gyara jinin Sarah da ya lalata ɗakin, abun mamaki kuma babu tsutsa ko ɗaya. Hajiya ɗaukar ƴaƴan tayi duka biyun ta rungume a jikinta tana jin wani irin ƙaunarsu na ratsa jikinta, "Sannu kinji, Allah yayi maki albarka uwata, sannu da ƙoƙari." Murmushi kawai Sarah tayi tare da sunkuyar da kai ƙasa. "Ɗauko mata mayafinta mu wuce asibitin." Faɗin Hajiya tana kallon Khalil ɗin, da sauri ya ɗauko hijjab a cikin wardrobe ya saka mata tare da miƙar da ita tsaye sannan ya ɗauko silipas ya saka mata. Sai da Hajiya ta saka masu kayan sanyi sannan ta miƙawa Khalil Hassan yayi masa kiran sallah a kunna tare da yi masa huɗuba da sunansa, (Ibrahim Khalil) Hussaini kuma ya saka masa sunan mahaifin Sarah (Nuhu). Hajiya riƙe da Hassan, Laure kuma ɗauke da Hussain suka fita daga ɗakin, Khalil ya kama hannun Sarah suka sauka ƙasa tare da fita daga ɗakin gaba ɗaya suka nufi parking space. A gidan baya ta zauna ita da Hajiya, shi kuma da Laure a gaba, kamar ance ya kalli ƙasa, sai ya hango kwalin _Mastika gum_ a ƙasa, da sauri ya kai hannu ya ɗauko tare da ɓare kwalin ya ɗau ɗaya ya jefa a baki yana murmushi don har ya manta rabon daya kai chewing gum bakinsa. Suna fita daga gidan keke napep ɗin da Aina'u ke ciki ya tsaya, zuciyarta sai da tayi wani irin tsalle ganin motar Khalil ya fito daga cikin gida, ko kamun ta yunkura motar Khalil ta kusa bakin titi don gidan yana gaba da titi ne. Haɗa kai tayi da guiwa tare da fashewa da kukan baƙin ciki. Juyowa mai napep ɗin yayi tare da faɗin, "Lafiya baiwar Allah?" Ba tare da tace komai ba ta fito daga napep ɗin saboda tsabar rashin imani ta bugi goshinsa da tafin hannunta tare da faɗin, " _Hell_ ga jinin wannan matsayin sassaucin hukuncinka gareni." Da sauri mai napep ɗin nan yaja kekensa ya bar layin don ya tsorata da abinda Aina'u tace, sai dai yana zuwa titin bypass, trailer tabi ta kansa. Aina'u kuwa shiga cikin gidan tayi rai a mugun ɓace ta nufi side ɗin Hajiya. A can asibiti kuwa, jariran a incubator aka saka su sannan itama uwar aka shiga kula da jikinta, sai dai aka mata ɗinki uku sannan aka saka mata ƙarin ruwa domin taji ƙarfin jikinta. Hajiya kuwa ta ɗauki waya ta dunga kiran dangi da abokan arziki tana shaida masu matar Khalil ta samu ƙaruwan ƴan biyu. Khalil kuwa bayan Sarah ta samu barci, sai ya sulale ya fita domin zuwa can gidansu Sarah ya shaida masu Sarah ta haihu. Wajajen ƙarfe goman Safiya, gaba ɗaya suna zaune tsakar gida suna karyawa, Na'ima ta kalli Lami tare da faɗin, "Lami baza ki duba baba? Tun safe ban ni ɗuriyarsa ba, ko wa'azin da ya saba kunnawa banji ya kunna ba." Taɓe baki tayi tare da faɗin, "Yesu ne yayi min maganinsa! Ai ba ƙaramin addu'a nake yi ba akan Nuhu ya daina kashe mana kunne da wannan karatu da wa'azin nan da yake saka mana ba, har fata nake Allah yasa Tv ɗin ya lalace ko kuma ya faɗo daga saman ya fashe." Miƙewa Na'ima tayi tare da nufa ɗakin baban ta ɗaga labule, wani irin ihuu ta saka tare da faɗin, "Baba ya mutu mun shiga uku!" Ai a sittin daga Lamin har sauran suka nufo ɗakin don ganin halin da yake ciki. Gashi nan dai kamar me rai kamar kuma gawa! Baki a karkace, hannu a lankwashe, ƙafa ɗaya da hannu a shanye. "Yes......" Da ƙarfi Hassana tace, "Dalla Lami ki rufe mana baki, baba na cikin wannan halin shine kike ƙoƙarin kira mana Yesu, Allah dai ya tsinewa wannan addini da kika koma!" Da sauri Lami tace, "Zan ci ubanki idan kika zagi addinina, ai gwara ni kowa yasan ba addinin sallah nake yi ba, kuma duk Sunday sai naje Church, ku Kuma fa? Sai dai kullum ayi ta faɗi a baki mu musulmai ne, amma ko sau ɗaya ba'a yin sallar!" A fusace Marfu'a tace, "Dan Allah Lami ku bar wannan maganar aji da lafiyar baba." Daidai nan suka jiyo sallamar Khalil a ƙofar gida don tun yana hanya yake kiran layin baba amma ba'a ɗagawa kasancewar bargo ya rufe wayar shiyasa su Aina'u basu ji ringing ɗin ba. "Kamar muryan mijin Sarah!" Faɗin Na'ima tare da fitowa daga ɗakin ta nufi kwar gida, "Alhamdulillah!" Faɗin Na'ima bayan taga Khalil ɗin tsaye a ƙofar gida, "Shigo Khalil, Allah ne ya turo mana kai wallahi. Babane babu lafiya yana can kwance gaba ɗaya rabin jikinsa ya shanye." Da sauri yace, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Tare da gitta Na'iman ya wuce ciki da sauri. Hassana da Marfu'a sai sharan hawaye suke yi ganin kamar babu rai a jikin baban, suna ganin Khalil suka matsa suka bashi hanya. Cicciɓan baba yayi tare da fito dashi daga ɗakin ya nufi mota, gaba ɗaya suka rufa masa baya har da Lami wacce ko arzikin mayafi babu a jikinta, hatta su Na'iman ma babu mayafin a jikinsu. Lami, baba Hassana da Marfu'a a baya, Na'ima kuma ta zauna gaba ita da Nuratu. Sai da suka hau titi sannan Khalil ya ɗan juyo ya kalli Lami tare da faɗin, "Mama, Sarah ta sauka, ta samu ƴan biyu duk maza yau da safe, dan girman Allah kar a faɗa mata halin da baba yake ciki don itama tana can asibitin ita da yaran don an saka su a kwalba ne kasancewar basu isa watannin haihuwa ba." Gaba ɗayansu cike da mamaki da kuma farin ciki suka furta, "Ƴan biyu! Inna lillahi, Hassana ashe Sarah ce zata riga ki." Na'ima ta ƙarisa da faɗin haka, Lami kuwa cewa tayi, "Yesu Almasihu nagode maka da wannan kyauta da kai min, a lokacin da ka kwace lafiyan mijina, sai kayi min kyauta da jika har biyu." Tana gama faɗin haka sai ta hau waƙa, " _Yayi! Yayi!! Yesu yayi!!! Yayi, yayi...._" "Ke dallah Lami ana jimamin halin baba kin zo kin wani dame mu da zancen banza! Yesun me? Mu Allah ne zai cecemu ba wani yesunki ba!" Faɗin Marfu'a dake kusa da ita. Lami kuwa sai da ta saka bayan hannu ta bugi Marfu'an sannan tace, " _Ya Allah mai-iko duka, Uban Ubangijinmu Isa Almasihu, wanda ba ya son mutuwar mai-zunubi ba, amma ya fi son shi juyo ga barin muguntassa, shi kuma yi rai; Ya bada iko da umurni ga masu-bautansa su furta, su fadi kuma ga mutanensa da su ke tuba da neman gafarar zunubansu. Allah ke gafartawa, yana kwancewa dukan masu-tuba da gaskiya, masu-bada gaskiya ga bisharassa mai-tsarki ba da munafunchi ba. Domin mu roke shi, shi ba mu tuba mai-gaskiya, da Ruhunsa Mai-tsarki, domin abubuwan da mu ke yi yanzu su gamshe shi; kuma sauran ranmu da ke nan gaba shiyi tsabta da tsarki, domin hakkanan a-karewa mu zo chikkin farin cikinsa na har abada, ta wurin Isa Almasihu Ubangijinmu. Ubangiji kar kayi duba ga saɓon yarinyata, ka yafe mata a cikin yafiyarka mai girma! Ka juyo da hankali da tunaninta ta gane gaskiya a cikin addinin ka ya Yesu Almasihu! Mijina kuma ka bashi lafiya da juriya duk da ya ɓace daga gaskiya, kar kayi duba da laifinsa, ka samu a cikin aljanna gaba ɗaya, Amin._" Wani irin dariya ne ya kusa kufcewa Khalil jin yanda surukar tasa ta dage da iya ƙarfinta tana addu'arsu ta kirista, gefe guda kuma yana jimamin rashin hankali irin na ƴan uwan matan nasa. "Ubangiji ba ya kare mu da komawa addininki Lami! Duk da nasan ba kullum nake sallah ba, amma bana fatan in mutu a cikin addinin Kirista, ai na taɓa jin wani wa'azi akan duk wanda yace La'ilaha illalah Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi, ba zai taɓa dauwama a wuta ba, so ina da hope ɗin zan shiga ko da kuwa wuta na fara shiga." Faɗin Marfu'a, da sauri Khalil ya juyo kuma hakan yayi daidai da wani uban burki da ya taka duk sai da suka tsorata, "Ke wacce irin jahila ce? Kina hauka ne? Kin san mecece wutar ubangiji kuwa? Ƙarya kike yi wallahi, baza ki taɓa iya jurewa azabar Allah ba, kar ki kuskura ki ƙara faɗin wannan kalmar, kiyi fatan ko hucin wuta kada Allah yasa kiji bare ki shiga ko da kuwa na daƙiƙa ɗaya ne! Wai tsaya, dukan ku kun taɓa zaman aji na islamiyya kuwa?" Girgiza kai suka yi gaba ɗaya. Dogon tsaki Khalil yaja tare da faɗin, "Akwai babban matsala!" Yana gama faɗin haka ya kunna motar tare da cigaba da tafiya ransa a ɓace. Har suka isa asibitinsa babu wanda ya ƙara ko tari, nan da nan aka shiga da baba emergency, sakamakon gwaje-gwajen da akai masa ya nuna jininsa yayi mugun hawa, wanda hakan yayi sanadin faɗuwarsa har ya samu mutuwar ɓarin jiki, ga kuma ciwon zuciya da ya kai matakin stage C. Sosai Khalil ya girgiza da ganin haka, abunda ya kawo ransa shine halin da ƴaƴansa da kuma matarsa ya kaisa wannan stage ɗin saboda tara abu a zuciya. Aina'u na shiga ɗaki ta soma jin wani irin kuuwa a kunnanta har sai da ta saka hannu biyu ta toshe kunnan tare da durƙushewa a ƙasa, can ta soma ji ana ɓarke kayan jikinta, sai da aka mata tsirara sannan aka kwara mata wani irin balaƴenƴen ruwan sayi mai ƙanƙara-ƙanƙara a jiki sannan aka shiga zubaba mata bulalan doki a jikin, yanda ƙaran dukan ke fita zaka fahimci ba wai mutum ko aljani ɗaya bane ke dukan, da wannan yace waaap, sai wannan yace shauuuu! Ba ƙaramin duka taci ba, don tun da ta shiga ciki ake dukanta har wajajan goman Safiya, ta suma yafi sau a ƙirga, gaba ɗaya jikini yayi ruɗu-ruɗu, sannan kuma aka shafe jikin da gishiri da yaji. Tsabar azaba Aina'u zawo ta dunga saki a kwance a ƙasan tiles. A can asibiti kuwa, duk wanda ya kalli yanda baba ya koma lokaci guda sai ka tausaya masa, ido ya juye, hannun da ƙafa na ɓarin dama sun shanye, harce kuma ya karye, basu Na'ima kaɗai ba, hatta Lami sai da ta fashe da kuka. Khalil jan su Na'iman gefe yayi ya shiga yi masu nasiha mai ratsa jiki, sannan ya shaida masu abubuwan da suke aikatawa ne ya jefa baba a cikin halin da yake ciki, sannan yayi masu alƙawarin idan har sun tuba sun komawa Allah duk sun daina yawace-yawacen da suke yi, shi kuma yayi masu alƙawarin akan su sai inda ƙarfinsa ya ƙare, kuma daga yau in dai kuɗi suke nema to su tambayesa, sannan ya bawa kowaccen su damar nemo sana'ar da zata riƙa yi shikuma daga nera ɗaya zuwa miliyan biyu zai bawa kowaccen su ta kama sana'a domin rufawa kai asiri, ya ƙara da faɗa masu duk wacce ta natsu a cikinsu in Sha Allah tana zaune Allah zai kawo mata mijin marainiya ya aurenta. Sannan kuma yace dukkansu sai sun koma islamiyya. Lami ma ya kirata gefe yayi ta rioƙonta akan dan girman Allah ta daina ingiza ƴaƴanta suna yin karuwanci, idan har kuɗi take buƙata tana da number ɗinsa ta kira ko nawa take da buƙata shi kuma yayi alƙawarin zai bata. Ranar dai kowa jigum-jigum ya kwana, Lami kuwa lokacin da Khalil ya kaita ɗakin da babies ɗin suke, kamar ta ɗebesu haka taji, wani irin ƙaunar yaran ya shigeta. Sarah kuwa ganin daga ƴan uwan nata har Lami duk sun koma wani silent, sai taji wani irin daɗi da natsuwa ya kamata. Babu wanda ya faɗa mata baba na asibitin har sai da ya kwana goma, Duk yanda suka ɗauka Sarah zata tashi hankalinta, sai suka ga tashin hankali yafi kwatancesu, kuka kuwa kwana tayi tana yi, yaran kuwa ƙin zuwa tayi ta basu nono saboda haushin Khalil da take ji na ɓoye mata mutuwa har biyu da kuma rashin lafiyar baban, don mutuwar Rabo ɗan wajen Na'ima da kuma Nafeesa, duk a ranar aka faɗa mata, tayi kuka kamar ranta zai bar jikinta har sai da jininta ya sake hawa. Dakyar Hajiya da Khalil suka lallasheta. Lami kuwa hankalinta gaba ɗaya ya koma wajen Aina'u ganin bata ganta a asibiti ba, rabon da ta saka Aina'un a idanunta ma har ta manta, duk a tunaninta tana wajen yawace-yawacen banzanta ne, haka nan sai taji hankalinta ya mugun tashi don ko lokacin da su Na'iman suke tashen yawon bin maza, basu wuce kwana uku ko sati a waje, sannan duk ranar duniya sai sunyi waya da ita, amma Aina'u kusan watanni uku kenan rabon da ta ganta kuma babu kiran waya, ko Lamin ta kira ta a waya bata ɗauka. Tagumi Lami ta zabga tana kallon baba da ya koma kamar wani tsumma, a hakan ma wai don yana Asibitin da ake kula dashi kenan! Ƙara kunnanta tayi zuwa bakin baba ganin magana yake yi amma bata jin abunda yake furtawa, don harcen ya riga ya karye. Sarah dake kusa dashi don kullum tana tare dashi, anan kuma take kwana duk da Lami da Na'ima suma suna nan, itama ta kawo nata kunnan amma bata fahimta ba, fita tayi ta kirawo Khalil domin yazo yaji ko shi zai gane, ko da Khalil yazo ya kara nashi kunnan, sai yaji kamar yana cewa Aliyu cikin karyewar harce, sai ya ɗago ya kalli Lami tare da faɗin, "Mama Ni dai ji nayi kamar yana faɗin Aliyu, kuna da wani ne mai suna haka?" Girgiza kai tayi tare da faɗin, "Gaskiya babu, da dai ma Lukman yace, sai ince ɗansa namiji yake nema." Da mamaki Khalil ya kalli Lami tare da faɗin, "Mama dama kina da ɗa namiji?" Gyaɗa kai tayi tare da share guntun hawaye tana kuma jin tsoron da kunyar faɗin Lukman ya mutu da kuma sanadin mutuwar tasa don ko ƴan uwansa basu sani ba, daga ita sai ƙawarta Aunty Rose Merry suka san komai, su Na'ima kuwa sun ɗauka yana can yawon banza da sace-sacen da ya saba. Khalil bai ƙara cewa komai ba sai juyawa da yayi ya kalli baba dake ta ƙoƙarin magana amma babu baki, kuma ba kowa yake kira ba sai Aina'u yana faɗin, "Allah ya isa tsakanina da Aina'u" su Khalil kuma Aina'un kawai suke ji shima kuma cikin karyewar harce sai kalmar yake yi masu kamar Aliyu. Bayan fitan Khalil daga ɗakin sai Lami ta juyo ta kalli Sarah tare da faɗin, "Sarah, kin san kuwa har yanzu babu wanda yasan inda Aina'u take! Yau watanni uku kenan rabon da na saka ta a idanu." Da sauri Sarah ta kalli Lami tare da faɗin, "Wai dama baku san tana gidana ba? Ai tana can wajen Hajiya, Maman Khalil." Da mamaki Lami tace, "Gidanki? Tun yaushe?" Sarah tace, "Ai ta jima, zata kai kusan watanni ukun da kwanaki, duk da nima sai in haɗa sati biyu ban ganta ba." Riƙe haɓa Lami tayi tare da faɗin, "Lallai Aina'u! Yanzu kuma ta san babanku ba lafiya amma ta rasa zuwa duba shi." Watsa hannu Sarah tayi tare da faɗin, "Ohooo! Ta damu dashi ne? Ni wallahi Lami, wani lokacin Aina'u tsoro take bani. Tana da mugun hali." Wani irin jijjiga baba ya fara yi yana watsa hannunsa na dama alamar dai magana yake yi amma babu mai gane abunda yake cewa, kuma Sarah yake kallo yana watsa hannun. Fadi yake Sarah ta kori Aina'u a gidanta, amma kuma bata gane ba sai kukan da take yi ganin yanda ya burkice, fita tayi da gudu tayi office ɗin Khalil, yana ciki yana duba wata petient ta afka tare da kamo hannunsa zuwa ɗakin baban. Allurar bacci yayi masa, nan da nan baccin ya kwashesa, sannan Khalil yace duk su fita daga ɗakin su bar shi ya huta. Aina'u kuwa kwananta goma a ɗakin Hajiya babu ci babu sha sai ƙarban azaba daga hannun _Hell Ofulafu_ take yi babu ƙaƙƙautawa. Dukan safe daban, na rana da ban, haka na dare. Kuma har wannan lokacin Hajiya bata san da dawowarta ba, ba ƙaramin alwashi da mugun nufi Aina'u take yi ba a zuciyarta duk lokacin da ta samu sassauci da yafiyar Hell, wani irin tsanar Sarah ta kuma ji ya ninku a zuciyarta. Watan su Sarah ɗaya a asibiti aka sallame su, idan kaga twins baza ka taɓa cewa bakwaini bane, sun yi ƙiba abunsu, haka ma Sarah ta ƙara cika tayi kyau, baba ma an sallame shi duk da jikin na nan dai jiya i yau, sai dai Khalil yace zai riƙa zuwa har gida yana yi masa gashi wanda in Sha Allah zai taimakawa jikin nasa. Satin na zagayo da sallamar su aka yi wani gagarumin taron sunan twins, _Sam'an_ da _Sauban_. Irin kyaututtukan da Sarah ta samu faɗi ɓata baki, a gaban idanun Aina'u akai komai, don ta samu sassaucin azabar, sai jinya jikinta da take yi yanzu, tayi wani irin rama da baƙi, haushi da tsanar kowa take yi a gidan, hotunan Khalilullah dake wayanta kawai take kallo taji sanyi azuciya. Khalil ya maida komai nasa da sunan Sam'an da Sauban, wani irin mahaukacin soyayya yake gwadawa Sarah da ƴaƴanta. Khalil ya bawa su Na'ima miliyan biyu-biyu kowaccen su har da Lami, sannan ya saya masu wani four bedroom flat a Jama'a road, tare da saka dukkansu a islamiyya kuma Alhamdulillah duk sun fara zuwa kuma natsuwa ta soma shiga jikinsu. Hajiya damuwarta ɗaya, ta rasa abunda ke mata daɗi a duniya, wani irin abu take ji ya tsaya mata a zuciya amma ta rasa menene wannan abun, sai ta zauna shuru tana tunani, duk tabi ta rame ita da ya Abdul-Hakeem. Kuma har yanzu ta kasa tambayarsa akan matarsa da kuma zaman gida da yake yi babu aiki. Aina'u kuwa ta warke garas, sai dai tsafinta ba zai taɓa ƙara amfani ba sai nan da shekara ɗaya, haka Hell ya faɗa mata. Baiwar Allah Sarah kuwa, yanzu bata da damuwar komai, ta warke garas kamar bata taɓa ciwo ba, tun da ta haihu bata ƙara ganin tsutsotsin nan ko guda ɗaya daga jikinta ba, sannan wannan warin da mijinta yake yi mata duk babu. Wani irin soyayya suke shimfiɗawa wanda ko lokacin da take amarya basu yi ba. Twins sun shiga wata shidda da haihuwa, yara tubarkalla don har tsayuwa suna yi idan suka kama abu, kamanninsu ya ƙara fitowa sosai da Khalil, ga wayau. Sun san Laure sosai don itace mai taya Sarah raino, amma kuma abunda ke matukar bawa Sarah mamaki shine, ko muryan Aina'u suka ji gaba ɗaya rikicewa suke yi suna kuka, Sam'an shi har wani kakkafewa yake yi.......... _Asha weekend lafiya 🤩_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *31* Tsaye take a tsakiyar ɗakin tana wani irin dariya mai tafe da hawaye baƙin ciki da kuma farin ciki lokaci guda, domin bayan tsawon shekara ɗaya har da wata uku, jiya da daddare _Hell Ofulafu_ ya dawo mata da makamanta, yanzu tana iya ganin komai ta tsakiyar tafin hannunta, sannan tana iya magana da _Hell_ da wannan mummunar halittar duk ta tafin hannun nata. Tsafinta ya ninku yanzu ta yanda tana iya ganin mutum idan taso har a jikin bango, sannan ta jikin bangon zata iya yi masa duk abunda taga dama, yanzu haka ma, tana kallon Sam'an da Sauban dake tsere a parlour, pampers ne kawai a jikinsu, tuntuni Sarah ke so tayi masu wanka amma da wannan yayi can, sai wancen ya zille yayi can, Khalil na zaune kan kujera sai dariya yake yi mata kuma yaƙi tashi ya taimaka ya kamo mata su, shekaransu ɗaya da wata uku cif, amma wayansu ya zarce tunanin mai karatu, ga magana a bakinsu kamar uwar aku. Idan Sarah ko Khalil suna so su tantancesu, sai su kira suna, misali sai suce Sam'an! To Sam'an ɗin ne zai juyo Sauban kuma harkan gabansa zai cigaba dayi kasancewar ko ita kanta Sarah sai tayi dagaske take bambance su, daga baya kamar sun gane, idan aka ce Sauban ko Sam'an, sai gaba ɗaya su juyo. Khalil ruɗewa yake yi sai ya shiga tambayar Sarah, "Dan Allah wanene Sam'an, wanene Sauban a cikinsu?" Taɓe baki take yi tare da faɗin, "Ka gano da kanka ai kai babansu ne, idan a waje aka tambaye ka yaya za kayi?" Sai Khalil yace, "To ai shiyasa nake son ki bambance min tunda ke kina gane su gudun kar inji kunya watarana!" Idan ya faɗi hakan sai ta nuna su ɗaya bayan ɗaya, ita kanta tana ganesu ne da ɗabi'unsu, Sauban yana da faram-faram kuma yana da dogon fuska, Sam'an kuma bai cika faram-faram ba, kuma fuskansa bata kai ta Sauban ɗin tsayi ba duk da shima dogon fuskan garesa, babu abunda suka ɗauko na Sarah idan ka cire dimple, amma bayan haka kaf kamannin Khalil suka yo. Wani kalan murtuke fuska Aina'u tayi ganin yanda Sarah da Khalil suke wasa suna zagaye parlourn su da ƴan biyun nasu. "Wannan shine ƙarshe farin cikinki a cikin gidan nan, ni Aina'u sai na baƙanta maki fiye da yanda kika baƙanta min, sai na wulaƙanta rayuwarki, sai na saka ki hawayen jini, sai na ruguza zuciyarki, sai na ɓalɓalta rayuwarki dana ƴaƴanki, sai na kashe ki da baƙin ciki, sai nayi kwanciyar aure da mijinki a gaban idanunki, sai na zama kishiyarki, na kuma ƙasƙantar dake. Babu aure tsakanina da mijinki, amma na rantse da Ubangijin mu Yesu Almasihu mai ceto, sai nayi tarayya da mijinki kuma a cikin gidan nan a gaban uban kowa, kuma duk wanda yace zai kawo mi shamaƙi ko shishshigi, sai na kashe shi!" Tana gama faɗin haka ta ɗauko wani icce wanda aka ɗaɗɗaure shi kamar ƴar tsana sannan ta jawo wani tulu daga ƙasan gado mai ɗauke da wani irin baƙin ruwa mai kauri sannan ta ambaci sunan Khalil sau uku sannan ta tsunduma iccen nan har sai da guiwar hannunta ya shige ciki sannan ta fiddo hannun, wani mugun murmushi ta saki tare da saka ɗayan hannunta ta fizgi gashin kanta sannan ta tura a cikin ramin idanun wannan iccen da ya koma ƴar tsana amma bana itace ba, sannan ta tsaki saitin zuciyar ƴar tsanar nan har sai da hannunta ya lume tare da ambatan sunanta sau uku sannan ta saki ƴar tsanan cikin tulun ya bata sautin 'tsumbul', sai ta mayar da tulun ƙarkashin gado tare da duƙawa ƙasan guiwowinta ta leƙa ƙarƙashin gadon ta jawo wasu ƴan tsanar guda biyar, ɗaya bayan ɗaya ta riƙa tsaka wani abu mai tsini a ƙahon zuciyarsu sannan ta jefa cikin tulun nan ta miƙe tana jin wani irin matsanaicin farin ciki ganin gaba ɗaya ɗakin ya turniƙe da hayaƙi da kuma wani irin duhu, can kuma bayan mintuna talatin komai ya washe, kuma dama _Hell_ yace idan har hakan ta faru bayan kammala aikinta, to hakan na nufin aikinta yayi! Khalil ya kai hannu zai cafki Sarah dake ƙoƙarin kama Sam'an yaji wani irin abu kamar mashi ya soki zuciyarsa da ƙarfi, wani irin baya yayi zai faɗi Sarah ta kai hannu ta riƙosa amma duk da haka sai da suka kai ƙasa saboda gaba ɗaya jikinsa ne ya saki. A ruɗe ta shiga kiran sunansa tana jijjigasa har hawaye ya wanke fuskanta, ƴan biyu kamar sun san abinda ke faruwa sai suma suka zagaye Khalil ɗin suna jijjiga cikinsa, shi kuwa duk yana jinsu, amma sai ya rasa shin a wani duniya yake, a hankali yaji zafin zuciyar na raguwa, can kuma sai ya soma jin wani baƙon al'amari na shiga zuciyarsa, kuma ya rasa shin farin ciki yake yi ko akasin haka. Zuwa can sai ya miƙe da sauri yana mai riƙe kansa, "Happy lafiya? Mai ke damunka?" Sarah ta faɗi tana mai kai hannu goshinsa, twins ma da gwarancinsu suka haɗa baki suka ce, "apy yafila? (Happy lafiya?)" Murmushi Khalil yayi tare da dungure masu kai yana faɗin, "Dan gidanku, daddy ba apy ba." Murmushi ƙarfin hali Sarah tayi don gaba ɗaya hankalinta bai jikinta, duniya bata ƙaunar Khalil yayi ciwo don bai iya ciwo ba. Kamun yayi yana jimawa, amma kuma idan ya tashi yi, kamar ba zai yi raiba haka yake. Tashi yayi tare da faɗin, "Kaina ne ya ɗan sara min, amma nasan ina shan magani zai tafi, bari naje na ɗan huta kamun lokacin sallah yayi." Gyaɗa masa kai kawai Sarah tayi jiki duk sake. Kumatunta ya kama tare da faɗin, "Smile now! Ba mutuwa zanyi ba, muna nan tare mutuwar ma baza ta raba mu ba, tare zata ɗauke mu." Duk da haka yaƙe kawai tayi, shi kuma ya hau sama ya barsu nan parlour. Jiki a sanyaye Sarah ta wuni, aikin ma dai kawai yinsa take yi. Shi kuwa Khalil, koda ya koma ɗakinsa, bai iya baccin ba, tunani kawai ya riƙa yi, can kuma ya sauko don haka nan yaji yana son zuwa side ɗin Hajiya. Saukowa yayi lokacin Sarah na ɗaya parlourn ita da yara, ba tare da ya neme su ba ya fice abunda bai taɓa yi ba. Ita kuwa Sarah bata san da fitarsa ba, ta ɗauka har a wannan lokacin yana sama a ɗakinsa. Aina'u kuma tana fitowa daga ɗakita, kai tsaye ɗakin Hajiya tayi hannunta riƙe da wani baƙin padlock, ba tare da knocking ba ta murɗa handle ɗin ƙofar da ƙarfi tare da faɗin, "Hajiya!" A razane kasancewar ita nata sihirin _Hell_ yace sai ta firgita tukun zai kamata. A razane Hajiyar ta juyo, cikin sauri Aina'u ta ɗaga padlock ɗin tare da datse shi tana dariyar samun nasara. "Aina'u kina buƙatar wani abu ne?" Hajiyan ta samu kanta da faɗin haka. Aina'u kuwa domin tabbatarwa sai cewa tayi, "Buɗe bakinki ki tsaya a haka." Nan take Hajiyar tayi kamar yanda Aina'un tace. Wani irin dariya Aina'u ta saki tare da faɗin, "To rufe bakin." Tuf Hajiya ta rufe tana mai bin Aina'u da idanu. Zaro mata idanu Aina'u tayi tare da faɗin, "Bar kallo na!" Da sauri Hajiya ta sunkuyar da kai ita kuma Aina'u ta maka mata harara tare da faɗin, "Da ace lokacin da na kira ki a waya domin ki dakatar da ɗanki ga auren yayata, kin dakatar, da yanzu kina zaune cikin lumana babu tashin hankali, amma tunda baki yi hakan ba, yanzu aka soma wasan!" Tana gama faɗin haka ta fice daga ɗakin tare da fitowa parlour dai-dai lokacin da Khalil ya turo ƙofa ya shigo, idanu huɗu suka yi da juna, wani irin ajiyar zuciya Khalil ya sauke tare da sakarwa Aina'u wani irin murmushi wanda ya kusa sumar da ita. "Aina'u!" Ya kira sunansa cikin wani irin salo, "Na'am Khalilullah mijin Saratu!" Ajiyar zuciya ya kuma saki for the second time sannan ya zauna tare da faɗin, "Zauna mana Ai'n." Yanda ya gajerta sunanta sai taji kamar duk duniya babu wanda ya iya kiran sunan kamarsa, zama tayi daf dashi kasancewar a 2sitter ya zauna, fuskantar yayi tare da faɗin, "Oh, Ai'n kamar ba cikin gidan nan kike ba, ko zuwa wajen ƴar uwarki bakya yi balle a haɗu a gaisa." Wani farrrrr da idanu tayi tare da faɗin, "To ai ku ɗinne love bird, sam baku buƙatar irin mu masu hana ruwa gudu kusa daku, kullum kafi son ganinka naniƙe jikin matarka." Kau da maganar yayi tare da faɗin, "To yanzu dai muna gayyatarki shashinmu domin taya mu hira." "As you wish, your excellency!" Dariya Khalil yayi tare da faɗin, "Sai kace wani gomna. Mu dai muna jiranki, na miƙa maki katin gayyata kullum da daddare kike zuwa kina taya mu hira!" Faɗin Khalil. "An gama ranka ya daɗe." Faɗin Aina'u. Daga nan Aina'u ta riƙa jansa da hira, sai ga Khalil har da kyakyatawa. Kamar yanda Khalil ya buƙata, da daddare sai ga Aina'u cikin wani irin mahaukacin kwalliyar ɗaukar hankali, gaba ɗaya suka kan dinning suna cin abinci ta murɗa handle ta shigo, Khalil ne ya fara juyawa fuskansa ɗauke da murmushi yana mai faɗin, "Ƙariso nan Aina'u ayi dinner ɗin dake. Sauban na riƙe a wajensa, jin muryan Aina'u duk sai ya rikice yana neman guduwa wajen uwarsa, Sam'an dake wajenta riƙe hannunta yayi gaam jikinsa na rawa. Sarah kuwa murmushi tayi tare da faɗin, "Aina'u kenan, kamar ba gida ɗaya muke ba! Ko kin koma gida ne?" Taɓe baki Aina'un tayi tare da faɗin, "Baki so gani na bane kawai." Ta faɗi hakane tare da jawo kujeran kusa da Khalil ta zauna a kai tare da kallon Khalil ɗin tare da narke fuska. tana mai faɗin, "To ayi serving ɗina mana, ko da kaina zanyi." Cikin sauri Khalil ya miƙe tare da ajiye Sauban, shi kuwa dama abunda yake jira kenan da gudu ya nufi gun mamarsa yana kuka, ita kuwa Sarah wani irin maɗaukakin mamaki ne ya rufeta ganin yanda jikin Khalil yake rawa don kawai zai zubawa Aina'u da basu taɓa ga macijiba abinci. Sai kawai ta zuba idanu tana kallon ikon Allah. "Ai'n ga couscous, ga jellof rice, wanne za'a zuba maki?" Ɗaga idanu sama tayi tare da faɗin, "Wanda kake ci shi zaka zuba min." Jellof rice ɗin ya zuba mata tare da kaza sannan ya ki plate ɗin har gabanta tare da faɗin, "Gashi _Ƙanwar matata_" wani irin ƙululun baƙin cikine ya mamaye zuciyar Aina'u jin sunan da ya kira ta dashi wai _Ƙanwar matata_! "Nafi gaban haka wallahi!" Aina'u ta faɗi cikin zuciya, amma a zahiri sai tayi wani irin murmushi tare da kallon yanayin Sarah ta gefen idanu, abun yayi wa Aina'u daɗi ganin confusion a idanun Saran. Spoon ta saka ta ɗebo abincin tare da sakawa a baki, lunshe idanu tayi jin wani daɗi da ya mamaye kunnuwanta don Sarah gwana ce wajen iya girki duk da ba yi suke yi a gida ba. Aina'u na cin abinci a lokaci guda kuma tana jan Khalil da hira, shi kuma kamar wani wawa ya saki baki sai ɓaɓɓaka dariya yake yi. Sarah miƙewa tayi ta bar wajen zuciyarta na susa, duk da tasan babu aure tsakanin Aina'un da Khalil ɗin idan dai har ba mutuwa tayi ba, sai taji wani irin matsanaicin kishi da damuwa yanda Khalil ɗin ya manta tana wajen, da dane, Aina'u bata ma isa ta ƙariso inda suke ba balle har ta zauna kusa dashi, da bata jin daɗin yanda Khalil ɗin yake ɗaurewa Aina'un fuska ganin su Na'ima yanzu har wani respect yake basu matsayin yayyin matansa, amma kuma ya kasa sabawa da Aina'u, sai ta bar hakan matsayin rashin haɗuwar jini, amma yanzu lokaci guda da taga wannan sauyin duk sai taji matsanaicin damuwa ya kamata. Bayan ta hau sama sai ta canzawa twins pampers tare da saka masu kayan baccinsu sannan ta sayar dasu har bacci ya ɗauke su lokacin ƙarfe tara da mintuna biyar amma har yanzu Khalil bai dawo ba, kwanciya tayi tare da rufe idanu amma sai taji gaba ɗaya baccin yaƙi zuwa, tashi tayi ta sauka a kan gadon tare da fitowa ta tsaya daga nan sama tana hangen Khalil kusa da Aina'u kamar zasu shigewa juna yana nuna mata abu a waya suna dariya. Da sauri ta juya ta bar wajen saboda bata son kawo zargi a zaman aurenta dashi. Ko da ta koma ɗaki, sam bacci ya kasa zuwan mata sai juyi take yi tana saƙe-saƙe a zuciya tare da duba agogo a wayarta, sai da agogo ya buga ƙarfe ɗaya sannan taji buɗe ƙofar Khalil ya shigo ɗakin, tana jinsa ya shiga toilet yayi wanka kasancewar kullum zai kwanta sai yayi wanka, kayan bacci ya saka sannan ya hayo gadon tare da gyarawa twins kwanciya ya mayar dasu ƙarshen gadon ahankali gudun kar su tashi sannan ya jawo Sarah jikinsa ya rungume, duk tana jinsa sai tayi kamar bacci take yi har ta soma jin saukar numfashinsa alamar baccin ya ɗaukesa. Ajiyar zuciya ta sauke domin ta rasa wani irin tunani za tayi, sai wajajen ukun dare bacci yayi gaba da ita. Washa gari da sassafe bata nuna masa komai ba ta haɗa masa breakfast da duk abunda zai buƙata, haka kayan da zai saka bayan ya fito daga wanka. Ita ta taimaka masa ya saka kayan sannan yayiwa twins kiss a kumatu kasancewar basu farka ba sannan suka sauko ƙasa tayi serving ɗinsa ya karya. Sun rabu kamar kullum bayan yayi hugging ɗinta tare da yi mata kiss ita kuma tayi masa addu'ar Allah ya tsare sannan ya tafi. Da sauri Aina'u dake kallon komai a bangon ɗakinta dake shashin Hajiya ta fito cikin uban kwalliya tare da isa inda yake yana ƙoƙarin buɗe mota, "Manyan gari kenan, har za'a fita ba tare da an ganni ba!" Da sauri Khalil ya kalleta tare da faɗin, "I'm so sorry Ai'n, na kusa nayi latti ne shine nake sauri, kin san jiya mun sha hira, abunda ya makarar dani kenan." "Kar inzo yau kenan?" Faɗin Aina'u tana wani kashe idanu. Waro idanu Khalil yayi tare da faɗin, "Wa! Ai ko da har ɗakin Hajiya zan biyo ki, baki san yanda hira dake yake matuƙar sani nishaɗi ba ko? Kar ma ki fara min wannan wasan." Wani shu'umin dariya Aina'u tayi tare da faɗin, "Hakane! To mu fita tare ka ɗan rage min hanya nima dama fitan zan yi." Da sauri ya buɗe mata gaban mota sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver yaja motar suka bar gidan. Sakin labule Sarah tayi tare da jinginar da bayanta jikin window ɗin tana faɗin, "Ya Allah ka tausaya min kasa ba abunda nake tunani bane akan mijina da ƙanwata. Wunin ranar sukuku tayi sa, ƙarfe shida Khalilullah ya dawo kamar yanda ya saba, sai dai kuma tare suka dawo da Aina'u kamar yanda suka fita tare, kasancewar Sarah na ɗakinsa tana fesa airfreshner, sai tayi saurin ɗaga labulan window jin ƙarar motarsa, gabanta ne ya buga da ƙarfi ganin Aina'u ta fito daga motar hannunta ɗauke da wata ƙatuwar leda bakinnan kamar zai yage tsabar washesa da take yi. Sakin labulan tayi tare da saukowa ƙasa sauri, buɗe ƙofar Khalil yayi ya shigo fuska ɗauke da fara'a, ganin yanayin matar tata duk sai jikinsa yayi sanyi, gashi tayi bala'in kyau cikin wani Indian material da tayi ɗinkin straight gown dashi, gashin kanta kuma ta kama shi in a middle ponytail, jelar gar dokin wuyanta, fuskanta yaci makeup mai ɗaukar idanu, "Wife, lafiya naga fuskanki haka?" Maimakon ta bashi amsar tambayarsa, sai cewa tayi, "Ina kuka je kai da Aina'u? You left this house together and you also came back together." Murmushi yayi tare da faɗin, "Wai Aina'u? Rage mata hanya nayi wai zata wajen ƙawarta, luckily kuma sai muka sake haɗuwa shiyasa muka dawo tare." Sarah bata iya cewa komai ba sai kallonsa da ta riƙa yi, "Come on, smile!" Ya faɗi yana mai bata side hug. Yau ma dai irin na jiya aka kuma, Aina'u ta kuma zuwa kuma still sai 1am Khalil ya dawo ɗakin, abun na matuƙar damun Sarah a zuciya, sam bata samun kulawar Khalil yanzu, ya kai yanzu ko kwalliya tayi bai kallo bare ya yaba, girki kuma Aina'u ta koma yi masa, idan Sarah ta zuba masa abinci, sai yace mata Aina'u zata kawo masa, tun Sarah na daurewa kusan sati Uku, har ta zuciya wata rana taje har side ɗin Hajiya ta samu Aina'u a ɗaki bayan Khalil ya wuce asibiti, zaune take tana kallon tafin hannunta, ba kowa bane a ciki sai Khalil dake zaune yana duba petient, bata san da zuwan Sarah ba kasancewar ba ita take kallo ba a wannan lokacin, turo ƙofar da Sarah tayi ne ya dawo da ita cikin hayyacinta tayi saurin kallon ƙofar don tasan Hajiya da Laure ko giyan wake suka sha baza su shigo mata ɗaki ba, wani kallon banza ta watsawa Sarah da taga itace a ƙofar ɗakin, a zuciye Sarah ta ƙarisa ɗakin tare da ɗauke Aina'u da mari sannan ta nunata da yatsa tare da faɗin, "Dan ubanki ki tattara kayanki ki bar gidan nan, idan ba haka ba, sai na kakkaryaki, shegiya ƴar iska, na gama gane take-taken ki, so kike ki ɗauke min hankalin miji ko? Don baki da kunya mijina kike so? To wallahi ahir ɗinki! In the first place ma na kasa gane uban da kike yi cikin gidan nan tunda ba gidan ubanki bane, to ki saurareni da kyau, ki tattara ki bar gidan nan tun kan inyi maki watsi da kayanki wallahi. Wawuya shashasha!" Tun da Sarah ta fara magana har ta dire Aina'u ko tari bata yi ba sai ma wani murmushi da take yi, amma deep down ita kaɗai tasan mai take shiryawa cikin zuciyarta. Sarah kuwa fita tayi tare da banging ƙofar. Har akai kwana uku Sarah bata kuma ganin Aina'u ba, sai tayi tunanin ko taji abinda ta faɗa mata ne ta bar gidan, sai dai kuma gaba ɗaya ta kasa gane kan Khalil, don wani lokacin har mancewa yake yi idan zai kirata sai yace, "Aina'u." Sarah gaba ɗaya hankalinta ya tashi ta soma tunanin mai Aina'u tayiwa Khalil haka. A ran kwana na huɗu, kawai sai ganin Khalil tayi ɗauke da akwatin kaya, Aina'u a bayansa shikuma ransa a mugun ɓace, a nan gaban Aina'u ya hau Sarah da faɗa abunda bai taɓa yi ba, "Wannan wani irin haukane da jahilci! Ƙanwar taki kika kora a gidan nan saboda selfishness ɗinkin? Kin bani mamaki Saratu! To yanzu na dawo da ita da kaina, she will stay here with us." Yana gama faɗin haka ya ɗauki akwatin tare da kallon Aina'u yace, "Ai'n, follow me." Da sauri Sarah tasha gabansa tare da faɗin, "Aina'u bata da ɗaki a sama." "Let go of my way Sarah Nuhu! Kar ki ja inyi maki abunda ban taɓa yi maki shi ba a daran nan." Baki sake Sarah ke kallonsa, yayin da Aina'u ke wani irin shu'umin murmushi. A gaban idanunta Aina'u ta bi bayan Khalil suka haura sama. Da daddare bayan Khalil ya dawo ɗakin Sara, don yau sun kai kusan 2am suna hira da Ai'n kamun ya dawo ɗakin Sarah. Sai da ya gama komai ya hawo kan gadon sannan Sarah ta miƙe ta zauna tare da kunna bedside lamp tare da faɗin, "Ka tashi za muyi magana Please!" A raunane tayi maganar yanda zai ji tausayinta, amma ko juyowa bai yi ba don juya mata baya yayi abunda bai taɓa faruwa ba tunda suka yi aure. Ƙara maimaita abunda tace tayi a karo na biyu, a fusace ya juyo tare da faɗin, "Baccin baza ki bari inyi cikin salama ba? Wato kin ɗauko wani hali da ba naki ba kin ɗaurawa kanki ba? Saboda tsabar kishi da rashin sanin ya kamata, shine za ki riƙa kishi da ƙanwarki ciki ɗaya, Aina'u fa ƙanwarki ce, _Ƙanwar matata!_ kin taɓa jin inda miji ya auri ƙanwar matarsa uwa ɗaya uba ɗaya kuma ba mutuwa tayi ba? Ni dalla malama kin isheni!" Yana gama faɗin haka ya fita daga ɗakin tare da bugo mata ƙofar da ƙarfi sai da twins suka firgita tare da tsala ihu. Aina'u kuwa daga ɗakinsa tana kallon komai, daga ita sai wata ƴar iskan rigar bacci da babu komai a ciki ta fito ta tsaya a bakin ƙofa, Khalil na zuwa wajen ta jawo hannunsa tare da shigo dashi ɗakin sannan ta murza key. Narai-narai tayi da fuska tare da shafa fuskansa zuwa ƙirjinsa ta shiga faɗin, "Kayi haƙuri ta hanaka bacci ko? Kar ka damu idan ita bata sonka, Ni ina sonka kuma zan kula da kai." Wani irin babu daɗi Khalil ya dunga ji amma bai san mai yasa ba ya kasa hanata abunda take yi, hannunsa ta kamo ta zaunar dashi a bakin gado tare da zama akan cinyarsa ta kamo ƙeyarsa tare da haɗe bakinsu waje ɗaya. Da sauri Khalil ya rufe idanu gabansa na faɗuwa da ƙarfi, can kuma ta ɗaga shi tare da turasa ya kwanta flat sannan ta hau kanshi ta shiga kissing ɗinsa, shi kuwa Khalil bai son lokacin da ya biye mata ba.......... _Na san yau zan sha caccaka, wallahi har gabana faɗuwa yake wajen rubuta page ɗin nan saboda nasan akwai wanda zasu tsine min tabbas, amma don Allah abunda nake so daku, kar ku kalli wannan page ɗin a wani mahanga ta daban, wallahi ko Khalil da Sarah + Hajiya suna addu'a da sauke Qur'ani kullum, abunda Allah ya rubuta sai ya faru, mutum bai taɓa wuce ƙaddararsa, Fiyayyan mahalicci ma asiri ya kamasa balle wani kashi Khalil_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *32* Gaba ɗaya Khalil ya rasa control ɗinsa, Aina'u ta juye masa kamar Sarah, yunƙurawa yayi tare da juyata ya koma kanta tare da birkice mata, sai sararaba sai da ya samu natsuwa sannan ya koma gefe, Aina'u kuwa cikin zuciyarta cewa tayi, "Na rantse da Yesu Almasihu babu uban da ya isa ya rabamu tunda na ɗanɗani zumanka, shegiya ƴar iska ashe ta san daɗin da take kwasa shiyasa kullum tana naniƙe da kai babu dare babu rana." Da sauri ta tashi zaune tana kallon Khalil da yaja zanin gado ya rufe jikinsa yana shashshekar kuka kamar wani ƙaramin yaro, "Heart, mai ya faru kake kuka?" Ta faɗi tana mai kai hannu jikinsa, wani irin tureta yayi da hannunsa ba tare da ya juyo ba yana mai jin baƙin ciki da dana sani har da na haihuwarsa da Hajiya tayi kasancewar ya kusanci Ƙanwar Matarsa wanda har ga Allah shi bai san yanda aka yi hakan ta faru ba, don gaba ɗaya Aina'u koma masa Sarah tayi, sai tunaninsa gaba ɗaya ya gushe, kuma bai dawo cikin hayyacinsa ba har sai da ya biya buƙatarsa da ita. Wani irin durowa Aina'u tayi tare da duƙawa ƙarƙashin gadon da suke kai, sai taga still tukunyar tsafinta nasan kuma bai canza kala ba, ɗagowa tayi ta kalli Khalil ɗin da har wannan lokacin shashshekar kukan yake yi yayi ruf da ciki, a hankali ta kuma duƙawa ta tura hannunta cikin tukunyar har sa da tsintsiyar hannunta ya shige sannan ta ɗago tare da hawa gadon, tun daga kan ƙeyarsa take shafa masa hannunta har zuwa kan ƙirjinsa, nan take ya mirgino tare da zuba mata idanu, still sai ta kuma rikiɗemasa zuwa Sarah, "Ina matuƙar ƙaunarki, sosai fa!" Ya faɗi yana mai kai hannu ya shafo fuskanta, caraf ta riƙe hannun tana mai jin wani irin sanyi a cikin zuciyarta don da tayi tunanin tsafin da tayi masa ya lalatace, ɗaura kansa tayi a ƙirjinsa tana yi masa tafiyar tsutsa a cikin kunne zuwa bayan kunnansa har bacci ya ɗaukesa, tana ganin haka ta ajiye kansa a kan pillow a hankali tare da sauka daga kan gadon ta kunna hasken ɗakin sannan ta jawo wannan tukunyar dake ƙarƙashin gado ta fito dashi tare da tsoma hannu ta ɗauko wannan mutum-mutumin itacen nan ta hau kan gadon tare da kaisa saitin ƙirjin Khalil, wannan baƙin ruwan ya riƙa ɗiga akai, sai da ruwan ya mamaye ƙirjin sannan Aina'u ta zaro wani abu mai kama da mashi ta ɗaga tare da cakawa da ƙarfi a ƙirjin wannan mutum-mutumin sai da Khalil dake bacci yayi wani irin zabura tare da dafe ƙirji, amma yana arba da fuskan Aina'u sai ya sakar mata murmushin tare da miƙa mata hannu alamar tazo garesa duk da yana kallon abinda ke hannunta amma bai iya ko ƙare masa kallo ba balle ya tanka. Sauka tayi ba tare da ta isa wajensa ba ta mayar da komai cikin ƙarƙashin gadon sannan ta kashe wutan ɗakin ta hau kan gadon ta shige jikinsa, a cikin daren nan sai da ta ƙara naiman Khalil sau uku sannan tayi bacci. Ɓangaren Sarah kuwa, raya darenta tayi da kuka, don yanda taga rana haka taga dare, idanunta yayi luhu-luhu, ji tayi sam baza ta iya jure rashin Khalil a kusa da ita ba, ta riga ta gama yanke shawarar zata cewa Khalil ko ita ko Aina'u, kuma ta san a irin ƙaunar da yake yi mata, itan zai zaɓa. A kunnanta akai kiran sallah, saukowa tayi daga kan gadon ta nufi bayi ta ɗauro alwala tare da tada sallah, bayan ta idar da sallar, sai ta miƙe ta hau gado saboda wani irin bacci dake fuzgar kasancewar bata samu bacci ba. Tana kwanciya baccin yayi gaba da ita. Can cikin baccinta taji ihun kukan Sam'an, da sauri ta tashi zaune tare da jawosa jikinta ta hau shayar dashi, shima Sauban kamar an tsikaresa sai ya tashi. Ko data gama shayar dasu, wayarta ta jawo ta kunna, da sauri ta diro daga kan gadon ganin bakwai da mintuna arba'in tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Breakfast ɗin Happiness." Tana gama faɗin haka ta fice ko sauraran su twins dake kuka saboda ta fita bata yi ba, jawo ƙofar tayi tare da soma saukowa daga steirs ɗin da sauri, saura steps huɗu ta sauko gaba ɗaya ta tsaya turus tana kallon ikon Allah, zaune Khalil yake a kan dinning, Aina'u kuma cikin wani irin shigar ɗaukar hankali tsaye a bayansa ta turo hannayenta ta saman kafaɗansa tana saka masa Irish a plate, daga nesa ma zaka ɗauka rungumesa tayi. Sarah har wani jiri taji yana neman yar da ita tayi saurin riƙe ƙarfen dake gefenta tana maimaita, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Cikin zuciyarta. "Ka cinye tass, ban so ka fita da yunwa." Faɗin Aina'u cikin kunnen Khalil ɗin har da ɗan cizon fatar saman kunnensa, shi kuma Khalil wani irin yaji yaja tare da cafko hannun Aina'un ya zagayo da ita tare da jan kujeran baya ya ɗaurata a kan cinyarsa sannan ya zagayo hannunsa ya rungumeta tare da faɗin, "Abincin kike so inci kuwa? Bari dai in baki tukwuicin daɗin da kika bani jiya!" A firgice suka juya gaba ɗaya suna kallon Sarah data kwatsatsa wani irin ihuuu tare da gungurowa saboda ƙafarta da ya kasa riƙeta sakamakon abunda taji ta kuma gani. Da sauri Khalil ya ture Aina'u dake jikinsa tare da ƙarisawa wajen Sarah har da haɗawa da gudu, jijjigata ya soma yi yana kiran sunanta da ƙarfi, Aina'u kuwa folding hannunta tayi tana kallonsu takaicin na neman kasheta, "Wato kai kana da taurin kai ko? Har yanzu tana maƙale a zuciyarka kenan! To zanyi maganin ka tabbas." Faɗin Aina'u cikin zuciya. Sarah kuwa tunda ta faɗo ƙasa ta fita daga hayyacinta, taimakon gaggawa Khalil ya soma bata ta hanyar bata numfashin bakinsa bayan ya toshe hancinta, wani irin numfashi taja tare da wawware idanunta, sai da ta kwashi second ashirin kamun ta saki wani ajiyar zuciya ta kuma zubawa Khalil idanu ko kyaftawa bata yi, "Mine!" Ya kirayi sunanta a hankali, caraf ta riƙe hannunsa tare da ƙanƙamesa ta shiga faɗin, "Mafarki Happiness! Mafarki nayi wai Aina'u tazo gidan nan tana neman shiga tsakaninmu. Ba gaskiya bane ko Happy?" Sarah ta faɗi tana fatan Allah yasa abunda taji ta kuma gani duk a mafarki ne. Aina'u najin haka ta ƙariso wajen tare da faɗin, "Na'am, mai kike cewa Aunty Sarah! Naji kamar kina kiran sunana." A firgice Sarah ta ɗago daga kan ƙirjin Khalil tana kallon Aina'un, can kuma ta miƙe da sauri tana kallon Khalil ɗin dake ɗuke ya kasa ko ɗago idanu balle ya kalleta saboda wani irin kunyanta da yake ji. Wasu irin ruwan hawaye Sarah ta shiga zubarwa tare da duƙawa akan guiwowinta ta shiga faɗin, "Happy, mai na rageka dashi a cikin gidan nan? Ta ina na gaza? Shin ka taɓa nemana a shimfiɗa na ƙaurace maka? Ƙanwata Khalil! Ƙanwata uwa ɗaya uba ɗaya kake nema Khalil!! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!! Ka cuce ni ka cuci rayuwarka, da iliminka, da matarka da ƴaƴanka da komai kake aikata zina! Wallahi tallahi baka yi min adalci ba." Ta ƙarisa maganar tana mai rushewa da kukan baƙin ciki, can kuma ta ɗago ta kalli Aina'u tare da faɗin, "Ke kuma asararriya wulaƙantacciya, watsatstsiya azzaluma muguwa mai shiga tsakanin mata da miji, anya kuwa ke jini nace Aina'u? Anya kuwa ba canje akai wa Lami a asibiti ba? Zo ki fice ki bar gidan nan ko wallahi inyi ajalinki, bazan taɓa bari kici galaba akan mijina ba!" Sarah na gama faɗin haka ta kwasa da gudu ta nufi kitchen tare da ɗauko wuƙa ta fito da gudu tayo kan Aina'u tana faɗin, "Fita ko in kashe ki sai dai nima a kashe ni!" Da sauri Khalil ya shiga tsakani tare da kwace wuƙar a hannun Sarah yana faɗin, "Baki da hankali ne Mine?" A zafafe tace, "Eh bani da shi! Tun ranar da ka fara naniƙewa Aina'u na rasa hankalina, kuma bazan taɓa dawowa cikin hankalina ba sai ranar da ka rabu da ita." Hannu biyu yasa ya riƙo damatsanta tare da faɗin, "Ki dawo cikin tunaninki Sarah, ni da Aina'u babu abunda ke tsakanin mu sai wa da ƙanwa, ita ɗin fa ƙanwarki ce, Aina'u Ƙanwar matata ce kawai." "Ƙarya ne, ni ba ƙanwar matarka bace kawai, ka faɗa mata gaskiya kawai tunda yanzu ta san komai, idan zata iya haƙuri, to! Idan kuma baza ta iya ba, hanya a buɗe take, amma maganar ni ƙanwar matarka ce kawai wannan ba haka yake ba, ka gama kwanciya dani a ɗaki jiya kana min ihun daɗi da sambatu, har kana faɗin baka taɓa samun natsuwa a jikin Maman twins ba kamar yanda jiyan ka samu a jikina, ohh duk ka manta da wannan kenan?" Zaro idanu Khalil yayi don ya san wallahi shi bai ce haka ba. Itama Aina'un zaro masa idanun tayi tare da faɗin, "Ko ba haka bane!" "Ya ke Kuma anan son kashe wuta kina ƙara rurawa!" Ko kamun su ankara Sarah tayi kukan kura ta wanke fuskan Aina'u da maruka hagu da dama tare da shaƙar mata wuya tana faɗin, "Sai na kashe ki yau a cikin gidan nan!" Da kyar Khalil ya janye Sarah a jikin Aina'u sai aika mata da maruka da naushi take yi, Aina'u kuwa wani irin zuciya ne ya yunƙurota, take ta danna yatsarta tsakiyar tafin hannunta sannan ta murza da ƙarfi. Nan take wani zuciya ya yunƙurowa Khalil ya ɗaga hannu tare da wanke fuskan Sarah hagu da dama sai da tayi taga-taga zata faɗi, da mugun mamaki take kallonsa hannunta dafe da kunci hawaye na tsiyaya. Khalil kuwa jawo Aina'u yayi ya rungume har da jijjigata kamar baby yana faɗin, "Akwai inda ke yi maki ciwo muje asibiti?" Girgiza kai Aina'u tayi tana wani narkewa tare da faɗin, "Ka ɗaukeni muje ɗakinka, tsoro nake ji kar ka fita ta nemi kashe ni, muje ɗaki kar ka fita ko ƙofa yau!" Cak ya ɗauketa tare da saɓata a kafaɗa ya gitta Sarah da tayi mutuwar tsaye. Aina'u kuwa wani irin gwalo rayiwa Sarah mai tsayawa a zuciya sannan taja hannunta wajen wuyanta alamar zan kashe ki sannan ta shiga nunata da ɗan yatsa tana jijjigawa alamar gargaɗi. Zubewa Sarah tayi a ƙasa tama kasa kuka sai kalle-kalle kawai take yi a ɗakin, can kuma ta girgiza kai tare da faɗin, "Tabbas wannan ba Khalil ɗina bane, Khalil ɗina bai son ganin ɓacin raina kuma bai son damuwata, dole akwai abunda Aina'u tayi masa, haka nan Khalil ba zai taɓa canza min ba. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!!" Haka Sarah ta dunga maimaitawa har kuka ya kufce mata. Tafi ƙarfin awa guda a wajen kamun ta tashi ta haura sama, daidai ɗakin Khalil ta jiyo saurin da ya kusa tsayar da numfashinta, "Ohh my God! Aina'u you're soooo sweet, wallahi kinfi zuma daɗi!! Na baki kaina ki cinyeni tasssss, show me Ai'n, show me that you love me, do it properly, ohhh myyyyyyy.........." Da mugun gudu Sarah ta bar wajen tare da faɗawa ɗakinta, ko kula su Sauban dake kuka bata yi ba ta shiga rera nata kukan, bata gansu ba, amma idanunta ya gama hasaso mata hotonsu gaba ɗaya a idanunta, data kulle idanu abunda take gani kenan, nan da nan jikinta ya ɗauki wani irin zafi mai tsanani tare da ciwon kai. Sauban ne ya tako ya iso wajen gadon tare da kama rigar baccinta ya shiga ja yana faɗin, "momiiii." Shima Sam'an sai ya taho shima yana kukan, da kyar ta iya kai hannun ta ɗauko su duka ta rungume a jikinta ta kuma fashewa da kuka, kamar wanda suka san kukan da take yi, suma sai suka ƙara fashewa da kukan. A haka ta shayar dasu hawayeta na ɗiga a jikinsu har suka ƙoshi sannan ta miƙe da kyar ta cire masu pampers sannan ta kaisu bayi tayi masu wanka ta shiryasu duk tana kukan sannan itama tayi wankan ta fito ko mai bata shafa ba ta zura doguwar riga tare da haɗa kayanta da na twins ɗin a cikin akwati ta goya Sam'an ta riƙe Sauban a ɗaya hannun ɗayan Kuma ta shiga jan akwatin, tana fitowa Aina'u na fitowa daga ɗakin Khalil don bayan sun gama abunda suka yi da Khalil ɗin sai ta shafa hannunta ta shiga hango Sarah daga ɗakinta tana ɓaɓɓaka dariya, don ba ƙaramin daɗin ganin halin da Sarah take ciki take yi ba. Ko kallonta Sarah bata yi ba duk da kuwa tana fitowa ta ganta, amma sai tayi kamar bata ganta ba don zuciya zai iya sakawa ta caki maƙogwaranta ta faɗi ta mutu. "Ke dawo nan!" Aina'u ta faɗi bayan ta murza tafin hannunta. Babu musu Sarah ta juyo ta dawo inda Aina'un take, "Menene a cikin akwatin nan kuma ina zaki?" Faɗin Aina'u. "Kaya twins ne da nawa, kuma gida zani." Sarah ta bata amsa cikin zuciyarta tana mamakin yanda akai take sauraran Aina'un. "To ki koma, babu inda zaki, ai baki fara ganin komai ba tukun, so nake zuciyarki ta buga ki mutu saboda baƙin ciki kamar yanda nima kika ɗanɗanamin baƙin ciki. Maza koma ɗaki yanzun nan!" Aina'u ta ƙarisa maganar da ƙarfi, "My love meke faruwa?" Faɗin Khalil daga ciki jin ihun Aina'un. "No, babu komai yi kwanciyarka." Komawa yayi ya kwanta don dama a kwancen yake, ita kuma tabi bayan Sara dake ƙoƙarin buɗe ɗakinta da harara. Tun daga wannan ranar Sarah ta koma hoto a cikin gidan ita da yaranta, don sai ta kwana bakwai bata saka Khalil a cikin idanunta ba, tayi wani irin mugun rama kamar mai ciwon ƙanjamau, ga wani irin mugun tsoron Aina'un da take yi, don har ɗaki Aina'u ke biyota tana bata command, ita ke masu girki tayi serving ɗinsu, sannan idan sun gama taje ta kwashe kayan ta kai kitchen ta wanke, da daddare kuma su dame ta da ihu ita da Khalil ɗin, kwana take yi bata bacci, amma duk da haka bata taɓa tunanin ta tashi ta raya daren ba ko da da raka'a biyu ta kai kukanta wajen Allah, babu abunda take yi sai kuka, sallolin nan biyar dai basu wuce ta, amma bata san tayi azkar ɗin safe dana maraice ba, ko kuma ta buɗe Qur'ani ta karanta ba. Sai dai ta zauna tsakiyar gado tayi ta kuka. Ɓangaren Khalil kuwa, yafi Aina'u rama, a fuskane kawai kamar yana farin ciki, amma deepdown zuciyarsa ciwo take masa, duk lokacin da zai sadu da Aina'u, koma masa take yi Sarah, sai bayan ya kammala sai ta rikiɗe ta dawo masa Aina'u, haka shima zai ta kuka har gari ya waye, yanzu sallar ma ya daina zuwa masallaci kwata-kwata, a nan ɗaki yake yi, kamun Aina'u ta soma korashi parlourn don _Hell_ yayi mata warning akan idan har yana Sallah a inda kayan tsafinta yake, komai zai lalace. Yauma Sarah na zaune akan gado tana sana'arta, sai ji tayi an bugo ƙofar da ƙarfi, da sauri ta ɗago jikinta na rawa ganin Aina'u ce, su Sauban kuwa dake wasa a ƙasa har sun yo kan Aina'u sun ƙanƙame, "Ki tattara kayanki tsaf ki koma ɗakin ƙasa da zama, ko da wasa kar in ƙara ganin ƙafarki a saman nan." Aina'u na gama faɗin haka ta fice daga ɗakin, don yau kama Khalil tayi a bakin window ɗin Sarah yana kallonsu ita da ƴaƴanta kasancewar akwai haske a barandar, ita kuma Aina'u ta tashi fitsari taga bai ɗakin shine ta fito ta gansa jikin window ɗin yana hawaye. Yana jin motsinta ya share hawaye da sauri tare da soma kame-kame. Ɗaki ta nuna masa da hannu, suf-suf-suf ya wuce ita kuma tabi window ɗin da harara tare da yin kwafa ta bishi ɗakin. Wannan dalilin ne ya saka ita kuma ta kori Sarah daga saman gaba ɗaya. Ita Sarah har cikin ranta ta san Aina'u bata bar Khalil haka ba, amma rashin dabara da hankali ya saka ta kasa kai kukanta zuwa ga Allah. Watan Sarah Shidda a cikin wannan bala'in amma ko sau ɗaya bata taɓa jaraba kai kukanta ga mahalicci ba, sai dai kuka wani lokacin kuma tace Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, tuni ta yaye su twins don daga ita har Khalil ɗin duk sun zama abun tausayi da tsoro don ba ƙaramin rama suka yi ba, shi kuwa Khalil duk ranar da yaje asibiti, don asibitin ma ba kullum take bari yake zuwa ba, sai couligue ɗinsa sun yi masa caaaa akan mai ke damunsa duk ya rame, wasu kuwa sun fara zargin halin da yake ciki na neman ƙanwar matarsa, don Aina'u kullum sai ta saka shi a gaba sun fita zuwa wajajen shaƙatawa tare, suyi hotuna wani lokacin ma a hotel suke kwana. Yau ya kasance Sunday babu inda Khalil yake zuwa, sai dai sau da yawa basa wuni a gida shi da Aina'un, don yana daga cikin ranakun fita yawonsu, zaune yake a parlour daga shi sai gajeran wando, Aina'u kuwa ta ɗaura kanta a kan cinyarsa tana danna waya, can wata ƙawarta ta turo mata da bp sai da ta gama kallo sannan ta nunawa Khalil tare da faɗin, "My love yau wannan style ɗin za muyi!" Ƙarban wayar yayi ya kalla da kyau sannan yace, "Kuma fa zai yi suger." Tashi Aina'u tayi tare da faɗin, "Bari ma ka gani dama bamu taɓa yi a parlour ba." Tana faɗin hakan ta kai hannu zata zame boxer ɗinsa, da sauri ya riƙe tare da faɗin, "Sarah might come out ita da yara, muje ciki kawai." "Ni kuma anan nake son muyi!" Tana gama faɗin hakan ta sutale masa wando tare da soma yi masa blowjob, tuni ya manta da batun su Sarah zasu iya fitowa ya hau moaning, gaba ɗaya ya fice daga hankalinsa kuma dama abunda Aina'un take so kenan, nan da nan ta cire ƴar iskar doguwar rigar dake jikinta ta yar ta hau kan Khalil ɗin daidai lokacin da twins suka fito parlourn kamar an jeho su. Da gudu Sarah ta fito daga ɗayan parlourn jin ihun su Khalil ɗin a parlour kuma taga lokacin da twins suka fita, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sarah ta faɗi da ƙarfi tare da kai hannu ta rufe idanun twins tana wani irin kuka, don ko da suka fito suka ga abunda Khalil ɗin suke yi, cak suka tsaya sunata kallo. Shi kuwa Khalil wani irin tsalle yayi tare da ture Aina'u yana kare jikinsa yana mai jin kamar ƙasa ta tsage ya shige ganin yaransa sun ga abunda yake yi. Hannunsu Sarah ta kama tana kuka tare da shigewa ɗayan parlourn. Da sauri Khalil ya saka wandonsa ba tare da ya kalli Aina'u ya wuce sama. Aina'u kuma tsaki tayi tare da ɗaukar rigarta ta saka ta zauna tana kaɗa ƙafa. Bayan mintuna talatin Sarah ta fito ta samu Aina'u a inda take, zubewa tayi kan guiwowinta tana kuka sosai tare da faɗin, "Aina'u dan girman Allah, dan ƙaunar da Allah yakewa Manzonsa s a w, idan kina ƙaunar ki shiga aljanna kiyi haƙuri ki koma gida ki fita daga rayuwar mijina ki warware koma menene ki kai masa don na san duk abunda yake yi ba cikin hayyacinsa yake ba." faɗin Sarah don ta mance Aina'un ma da daɗe da barin musulunci. Wani irin dariya Aina'u ta fashe dashi tare da faɗin, "Wallahi babu uban da ya isa ya raba ni da Khalil, kuma da gaske mijinki ba a hayyacinsa yake ba, amma kuma har ya mutu babu wanda ya isa ya warware abunda nayi." Faɗin Aina'u tare da miƙewa ta hau sama. Sarah ta jima tana kallonta kamun ta koma ta kamo hannun twins ɗin suka fita daga ɗakin don ta gama yanke hukuncin mayar dasu side ɗin Hajiya za tayi saboda gudun gurɓacewar tarbiyansu. Tana shiga ɗakin Hajiya ta idda Laure bisa darduma ta kai kanta ƙasa sa shashsheƙar kuka take yi tana ganawa da ubangijinta. Turus ta tsaya tana auna hauka da rashin hankalin ta, "Idan dai har Laure zata yi sujjada tana kuka domin buƙatarta wajen ubangiji, to ni mai na tsaya yi kenan? Tabbas babu maganin da Ubangiji bai dashi.........." *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *33* Koda Laure ta ɗago fuskanta, jaga-jaga yayi da hawaye saboda kukan da tayi, zama Sarah tayi akan kujera hannunta riƙe dana twins tana ta kallonta har ta idar da sallar. Bayan ta shafa addu'a sai tayiwa Sarah murmushi tana mai miƙawa twins hannu, gaba ɗaya sai suka tafi wajenta, Sarah miƙewa tayi ta nufi ɗakin Hajiya, sai da ta Kwankwasa sannan ta murɗa ta shiga, zaune ta samu Hajiya ta zabga uban tagumi, duk da irin ramar da Sarah tayi, ba ƙaramin tsoro da tausayi Hajiya ta bata ba saboda yanda ta koma ta yanƙwane, "Hajiya ina wuni?" A ɗan tsorace Hajiya ta ɗago tana kallon Sarah don bata ji shigowarta ba. "Lafiya ƙalau Sarah, zauna mana, ina ƴan biyu kyautar Allah?" "Suna parlour wajen Laure." Sarah ta bata amsa hawaye na ciccikowa daga idanunta. Wani ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da kallon Sarah tace, "Sarah ban san mai ke faruwa a cikin gidan nan ba, komai ya tsaya cak, babu walwala da farin ciki, zukatu cunkushe suke da baƙin ciki, hasken dake gidan nan gaba ɗaya ya dusashe, ƴaƴana sun manta dani, Marmari bai taɓa yini bai kirani a waya ba, Muhammad Kabir shima bai taɓa kwana ba tare da yaji muryata ba, amma yanzu tsayin shekara ɗaya har da watanni biyar rabon da naji muryansu, ko balle kuma su tako suzo inda nake, na rasa wannan wani irin al'amari ne wannan, uwata!" Hajiya ta ƙarisa maganar hawaye na zubo mata. Gaba ɗaya sai jikin Sarah yayi mugun sanyi ganin tsohuwa na hawaye. Hannunta Sarah ta dafa tare da faɗin, "Hajiya kiyi haƙuri, amma ni a tunanina ba hakannan ba su ya Abdallah zasu ƙaurace maki har na tsawon shekara ɗaya da watanni! Hajiya addu'a da roƙon Allah har da sadaka zaki fara daga yau akan Allah ya karkato maki da dukkan hankalinsu a kanki, in Sha idan muka miƙawa Allah lamuranmu da kyakkyawar yaƙini, in Sha Allah zai yaye mana damuwarmu, Hajiya gaba ɗaya mun mance da Allah shiyasa shima ya mance damu, kuma na tabbata idan muka koma garesa zai amshi buƙatunmu da hannu bibbiyu. Hajiya ban san cewar duk tsawon shekarun nan aikin banza nake yi ba wajen raya darena da kuka ba sai yau da na shigo ɓangaren nan na tarar da Laure na ganawa da ubangijinta tare da ƙasƙantar da kanta tana kuka. Hajiya muyi koyi da Laure in Sha Allah duk matsalolinmu zasu gushe!" Shuru Hajiya tayi tana sauraren Sarah cike da jin kunya da kuma dana sani akan rashin kai kukanta tuntuni zuwa ga mahalicci, sai hakan ya tuno mata da marigayi (Nuruddeen Muhammad) mahaifinsu Khalil, da wani abu ya shige masa duhu ko kuma yana fuskantar matsaloli, nan da nan yake ƙara nau'ikan ibadu akan wanda yake yi, dama kuma azumin litinin da Alhamis ya zame masa jiki da kuma sallar dare, sai ya ƙara ninkawa, almajirai yake tarawa fiye da ɗari kuma ya shiga cikinsu su sauke ƙur'ani sau goma a cikin sati guda, sannan ya shiga sadaka a masallatai tare da gidajen maru, maƙowa kuwa kyautatawarsu daban take, hakan ne ya saka duk tuggun da ƴan uwansa suke binsa dashi yake koma masu. Kuma ƙa'ida ne lokaci da yake raye, tun su Khalil na ƙanana sai ya haɗa kansu har matan sun sauke ƙur'ani duk bayan kwana goma, bayan rasuwarsa da kuma yanayin aikinsu gami da mai da hankali kan tsantsan boko ya saka suka watsar da komi, kuma Lokacin da yake da rai, kullum gidan cikin sauraren karatun Alƙur'ani ake. Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da kallon Sarah tace, "Tabbas Saratu duk abunda kika faɗi hakane. Wato lokacin da mahaifinsu Khalil yake da rai, wallahi kullum cikin gidan nan karatun Alƙur'ani ake saurare, sannan duk bayan wani lokaci, Alai sai ya tara almajirai anyi saukar ƙur'ani da sadaka, bayan rasuwarsa ne komai ya watse!" "Hajiya a shawarce, ya kamata komai da ake yi cikin gidan nan ya dawo har abada." Faɗin Sarah. "In Sha Allah, uwata. Nagode maki sosai da tunatarwarki uwata, Allah yayi maki albarka." Faɗin Hajiya. Sarah ta amsa da ameen tare da miƙewa ta fita daga ɗakin, a parlour, su twins na ganin mahaifiyarsu sai suka bar jikin Laure da sauri tare da ƙarisowa wajenta, Sarah tayi-tayi su koma a atafau suka ƙi, haka nan ta koma side ɗinta dasu, babu kowa a parlour sai tayi saurin shigewa ɗaki don kallo kujeran dake parlourn zai iya saka ta faɗi ta mutu, don gaba ɗaya hoton Khalil da Sarah take gani tsirara a kan kujerar. Aina'u kuwa duk abubuwan da Sarah ta tattauna da Hajiya tana kallon komai daga ɗaki, wani ƙuƙulun takaici ne ya tokare mata waya ganin Sarah tun ba'a je ko ina ba tana son lalata mata shirinta. Tashi tayi ta kullo ƙofar kasancewar ko da Khalil ya bar parlourn ɗazu, ɗakin Sarah ya shige ya kulle kansa, sai ta ɗuka ta fiddo wannan tukunyar tare da tura hannun ciki ta ɗauko wannan mutum-mutumin na itace ta matse saitin zuciyarsa da ƙarfi tare da tsundumawa cikin tulun sannan ta kuma cirowa ta ƙara danna ƙirjinsa sannan ta saki daga sama ya faɗa tsumbul a cikin tulun tare da mayar da tulun ƙasan gado sannan ta shafa tsakiyar tafin hannunta sai ga hoton fadwa ƴar wajen Marfu'a, Bobo da Nana ƴan wajen Hassana, mimi ƴa guda da ta ragewa Na'ima, Sai Sultee da haidar ƴaƴan Nuratu. Wani murmushi tayi tare da zana maciji a hannunta, nan take macijin ya soma motsi tare da tafiya da sauri-sauri, ɗaya bayan ɗaya macijn nan ya dunga saransu suna zuba ihu kasancewar gaba daya suna wasa ne a tsakar gidan, yayin da iyayensu suke makarantar dake gaban gidan kaɗan, Na'ima ce kawai bata je saboda fama da ciwon kai da take yi kwana biyu, Lami kuma tana ɗaki ta saki ac tana sharar barci don bata jima da dawowa gidan ba daga gidan Aunty Rose Merry. Da gudu Na'ima ta fito jin wani irin mahaukacin ihu da Mimi ta saki sakamakon saran maciji, dai-dai nan Lami itama ta fito da sauri, a kan idanunsu macijin ya sulale yabi bayan flowers ya ɓace amma su basu ga ɓacewar nasa ba. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" "Lord of Jesus!" A tare Lami da Na'ima suka faɗi haka sannan suka yi kan ƴaƴan da gudu suna jijjigasu, cikin ƙanƙanin lokaci har fatan jikinsu ta sauya kala ta koma green yayin da baƙin kumfa ke fita daga bakunansu suna wani irin jijjiga, kuka Na'ima ta fashe dashi tare da ɗaura hannu a kai, can kuma ta nufi gate da gudu ta fita ko mayafi babu tana kuka tana faɗin a taimaka mata, tare suka dawo da maza biyar cikin gida, inda yaran suke ta kaisu tana kuka, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Mai ya same su?" Gaba ɗaya suka faɗi suna mai isa kusa da yaran tare da taɓa su. "Macijine ya sare su, nima ihunsu naji na fito sai naga macijin da sauri yabi bayan flowers ɗin na." Ɗaya daga cikin su ya nufi bayan flowers ɗin yana dubawa, "Tabbas kuwa! Ga saɓarshi nan a nan wajen!" Ya faɗi yana mai ɗago saɓar macijin. Huɗun da suke kan yaran suka kalli juna bayan tabbatar da babu sauran numfashi a jikin yara, "Yaro yi min bayani, sun mutu ko?" Faɗin Lami tana mai duƙowa tare da taɓa wuyan Mimi dake daf da ita. "Iya sai dai haƙuri, Allah ya riga ya ɗauki rayuwar waɗannan ƴaƴan." "Yesuuuuuu! Wannan azaba da jarabawar ya isa haka! Muna yabonka Ya Allah: mun dauki cewa kai ne Ubangiji. Dukan duniya tana yi maka sujadda, Uba Ma-dauwami. Agareka Malaïku duka suna tada murya, da Sammai da Ikoki duka da ke cikinsu. A gareka Charubin da Sarafin kullayomi suna tada muriya. Mai-tsarki, Mai-tsarki, Mai-tsarki: Ubangiji Allah Mai-runduna. Samma da kasa cike su ke da Sarautar darajarka. Jama’a masu daraja ta zamaninka tana yabonka. Managarcin zumunta ta Annabawa tana yabonka. Jama’a mai-daraja ta Masu-shahada suna yabonka. Ekklisiya mai-tsarki cikin dukan iyakar duniya tana shaidanka: Ya Uba mai-sarauta mara-iyaka: Danka kuma mai-girma, mai-gaskiya, ma-kadaici: Ruhu Mai-tsarki kuma Mai-taimako. Kai ne Sarkin Daraja: Ya Almasihu. Kai ne Da matabaci na Uba. Sa’anda ka dauka ma kanka ka ceci mutane, ba ka yi kyamar cikin buduruwa ba. Sa’anda ka yi nasara da zafin mutuwa, ka budi Mulkin Samma ga masu-bada gaskiya duka. Kana zaune ga hanun damar Allah (Astagfutullah) a cikin darajar Uba. Muna bada gaskiya za ka zo ka zama mai-shari’anmu. Muna rokonka fa, ka taimaki bayinka: wandanda ka fanshe su da jininka mai-daraja: Ka maishe su a-cikin lissafin tsarkakanka, a-cikin daraja ta har abada. Ya Ubangiji ka ceci jama’arka, ka sa ma gadonka albarka. Ka malke su: ka ɗaɗɗaga su har abada. Yo da gobe muna girmama ka; Muna sujadda ga sunanka kuma kullum ba matuka. Ya Ubangiji da yardarka ka tsare mu kar mu mutu da zunubi. Ya Ubangiji ka yi mana jinkai: ka yi mana jinkai. Ya Ubangiji ka bar jinkanka shi rufto mana: da shike ban gaskiyarmu tana gareka. Ya Ubangiji, a-gareka na bada gaskiya, kada ka bar ni na rude har abada. Wannan yara da suka koma izuwa gareka a yau, ka hura ruhinsu a cikin tsarkinka, ka yafesu a cikin irin yafiya naka, mu kuma ka karemu kar muyi mutuwa irin nasu, Yaaa Yesu Almasihu uba!" Kallon-kallo mutanan nan suka shiga yi, don duk a tunaninsu Lami musulmace duk ganin da suke yi mata, sai yaji da suka ji uban yabo da ta kwararo suka fahimta, "Ashe aljihun baya ce!" Ɗayan ya kalli ƴan uwansa ya faɗi, shi kuma mai riƙe da fatar maciji yace, "To Allah ya ƙara nauyin ƙasa!" A fusace Na'ima tace, "To ba amin ba! Wannan wani irin Magana ce haka kuke yi? Ai ko da ace a cikin addinin Kirista aka haifi su Mimi bai kamata kuce haka ba tunda dai basu san komai ba, kuma ko yanzu a makarantar Annabi Ibrahim zasu tashi in Sha Allah! Balle kuma Ni uwarsu acikin musulunci aka haife ni kuma, na furta kalmar Ashhadu Allah ilaha Illallah, Wa Ashhadu anna Muhammadan abduhu wa rasuluhu!" Da sauri mutumin yace, "Allah ya baki haƙuri, kiyi haƙuri dan Allah!" Na'ima bata kuma cewa komai ba sai kukan da take yi. Ita ta riƙa ɗaukar ƴaƴan tana kaisu ɗaki tare da rufesu har kai, bata yarda ko gawa ɗaya Lami ta taɓa ba, sai da ta kulle ɗakin sannan ta fito sanye da hijjab tana kuka ta nufi makarantarsu, shugabar makarantar ta sanarwar komai tare da roƙonta akan tazo tayiwa yaran wanka ta shiryasu. Sosai shugaban makarantar mai suna Malama Nusaiba ta tausaya mata tare da lallashinta ta kuma bata baki sannan ta kira su Nuratu don saura mintuna goma a tashi a islamiyar, suma sai da tayi masu nasiha mai ratsa jiki sannan ta shaida masu abunda ke faruwa, kuka suka fashe dashi duka, bata hanasu ba kasancewar ba kururuwa suke yi ba. Tare suka koma gidan har da Malama, kuma kamar yanda Na'ima ta buƙata, malamar ce tayi masu wanka sannan ta suturtasu da kikkafani. Khalil na kwance yayi ruf da ciki akan gado, ya rasa duniya mai ke yi masa daɗi, gaba ɗaya ji yake ya tsani kansa gaba, "Why am I even alive?" Be san sanda ya faɗi hakan ba yana mai kaiwa katifa nausuka kamar zararre! Burum Aina'u ta faɗo ɗakin tare da kama ƙugu tana kallonsa idanu a ƙanƙance, da sauri ya miƙe zaune yana kallonta gabansa na faɗuwa don duk lokacin da ta zuba masa idanu haka, matsanaicin tsoronta yake ji har gabansa na bugawa da sauri-sauri. Nuna kanta tayi tare da faɗin, "Ni! Ni zaka wulaƙanta Khalil saboda kaga matarka da ƴaƴanka? Wato idan mutuwa zanyi sai dai in mutu ko? Ka san cewar ban kawo ba, amma saboda tsabar iskanci da wulaƙanci shine ka sauka ka barni da wahala ko?" Ko mai Khalil bai iya ce mata ba, ji yake ƙirjinsa yayi masa wani irin zafi da ƙunci, hawaye ne yaji suna neman zubowa amma bai basu sararin haka ba, yana jin mugun tsanar Aina'u kamar ya kasheta, amma yana jin sam ko afuska ba zai iya nuna mata hakan ba, duk haushi da tsanar da yake yi mata, idan har suka haɗa idanu sai yaji komai ya washe. "Ina magana ka min shuru! Mahaukaciya ka mayar dani ko kuma me?" Ta faɗi a tsawace. Sam Khalil bai tsorata da tsawarta ba, amma yana ɗagowa suka haɗa idanu da Aina'u be san lokacin da ya furta, "Kiyi haƙuri dan Allah" ba. Harararsa tayi tare da faɗin, "Idan kana so inyi haƙuri in yafe maka, ka tashi yanzu ka sauka ƙasa ka samu ruɓaɓɓiyar matarsa ka koreta ita da ƴaƴanta, idan ba haka ba kuma...." Ta ƙarisa maganar tare da jan ɗan yatsarta akan kuyanta. Ƙura mata idanu Khalil yayi ko kyaftawa bai yi ba, wani uban tsawar ta kuma daka masa tare da faɗin, "Ko baka ji bane?" Da sauri ya miƙe tare da faɗin, "As you wish Ai'n!" Yana gama faɗin haka ya gittata ya fita daga ɗakin. Wani irin tsalle Aina'u ta daka tare da faɗin, "Yyyesss!" Khalil na fita daga ɗakin wasu zafafan hawaye suka shiga zubowa daga idanunsa har zuwa kan ƙirjinsa, kamar kwai ya fashe a cikinsa haka ya riƙa takawa har zuwa ƙofar ɗakin Sarah. Ya jima tsaye kamun ya saka hannu ya murɗa handle ɗin ƙofar ya shiga, duƙe take a bakin gado tana sakawa Sam'an wando, da farin ciki gami da ihu yace, "Daddy!" Yana mai nuna shi da hannu. Da sauri Sarah ta waiga tana kallon Khalil ɗin dake bakin ƙofa yana kallon ƙasa hawaye na tsiyayo masa har yana ɗiga a ƙasa. Kallon su Sam'an tayi tare da faɗin, "You two should go and play in the parlour, will meet you there in the next two minutes!" Da sauri Sauban yace, "With daddy?" Ya faɗi hakane yana mai nunasa da hannu. Ɗaga masa kai tayi tare da sauko dashi daga kan gado, dukkansu sai da suka yi shaking hannun daddynsu, har zasu wucesa sai ya dawo dasu baya ya rungume a jikinsa tare da fashewa da kuka yana mai shafa fuskansu. Sarah ce ta ƙariso wajen itama kukan take yi sosai tare da kama hannunsu ta fitar dasu sannan ta jawo ƙofar ta rufe. Kallonsa ta riƙa yi hawaye na zubar mata, shi kuma kansa a ƙasa yana zubda hawaye kuma ya kasa ɗagowa ya kalleta, "Happiness!" Ta kira sunansa a hankali. Da wani irin ƙarfi ya jawota jikinsa ya rungume ƙas tare da sakin kuka kamar yaro, irin ruƙon da yayi mata sai da taji kamar haƙarƙarinta zai ɓaɓɓalle, "Ɗan sassauta kaɗan." Sarah ta faɗi muryanta na rawa don wani irin shauƙi da missing ɗin mijinta ne ya dirar mata, "Saraaah!" Ya kirayi sunanta cikin wani irin raunataccen murya tare da riƙeta gam-gam yana jin wani irin natsuwa na mamayesa, don ba zai iya tuna when last ya riƙeta haka ba. "Sarah meke faruwa damu! Sarah na haukace, ban cikin hayyacina, ban san meke faruwa dani ba, ina jin kamar an ɗauke Khalil ɗin dake cikin jikina, Saratuuuuuu." Ya ƙarasa kiran sunansa tare da fashewa da kuka jikinsa na rawa. Wani irin tausayinsa ne ya mamaye zuciyarta, soyayya da ƙaunarsa na kuma ruruwa a zuciyarta, a lokaci guda kuma tana aikawa Aina'u da kwandon tsinuwa na raba tsakaninsu da tayi. Don Sarah duk wannan abubuwan dake faruwa har ganinsa turmi da taɓaryan da tayi da Aina'u, bai taɓa sakawa taji ta tsaneshi ba, saboda tayi imani duk abunda yake yi ba'a cikin hayyacinsa yake ba, sai dai baƙin ciki da takaici kam ta ɗebe shi iya ɗiba, don ta tabbata da za'a gwada zuciyarta, za'a tabbatar ta samu matsala, Hassan jini kuwa idan yana kaiwa million, to nata sai ya wuce, don babu ranar da bata kwana ta kuma tashi da ciwon kai mai tsanani. "Addu'a itace makamin mumini daddyn twins, ka tashi tsaye ka kai kukanka gaban Ubangiji! Ka rage bacci ka raya darenka wajen roƙon ubangiji, ka yawaita saurarar karatun Alƙur'ani in Sha Allah duk wani abun da yake damunka a zuciyarka zai yaye kuma zaka samu sauƙi. Mun samu jin daɗin duniya, mun bar ubangiji shiyasa Allah ya barmu, amma idan muka miƙa wuya zuwa ga mahalicci, komai zai wuce kamar ba'a yi ba." Ƙara rungumeta yayi tare da faɗin, "Hakane! Hakane!! Maganar ki haka take Mine." Sun kusa mintuna biyar a haka suna jin bugun zuciyar juna kumun zuwa can yayi saurin janyeta a jikinsa ya nufi wardrobe tare da soma zubo da kayan sawanta dana su twins a kan gado kuma a lokaci guda yana kuka. Da sauri ta nufesa tare da kamo hannunsa tana faɗin, "Haolii menene haka? Mai yasa kake fiddo mana da kayan sawarmu?" Fincike hannunsa tayi ba tare da yace mata komai ba ya cigaba da fito da kayan kuma yana hawaye. Ƙara kamo hannun nasa tayi tare da faɗin, "Menene haka Khalil!" Da ƙarfi yace,"Ki sake ni Mine, ki sake ni dan Allah!" Ya faɗi tare da sakin rigar da ya ɗauko ya zauna a bakin gadon tare da riƙe kansa yana kuka. Duƙawa tayi a gabansa itama tana kukan tare da soma faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir!" Tun tana maimaitawa ita kaɗai har shima Khalil ɗin ya ɗauka, duk sai suka cika ɗakin da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un." Aina'u dake ɗaki tana kallon komai a tafin hannunta ta kwaso da uban gudu har tana a dungure a steirs, ko kamun ta ida dungurowa ta saka yatsa ta caki tafin hannunta da ƙarfi, a take Khalil dake zaune ya zabura da ƙarfi tare da ture Sarah ya shiga faɗin, "Tashi! Ki tashi ki kwashi duka kayanki ku bar min gida ke da yaranki sai na neme ki!! Ki tashi nace!!!" A kiɗime Sarah ta tashi don ba ƙaramin ruɗewa tayi ba da jin wawan tsawar da ya buga mata. Ƙaton akwatinta ya jawo tare da soma loda kayanta dana yaran a ciki dai-dai lokacin da Aina'u ta banko ƙofar ɗakin ta shigo tana huci, "Wato kai kake haɗa mata kayan ko? To zo ka fice ta haɗa da hannunta." Idanu jazir Sarah ta kalli Aina'u tare da faɗin, "Aina'u ke ƴar wuta ce babu tantama! Baza ki taɓa gamawa da duniya lafiya. Fir'auna Kina samanki yake Aina'u. Uwa da uba ɗaya suka haife mu, amma wallahi tallahi billahil azeem bazan taɓa yafe maki ba ko da zanga kabarinki naci da wuta! Kin shiga tsakani na da mijina, kin shiga tsakani uwa da ƴaƴanta, Aina'u mutuwarki abun tsoro ce wallahi." Wani irin shu'umin murmushi Aina'u tayi tare da kallon Khalil tace, "Kana jin abunda take faɗi baza ka ɗau mataki ba?" Khalil dai bai ce komai ba, Sarah kuma a zuciye ta ƙarisa wajen Aina'u tare da wanke fuskanta da mari hagu da dama tare da fashewa da kuka tana faɗin, "Allah ya tsine maki Aina'u, Allah ya tsine maki albarka muguwa azzaluma, mara imani! A kafuran ma ke dutse ce, makamashin wutan jahannama! Yanzu baki ji komai ba Aina'u? Ki kwanta da mijina agaba da ƴaƴana Aina'u! Mijin yarki Aina'u!! Anya akwai tsoka a ƙirjinki kuwa? Aina'u ke ƴar wuta ce!" Wani kallo Aina'u tayiwa Khalil tare da faɗin, "Kamar yanda ta ɗaga hannu ta wanke fuskata da mari, haka nake so ka ɗaga naka hannun ka wanke fuskanta da mari, ka nuna mata babu wanda ya isa ya taɓa ni a gabanka ya zauna lafiya ko uban wanene kuwa!" Da sauri Khalil ya ce, "Aina'u......" "Don as I said!" Ta katse shi da ƙarfi. Juyawa yayi ya kalli Sarah tare da nuna mata ƙofa yace, "Get out of this house right now, and don't forget to go with your kids!" Hawaye kawai Sarah keyi tana kallonsa, irin kallon kar kayi min haka. Juya baya yayi yana hawaye gabansa na wani irin faɗuwa. Sarah kuwa wani irin kuka ne ya kufce mata, da sauri ta ƙarisa kusa dashi ta ɗuka tare da riƙe ƙafafunsa ta shiga faɗin, "Happiness, Kar Kayi min haka, ka manta alƙawarin da kayi min? Ka manta kace min zamu kasance tare, for better for worse, ka mance kace baza ka taɓa bari nayi hawayen baƙin ciki ba, ka manta kace an halicceni ne domin ka, kai ma Kuma an halicce ka ne domin ni? Ka dubi girman Allah ko don Sam'an da Sauban ka barni a ɗakin mijina." Da ƙarfi Aina'u tace, "Capital NO! You're more welcome. Park your things and get lost!" "Da mijina nake magana ba dake ba Aina'u!" Sarah ta faɗi da ƙarfi. Wani shu'umin murmushi Aina'u tayi tare da faɗin, "To ai shi kansa mijin da umarnina yake amfani. Ko baki san ni nace ya kore ki ba?" Sarah bata bata amsa ba ta cigaba da yiwa Khalil magiya. Tureta Khalil yayi tare da faɗin, "Please Sarah, don't make things worse, just do as I said." Yana gama faɗin haka ya tashi ya fita. Aina'u sai da tayi mata gwalo sannan ta fice daga ɗakin, "Sarah ki tashi kawai ki tafi kar ƴar iskan nan ta saka Khalil ya yanke igiyoyin aurenki dake kansa." Wata zuciyar ta faɗa mata haka. Da sauri ta tattare kayan ta zuba a akwati ta zuge zip tare da saka hijjab sannan ta jawo akwatin zuwa parlour ta ɗauki Sam'an ta riƙe Sauban kuma ta goya shi, sai da ta ƙarewa parlourn kallo sannan ta murɗa handle ta fita tana kuka, tana zuwan wajen gate, kamar ance ta juyo, sai ta ganshi a bayanta yana hawaye, buɗe hannunta yayi tare da saka mata Atm card ɗinsa tare da faɗin, "Current account, date of birth ɗinki ne pin ɗin. Ki kular min da kanki da yaranmu." Caraf Sarah ta rike hannun tana kuka tana girgiza masa kai, shima hawayen yake yi tare da ƙoƙarin kwatar hannunsa, da kyar ya zame hannun tare da yiwa Sam'an kiss a goshi yace, "I'm going to miss you son, ku tayani neman gafarar mummynku." Yana gama faɗin haka ya juya da sauri. Kuka sosai Sarah tayi ta rusawa kamun ta juya tare da jan akwatin suka fice daga gidan.......... ( _Wannan scene ɗin ya taɓa min Heart 😭 da gaskiyar Sarah da tace Aina'u ƴar wuta ce_) *Kuyi haƙuri da rashin ganin update jiya, transformer ɗin mu ce ta buga* *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_MATAR SAYYADEE_* *Paid book 08128755583* 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *34* Sai da ta juyo ta kuma ƙarewa gidan kallo sannan ta soma tafiya tana hawaye, kasancewar gidan babu nisa da bakin titi nan da nan ta iso bakin titin tana nishi don ba ƙaramin kaya bane a cikin akwatin har da atamfofinta na lefe kusan kala ashirin a ciki wanda ba'a ɗinka ba, don ta kwashe wasu ta saka cikin wardrobe da kuma wasu akwatinan don da maƙil yake da kaya, yanzu kuma ga kayanta dana su Sauban a ciki sannan kuma ga goyo ga kuma Sam'an dake hannu. Tsaye tayi a bakin titin tana tunanin inda zata, don ji tayi gaba ɗaya bata ƙaunar komawa gidansu, gashi kuma babu wani wajen da take dashi da zata je. "Lafiya state!" Ta faɗi a bayyane tare da saurin nufa wani shagon pos dake bakin titin ta ciri dubu hamsin tana yin hamdala a zuciya saboda taimakonta da Allah yayi wajen sa Khalil ɗin ya kawo mata ATMcard ɗinsa da yanzu bata san yanda za tayi ba don ita bata samu sararin da ta ɗauko nata ATM ɗin ba da kuma kuɗinta da take ajiye a ɗakin duk lokacin da Khalil ɗin yayi mata kyauta. Napep ta tsayar tace masa tashar kawo ze kaita, shi dakansa ya fito ya saka mata akwatin a ciki sannan ta shiga, har cikin tashar ya kaita tare da fiddo mata da kayanta sannan ta biya shi hakkinsa ta ja akwatin ta soma tafiya, nan da nan aka soma tambayarta inda zata, "Nasarawa zani!" Da sauri wani tsoho a ciki yace, "Taho nan muje dama ke kawai muke jira motar ta cika." Hamdala tayi cikin zuciyarta jin saura mutun ɗaya, don ta bala'in ƙosawa ta bar kaduna. Bayan kowa ya bada kuɗin mota tare da rubuta address da number waya da suna sannan driver yaja motar suka ɗau hanya. Sai da suka hau hanya sosai sannan gabanta ya hau faɗuwa kasancewar bata taɓa zuwa ba, sunan garin da unguwan kawai take ji a bakin baba, ga kuma ƴan biyu da suke ta yi mata kuka a cikin motar, sai wajajen ƙarfe biyar suka isa, daga nan ta roƙi mai motar akan y taimaka mata wanba zata kuma bata san garin ba, nan ya sakata a motar wamba, ko da suka isa wamba, da tambaya aka kawota layin abakwa da take ji baba Nuhu na yawan ambata matsayin layinsu. Kalle-kalle kawai take yi ta rasa inda zata nufa, gashi isha'i ake neman yi don garin ya soma duhu, wajen wani gindin bishiya ta nufa inda ta hango dattijai su bakwai a zaune a kan tabarma, da kyar take tafiya, Sauban yayi bacci a bayanta, Sam'an shima haka sagale a kafaɗanta, ga kuma ƙatuwar akwati tana ja. Har ƙasa ta ɗuka bayan tayi sallama sun amsa mata, sai duk suka zuba mata idanu suna kallonta da mamaki, gashi dai bata yi kama da mabaraciya ba balle suyi tunanin bara tazo yi. "Sannunku da hutawa baba, Ina wuni?" Faɗin Sarah, sai gaba ɗaya suka amsa mata da "Lafiya ƙalau." Cikin gurɓatacciyar hausarsu. "Baba dan Allah tambaya nake yi, ina neman gidan wani ana ce masa Nuhu, amma ya jima da barin garin nan." Kallo-kallo suka shiga yi, can kuma ɗaya daga ciki yayi wa na kusa dashi magana a kunne, sai wanda aka yiwa maganar a kunne yace, "Nuhu? Shekarunsa nawa da barin nan, kuma kin tabbata ɗan nan ɗin ne?" Shuru Sarah tayi na ƴan wasu daƙiƙu kamun tace, "Eh to, a yanda dai yake bamu labari ya tabbatar mana dashi haifaffan nan ne, kuma yace sunan unguwarmu layin abakwa, sunan mahaifinsa Murtala, mahaifiyarsa kuma Zainabu! Sannan kuma ya bar garin nan shekaru talatin da huɗu kenan, ya bar garin ne saboda ƴan uwansa basu so ya auri budurwar da yake so kasancewar ta kirista mai suna Elizabeth ana yi mata inkiya da (Lami)." Gaba ɗaya wajen suka ɗauka da faɗin, "La'ilaha illalah Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama! Wannan ai Nuhu na wajen mu take magana a kai!" Ɗaya daga cikinsu ya ƙarisa maganar da faɗin haka. "Ke yarinya ya kuke dashi?" Tun kamun tayi magana wanda ke ɗan gab da ita yace, "Tun da yarinyar ta ɗuka anan nake kallon fuskanta, babu hoton wanda na gani a kwance a fuskanta sai na ɗan uwana Nuhu." Ya ƙarisa maganar yana share guntun hawaye. "Ƴarsa ce ni!" Sarah ta faɗi muryanta na cracking. Su uku dake wajen suka miƙe a tare tare da faɗin, "Taso yarinya, gida kika zo, duk nan iyayenki ne." Wani irin sanyi da salama Sarah taji yana shiga jikinta. Miƙewa tayi ta soma bin bayansu kasancewar ɗayan ya ɗauki akwatin yayi gaba, sai ya kasance yaran ne kawai a hannunta da ƙaramin handbag ɗin da ta saya a lokacin da suka sauka. Ƙatoton gidane irin na da ɗin nan wanda aka yi sa da ginin ƙasa, sai dai yasha gyara da abubuwan zamani, kuma akwai wasu gina-gine guda biyu a tsakiyar gidan da aka yi su da cement blocks. Ɗaya daga cikin ginin bulo suka nufa mai kyau dashi, Sarah sai kalle-kalle take yi hannunta dafe da bayan Sam'an dake kwance a kafaɗanta. Hannu ya saka ya murɗa handle ɗin ƙofar tare da yin sallama sannan ya shiga. Babu kowa a parlourn sai fankar sama dake gudu sosai. "Zauna mana, suna cikine, bari na kira su." Ya faɗi hakan yana mai nuna mata kujera sannan ya bi wani ɗan dogon hanya a parlourn. Sarah kuwa kamun ta zauna sai da ta gama ƙarewa tsaftaccen parlourn mai ɗauke da set ɗin kujeru da kuma Tv bango 32 inches da idanu sannan ta shimfiɗar da Sam'an a kan 3sitter tare da kwanto Sauban sannan ta zauna ta rungumesa tana cigaba da ƙarewa parlourn kallo har idanunta suka sauka akan wani ƙatoton hoto a jikin bangon ɗaki ta bangon arewa, ƙurawa hoton idanun tayi duk da kuwa irin Black and White ɗin nan ne, su huɗu ne reras a jikin hoton, waro idanu tayi sosai tana ƙara kallon hoton da kyau, baba Nuhu ne zaune a kan wata farar kujeran ƙarfe shigen irin ta sarauta, sai wani ta gefen hagunsa mai irin kamanninsa babu bambanci yana murmushi sannan ya dafa mai kama dashi sak ɗin nan dake zaune a kan kujera, sai wannan mutumin da ya kawota cikin ɗakin da take yanzu a ta gefen wanda ya dafa baba Nuhu ya ɗan leƙo shima yana murmushi, sai shima mai kama dashi sak ta hannun damar wanda ke zaune a kan kujera ya turo hulan kansa gaba tulun gashin da ya tara ya fito ta baya da kuma gefe-gefe kansa stil shima yana murmushi, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, kaii! Kenan da baba da wannan mai kama dashi ɗin ƴan biyu ne, shima kuma wannan da ya kawo ni nan shima ɗin ƴan biyune kenan? Kenan anan nayi gadon ƴan biyu, ikon Allah!" Cike da tsantsan mamaki tayi maganar a bayyane. Daga ƙarshe sai ta tashi ta isa wajen hoton tana kallo daga tsaye. Da wani irin ihuu da murna taji an rungumeta ta baya, da sauri ta waigo tana mai cin karo da fuskan wata kyakkyawar yarinya mai kama da ita, gaba ɗayansu waro idanu suka yi suna mai shafa fuskansu suna kuma dariya at the same time, "Sunana Suhana, yarinyar wannan dake zaune a hotonan!" Suhana ta faɗi tana mai nuna hoton wanda ke zaune, don ita Sarah a tunaninta ma shine baba Nuhu, sai Suhana ta nuna shi matsayin mahaifinta, sai ta fahimci baba Nuhu shine na tsayan. "Abbana da Abbanki are twins!" Suhana ta kuma faɗi tana dariya tare da kamo hannun Sarah wacce ke ta kallon fuskar Suhana kuma murmushi yaƙi barin fuskanta. "Uwar surutu, kin tsareta da surutun ko? Ai sai ki wuce ki haɗa mata ruwan zafi a bayi tayi wanka taji daɗin jikinta sai taci abinci." Faɗin wannan da ya kawo ta cikin gidan cikin yaren _Nindire_, bayansa kuma wata kyakkyawar mata ce mai fara'a sosai, haƙorinta guda ɗaya na gefen dama na Makka ne sai kyalli yake yi. "Wallahi ga kama nan, ai surprise zamu bawa su Ya Hassan da Nnanne, sai da safe tukun duk zasu ganta." Faɗin matar tana kallon Suhana tare da faɗin, "Saura kuma kije ki faɗa masu, don na sanki da tsinannan surutu!" Turo baki Suhan tayi tare da faɗin, "kaji ta ko Ba Lukman!" Da sauri Sarah ta kalli wanda Suhan ɗin ta kira da Ba Lukman tana murmushi gano ashe wanta Lukman sunan wannan ɗin baba ya saka masa. "Baki faɗa mana sunanki ba yarinya!" Faɗin Ba Lukman. Sunkuyar da kai Sarah tayi tare da faɗin, "Sunana Saratu!" Da sauri ba Lukman yace, "Kai! Kai!! Kai!!! Suna mai girma da daraja Nuhu ya saka maki, ai sunan wacce ta riƙe mu duka kenan har shi bayan mutuwar mahaifiyarmu, kuma ita ɗin ƙanwace ga mahaifiyarmu uwa ɗaya uba ɗaya." Murmushi Sarah tayi yayin da matar Ba Lukman ta nufi inda twins suke tana kallonsu, "Tubarkalla ma sha Allah! Kaga ƴaƴa kyawawa kamar su suka yi kansu, ni wannan ma ai sun fiku nuna kamanni, taɓ! Zan iya bambance su kuwa?" Ta faɗi cikin yare, Sarah da bata jin ko zo in kashe ka, sai binsu da idanu take yi. Ba Lukman ma ƙarisawa kusa dasu yayi yana kallonsu cike da ƙaunarsu daidai lokacin da Sauban ya farka yana mai furta, "Mummyyyy, I want to piii." Ko kamun tayi wani motsi har Suhana ta isa wajen tare da sunkutoshi, shi kuwa bai mata ƙiwa ba, don suna matukar kama da Sarah shiyasa bai gane ba Sarah bace ta ɗauke shi, po ta ɗauko wankakke tas kamar ba'a komai a ciki ta ɗaurasa a kai, tana kallon fuskansa, "Momma, har da pupu zan yi!" Dariya Suhana tayi tare da faɗin, "To kayi!" Kallonta Sauban yayi ta yi kamar yana so ya gano ba mummynsa bace, sai da ya gama kashin ta wanke masa, wajen mayar masa da wando suka soma faɗa don yaƙi sam ya mayar da wandon, daga ƙarshe sai ya lankwashe ƙafar yana kuka, leƙowa Suhana tayi tare da faɗin, "Yaƙi yarda in mayar masa da wando." Sarah nufar akwatinsu tayi ta kwantar tare da fiddo masa wani wandon ta miƙawa Suhan tana mai faɗin, "Ai su haka suke, idan suka yi pupu basu taɓa yarda su mayar da wandon jikinsu sai dai wani." "Yaran nawa ashe ƴan gayu ne!" Faɗin Suhana bayan ta karɓi wandon. "Saratu ki shiga wancen bayin kiyi wanka sai kizo kici abinci." Kai sunkuye Sarah tace, "To Baba!" Ta ƙarisa maganar tare da cire hijjab ɗin jikinta ta ninke ta ajiye a hannun kujera sannan ta nufi bayi. Suhana na dawowa parlourn Sam'an shima ya tashi, sai ta haɗa su ta rungume duka a jikinta. Bayan Sarah ta fito daga wanka, sai Suhana ta nuna mata ɗakin da zata shiga domin tayi shiri ita kuma ta nufi bayi da twins domin yi masu wanka. Sarah tana shiga ɗakin, ko mai bata shafa ba, riga kawai ta zura tare shimfiɗa dardumar da ta gani a gefen gado tare shimfiɗawa ta saka hijjab ta tada sallah, sai da tayi na magrib da isha sannan ta kuma tada sallah tayi raka'a biyu, a sujadarta na ƙarshe ta shiga kwararo bukatun tana kuka sosai. Ta jima a sujada tana kai kukanta ga mahaliccinta...... _Anticipate a long page tomorrow, wallahi har yanzu ban jin daɗi, Wannan ma dakyar nayi_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* _MATAR SAYYADEE_ 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *35* Bayan ta idar da sallar, sai ta jingina da gado tana tunanin Khalil hawaye na zubo mata, hannu ta ɗaga sama tare da faɗin, "Ubangiji mahaliccin sammai da ƙassai, mai kowa mai kome, ga bawanka nan Ibrahim, ka kiyaye shi daga sharri da tsafin Aina'u, ga kwato shi daga hannun azzaluma mara imani Aina'u, ya Hayyu ya Ƙayyumu, alfarman soyayyar dake tsakaninka da mafificin halitta, Muhammadur Rasulullah (SAW) ka ceto mijina daga halakar Aina'u ya rabbis samawati al'ardi." Ta ƙarisa maganar tare da fashewa da kuka. Juyawa tayi ta kai hannu kan handbag ɗinta dake kan gado tare da buɗe zip domin ta ɗauko wayarta, a firgice ta soma zazzage jakarta tana neman wayarta mai tsada da Khalil ya canza mata ranar da suka yi celebrating first anniversary ɗinsu bayan haihuwar twins. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wallahi to duk yanda aka yi a tasha aka sace wayar nan, shikenan I missed everything including our history pictures!!" Faɗin Sarah tana mai fashewa da kuka, don sam ba satar wayar bane yafi tsaya mata a rai, hotuna da videos ɗin dake cikin wayar ne wanda dawowarsu zai yi matuƙar wuya ke mugun bata takaici. Jin alamar ana nufo ɗakin sai tayi saurin goge hawayenta tana mai ƙirƙirar smiling face tana ɗaurawa a nata fuskan. "Assalamu alaikum, Maman twins kin idar?" Faɗin Suhana, ganin Sarah a zaune sai ta juya ta koma parlourn, can sai gata da abincin a rufe a plate, murmushi Sarah tayi mata tare da faɗin, "Nagode Suhan." Murmushin itama Suhan ɗin tayi mata tare da faɗin, "Bari naje parlour wajen su twins, don har yanzu basu gane bake bace ba." Ta faɗi hakane tare da miƙewa ta fita. Bayan fitan ta, Sarah sai ta buɗe plate ɗin, alalen gwangwani ne yaji miyan source da hanta. Guda ɗaya kawai Sarah ta iya ci ta rufe, don da kyar take haɗiyewa saboda damuwar dake cinta a rai, data rufe idanunta, Khalil kawai take gani yana yi mata gizo, idan ta tuna lokacin da suke farin ciki kamun zuwan Aina'u, sai taji daɗi har sai hakan ya bayyana a fuskanta, idan kuma ta tuna baƙin cikin da Aina'u ta ƙunsa mata, sai taji hawaye na wanke fuskanta. Wani ƙaramin ƙur'ani ta gani irin mai zip ɗin nan a side drawer, hannu ta kai ta ɗauko tare da zuge zip ɗin ƙasa, ajiyar zuciya ta saki tana mai ƙoƙarin tuna when last ta riƙe ƙur'ani a hannunta ta karanta, kuka ta fashe dashi ganin ta kasa tuna wani lokaci ne na ƙarshe data ɗauki Qur'ani domin karatu, ko a can gida sai dai idan zata goge ta saka masa turare take ɗauka, amma bayan haka kam, bata ɗauka domin niyyar karatu, har akai azumi guda biyun da tayi a gidan Khalil, bata taɓa karatun ƙur'ani ba, sai dai ana yin asham wani lokacin har da tahajjut kasancewar masallacin a cikin gidansu Khalil ɗin yake, "Dole ko mai aka yi mana ya kama mu tunda mun saki Allah mun kama Duniya!" Faɗin Sarah cikin zuciya. Suratul Yusuf ta buɗe ta soma karantawa don surar na ɗaya daga cikin surorin da take matuƙar so a cikin Alqur'ani don sai da ta haddace tsaf amma rashin muraji'a yasa duk ya zube, suratul Ma'ida, Maryam, Buruj da Nisa'i, don Nisa'i ma gaba ɗaya surar ta haddace ita da Kahfi, don lokacin da suke tashin ƙawance da Muneeba, duk juma'a sai sun sauketa don musaffa suke yi. Sarah bata iya baccin kirki ba, Allah yaso ma Suhan tazo tayi mata sallama a kan tare zasu kwana a ɗayan ɗakin ita da ƴan biyu, ita kuma Sarah anan ta kwana ita kaɗai, sai dai rabi da kwata na cikin daren, raya shi tayi da tsayuwan dare saboda ta kasa baccin. A idanunta akai sallar asubah, abunda yayi matuƙar burgeta a gidan shine, tun bayan saukowar masallaci take jin sautukan ƙira'a mabanbanta na Alkur'ani cikin muryoyin maza da mata ya ɗume gidan, sai kawai itama ta hau karatu da wannan ƙur'anin data gani a ɗakin. Sai ƙarfe takwas daidai taji gidan ya ɗauki tsit, sai itama ta saka aya sannan ta rufe ƙur'anin tana mai yin sujada ɗon ta tsaya ne a kan ayar da ake sujada. Suhan ce ta shigo ita da twins har anyi masu wanka amma sun ƙi yarda ko wando ta saka masu, akwatin kayansu Sarah ta buɗe tare da fiddo kayansu ta mikawa Suhan ɗin tare da rufe akwatin ta miƙe tsaye tana nannaɗe dardumar, "Maman twins ki fito za muje muyi breakfast, you will be shock idan muka shiga side ɗin Nnanne." Ba tare da ta cire hijjab tabi bayan Suhan data rigata fita, Sarah tayi mamaki ganin duk da twins sun ganeta amma basu ƙoƙarin gudu daga wajen Suhan ba duk ƙiwarsu. Bata taras da kowa ba a parlourn, duk sun hallara ɗakin Nnanne, "Ina su Ba Lukman?" Faɗin Sarah, "Suna can ɗakin Nnanne." Suhan ta bata amsa tare da fita both hannunta na ɗauke da twins. "Da kin ajiyesu su taka da ƙafursu, sai baki wahala suke yi." Faɗin Sarah, su kuwa twins najin haka suka ƙare lafewa a jikin Suhan, Suhan Kuma cewa tayi, "Ai wallahi ban sauke su." Dariya kawai Sarah tayi don ta lura Suhan ɗin na matuƙar ƙaunar twins, itama sai taji tana ƙaunar Suhan ɗin. Sun ɗan yi tafiya kamun suka iso sashen Nnanne da yake da girman ban mamaki, ga uban uban takalma birjik a ƙofar ɗakin na maza da kuma na mata. Sallama su Sarah suka yi kamun suka shiga ciki, da maɗaukakin mamaki Sarah ta take kallon jama'ar dake ɗakin suna zazzaune akan ƙatuwar carpet ɗin dake shimfiɗe a ɗakin sun zagaye wata farar tsohuwa mai mugun kwarjini da kuma kamala kasancewar mai riko da ibada, ta tsufa sosai, amma babu ruɗewa a tattare da ita saboda zuciya da gangan jikinta sun ginu ne akan Addinin Allah cikin tafarkin _SUNNAR MA'AIKI SAW_. Suna shigowa gaba ɗaya idanu ya koma kan Sarah da kuma ƴan biyu dake hannun Suhan, gyaran muryan Nnanne tayi, sai koma ya dawo cikin nutsuwarsa don sun san dokar, babu mai magana har sai an kammala cin abinci kamun nan ake gabatar da meeting na tsawon awanni biyu rak, a dunƙule Sarah ta gaishe da duk manyan wajen, cike kuma da sakin fuska suka amsa mata gaisuwarta sannan suka nemi waje suka zauna, daga nan ƴan aikin gidan wanda a ƙalla sun kai ashirin suka gabatar da abinci, daga kowa yayi serving kansa, tunda aka fara cin abinci babu wanda ya ƙara ko kwakwkwarar motsi har suka kammala sannan ƴan aiki suka ƙara zuwa suka kwashe komai. Nnanne kuwa tun da takai lomar abinci ɗaya baki take kallon Sarah har ta kammala baya yi cokali biyar kwarara ba. Shuru gaba ɗaya ɗakin yayi ana jiran Nnanne ta soma yin magana don hakane zai bawa Kowa damar yin magana, ita kuwa Nnanne taƙi magana sai kallon Sarah da take yi kawai babu kyaftawa, "Yarinya!" Ta faɗi slowly still tana kallon Sarah. A hankali Sarah ta ɗago tana kallon Nnanne, nan take taji wasu irin ruwan hawaye na kwaranyo mata akan fuskanta ganin gaba ɗaya ɗakin nan da take duk yawansu ƴan uwan mahaifinta ne. "Yarinya daga ina, kuma ke wacece?" Nnanne ta kuma jeho mata wata tambayar, Sai da Sarah taja majina kamun tace, "Sunana Sarah, mahaifina kuma sunansa Nuhu kuma a nan gidan aka haifesa." Ta faɗi hakan tana mai nuna Ba Nura (Mai kama da Baba Nuhu) tare da cigaba da faɗin, "Sak haka Babana yake" ta ƙarisa maganar tare da rushewa da kuka tuno halin da Baba yake ciki na mutum-gawa. Wani irin ajiyar zuciya Nnanne tayi tare da soma goge hawayen da yake shirin zubowa, matan ɗakin masu raunin zuciya har sun soma kuka, Nnanne miƙawa Sarah hannu tayi alamar ta taho kusa da ita, da rarrafe Sarah ta ƙarisa tare da rungumeta ta fashe da tsumamman kuka wanda ya taɓa zuciyar mutane da dama dake ɗakin. "Ina ɗana? Ina kika baro min Hussaini na!" Faɗin Nnanne cikin kuka. Ƙara kwakwuneta Sarah tayi tare da faɗin, "Ina can Kaduna, Yana can Nnanne kullum bashi da magana sai taku, duk lokacin da zai bani labarinku, cemin yake yi ba zai iya haɗa idanu daku ba saboda abunda ya aikata maku. Nnanne baba yana can kwance kamar gawa, ba magana babu motsi!" Sarah na kowa nan sai ta kuma fashewa da kuka sosai har tana ƙanƙame jikinta duk kukan gaba ɗaya da biyu take yinsa, tunowa take da halin da Baba yake ciki da kuma halin da take ciki yanzu, sai kukan ya zama biyu. Kuka Nnanne ta fashe dashi wanda ya tada hankalin dattijan dake ɗakin sai duk suka taso suka zagayeta suna bata baki. "Na janye dokar da na saka akan Hussaini, na janye wallahi. Kuje ku taho da ɗan uwanku, kuje Hassan ku taho dashi. Ina son ganinsa kamun na koma ga Allah. Na yafe masa har abada, na yafe maka Nuhuna." Ko wannensu sai da ya share guntun hawaye. Ba Lukman kuwa wani irin farin cikine ya lulluɓesa yana mai jin daɗin saukowar Nnanne, domin ba dadun ita ba, da tuni sun nemi Baba Nuhu a duk inda yake." Hannun Nnanne a kan Sarah tare da faɗin, "Jikanta kuma takwarata, bani labarin ɗana Nuhu!" Gyara zama Sarah tayi tare da faɗin, "Nnanne idan har kina da ƙarfin zuciyar ji, to ki saurareni sai dai labarin Babana ko kuma ince maki dukkanmu, ba labari bane mai daɗin ji!" Gaba ɗaya ɗakin wani irin tsit yayi na wasu daƙiƙu kamun Sarah taja wani numfashi tare da soma faɗin...., "Tun da nake ban taɓa ganin mutum mai haƙuri da sauƙin kai kamar mahaifina ba, mu shidda ya haifa mata sai namiji ɗaya, Na'ima, Nuratu, Hassana, Lukman (Tana faɗin sunan Lukman, Ba Lukman ya ɗago don ya san tabbas shi akai wa takwara) Marfu'a, Ni Saratu da kuma autarmu Aina'u......." Tun daga karayar arzikin baba, taɓarɓarewar tarbiyansu Na'ima da irin karuwancin da suka zuba sanadin huɗubar Lami, lalacewar Lukman, sanadin shiga islamiyarta, aikin da tayi a restaurant wanda shine sanadin haɗuwarta da Khalil, cikin da yayi mata zuwa zubewarsa, gwagwarmayar da aka yi kamun auran da kuma auren, farin cikin da ta samu a gidan zuwa ciwon da tayi na tsutsa da irin kulawar da Khalil ɗin ya bata har zuwan Aina'u gidan, haihuwarta, ciwon Baba (duk da bata faɗa masu sanadi ba don itama bata sani ba) da kuma iskanci da mulkin da Aina'u ta zuba har izuwa sanadin barowarta kaduna duk sai da ta zayyane masu tana kukan fitar hayyaci. Ba ita kaɗai ba, gaba ɗaya ɗakin yara da manya kuka suke yi, "Haka Nuhu yaga rayuwa? Yanzu ƴaƴan Nuhu ne suka yi karuwanci har da ƴaƴan shegu! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!" Faɗin Nnanne tana mai dafe saitin zuciyarta, ɗaya hannunta kuma yana riƙe da hannun Sarah dake kuka. Gaba ɗaya ɗakin babu wanda bai ji mugun tausayi Sarah ba jin halin bala'in data shiga sanadin ƙanwarta ciki ɗaya! "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Nnanne!!" Ba Lukman ya faɗi da ƙarfi ganin Nnanne zata dungura don suma tayi. Nan da nan suka kwashe ta zuwa asibiti. Sai da Hajiya tayi sati tana jinya kamun aka sallame don jininta ne ya hau sosai, Sarah kuwa taga ƙaryar wani abu wai shi dangi, don kuwa irin jama'ar dake tururuwar zuwa ganinta sunfi ƙarfin a ƙirga, wannnan ya jata riiii zuwa gidansa, sai wancen ma yaja. Ɓangaren Hajiya kuwa, tun bayan tafiyar Sarah da kwana biyu wanda bata ma san bata gidan ba ta tashi tsaye sosai akan roƙon Allah, waya ta buga Maiduguri tare da faɗin buƙatunta wajen wani babban malamin musulunci tace a haɗa almajirai suyi mata sauka zata turo da abun sadaka ta waya, sannan ta kira malamin da yake masu saukar Qur'ani tun lokacin da Alai yake da rai, ta faɗa masa buƙatunta, kasancewar girma yà kama shi sosai, sai ya saka ƴaƴansa da almajirasa suka cika gidan Hajiya da karatu, ranar ba'a gidan Aina'u da Khalil suka kwana ba, ihu ta riƙa masa a kan su bar gidan, sai da aka haɗa kwanki goma ana sauka a gidan tare da buɗe gidan da hayaƙin shaiɗanu. A rana ta goma sha huɗu, Aina'u ta taso Khalil suka dawo gidan, kai tsaye ɗakin Hajiya ta nufa tana kwala kiran, "Bilkisu! Bilkisu!! Ki fito nan tsohuwar munafuka annaminiya" tana tafiya hannunta riƙe dana Khalil har parlourn Hajiya, da sauri Hajiya ta fito tana ƙarewa Aina'u dake riƙe da hannun Khalil kallo, "Menene haka nake gani Khalilullah!" Hajiya ta nuna hannun Aina'u dake riƙe dana Khalil fuskanta ɗauke da mamaki, " _ƙanwar matarka_ ce fa Ibrahim!" Wani wawan harara Aina'u ta jefi Hajiya dashi tare da yin wani irin dariyar ƴan iska sannan wani janyo Khalil ɗin tare da riƙo kansa ta haɗe bakinsu waje ɗaya. Da sauri Hajiya ta rintse idanunta gabanta na wani irin bugawa tana istigfari cikin zuciya. "Wallahi kika ƙara yin magana akan alaƙata da ɗanki, yanzu gabanki zan sutale masa wando kuma kina kallo zai yi amfani dani, wata ƙila na har rabo ya shiga tsakani!" Wasu irin zafafan hawayene suka shiga kwaranyo daga idanun Hajiya har tsikar jikinta na tashi, "Na taso maki da sha'awar shekaru ko? Kar ki damu idan ƙaiƙayi yake maki, inada mutane dai-dai dake da zasu iya biya maki buƙata." Wani irin kuka Hajiya ta fashe dashi mai ƙarfi kuma har wannan lokacin idanunta a rufe suke, "Ibrahim a gabanka, a gabanka _Ƙanwar matarka_ take faɗa min irin wannan maganar amma ka kasa ko tari mai ƙarfi, a gabanka Mu'azzam!!" Hajiya ta faɗi tana kuka. Khalil kuwa tunda ya sunkuyar da kanshi a ƙasa hawaye masu uban gudu suke sauka a akan tiles, ya kasa ko ɗagowa, jikinsa ne kawai ke karkarwa. "Ba kukanki nazo inji a nan ba, zuwa nayi inyi maki kashedi akan kar ki kuskura ki kuma kiran wasu ƴan iska gidan nan suzo suna yin tsaface-tsaface, kinji ko baki ji ba?" Wani irin haske ne ya gilma a fuskan Aina'u har sai da taji shock, Hajiya ta nuna mata ƙofar fita tare da faɗin, "Wa ya haifi ubanki da har zaki shigo cikin gidan ChiefJustice Nurudden kice zaki bawa matarsa order, fita kamun na saka a ƙarar da zuri'ar ku!" Hajiya ta faɗi a tsawace. Baya Hajiya tayi zata faɗi saboda wani gigitacen mari da Aina'u ta ɗauketa dashi tare da faɗin, "Kul! Kika ƙara ɗaga hannunki a jikina. In kwanta da ɗan naki in bashi natsuwa har sai da ya manta sunanki, shine zaki saka min da mari, ƙarya kike yi wallahi!" Hannu dafe da kunci Hajiya ta kalli Khalil da ya tarota tare da zaunar da ita a kan kujera, "Khalil har lalacewaka ta kai haka? A gaban idanunka _Ƙanwar matarka_ ta ɗaga hannu ta mare Ni." Jikin Khalil wani irin rawa yake yi har naman jikinsa na ɗagawa haƙorinsa na haɗuwa dana juna a lokacin guda gashin dake kwance a jikinsa suna wani irin mimmiƙewa, idanunsa kuwa sun koma wani irin abun tsoro saboda yanda suka kaɗa sukai jazur............ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* _MATAR SAYYADEE_ 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *36* Ganin yanda gaba ɗaya yanayinsa ya canza, sai ta soma ja da baya kaɗan-kaɗan tana kuma murza tafin hannunta a lokaci guda, sai dai gabanta ne ya yanke ya faɗi da ƙarfin tsiya jin bata ji wannan sanyin da ta saba ji ba a duk lokacin da ta murza tafin hannun, da saurin ta fiddo tafin hannun tana kallo gabanta na wani irin zullon tashin hankali, "Na shiga uku tafin hannuna yayi baƙi!" Ta faɗi da ƙarfi ganin har hayaƙi yake yi, a dai-dai wannan lokacin ne kuma Khalil ya wani irin shaƙo wuyanta tare da ɗagata ya buga a ƙasa dai-dai lokacin da Laure ta shigo parlourn da gudu tana faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Hajiya hayaƙi a ɗakinki." Cak ta tsaya tana mai kai hannu kan maƙogwaronta tare da kallon Hajiya da itama take kallonta cikin tsantsan mamaki da kuma farin ciki. Laure nuna bakinta tayi sannan ta nuna Hajiya cikin mamaki, hajiyan sai ta gyaɗa mata kai alamar eh tabbas taji fitar muryanta. Kuka Laure ta fashe dashi tare da kai goshinta ƙasa tayi sujada. Khalil kuwa wani irin kwallon tashin hankali ya riƙa yi da Aina'u tana buguwa da edge ɗin bangon ɗakin yana faɗin, "Mahaifiyata kika ɗaga hannu kika mara? Mahaifiyar tawa!!" Baki, kai da hancin Aina'u sai tsiyayar da jini yake yi tsabar naushi da Khalil ke aza mata, da sauri Hajiya ta nufi Khalil tare da faɗin, "Mu'azzam ka sake kyaketa haka, ka kyaleta nace!" Faɗin Hajiya da ƙarfi, shi kuwa Khalil bai saurareta ba ya cigaba da naushin Aina'u a duk inda ya samu a jikinta, fuska, baki, ciki da ƙirjinta duk sun nausu, sai da Hajiya ta shiga tsakiya tukunna Khalil ya dakata da dukanta, ita kuwa Aina'u sai tsiyayar da jini take yi, tafin hannunta kuwa ta murza yafi sau shurin masaƙi. Ganin Hajiya a tsakiyarsu, da sauri ta rarrafa ta fice daga ɗakin ta nufi ɓangaren Sarah riƙe da cikinta. Tana shiga sama ta haura zuwa ɗakin Khalil ɗin tare da duƙawa ta janyo tukunyar tsafinta, sai dai tana gama fuddoshi ya bada sautin fuuus ya watse a ɗakin, nan da nan ɗakin ya ɗauki wani irin ɗoyi, kuma hayan yayi daidai da wani irin murɗawa da cikin Aina'un yayi, ƙafafuwanta su hau wani irin rawa, idanunta na wani irin far-far-far kamar wacce kwayar idanunta zasu faɗo ƙasa, nan da nan wani irin guguwa ya tashi a tsakiyar ɗakin na kusan tsayin mintuna biyar kamun _Hell Ofulafu_ ya bayyana a tsakiyar ɗakin rabin fuskansa a ƙone, shi kuwa mummunar halittar nan gaba ɗaya jikinsa a ƙone yake. Wata shimfiɗeɗiyar bulalace a hannun Hell Wanda gefe-gefe bulalan wasu irin manya-manyan ƙayoyi ne masu matukar tsini da kaifi, jikin Aina'u wani irin rawa ya ɗauka ganin Hell da wannan bulala. Ɗaga bulalan yayi tare da shimfiɗa mata sai da ya zagaye jikinta har zuwa kan fuskanta, wani irin ihuu ta saki wanda ya ɗauki gidan gaba ɗaya, nan da nan jikinta ya hau tsirtuwar jini har zuwa fuskan, don bulalan yana sauka a kan fatan jikinta ya taho da fatarta, haka ya dunga zubaba mata bulalan tana ihu tana birgima, bayan ya gama farfashe jikinta sannan ya zaro wata doguwar ƙarfe wanda kallo ɗaya zaka yiwa Ƙarfen zaka tabbatar ya ɗauki awanni a cikin wuta saboda irin jan da yayi. Ba tare da tausayi ba ya dunga ɗaura wannan ƙarfen a ko'ina na fatar jikinta, Aina'u tsabar azaba ko kuka ta kasa yi sai wani jan numfashi da ta riƙa yi. Hello bai haƙura ba sai da ya banƙare Aina'u sannan ya fiddo da wani abu kamar kwaɗo mai matukar muni da azababben wari ya tura cikin gabanta sai har sai da tsintsiyar hannunsa ya shige ciki. Aina'u wani mahaukacin gurnani ta saki wanda ya taho da wani mulmulallan jini da bakinta, Hell na ciro hannunsa a gabanta jini ya biyo baya baƙiƙƙirin mai masifaffan wari. Wani irin dariya ya shiga ɓaɓɓakawa kamun ya dafa mummunar halittar nan suka ɓace, Aina'u kuwa sai wani irin birgima da buga kanta a ƙasa take yi saboda mummunar azabar da take yi mai wuyar fasaltuwa, bayan jinin dake biyu jikinta da gabanta, wani manya-manyan tsutsotsi da ƙananan baƙaƙen kunamu suka shiga fitowa ta gabanta kuma masu cizo da tsungulin, Aina'u sai zaro harce take yi tana wani irin surutan gigin azabar da take ji a cikin jikinta. Wani irin ɗaukar zafi jikinta ya soma yi kamar ana dafa mata jikin, da kyar ta iya cire komai na jikinta tana wani irin gurnanin azaba, kuka ta fashe dashi gani yanda tsokar naman jikinta ke yankowa yana faɗowa kuma duk tsokar data faɗo, wasu fararan tsutsotsi ne ke mamaye wajen suna tsungulin jikinta. Hatta naman dake wuyanta zazzagowa yayi ya faɗo kana ganin tafiyar maƙogwaronta, idanunta sunyi wani irin ɓulu-ɓulu sun zama abun tsoro, cikin ƴan wasu mintuna gaba ɗaya kamannin Aina'u ya sauya ta koma wata abun tsoro, fuskansa ya mokaɗe, bakinta ya turo yayi tsini kamar na kare, haƙoranta sun turo sunyi cirko-cirko a baki. Ɓangaren Hajiya kuwa, Khalil na tsaye ya yanke jiki ya faɗi yana wani irin jijjiga kamar mai farfaɗiya, ruɗewa Hajiya tayi tana faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Laure! Laure!! Laure na shiga uku ki taimaka min ya zanyi." Daidai nan aka murɗo ƙofar aka shigo, ya Abdul-Hakeem ne da Aunty Maryam ce wacce tayi wani irin mahaukacin rama kamar wacce ta tashi daga ciwo, "Alhamdulillah, Abdul-Hakeem taimaka min mu kaita asibiti dan Allah!" A raunane Aunty Maryam tace, "Hajiya ba asibiti za'a kai shi ba, daddyn moon ɗauke shi ka mayar dashi kan kujera ka bashi wannan maganin mu gani." Ta ƙarisa maganar tana mai fiddo wani goran magani a cikin jakarta. Cicciɓarsa ya Abdul-Hakeem yayi tare da mayar dashi kan kujera sannan ya karɓi goran hannun Aunty Maryam ya bude tare da buɗe bakin Khalil yayi bismillah ya zuba masa har sau uku. Cikin minti ɗaya ya miƙe da sauri yana faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Ya faɗi hakane tare da ɗaura hannunsa biyu a kai yana girgiza kai. "Hajiya meke damuwa? 'Hajiya mafarki nayi ko? Ba gaskiya bane duk abunda na gani ko? _Ƙanwar matata_ bata zo cikin gidan nan ta raba ni da matata ba ko? Hajiya Sarah tana ɗakinta ko?" Dafa shi Hajiya tayi tare da faɗin, "Kwantar da hankalinka Khalil, dawo cikin na tsuwarka." Da sauri Khalil yace, "Hajiya natsuwata baza ta taɓa dawowa ba har sai kun faɗa min duk abunda nake tunanin ya faru bai faru ba. Hajiya kinsan abunda ke min gizo a idanuna kuwa? Hajiya kin san bala'in da nake gani kuwa!" Da wani irin ihu yake maganar domin kwanciyar da yayi da Aina'u agaban twins da Sarah kawai yake dawo masa cikin idanunsa. "Khalil ba mafarki kake yi ba!" Faɗin ya Abdul-Hakeem. Wani irin duum Khalil ɗin yaji a cikin kansa, "Dagaske ne na koreta, dagaske ne da kaina na kori matata, dagaske na kwanta da _ƙanwar matata_ agaban matata da ƴaƴana. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wai meke faruwa dani ne, ku faɗa min!" Ihun da yayi sai da ya razana kowa a cikin ɗakin. Ya Abdul-Hakeem ya kalli Aunty Maryam tare da faɗin, "Mommyn moon yi masu bayanin da kika min!" Hawaye na kwaranyo a idanun Aunty Maryam ta soma faɗin, "Hajiya tun da uwata ta haife ni, ban taɓa ganin azzaluma kuma mushrika irin Aina'u ba, duk wani bala'in dake faruwa a cikin gidan nan sanadinta ne, Aina'u itace sanadin kurmancewar Laure, rashin lafiyar da kika yi har ya zazzago da idanunki, rashin kiranki da ya LTG da ya barrister, domin ita ta karkatar da hankalinsu da barin nemanki, mutuwar jinjirar Nafeesa da kuma korata da daddyn moon yayi har da dakatar dashi da akai a wajen aiki. Aina'u matsafiyace ta gaske, domin bokanta a tare da ita yake koda yaushe, tana matsa tafin hannunta yake bayyana a ciki, sannan kuma tana kallon komai da kowa dake cikin gidan nan ta cikin tafin hannun, har kisa tana iya aikatawa ta hakan. A ranar da na kamata tana magana da bokan, a ranar ta saka ya Abdul-Hakeem ya sake ni, sannan tayi min kashedi akan idan har na faɗawa wani abunda naga tana yi, sai tayi min irin abunda tayiwa Laure. Tun da na bar gidan nan, kullum a firgice nake kwana har na tsawon shekara ɗaya da rabi duk da cewar wata na biyu a gida baban moon ya turo min da text akan ya mayar dani sai dai kuma inyi haƙuri ba zai iya dawo dani cikin nan gidan ba, a hakan nayi ta hakuri ina kai wa Allah kukana babu dare babu rana, ban taɓa tunkarar kowa da Maganar ba, sai ranar da naje taron wani wa'azi a makarantar da nayi sauka, sai nayi katari malamin yana ta wa'azi akan harkan bin boka har da kuma addu'o'in da mutum zai lazimci yi domin kariya, tun da na fara wannan addu'o'in babu dare babu rana ina roƙon Allah ya karya alkadarin Aina'u da tsinannun matsafanta, cikin ƙanƙanin lokaci tsoran Aina'u ya fita daga cikin zuciyata har na nemi mijina na bashi addu'o'in shima da kuma magungunar da zai riƙa sha da kuma turare gidan, to sai kuma kwanakin baya yazo ya faɗa min kin kawo almajirai sunata sauke alƙur'ani, sosai hakan yayi min daɗi ganin zamu haɗa hannu mu yaƙi azzaluma Aina'u. Khalil kayi haƙuri, Allah zai saka mana kai da matarka, domin ta cutar da kowa na cikin gidan. Kuma Allah ba azzalumin bawansa bane, baya taɓa kama mutum da laifin da ya aikata ba da gangan ba, kayi komai ne bisa tsafi da makirci irin na shaiɗaniya kuma annoba Aina'u." Da wani irin speed Khalil ya bar ɗakin ya nufi nashi side ɗin, Hajiya da ya Abdul-Hakeem har da Aunty Maryam da Laure suka bi bayansa. Khalil bai tsaya murɗa handle ɗin ƙofar ba, kafaɗa ya saka ya bugi ƙofar da wani irin mahaukacin ƙarfi sai ga ƙofar a ɓalle, faɗawa ɗakin yayi idanunsa a rufe tsabar zafin zuciya da fusata, dai-dai nan ya Abdul-Hakeem ya faɗo ɗakin shima, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Faɗin ya Abdul-Hakeem da ƙarfi saboda ganin wani mummunar halitta mai ban tsoro a nannane kuma fatar jiki na zagwanyewa sannan tsutsotsi na fita, ga kuma ƙananan kunamu baƙaƙe masu cizo dake fitowa daga gaban Aina'u, gaba ɗaya tayi watsi da kayan dake jikinta. Rintse idanu yayi tare da faɗin, "Allahumma arji'ini fi musibati wa aklifni khairan minha, wannan wacece haka? Hajiya kar ki shigo don Allah!" Ya fadi don baya son Hajiyar ta razana. Amma tuni Hajiyar ta sako kai ta shigo ɗakin, zuuu ta tafi zata faɗi saboda razanar da tayi ganin Aina'un. "Nice Aina'u, ku taimaka min ku kaini asibiti, wallahi mutuwa zan yi, ku taimaka min!" Faɗin Aina'u, wanda bai san abinda ta aikata ba, dole yaji tausayin halin da take ciki. Maƙogwaro a waje, tsokar fata sai yankowa take tana faduwa tsutsa na cin ramin wajen da tsokar ta faɗo, ga tsutsotsi da baƙaƙen ƙananan kunamun dake fitowa daga gabanta masu azabar harbi da ciwo, idanu sun zazzago, baki ya turo uwa na kare, ga kuma zafi da mummunar wari da jikinta yake yi, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Faɗin Hajiya tare da fashewa da kuka tana faɗin, "Aina'u, kece kika dawo haka? La haula wala quwata illah Billah! Aina'u kin ga ƙarshen aikata sharri ko!" Hajiya na ida zancenta Aina'u ta ɗuka kamar kare ta hau kukan jaki kamar zata fasa ɗakin, can kuma kamar an tambayeta ta soma confessing abubuwan data aikata, "Abia naje nayi mummunar tsafi domin in samu zuciyar Khalil, ban san sau nawa wani inyamuri mai suna Ugo yayi amfani dani ba, nayi kwanaki cikin tukunyar tsafi, sannan na kashe mutane babu adadi, daga cikin akwai jikanki ƴar wajen Nafeesa, ni na sadaukar da jininta wa Hell, sannan nice na kashe Nafeesa da mijinta ta hanyar tura aljani ya tsotse jininta sannan ya bude tukunyar gas wanda hakan yayi sanadin rayuka da dama. Nice na kashe ƴaƴan ƴan uwana duka ta hanyar tura aljani ta suffar maciji ya sare shi, nice na kashe ɗan adaidaita sahu saboda rashin tafiya da sauri da yayi har na rasa damar kashe ƴan biyun Sarah tun suna jarirai, Ni ce na tura Muneeba cikin duniya wanda har yanzu tana ta tafiya bata san inda kanta yake ba, nice nayi wa Khalil mummunar tsafi yayi ta amfani dani ba cikin hayyacinsa ba, sannan nice na tura na saka Hell ya tura aljami mantau cikin kwakwalwar Ya Abdullah da ya barrister domin su manta dake Hajiya har abada, nice nayi asiri Abdul-Hakeem ya saki matarsa domin ta gano sirina, sannan na saka aka dakatar dashi daga wajen aiki, kuma duk na samu ƙarfin tsafin nan ne ta silar kwanciyar aure da nayi da mahaifin da yayi sanadin zuwana duniya domin hakan shine cikar tsafina, na samu nasarar kwanciya dashi ne ta sanadin tsafin da nayi masa sannan na juye masa sak Lami, sai bayan ya gama amfani dani sannan hankalinsa ya dawo jikinsa, baƙin cikin haka ya saka ya yanke jiki ya faɗi, dalilin faɗuwar da yayi shine silar ciwon da yake fama dashi yanzu na shanyewar ɓarin jiki." Tsabar zuciyar Hajiya ta kasa ɗaukar abunda taji daga bakin Aina'u, faɗuwa ƙasa tayi a sume. Khalil kuma yayi kan Aina'u da dukan fitar rai. Sai Abdul-Hakeem ya rasa wa zai riƙe a cikinsu, daka ƙarshe dai ya bawa Hajiya taimakon gaggawa ta hanyar fitar da ita daga ɗakin ya yayyafa mata ruwa, sai da ta farfaɗo tukun ya koma ɗakin ya riƙe Khalil dake neman kashe Aina'u, "Baka da hankali ne Khalil? Mai yasa zaka kashe gawar da ba taka ba? Ai wannan yarinyar bata buƙatar komai na hukunci daga gare mu, hukuncin da Allah ma yayi mata tun a nan duniyar ya isheta wallahi." "Ka barni na kasheta dan girman Allah Ya Abdul-Hakeem!" Fadin Khalil yana kuka sosai. "Wallahi ba zan bari ka rage mata nauyi ba. Ɗan yatsarka ɗaya ma ba zan bari ya kuma taɓata ba." Ya faɗi tare da kama hannunsa ya fito da shi daga ɗakin sannan ya jawo karyayyan ƙofar ya rufe. Ƙasa suka sauka inda Hajiya take tana kuka sosai, idanunta sun kaɗa sunyi jajur tuno autarta Nafeesa. Kallon Khalil Hajiya tayi tare da faɗin, "Kaga sakamakon rashin ji ko Khalil? Da ace baka ɗurawa ƴar mutane ciki ba, yaushe har wannan bala'in zai shigo cikin gidan mu. Ka kwaso mana dangin matsafa, dangin masifa da bala'i cikin gidanmu muna zaune lafiya! Me za ayi da irin wannan tsinannen zuri'a, wallahi haɗa zuri'a da irin yarinyar nan mafisa ce babba rayuwa, ina jin dama ace ban haifeka ba Khalil, da duk haka bai faru damu ba. Sanadinka rayuka da dama sun salwanta, ƴata, autata Nafeesa ta kashe min ita, ta ashe ƴarta wacce idan ina ganinta zanji sanyi, ta kashe mijin, ta kashe kowa! Allah ya isa tsakani na da wannan ƴar iskan yarinyar. Ibrahim, aurenka da Saratu bai amfane mu da komai ba sai bala'i da masifa, kuma ka rubuta ka ajiye, idan har nice nayi naƙuda sannan na tsuguna na haifeka, ba amince maka ka dawo da Saratu cikin gidan nan ba, ƴaƴa kuma a dawo dasu zan riƙe!" _Wacece take ganin Hajiya bata kyauta ba? Ni dai na fahimci ciwon da take ji_ 😬🤐 *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* _MATAR SAYYADEE_ 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *37* Hajiya na gama faɗin haka ta miƙe ta fita fuuu tana sharar hawaye. Khalil kuwa mutuwar tsaye yayi a wajen yana jin wani irin matsanaicin bugun zuciya kamar zata faso ƙirjinsa ta fito, Abdul-Hakeem kallonsa yayi tare da ɗaga hannunsa yana shafa ƙirjinsa alamar he should calm down sannan ya fita ya bi bayan Hajiya. Aunty Maryam ƙarisowa tayi kusa da Khalil tare da faɗin, "Khalil ka kwantar da hankalinka, in Sha Allah Hajiya zata sauko. Maganar laifi kuma, ba laifin Sarah bane, Sarah bata da laifi akan abinda Aina'u ta aikata, ita kanta Sarah ai Aina'un ta cutar da ita, don wannan tsutsotsin da ta riƙa fitarwa warin nan ai babbar cutarwa ce! In Sha Allah hajiya zata sauko, don tabbas babu laifin Sarah a cikin abinda Aina'u ta aikata, kuma wallahi ko da ba Sarah ka aura ba, Aina'u sai ta shigo cikin gidan nan ta wata hanya daban ta cutar damu don hakan rubutacce ne a cikin ƙaddarar mu, kuma muma duk muna da namu laifin na sake da muka yi da Allah muka kama jin daɗin duniya, mun manta da azkar da karatun Alƙur'ani wanda Alai ya gina a cikin gidan nan, mun ɗauka kawai salloli biyar da azumin watan Ramadan ɗin da muka riƙe kawai sune dolen mu. Wannan izinace a gare mu dukanmu. Amma tabbas Sarah bata da laifin komai, kuma ina ji a jikina zata sauko nan kusa, yanzu dai shawarar da zan baka itace, tunda har Hajiya tayi fushi haka har ta furta waɗannan kalamai, ka kyaleta na wasu lokaci, kar ka kuskura ka tunkareta da maganar, ka bari har ta huce tukun." Gyaɗa kai Khalil yayi tare da faɗin, "Shikenan, Nagode Aunty Maryam!" Yana faɗin haka ya fita ya bar ɗakin, side ɗin Hajiya ya koma ya nufi ainahin ɗakinsa dake sashen, buɗe Ƙofar yayi ya shiga ciki, ɗakin nan kamar yanda yake, bayi ya nufa ya dunga cuɗa kansa kamar zai yage fatar dake jikinsa saboda tuna ya haɗa jiki da Aina'u. Ya jima kamun ya fito daga wanka, wajen mirror ya nufa yana ƙarewa kansa kallo ganin yanda ya koma kamar mahaukaci, gashin kansa yayi buzu-buzu babu gyara. Hawaye zafafa yaji suna biyo ƙirjinsa sakamakon tuno duk abubuwan da yayiwa Sarah, "Hajiya ki taimakeni kar ki raba ni da uwar ƴaƴata!" Ya faɗi yana mai zama a kan kujerar dake gaban mirror ɗin tare da ɗaura kai a kan drawer. Ya jima a haka kamun ya tashi ya saka don ko shafa mai bai yi ba. Fitowa yayi daga ɗakin, kiciɓis suka yi da Laure a ƙofar ɗakinsa, kanta a ƙasa don kuka take yi tace, "Ya kalif kaje inji Hajiya!" Ba tare da yace komai ba ya gittata ya wuce. Ɗakin hajiyan ya nufa, sai da ya Kwankwasa sannan ya shiga ciki, zaune ya same tana waya kamar zata taune harshe don masifa, "To shikenan sai kazo goben, don wasu abubuwan ma baza su faɗu ba har sai ka iso, ku taho kai da Ayshan." Faɗin Hajiya. Tun da tace ku taho kai da Ayshan, Khalil ya fahimci da Ya Abdullahi take magana. Ajiye wayar tayi tare da kallonsa tace, "Khalilullah, ka dai ji abunda na faɗa maka ko? Tom! Yanzu abunda nake so da kai, kayi maza ka tashi ka tafi gidansu yarinyar nan ka taho min da jikokina, sannan ka tabbatar kamun ka dawo cikin gidan nan ka tsinke igiyar dake tsakaninka da ita, sannan gobe in Sha Allah idan Marmari daga nesa ya iso yaga wannan la'ananniyar yarinyar data tarwatsamin gida, zaka nemo akori kura a kwasheta a kai ta gidan iyayenta can susan yanda za suyi da ita, mu baza mu yafe mata ba, amma kuma baza muyi mata komai ba domin Allah ya riga ya soma nuna mata iyakarta tun a nan gidan duniya! Sauran kuma sai mun je can. Don haka ka tashi maza ka bar gidan nan kayi abunda na umarce ka da kayi." Ta ƙarisa maganar tana mai nuna masa hanya. Ya kwashi kusan mintuna biyu jikinsa na rawa kamun ya miƙe ya fita daga ɗakin. Kai tsaye parking lot ya nufa ya buɗe mota ya shiga yayi reverse ya bar gidan, a hanya babu abunda yake yi sai goge zufa kuma a lokaci guda gabansa na wani irin bugawa da ƙarfin tsiya, kuma hakan ƙara faruwa ne idan ya ƙara kusa da unguwarsu Sarah. A ƙofar gidan yayi parking sannan ya fito daga cikin motar, glasses ɗinsa ya fiddo ya saka saboda yanda idanunsa suka yi jazur. Kallon layin ya riƙa yi, domin tunda ya saya masu gidan zai iya irga zuwansa unguwar. Gaban gate ɗin gidan ya tsaya tare da kai hannu ya Kwankwasa gidan sau uku, jin alamar ana cire jamlock sai ya ɗan matsa baya kaɗan yana jiran a buɗe Ƙofar. Murmushi ta sakar masa tare da faɗin, "Ah Khalil kai ne a gidan namu yau? Wallahi yanzu muka gama magana da mama (Lami, kasancewar malamar mu ta hana su kiran sunanta kai tsaye. Tace masu hakan rashin tarbiyya ne da nuna rashin ɗa'a ga mahaifiya )" Faɗin Na'ima wacce gaba ɗaya ta rame kamar ba Na'ima ƴar gayu ba. Murmushin kawai ya iya mata, "Shigo mana ka tsaya a tsaye." Ta faɗi tare da matsa masa, shigowa yayi yana mai ƙara gyara zaman glasses ɗin fuskansa, a tsakar gidan ya taras da Lami da sauraran ƴaƴanta, sai dai yaji gidan tsit ba kamar yanda ya saba jin hayaniyar yaransu ba aduk sanda ya leƙo, kasancewar yana zuwa masu da abun motsa baki, suna jin muryansa ko da basu tsakar gidan suke fitowa da gudu suna masa oyoyo. Har ƙasa Khalil ya tsuguna tare da faɗin, "Mama ina wuni, na same ku lafiya?" Sai da Lami ta ƙura masa idanu na kusan tsayin mintuna biyu kamun tace, "Lafiya Khalil? Shin kayi dogon jinya ne? Amma Saratu bata kyauta ba da bata zo ta faɗa ba, ashe shiyasa kenan babu ganta wajen zaman makoki ba!" Faɗin Lami cikin jimami. Gaban Khalil ne ya buga da wani irin ƙarfi jin abunda Lami tace, amma kuma sai yayi saurin kawar da hakan cikin ransa tare da furta, "Mama wanene ya mutu har akai zaman makoki bamu sani ba?" Nuna su Na'ima tayi tare da faɗin, "Gaba ƴaƴansu ne suka mutu sakamakon saran maciji!" Na'ima har idanunta sun cicciko da hawaye sakamakon tado mata da mikin da Lami tayi. Khalil kuma sai yanzu ya tuna abunda Aina'u tace lokacin da take confessing, cewar ta tura maciji ya sari duka ƴaƴan gidan ta bawa bokanta jininsu. "Wannan yarinyar tsinanniya ce ta ƙarshe!" Faɗin Khalil cikin zuciya. Shuru yayi na wasu lokaci kamun yace, "Mama idan babu damuwa ina son magana da dukkan ku dan Allah, amma kamun nan bari na duba Baba tukun." Jinjina kai Lami tayi, yayin da shikuma ya miƙe ya nufi ɗakin baba wanda har yau yana nan kwance kamar gawa. Sallama yayi tare da saka hannu ya cire takalmin ƙafarsa sau ciki sannan ya shiga, baba na nan kwance a kan gadon, Sai dai cikin tsafta yake don ba ƙaramin ƙoƙari su Na'ima suke yi ba wajen kula da tsaftar baban kasancewar anan yake bowali da bahaya! Har gaban gadon Khalil ya jawo kujera tare da zama sannan ya kamo hannun baba dake bacci tare da soma faɗin, "Baba kayi haƙuri duk da nasan cewar kalmar ciwo zata ƙara saka maka cikin zuciya! Tabbas ko da ban san ainahin ciwon da kake ji ba matsayin ka na uba, amma zan iya ɗan kwatanta ko da kaɗan ne. Kayi haƙuri, shine kawai abunda zan iya ce maka. Sannan in Sha Allah baba bazan taɓa bari rayuwar Sarah dana sauran ƴaƴanka ya taɓarɓare ba kamar na Aina'u, nayi maka wannan alƙawarin, zan tsaya tsayin daka a kansu, Ni ba sirikinka bane kawai, Ni ɗane a wajenka kuma yayyinsu Na'ima. Kai kuma Baba in Sha Allah zaka warke kuma ka cigaba da harkokinka kamar da. Kayi haƙuri baba!" Abunda ya matuƙar bawa Khalil mamaki jin Baba ya ɗamki hannunsa ya riƙe gam-gam kuma a lokaci guda hawaye na zirarowa daga kwarmin idanunsa har suna shiga kunnensa. Khalil ɗaura ɗayen hannunsa yayi a kan na Baba tare da riƙe hannun da ƙarfi yana kallon fuskan baban dake a rufe kuma yana zubar da hawaye. "Kayi haƙuri baba, in Sha Allah zaka samu cikakken lafiya." Baba magana yake so yayi, amma babu damar haka, a zuciyarsa kuwa cewa yake, "Dan girman Allah Ibrahim kar ka nema min lafiya, ka barni a haka, ni fatana ɗaya in koma ga Allah cikin gaggawa kuma tare da imani, don baƙin cikin dake cin zuciyata ni kaɗai na san shi. Dan Allah Khalil ka barni a haka." Da kyar Khalil ya iya zame hannun Baba a cikin nashi sannan ya fita daga ɗakin, dama kuma Na'ima na jiransa domin tayi masa jagora zuwa parlourn Lami, yana fitowa tayi gaba, shi kuma ya bita a baya har cikin ɗakin Lamin. Be zauna a kan kujera ba, a ƙasa ya zauna tare da zare glasses ɗin dake maƙale a idanunsa ya ajiye a gefe yana kallon mutanan dake ɗakin cikin dabara, amma har ya gama kallosu bai hango fuskan annurin zuciyar tasa ba a cikinsu. Kai a sunkuye ya kuma gaida Lami a karo na biyu tare da yi mata ta'aziyar jikokinta ƴan gaba da fatiha sannan ya ɗaura da faɗin, "Haƙiƙa na taho maku da labari mai girgizarwa da tashin hankali gami da baƙin ciki!" Yana kaiwa nan ya ɗan dakata na wasu daƙiƙu, yayin da Na'ima ta shiga nanata "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Kasancewar malamar su ta faɗa masu duk ɗayansu da ya faɗa cikin wata masifa to ya karantata. Lami kuwa da ƙarfi ta faɗi, "Yesu Almasihu mai ceto, ka kawo ɗauki da sassauci, ka sanyaya zuciyarmu da ruwa mai tsarki." Khalil kuwa bayan dogon ajiyar zuciya sai ya soma basu labari tiryan-tiryan, bai rage komai a cikin abubuwan da Aina'u ta aikata ba, har kwanciyar aure da yayi da ita sai da ya faɗa masu, kashe-kashen da tayi har zuwa koran da ta saka yayi wa Sarah da kuma halin da Aina'un take ciki yanzu na girban abubuwan data shuka. Kif! Lami ta faɗo daga kan kujera ta sume, yayin da su Na'ima suka fashe da kuka jikinsu na rawa jin abubuwan da Aina'u ta aikata daga ciki har da kwanciyar aure da tayi da mahaifinsu. Hassana ce tayi kan Lami tare da yayyafa mata ruwa ta farfaɗo, wani irin kuka Lami ta fashe dashi tare da faɗin, "Ubanmu wanda ke cikin Sama, na tsarkake sunanka, mulkinka shi zo akan abin da ka ke so ayi shi cikin duniyar nan kammar yada ake yinsa cikin sama. Ka gafarta mana laifinmu, kamar yarda muna gafarta ma waɗanda su ke yi mamu laifi. Kada ka kai mu wurin jaraba, amma ka cece mu daga Shaiɗan. Duka mulki, da iko da girma naka ne, har abada. Kada ka kama ni da laifin haihuwar Aina'u ya Yesu Almasihu! Na san ita mai saɓo ce mummana a gareka, saɓo mafi muni shine kwanciya da mahaifin daya haife ka, ya Yesu amintace, bani da laifi akan abinda ƴata ta aikata, kayi mata hukunci amma ka cire mu Ni da sauran ƴaƴana. Mai girma Yesu Almasihu, na duƙa da duka guiwowina a ƙasa ina neman yafiya da yafiyarka, ka amsa min, Amin." Khalil duƙar da kai kawai yayi yana jiran ace masa ga inda matarsa take. Na'ima da su Hassana kuwa kamar zuciyarsu zai fito saboda irin kukan da suke yi, "Mama dan girman Allah Aina'u ƴarki ce? Anya kuwa ba canje aka yi maki a asibiti ba? Ina ina ganin babanmu bashi ya haifi Aina'u ba, ɗan halak ba zai taɓa yin tarayya da mahaifinsa ba." Faɗin Na'iman. Sai da Lami ta fyace majina sannan tace, "Na rantse da girman Yesu Almasihu mai ceto, Ni da mahaifinku Nuhu muka haifi Aina'u, Aina'u ƴata ce, kuma ƴar Nuhu ce, Ni ina ganin baƙin da Mahaifiyata pasto Emanuella tayi min ne yake bina, don ta taɓa tsine min lokacin da zan auri mahaifinku Nuhu. To ni babban tashin hankalina shine, kai Khalil kace ka kori Sarah, to tun yaushe? Don Sarah dai bata zo gidan nan ba." Da sauri Khalil ya ɗago tare da faɗin, "What! Bata zo nan gidan ba? To ina zata je daya wuce nan ɗin." Duk a gigice yayi maganar kuma ya miƙe tsaye. "Gaskiya Saratu bata zo gidan nan ba!" Lami ta kuma faɗi tare da kallon su Na'iman dake kuka tace, "Ko ku kun ganta?" Girgiza kai suka yi dukansu, Khalil yace, "Wallahi yau kimanin kwanaki goma sha bakwai kenan da barin ta gidana, to idan bata zo nan ba, ina zata kenan? Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Allah ka tsare min matata da ƴaƴana a duk inda suke." Lami hannu ta ɗauka akai tare da soma kwarara ihu har da kwance zani tana faɗuwa a ƙasa tare da faɗin, "ƴata kina ina, ina kika je kika ɓuya? Yesu Almasihu ka nuna min hanya cikin sauƙi!" Khalilullah fita yayi da sauri tare da barin gidan hankalinsa a bugun tashe, buɗe mota yayi tare da shiga ya ɗaura kansa akan steri yana tunanin hanyar da zai fara neman Sarah. Kwankwasa masa glass yaji ana yi, a hankali ya ɗago tare da sauke glass ɗin motar Kasancewarta tinted, "Muneeba!" Ya kira sunanta da mamaki don rabon da ya sakata a idanunsa tun lokacin data kawo masu ziyara lokacin Sarah na fama da cutar tsutsotsin nan, don shi bai ma san tafiyarta ba, kuma tun daga ranar bai Kum samun labarinta ba. Buɗe mata murfin motar yayi tare da faɗin, "Naji daɗin ganinki, shigo ciki Please." Girgiza kai tayi tare da faɗin, "Kayi haƙuri ba zan iya shigowa ba, domin a yanzu haka maganar da nake faɗa maka idan har Babana ya samu labarin to tabbas zan fuskanci mummunar hukunci mai tsanani don ya haramta min nufa inda kuke ko yin magana da ɗayanku. Kaga wancen makarantar, acan nake koyarwa, fitowata kenan na ganka ka fito daga gidan nan shine nace bari na ƙariso mu gaisa." Shuru yayi na wasu ƴan daƙiƙu sannan yace, "Mai ke faruwa ne Muneeba?" Dafa glass ɗin motar tayi tare da faɗin, "Abunda ya wuce ya wuce, amma dai bari na tsungulo maka kaɗan daga halin da na shiga sanadin zuwa gidan ka wancen ranar. Bayan naga halin da ƙawata take ciki, sai na tashi da sauri domin zuwa wajen iyayena su taimaka mata da magungunan karya sammu da kuma addu'o'in da zata riƙe ya zama makaminta don its obvious matarka sammu ne a jikinta. To ina fitowa kawai naji an taɓa ni ta baya, juyowar da zanyi sai muka yi idanu huɗu da ƙanwar matarka, sai ta daki goshina tare da cewa in kalli gabas inyi tafiya kar in kuma dawowa gidan! To tun daga wannan lokacin ban kuma sanin inda kai na yake ba sai tafiya kawai nake ta yi, amma kasancewar iyayena ma'abota ambaton Allah ne haka nima kuma na tashi da wannan ɗabi'a shiyasa Allah ya sauƙaƙa min wahala ban jima ina garari ba aka gano inda nake aka dawo dani gida, sai dai na sha jinya mai tsayi kamun na samu kaina, bayan na dawo cikin hayyacina ne na shaidawa iyayena abunda ya faru, to daga nan ne sukai min iyaka daku, sannan suka ce in dai addu'a ce aduk inda aka yi to da cikin ƙarƙashin ƙasa ne zata karɓu indai anyi ta cikin yaƙini, saboda haka zasu riƙa bin ku da addu'a daga nan inda suke ba sai na kuma takawa inda kuke ba, sannan Babana ya saka min doka mai tsauri akan kar in kuskura ko hanyar gidanku na ƙara bi ta wajen." Shuru Khalil yayi yana mamakin irin mugun hali da rashin imanin Aina'u. "Allah ya saka maki Muneeba, muma Aina'u tayi mana muguwar cutarwa da tafi wanda tayi mai, sai dai kawai Allah yayi mana sakayya!" Rausayar da kai Muneeba tayi tare da faɗin, "Ameen, a gaida Saran, sai anjima." Tana gama faɗin haka ta ɗaga masa hannu sannan ta wuce. Ɗaga glass ɗin sama yayi tare da kunna motar ya bar wajen, a kan hanya sai saƙe-saƙe yake yi ta inda zai fara neman Sarah, ɗilin! Yaji saƙo ya shigo cikin wayarsa, kamar ba zai duba ba, sai kuma ya mika hannu ya ɗauko wayar dake kan seat ɗin gefensa, ganin debit alert daga GTbank sai yayi tsaki ya ajiye wayar, can kuma ya taka wani mahaukacin burki a tsakiyar titi, Allah yaso babu wanda ke binsa a baya, hannunsa na rawa ya ɗauko wayar ya shiga cire key da sauri, 'wrong pin' ya nuna masa kasancewar da sauri yake danna code ɗin. Khalil bai taɓa dana sanin saka pin a rayuwarsa ba sai yau don ƙosawa yayi ya buɗe wayar, ƙara sakawa yayi stil cikin sauri, wannan karan ya bude, shiga message ɗin yayi ya shiga karantawa da sauri, wani irin sanyin Ni'ima ce ta shiga bin saƙo da lungu jikinsa, "Allah Ubangijin mai kowa mai kowai, mai sauƙaƙawa bawa a cikin matsala, Allah Nagode da a wancen lokacin ka bani courage ɗin bata ATMcard ɗina." Faɗin Khalil sakamakon ganin debit alert daga Nasarawa, Lafiya state. "Wamba, unguwar abakwa!" Ya kuma faɗi a bayyane tuno lokacin da yake tambaye Sarah a kan wani yare su har ta faɗa masa sunan garinsu har da unguwar. "Alhamdulillah!" Ya kuma faɗi daidai da lokacin da wayarsa tayi ƙara, ganin Hajiya ke kiran wayar sai da gabansa ya faɗi. Jiki a sanyaye ya ɗaga wayar, "Ka dawo gida tunda ba'a can aka haife ka ba, kuma Marmari ya biyo jirgin sojoji yazo, isowarsa kenan shi da Ayshan. Abu na gaba kuma, kar ka kuskura ka shigo cikin gidan nan idan har ka san akwai igiyar aurenka aka ƴar dangin matsafan nan!" _Wai me Hajiya take nufi damu ne_😞 _Kuyi haƙuri dan Allah da rashin ganin update jiya, wani ɗan matsala aka samu_ *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* _MATAR SAYYADEE_ 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *38* "Hajiya dan........." Ko kamu ya ƙarisa abun da yake shirin faɗa har Hajiya ta yanke wayarta. Hannu ya kai ya daki steari da ƙarfi tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Haba Hajiya!! Habaaa!!!" Ya jima kamun ya kunna motar ya sau hanya, "Wannan shi ake kira ga ƙoshi ga kwanan yunwa!" Ya faɗi bayyane, can kuma ya kuma ɗaukar wayar ya sake dailing number ɗin Sarah, " _The number you're trying to call is currently switched off, please try again later. Thank you_." Tsaki yayi tare da ajiye wayar a gefe ya nufi gida don bai san dame Ya Abdullah yazo ba. Tafiyar da zai yi ta mintuna sha biyar, amma saboda tsoro da tashin hankali cikin mintuna talatin da biyar ya iso layinsu. Tun da ya hango uban sojoji uwa saƙago sun tsatstsaya ya kuma tabbatarwa kansa ya LTG ya iso gidan. Horn yayi, mai gadi ya wangale gate shi kuma ya shiga tare da parking sannan ya fito yana tafiya sumimi-sumumi kamar an tsoma jaba a cikin koko. Tun da ya doshi ɗakin Hajiya yake jin koke-koken mata na fitowa daga ɗakin. Shahada yayi tare da ɗaga labule ya shiga. Turus ya tsaya yana kallon matan dake ɗakin tare da mamakin yaushe suka iso all the way from Maiduguri. Duƙawa yayi har ƙasa tare da soma gaishe su, yayin da kansa a ƙasa ya shiga gaida ya Abdullahi da tun shigowarsa kallo ɗaya kawai yayi masa ya kau da kai. "Wallahi, tallahi Hajiya baza mu taɓa yarda ba, sai an ɗauki mataki akan wannan abu da ƙanwar matar ya Khalil tayi masa, ta cuce mu ta raba mu da ƴar uwarmu, kema kuma tayi ƙoƙarin raba mu dake, baza mu yafe mata ba akan wannan abu da tayi mana. Hajiya ko gawan Nafeesa ban gani ba!" Ta ƙarisa maganar tare da fashewa da kuka mai ciwo. "Har da jaririyar da bata ji ba bata gani ba, yarinyar da bata jima da shaƙar iskar duniyar ba, wannan wani irin rashin imani ne haka!!" Aysha ta sake faɗi tana mai kwanciya akan cinyar Aunty Yagana, ƙanwar Hajiya. Shafa kanta Aunty Yaganar tayi tare da faɗin, "Aysha duk wacce imaninta zai bar jikinta har ta iya kwanciyar aure da mahaifinta, to wallahi babu abunda baza ta iya aikatawa ba, da a zamanin annabawa tazo, to tana ɗaya daga cikin wacce zata iya yunƙurin kashe Annabi! Wallahi Hajiya ina bayanki ɗari bisa ɗari, kar ki sake ki yarda matar Khalil ta dawo cikin gidan nan, mai za ayi da zuri'a irin tasu, zuri'ar matsafa, zuri'a karuwai ƴan dangi Arna!! Ai wallahi don dai kisa haramun ne, da ko ƴaƴan da Khalil suka haifa tare, shaƙe wuyansu kawai za ayi su mutu kowa ya huta. To sun tsotsi nonon tsiya!" Faɗin Aunty Yagana a mugun zuciye, don har ta kusan fin Hajiya ɗaukar zafi. Khalil lokacin guda yaji haushin Aunty Yagana ya rufesa jin abunda tace akan ƴaƴasa, nan da nan ya ɗaure fuska tamau. "Kayi abunda na umarce ka dashi ko kuwa???" Faɗin Hajiya tana watsawa Khalil harara. Ko kamun yayi wani yunƙurin yin magana tuni Aunty Falmata mai bin Aunty Yagana tace, "Ba magana ake yi maka ba don ubanka? Ko sai na taso ba na shaƙi wuyarka!" Ta ƙarisa da ƙarfi har sai da Khalil ya razana, "Hajiya wallahi, tallahi daga gidan nake, su kansu iyayenta basu san bata gidana ba, ashe dana koreta ba gida tayi ba, can dangin babanta ta nufa." Ya ƙarisa maganar a tausaye. "Dubi yanda yake wani rausayar da kai kamar maraya, to ubanka zaka ci, kuma dole ka rabu da yarinyar nan tun da ba tare aka haife ku ba. Yaro duk kabi ka zama wawa a kan mace!" Faɗin Aunty Yagana. "Uhm! Baku ji wata maganar banza da yake yi ba, wai ta tafi dangin mahaifinta. Ina ce nan Marmari yayi bincike lokacin auren naku, kowa cewa yake bai san asalin mahaifinta ba, su dai kawai tarewarsu suka gani a unguwar, kuma babu wanda ya taɓa ganin wani ko wata daga cikin ƴan uwansu yazo gidan, kaii Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'una, wannan fitina haka!" Hajiya ta faɗi har da buga cinya. Tun da suka fara magana ko tari ya Abdullahi bai yi ba yanzu da yayi gyaran murya tare da faɗin, "Hajiya, tun farko irin haka na guda shiyasa naƙi auren don zuciyata bai kwanta da ahalin ba, amma Hajiya kece ki kai ta tausata akan inyi haƙuri ayi auren tunda dai mutane huɗu sun bata shaida a kan ita matar Khalil ɗin, sannan kika ƙara da faɗin, laifin wani bai shafan wani. To Hajiya yanzu hakan ma haƙuri za kiyi tunda dai an riga an haɗa zuri'ar nan kuma laifi bana matar Khalil bane, na ƙanwar matarsa ce, kuma laifin ƙanwar matarsa babu yanda za ayi ya shafi matarsa, tunda ke shaida ce hatta ita kanta matar tasa ba barinta tayi ba. A bar abunda ya wuce ya wuce, sai a tari gaba kawai." Tsabar zuciyar Hajiya na tuƙuƙi, ta buɗe baki za tayi magana ta shaƙe da miyau, take ta hau wani irin mugun tari, idanunta na zubar da hawaye. Da sauri Laure ta nufi kitchen ta ɗauko bottle wata ta buɗe tare da kawowa Hajiyar, da sauri Hajiya ta karɓa ta kafa kai, sai da tasha rabi sannan ta ajiye goran tana mai da numfashin. Babu abunda kake ji a ɗakin sai "Sannu Hajiya!" Sai da ta lafa sosai sannan ta shiga faɗin, "Marmari idan har ka san ba zuwa kayi ka taimaka min muyi wannan yaƙin tare ba, to ka tashi ka koma tun yamma bata yi maka ba, don ka san wallahi, ba zan taɓa yarda Saratu ta kuma zama da Khalil ba in har nice na haifesa, idan kuma zai yi mani musu da gardama, sai in sallawa duniya shi!" "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Hajiya!" Khalil ya faɗi da ƙarfi har da dafe ƙirji yana zaro idanu. "Haba Ya Bilki, ai wannan furucin bai kamata ya fito daga bakinki ba matsayinki na uwa, idan ki kai haka ai sun ci riba. Hakan ma ba zata faru ba, Khalil ai me biyayya ne, ko ba haka ba Ibrahim, mai sunan ɗan gatan Allah!" Faɗin Aunty Yagana har da dariya. Sunkuyar da kai yayi tare da gyaɗa kan alamar eh. Aunty Falmata kuwa cewa tayi, "Yauwa Khalil, ko kai fa! Yanzu abunda za ayi, dubawa za kayi cikin dangi na nan ko na can Maiduguri, a kwai ƴan mata tsala-tsala, na san dai ba zai wuce kyal-kyal banzar matar nan taka bace kake ganin baza ka samu sama da ita ba kasancewar jajur kuma kyakkyawa, to akwai waɗanda suka fita komai a cikin dangin ubaka dana uwarka. Dangin ubanka akwai irin su, Ajaja, Gona, Am'an, yaba, yakaruu duk kyawawane duk da kuwa baƙaƙe ne, idan kuma basu yi maka ba, sai ka tafi dangin uwarka, ka san dai Shuwa ba baya ba wajen kyau, gasu Hindatu, Rakiya, Raliya dasu Aysha da Ameena, kai nayi tuya na mance da albasa, ga wannan ƴa ƴar wajen Mariya, _Habbooba_! Kai ita ma na zaɓa maka, Yarinya kamar India, yanda kasan ita tayi kanta tsabar kyau, ga gashi don san yana ɗaya daga cikin abubuwan dake tsole maku idanu ku maza." Caraf Hajiya tace, "Wallahi ni Habbooban ma tafi kwanciya min a rai, kawai ayi magana da iyayenta, idan sun amince sai ayi magana. So nake ayi komai cikin gaggawa, kuma ni wallahi na haƙura da zamansa a nan Nigeria kuma dama ni na matsa a kan ya dawo nan ɗin, to yanzu na haƙura, ana ɗaura auren sai ya tattara matarsa su koma cen _Las Vegas_ ɗinsa da zama." Da gefen idanu Ya Abdullahi ya kalli Hajiya tare da ɗan yin murmushin gefen baki tare da miƙewa yace, "Muje can side ɗin naka naga yarinyar!" Yana gama faɗin haka ya fice, da sauri gaba ɗaya mutanen ɗakin suka miƙe suka fito don suma duk abunda ake yin basu ga Aina'u ba. Jiki a sanyaye Khalil ya miƙe yabi bayan ya Abdullah zuwa side ɗinsa, shi ya saka key ya buɗe sannan ya shiga, ya Abdullahi yabi bayansa, su Hajiya kuma suka bi bayan ya Abdallah. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Kuna jin warin da nake ji kuwa a cikin ɗakin nan kamar gawa ta ruɓe?" Faɗin Nafeesa tana mai toshi hancinta. Gaba ɗaya sauran ma toshe hancinsu suka yi, "Allah yasa ba wannan shaiɗaniyar bace ta mutu a cikin gidan mu!" Hajiya ta faɗi. Cikin sauri Khalil ya nufi sama yana tsallake step bibbiyu. Ƙafa ya saka ya daki ƙofar ta bulle da ƙarfi, da wani uban sauri ya koma baya yana toshe hanci tare da zaro idanu, "Wa'innahu Sulaimanu!" Faɗin Aunty Yagana da aunty Falmata. "Ibrahim menene wannan ka ajiye a ɗakin ka." Ɗagowa Aina'u tayi cikin wa.i irin mugun azaba tare da faɗin, "Ku taimaka min, ku taimakeni Aina'u ce!" Kuka Hajiya ta fashe dashi tare da faɗin, "Wallahi tallahi jama'a mu kiyaye ALLAH! Mu kiyaye ALLAH jama'a!! Yanzu wannan yarinya Aina'u ce ta koma haka?" Kallonta Nafeesa take tayi cikin tsoro, ganin da tayi mata na ƙarshe shine ranar da tazo washa garin auren su Khalil. Yanzu kam ta lalace, tsirara take a cikin ɗakin, maƙogwaronta a waje, idanunta ya zazzago, ko ina a jikinta babu inda babu rami zuƙuƙu, duk inda tsokar ta yanko ta faɗo, tsutsotsi ke cunkusuwa a wajen suna cin sauran naman dake wajen. Gaba ɗaya Aina'u ta fice daga hayyacinta, gashin kanta duk ta gama fuzgar shi, haƙoranta duk jini ta gama tattaune leɓenta. Sai wani irin miƙewa take yi tana zabura sannan sai ta fasa ihu tare da kai hannu gabanta ta kwakwulo kunamu ta watsar a tsakar ɗakin sannan ta hau burgima tana buga kanta da bango. "Hajiya a fitar da yarinyar daga gidan nan, ta koma can gidan iyayenta dan Allah!" Fadin Nafeesa jikinta na wani irin rawar tashin hankalin ganin halin da Aina'u take ciki. Ya Abdallah kuwa girgiza kai yayi tare da saurin barin waje yana mai faɗin, "Hajiya yanzu yarinyar nan zata bar gidan nan, ku fito mu fita." Gaba ɗaya suka bi bayansa, Khalil kuwa sai da ya kalli Aina'u sannan yace, "Ban taɓa jin ɗigon tausayinki ba Aina'u, domin kuwa kin cutar dani matuƙa, Kuma idan har Hajiya tayi nasarar rabani da matata, hmmm!" Yana gama faɗin haka ya fice daga ɗakin da sauri hawaye na zubar masa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya Abdallah ya kirawo wani mai akori kura ya bashi 50k ya toshe hanci tare da saka glove, bayan lulluɓe jikin Aina'u ya kinkimeta ya saka a bayan akori kuran ya tada mota ya nufi jama'a road can gidansu Lami. Lokacin da aka shigo da Aina'u gidan, ihu Lami ta riƙa yi tana tuma a ƙasa, su Na'ima kuwa tsoron Allah ne ya ƙara huda zukatansu, duk da halin Aina'u sai da ta ɗan basu tausayi. Saboda tsananin warin da take yi, ɗaki ɗaya da akai masu ƙatoto saboda kiwo suka share sannan suka ajiye ta a ciki, babu abunda take yi sai tone-tonen abubuwan da tayi. Lami na jin sunan _Hell Ofulafu_ gabanta ya buga da ƙarfi ta fito daga ɗakin tana faɗin, "Rose Merry! Rose Merry ce kawai zata iya kai Aina'u wajen Hell! Yesu Almasihu ka kawo ƙarshe Rose a wannan rana mai albarka ta Sunday." Faɗin Lami tare da fizgar zanin dake kan igiya ta fita fuuuuuuuu. Saboda tsabar tashin hankali Lami ko abun hawa bai hau bata hau ba, haka tayi ta tafiya a ƙafa har ta isa gidan Rose Merry. Knocking ta hau yi a ƙofar gidan kamar zata ƙarya duk da kuwa akwai kwaɗo dake nuna alamun mutanan gidan basa nan, don anty Rose Merry idan ta tafi church duk Sunday bata dawowa sai bayan la'asar ko kuma gab la'asar. "Madam ai gidan a kulle yake, kalli padlock ɗin mana." Faɗin wata bayarabiyar mata mai ɗauke da ƙaton bawon gorunan magani a kai, sai a sannan ta kalli kwaɗon tare da kai hannu ta taɓa, zamewa tayi ta zauna akan dakalin gidan, don ji take ba zata iya taɓa tafiya ba tare da tayi ido huɗu da Rose Merry ba. Ta kusan awa ɗaya a wajen kamun Aunty Rose Merry ta ƙariso wajen cikin shigar farar atamfa mai ratsin sky blue, sai farar rigar less da kuma sky blue ɗin gwaggwaro. Tana ganin Lami ta washe baki tare da faɗin, "Elizabeth Akanchewa Uchendo, ƙawata, my childhood friend." "Stop that nonesense Rose Merry David Anthony! I came here to ask of what you did to my daughter! You've poisoned my daughter's heart Merry, Yesu Almasihu ya tsine maki, Ƙawancena dake babu alheri a ciki, ke guba ce, ke shaiɗaniya ce, kin kai min ƴata wajen azzalumin nan _Hell Ofulafu_, tun ranar farko da kika fara kai ni Abia na san wannan mugun mutum ne mara imani, duk tsafin da ake yi a gidanmu, baza su iya rashin imanin da Hell yake yi ba, yanzu na ƙara tabbatar da cewa kece kika kashe min ɗana Lukman, kuma ki sani, na rantse da tsafin Babana, You will pay for what you did!" Lami na gama faɗin haka ta juya zata bar wajen, da hannu ɗaya Aunty Rose ta jawo kafaɗanta tana wani irin murmushin mugunta, sai da ta juyo da Lami gaba ɗaya sannan ta kyasta babban yatsarta da kuma manuniya tare da faɗin, "Hey Elizabeth, do you think I came all the way from Nassarawa state to Kaduna, just because of our friendship? You're a fool, a big fool Elizabeth! Nazo Kaduna ne domin mijinki, don mijinki Elizabeth! Tun ranar da na fara ganin Nuhu, naji ina matuƙar ƙaunarsa, amma kuma sai kika min shigar sauri, sannan kuma kin tuna abunda Akanchewa Uchendo ina nufin mahaifinki yayi wa Babana, yayi masa asiri ya raba shi da mamana, ya raba shi da duka arzikinsa sannan ya mayar dashi makaho, Ni kuma gani har yanzu ban taɓa aure ba. Kina tunanin sai ni kuma in zuba maki idanu ki auri ɗan gidan malaman can, sannan kuma in barku kuyi zaman lafiya?" Sai ta girgiza kai tare da ɗaukar ƙafa ɗaya a kan dakali sannan tace, "Bari na faɗa maki abunda baki sani ba Elizabeth, nice sanadin lalacewar duka ƴaƴanki, Ni na kai sunanki wajen Hell, nayi amfani da kwaɗayin duniyarki, na saka Hell ya sakaki kika kai ƴaƴanki ga halaka, sannan ɗan ki tilo namiji na saka masa cutar sata da kuma shaye-shaye, ƴa ɗaya ce ta gagare ni, ita ce Saratu, Ni na saka Hell ya saka maki tsanar mijinki da jin haushinsa da kuma rashin ganin ƙimarsa, sannan Ni nasanwa mijinki karayar arziki bayan na nakasta ƙafarki, ƴarki kuma Aina'u, banyi mata komai ba, jinin mahaifinki ne ke yawo a jikinta, don ita ce tayo gadon ubanki gaba ɗaya har ta damesa ta shanye. Kuma Lami yanzu aka fara wasan a tsakanin mu. Ban san mai Aina'u tayi ba, amma tun da tace min tana so in haɗata da Hell na tabbatar Aina'u ɗiyarki ce, domin bata yada halinki dana mahaifinki ba. Mu zuba ni da ke Elizabeth!" Tana gama faɗin haka tayi wani murmushi tare da kaucewa ta nufi wajen ƙofa ta buɗe tare da shiga ta bugo ƙofa. Lami ta jima a tsaye tana jujjuya maganganun Rose Merry kamun taja jiki a sanyaye ta nufi gida. "Ai da zafi-zafi akan daki ƙarfe Hajiya Mariya, Ni dai idan har ba'a tsayarwa Habbooba miji ba, nayi wa Khalil kamu!" Faɗin Hajiya tana murmushi.............. _Kar ku damu, zamu haɗu gobe in Sha Allah. Na san nayi laifi kam_ 😬 *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* _MATAR SAYYADEE_ 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *39* Cike da farin ciki Hajiya Mariya tace, "Hajiya Bilki wanene zai ƙi son haɗa jini dake? Ai wallahi ko an tsayarwa Habbooba miji, haƙuri za'a bashi, gida bai ƙoshi ba ba'a baiwa na dawa ba, balle kuma Habbooba bata da wani tsayayye miji. Ba'a jima da kammala degree ɗinta ba. Yanzu ne ta ɗan soma kula samarin ma." Wani ajiyar zuciyar farin ciki Hajiya ta sauke tare da faɗin, "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Shikenan tuwona maina, yanzu abunda za'a yi, ki ɗan fara Kwankwasawa Alhj Mutallab da maganar kamun daga nan su Marmari su zo tambayar aure, don so nake kawai da sun zo, har lokacin biki a tsayar. Allah yasa dai kar Habbooba ta bamu matsala!" "Hajiya baki da matsala, Habbooba kuma babu matsala daga wajenta in Sha Allah." Layla dake gefen Hajiya Mariya sai jan gyalen lifayan data naɗe jikinta take yi tana faɗin, "Umm! Umm!!" Ita kuma haj Mariya sai kai mata duka take yi tana bige hannunta, sai da ta gama wayar sannan ta kalleta a fusace tare da soma magana cikin yaren Shuwa, "Mai yasa baki da hankali ne Layla? Kin san da wacce nake magana amma sai takura ni kike yi, baki bari in gama wayar tukun sannan kiyi min duk maganar da zaki yi min!" Turo baki kyakkyawar farar yarinyar tayi tare da faɗin, "Haba Umm, why always Habbooba? Komai Habbooba, duk abunda kika samu, Habbooba, idan kyauta za kiyi, Habbooba is the first person to received before everyone, haba Umm!" Layla ta ƙarisa maganar cikin ɗacin zuciya. "To yanzu kuma me nayi Layla?" Faɗin Hajiya Mariya tana mai zama kusa da Laylan. "Naji lokacin da kuke magana da Aunty Yagana a parlour, shine kika yi sauri kika dawo bedroom ɗinki, and then yanzu kuma kina magana da aunty Bilkin Kaduna, kuma i heard anything you were saying, it all about uniting Habbooba and that son of her's!" Janyota jikinta tayi tare da faɗin, "Haba Layla, ba wai nafi son Habbooba bane a kanki, kin ga you're just 18years, amma ita she's 27years, kin ga dole ita zan so na fara kawaswa a nan gidan tafi gidan nata mijin kamun ke. Be petient, in Sha Allah kema mijinki na nan zuwa soon!" Shuru Layla tayi bata ƙara cewa komai ba. Tayi haj Mariya tayi tare da fita daga bedroom ɗinta ta nufi na Habbooba, tun daga corridor ɗin da zai sadata da ɗakinta take jiyo sautin wakar _Allela Belela_ kamar zai fasa dodon kunnenta, sai data toshe kunnen sannan ta iya ƙarisawa har cikin ɗakin Habbooban sannan ta kai hannu ta zare socket ɗin radion ta jefar. Wata fara tass ɗin budurwa ce kwance a kan gado daga ita sai wani Short kalar baby pink wanda ya tsaya mata iya cinya, sai rigar short ɗin ta kamfanin Armani da ya kawo dai-dai inda short ɗin ya tsaya mata, gashinta baƙi siɗik mai uban tsayi daya barbazu akan gagon, rubutu take yi a kan wani jotter kuma a lokaci guda tana kallon screen ɗin iPhone X ɗinta, jin waƙar da take sauraro ya tsaya cak sai tayi saurin juyowa da sauri, kyakkyawa ce ta bugawa a jarida, gashinta ya watsu baya, wasu kuma suka rufe gefen fuskanta, hannu ta saka ta mayar da gashin baya tare da turo baki ganin mahaifiyarta ce da wannan aikin. "Habbooba." Mahaifiyar ta kira sunanta a hankali tare da zama a bakin gadon, cikin sauri Habbooba ta kawo kanta ta ɗaura a kan cinyar maman tata, "Ya Rasulullahi, Habbooba na hana ki ƙure sauti a ɗakinki, idan za kiji waka, ki riƙa saka sautin daidai kunnanki dan Allah!" "Umm, idan ban saka volume dayawa ba, waƙar bai min daɗi sosai." Faɗin Habbooba. Ajiyar zuciya Umm tayi tare da faɗin, "Habbooba!" Ɗagowa tayi ta kalli Umm ɗin jin yanda ta kira ta with seriousness, "Na'am, Umm!" "Kin san wannan?" Umm ta faɗi tare da nuna mata hoton Khalil lokacin yana _Las Vegas_, tsaye jikin wani ƙarfe hannunsa biyu sanye cikin aljihun wandonsa yana sanye cikin wata navy blue ɗin bodyhug irin highneck ɗin nan, murmushin kwance a fuskansa wanda ya bayyanar da 2dimples ɗinsa, ba ƙaramin kyau yayi ba. Ƙarɓan wayar tayi a hannun Umm tare da zoomin picture ɗin sosai tana faɗin, "Wow! He look familiar, amma na rasa inda na taɓa ganinsa. Yana da kyau sosai Umm." Wani murmushin jin daɗi Umm tayi tare da karɓan wayar sannan tace, "Future husband ɗinki ne!" Waro idanu Habbooba tayi tare da tashi zaune tace, "Umm, are you for real? Like da gaske kike Umm?" Dariya Umm tayi tare da faɗin, "Ni na taɓa yi maki ƙarya ne? Mahaifiyarsa ce ta buƙaci ya ƙara aure saboda bata son first wife ɗinsa da yake zaune da ita, shine ta zaɓe ki a matsayin matar da zai aura, kuma kin san ko shi ɗin ɗan wanene?" Girgiza kai Habbooba tayi gabanta na faɗuwa jin yana da mata, don it's obvious Shuwa basu ƙaunar kishiya! "Ɗan _late CJN Nurudden Muhammad_ ne, kuma kin san dai CJN Nurudden Muhammad mijin cousin ɗita ce, don da mahaifin haj Bilki, da Mahaifiyata, ubansu ɗaya, uwa ce kowa da tasa." Jinjina kai Habbooba tayi tare da faɗin, "Na tuna, na tuna inda na taɓa ganinsa, lokacin da muka je ta'aziyar mahaifinsa ne na taɓa ganinsa, he's a medical doctor ko?" Jinjina kai Umm tayi tare da faɗin, "Tabbas shine, kin gane sa." A sanyaye Habbooba tace, "Umm I love him, but yana da mata kika ce." Ta ƙarisa maganar cike da rauni. Kamo hannunta Umm tayi tare da faɗin, "Come on, sai kace ba Shuwa ba, Kar ki bani kunya mana, Shuwa ba'a san mu da tsoran kishiya ba, kishiya ko wacece ita bata bamu tsoro. Ni dama kuma amincewarki nake so, kuma baki san wani abu ba, ita matar tasa ma, sakinta za ayi don ita mahaifiyar tasa cewa tayi dole ya saki first wife ɗinsa, kuma da zarar anyi auren, _Las Vegas_ zaku wuce acan za kuyi zaman ku." Wani irin runguma Habbooba tayi wa Umm tare da faɗin, "Na amince Umm, zan aure shi kuma ni dama tun ganin da nayi masa na farko naji ina matuƙar sonsa." Shafa kanta Umm tayi tare da miƙewa fuskanta cike da murmushi ta bar ɗakin. Bayan kwana biyu! "Khalil ka san mai yasa nayi kiranka a gaban ƴan uwanka gasu gaba ɗaya?" Faɗin Hajiya tana yin nuna gasu, ya Abdullah, ya Abdul-Hakeem, ya Barrister, da kuma Aysha. Girgiza kai Khalil yayi, don shi da badan ritsa shi da aka yi ba, da yanzu haka yana hanyar Nassarawa wajen matarsa, "Yauwa, to na kiraka ne in kuma jaddada maka maganata akan sakin matarka, Ibrahim wallahi dole ne ka saki yarinyar nan, ƴaƴa kuma ni da kai na zan aika har Nassarawar a ɗauko min su, kar ka damu ba zan barka babu mace ba tunda ka riga ka saba da mata, na zaɓo maka cikin dangi, ba kuma ƴar kowa bace sai ƴar ƙanwata Habbooba, yarinya fara tas kyakkyawa da ita. Don haka idan ba so kake na ɗaga maka nono ba, dole ne ka saki yarinyar nan, ehe. Aure kowa ya san ba dole bane, shikuwa saki surah sukutum aka saukar a kansa, Allah da kansa shi ya halatta sakin aure! Kuma na riga nayi rantsuwa sai ka saki Saratu!" Kan Khalil a ƙasa babu abunda yake zubarwa face hawaye. Ya Abdullah gyaran murya yayi tare da faɗin, "Hajiya, Ta yiwu ɗaya daga cikin dalilan da ya sa ake kiran wannan sura da sunan surar saki (Ɗalak) shi ne irin hukunce hukuncen sakin da suke ƙunshe a cikinta makil, wanda wannan yana nuna mana irin la'akarin da shari'ar musulunci ta yi dangane da al'amarin saki, saboda irin hatsarin da yake da shi, domin abu ne wanda in har ba'a yi da gaske ba, kuma ba'a yi shi yanda musuluci ya zo da shi ba, sai ka samu ya taimaka wajen wargaza al'umma da tarbiyyar iyali, kana da haifar da gaba da kiyayya a tsakanin dangi. Kamar yanda rashin kiyaye hukuncin sakin ke iya haifar da aure kan aure, wanda daga karshe a dinga haife 'ya'ya marasa tabbas ɗin iyaye. Kamar yanda kuma, shi saki ba wani abu ne wanda shari'a ke ƙarfafa gudanar da shi ba, bil hasali ma shi ne halas wanda Allah ya fi ƙi, kamar yanda ya zo a mashahuriyar ruwaya daga Ma'asumai (A.S.) "Babu wani abu da Allah ya halatta kuma yake fushi da shi fiye da saki. Wannan ruwayar ta zo cikin Wasa'ilus shi'ah juzu'i na 15 shafi na 266. Sai dai kuma wani abin tambaya a nan shi ne, mene ne ya sa shari'a ta halatta yin saki ? Amsa a nan ita ce a irin hali na zaman yau da gobe na ma'aurata a wasu lokuta za ka samu cewa akwai wasu halaye waɗanda suke faruwa marasa daɗi wanda in da za'a tilasta ci gaba da zama da juna a tare da waɗannan halayen, sai mu samu rayuwa za ta yi ma wanda yake cutuwa, tsanani da kunci wanda zai iya kaiwa ga halaka da abin da ya yi kama da haka. To saboda Allah ne mahaliccin kowa da komai, kuma asanin abin da zai kai ya kawo, don haka ya kawo magani da mafita a duk lokacin da irin waɗannan matsaloli suka bijiro a tsakanin ma'aurata, wanda wannan magani shi ne saki, duk da cewa ba'a son al'amarin ya kai ga haka, sai ya zama dole. Musulunci addini ne da ya ƙunshi komai da komai don inganta rayuwar ɗan Adam a duniya da Lahira. Bai bar ɗan Adam ya yi amfani da hankali da tunaninsa kawai don tsara wa kansa makoma ba, saboda shi ɗan Adam mai rauni ne, mai son zuciya ne, mai haɗakma ne, mai rowa ne, kai ƙarewa ma mai butulci ne ga wanda Ya halicce shi. To in har zai yi butulci ga Mahaliccinsa, ta yaya zai tsara rayuwar da sauran abokan zamansa za su ji daɗi? Aure daya ne daga cikin ginshiƙan rayuwar al’umma, wannan ya sa Musulunci bai bar shi sasakai ba ƙa’idoji da dokoki ba. Kuma baya ga ƙa’idojin zamantakewa a tsakanin ma’auratan, duk da ba a fata, amma ya tsara yadda za a rabu idan aka kasa samun jituwa ko maslaha a tsakanin miji da matar. Saki a matsayin zaɓi na ƙarshe: Ko da yake an halasta saki a Musulunci alama ce ta sassauci da aiki da tsarin shari'ar Musulunci, kiyaye haɗin kai na iyali yana ɗaukar fifiko don kare yara. Saboda wannan dalili, saki a koda yaushe zabin karshe ne, bayan gajiyar dukkan hanyoyin sulhu. Misali, Allah yana magana da maza yana tambayar su da su yi ƙoƙari don kiyaye auren, koda sun ƙi matansu: Ku zauna da su bisa tushen kyautatawa da adalci. To, idan kun ƙi su, akwai tsammãnin ku, ku ƙi wani abu, kuma Allah ya sanya albarka a cikinta. Surah 4 Aya 19 Haka nan ayar nan tana magana ne ga mata suna tambayarsu irin wannan: Idan mace ta ji tsoron zalunta ko tawaya daga bangaren mijinta, Bãbu laifi a kansu idan suka yi sulhu a tsakãninsu, Surah 4 Aya 128, wannan ayar tana magana ne ga dangi ko kuma al'umma don wannan manufa ta kubutar da wannan alaka, wanda Allah bai sauwake wa karya ba: Idan kun ji tsõron sãɓa a tsakãninsu, (biyu) masu sasantawa, daya daga danginsa, da sauran daga nata; idan suna fatan zaman lafiya, Allah zai daidaita su: Kuma Allah Masani ne, kuma Masani ne ga dukkan komai. Surah 4 Aya 35, Amma, idan bayan gajiyar dukkan hanyoyin sulhu, Ƙiyayyar da ke tsakanin miji da mata har yanzu ta fi haƙuri, sannan saki ya zama babu makawa. Ga kuma hazakar shari’ar Musulunci, wanda ke da amfani, maimakon hanyoyin da ba su dace ba, zuwa ga haƙiƙanin yanayi. Maƙasudin aure, da kuma duk wani ɓangare na rayuwar dan Adam, su ne don cimma farin ciki da nagarta. Don haka, lokacin da aka hana mutane hakkinsu na kashe auren da ba a yi daɗi ba, waɗannan biyun an keta su sosai. Wannan shine, kamar yadda ma'aurata za su rayu cikin wahala, wanda zai iya kai su ga rashin imani a aure. Don haka saki a cikin wannan yanayin - idan an auna har zuwa bala'in rarrabuwar iyali – zai zama ƙasa da bala'i. Maza suna da hakkin saki. Idan mutum baya son kiyaye aurensa saboda wani dalili, sai ya saki matarsa ​​kuma ya biya mata kudi ta hanyar biyan ta abin da ake ce wa mut’a. Wannan kari ne akan abin da ake yi mata na kudi akai-akai, idan har tana da hakkin 'ya'yansu. Saki ya fara aiki da zarar miji ya furta ko ya rubuta duk wata ka'idojin saki na shari'a kamar: ‘Na sake ki’ ko ‘kin sakeki’...da sauransu. Miji na iya yin wadannan ko dai da kansa ko kuma ta hanyar manzo (Ɗan aike).Idan har sha'awar mace ce ta yanke auren, lamarin ya zama daban. Dalilinta na iya zama cewa ta sami rashin lafiya, miji baya iya ciyar da ita kudi ko kuma ba ya da karfin jima'i. Za ta iya tabbatar da wadannan aibu a gaban alkali, sai alkali ya ba ta saki tare da samun cikakkiyar damar samun dukkan hakkokinta na kudi. Hakanan, idan mijin ya kyautata mata amma ba ta son ci gaba saboda wani dalili na zuci, sai ta tambaya me ake ce masa khul’. Wannan yana nufin a ba da saki amma ba tare da samun dama ga haƙƙin kuɗi ba, da kuma biyawa mijin sadakin da ya riga ya biya akan aurenta. Hajiya, duk na kori maki wannan jawaban ne saboda kisan cewa shi fa kalmar saki ba abun da za ayi wasa dashi bane, A wasu lokuta, furta kalmar saki ya zama mara amfani. Daga cikin wadannan har da lokacin da miji yake:1.) Buguwa. 2.) Wani ya tilasta musu furta su. 3.) Cikin tsananin bacin rai har bai san abinda yake fada ba. 4.) A cikin yanayi mara kyau na hankali, kamar hauka na wucin gadi, farfadiya ko a cikin suma. A irin wadannan lokuta, saki banza ne. Kin ga kuma Khalil na ƙaunar matarsa, kece kawai kike son tilasta masa ya sake ta. Hajiya bari nayi maki wani tambaya dan Allah, shin a zaman da kika yi da matar Khalil na kimanin shekaru biyu da ɗoriya, shin kin taɓa ganin wani mummunar hali da take dashi? Shin ta taɓa zaginki? Ta taɓa dukanki? Ta taɓa hana ɗanki zuwa gareki ko kuma yi maki wani alkhairin? Bin bata girmamaki da yi maki biyayya?" Shuru Hajiya tayi, can kuma ta girgiza kai tare da faɗin, "Ko ɗaya, Saratu bata taɓa yi min ɗaya daga cikin abubuwan daka lissafo ba." "To kin gani Hajiya! Hakan na nufin baiwar Allahn nan bata yi maki komai ba, kawai laifin ƴar uwarta ne yake son shafarta. Hajiya dan girman ubangijin halitta, ki sassautawa zuciyarki ki bar maganar Khalil ya saki matarsa, wallahi Allah zai yi fushi dake idan har kika tilasta masa rabuwa da matarsa, don wallahi zaki iya haddasa ɓanna a bayan ƙasa, zata iya yuwuwa, ki tsinke igiyar dake tsakaninsu, amma kuma suje suna bibiyar juna a waje bayan babu aure tsakanin su, kuma kin ga idan har haka ta faru, wallahi kina da babban kamasho! Hajiya ina roƙon wannan Alfarmar, ki sassautawa Ibrahim kar ki raba shi da matarsa dan Allah!" Ya Abdallah ya ƙarisa maganar a tausashe. "Uhm! Naji bayanka Marmari, kuma na gamsu, sai dai nima ina da nawa sharuɗɗan." Gyara zama Ya Abdullahi yayi, Khalil wani sanyin rahama ne ya shiga ziyartar lungu da saƙon jikinsa jin Hajiya ta janye ƙudurin saki, he is willing to accept all her sharuɗɗa in har zata amince ya cigaba da zama da his light. "Na farko dai dole ne ya auri Habbooba, na biyu, kar ya kuskura ya wulaƙanta min ƴa saboda matarsa kuma kar ya bawa matarsa fuskan da zata wulaƙantamin ƴa saboda tana taƙamar ita ce matar so, na uku, yayi takakkiya har Maiduguri yaje ya nemo soyayyar Habbooba, don ita ba _matar shige_ bace, idan har ya cika duk wannan, na amince ya cigaba da zama da matarsa, zan yi azumi uku na rantsuwar da nayi." Faɗin Hajiya, "To kai kaji Khalil, shin ka amince na abunda Hajiya tace." Gabansa na bugun tara-tara ya ɗago ya kalli ya Abdallah, sannan ya kalli Hajiya tare da sunkuyar da kai ya furta, "Na amince da duk abunda kika ce Hajiya. Zan je Nassarawa na dawo da Sarah, bayan na dawo sai in tafi Maidugurin!" ( _Ni kuwa nace Uhmmm! To me zance ni Matar Sayyadeen banda uhm ɗin? Dan-dan-dan-dan-dan-dan! Akafta_ 🙆) *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* _MATAR SAYYADEE_ 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜 *40* Taɓe baki Hajiya tayi, don gaba ɗaya Sarah ta gama ficewa daga zuciyarta. "Allah ya kiyaye hanya! Yaushe zaka wuce?" Ɗan shuru yayi, sai kuma can yace, "Hajiya, idan so samu ne in tafi tun yau!" Ya ƙarisa maganar a raunane. Wannan karon ma taɓe bakin tayi tare da faɗin, "Allah ya jiyaye hanya, ka dai tabbatar kana tafiya kana sauraran karatun Alkur'ani, sannan kana isa ka kuma tabbatarwa da Li'ilafi a bakinka, atoh! Na dai faɗa maka." Murmushi ya Abdallah da ya Abdul-Hakeem suka yi a lokaci guda, yayin da Khalil yace, "In Sha Allah Hajiya." Yana gama faɗin haka ya miƙe jikinsa har rawa yake yi ya fice, ya ƙosa yaje yaga halin da matarsa take ciki. "Uhm, dubi yanda jikinsa ke rawa akan mace kamar wawa, Allah dai ya kyauta!" Faɗin Hajiya tana wani rausayar da kai. Wannan karon ya Barrister ne yayi dariyar yana mai sunkuyar da kai don yanda Hajiyar ta rausayar da kai ba ƙaramin dariya ta bashi ba. Khalil kuwa wuta-wuta ya tafi ya ɗauko ɗayan ATMcard ɗinsa da kuma 200k da yake dashi cash a ƙasa sannan ya canza kaya sharp-sharp ya fito ya ɗago ɗakin Hajiya, kallo ɗaya Hajiya tayi masa tace, "Uhm" tare da kawar da kai. Har gabanta ya isa tare da faɗin, "Hajiya kiyi addu'a zan tafi." "Allah ya tsare ya kiyaye hanya." Shine abunda tace kanta a juye. Miƙewa yayi tare da kallon yayyin nasa tare da faɗin, "Zan wuce, a saka ni cikin addu'a yaya." Gaba ɗaya suka haɗa baki wajen faɗin, "Allah ya kiyaye hanya Ibrahim." Ya Abdallah ya ƙara da faɗin, "A gaida iyayen matar naka, kar kuma ka manta ka tafi hannu rabbana, kayi masu tsaraba a hanya." Da "In Sha Allah." Khalil ya amsa. "Allah ya kiyaye hanya yaya Khalif, a gaida Aunty Sarah da ƴan biyu, a faɗa masu nayi kewarsu." Faɗin Laure. "Ameen Laure, in Sha Allah zasu ji." "Ƙarshen kewa, je kwaso kayanki ki bishi ku tafi." Faɗin Hajiya tana mai zabgawa Laure harara. Shi kansa Khalil ɗin sai da ya murmusa kamun ya fice daga ɗakin. Kai tsaye wajen mota ya nufa tare da shiga ya tada ya bar gidan ya ɗau hanya. A can Nassarawa kuwa, Nnanne ce a ɗaki daga ita sai Sarah wacce ke zaune a wajen ƙafafunta. "Takwarata, zan baki labarin wanene mahaifinki da kuma mahaifiyarki. Kin ganni nan, bani ce na haifi ubanki ba, amma yanda nake sonsa da ƙaunarsa, ko mahaifiyarsa sai da ta nuna min ta jikinta ya hudo yazo duniya. Ni da mahaifiyar Nuhu, uwarmu ɗaya, uban kowa da dashi. Don bayan mutuwar mahaifin ya Rahmatu, shine Mahaifiyarmu ta auri babana. Ita tasha mama ta sakarmun, gaba da bayan mahaifiyarmu, Nindire ne, kuma anan cikin wamba aka haifi mamanmu, gadon gidanmu shine ilimi, don sunan gidanmu, gidan malamai. Ubansu Nuhu, da Mahaifiyarmu ni da mahaifiyar Nuhu, uwa ɗaya uba ɗaya suka haifesu, kin ga kenan auren zumunci akai wa mahaifiyar Nuhu da mahaifinsa. Mahaifiyarsu Nuhu, kakarki kenan, macece mai haƙurin gaske, da wuya mutun yaga ɓacin ranta, ko shi mahaifinsu Nuhun, yace har ta koma ga Allah bai taɓa ganin ɓacin ranta ba, ga biyayyar aure! Bayan rasuwarsa ne mahaifinmu ya bashi ni, don ya Rahmatu tana haihuwarsu Nuhu da Nura jini ya ɓalle ta amsa kiran Ubangiji. Bata taɓa haihuwar ɗa ɗaya ba, baban ku Lukman da Kamal sune ƴaƴanta na fari, bayan ta yaye su ne ta haifi su mahaifinki, ina tunanin ita kika gado. A wannan lokacin ni kuma mijina zaman mu ya ƙare, haihuwar mu ɗaya dashi, Ruƙayyatu, gaba ɗaya dai zaman namu dashi na shekara ɗaya ne auren ya mutu, kuma ban kuma wani auren ba, ashe rabon Alyasa'a ne. Bayan arba'in ɗin yayata Rahmatu, aka ɗaura aure na da Alyasa'a, ni na cigaba da shayar dasu ƴan biyu tare da rainon su Lukman da Kamal. Yarane masu matuƙar tarbiyya, tun sun Lukman nada shekaru goma sha ɗaya suka haddace Alkur'ani, don yaro ma ba'a saka shi boko sai ya haɗa izu goma. Na haifi ƴaƴa hudu a nan gidan, Raliya, Zainabu, Khadijah da Usman. Duk a cikin ƴaƴana nafi ƙaunar Nuhu, don yarone mai sanyin hali da biyayya, duk da sauran ma suna da biyayya, amma Nuhu daban ne, abunda yasa ake saurin bambamce su kenan da tagwaininsa, don Nura sak nine, yana da zafin rai da kuma riƙo. Lokacin da suka kammala secondary School, basu cigaba da makarantar gaba ba, sai kowanne ya cigaba da sana'ar da yake yi, Lukman harkar noma yake yi, Kamal kuma sana'ar fata, Nura kuma harkan kayan mata yake yi, wanda kuke kira konsimetis (Cosmetics), shi kuma Nuhu sai ya zaɓi harkar tafiye-tafiye a mota yana tuƙa irin manyan motocin nan. Duk abunda nace wa Nuhu ina so, sai dai idan bai da shi, sannan idan nace masa bani son abu kaza, har abada ya bar abun nan duk son da yake masa. A can ƙasan layin nan, idan kika yi kwana daga hannu dama, layine na wasu mutane wanda basa addinin musulunci, ɓangare ɗaya, addinin kakanni suke yi, bautar gumaka (Traditional religion), ɗayan ɓangaren kuma, kiristoci ne, (Christianity religion), sam waɗannan addinai biyu, basa shiri da juna, kuma basa ga maciji. Pasto Emmanuelle, wasu kuma suna kiranta Debora, itace mahaifiyar mahaifiyarki, ita ta kasance cikakkiyar kirista ta Catholic, irin masu zafin nan ne su, kamun zamanta pasto, ko kuma ince maki kamun ta girma izuwa pasto, sun ƙulla soyayya da mahaifin Debora (Mahaifiyarki), kuma shi mahaifin Debora yana bin addinin kakanni ne wanda kiristoci basu yarda dashi ba, kuma suna ganin addinin da suke yi bana gaskiya bane, sannan dangin Samuel (Akanchewa Uchendo), sun ƙasance ƙasurgumamun matsafa ne na bugawa a jarida. An kai ruwa rana sosai kamun dangin biyun nan suka amince da aurensu wanda sai da Samuel yayi mata ƙaryar ya koma addininta na kiristanci sannan akai auren wanda kuma a zahirin gaskiya bai koma addininta ba, yana nan yana tsafinsa. Bayan haifuwar Elizabeth, mahaifiyarki Kenan, sai a lokacin Debora ta gano cewar Samuel bai bar addininsa ba, yana nan kuma yana tsafinsa, dalilin haka ta kaisa kotu suka rabu tare da goyon bayan iyayenta sannan kuma ta kwace Elizabeth ta mayar da ita hannunta. Su kuma iyayen Samuel sun ji haushin haka sosai, sai suka yi wani mummunar tsafin da yayi sanadin rayuwar iyayen Debora ta hanyar dogon jinya da kuma aman jini. Bayan mutuwarsu, hakan ya ƙara tsananta wutar gaban dake tsakanin two families ɗin sosai har ta kai ga sai da hukuma ta shiga tsakanin su. Samuel baya zuwa ganin Elizabeth, haka itama Elizabeth bata zuwa ganin Samuel kamar ba mahaifinta ba, don mahaifiyarta ta nuna mata cewar ai dangin Samuel gaba ɗaya ƴan wuta ne. Duk lokacin da Nuhu yazo Nassarawa, yana yawan zuwa can unguwarsu Elizabeth kasancewar yana da abokin da suke aikin mota tare, duk da Chidebere ba musulmi bane, amma yarone yaron kirki don na jima ina masa fatan hasken musulunci. To a wannan unguwar Nuhu yaga ƙawar Elizabeth (Lami) kuma yaji yana sonta. A yanda labari yazo min, ita Elizabeth ɗin ya samu da zancen kasancewarta babbar ƙawarta domin ta shawo masa kan ita Merry ɗin. Amma bayan wasu kwanaki Kwatsam, sai Nuhu yazo ya same ni da zancen yana son wata yarinyar ƴar unguwar wai ita Elizabeth, koda yazo min da wannan zancen, koren kare nayi masa tare da faɗa masa in har nice mahaifiyarsa, to ban yarda ya ƙara kallon unguwar ba balle ma ya ƙara zuwa wajen yarinyar. Tun daga wannan rana kuwa, ban kuma jin makamancin labarin ba, sai na ɗauka ya watsar da zancen. Amme me, bayan wasu watanni, sai ga motocin ƴan sanda har biyu a ƙofar gidan nan, lokacin mahaifinsu Nuhu na fama da cutar ciwon ciki na ajali, sai ga sallama wai ana neman mu a police station, duk da Alyasa'a bai jin daɗi haka ya kwashi jiki shi dasu Lukman da shi kansa Nuhun suka tafi caji ofis, acan caji ofis sai da akai masu tijara sannan aka rubuta yarjejeniya akan babu Nuhu babu kula Elizabeth, Wai a cewarsu zai ɓata mata tarbiya kuma ya hure mata kunne. Sosai wulaƙancin da akai masu a caji ofis ya tsayawa Alyasa'a a zuciya har yayiwa Nuhu furucin idan har ya sake ya ƙara kula masu ƴa to bai yafe masa ba. Ni kai na kamar zan ari baki wajen faɗa. Ashe a can gidansu Elizabeth kuma, tana can tana ta ihu da kuma akan ita tana son Nuhu a haka, kuma idan aka rabata dashi zata kashe kanta. Ance har coci-coci aka kaita ana mata addu'a akan ta dawo cikin hayyacinta, amma tana nan kan bakanta. Wata rana da daddare ta haɗa kayanta ta gudu gidan babanta, a wannan ranar sai da Samuel yayi shagali ana ta yanke-yanken dabbobi, saboda ya ƙuntatawa Pasto Emanuella Debora rai, sai yayi alƙawarin sai ya cika mata burinta na auren Nuhu. Ranar da farin ciki Elizabeth ta kwana. A can gidan pasto Deborah kuwa, ba ƙaramin tashin hankali ta samu ba, don ta san idan har haka ta kasance, sosai zata samu koma baya daga mabiyanta. Don da yawan mutane zasu daina zuwa cocinta balle su saurareta. Har gida taje ta samu Samuel akan ya bata ƴarta, amma ya nuna mata sam bai san wannan maganar ba, ƴarshi ita ta zaɓi dawowa ƙarƙashinsa, amma kuma ga Elizabeth nan, idan ta yarda zata bita, to ta kama hannunta su wuce. Amma ƙememe Elizabeth ta nuna baza tabi Pasto Debora ba. Debora a zuciye ta fice daga gidan, in taƙaice maki dai magana har kotu, kuma Samuel ne da nasara, don Elizabeth ta nunawa alƙali cewar bada ƙarfi mahaifinta ya mayar da ita gidansa ba, itace taji tana son komawa da zama wajen mahaifinta. Ana fitowa daga kotu pasto Emanuella ta kira taron ƴan jarida ta shaidawa duniya ta tsinewa Elizabeth, yanzu ba ƴarta bace ba har sai lokacin da ta dawo wajenta gaba ɗaya ta kuma bata haƙuri tare da fita harkan Musulmin saurayin da take so gaba ɗaya. Duk wannan bala'in da ake yi, ashe kullum idan har Nuhu na gari yana gidan matsafan nan wajen ɗiyar Debora, a can yake cin abinci. Lokacin da mahaifinsa ya samu wannan labarin a cikin gari, kusan faɗuwa ya kusa yi kuma dama gashi ba isasshen lafiya ba, nan muka tara Nuhu muna masa faɗa sosai. Wani ihu daya kwatsatsamin bani ba, hatta mahaifinsa sai da ya firgita, Nuhu babu kunya ya shiga cemin, 'Ke ba Mahaifiyata bace, baki isa ki yankewa gobena hukunci ba, don haka babu wani banzan da ya isa ya hanani auren Elizabeth Lami'. Dafe ƙirji Alyasa'a yayi tare da faɗin, har dani kake faɗawa haka Nuhu?' Nuhu sai ya riƙe ƙugu ya ɗage kai yana hura hanci. Zamewa ƙasa Alyasa'a yayi tare da kallona na buɗe baki zanji magana kenan yace, 'Bar shi Saratu, bar shi! Yaje duniya zata koya masa hankali. Ban amincewa ɗan da na haifa ya ƙara yi masa magana ba, sannan ban yarda ya ƙara zama min a cikin gida ba, sannan duk wani abu da yasan nawane, ya ajiye ya tafi!" Yana gama faɗin haka ya juya ya shige ɗaki. Ina kallon lokacin da yake share hawaye. Shi kuwa Nuhu kaɗa kai yayi ya fice yan faɗin 'To se me don an kore ni, duniya ai faɗi ce da ita.' wannan rana ita ce ranar da na saka Nuhu a idanuna na ƙarshe. Daga ƙarshe muka samu labarin wai ya musuluntar da Elizabeth har sunyi aure sun bar garin. Basu fi wata biyar da barin garin ba, Alyasa'a ya amsa kiran Ubangiji, amma kin san wani abu, tsakanin ɗa da mahaifa, kamun Alyasa'a ya cika sai da ya furta kalmar yafiya ga mahaifinki. Wannan shine labarin sanadin barin gida da mahaifinki yayi." Sosai Sarah ke kuka kamar ranta zai bar jiinta. "Nnanne ina ji a jikina Babana ba'a cikin hayyacinsa yayi maku duk abinda yayi maku ba, ke da kanki kin ce baban mamana matsafine, kuma yayi alƙawarin cikawa mamana burinta domin ya baƙantawa mahaifiyar mamana, to wallahi zai iya komai daga ciki har da juya kwakwalwar mamana. Kuma jikina ya bani, shi ya mayar da soyayyar da Babana kewa Aunty Rose Merry izuwa kan mamana domin ya samu cikar burinsa, tunda tun farko ai Aunty Rose Merry ɗin Baba ke so ba Mamana ba. Nnanne akwai alamar tambaya akan wannan batu!" Shuru Nnanne tayi na wasu daƙiƙu tare da faɗin, "To, Allah masanin gaibu Saratu. Mahaifin mamanki ne kawai zai iya warware wannan ƙullin, idan shi sanadi ko bashi bane." Da sauri Sarah ta kalleta tare da faɗin, "Yana nan a raye ne?" Jinjina kai Nnanne tayi tare da faɗin, "daga Samuel har pasto Emanuella Debora suna nan a raye!" Dafa Nnanne tayi tare da faɗin, "Nnanne idan kinyi min lamuni, zan je gidan domin na gana dashi mahaifin maman nawa." Murmushi Nnanne tayi tare da faɗin, "Bashi kaɗai ba, har ita pasto ɗin zan so ki kai mata ziyara. Idan kin nutsu zuwa gobe, zan saka a kai ki. Idan zaki tafi, zan baki kuɗi sai ƴar wajen Lukman ta raka yi." Da sauri Sarah tace, "Nnanne Ina da isassun kuɗi, Khalil ya bani ATMCARD ɗinsa domin nayi amfani da kuɗin ciki idan buƙatar haka ta taso." "To ma sha Allah!" Faɗin Nnanne. Sarah kuma tashi tayi tare da faɗin, "Nnanne zan fita na ciro kuɗin yanzu nayi sayayyar, kin ga goben sai dai kawai mu wuce." Gyaɗa mata kai Nnanne tayi. A nan gaban ƙofar gidansu ta ciri dubu hamsin. Kuma a wannan lokacin ne Khalil yaga alert ɗin kuɗi ya shigo wayarsa wanda hakan ya nuna masa inda Sarah take. Washa gari tun ƙarfe goma Sarah ta saka Suhana a gaba akan ta tashi su tafi gidan Samuel. "Wai ke baki da kunya ko? Kakanki ne kike kiran sunansa gatsau haka? Kaka Samuel zaki ce!" Harara Sarah ta maka mata tare da faɗin, "Anƙi ace kakan, kako ba kaka. Kaji wani suna wai Samuel!" Ta ƙarisa maganar tare da bushewa da dariya. "Baki da kirki maman twins!" Faɗin Suhana tana ƙarisa sakawa Sam'an takalmi. "Wai auntyn Sam'an, dasu za muje?" Faɗin Sarah. Hannun Sam'an ɗin ta kama tare da faɗin, "Kwarai kuwa! Sauban muje kaji." Ta faɗi tana riƙe hannayensu. Komai Sarah bata ce ba har suka fito parlourn, matar ba Lukman suka samu a parlour, "Aunty zamu wuce!" Faɗin Sarah. "To Sarah, Kar dai a manta ayi addu'a, sannan idan sun baku nama, kar kuci." Da "To" suka amsa sannan suka fita daga ɗakin, sai da suka ƙara zuwa wajen Nnanne suka yi mata sallama sannan suka fito. Kasancewar babu nisa, a ƙafa suka yi ta takawa har suka gangara, sun zo wajen ƙofar gidan wani makeken gida wanda gaba ɗaya wanda shi ya haska unguwar, sai Suhana ta taɓo Sarah tare da faɗin, "Sis ga gidan kakarki, pasto Emanuella Debora." Ɗaga kai Sarah tayi, babu abunda idanunta suka fara ganin sai tafkeken sunanta a jikin saman gidan, _Pasto Emanuella Debora Gabriel House_. "Lallai matarnan taji kuɗi, duk wannan uban gidan nata ne?" Gyaɗa mata kai Suhana tayi tare da faɗin, "Kuma ƴata rak kawai gareta, Mahaifiyarki!" Taɓe baki Sarah tayi suka cigaba da tafiya har zuwa wani ƙaton ginin ƙasa, rabin katangar ta zube kana iya hango mutanan dake ciki, ga manya-manyan tukwane nan a kan murhun duwatsu har huɗu, gefe kuma ƴan matane su kusan bakwai da ɗaurin ƙirji, wasu kuma ɗan siketi ni iya ƙauri sai riga da bata gama rufe cibiya ba da uban kitson attachment har baya, farcen hannu zaƙo-zaƙo da ƙumba. Wasu tsoffi kuma zagaye a akan wani banci suna wani abun da su Sarah basu sani ba don basu iya hangowa. Can gefe kuma samarine da manyansu suna shan wani abu a kofi, wasu kuma suna buɗe wannan tukunyar suna ɗeban abun ciki suna sha. "Kin ga wancen abun da suke sha a kofi, sunansa burkutu." Faɗin Suhana. "Burkutu dai!" Sarah ta faɗi tana kallon Suhana, jinjina mata kai tayi daidai lokacin da suka iso ƙofar gidan. "Gafaranku dai!" Faɗin Suhana. Gaba ɗaya mutanan gidan suka zuba masu idanu, "Lafiya?" Wata budurwa mai ɗaurin ƙirji ta faɗi. "Mun zo wajen baba Samuel ne." Faɗin Suhana. Da hannu suka yi masu nuni da ɗakin, domin idan da sabo sun saba ganin musulmai suna zuwa gidan wajen baba Samuel domin yayi masu aikin asiri kasancewarsa shahararren matsafi. Daga asabarin dake ƙofar suka yi sannan suka shiga. Ɗagowa wani tsamurarren tsoho yayi tare da kallonsu, wani murmushi ya saki sannan ya nuna masu wajen zama tare da kallon Sarah yace mata, "Jikata, ƴa ga Elizabeth! Kin zo nan ne domin son sanin mahaifinki Nuhu yana cikin hayyacinsa ya ƙi bin umarnin Mahaifansa ya auri Elizabeth ko?" Da mugun mamaki Sarah ta kalli Suhan sannan ta mayar da kallonta izuwa ga Baba Samuel. Murmushi yayi tare da nuna mata tukunyar tsafin dake gabansa, sannan yace, "Duk wanda ya iso ƙofar gidana tukunyar tsafina take faɗa min zuwansa da kuma abunda ya kawosa gare ni. Ina ƴata Elizabeth?" Shuri Sarah tayi tana kallonsa, babu ta inda ta hango kamannin mamanta a jikin wannan yamutsatstsan tsohon, sai dai tabbas taga wani baƙin halitta dake cikin kwayan idanunsa wanda akwai shi sak a idanun Lami. Dariya Baba Samuel yayi mai sauti wanda ya saka Sarah saurin kallonsa ita da Suhana. "Tabbas hasashenki gaskiya ne! Ni na juya tunanin mahaifinki, sannan ni na sanya soyayyar ƙawar mahaifiyarki ya juye na mahaifiyarki a zuciyar babanki, Elizabeth bata taɓa son Nuhu ba, haka Nuhu bai taɓa son Elizabeth ba, nayi amfani da dutse ɗaya ne na jefi tsuntsu biyu, na haɗa wannan soyayyar ne domin in wulaƙanta tsohuwar matata pasto Emanuella Debora Gabriel, na biyu kuma domin in rama abunda mahaifin Rose Merry yayi min, kuma naji daɗi sosai saboda na rama komai cikin sauƙi." Ya ƙarisa maganar yana dariyar jin daɗi. Miƙewa Sarah tayi tare da kama hannun Suhan tace, "Tashi mu tafi Suhan, tsoro tsohon nan yake bani!" "Mijinki yana hanya, yanzu haka yana cikin unguwar nan yana cigiyar gidanku, sannan nan da wasu kwanaki masu zuwa, mijinki zai sake auren wata ƴarinya kyakkyawa wacce za tayi yunƙurin kwace maki fada a cikin gidanki, baza ku taɓa jituwa da ita ba, yarinya ce mai tsananin kishi, sannan uwar mijinki bata sonki yanzu, kuma akwai wani abun mamaki da zai faru kuma zai girgiza uwar miji kuma sannan........." "Muje Suhan!" Sarah ta faɗi da ƙarfi jikinta na rawa. Da sauri Suhan ɗin tayi gaba, yayin da Baba Samuel ya ɗaga murya tare da faɗin, "Idan kina neman wani taimako, kiyi gaggawan zuwa nan, cikin ƴan daƙiƙu zan gyara maki komai." ( _Mu haɗe tomorrow, walleh na gaji_) *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262* *_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_* _MATAR SAYYADEE_